The Old Testament of the Holy Bible

Farawa 1

Allah ya Halicci Duniya ya kuma Halicci Mutum

1 A sa'ad da Allah ya fara halittar Sama da duniya, 2 duniya ba ta da siffa, sarari ce kawai, duhu kuwa yana lulluɓe da fuskar zurfin teku, Ruhun Allah kuma yana shawagi bisa ruwayen. 3 Allah ya ce, “Bari haske ya kasance,” sai kuwa ya kasance. 4 Allah ya ga hasken yana da kyau. Allah ya raba tsakanin hasken da duhu, 5 ya ce da hasken, “Yini,” duhu kuwa, “Dare.” Ga maraice, ga safiya, kwana ɗaya ke nan. 6 Allah ya ce, “Bari sarari ya kasance tsakanin ruwaye, don ya raba tsakaninsu.” 7 Allah kuwa ya yi sarari, ya kuma raba tsakanin ruwayen da suke ƙarƙashin sararin da ruwayen da suke birbishin sararin. Haka nan kuwa ya kasance. 8 Allah ya ce da sarari, “Sararin sama.” Ga maraice, ga safiya, kwana na biyu ke nan. 9 Allah kuwa ya ce, “Bari ruwayen da suke ƙarƙashin sararin su tattaru wuri ɗaya, bari kuma sandararriyar ƙasa ta bayyana.” Haka nan kuwa ya kasance. 10 Allah ya ce da sandararriyar ƙasar, “Duniya,” tattaruwan ruwayen da aka tara kuwa, ya ce da su, “Tekuna.” Allah ya ga yana da kyau. 11 Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa ta fid da tsire-tsire, na masu ba da tsaba, da itatuwa masu ba da 'ya'ya, kowanne bisa ga nasa iri, waɗanda suke da 'ya'ya masu ƙwaya a cikinsu, waɗanda irinsa ke cikin duniya.” Haka nan kuwa ya kasance. 12 Ƙasa ta fid da tsire-tsire, na masu ba da 'ya'ya waɗanda suke da ƙwayar irinsu a cikinsu, Allah ya ga yana da kyau. 13 Ga maraice, ga safiya, kwana na uku ke nan. 14 Allah kuwa ya ce, “Bari haskoki su kasance a cikin sararin, su raba tsakanin yini da dare, su kuma zama alamu, da yanayi na shekara, da wokatai. 15 Bari kuma su zama haskoki a cikin sarari su haskaka duniya.” Haka nan kuwa ya kasance. 16 Allah kuwa ya yi manyan haskokin nan biyu, haske mafi girma ya mallaki yini, ƙaramin kuwa ya mallaki dare, ya kuma yi taurarin. 17 Allah ya sa su a cikin sarari su haskaka duniya, 18 su yi mulkin yini da kuma dare, su raba tsakanin haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau. 19 Ga maraice, ga safiya, kwana na huɗu ke nan. 20 Allah kuwa ya ce, “Bari ruwaye su fid da ɗumbun masu rai, bari tsuntsaye kuma su riƙa tashi bisa duniya ƙarƙashin sarari.” 21 Allah kuwa ya halicci manya manyan dodani na teku da kowane irin mai rai da yake motsi, waɗanda suke a cikin ruwaye, da kuma kowane irin tsuntsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau. 22 Sai Allah ya sa musu albarka, yana cewa, “Ku hayayyafa, ku kuma riɓaɓɓanya, ku cika ruwayen tekuna, tsuntsaye kuma ku hayayyafa cikin duniya.” 23 Ga maraice, ga safiya, kwana na biyar ke nan. 24 Allah kuwa ya ce, “Bari duniya ta fid da masu rai bisa ga irinsu, shanu, da abubuwa masu rarrafe, da dabbobin duniya bisa ga irinsu.” 25 Allah kuwa ya yi dabbobin gida bisa ga irinsu, da kuma na jeji, manya da ƙanana, da kowane irin mai rarrafe bisa ƙasa bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau. 26 Allah kuma ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, da kamanninmu, su mallaki kifayen da suke a cikin teku, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobi, da dukan duniya, da kowane abu mai rarrafe da yake rarrafe bisa ƙasa.” 27 Haka nan fa, Allah ya halicci mutum cikin siffarsa, cikin siffar Allah, Allah ya halicci mutum, namiji da ta mace ya halicce su. 28 Allah kuwa ya sa musu albarka, ya ce musu, “Ku hayayyafa ku riɓaɓɓanya, ku cika duniya, ku yi iko da ita, ku mallaki kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma dukan abin da yake da rai da yake kai da kawowa cikin duniya.” 29 Allah kuwa ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da tsaba da yake bisa fuskar dukan duniya, da kowane itace da yake da ƙwaya cikin 'ya'yansa su zama abincinku. 30 Na ba da kowane irin ɗanyen tsiro domin ci, ga kowace irin dabba da take duniya, da kowane irin tsuntsu da yake sararin sama, da kowane irin abin da yake rarrafe bisa duniya, da dai iyakar abin da yake numfashi.” Haka nan ya kasance. 31 Allah kuwa ya ga dukan abin da ya yi, ga shi kuwa yana da kyau ƙwarai. Ga maraice, ga safiya, kwana na shida ke nan.

Farawa 2

1 Da haka aka gama yin sama da duniya, da rundunansu. 2 A kwana na bakwai Allah ya gama aikinsa wanda ya yi. Ya kuwa huta a kan kwana na bakwai daga dukan aikinsa da ya yi. 3 Domin haka Allah ya sa wa kwana na bakwai albarka, ya tsarkake shi, don a cikinsa Allah ya huta daga dukan aikin da ya yi na halitta. 4 Waɗannan su ne asalin sama da duniya sa'ad da aka halicce su. A ranar da Ubangiji Allah ya yi duniya da sama, 5 a sa'an nan ba tsire-tsiren saura a duniya, ƙananan ganyayen saura kuma ba su riga sun tsiro ba, gama Ubangiji Allah bai sa a yi ruwa bisa duniya ba tukuna. A lokacin kuwa babu wani wanda zai noma ƙasar, 6 amma sai ƙāsashi yake tasowa daga ƙasa ya shayar da fuskar ƙasa duka. 7 Sa'an nan Ubangiji Allah ya siffata mutum daga turɓayar ƙasa, a cikin kafafen hancinsa kuwa ya hura numfashin rai, mutum kuma ya zama rayayyen taliki.

Gonar Aidan

8 Ubangiji Allah kuwa ya dasa gona a Aidan, wajen gabas, a can ya sa mutumin da ya siffata. 9 Ubangiji Allah ya sa kowane itace mai kyan gani, mai amfani domin abinci, ya tsiro, itacen rai kuwa yana tsakiyar gonar, da kuma itacen sanin nagarta da mugunta. 10 Wani kogi kuma ya malalo daga Aidan ya shayar da gonar, daga nan kuwa ya rarrabu ya zama kogi huɗu. 11 Sunan na fari Fishon, shi ne yake malala kewaye da dukan ƙasar Hawila, inda akwai zinariya. 12 Zinariyar ƙasar nan kuwa kyakkyawa ce. Akwai kuma duwatsu masu daraja a wurin. 13 Sunan kogi na biyu Gihon, shi ne wanda yake malala kewaye da ƙasar Kush. 14 Sunan kogi na uku Taigiris ne, wanda yake malala gabashin Assuriya. Kogi na huɗu kuwa Yufiretis ne. 15 Ubangiji Allah ya ɗauki mutumin ya zaunar da shi cikin gonar Aidan ya noma ta, ya kiyaye ta. 16 Ubangiji Allah ya yi wa mutumin umarni, ya ce, “Kana da 'yanci ka ci daga kowane itace da yake a gonar, 17 amma daga itacen sanin nagarta da mugunta ba za ka ci ba, gama a ranar da ka ci shi za ka mutu lalle.” 18 Sa'an nan sai Ubangiji Allah ya ce, “Bai kyautu mutumin ya zauna shi kaɗai ba, zan yi masa mataimakin da ya dace da shi.” 19 Haka nan fa, daga cikin ƙasar, Ubangiji ya siffata kowace dabba ta cikin saura da kowane tsuntu na sararin sama, ya kawo su wurin mutumin, ya ga yadda zai kiraye su, duk abin da mutumin ya kirayi mai ran kuwa, sunansa ke nan. 20 Mutumin ya bai wa dabbobi duka suna, da tsuntsayen sararin sama, da kowace irin dabba da take cikin saura, amma ba a sami mataimaki wanda ya dace da mutumin ba. 21 Sai Ubangiji Allah ya sa barci mai nauyi ya kwashe mutumin. Lokacin da yake barci Ubangiji Allah ya cire ɗaya daga cikin haƙarƙarinsa ya cike wurin da nama, 22 haƙarƙarin nan kuwa da Ubangiji Allah ya cire daga mutumin ya yi mace da shi, ya kuwa kawo ta ga mutumin. 23 Sai mutumin ya ce, “Yanzu dai wannan ƙashi ne daga ƙasusuwana, nama ne kuwa daga namana, za a kira ta mace, don daga cikin mutum aka ciro ta.” 24 Domin haka mutum yakan rabu da mahaifinsa da mahaifiyarsa ya kuwa manne wa matarsa, sun zama ɗaya. 25 Da mutumin da matarsa dukansu biyu a tsiraice suke, ba su kuwa ji kunya ba.

Farawa 3

Faɗuwar Mutum

1 Maciji ya fi kowace dabba da Ubangiji Allah ya yi wayo. Ya ce wa matar, “Ko Allah ya ce, ‘Ba za ku ci daga wani itace da yake a gonar ba?’ ” 2 Sai matar ta ce wa macijin, “Mā iya ci daga cikin itatuwan gonar, 3 amma Allah ya ce, ‘Ba za ku ci daga cikin 'ya'yan itacen da yake tsakiyar gonar ba, ba za ku taɓa shi ba, don kada ku mutu.’ ” 4 Amma macijin ya ce wa matar, “Hakika ba za ku mutu ba. 5 Gama Allah ya sani a ranar da kuka ci daga itacen nan idanunku za su buɗe, za ku kuwa zama kamar Allah, ku san nagarta da mugunta.” 6 Matar ta ga yadda itacen yana da kyau, 'ya'yansa kuma kyawawa, abin sha'awa ne kuma ga ido, abin marmari ne domin ba da hikima, ta tsinka daga 'ya'yansa, ta kuwa ci, ta kuma bai wa mijinta waɗansu, shi kuma ya ci. 7 Sai dukansu biyu idanunsu suka buɗe, sa'an nan suka gane tsirara suke, sai suka samo ganyayen ɓaure suka ɗinɗinka suka yi wa kansu sutura. 8 Da suka ji motsin Allah yana yawo a gonar da sanyin la'asariya, sai mutumin da matarsa suka ɓuya wa Ubangiji Allah cikin itatuwan gonar. 9 Amma Ubangiji Allah ya kira mutumin, ya ce, “Ina kake?” 10 Sai ya ce, “Na ji motsinka cikin gonar, na kuwa ji tsoro, domin tsirara nake, na kuwa ɓoye kaina.” 11 Ya ce, “Wa ya faɗa maka tsirara kake? Ko ka ci daga cikin itacen da na ce kada ka ci ne?” 12 Mutumin ya ce, “Matar nan da ka ba ni, ita ce ta ba ni 'ya'yan itacen, na kuwa ci.” 13 Ubangiji Allah kuma ya ce wa matar, “Mene ne wannan da kika yi?” Matar ta ce, “Macijin ne ya yaudare ni, na kuwa ci.” 14 Ubangiji Allah ya ce wa maciji, “Tun da ka aikata wannan, za a hukunta ka. Kai kaɗai wannan la'ana za ta bi. Daga yanzu rubda ciki za ka yi tafiya, turɓaya za ka ci muddin rayuwarka. 15 Zan sa ƙiyayya tsakaninka da matar, tsakanin zuriyarka da zuriyarta, shi zai ƙuje kanka, kai za ka ƙuje diddigensa.” 16 Ga matar kuwa ya ce, “Zan tsananta naƙudarki ainun, da azaba za ki haifi 'ya'ya, duk da haka muradinki zai koma ga mijinki, zai kuwa mallake ki.” 17 Ga Adamu kuwa ya ce, “Ka kasa kunne ga muryar matarka, har ka ci daga 'ya'yan itacen da na dokace ka, ‘Kada ka ci daga cikinsu.’ Tun da ka aikata wannan za a la'antar da ƙasa saboda kai, da wahala za ka ci daga cikinta muddin rayuwarka. 18 “Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za ta ba ka, za ka kuwa ci ganyayen saurar. 19 Za ka yi zuffa da aiki tuƙuru kafin ka sami abinci, har ka koma ƙasa, gama da ita aka siffata ka, kai turɓaya ne, ga turɓaya kuma za ka koma.” 20 Mutumin ya sa wa matarsa suna Hawwa'u, domin ita ce uwar 'yan adam. 21 Ubangiji Allah kuwa ya yi wa mutumin da matarsa tufafi na fata, ya suturce su.

An Fitar da Adamu da Hawwa'u daga Gonar

22 Sa'an nan Ubangiji Allah ya ce, “Ga shi, mutum ya zama kamar ɗaya daga cikinmu, ya san nagarta da mugunta, yanzu fa, kada ya miƙa hannunsa ya ɗiba daga cikin itacen rai ɗin nan, ya ci, ya rayu har abada.” 23 Domin haka Ubangiji Allah ya fisshe shi daga cikin gonar Aidan, ya noma ƙasa, wato, inda aka ɗauko shi. 24 Ya kori mutum kuma a gabashin gonar Aidan, ya kafa kerubobi, da kuma takobi mai harshen wuta wanda yake jujjuyawa ko'ina don su tsare hanya zuwa itacen rai.

Farawa 4

Kayinu da Habila

1 Adamu kuwa ya san matarsa Hawwa'u, ta kuwa yi ciki, ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Na sami ɗa namiji da iznin Ubangiji.” 2 Ta kuma haifi ɗan'uwansa Habila. Habila makiyayin tumaki ne, Kayinu kuwa manomi ne. 3 Wata rana, sai Kayinu ya kawo sadaka ga Ubangiji daga amfanin gona. 4 Habila kuwa ya kawo nasa ƙosassu daga cikin 'ya'yan fari na garkensa. Ubangiji kuwa ya kula da Habila da sadakarsa, 5 amma Kayinu da sadakarsa, bai kula da su ba. Saboda haka Kayinu ya husata ƙwarai, har ya kwantsare fuskarsa. 6 Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Me ya sa ka husata, me kuma ya sa har fuskarka ya kwantsare? 7 In da ka yi daidai, ai, da ka yi murmushi. Amma tun da ka yi mugunta, to, zunubi zai yi fakonka don ya rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so ya mallake ka, amma tilas ne ka rinjaye shi.” 8 Kayinu ya ce wa ɗan'uwansa Habila, “Mu tafi cikin saura.” A lokacin da suke cikin saura, sai Kayinu ya tasar wa ɗan'uwansa Habila, har ya kashe shi. 9 Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina Habila ɗan'uwanka?” Ya ce, “Ban sani ba, ni makiyayin ɗan'uwana ne?” 10 Sai Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Muryar jinin ɗan'uwanka tana yi mini kuka daga ƙasa. 11 Yanzu fa, kai la'ananne ne daga cikin ƙasar da ta buɗe baki, ta karɓi jinin ɗan'uwanka daga hannunka. 12 In ka yi noma, ƙasar ba za ta ƙara ba ka cikakken amfaninta ba, za ka zama mai yawo barkatai, mai kai da kawowa a duniya.” 13 Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Hukuncina ya fi ƙarfina. 14 Ga shi, yanzu ka kore ni a guje daga fuskar ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, mai kai da kawowa a duniya, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.” 15 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Wanda duk ya kashe Kayinu, za a rama masa har sau bakwai.” Ubangiji kuma ya sa wa Kayinu tabo, domin duk wanda ya iske shi kada ya kashe shi. 16 Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya zauna a ƙasar Nod, gabashin Aidan.

Zuriyar Kayinu

17 Kayinu ya san matarsa, ta kuwa yi ciki ta haifi Anuhu, ya kuwa gina birni ya sa wa birnin sunan ɗansa, Anuhu. 18 An haifa wa Anuhu ɗa, wato, Airad. Airad ya haifi Mehuyayel, Mehuyayel kuwa ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifi Lamek. 19 Lamek ya auri mata biyu, sunan ɗayar Ada, ta biyun kuwa Zulai. 20 Ada ta haifi Yabal, shi ne ya zama uban mazaunan alfarwa, makiyayan dabbobi. 21 Sunan ɗan'uwansa Yubal, wanda ya zama uban makaɗan garaya da mabusan sarewa. 22 Zulai kuwa ta haifi Tubal-kayinu, shi ne asalin maƙeran dukan kayayyakin tagulla da na baƙin ƙarfe. Sunan 'yar'uwar Tubal-kayinu Na'ama ne. 23 Lamek kuwa ya ce wa matansa, “Ada da Zulai, ku ji muryata, ku matan Lamek ku ji abin da nake cewa, na kashe mutum domin ya yi mini rauni, saurayi kuma don ya buge ni. 24 Idan an rama wa Kayinu sau bakwai, hakika na Lamek, sai sau saba'in da bakwai.”

Zuriyar Shitu

25 Sai kuma Adamu ya san matarsa, ta kuwa haifi ɗa, ta raɗa masa suna Shitu, gama ta ce, “Allah ya arzuta ni da ɗa maimakon Habila wanda Kayinu ya kashe.” 26 Ga Shitu kuma aka haifi ɗa, ya kuwa raɗa masa suna Enosh. A wannan lokaci ne mutane suka fara kira bisa sunan Ubangiji.

Farawa 5

Zuriyar Adamu

1 Wannan shi ne littafin asalin Adamu. A sa'ad da Allah ya halicci mutum, ya yi shi cikin siffar Allah. 2 Namiji da ta mace ya halicce su, ya sa musu albarka, ya sa musu suna, Mutum, sa'ad da aka halicce su. 3 Da Adamu ya yi shekara ɗari da talatin, ya haifi ɗa cikin kamanninsa da cikin siffarsa, ya kuwa sa masa suna Shitu. 4 Bayan da Adamu ya haifi ɗansa Shitu, ya yi shekara ɗari takwas, sa'an nan ya haifi 'ya'ya mata da maza. 5 Haka nan kuwa dukan kwanakin Adamu shekara ce ɗari tara da talatin, ya rasu. 6 Da Shitu ya yi shekara ɗari da biyar, ya haifi Enosh. 7 Bayan da Shitu ya haifi Enosh ya rayu shekara ɗari takwas da bakwai, ya haifi 'ya'ya mata da maza. 8 Haka nan kuwa dukan kwanakin Shitu shekara ce ɗari tara da goma sha biyu, ya rasu. 9 Da Enosh ya yi shekara tasa'in, ya haifi Kenan. 10 Bayan Enosh ya haifi Kenan ya rayu shekara ɗari takwas da goma sha biyar, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 11 Haka nan kuwa dukan kwanakin Enosh shekara ce ɗari tara da biyar, ya rasu. 12 Sa'ad da Kenan ya yi shekara saba'in, ya haifi Mahalalel. 13 Bayan da Kenan ya haifi Mahalalel ya yi shekara ɗari takwas da arba'in, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 14 Haka nan kuwa dukan kwanakin Kenan shekara ce ɗari tara da goma, ya rasu. 15 Sa'ad da Mahalalel ya yi shekara sittin da biyar ya haifi Yared. 16 Bayan da Mahalalel ya haifi Yared, ya yi shekara ɗari takwas da talatin, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 17 Haka nan kuwa dukan kwanakin Mahalalel shekara ce ɗari takwas da tasa'in da biyar, ya rasu. 18 Sa'ad da Yared ya yi shekara ɗari da sittin da biyu, ya haifi Anuhu. 19 Bayan da Yared ya haifi Anuhu ya yi shekara ɗari takwas ya haifi 'ya'ya mata da maza. 20 Haka nan kuwa dukan kwanakin Yared shekara ce ɗari tara da sittin da biyu, ya rasu. 21 Sa'ad da Anuhu ya yi shekara sittin da biyar, ya haifi Metusela. 22 Bayan da Anuhu ya haifi Metusela, ya yi tafiya tare da Allah shekara ɗari uku ya haifi 'ya'ya mata da maza. 23 Haka nan kuwa dukan kwanakin Anuhu shekara ce ɗari uku da sittin da biyar. 24 Anuhu ya yi tafiya tare da Allah, Allah kuwa ya ɗauke shi, ba a ƙara ganinsa ba. 25 Sa'ad da Metusela ya yi shekara ɗari da tamanin da bakwai, ya haifi Lamek. 26 Bayan da Metusela ya haifi Lamek ya yi shekara ɗari bakwai da tamanin da biyu, ya haifi 'ya'ya mata da maza. 27 Haka nan kuwa dukan kwanakin Metusela shekara ce ɗari tara da sittin da tara, ya rasu. 28 Sa'ad da Lamek ya yi shekara ɗari da tamanin da biyu, ya haifi ɗa, 29 ya sa masa suna Nuhu, yana cewa, “Daga gare shi za mu sami sauƙin aikinmu da wahalar hannuwanmu a ƙasar da Ubangiji ya la'anta.” 30 Bayan da Lamek ya haifi Nuhu ya yi shekara ɗari biyar da tasa'in da biyar, ya haifi 'ya'ya mata da maza. 31 Haka nan kuwa dukan kwanakin Lamek shekara ce ɗari bakwai da saba'in da bakwai, ya rasu. 32 Sa'ad da Nuhu ya yi shekara ɗari biyar, ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.

Farawa 6

Muguntar 'Yan Adam

1 Da mutane suka fara yawaita a duniya suka kuwa haifi 'ya'ya mata, 2 sai 'ya'yan Allah suka ga 'yan matan mutane kyawawa ne, suka zaɓi waɗanda suke so, suka aura. 3 Sai Ubangiji ya ce, “Numfashina ba zai zauna cikin mutum har abada ba, gama shi mai mutuwa ne. Nan gaba kwanakinsa ba zai ɗara shekara ɗari da ashirin ba.” 4 A waɗannan kwanaki kuwa, 'ya'yan Allah suka shiga wurin 'yan matan mutane, suka kuwa haifa musu 'ya'ya. Su ne manya manyan mutanen dā, shahararru. 5 Ubangiji kuwa ya ga muguntar mutum ta ƙasaita a duniya, dukan zace-zacen tunanin zuciyarsa kuma mugunta ne kullayaumin. 6 Ubangiji ya damu da ya yi mutum a duniya, abin ya ɓata masa zuciya ƙwarai. 7 Sai Ubangiji ya ce, “Zan shafe mutum daga duniya, mutum da dabba, da masu rarrafe, da tsuntsayen sararin sama, gama na damu da na halicce su.” 8 Amma Nuhu ya sami tagomashi a gaban Ubangiji. 9 Waɗannan su ne zuriyar Nuhu. Nuhu adali ne, salihi ne kuma a cikin zamaninsa. Nuhu ya yi tafiya tare da Allah. 10 Nuhu kuwa ya haifi 'ya'ya uku, Shem, da Ham, da Yafet. 11 Amma dukan sauran mutane mugaye ne a gaban Allah, muguntarsu kuwa ta bazu ko'ina. 12 Allah ya dubi duniya, ga shi kuwa ta ɓaci, gama dukan mutane sun lalatar da tafarkunsu a cikin duniya.

Nuhu ya Sassaƙa Jirgi

13 Allah ya ce wa Nuhu, “Na riga na yi niyyar hallaka dukan talikai, gama duniya tana cike da ayyukansu na zunubi. 14 Ka sassaƙa wa kanka jirgi na itacen gofer, ka yi ɗakuna a cikin jirgin, ka dalaye cikinsa da bayansa da ƙaro. 15 Ga yadda za ka sassaƙa shi, tsawon jirgin ƙafa ɗari huɗu da hamsin, faɗinsa ƙafa saba'in da biyar, tsayinsa ƙafa arba'in da biyar. 16 Ka yi wa jirgin rufe, ka bar inci goma sha takwas tsakanin rufin da gyaffansa. Ka yi shi hawa uku, ka yi ƙofa a gefe. 17 Gama ga shi, zan kawo rigyawa bisa duniya, ta hallaka dukan mai numfashin rai da yake ƙarƙashin sama, dukan abin da yake a duniya zai mutu. 18 Amma ni zan kafa alkawari tsakanina da kai, za ka shiga cikin jirgin, kai da 'ya'yanka, da matarka, da matan 'ya'yanka tare da kai. 19 Daga kowane irin mai rai kuma za ka shigar da biyu biyu a cikin jirgin, domin su rayu tare da kai, amma su kasance namiji da ta mace. 20 Tsuntsaye bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kowane irin mai rarrafe a ƙasa bisa ga irinsa, biyu biyu na kowane iri za su shiga tare da kai, su rayu. 21 Ka ɗauki kuma kowane irin abinci da ake ci, ka tanada, zai kuwa zama abincinka da nasu.” 22 Nuhu ya yi dukan abin da Allah ya umarce shi.

Farawa 7

Ruwan Tsufana

1 Sai Ubangiji ya ce wa Nuhu, “Ka shiga jirgin, kai da iyalinka duka, gama na ga a wannan zamani, kai adali ne a gare ni. 2 Daga cikin dabbobi masu tsarki ka ɗauki bakwai bakwai, namiji da ta mace, marasa tsarki kuwa namiji da ta mace, 3 da kuma tsuntsayen sararin sama bakwai bakwai, namiji da ta mace, domin a wanzar da irinsu a duniya duka. 4 Gama da sauran kwana bakwai kāna in sa a yi ruwa a duniya yini arba'in da dare arba'in. Dukan abu mai rai wanda na yi zan shafe shi daga duniya.” 5 Nuhu kuwa ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarce shi. 6 Nuhu yana da shekara ɗari shida lokacin da Ruwan Tsufana ya kwararo bisa duniya. 7 Nuhu da 'ya'yansa da matarsa, da matan 'ya'yansa tare da shi suka shiga jirgi, domin su tsira daga Ruwan Tsufana. 8 Daga dabbobi masu tsabta da marasa tsabta, da na tsuntsaye, da na kowane mai rarrafe a ƙasa, 9 biyu biyu, namiji da mata, suka shiga jirgi tare da Nuhu, kamar yadda Allah ya umarci Nuhu. 10 Sai bayan kwana bakwai ruwayen suka kwararo bisa duniya. 11 A ranar sha bakwai ga wata na biyu, na shekara ta ɗari shida na rayuwar Nuhu, a ran nan sai dukan maɓuɓɓugai na manyan zurfafa suka fashe, tagogin sammai suka buɗe. 12 Ruwa yana ta kwararowa bisa duniya yini arba'in da dare arba'in. 13 A wannan rana Nuhu da 'ya'yansa, Shem, da Ham, da Yafet, da matar Nuhu da matan 'ya'yansa tare suka shiga jirgin, 14 su da kowace dabbar jeji bisa ga irinta, da dukan dabbobin gida bisa ga irinsu, da kowane mai rarrafe wanda yake rarrafe bisa ƙasa, bisa ga irinsa, da kowane tsuntsun gida da na jeji wanda yake numfashi. waɗanda suka shiga, namiji ne da ta mace na kowane taliki, suka shiga jirgin kamar yadda Allah ya umarce shi. Sai Ubangiji ya kulle jirgi daga baya. 17 Aka yi ta kwararo ruwa bisa duniya har kwana arba'in, ruwayen kuwa suka ƙaru, har suka ɗaga jirgin sama, ya kuwa tashi can ƙoli birbishin duniya. 18 Ruwa ya bunƙasa ya ƙaru ƙwarai bisa duniya, jirgin kuwa ya yi ta yawo bisa fuskar ruwaye. 19 Ruwa kuwa ya bunƙasa ainun a bisa duniya, har ya rufe kawunan dukan duwatsu masu tsayi da suke ƙarƙashin sammai duka. 20 Ruwa ya bunƙasa bisa duwatsu ya yi musu zara da ƙafa ashirin da biyar. 21 Duk taliki wanda yake motsi bisa duniya ya mutu, da tsuntsaye, da dabbobin gida, da na jeji, da dukan masu rarrafe waɗanda suke rarrafe bisa duniya, da kowane mutum, 22 da kowane abu da yake bisa sandararriyar ƙasa wanda yake da numfashin rai cikin kafafen hancinsa ya mutu. 23 Ubangiji ya shafe kowane mai rai wanda yake bisa ƙasa, da mutum, da dabba, da masu rarrafe, da tsuntsayen sararin sama, an shafe su daga duniya. Nuhu kaɗai aka bari, da waɗanda suke tare da shi cikin jirgi. 24 Ruwa kuma ya mamaye duniya har kwana ɗari da hamsin.

Farawa 8

Ƙarshen Ruwan Tsufana

1 Allah kuwa ya tuna da Nuhu da dukan dabbobin gida da na jeji waɗanda suke cikin jirgi tare da shi. Allah ya sa iska ta hura bisa duniya, ruwaye suka janye. 2 Maɓuɓɓugan zurfafa da tagogin sammai suka rufe, aka dakatar da ruwa daga sammai, 3 ruwa ya yi ta janyewa daga duniya. Bayan kwana ɗari da hamsin sai ruwa ya ragu. 4 Ya zama kuwa a ran sha bakwai ga wata na bakwai, sai jirgin ya tafi ya tsaya bisa kan dutsen Ararat. 5 Ruwa ya yi ta raguwa har wata na goma. A ran ɗaya ga wata na goma, sai kawunan duwatsu suka ɓullo. 6 A ƙarshen kwana arba'in Nuhu ya buɗe tagar jirgin da ya yi, 7 sai ya saki hankaka. Hankaka ya yi ta kai da kawowa har lokacin da ruwan ya ƙafe a duniya. 8 Sai kuma ya aiki kurciya ta gani ko ruwa ya janye, 9 amma kurciyar ba ta sami inda za ta sauka ba, sai ta komo wurinsa cikin jirgi, gama har yanzu ruwa na rufe ƙasa duka. Sai ya miƙa hannunsa ya ɗauko ta ya shigar da ita cikin jirgi tare da shi. 10 Ya jira kuma har kwana bakwai, sai kuma ya sāke aiken kurciyar daga cikin jirgin. 11 Kurciyar kuwa ta komo wurinsa da maraice, ga shi kuwa, a bakinta sabon tohon zaitun wanda ta tsinko, domin haka Nuhu ya gane ruwa ya janye daga duniya. 12 Sai ya sāke dakatawa har kwana bakwai, ya kuma aiki kurciya, amma ba ta ƙara komowa wurinsa ba. 13 A rana ta fari ga wata na fari na shekara ta ɗari shida da ɗaya na Nuhu, ruwa ya ƙafe a duniya. Sai Nuhu ya buɗe murfin jirgin, ya duba, sai ga ƙasa busasshiya. 14 Ran ashirin da bakwai ga wata na biyu, duniya ta bushe. 15 Sa'an nan sai Allah ya ce wa Nuhu, 16 “Fito daga cikin jirgi, kai da matarka, da 'ya'yanka da matan 'ya'yanka tare da kai. 17 Ka fito da kowane abu mai rai tare da kai, dukan talikai, wato, tsuntsaye, da dabbobi, da kowane abu mai rarrafe da yake rarrafe bisa ƙasa, domin su hayayyafa su kuma riɓaɓɓanya a duniya.” 18 Sai Nuhu ya fito, da 'ya'yansa, da matarsa da matan 'ya'yansa tare da shi, 19 da kowace irin dabba, da kowane mai rarrafe, da kowane irin tsuntsu, da kowane irin abu da yake motsi a bisa duniya, suka fito daga jirgi ɗaki ɗaki bisa ga irinsu.

Nuhu ya Miƙa Hadaya

20 Nuhu ya gina wa Ubangiji bagade, ya ɗiba daga cikin kowace irin dabba mai tsarki, da kowane tsuntsu mai tsarki, ya miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden. 21 Sa'ad da Ubangiji ya ji ƙanshi mai daɗi, sai ya ce, “Ba zan ƙara la'anta ƙasa sabili da mutum ba, ko da yake zace-zacen zuciyar mutum mugunta ne tun daga ƙuruciyarsa. Ba zan kuma ƙara hallaka kowane mai rai ba kamar yadda na yi a dā. 22 Muddin duniya tana nan, lokacin shuka da lokacin girbi, damuna da rani, yini da dare, ba za su daina ba.”

Farawa 9

Allah ya Yi Alkawari da Nuhu

1 Allah kuwa ya sa wa Nuhu da 'ya'yansa albarka, ya ce musu, “Ku yi 'ya'ya ku hayayyafa, ku cika duniya. 2 Kowace dabba ta duniya, da kowane tsuntsu na sararin sama, da kowane mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifaye na teku, za su riƙa jin tsoronku suna fargaba. An ba da su a hannunku. 3 Kowane abu mai motsi wanda yake da rai, zai zama abincinku. Daidai kamar yadda na ba ku ɗanyun ganyaye, na ba ku kome da kome. 4 Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, shi ne naman da jininsa yake cikinsa, wato, mushe. 5 Idan wani ya kashe ka zan hukunta shi da mutuwa. Zan kashe dabbar da za ta kashe ka, zan hukunta duk wanda ya kashe mutum ɗan'uwansa. 6 “Duk wanda ya kashe mutum, ta hannun mutum za a kashe shi, gama Allah ya yi mutum cikin siffarsa. 7 Amma ku, ku yi 'ya'ya ku hayayyafa, ku riɓaɓɓanya a duniya ku yawaita a cikinta.” 8 Allah kuwa ya ce wa Nuhu da 'ya'yansa. 9 “Ga shi, na kafa alkawari tsakanina da ku da zuriyarku a bayanku, 10 da kowane mai rai da yake tare da ku, da tsuntsaye, da dabbobin gida da na jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin, kowane mai rai na duniya. 11 Na kafa alkawarina da ku. Daɗai ba za a ƙara hallaka talikai duka da ruwa ba, ba kuma za a ƙara yin Ruwan Tsufana da zai hallaka duniya ba.” 12 Allah ya ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da yake tsakanina da ku, da kowane mai rai da yake tare da ku, har dukan zamanai masu zuwa, 13 na sa bakana cikin girgije, ya zama alamar alkawari tsakanina da duniya. 14 Sa'ad da na kawo gizagizai bisa duniya, aka ga bakan a cikin gizagizai, 15 zan tuna da alkawarin da yake tsakanina da ku, da kowane mai rai da dukan talikai. Ruwa kuma ba zai ƙara yin rigyawar da za ta hallaka talikai duka ba. 16 Sa'ad da bakan yake cikin girgije zan dube shi, in tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da kowane mai rai da dukan talikan da yake bisa duniya.” 17 Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawari wanda na kafa tsakanina da dukan talikan da suke bisa duniya.”

Nuhu da 'Ya'yansa Maza

18 'Ya'yan Nuhu waɗanda suka fito daga jirgi su ne Shem, da Ham, da Yafet. Ham shi ne mahaifin Kan'ana. 19 Su uku ɗin nan su ne 'ya'yan Nuhu, daga gare su duniya za ta cika da mutane. 20 Nuhu shi ya fara noma, ya yi gonar inabi. 21 Ya sha daga cikin ruwan inabin ya kuwa bugu, ya kwanta tsirara a cikin alfarwarsa. 22 Sai Ham, mahaifin Kan'ana, ya ga tsiraicin mahaifinsa, ya faɗa wa 'yan'uwansa biyu waɗanda suke waje. 23 Sai Shem da Yafet suka ɗauki riga, suka ɗibiya bisa kafaɗunsu, suka yi tafiya da baya da baya suka rufa tsiraicin mahaifinsu, suka juya fuskokinsu, ba su kuwa ga tsiraicin mahaifinsu ba. 24 Sa'ad da ruwan inabin ya sau Nuhu, ya san abin da ƙaramin ɗansa ya yi masa. 25 Sai ya ce, “La'ananne ne Kan'ana, bawan bayi zai zama ga 'yan'uwansa.” 26 Ya kuma ce, “Bari Ubangiji Allahna, ya sa wa Shem albarka, Kan'ana kuwa ya bauta masa. 27 Allah ya sa Yafet ya yawaita, ya sa ya zauna a alfarwan Shem, Kan'ana kuwa ya bauta masa.” 28 Bayan Ruwan Tsufana, Nuhu ya yi shekara ɗari uku da hamsin. 29 Shekarun Nuhu duka ɗari tara da hamsin ne, ya rasu.

Farawa 10

Zuriyar 'Ya'yan Nuhu, Maza

1 Waɗannan su ne zuriyar 'ya'yan Nuhu, da Shem, da Ham, da Yafet. Bayan Ruwan Tsufana sai aka haifa musu 'ya'ya. 2 'Ya'yan Yafet ke nan, da Gomer, da Magog, da Madai, da Yawan, da Tubal, da Meshek, da Tiras. 3 'Ya'yan Gomer kuma Ashkenaz, da Rifat, da Togarma. 4 'Ya'yan Yawan kuma Elisha, da Tarshish, da Kittim, da Rodanim. 5 Daga waɗannan ne mazauna a bakin gāɓa suka yaɗu bisa ga ƙasashensu, kowanne da harshensa, bisa ga iyalansu da kabilansu. 6 'Ya'yan Ham su ne Kush, da Mizrayim, da Fut, da Kan'ana. 7 'Ya'yan Kush kuma Seba, da Hawila, da Sabta, da Ra'ama, da Sabteka. 'Ya'yan Ra'ama kuwa Sheba da Dedan. 8 Kush ya haifi Lamirudu, shi ne mutumin da ya fara ƙasaita cikin duniya. 9 Shi riƙaƙƙen maharbi ne a gaban Ubangiji, domin haka akan ce, “Shi kamar Lamirudu ne riƙaƙƙen maharbi ne a gaban Ubangiji.” 10 Farkon inda ya kafa mulkinsa a Babila, da Erek, da Akkad, da Kalne ne, dukansu a ƙasar Shinar suke. 11 Daga wannan ƙasa ya tafi Assuriya ya gina Nineba da Rehobot-ir, da Kala, 12 da Resen wadda take tsakanin Nineba da Kala, wato, babban birni. 13 Mizrayim shi ne mahaifin Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Neftuhawa, 14 da Fatrusawa, da Kasluhawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa. 15 Kan'ana ya haifi Sidon ɗan farinsa, da Het, 16 shi ne kuma mahaifin Yebusiyawa, da Amoriyawa, da Girgashiyawa, 17 da Hiwiyawa, da Arkiyawa, da Siniyawa, 18 da Arwadiyawa, da Zemarawa da Hamatiyawa. Bayan haka sai kabilan Kan'aniyawa suka yaɗu. 19 Yankin ƙasar Kan'aniyawa kuwa ya milla tun daga Sidon, har zuwa wajen Gerar, har zuwa Gaza, zuwa wajen Saduma, da Gwamrata, da Adma, da Zeboyim, har zuwa Lasha. 20 Waɗannan su ne 'ya'yan Ham, bisa ga iyalansu, da harsunansu da ƙasashensu, da kabilansu. 21 An kuma haifa wa Shem, wan Yafet, 'ya'ya, shi ne kakan 'ya'yan Eber duka. 22 'Ya'yan Shem su ne Elam, da Asshur, da Arfakshad, da Lud, da Aram. 23 'Ya'yan Aram kuma Uz, da Hul, da Geter, da Meshek. 24 Arfakshad ya haifi Shela, Shela ya haifi Eber. 25 An haifa wa Eber 'ya'ya biyu, sunan ɗayan Feleg, gama a zamaninsa aka raba ƙasa, sunan ɗan'uwansa kuwa Yokatan. 26 Yokatan ya haifi Almoda, da Shelef, da Hazarmawet, da Yera, 27 da Adoniram, da Uzal, da Dikla, 28 da Ebal, da Abimayel, da Sheba, 29 da Ofir, da Hawila da Yobab, dukan waɗannan 'ya'yan Yokatan ne. 30 Yankin ƙasar da suka zauna shi ne ya milla tun daga Mesha, har zuwa wajen Sefar, ƙasar tudu ta gabas. 31 Waɗannan su ne 'ya'yan Shem bisa ga iyalansu, da harsunansu, da ƙasashensu, da kabilansu. 32 Waɗannan duka su ne zuriyar Nuhu, bisa ga lissafin asalinsu, bisa ga kabilansu. Daga waɗannan ne al'ummai suka yaɗu bisa duniya bayan Ruwan Tsufana.

Farawa 11

Hasumiyar Babila

1 A lokacin, harshen mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce. 2 Sa'ad da mutane suke ta yin ƙaura daga gabas, sai suka sami fili a ƙasar Shinar, suka zauna a can. 3 Sai suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi aiki da tubali maimakon dutse, katsi kuma maimakon lāka. 4 Sai suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni, da hasumiya wadda ƙwanƙolinta zai kai can cikin sammai domin mu yi wa kanmu suna, domin kada mu warwatsu ko'ina bisa duniya.” 5 Ubangiji kuwa ya sauko ya ga birnin da hasumiyar da 'yan adam suka gina. 6 Ubangiji kuwa ya ce, “Ga su, su jama'a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne, to fa, ga irin abin da suka fara yi, ba abin da za su shawarta su yi da zai gagare su. 7 Zo mu sauka, mu dagula harshensu, domin kada su fahimci maganar juna.” 8 Haka kuwa daga wurin Ubangiji ya warwatsa su ko'ina bisa duniya, sai suka daina gina birnin. 9 Domin haka aka kira sunan wurin Babila, domin a nan ne Ubangiji ya dagula harshen dukan duniya, daga nan ne kuma Ubangiji ya warwatsa su ko'ina bisa duniya.

Zuriyar Shem

10 Waɗannan su ne zuriyar Shem. Lokacin da Shem yake da shekara ɗari, ya haifi Arfakshad bayan Ruwan Tsufana da shekara biyu. 11 Shem kuwa ya yi shekara ɗari biyar bayan haihuwar Arfakshad, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 12 Sa'ad da Arfakshad yake da shekara talatin da biyar ya haifi Shela. 13 Arfakshad kuwa ya yi shekara arbaminya da uku bayan haihuwar Shela, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 14 Sa'ad da Shela yake da shekara talatin, ya haifi Eber, 15 Shela kuwa ya yi shekara arbaminya da uku bayan haihuwar Eber, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 16 Sa'ad da Eber ya yi shekara talatin da huɗu ya haifi Feleg, 17 Eber kuwa ya yi shekara arbaminya da talatin, bayan haihuwar Feleg, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 18 Sa'ad da Feleg ya yi shekara talatin ya haifi Reyu. 19 Feleg ya yi shekara metan da tara bayan haihuwar Reyu, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 20 Sa'ad da Reyu ya yi shekara talatin da biyu ya haifi Serug. 21 Reyu kuwa ya yi shekara metan da bakwai bayan haihuwar Serug, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 22 Sa'ad da Serug ya yi shekara talatin ya haifi Nahor, 23 Serug kuwa ya yi shekara metan bayan haihuwar Nahor, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 24 Sa'ad da Nahor ya yi shekara ashirin da tara, ya haifi Tera, 25 Nahor kuwa ya yi shekara ɗari da goma sha tara bayan haihuwar Tera, ya kuma haifi 'ya'ya mata da maza. 26 Sa'ad da Tera ya yi shekara saba'in, ya haifi Abram, da Nahor, da Haran. 27 Yanzu dai waɗannan su ne zuriyar Tera, Tera ya haifi Abram, da Nahor, da Haran, Haran kuwa shi ne ya haifi Lutu. 28 Haran kuwa ya rasu a idon mahaifinsa Tera a ƙasar haihuwarsa, a Ur ta Kaldiyawa. 29 Da Abram da Nahor suka yi aure, sunan matar Abram Saraya, sunan matar Nahor kuwa Milka, ita 'yar Haran ce, mahaifin Milka da Iskaya. 30 Saraya kuwa ba ta haihuwa, wato, ba ta da ɗa. 31 Sai Tera ya ɗauki ɗansa Abram da Lutu ɗan Haran, jikansa, da Saraya surukarsa, wato, matar ɗansa Abram, suka tafi tare, daga Ur ta Kaldiyawa zuwa ƙasar Kan'ana, amma da suka isa Haran, suka zauna a can. 32 Kwanakin Tera shekara ce metan da biyar, Tera kuwa ya rasu a Haran.

Farawa 12

Allah ya Kira Abram

1 Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka fita daga ƙasarka, da danginka, da gidan mahaifinka zuwa ƙasar da zan nuna maka. 2 Zan kuwa maishe ka al'umma mai girma, zan sa maka albarka, in sa ka ka yi suna, domin ka zama sanadin albarka. 3 Waɗanda suka sa maka albarka zan sa musu albarka, amma zan la'anta waɗanda suka la'anta ka. Dukan al'umman duniya za su roƙe ni in sa musu albarka kamar yadda na sa maka.” 4 Abram kuwa ya kama hanya bisa ga faɗar Ubangiji, Lutu kuma ya tafi tare da shi, Abram yana da shekara saba'in da biyar sa'ad da ya yi ƙaura daga Haran. 5 Abram kuwa ya ɗauki matarsa Saraya da Lutu, ɗan ɗan'uwansa, da dukan dukiyarsu, da dukan mallakarsu waɗanda suka tattara a Haran. Sa'ad da suka kai ƙasar Kan'ana, 6 Abram ya ratsa ƙasar zuwa Shekem, wurin itacen oak na More. A lokacin nan Kan'aniyawa suke a ƙasar. 7 Sai Ubangiji ya bayyana ga Abram, ya ce, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa.” Sai ya gina bagade ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi. 8 Ya zakuɗa daga nan zuwa dutsen da yake gabashin Betel, ya kafa alfarwarsa, Betel tana yamma, Ai tana gabas, a nan ya gina wa Ubangiji bagade, ya kira bisa sunan Ubangiji. 9 Abram kuwa ya ci gaba da tafiya, ya nufi zuwa wajen Negeb.

Abram a Masar

10 A lokacin nan ana yunwa a ƙasar. Sai Abram ya tafi Masar baƙunci, gama yunwa ta tsananta a ƙasar. 11 Sa'ad da yake gab da shiga Masar, ya ce wa matarsa, Saraya, “Na sani ke kyakkyawar mace ce, 12 lokacin da Masarawa suka gan ki za su ce, ‘Wannan matarsa ce,’ za su kashe ni, amma za su bar ki da rai. 13 Ki ce ke 'yar'uwata ce, domin dalilinki kome sai ya tafi mini daidai a kuma bar ni da raina.” 14 Sa'ad da Abram ya shiga Masar sai Masarawa suka ga matar kyakkyawa ce ƙwarai. 15 Da fādawan Fir'auna suka gan ta, sai suka yabe ta a gaban Fir'auna. Aka ɗauke ta aka kai ta gidan Fir'auna. 16 Saboda ita Fir'auna ya yi wa Abram alheri. Abram yana da tumaki, da takarkarai, da jakai maza, da barori mata da maza, da jakai mata, da raƙuma.

17 Sai Ubangiji ya wahalar da Fir'auna da gidansa da manya manyan annobai saboda matar Abram, Saraya. 18 Sai Fir'auna ya kirawo Abram, ya ce, “Mene ne wannan da ka yi mini? Don me ba ka faɗa mini ita matarka ce ba? 19 Don me ka ce ita 'yar'uwarka ce, har na ɗauke ta ta zama matata? To, ga matarka, ka ɗauke ta ka tafi.” 20 Fir'auna kuma ya umarci mutanensa a kan Abram, su raka shi da matarsa, da dukan abin da yake da shi.

Farawa 13

Rabuwar Abram da Lutu

1 Domin haka Abram ya bar Masar zuwa Negeb, shi da matarsa, da abin da yake da shi duka tare da Lutu. 2 Yanzu Abram ya arzuta da dabbobi, da azurfa, da zinariya. 3 Ya yi ta tafiya daga Negeb har zuwa Betel, har wurin da ya kafa alfarwarsa da fari, tsakanin Betel da Ai, 4 a inda dā ya gina bagade. A can Abram ya kira bisa sunan Ubangiji. 5 Lutu wanda ya tafi tare da Abram, shi kuma yana da garkunan tumaki, da na shanu, da alfarwai, 6 domin haka ƙasar ba ta isa dukansu biyu su zauna tare ba, saboda mallakarsu ta cika yawa, har da ba za su iya zama tare ba. 7 Akwai rashin jituwa kuma a tsakanin makiyayan dabbobin Abram da makiyayan dabbobin Lutu. Mazaunan ƙasar, a lokacin nan Kan'aniyawa da Ferizziyawa ne. 8 Abram ya ce wa Lutu, “Kada rashin jituwa ya shiga tsakanina da kai ko tsakanin makiyayanka da nawa, gama mu 'yan'uwa ne. 9 Ba ƙasar duka tana gabanka ba? Sai ka ware daga gare ni. In ka ɗauki hagu in ɗauki dama, in kuwa ka ɗauki dama ni sai in ɗauki hagu.” 10 Lutu ya ɗaga idanunsa sama ya dubi kwarin Urdun, ga shi kuwa da dausayi mai kyau ƙwarai, sai ka ce gonar Ubangiji, kamar ƙasar Masar wajen Zowar, tun kafin Allah ya hallaka Saduma da Gwamrata. 11 Domin haka, Lutu ya zaɓar wa kansa kwarin Urdun duka, Lutu kuma ya kama hanya ya nufi gabas. Haka fa suka rabu da juna. 12 Abram ya zauna a ƙasar Kan'ana, Lutu kuwa ya zauna a biranen kwari, ya zakuɗar da alfarwarsa har zuwa Saduma. 13 Mutanen Saduma kuwa mugaye ne masu aikata zunubi ƙwarai gāba da Ubangiji.

Abram ya yi Ƙaura zuwa Hebron

14 Sai Ubangiji ya ce wa Abram, bayan da Lutu ya rabu da shi, “Ɗaga idanunka sama, daga inda kake, ka dubi kusurwoyin nan huɗu, 15 gama dukan ƙasan nan da kake gani kai zan ba, da zuriyarka har abada. 16 Zan mai da zuriyarka kamar turɓayar ƙasa, har in mutum ya iya ƙidaya turɓayar ƙasa, to, a iya ƙidaya zuriyarka. 17 Tashi, ka yi tafiya cikin ratar ƙasar da fāɗinta, gama zan ba ka ita.” 18 Sai Abram ya cire alfarwarsa, ya zo ya zauna kusa da itatuwan oak na Mamre, waɗanda suke Hebron. A can ya gina wa Ubangiji bagade.

Farawa 14

Abram ya 'Yanto Lutu

1 A zamanin Amrafel Sarkin Shinar, shi da Ariyok Sarkin Ellasar, da Kedarlayomer Sarkin Elam, da Tidal Sarkin Goyim, 2 suka fita suka yi yaƙi da Bera Sarkin Saduma, da Birsha Sarkin Gwamrata, da Shinab Sarkin Adma, da Shemeber Sarkin Zeboyim, da kuma Sarkin Bela, wato, Zowar. 3 Waɗannan sarakuna biyar suka haɗa kai don su kai yaƙi, suka haɗa mayaƙansu a kwarin Siddim, inda Tekun Gishiri take. 4 Shekara goma sha biyu suka bauta wa Kedarlayomer, amma suka tayar a shekara ta goma sha uku. 5 A shekara ta goma sha huɗu Kedarlayomer da sarakunan da suke tare da shi suka zo suka cinye Refayawa cikin Ashterotkarnayim, da Zuzawa cikin Ham, da Emawa cikin Filin Kiriyatayim, 6 da kuma Horiyawa cikin dutsen nan nasu, wato, Seyir, har zuwa Elfaran a bakin jeji. 7 Sai suka juya suka je Enmishfat, wato, Kadesh, suka kuwa cinye ƙasar Amalekawa da kuma ta Amoriyawa waɗanda suka zauna cikin Hazazontamar. 8-9 Sai Sarkin Saduma, da Sarkin Gwamrata, da Sarkin Adma da Sarkin Zeboyim, da Sarkin Bela, wato, Zowar, suka fita suka ja dāga da Kedarlayomer Sarkin Elam, da Tidal Sarkin Goyim, da Amrafel Sarkin Shinar, da Ariyok Sarkin Ellasar a kwarin Siddim, sarakuna huɗu gāba da biyar. 10 Akwai ramummukan kalo da yawa a kwarin Siddim. Da Sarkin Saduma da na Gwamrata suka sheƙa da gudu sai waɗansunsu suka fāɗa cikin ramummukan, sauran kuwa suka gudu zuwa dutsen. 11 Sai abokan gāba suka kwashe dukan kayayyakin Saduma da na Gwamrata, da abincinsu duka, suka yi tafiyarsu. 12 Suka kuma kama Lutu ɗan ɗan'uwan Abram, wanda yake zaune a Saduma, da kayayyakinsa, suka yi tafiyarsu. 13 Sai wani da ya tsere, ya zo ya faɗa wa Abram Ba'ibrane wanda yake zaune wajen itatuwan oak na Mamre, Ba'amore, ɗan'uwan Eshkol da Aner, waɗanda suke abuta da Abram. 14 Lokacin da Abram ya ji an kama danginsa wurin yaƙi sai ya shugabanci horarrun mutanensa, haifaffun gidansa, su ɗari uku da goma sha takwas, suka bi sawun sarakunan har zuwa Dan. 15 Da dad dare sai ya kasa jarumawansa yadda za su gabza da su, shi da barorinsa, ya kuma ɗibge su, ya kore su har zuwa Hoba, arewacin Dimashƙu. 16 Sai ya washe kayayyakin duka, ya kuma ƙwato ɗan'uwansa Lutu da kayayyakinsa da mata da maza.

Malkisadik ya Sa wa Abram Albarka

17 Sai Sarkin Saduma ya fita ya taryi Abram sa'ad da ya komo daga korar Kedarlayomer da sarakunan da suke tare da shi, a Kwarin Shawe, wato, Kwarin Sarki. 18 Sai Malkisadik Sarkin Salem, wato, Urushalima, ya kawo gurasa da ruwan inabi. Shi firist ne na Allah Maɗaukaki. 19 Ya kuwa sa wa Abram albarka ya ce, “Shi wanda ya yi sama da ƙasa, Allah Maɗaukaki ya sa wa Abram albarka. 20 Ga Allah Maɗaukaki yabo ya tabbata, shi wanda ya ba ka maƙiyanka a tafin hannunka!” Abram kuwa ya ba shi ushiri na duka. 21 Sai Sarkin Saduma ya ce wa Abram, “Ka ba ni mutanen, amma ka riƙe kayayyakin don kanka.” 22 Amma Abram ya ce wa Sarkin Saduma, “Na riga na rantse wa Ubangiji Allah Maɗaukaki, wanda ya yi sama da ƙasa, 23 cewa, ba zan ɗauki ko da zare ɗaya ko maɗaurin takalmi ba, ko kowane abin da yake naka, domin kada ka ce, ‘Na arzuta Abram.’ 24 A ni kaina ba zan ɗauki kome ba illa abin da samari suka ci, da rabon mutanen da suka tafi tare da ni. Sai dai kuma Aner, da Eshkol, da Mamre su ɗauki nasu rabo.”

Farawa 15

Alkawarin da yake tsakanin Allah da Abram

1 Bayan waɗannan al'amura, maganar Ubangiji ta zo ga Abram cikin wahayi cewa, “Abram, kada ka ji tsoro, ni ne garkuwarka, kana da lada mai yawa.” 2 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, me za ka ba ni, ga shi kuwa, ba ni da ɗa? Ko kuwa Eliyezer na Dimashƙu ne zai gāje ni?” 3 Abram kuma ya ce, “Ga shi, ba ka ba ni zuriya ba, ga shi ma wani yaron gidana ne zai gāje ni.” 4 Sai ga maganar Ubangiji ta zo gare shi cewa, “Mutumin nan, ba shi zai gāje ka ba, ɗan cikinka shi zai gāje ka.” 5 Sai Ubangiji ya fito da shi waje ya ce, “Ina so ka dubi sararin sama, ka kuma ƙidaya taurari, in kana iya ƙidaya su.” Sai kuma ya ce masa, “Haka zuriyarka za ta zama.” 6 Ya amince da Ubangiji, Ubangiji kuwa ya lasafta wannan adalci ne a gare shi. 7 Ubangiji kuma ya ce masa, “Ni ne Ubangiji wanda ya fisshe ka daga Ur ta Kaldiyawa, don in ba ka wannan ƙasa ka gāje ta.” 8 Amma Abram ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, yaya zan mallake ta?” 9 Ya ce masa, “Kawo mini karsana bana uku, da burguma bana uku, da rago bana uku, da hazbiya da ɗan tattabara.” 10 Ya kawo masa waɗannan abu duka, ya yanyanka su ya tsattsaga su a tsaka, ya ajiye su gab da juna, amma bai tsaga tsuntsayen a tsaka ba. 11 Sa'ad da tsuntsaye masu cin nama suke sauka bisansu sai Abram ya kore su. 12 Sa'ad da rana take faɗuwa, barci mai nauyi ya kwashe Abram, sai ga babban duhu mai bantsoro ya rufe shi. 13 Ubangiji ya ce wa Abram, “Ka sani lalle ne zuriyarka za ta yi baƙunci cikin ƙasar da ba tata ba ce, za ta kuwa yi bauta, za a kuma tsananta mata har shekara arbaminya, 14 amma zan hukunta al'ummar da suka bauta wa, daga baya kuma da dukiya mai yawa za ta fita. 15 Kai kuwa, cikin salama za ka koma ga iyayenka, da kyakkyawan tsufa za a binne ka. 16 A tsara ta huɗu kuma, zuriyar za ta komo nan, domin adadin muguntar Amoriyawa bai cika ya kai iyaka ba tukuna.” 17 Sa'ad da rana ta fāɗi aka kuwa yi duhu, sai ga tanderun wuta mai hayaƙi da jiniya mai harshen wuta suka ratsa tsakanin abubuwan nan da aka tsattsaga a tsaka. 18 A wannan rana Ubangiji ya yi wa Abram alkawari ya ce, “Ga zuriyarka na ba da wannan ƙasa, daga Kogin Masar zuwa babban kogi, wato, Kogin Yufiretis ke nan, 19 ƙasar Keniyawa, da Kenizziyawa, da Kadmoniyawa, 20 da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Refayawa, 21 da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Girgashiyawa, da kuma Yebusiyawa.”

Farawa 16

Hajaratu da Isma'ilu

1 Saraya matar Abram ba ta taɓa haihuwa ba, amma tana da baranya Bamasariya, sunanta Hajaratu. 2 Sai Saraya ta ce wa Abram, “To, ga shi, Ubangiji ya hana mini haihuwar 'ya'ya. Shiga wurin baranyata, mai yiwuwa ne in sami 'ya'ya daga gare ta.” Abram kuwa ya saurari murya matarsa Saraya. 3 A lokacin nan kuwa Abram yana da shekara goma da zama a ƙasar Kan'ana sa'ad da Saraya matar Abram ta ɗauki Hajaratu Bamasariya, baranyarta, ta bai wa Abram mijinta ta zama matarsa. 4 Abram kuwa ya shiga wurin Hajaratu, ta kuwa yi ciki. Da ta ga ta sami ciki sai ta dubi uwargijiyarta a raine. 5 Sai Saraya ta ce wa Abram, “Bari cutar da aka cuce ni da ita ta koma kanka! Na ba da baranyata a ƙirjinka, amma da ta ga ta sami ciki, sai tana dubana a raine. Ubangiji ya shara'anta tsakanina da kai.” 6 Amma Abram ya ce wa Saraya, “Ga shi, baranyarki tana cikin ikonki, yi yadda kika ga dama da ita.” Saraya ta ƙanƙanta ta, sai Hajaratu ta gudu daga gare ta. 7 Mala'ikan Ubangiji kuwa ya sami Hajaratu a gefen wata maɓuɓɓugar ruwa a jeji, wato, maɓuɓɓugar da take kan hanyar Shur. 8 Sai ya ce, “Ke Hajaratu, baranyar Saraya, ina kika fito, ina kuma za ki?” Ta ce, “Gudu nake yi daga uwargijiyata Saraya.” 9 Mala'ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki, ki yi mata ladabi.” 10 Mala'ikan Ubangiji kuma ya ce mata, “Zan riɓaɓɓanya zuriyarki ainun har da ba za a iya lasafta su ba saboda yawansu.” 11 Mala'ikan Ubangiji kuma ya ƙara ce mata, “Ga shi, kina da ciki, za ki haifi ɗa, za ki kira sunansa Isma'ilu, domin Ubangiji ya lura da wahalarki. 12 Zai zama mutum ne mai halin jakin jeji, hannunsa zai yi gāba da kowane mutum, hannun kowane mutum kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zaman magabtaka tsakaninsa da 'yan'uwansa duka.” 13 Sai ta kira sunan Ubangiji wanda ya yi magana da ita, “Kai Allah ne mai gani,” gama ta ce, “Ni! Har na iya ganin Allah in rayu?” 14 Domin haka aka kira sunan rijiyar, Biyer-lahai-royi, tana nan tsakanin Kadesh da Bered. 15 Hajaratu ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya sa wa ɗa da Hajaratu ta haifa suna, Isma'ilu. 16 Abram yana da shekara tamanin da shida sa'ad da Hajaratu ta haifa masa Isma'ilu.

Farawa 17

Kaciya ita ce Shaidar Alkawarin

1 A lokacin da Abram yake da shekara tasa'in da tara Ubangiji ya bayyana gare shi, ya ce masa, “Ni ne Allah Mai Iko Dukka. Ka yi mini biyayya, ka zama kamili. 2 Zan yi maka alkawari, in ba ka zuriya mai yawa.” 3 Sai Abram ya yi ruku'u, Allah kuwa ya ce masa, 4 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi maka, za ka zama uba ga al'ummai masu ɗumbun yawa. 5 Ba za a ƙara kiran sunanka Abram ba, amma sunanka zai zama Ibrahim, gama na sa ka, ka zama uba ga al'ummai masu ɗumbun yawa. 6 Zan arzuta ka ainun, daga gare ka zan yi al'ummai, daga gare ka kuma sarakuna za su fito. 7 “Zan kafa alkawarina da kai, da zuriyarka a bayanka cikin dukan tsararrakinsu, madawwamin alkawari ke nan, in zama Allahnka da na zuriyarka a bayanka. 8 Zan ba ka, kai da zuriyarka a bayanka, ƙasar baƙuncinka, wato, dukan ƙasar Kan'ana ta zama mallakarka har abada, ni kuwa zan zama Allahnsu.” 9 Allah kuma ya ce wa Ibrahim, “Kai fa, sai ka kiyaye alkawarina, da kai da zuriyarka a bayanka cikin dukan tsararrakinsu. 10 Wannan shi ne alkawarina da za ka kiyaye, da kai da zuriyarka a bayanka. Sai a yi wa kowane ɗa namiji kaciya. 11 Loɓarku za ku yanke, don alamar alkawari a tsakanina da ku. 12 Daga yanzu duk namijin da aka haifa a cikinku za a yi masa kaciya a rana ta takwas har dukan tsararrakinku, ko haifaffen gida ne, ko sayayye da kuɗi daga kowane baƙo wanda ba na zuriyarku ba. 13 Duka biyu, da wanda aka haifa daga gidanka, da wanda ka saya da kuɗi, za a yi musu kaciya. Da haka alkawarina zai kasance cikin jikinku, madawwamin alkawari ke nan. 14 Kowane ɗa namiji da bai yi kaciya ba, wato, wanda bai yi kaciyar loɓarsa ba, za a fitar da shi daga jama'arsa, don ya ta da alkawarina.” 15 Allah ya ce wa Ibrahim, “Ga zancen matarka Saraya, ba za ka kira sunanta Saraya ba, amma Saratu ne sunanta. 16 Zan sa mata albarka, banda haka kuma zan ba ka ɗa ta wurinta, zan sa mata albarka, za ta kuwa zama mahaifiyar al'ummai, sarakunan jama'a za su fito daga gare ta.” 17 Sai Ibrahim ya yi ruku'u, ya yi dariya a zuciyarsa, ya ce wa kansa, “Za a haifa wa mai shekara ɗari ɗa? Zai yiwu Saratu mai shekara tasa'in ta haifi ɗa?” 18 Sai Ibrahim ya ce wa Allah, “Da ma dai a bar Isma'ilu kawai ya rayu a gabanka.” 19 Allah ya ce, “A'a, matarka Saratu ita ce za ta haifa maka ɗa, za ka raɗa masa suna Ishaku. A gare shi zan tsai da alkawarina madawwami, da kuma ga zuriyarsa a bayansa. 20 Ga zancen Isma'ilu kuwa, na ji, ga shi, zan sa masa albarka in kuma riɓaɓɓanya shi ainun. Zai zama mahaifin 'ya'yan sarakuna goma sha biyu, zan maishe shi al'umma mai girma. 21 Amma ga Ishaku ne zan tsai da alkawarina, wato, wanda Saratu za ta haifa maka a baɗi war haka.” 22 Sa'ad da Allah ya gama magana da Ibrahim, sai ya tafi ya bar Ibrahim. 23 Ibrahim kuwa ya ɗauki Isma'ilu ɗansa, da dukan bayi, haifaffun gidansa, da waɗanda aka sayo su da kuɗinsa, ya kuwa yi wa kowane namiji na jama'ar gidansa kaciyar loɓarsa a wannan rana bisa ga faɗar Allah. 24 Ibrahim na da shekara tasa'in da tara sa'ad da aka yi masa kaciyar loɓarsa. 25 Isma'ilu ɗansa yana ɗan shekara goma sha uku sa'ad da aka yi masa kaciya. 26 A wannan rana, Ibrahim da ɗansa Isma'ilu aka yi musu kaciya, 27 da mazajen gidansa duka, da waɗanda suke haifaffun gidan da waɗanda aka sayo da kuɗi daga baƙi, aka yi musu kaciya tare da shi.

Farawa 18

An Alkawarta Haihuwar Ishaku

1 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ibrahim kusa da itatuwan oak na Mamre, a lokacin da yake zaune a ƙofar alfarwarsa da tsakar rana. 2 Da ya ɗaga idonsa, ya duba sai ga mutum uku suna tsaye a gabansa. Da ya gan su, sai ya sheƙa da gudu daga ƙofar alfarwar, don ya tarye su. Ya yi ruku'u, 3 ya ce, “Ya Ubangiji, in na sami tagomashi a gabanka, kada ka wuce gidana. A shirye nake in yi muku hidima. 4 Bari a kawo ɗan ruwa ku wanke ƙafafunku, ku shaƙata a gindin itace, 5 ni kuwa in tafi in kawo ɗan abinci, don rayukanku su wartsake, bayan haka sai ku wuce, tun da yake kun biyo ta wurin baranku.” Sai suka ce, “Madalla! Ka aikata bisa ga faɗarka.” 6 Ibrahim kuwa ya gaggauta zuwa cikin alfarwa wurin Saratu, ya ce, “Ki shirya mudu uku na gari mai laushi da sauri, ki cuɗa, ki yi waina.” 7 Sai Ibrahim ya sheƙa zuwa garke, ya ɗauki maraƙi, matashi mai kyau, ya ba baransa, ya kuwa shirya shi nan da nan. 8 Ya ɗauki kindirmo da madara, da maraƙin da ya shirya, ya ajiye a gabansu, ya tsaya kusa da su a gindin itacen a sa'ad da suke ci. 9 Suka ce masa, “Ina Saratu matarka?” Ya ce, “Tana cikin alfarwa.” 10 Baƙon ya ce, “Na yi maka alkawari matarka Saratu za ta haifi ɗa a wata na tara nan gaba. Zan sāke zuwa a lokacin.” Saratu kuwa tana ƙofar alfarwa, a bayansu, tana kasa kunne. 11 Ga shi kuwa, Ibrahim da Saratu sun tsufa, sun kwana biyu, gama Saratu ta daina al'adar mata. 12 Sai Saratu ta yi dariya a ranta, tana cewa, “Bayan na tsufa mai gidana kuma ya tsufa sa'an nan zan sami wannan gatanci?” 13 Ubangiji ya ce wa Ibrahim, “Me ya ba Saratu dariya, har da ta ce, ‘Ashe zan haifi ɗa, a yanzu da na riga na tsufa?’ 14 Akwai abin da zai fi ƙarfin Ubangiji? A ajiyayyen lokaci zan komo wurinka, cikin wata tara, Saratu kuwa za ta haifi ɗa.” 15 Amma Saratu ta yi m�su, tana cewa, “Ai, ban yi dariya ba,” Gama tana jin tsoro. Ya ce, “A'a, hakika kin yi dariya.”

Ibrahim ya Yi Roƙo don Saduma

16 Sai mutanen suka tashi daga wurin, suka fuskanci Saduma, Ibrahim kuwa ya yi musu rakiya ya sallame su. 17 Ubangiji ya ce, “Zan ɓoye wa Ibrahim abin da nake shirin aikatawa? 18 Ga shi kuwa, Ibrahim zai ƙasaita ya zama al'umma mai iko, sauran al'umman duniya duka za su sami albarka ta dalilinsa. 19 Gama na zaɓe shi don ya umarci 'ya'yansa da gidansa domin su kiyaye tafarkin Ubangiji a bayansa, su riƙe adalci da shari'a.” Ubangiji ya tabbatar wa Ibrahim da abin da ya alkawarta masa. 20 Sai kuma Ubangiji ya ce, “Tun da yake kuka a kan Saduma da Gwamrata ya yi yawa, zunubinsu kuma ya yi muni ƙwarai, 21 zan sauka in gani ko sun aikata kamar yadda kukan ya zo gare ni, zan bincike.” 22 Sa'an nan mutanen suka juya daga nan, suka nufi Saduma, amma Ibrahim ya tsaya a gaban Ubangiji. 23 Sai Ibrahim ya matso kusa, ya ce, “Ashe, za ka hallaka adali tare da mugun? 24 Da a ce, akwai masu adalci hamsin cikin birnin, za ka hallaka wurin, ba za ka yafe su saboda masu adalcin nan hamsin waɗanda suke cikinsa ba? 25 Wannan ya yi nesa da kai, da ka aikata irin haka, wato, da za ka aza mai adalci daidai yake da mugu! Wannan ya yi nesa da kai! Mahukuncin dukan duniya ba zai yi adalci ba?” 26 Sai Ubangiji ya ce, “In na sami adalai hamsin a cikin birnin Saduma, zan yafe wa dukan wurin sabili da su.” 27 Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji, ni da nake ba kome ba ne, amma turɓaya ne da toka. 28 Da a ce za a rasa biyar daga cikin adalai hamsin ɗin, za ka hallaka birnin duka saboda rashin biyar ɗin?” Sai ya ce, “Ba zan hallaka shi ba in na sami arba'in da biyar a wurin.” 29 Ya kuma sāke yin masa magana, ya ce, “Da a ce za a sami arba'in a wurin fa?” Ya amsa ya ce, “Sabili da arba'in ɗin ba zan yi ba.” 30 Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan yi magana. Da a ce za a sami talatin a wurin fa?” Ya amsa, “Ba zan yi ba, in na sami talatin a wurin.” 31 Ya ce, “Ga shi, na jawo wa kaina in yi magana da Ubangiji. Da a ce za a sami ashirin a wurin fa?” Ya amsa ya ce, “Sabili da ashirin ɗin ba zan hallaka shi ba.” 32 Sai ya ce, “Kada dai Ubangiji ya husata, zan sāke yin magana, sau ɗayan nan kaɗai. Da a ce za a sami goma a wurin fa?” Ya amsa ya ce, “Sabili da goma ɗin ba zan hallaka shi ba.” 33 Ubangiji kuwa ya yi tafiyarsa, bayan ya gama magana da Ibrahim. Ibrahim kuwa ya koma gida.

Farawa 19

Zunubin Sadumawa ya Haɓaka

1 Mala'ikun nan biyu kuwa suka isa Saduma da maraice, Lutu kuwa yana zaune a ƙofar Saduma. Sa'ad da Lutu ya gan su sai ya miƙe ya tarye su. Sai ya yi ruku'u a gabansu, 2 ya ce, “Iyayengijina, ina roƙonku ku ratse zuwa gidan baranku, ku kwana, ku wanke ƙafafunku, da sassafe kuma sai ku kama hanyarku.” Suka ce, “A'a, a titi za mu kwana.” 3 Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka ratse suka shiga gidansa, ya shirya musu liyafa, ya toya musu abinci marar yisti, suka ci. 4 Amma kafin su shiga barci, mutanen birnin Saduma, samari da tsofaffi, dukan mutane gaba ɗaya suka kewaye gidan. 5 Suka kira Lutu suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka da daren nan? Fito mana da su waje, don mu yi luɗu da su.” 6 Lutu ya fita daga cikin gida ya rufe ƙofar a bayansa ya je wurin mutane, 7 ya ce, “Ina roƙonku 'yan'uwana, kada ku aikata mugunta haka. 8 Ga shi, ina da 'ya'ya mata biyu waɗanda ba su san namiji ba, bari in fito muku da su waje, ku yi yadda kuka ga dama da su, sai dai kada ku taɓa mutanen nan ko kaɗan, gama sun shiga ƙarƙashin inuwata.” 9 Amma suka ce, “Ba mu wuri!” Suka kuma ce, “Wannan mutum ya zo baƙunci ne, yanzu kuma zai zama alƙali! Yanzu za mu yi maka fiye da yadda za mu yi musu.” Sai suka tutture Lutu suka matsa kusa don su fasa ƙofar. 10 Amma baƙin suka miƙa hannunsu, suka shigar da Lutu cikin gida inda suke, suka rufe ƙofa. 11 Sai suka bugi mutanen da suke ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu suna laluba inda ƙofa take.

Lutu ya Bar Saduma

12 Mutanen suka ce wa Lutu, “Kana da wani naka a nan? Ko surukai, ko 'ya'ya mata da maza, ko dai kome naka da yake cikin birnin? Fito da su daga wurin, 13 gama muna gab da hallaka wurin nan, domin kukan da ake yi a kan mutanen ya yi yawa a gaban Ubangiji. Ubangiji kuwa ya aiko mu, mu hallaka birnin.” 14 Sai Lutu ya fita ya faɗa wa surukansa waɗanda za su auri 'ya'yansa mata, “Tashi, ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma sai surukansa suka aza wasa yake yi. 15 Sa'ad da safiya ta gabato, mala'ikun suka hanzarta Lutu, suna cewa, “Tashi, ka ɗauki matarka da 'ya'yanka biyu mata da suke nan, don kada a shafe ku saboda zunubin birnin.” 16 Amma da ya yi ta ja musu rai, sai mutanen suka kama hannunsa, da na matarsa, da na 'ya'yansa biyu mata, saboda jinƙan da Ubangiji ya yi masa, suka fitar da shi suka kai shi a bayan birnin. 17 Sa'ad da suka fitar da shi, suka ce, “Ka gudu domin ranka, kada ka waiwaya baya, ko ka tsaya ko'ina cikin kwari, gudu zuwa tuddai domin kada a hallaka ka.” 18 Sai Lutu ya ce musu, “A'a, ba haka ba ne iyayengijina, 19 ga shi, baranka ya sami tagomashi a idonka, ka kuwa nuna mini babban alheri da ka ceci raina, amma ba zan iya in kai tuddan ba, kada hatsarin ya same ni a hanya, in mutu. 20 Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.” 21 Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba. 22 Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa wurin.” Domin haka aka kira sunan garin Zowar.

Halakar Saduma da Gwamrata

23 Da hantsi Lutu ya isa Zowar. 24 Sai Ubangiji ya yi ta zuba wa Saduma da Gwamrata wutar kibritu daga sama, 25 ya hallakar da waɗannan birane, da dukan kwarin, da dukan mazaunan biranen, da tsire-tsire. 26 Amma matar Lutu da take bin bayansa ta waiwaya, sai ta zama surin gishiri. 27 Da sassafe kuwa sai Ibrahim ya tafi wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji, 28 ya duba wajen Saduma da Gwamrata, da wajen dukan ƙasar kwari, sai ya hangi, hayaƙi yana tashi kamar hayaƙin da yake fitowa daga matoya a bisa ƙasar. 29 Amma sa'ad da Allah ya hallaka biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya fid da Lutu daga halakar.

Asalin Mowabawa da Ammonawa

30 Lutu ya fita daga Zowar, ya zauna cikin tuddai da 'ya'yansa biyu mata, gama yana jin tsoro ya zauna a Zowar. Ya zauna a cikin kogo da 'ya'yansa biyu mata. 31 Sai 'yar farin ta ce wa ƙaramar, “Mahaifinmu ya tsufa, ba wanda zai aure mu yadda aka saba yi ko'ina a duniya. 32 Zo dai, mu sa mahaifinmu ya sha ruwan inabi, sa'an nan sai mu kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.” 33 Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi. Da daren nan kuwa 'yar farin ta shiga ta kwana da mahaifinta, shi kuwa bai san da kwanciyarta ba balle fa tashinta. 34 Kashegari kuma, 'yar farin ta ce wa ƙaramar, “Ga shi, daren jiya na kwana da mahaifina, bari daren yau kuma, mu sa shi ya sha ruwan inabi, ke ma sai ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.” 35 Saboda haka suka sa shi ya bugu da ruwan inabi a wannan dare kuma, ƙaramar ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san da kwanciyarta ba balle fa tashinta. 36 Haka nan kuwa, 'ya'yan Lutu biyu ɗin nan suka sami ciki daga mahaifinsu. 37 Ta farin, ta haifi ɗa namiji, ta sa masa suna Mowab. Shi ne asalin Mowabawa har yau. 38 Ƙaramar kuma ta haifi ɗa namiji, ta sa masa suna Benammi, shi ne asalin Ammonawa har yau.

Farawa 20

Ibrahim da Abimelek

1 Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi zuwa wajen karkarar Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. A lokacin da Ibrahim yake baƙunci a Gerar, 2 ya ce, matarsa Saratu 'yar'uwarsa ce. Sai Abimelek Sarkin Gerar ya aika, aka ɗauko masa Saratu. 3 Amma Allah ya zo wurin Abimelek cikin mafarki da dad dare ya ce masa, “Mutuwa za ka yi saboda matar da ka ɗauko, gama ita matar wani ce.” 4 Abimelek bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ubangiji, za ka hallaka marar laifi? 5 Ba shi ya faɗa mini, ‘Ita 'yar'uwata ce’ ba? Ba ita kanta kuma ta ce, ‘Shi ɗan'uwana ne’ ba? Cikin mutunci da kyakkyawan nufi na aikata wannan.” 6 Allah ya ce masa cikin mafarki, “I, na sani ka yi wannan cikin mutunci, ai, ni na hana ka ka aikata zunubin, don haka ban yarda maka ka shafe ta ba. 7 Yanzu fa, sai ka mayar wa mutumin da matarsa, gama shi annabi ne, zai yi maka addu'a, za ka kuwa rayu. In kuwa ba ka mayar da ita ba, ka sani hakika za ka mutu, kai, da dukan abin da yake naka.” 8 Abimelek ya tashi da sassafe, ya kira barorinsa duka ya kuma faɗa musu waɗannan abubuwa duka. Mutanen kuwa suka ji tsoro ƙwarai. 9 Abimelek kuwa ya kira Ibrahim, ya ce masa, “Me ke nan ka yi mana? Wane laifi na yi maka, da za ka jawo bala'i mai girma haka a kaina da mulkina? Ka yi mini abin da bai kamata a yi ba.” 10 Abimelek kuma ya ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan abu?” 11 Ibrahim ya ce, “Na yi haka, domin ina zaton babu tsoron Allah ko kaɗan a wannan wuri, shi ya sa na zaci, kashe ni za a yi saboda matata. 12 Banda haka nan ma, hakika ita 'yar'uwata ce, 'yar mahaifina amma ba ta mahaifiyata ba ce. Na kuwa aure ta. 13 A lokacin da Allah ya raba ni da gidan mahaifina, ya sa ni yawaceyawace, na ce mata, ‘Wannan shi ne alherin da za ki yi mini a duk inda muka je, ki ce da ni ɗan'uwanki ne.’ ” 14 Abimelek ya ɗauki tumaki da takarkarai, da bayi mata da maza, ya ba Ibrahim, ya kuma mayar masa da matarsa Saratu. 15 Abimelek kuwa ya ce, “Ga shi, ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda ya yi maka daɗi.” 16 Ga Saratu kuwa ya ce, “Ga shi, na ba ɗan'uwanki azurfa guda dubu, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa, cewa, ba ki da laifi.” 17 Ibrahim ya yi addu'a ga Allah, Allah kuwa ya warkar da Abimelek, da matarsa, da bayinsa mata, har kuma suka sami haihuwa. 18 Gama dā Allah ya kulle mahaifar dukan gidan Abimelek saboda Saratu matar Ibrahim.

Farawa 21

Haihuwar Ishaku

1 Ubangiji ya yi wa Saratu alheri kamar yadda ya alkawarta. 2 Saratu kuwa ta yi ciki, ta haifa wa Ibrahim ɗa cikin tsufansa a lokacin nan da Allah ya faɗa masa. 3 Sai Ibrahim ya raɗa wa ɗansa wanda Saratu ta haifa masa, suna, Ishaku. 4 Ibrahim ya yi wa Ishaku ɗansa kaciya yana da kwana takwas, kamar yadda Allah ya umarce shi. 5 Ibrahim kuwa yana da shekara ɗari sa'ad da aka haifa masa ɗansa Ishaku. 6 Saratu ta ce, “Allah ya sa na yi dariya, har dukan wanda ya ji zai yi dariya tare da ni.” 7 Ta kuma ce, “Dā wa zai iya ce wa Ibrahim Saratu za ta bai wa 'ya'ya mama? Duk da haka cikin tsufansa na haifa masa ɗa.” 8 Yaron ya yi girma, aka yaye shi, Ibrahim kuwa ya yi babban biki a ranar da aka yaye Ishaku.

Korar Hajaratu da Isma'ilu

9 Amma Saratu ta ga ɗan Hajaratu Bamasariya wanda ta haifa wa Ibrahim yana wasa da ɗanta Ishaku. 10 Sai ta ce wa Ibrahim, “Ka kori wannan baiwa da ɗanta, gama ɗan baiwan nan ba zai zama magaji tare da ɗana Ishaku ba.” 11 Abin ya ɓata wa Ibrahim zuciya ƙwarai sabili da ɗansa. 12 Amma Allah ya ce wa Ibrahim, “Kada zuciyarka ta ɓaci saboda yaron da kuma baiwarka. Kome Saratu ta faɗa maka, ka yi yadda ta ce, gama ta wurin Ishaku za a riƙa kiran zuriyarka. 13 Zan kuma yi al'umma daga ɗan baiwar, domin shi ma zuriyarka ne.” 14 Ibrahim ya tashi da sassafe, ya kuma ɗauki gurasa da salkar ruwa, ya bai wa Hajaratu, ya ɗora kafaɗarta. Sai ya ba ta ɗanta, ya sallame ta. Ta tafi ta yi ta yawo cikin jejin Biyer-sheba. 15 Sa'ad da ruwan salkar ya ƙare, sai ta yar da yaron a ƙarƙashin wani ƙaramin itace. 16 Sai ta tafi, ta zauna ɗaura da shi da 'yar rata, misalin nisan harbin baka, gama ta ce, “Don kada in ga mutuwar yaron.” Da ta zauna can daura da shi, sai yaron ya ta da muryarsa ya yi ta kuka. 17 Allah kuwa ya ji muryar yaron, mala'ikan Allah kuma ya kira Hajaratu daga sama, ya ce mata, “Me ke damunki, Hajaratu? Kada ki ji tsoro gama Allah ya ji muryar yaron a inda yake. 18 Tashi, ki ɗauki yaron, ki rungume shi da hannunki gama zan maishe shi babbar al'umma.” 19 Sai Allah ya buɗe idanunta, ta ga rijiyar ruwa, ta kuwa tafi, ta cika salkar da ruwa ta ba yaron ya sha. 20 Allah kuwa yana tare da yaron, ya kuwa yi girma, ya zauna a jeji, ya zama riƙaƙƙen maharbi. 21 Ya zauna a jejin Faran. Sai mahaifiyarsa ta auro masa mata daga ƙasar Masar.

Ibrahim da Abimelek suka Ƙulla Yarjejeniya

22 A lokacin nan fa, ya zamana Abimelek, da Fikol shugaban sojojinsa ya zo ya ce wa Ibrahim, “Allah yana tare da kai cikin sha'aninka duka, 23 don haka, yanzu sai ka rantse mini da Allah, cewa, ba za ka ci amanata, ko ta 'ya'yana, ko ta zuriyata ba, amma kamar yadda na riƙe ka cikin mutunci, haka za ka yi da ni da ƙasar da ka yi baƙunta a ciki.” 24 Sai Ibrahim ya amsa, “I, zan rantse.” 25 Sa'ad da Ibrahim ya kawo kuka ga Abimelek a kan rijiyar ruwa wadda barorin Abimelek suka ƙwace, 26 Abimelek ya ce, “Ban san wanda ya yi wannan abu ba, ba ka faɗa mini ba, ban kuwa taɓa ji ba sai yau.” 27 Ibrahim ya ɗibi tumaki da takarkarai ya bai wa Abimelek, su biyu ɗin kuwa suka yi alkawari. 28 Ibrahim ya ware 'yan raguna bakwai daga cikin garke. 29 Abimelek ya ce wa Ibrahim, “Ina ma'anar waɗannan 'yan raguna bakwai da ka keɓe?” 30 Ya ce, “Waɗannan 'yan raguna bakwai za ka karɓe su daga hannuna domin su zama shaida a gare ni, cewa, ni na haƙa rijiyan nan.” 31 Don haka aka kira wannan wuri Biyer-sheba, domin a can ne su duka suka yi rantsuwa. 32 Saboda haka suka yi alkawari a Biyer-sheba. Sai Abimelek, tare da Fikol shugaban sojojinsa, ya tashi ya koma ƙasar Filistiyawa. 33 Ibrahim kuma ya dasa itacen tsamiya a Biyer-sheba, a can ya yi kira bisa sunan Ubangiji, Allah Madawwami. 34 Ibrahim kuwa ya daɗe yana baƙunci a ƙasar Filistiyawa.

Farawa 22

An Umarci Ibrahim ya yi Hadaya da Ishaku

1 Bayan waɗannan al'amura Allah ya jarraba Ibrahim ya ce masa, “Ibrahim!” Sai ya ce, “Ga ni.” 2 Ya ce, “Ɗauki ɗanka, tilon ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi ƙasar Moriya, a can za ka miƙa shi hadayar ƙonawa a bisa kan ɗayan duwatsun da zan faɗa maka.” 3 Sai Ibrahim ya tashi tun da sassafe, ya ɗaura wa jakinsa shimfiɗa ya kuwa ɗauki biyu daga cikin samarinsa tare da shi, da kuma ɗansa Ishaku, ya faskara itace na yin hadayar ƙonawa. Ya kuwa tashi ya tafi inda Allah ya faɗa masa. 4 A rana ta uku Ibrahim ya ta da idanunsa ya hangi wurin daga nesa. 5 Ibrahim ya ce wa samarinsa, “Ku tsaya nan wurin jakin, ni da saurayin za mu yi gaba mu yi sujada, sa'an nan mu komo wurinku.” 6 Ibrahim ya ɗauki itacen hadayar ƙonawa, ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuma ya ɗauki wuta da wuƙa a hannunsa. Dukansu biyu kuwa suka tafi tare. 7 Ishaku ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba!” Sai ya ce, “Ga ni, ɗana.” Ya ce, “Ga wuta, ga itace, amma ina ragon hadayar ƙonawa?” 8 Ibrahim ya ce, “Allah zai tanada wa kansa ragon hadayar ƙonawa, ya ɗana.” Sai su biyu suka tafi tare. 9 Sa'ad da suka zo wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya jera itace a kai. Ya ɗaure Ishaku ɗansa, ya sa shi a bisa itacen bagaden. 10 Sai Ibrahim ya miƙa hannu ya ɗauki wuƙar don ya yanka ɗansa. 11 Amma mala'ikan Ubangiji ya yi kiransa daga sama, ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai ya ce, “Ga ni.” 12 Ya ce, “Kada ka sa hannunka a kan saurayin, kada kuwa ka yi masa wani abu, gama yanzu na sani kai mai tsoron Allah ne, da yake ba ka ƙi ba da ɗanka, tilonka, a gare ni ba.” 13 Ibrahim ya ta da idanunsa, ya duba, ga rago kuwa a bayansa, da ƙahoni a sarƙafe cikin kurmi. Ibrahim kuwa ya tafi ya kamo ragon, ya miƙa shi hadayar ƙonawa maimakon ɗansa. 14 Sai Ibrahim ya sa wa wurin suna, “Ubangiji zai tanada,” kamar yadda ake faɗa har yau, “A bisa kan dutsen Ubangiji, za a tanada.” 15 Mala'ikan Ubangiji kuma ya sāke kiran Ibrahim, kira na biyu daga sama, 16 ya ce, “Na riga na rantse da zatina, tun da ka yi wannan, ba ka kuwa ƙi ba da tilon ɗanka ba, 17 hakika zan sa maka albarka, zan riɓaɓɓanya zuriyarka kamar taurarin sama, kamar yashi kuma a gāɓar teku. Zuriyarka za su mallaki ƙofar maƙiyanka, 18 ta wurin zuriyarka kuma al'umman duniya za su sami albarka, saboda ka yi biyayya da umarnina.” 19 Sai Ibrahim ya koma wurin samarinsa. Suka tashi suka tafi Biyer-sheba tare. Ibrahim ya yi zamansa a Biyer-sheba.

Zuriyar Nahor

20 Ana nan bayan waɗannan al'amura, aka faɗa wa Ibrahim, “Ga shi, Milka ta haifa wa ɗan'uwanka Nahor, 'ya'ya. 21 Uz ɗan fari, da Buz ɗan'uwansa, da Kemuwel mahaifin Aram, 22 da Kesed, da Hazo, da Fildash, da Yidlaf, da Betuwel.” 23 Betuwel kuwa ya haifi Rifkatu, su takwas ɗin nan Milka ta haifa wa Nahor, ɗan'uwan Ibrahim. 24 Banda haka, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifi Teba, da Gaham, da Tahash, da Ma'aka.

Farawa 23

Ibrahim ya Sayi Makabarta a Rasuwar Saratu

1 Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya, 2 sa an nan ta rasu a Kiriyat-arba, wato, Hebron, a ƙasar Kan'ana. Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makoki, yana baƙin ciki domin Saratu. 3 Ibrahim ya bar gawar matarsa, ya je ya ce wa Hittiyawa, 4 “Ni baƙo ne, ina tsakaninku, ina zaman baƙunci. Ku sayar mini da wurin yin makabarta, domin in binne matata, in daina ganinta!” 5 Hittiyawa suka amsa wa Ibrahim suka ce, 6 “Ka ji mu, ya shugaba, gama kai yardajjen Allah ne a tsakaninmu. Ka binne matarka a kabari mafi kyau na kaburburanmu, ba waninmu da zai hana maka kabarinsa, ko ya hana ka ka binne matarka.” 7 Ibrahim ya tashi ya sunkuya wa Hittiyawa, mutanen ƙasar. 8 Sai ya ce musu, “Idan kun yarda in binne matata in daina ganinta, to, ku ji ni, ku roƙar mini Efron Bahitte ɗan Zohar, 9 ya ba ni kogon Makfela nasa na can ƙarshen saurarsa. Bari ya sallama mini wurin a gabanku a cikakken kuɗinsa, ya zama mallakata domin makabarta.” 10 A sa'an nan Efron yana tare da Hittiyawa. Sai Efron Bahitte ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan Hittiyawa, da gaban dukan waɗanda suke shiga ta ƙofar birninsa, ya ce, 11 “Ba haka ba ne, ya shugaba, ka ji ni. Na ba ka saurar, da kogon da yake cikinta. A gaban jama'ata na ba ka ita, ka binne matarka.” 12 Ibrahim kuwa ya sunkuya a gaban jama'ar ƙasar. 13 Ya ce wa Efron, a kunnuwan jama'ar ƙasar, “In dai ka yarda, ka ji ni. Zan ba da kuɗin saurar. Ka karɓa daga gare ni don in binne matata a can.” 14 Efron ya amsa wa Ibrahim, 15 “Ya shugabana, ka ji ni, don ɗan yankin ƙasa na shekel ɗari huɗu, a bakin me yake, a tsakaninmu? Binne matarka.” 16 Ibrahim ya yarda da Efron. Ibrahim kuwa ya auna wa Efron yawan shekel da ya ambata a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu bisa ga nauyin da 'yan kasuwa suke amfani da shi a wancan lokaci. 17 Don haka saurar Efron da ke cikin Makfela wadda take gabashin Mamre, da saurar, da kogon da yake ciki, da dukan itatuwan da suke cikin saurar, iyakar girmanta duka 18 an tabbatar wa Ibrahim, cewa, mallakarsa ce a gaban Hittiyawa, a gaban dukan waɗanda suke shiga ta ƙofar birninsu. 19 Bayan wannan, Ibrahim ya binne Saratu matarsa a kogon da yake a saurar Makfela a gabashin Mamre, wato, Hebron, cikin ƙasar Kan'ana. 20 Da saurar, da kogon da yake cikinta, aka tabbatar wa Ibrahim mallakarsa ce don makabarta da iznin Hittiyawa.

Farawa 24

Aka Auro wa Ishaku Mata

1 Yanzu Ibrahim ya tsufa, ya kuwa kwana biyu. Ubangiji kuma ya sa wa Ibrahim albarka a cikin abu duka. 2 Ibrahim ya ce wa baransa, daɗaɗɗen gidansa wanda yake hukunta dukan abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata, 3 ka rantse da Ubangiji na sama da duniya, cewa, ba za ka auro wa ɗana mata daga 'yan matan Kan'aniyawa waɗanda nake zaune a tsakaninsu ba. 4 Amma za ka tafi ƙasata, daga cikin dangina ka auro wa ɗana Ishaku mata.” 5 Sai baransa ya ce masa, “Watakila matar ba za ta yarda ta biyo ni zuwa wannan ƙasa ba, tilas ke nan, in koma da ɗanka ƙasar da ka fito?” 6 Ibrahim ya ce masa, “Ka kiyaye wannan fa, kada ka kuskura ka koma da ɗana can. 7 Ubangiji Allah na Sama wanda ya ɗauke ni daga gidan mahaifina daga ƙasar haihuwata, wanda ya yi magana da ni ya kuma rantse mini, ‘Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa,’ shi zai aiki mala'ikansa a gabanka. Za ka kuwa auro wa ɗana mata daga can. 8 Amma idan matar ba ta yarda ta biyo ka ba, ka kuɓuta daga rantsuwan nan tawa. Kai dai kada ka koma da ɗana can.” 9 Sai baran ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar Ibrahim maigidansa, ya kuwa rantse masa zai yi. 10 Baran ya ɗibi raƙuma goma daga cikin raƙuman maigidansa. Ya tashi, yana ɗauke da tsaraba ta kowane irin abu mai kyau na maigidansa a hannunsa. Ya kama hanyar Mesofotamiya zuwa birnin Nahor. 11 Ya durƙusar da raƙumansa a bayan birnin, kusa da bakin rijiyar ruwa da maraice, wato, lokacin da mata sukan tafi ɗebo ruwa. 12 Sai ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim. 13 Ga shi kuwa, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa, ga kuma 'yan matan mutanen birnin suna fitowa garin ɗibar ruwa. 14 Bari budurwar da zan ce wa, ‘Ina roƙo, ki sauke tulunki domin in sha,’ wadda za ta ce, ‘Sha, zan kuma shayar da raƙumanka,’ bari ta zama ita ce wadda ka zaɓa wa baranka Ishaku. Ta haka zan sani ka nuna madawwamiyar ƙaunarka ga maigidana.” 15 Kafin ya rufe baki, sai ga Rifkatu wadda aka haifa wa Betuwel ɗan Milka, matar Nahor ɗan'uwan Ibrahim, ta fito da tulun ruwanta a bisa kafaɗarta. 16 Budurwa mai kyan tsari ce. Tana da kyan gani ƙwarai, budurwa ce, ba wanda ya taɓa saninta. Ta gangara zuwa rijiyar ta cika tulunta, ta hauro. 17 Sai baran ya tarye ta a guje, ya ce, “Roƙo nake, ki ba ni ruwa kaɗan daga cikin tulunki in sha.” 18 Ta ce, “Sha, ya shugabana.” Nan da nan ta sauke tulunta ta riƙe a hannunta, ta ba shi ya sha. 19 Sa'ad da ta gama shayar da shi, ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka kuma, har su gama sha.” 20 Sai nan da nan ta bulbule tulunta a cikin kwami, ta sāke sheƙawa a guje zuwa rijiyar, ta kuwa ɗebo wa raƙumansa duka. 21 Mutumin kuwa ya zura mata ido, shiru, yana so ya sani ko Allah ya arzuta tafiyarsa, ko kuwa babu? 22 Sa'ad da raƙuman suka gama sha, mutumin ya ɗauki zoben zinariya mai nauyin rabin shekel, ya sa mata a hanci. Ya kuma ɗauki mundaye biyu na shekel goma na zinariya ya sa a hannuwanta, 23 ya ce, “Ki faɗa mini ke 'yar gidan wace ce? Akwai masauki a gidan mahaifinki inda za mu sauka?” 24 Sai ta ce masa, “Ni 'yar Betuwel ce ɗan Milka wanda ta haifa wa Nahor.” 25 Ta ƙara da cewa, “Muna da isasshen baro da harawa duka, da kuma masauki.” 26 Mutumin ya yi ruku'u ya yi wa Ubangiji sujada, 27 ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa ga maigidana ba. Ubangiji ya bi da ni har zuwa gidan ɗan'uwan maigidana.” 28 Budurwar ta sheƙa a guje zuwa gida wurin mahaifiyarta ta faɗi waɗannan abubuwa. 29 Rifkatu kuwa tana da ɗan'uwa sunansa Laban. Sai Laban ya sheƙo zuwa wurin mutumin a bakin rijiya. 30 Sa'ad da ya ga zoben da mundaye da suke hannuwan 'yar'uwarsa, sa'ad da kuma ya ji maganar Rifkatu 'yar'uwarsa cewa, “Ga abin da mutumin ya faɗa mini,” sai ya je wurin. Ya kuwa same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar. 31 Ya ce masa, “Shigo, ya mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.” 32 Mutumin ya shiga gidan, Laban kuwa ya sauke raƙuman, ya ba shi baro da harawa domin raƙuma, da ruwa ya wanke ƙafafunsa da ƙafafun waɗanda suke tare da shi. 33 Aka sa abinci a gabansa domin ya ci, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Laban ya ce, “Faɗi maganarka.” 34 Ya ce, “Ni baran Ibrahim ne. 35 Ubangiji ya sa wa maigidana albarka ƙwarai, ya kuwa zama babba, ya ba shi garkunan tumaki da na shanu, da azurfa da zinariya, da barori mata da maza, da raƙuma da jakai. 36 Saratu ta haifa wa maigidana ɗa cikin tsufanta, a gare shi kuma ya ba da dukan abin da yake da shi. 37 Maigidana ya rantsar da ni da cewa, ‘Ba za ka auro wa ɗana mace daga cikin 'ya'yan Kan'aniyawa waɗanda nake zaune a ƙasarsu ba, 38 amma ka tafi gidan mahaifina da dangina, ka auro wa ɗana mace.’ 39 Sai na ce wa maigidana, ‘Watakila matar ba za ta biyo ni ba.’ 40 Amma ya amsa mini ya ce, ‘Ubangiji wanda nake tafiya a gabansa zai aiki mala'ikansa tare da kai, ya arzuta hanyarka, za ka kuwa auro wa ɗana mace daga cikin dangina daga gidan mahaifina. 41 Sa'an nan za ka kuɓuta daga rantsuwata. Sa'ad da ka zo wurin dangina, idan kuwa ba su ba ka ita ba, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’ 42 “Yau kuwa da na iso bakin rijiyar, sai na ce a raina, ‘Ya Ubangiji, Allah na shugabana Ibrahim, in nufinka ne ka arzuta tafiyata. 43 Ga ni, ina tsaye a bakin rijiyar kuwa, bari budurwar da za ta fito ɗibar ruwa, wadda in na ce mata, “Roƙo nake, ba ni ruwa kaɗan daga ruwan tulunki in sha,” 44 in ta amsa mini, “To, sha, zan ɗebo wa raƙumanka kuma,” bari ta zama ita ce wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’ 45 Kafin in gama tunani a zuciyata, sai ga Rifkatu ta fito ɗauke da tulun ruwa a kafaɗarta, ta gangara zuwa rijiya ta ɗebo. Na ce mata, ‘Roƙo nake, ki ba ni, in sha.’ 46 Nan da nan ta sauke tulunta daga kafaɗarta, ta ce, ‘To, sha, zan kuma shayar da raƙumanka.’ Na sha, ta kuma shayar da raƙuman. 47 Na kuwa tambaye ta, ‘'Yar gidan wane ne ke?’ Ta ce, ‘Ni 'yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ Sai na sa mata zobe a hanci, mundaye kuma a hannu. 48 Sa'an nan na yi ruku'u, na yi wa Ubangiji sujada, na yabi Ubangiji Allah na maigidana, Ibrahim, wanda ya bishe ni a hanya sosai, in auro wa ɗansa 'yar danginsa. 49 Yanzu fa, idan za ku amince ku gaskata da maigidana, ku faɗa mini, in ba haka ba, sai ku faɗa mini, domin in san abin yi, in juya dama ko hagu.” 50 Laban da Betuwel suka amsa suka ce, “Wannan al'amari daga Ubangiji ne, ba mu da iko mu ce maka i, ko a'a. 51 Ga Rifkatu nan gabanka, ka ɗauke ta ku tafi, ta zama matar ɗan maigidanka, bisa ga faɗar Ubangiji.” 52 Sa'ad da baran Ibrahim ya ji wannan, ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya yi sujada a gaban Ubangiji. 53 Sai baran ya kawo kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, ya bai wa Rifkatu, ya kuma ba ɗan'uwanta da mahaifiyarta kayan ado masu tsada. 54 Shi da mutanen da suke tare da shi suka ci suka sha, suka kwana wurin. Da suka tashi da safe, sai ya ce, “A sallame ni, in koma wurin maigidana.” 55 Ɗan'uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Ka bar budurwar tare da mu har ɗan lokaci, kada ya gaza kwana goma, bayan wannan ta tafi.” 56 Amma ya ce musu, “Kada ku makarar da ni, tun da yake Allah ya arzuta tafiyata, a sallame ni domin in koma wurin maigidana.” 57 Suka ce, “Za mu kira budurwar mu tambaye ta.” 58 Suka kirawo Rifkatu suka ce mata, “Za ki tafi tare da wannan mutum?” Sai ta ce, “Zan tafi.” 59 Suka kuwa sallami Rifkatu 'yar'uwarsu da uwar goyonta, da baran Ibrahim da mutanensa. 60 Suka sa wa Rifkatu albarka, suka ce mata, “'Yar'uwarmu, ki zama mahaifiyar dubbai, Har dubbai goma, Bari zuriyarki kuma su gāji ƙofofin maƙiyansu!” 61 Sai Rifkatu da kuyanginta suka tashi suka hau raƙuman, suka bi mutumin. Haka nan kuwa baran ya ɗauki Rifkatu ya koma. 62 A lokacin kuwa Ishaku ya riga ya zo daga Biyer-lahai-royi yana zaune a Negeb. 63 A gabatowar maraice, sai Ishaku ya fita saura ya yi tunani, ya ɗaga idanunsa ya duba, ya ga raƙuma suna zuwa. 64 Da Rifkatu ta ɗaga idanunta, ta hangi Ishaku, sai ta sauka daga raƙumi, 65 ta ce wa baran, “Wane ne mutumin can da yake zuwa daga saura garin ya tarye mu?” Sai baran ya ce, “Ai, maigidana ne.” Ta ɗauki mayafinta ta yi lulluɓi. 66 Sai baran ya faɗa wa Ishaku dukan abin da ya yi. 67 Ishaku kuwa ya shiga da ita cikin alfarwarsa ya ɗauki Rifkatu ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta. Ta haka Ishaku ya ta'azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

Farawa 25

Sauran Zuriyar Ibrahim

1 Ibrahim ya auro wata mace kuma, sunanta Ketura. 2 Ta haifa masa Zimran, da Yokshan, da Medan, da Madayana, da Yisbak, da Shuwa. 3 Yokshan ya haifi Sheba da Dedan. 'Ya'yan Dedan su ne Asshurim, da Letushim, da Le'umomim. 4 'Ya'yan Madayana su ne Efa, da Efer, da Hanok, da Abida, da Eldaya. Waɗannan duka 'ya'yan Ketura ne. 5 Ibrahim ya ba Ishaku dukan abin da yake da shi. 6 Amma ga 'ya'yan ƙwaraƙwarai Ibrahim ya ba da kyautai, ya sallame su tun yana da rai, su tafi nesa da Ishaku zuwa can cikin ƙasar gabas.

Rasuwar Ibrahim da Jana'izarsa

7 Waɗannan su ne kwanakin shekarun Ibrahim a duniya, shekara ɗari da saba'in da biyar. 8 Ibrahim ya ja numfashinsa na ƙarshe ya kuwa rasu cikin kyakkyawan tsufa, tsoho ne mai shekaru masu yawa, aka kai shi ga jama'arsa, waɗanda suka riga shi. 9 Ishaku da Isma'ilu 'ya'yansa suka binne shi a kogon Makfela a saurar Efron ɗan Zohar Bahitte, gabashin Mamre, 10 wato, saurar da Ibrahim ya saya a wurin Hittiyawa. Can ne aka binne Ibrahim gab da Saratu matarsa. 11 Bayan rasuwar Ibrahim, Allah ya sa wa Ishaku ɗansa albarka. Ishaku kuwa ya zauna a Biyer-lahai-royi.

Zuriyar Isma'ilu

12 Waɗannan su ne zuriyar Isma'ilu ɗan Ibrahim, wanda Hajaratu Bamasariya, baranyar Saratu, ta haifa wa Ibrahim. 13 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Isma'ilu, maza, bisa ga haihuwarsu. Nebayot ɗan farin Isma'ilu, da Kedar, da Adbeyel, da Mibsam, 14 da Mishma, da Duma, da Massa, 15 da Hadad, da Tema, da Yetur, da Nafish, da Kedema. 16 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Isma'ilu, bisa ga ƙauyukansu da zangonsu, hakimai goma sha biyu, bisa ga kabilansu. 17 Waɗannan su ne shekarun Isma'ilu a duniya, shekara ɗari da talatin da bakwai, ya ja numfashinsa na ƙarshe ya rasu, aka kai shi ga jama'arsa waɗanda suka riga shi. 18 Mazauninsa a tsakanin Hawila ne da Shur, wanda yake ɗaura da Masar wajen Assuriya. Suka ware daga danginsu suka yi zamansu.

Haihuwar Isuwa da Yakubu

19 Waɗannan su ne zuriyar Ishaku ɗan Ibrahim, Ibrahim ya haifi Ishaku. 20 Ishaku yana da shekara arba'in sa'ad da ya auri Rifkatu, 'yar Betuwel Ba'aramiye daga Fadan-aram 'yar'uwar Laban Ba'aramiye. 21 Ishaku kuwa ya yi addu'a ga Ubangiji domin matarsa Rifkatu, da shike ita bakarariya ce. Ubangiji ya ji addu'arsa, sai matarsa Rifkatu ta yi ciki. 22 'Ya'yan kuwa suka kama kokawa da juna a cikinta, har ta ce, “In haka ne don me zan rayu?” Sai ta je ta tambayi Ubangiji. 23 Sai Ubangiji ya ce mata, “Al'umma biyu suke a cikin mahaifarki, mutum biyu da za ki haifa, za su rabu da juna, ɗayan zai fi ɗayan ƙarfi, babban zai bauta wa ƙaramin.” 24 Sa'ad da kwanakin haihuwarta suka cika, sai ga shi, ashe, tagwaye ne suke a cikin mahaifarta. 25 Na farin ya fito ja wur kamar riga mai gashi, saboda haka suka raɗa masa suna Isuwa. 26 Daga baya kuma ɗan'uwansa ya fito, hannunsa na riƙe da diddigen Isuwa, saboda haka aka raɗa masa suna Yakubu. Ishaku yana da shekara sittin sa'ad da ya haife su.

Isuwa ya Sayar da Matsayinsa na Ɗan Fari

27 Sa'ad da yaran suka yi girma, Isuwa ya zama ƙwararren maharbi, ya zama mutumin jeji, Yakubu kuwa kintsattse ne mai son zaman gida. 28 Ishaku ya ƙaunaci Isuwa saboda yakan ci naman da ya farauto, amma Rifkatu ta ƙaunaci Yakubu. 29 Wata rana, sa'ad da Yakubu yake dafa fate, Isuwa ya komo daga jeji, yana jin yunwa ƙwarai. 30 Sai Isuwa ya ce wa Yakubu, “Ka ɗibar mini jan fatenka in sha, gama ina fama da yunwa!” Saboda haka aka kira sunansa Edom. 31 Yakubu ya ce, “Sai dai ko in yau za ka sayar mini da matsayinka na ɗan fari.” 32 Sai Isuwa ya ce, “Ni da nake bakin mutuwa, wane amfani matsayina na ɗan fari zai yi mini?” 33 Yakubu ya ce, “Yau sai ka rantse mini.” Sai ya rantse masa ya kuwa sayar wa Yakubu da matsayinsa na ɗan fari. 34 Sa'an nan Yakubu ya ba Isuwa gurasa da faten wake, ya ci ya sha, ya tashi ya yi tafiyarsa. Ta haka Isuwa ya banzatar da matsayinsa na ɗan fari.

Farawa 26

Ishaku a Gerar da Biyer-sheba

1 Aka sāke yin yunwa a ƙasar, banda wadda aka yi a zamanin Ibrahim. Sai Ishaku ya tafi Gerar wurin Abimelek, Sarkin Filistiyawa. 2 Ubangiji kuwa ya bayyana gare shi, ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar, ka zauna a ƙasar da zan faɗa maka. 3 Ka yi baƙunci cikin wannan ƙasa, ni kuwa zan kasance tare da kai, zan sa maka albarka, gama a gare ka da zuriyarka ne na ba da waɗannan ƙasashe, zan kuwa cika rantsuwar da na yi wa Ibrahim mahaifinka. 4 Zan riɓaɓɓanya zuriyarka kamar taurarin sararin sama, zan kuwa ba zuriyarka dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin zuriyarka kuma al'umman duniya duka za su sami albarka, 5 saboda Ibrahim ya yi biyayya da muryata, ya kuma kiyaye umarnina, da dokokina, da ka'idodina, da shari'una.” 6 Ishaku ya yi zamansa a Gerar. 7 Sa'ad da mutanen wurin suka tambaye shi matarsa, ya ce, “Ita 'yar'uwata ce,” gama yana jin tsoro ya ce, “Ita matata ce,” don kada mutanen wurin su kashe shi saboda Rifkatu, da yake ita kyakkyawa ce. 8 Sa'ad da ya dakata 'yan kwanaki a can, sai Abimelek, Sarkin Filistiyawa ya duba ta taga, ya ga Ishaku ya rungumi Rifkatu. 9 Sai Abimelek ya kira Ishaku, ya ce, “Ashe lalle ita matarka ce, ƙaƙa fa ka ce, ‘Ita 'yar'uwata ce?’ ” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.” 10 Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ai, da wani daga jama'a ya kwana da matarka a sawwaƙe, da ka jawo laifi a bisanmu.” 11 Abimelek ya umarci dukan mutane ya ce, “Duk wanda ya taɓa mutumin nan ko matarsa, za a kashe shi.” 12 Ishaku ya yi shuka a waccan ƙasar, a shekarar nan kuwa ya girbe cikakken amfani. Ubangiji ya sa masa albarka, 13 har mutumin ya arzuta, ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri. 14 Da yake ya yi ta arzuta da garken tumaki, da na shanu, da iyali masu yawa, Filistiyawa suka ji ƙyashinsa. 15 Saboda haka, Filistiyawa don kishi sai suka ciccike rijiyoyin da ƙasa, waɗanda barorin mahaifinsa, Ibrahim, suka haƙa tun Ibrahim yana da rai. 16 Abimelek kuwa ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu, gama ka fi ƙarfinmu.” 17 Don haka Ishaku ya bar wurin, ya yi zango cikin kwarin Gerar, ya yi zamansa a can. 18 Sai Ishaku ya sāke haƙa rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa sun tattoshe su bayan rasuwar Ibrahim. Ishaku kuma ya sa wa rijiyoyin sunayen da mahaifinsa ya sa musu. 19 Amma sa'ad da barorin Ishaku suka haƙa rijiya a kwarin, sai suka tarar da idon ruwa. 20 Makiyayan Gerar kuwa suka yi faɗa da makiyayan Ishaku, suna cewa, “Ruwan namu ne.” Saboda haka Ishaku ya sa wa rijiyar suna Esek, domin sun yi jayayya a kanta. 21 Suka haƙa wata rijiya, suka yi jayayya a kan wannan kuma, ya sa mata suna Sitna. 22 Sai ya zakuɗa daga nan ya haƙa wata rijiya kuma, amma ba su yi jayayya a kan wannan ba, don haka ya sa mata suna Rehobot, yana cewa, “Gama yanzu Ubangiji ya yalwata mana, za mu hayayyafa a ƙasa.” 23 Daga nan ya haura zuwa Biyer-sheba. 24 Da daren nan Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka, kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan sa maka albarka in riɓaɓɓanya zuriyarka saboda bawana Ibrahim.” 25 Ishaku ya gina bagade a wurin ya kira bisa sunan Ubangiji, a can kuwa ya kafa alfarwarsa. A can ne kuma barorin Ishaku suka haƙa rijiya.

Yarjejeniya tsakanin Ishaku da Abimelek

26 Abimelek ya zo daga Gerar tare da Ahuzat mashawarcinsa da Fikol shugaban sojojinsa, don ya ga Ishaku. 27 Sai Ishaku ya ce musu, “Me ke tafe da ku zuwa gare ni, ga shi kun ƙi ni, kun kuma kore ni nesa da ku?” 28 Suka ce, “Lalle, mun gani a fili Ubangiji yana tare da kai, saboda haka muke cewa, bari rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai, bari kuma mu ƙulla alkawari da kai, 29 cewa, ba za ka cuce mu ba, daidai kamar yadda ba mu taɓe ka ba, ba mu yi maka kome ba sai alheri, muka kuwa sallame ka cikin salama. Yanzu, kai albarkatacce ne na Ubangiji.” 30 Sai ya shirya musu liyafa, suka ci suka sha. 31 Suka tashi tun da sassafe suka rantse wa juna, Ishaku ya sallame su, suka tafi cikin salama. 32 Ya zama kuwa a wannan rana, barorin Ishaku suka zo suka faɗa masa zancen rijiyar da suka haƙa, suka ce masa, “Mun sami ruwa.” 33 Ya sa mata suna Sheba, domin haka har yau sunan birnin Biyer-sheba. 34 Sa'ad da Isuwa yake da shekara arba'in, ya auro Judit, 'yar Biyeri Bahitte, da Basemat 'yar Elon Bahitte, 35 suka baƙanta wa Ishaku da Rifkatu rai.

Farawa 27

Yakubu ya Karɓi Albarka daga wurin Ishaku

1 Lokacin da Ishaku ya tsufa, idanunsa kuma suka yi duhu har ba ya iya gani, sai ya kira Isuwa babban ɗansa, ya ce masa, “Ɗana!” Sai ya amsa, “Ga ni nan.” 2 Ishaku ya ce, “Ga shi, na tsufa, ban san ranar rasuwata ba. 3 Yanzu fa, ka ɗauki makamanka, da kwarinka da bakanka, ka tafi jeji ka farauto mini nama, 4 ka shirya mini abinci mai daɗi irin wanda nake so, ka kawo mini in ci, don in sa maka albarka kafin in rasu.” 5 Rifkatu kuwa tana ji lokacin da Ishaku yake magana da ɗansa Isuwa. Don haka, sa'ad da Isuwa ya tafi jeji garin ya farauto nama ya kawo, 6 sai Rifkatu ta ce wa ɗanta Yakubu, “Na ji mahaifinka ya yi magana da ɗan'uwanka Isuwa, ya ce, 7 ‘Kawo mini nama, ka shirya mini abinci mai daɗi in ci, in sa maka albarka a gaban Ubangiji kafin in rasu.’ 8 Yanzu fa, ɗana, ka biye wa maganata yadda zan umarce ka. 9 Je ka garke, ka kamo 'yan awaki biyu kyawawa, domin in shirya abinci mai daɗi da su domin mahaifinka, irin wanda yake so. 10 Kai kuwa ka kai wa mahaifinka, ya ci, domin ya sa maka albarka kafin ya rasu.” 11 Amma Yakubu ya ce wa Rifkatu mahaifiyarsa, “Ga shi fa, ɗan'uwana Isuwa gargasa ne, ni kuwa mai sulɓi ne. 12 Watakila, baba zai lallaluba ni, zai kuwa ce, ruɗinsa nake yi, in kuwa jawo wa kaina la'ana maimakon albarka.” 13 Sai mahaifiyarsa ta ce masa, “La'anarka ta faɗo bisa kaina, ɗana. Kai dai ka yi biyayya da maganata. Je ka, ka kamo mini.” 14 Ya tafi ya kamo su, ya kawo su ga mahaifiyarsa, mahaifiyarsa kuwa ta shirya abinci mai daɗi irin wanda mahaifinsa yake so. 15 Rifkatu ta ɗauki riguna mafi kyau na babban ɗanta Isuwa waɗanda suke wurinta cikin gida, ta kuwa sa wa Yakubu ƙaramin ɗanta su, 16 fatun 'yan awakin kuwa ta naɗe wa hannuwansa, da sashen dokin wuyansa mai sulɓi. 17 Sai ta bai wa ɗanta, Yakubu, abinci mai daɗin ci da gurasar da ta shirya. 18 Ya kuwa shiga wurin mahaifinsa, ya ce, “Baba.” Mahaifin ya ce, “Ga ni, wane ne kai, ya ɗana?” 19 Yakubu ya ce wa mahaifinsa, “Ni ne Isuwa ɗan farinka. Na yi yadda ka faɗa mini, in ka yarda ka tashi ka ci naman da na harbo, domin ka sa mini albarka.” 20 Amma Ishaku ya ce wa ɗansa, “Ƙaƙa aka yi ka same shi da sauri haka, ɗana?” Sai ya amsa, “Domin Ubangiji, Allahnka, ya ba ni sa'a.” 21 Ishaku kuwa ya ce wa Yakubu, “Matso kusa in ka yarda, don in lallaluba ka, ɗana, domin in hakikance ko kai ne ɗana Isuwa, ko babu.” 22 Saboda haka Yakubu ya matsa kusa da Ishaku mahaifinsa, sai ya lallaluba shi, ya ce, “Murya, muryar Yakubu ce, amma hannuwa, hannuwan Isuwa ne.” 23 Amma bai gane shi ba, gama hannuwansa gargasa ne kamar hannuwan ɗan'uwansa Isuwa, saboda haka ya sa masa albarka. 24 Ya ce, “Hakika, kai ne ɗana Isuwa?” Ya amsa, “Ni ne.” 25 Ya ce, “Kawo mini naman da ka harbo, in ci in sa maka albarka.” Sai ya kawo masa, ya kuwa ci, ya kawo masa ruwan inabi, ya sha. 26 Mahaifinsa Ishaku kuwa ya ce masa, “Zo kusa ka sumbace ni, ɗana.” 27 Don haka ya zo kusa ya sumbace shi. Ishaku ya sansana rigunansa, ya sa masa albarka, ya ce, “Duba, ƙanshin ɗana Yana kama da ƙanshin jeji Wanda Ubangiji ya sa wa albarka! 28 Allah ya ba ka daga cikin raɓar sama, Daga cikin ni'imar ƙasa, Da hatsi a yalwace da ruwan inabi. 29 Bari jama'a su bauta maka, Al'ummai kuma su sunkuya maka. Za ka yi shugabancin 'yan'uwanka, Allah ya sa 'ya'yan mahaifiyarka su sunkuya maka. La'ananne ne dukan wanda ya la'anta ka, Albarkatacce ne dukan wanda ya sa maka albarka.” 30 Ishaku yana gama sa wa Yakubu albarka, Yakubu yana fita daga gaban mahaifinsa ke nan sai ga Isuwa ɗan'uwansa ya komo daga farauta. 31 Shi kuma ya shirya abinci mai daɗin ci, ya kawo wa mahaifinsa. Sai ya ce wa mahaifinsa, “In ka yarda baba, ka tashi, ka ci naman da na harbo don ka sa mini albarka.” 32 Mahaifinsa Ishaku ya ce masa, “Wane ne kai?” Ya amsa, “Ni ne ɗanka, ɗan farinka, Isuwa.” 33 Ishaku kuwa ya yi makyarkyata ƙwarai, ya ce, “Wane ne wannan fa, da ya farauto naman ya kawo mini, na kuwa cinye kafin ka zo, har na sa masa albarka?�I, albarkatacce zai zama.” 34 Da Isuwa ya ji kalmomin mahaifinsa, sai ya yi k�wwa da kuka mai tsananin gaske, ya ce wa mahaifinsa, “Ka sa mini albarka, har da ni ma, ya babana.” 35 Amma ya ce, “Ɗan'uwanka ya zo cikin makirci, ya karɓe albarkarka.” 36 Isuwa ya ce, “Ba saboda haka ne aka raɗa masa suna Yakubu ba? Gama sau biyu ke nan yake yi mini ƙwace. Ya ƙwace mini matsayina na ɗan fari, ga shi kuma, yanzu ya ƙwace mini albarkata.” Sa'an nan ya ce, “Ba sauran albarkar da ka rage mini?” 37 Ishaku ya amsa wa Isuwa ya ce, “Ga shi, na shugabantar da shi a kanka da dukan 'yan'uwansa na ba shi su, su zama barorinsa, na ba shi hatsi da ruwan inabi. Me zan yi maka kuma, ya ɗana?” 38 Sai Isuwa ya ce wa mahaifinsa, “Iyakar albarkar da kake da ita ke nan, baba? Har da ni ma ka sa mini albarka, babana.” Isuwa ya ta da murya ya yi kuka. 39 Sai Ishaku mahaifinsa ya amsa masa ya ce, “Ga shi, ni'imar ƙasar za ta nisanci mazauninka, Raɓar samaniya can ƙwanƙoli za ta nisance ka. 40 Ta wurin takobinka za ka rayu Za ka yi wa ɗan'uwanka barantaka, Amma sa'ad da ka ɓalle, Za ka kakkarye karkiyarsa daga wuyanka.” 41 Isuwa dai ya ƙi jinin Yakubu saboda albarkar da mahaifinsa ya sa masa. Sai Isuwa ya ce a ransa, “Kwanakin makoki domin mahaifina suna gabatowa, sa'an nan zan kashe Yakubu ɗan'uwana.” 42 Amma maganganun Isuwa babban ɗanta suka kai a kunnen Rifkatu. Saboda haka, sai ta aika aka kirawo Yakubu ƙaramin ɗanta. Ta ce masa, “Ga shi, ɗan'uwanka Isuwa, yana ta'azantar da kansa da nufin ya kashe ka, ya ɗau fansa. 43 Domin haka, ɗana, ka ji muryata, ka tashi ka gudu zuwa wurin Laban ɗan'uwana a Haran, 44 ka zauna tare da shi 'yan kwanaki, har zafin fushin ɗan'uwanka ya huce, 45 ya manta da abin da ka yi masa, sa'an nan zan aika in komo da kai daga can. Don me zan rasa ku, ku biyu a rana ɗaya?”

Ishaku ya Aika da Yakubu wurin Laban

46 Rifkatu kuwa ta ce wa Ishaku, “Na gaji da raina saboda matan Hittiyawa. Idan Yakubu zai auri ɗaya daga cikin waɗannan mata na Hittiyawa, wato, daga matan ƙasar, wane amfani raina zai daɗa mini?”

Farawa 28

1 Ishaku ya kira Yakubu ya sa masa albarka, ya umarce shi da cewa, “Ba za ka auri ɗaya daga cikin 'ya'yan matan Kan'aniyawa ba. 2 Tashi, ka tafi Fadan-aram, zuwa gidan Betuwel kakanka na wajen mahaifiya, ka zaɓo wa kanka mata daga cikin 'ya'ya mata na Laban ɗan'uwan mahaifiyarka a can. 3 Allah Maɗaukaki ya sa maka albarka, ya sa ka hayayyafa ya riɓaɓɓanya ka, ka zama ƙungiyar jama'o'i, 4 ya kuma sa ka sami albarkar Ibrahim da zuriyarka tare da kai, har da za ka amshe ƙasar baƙuncinka wadda Allah ya bai wa Ibrahim!” 5 Da haka, Ishaku ya sallami Yakubu, ya kuwa tafi Fadan-aram wurin Laban, ɗan Betuwel Ba'aramiye ɗan'uwan Rifkatu, mahaifiyar Yakubu da Isuwa.

Isuwa ya Ƙara Auro Wata

6 Yanzu Isuwa ya ga Ishaku ya sa wa Yakubu albarka, ya kuwa sallame shi zuwa Fadan-aram domin ya auro mace daga can. Da Isuwa ya ga Ishaku ya sa wa Yakubu albarka ya kuma umarce shi da cewa, “Ba za ka auro wata daga cikin 'yan matan Kan'aniyawa ba,” 7 ya kuma ga Yakubu ya biye wa mahaifinsa da mahaifiyarsa, har ya tafi Fadan-aram, 8 sai Isuwa ya gane 'yan matan Kan'aniyawa ba su gamshi Ishaku mahaifinsa ba. 9 Saboda haka Isuwa ya tafi wurin Isma'ilu ya auro Mahalat 'yar'uwar Nebayot, 'yar Isma'ilu ɗan Ibrahim, banda matan da yake da su.

Mafarkin Yakubu a Betel

10 Yakubu ya bar Biyer-sheba ya kama hanya zuwa Haran. 11 Da ya isa wani wuri, sai ya kwana can a wannan dare, don rana ta riga ta faɗi. Ya ɗauki ɗaya daga cikin duwatsun da suke wurin, ya yi matashin kai da shi, ya kwanta, ya yi barci. 12 Ya yi mafarki, ga wani tsani tsaye daga ƙasa, kansa ya kai sama, sai ga mala'ikun Allah suna hawa da sauka ta kansa! 13 Ga shi kuwa, Ubangiji na tsaye a kansa yana cewa, “Ni ne Ubangiji, Allah na Ibrahim, mahaifinka, da Ishaku, ƙasar da kake kwance a kai, zan ba ka ita da zuriyarka. 14 Zuriyarka kuwa za su zama kamar turɓayar ƙasa, za su kuma bazu zuwa gabas da yamma, kudu da arewa. Ta wurinka da zuriyarka, iyalan duniya duka za su sami albarka. 15 Ga shi, ina tare da kai, zan kiyaye ka duk inda ka tafi, zan kuwa komo da kai ƙasar nan, gama ba zan rabu da kai ba, sai na aikata abin nan da na hurta maka.” 16 Yakubu ya farka daga barcinsa, ya ce, “Hakika, Ubangiji yana wurin nan, ni kuwa ban sani ba.” 17 Ya tsorata, sai ya ce, “Wane irin wuri ne wannan mai banrazana haka! Ba shakka wannan wurin Allah ne, nan ne kuma ƙofar Sama.” 18 Sai Yakubu ya tashi tun da sassafe, ya ɗauki dutsen da ya yi matashin kai da shi, ya kafa shi al'amudi, ya kuwa zuba mai a kan al'amudin. 19 Ya kira sunan wurin nan Betel, amma da farko, sunan birnin, Luz. 20 Yakubu ya yi wa'adi da cewa, “Idan Allah zai kasance tare da ni, ya kiyaye ni cikin tafiyan nan da nake yi, ya kuma ba ni abincin da zan ci, da suturar da zan sa, 21 har kuma in sāke komowa gidan mahaifina da salama, da Ubangiji ya zama Allahna, 22 wannan dutse kuwa wanda na kafa shi al'amudi zai zama wurin sujada ga Allah. Daga cikin dukan abin da ya ba ni, zan ba shi ushirinsa.”

Farawa 29

Yakubu ya Isa Gidan Laban

1 Yakubu kuwa ya ci gaba da tafiyarsa, har ya kai ƙasar Mesofotamiya. 2 Da ya duba haka sai ya ga rijiya cikin saura, ga kuwa garken tumaki uku suna daura da ita, gama daga cikin rijiyar nan ake shayar da garkunan. Murfin rijiyar, dutse ne, babba. 3 A sa'ad da garkunan suka tattaru a wurin, makiyayan sukan kawar da dutsen daga bakin rijiyar, su shayar da su, sa'an nan su mayar da dutsen a wurinsa, a bisa bakin rijiya. 4 Yakubu ya ce musu, “'Yan'uwana, daga ina kuka fito?” Suka ce, “Daga Haran muke.” 5 Sai ya ce musu, “Kun san Laban ɗan Nahor?” Suka ce, “Mun san shi.” 6 Ya ce musu, “Lafiyarsa ƙalau?” Suka ce, “I, lafiya ƙalau yake, ga ma Rahila 'yarsa, tana zuwa da bisashensa!” 7 Ya ce, “Ga shi kuwa, da sauran rana da yawa, lokacin tattaruwar dabbobi bai yi ba, me zai hana ku shayar da tumakin, ku sāke kai su wurin kiwo?” 8 Amma suka ce, “Ba za mu iya ba, sai sauran garkunan duka sun taru, sa'an nan a kawar da dutsen daga bakin rijiyar, sa'an nan mu shayar da garkuna.” 9 Kafin ya rufe baki, sai ga Rahila ta zo da bisashen mahaifinta, gama ita take kiwonsu. 10 Sa'ad da Yakubu ya ga Rahila, 'yar Laban kawunsa, da bisashen, sai Yakubu ya hau ya kawar da dutsen daga bakin rijiyar, ya shayar da garken Laban, kawunsa. 11 Yakubu kuwa ya sumbaci Rahila, ya fara kuka da ƙarfi. 12 Ya faɗa mata shi dangin mahaifinta ne, shi kuma ɗan Rifkatu ne, sai ta sheƙa ta faɗa wa mahaifinta. 13 Sa'ad da Laban ya sami labari a kan Yakubu ɗan 'yar'uwarsa, sai ya sheƙo ya tarye shi, ya rungume shi, ya sumbace shi, ya kawo shi a gidansa. Yakubu ya labarta wa Laban al'amura duka. 14 Laban ya ce masa, “Hakika, kai ƙashina ne da namana!” Yakubu ya zauna wata guda tara da Laban.

Yakubu ya yi wa Laban Barantaka domin Rahila da Lai'atu

15 Laban kuwa ya ce wa Yakubu, “Don kana dangina, za ka yi mini barantaka a banza? Ka faɗa mini, nawa zan biya ka?” 16 Laban dai yana da 'ya'ya mata biyu, sunan babbar Lai'atu, sunan ƙaramar kuwa Rahila. 17 Lai'atu dai ba kyakkyawa ba ce, amma Rahila kyakkyawa ce, dirarriya. 18 Yakubu ya ƙaunaci Rahila, sai ya ce wa Laban, “Zan yi maka barantaka shekara bakwai domin 'yarka Rahila.” 19 Laban ya ce, “Gara in ba ka ita da in ba wani dabam, zauna tare da ni.” 20 Saboda haka, ya yi barantaka shekara bakwai domin Rahila, amma a ganinsa kamar 'yan kwanaki ne saboda ƙaunar da yake mata. 21 Yakubu ya ce wa Laban, “Ba ni matata domin in shiga wurinta, domin lokacin da muka shirya ya cika.” 22 Sai Laban ya tattara mutanen wurin duka, ya yi biki. 23 Amma da maraice, ya ɗauki 'yarsa Lai'atu ya kawo ta wurin Yakubu, Yakubu ya shiga a wurinta. 24 (Laban ya ba 'yarsa Lai'atu Zilfa ta zama kuyangarta). 25 Da gari ya waye kuma ga shi, ashe, Lai'atu ce. Sai Yakubu ya ce wa Laban, “Mene ne wannan da ka yi mini? Ba don Rahila na yi maka barantaka ba? Don me ka yaudare ni?” 26 Laban ya ce, “A nan wurinmu ba a yin haka, a aurar da ƙarama kafin 'yar fari. 27 Ka jira, bayan kwana bakwai na lokacin auren sun wuce, sa'an nan za mu ba ka Rahila saboda barantakar da za ka yi mini shekara bakwai nan gaba.” 28 Yakubu kuwa ya yi haka ɗin, ya cikasa makon, sa'an nan Laban ya aurar masa da 'yarsa Rahila. 29 (Laban ya ba 'yarsa Rahila Bilha, kuyangarsa, ta zama kuyangarta). 30 Sai Yakubu ya shiga wurin Rahila, amma ya fi ƙaunar Rahila da Lai'atu. Ya yi wa Laban barantaka waɗansu shekara bakwai kuma.

An Haifa wa Yakubu 'Ya'ya

31 Sa'ad da Ubangiji ya ga ana ƙin Lai'atu, ya buɗe mahaifarta, amma Rahila bakarariya ce. 32 Lai'atu fa ta yi ciki ta haifi ɗa, ta raɗa masa suna Ra'ubainu, gama ta ce, “Saboda Ubangiji ya dubi wahalata, hakika, yanzu mijina zai ƙaunace ni.” 33 Ta sāke yin ciki, ta haifi ɗa, ta ce, “Saboda Ubangiji ya ji ana ƙina ya ba ni wannan ɗa kuma,” ta kuwa raɗa masa suna Saminu. 34 Sai kuma ta sāke yin ciki, ta haifi ɗa, ta ce, “Yanzu, a wannan karo mijina zai shaƙu da ni, domin na haifa masa 'ya'ya uku maza.” Saboda haka ta raɗa masa suna Lawi. 35 Har yanzu kuwa ta sāke yin ciki, ta haifi ɗa, ta ce, “A wannan lokaci zan yabi Ubangiji.” Saboda haka ta raɗa masa suna Yahuza. Daga nan sai ta daina haihuwa.

Farawa 30

1 Sa'ad da Rahila ta ga ba ta haihuwa, sai ta ji kishin 'yar'uwarta, ta kuma ce wa Yakubu, “Ka ba ni 'ya'ya, in kuwa ba haka ba, zan mutu!” 2 Fushin Yakubu ya yi ƙuna a kan Rahila, ya ce, “Ina daidai da Allah ne, wanda ya hana ki haihuwa?” 3 Sai ta ce, “Ga kuyangata Bilha, ka shiga wurinta, domin ta haihu bisa gwiwoyina, domin ni ma in sami 'ya'ya ta wurinta.” 4 Don haka ta ba shi Bilha ta zama matarsa. Yakubu kuwa ya shiga wurinta. 5 Bilha kuwa ta yi ciki, ta haifa wa Yakubu ɗa. 6 Rahila ta ce, “Allah ya baratar da ni, ya ji muryata, ya kuwa ba ni ɗa.” Saboda haka ta raɗa masa suna Dan. 7 Bilha, kuyangar Rahila, ta sāke yin ciki, ta haifa wa Yakubu ɗa na biyu. 8 Sai Rahila ta ce, “Da gawurtacciyar kokawa na yi kokawa da 'yar'uwata, har na yi rinjaye,” sai ta raɗa masa suna Naftali. 9 Sa'ad da Lai'atu ta ga ta daina haihuwa, sai ta ɗauki kuyangarta Zilfa, ta ba Yakubu ta zama matarsa. 10 Kuyangar Lai'atu, Zilfa, ta haifa wa Yakubu ɗa. 11 Lai'atu kuma ta ce, “Sa'a!” Saboda haka ta sa masa suna Gad. 12 Kuyangar Lai'atu ta sāke haifa wa Yakubu ɗa na biyu. 13 Lai'atu ta ce, “Ni mai farin ciki ce! Gama mata za su ce da ni mai farin ciki,” saboda haka ta raɗa masa suna Ashiru. 14 A kwanakin kakar alkama, Ra'ubainu ya fita ya samo manta mahaifiya a saura, ya kawo wa mahaifiyarsa Lai'atu. Sai Rahila ta ce wa Lai'atu, “Ina roƙonki, ɗiba mini daga cikin manta uwar da ɗanki ya samo.” 15 Amma ta ce mata, “Kanƙanen abu ne da kika ƙwace mini mijina? Za ki kuma ƙwace manta uwar da ɗana ya samo kuma?” Rahila ta ce, “To, in haka ne, bari ya kwana tare da ke a daren yau a maimakon manta uwar da ɗanki ya samo.” 16 Sa'ad da Yakubu ya komo daga saura da maraice, Lai'atu ta fita ta tarye shi, ta ce, “Sai ka shigo wurina, gama na riga na ijarar da kai da manta uwar da ɗana ya samo.” Saboda haka ya kwana tare da ita a daren nan. 17 Allah ya saurari Lai'atu, ta kuwa yi ciki ta haifa wa Yakubu ɗa na biyar. 18 Lai'atu ta ce, “Allah ya yi mini sakamako domin na ba da kuyangata ga mijina,” saboda haka ta raɗa masa suna Issaka. 19 Lai'atu ta sāke yin ciki ta kuwa haifa wa Yakubu ɗa na shida. 20 Sai Lai'atu ta ce, “Allah ya wadata ni da kyakkyawar baiwa, yanzu mijina zai darajanta ni, domin na haifa masa 'ya'ya maza shida,” ta raɗa masa suna Zabaluna. 21 Daga baya ta haifi 'ya mace, ta kuwa raɗa mata suna Dinatu. 22 Allah kuwa ya tuna da Rahila, ya saurare ta, ya buɗe mahaifarta. 23 Ta yi ciki ta haifa ɗa, ta ce, “Allah ya kawar da zargina,” 24 ta sa masa suna Yusufu, tana cewa, “Da ma a ce Ubangiji ya ƙara mini wani ɗa!”

Yakubu ya Yi Jinga da Laban

25 Bayan da Rahila ta haifi Yusufu, Yakubu ya ce wa Laban, “Ka sallame mu, domin mu tafi gidanmu a ƙasarmu. 26 Ka ba ni matana da 'ya'yana waɗanda na yi maka barantaka saboda su, ka bar mu mu tafi, ka dai san ɗawainiyar da na yi maka.” 27 Amma Laban ya ce masa, “Da za ka yarda mini, sai in ce, na fahimta bisa ga istihara, cewa, Ubangiji ya sa mini albarka saboda kai. 28 Ka faɗa mini ladanka in ba ka.” 29 Yakubu ya ce masa, “Kai da kanka ka san barantakar da na yi maka, yadda bisashenka suka yawaita a hannuna. 30 Gama kafin in zo, kana da 'yan kima ne, ga shi, sun ƙaru da yawa, Ubangiji kuwa ya sa maka albarka duk inda na juya. Amma yanzu, sai yaushe zan hidimta wa nawa gidan?” 31 Ya ce, “Me zan ba ka?” Yakubu ya ce, “Ba za ka ba ni kome ba, in da za ka yi mini wannan, sai in sāke kiwon garkenka in lura da shi, 32 bar ni, in ratsa garkenka duka yau, in keɓe dukan masu dabbare-dabbare da tumaki babare-babare, da kowane ɗan rago baƙi, da dabbare-dabbare da babare-babare na awaki, waɗannan ne za su zama ladana. 33 Ta haka amincina zai shaide ni a gabanka a sa'ad da ka zo bincike hakkina. Duk wanda aka iske ba dabbare-dabbare ba ne, kuma ba babare-babare ba ne cikin awaki, ba kuma baƙi ba ne a cikin raguna, in aka samu a wurina, sai a ɗauka, na sata ne.” 34 Laban ya ce, “Madalla! Bari ya kasance kamar yadda ka faɗa.” 35 Amma a ran nan Laban ya ware bunsuran da suke dabbare-dabbare da masu sofane, da dukan awakin da suke dabbare-dabbare da kyalloli, da dukan baƙaƙen tumaki, ya danƙa su a hannun 'ya'yansa maza, 36 ya sa nisan tafiya ta kwana uku tsakaninsu da Yakubu, Yakubu kuma ya ci gaba da kiwon sauran garken Laban. 37 Yakubu ya samo ɗanyun tsabgogin aduruku, da na katambiri, da na durumi, ya ɓare ya bayyanar da fararen zane-zanensu a fili. 38 Ya kafa tsabgogin da ya ɓare a gaban garkuna a magudana, wato, kwamame na banruwa, don sukan yi barbara a wurin sa'ad da suka zo shan ruwa. 39 Garkunan suka yi barbara a gaban tsabgogin, don haka garkunan sukan haifi masu zāne, dabbare-dabbare da masu sofane. 40 Yakubu kuwa yakeɓe 'yan raguna, ya sa garkuna su fuskanci tsabgogin da ya shasshauta, da dukan baƙaƙen da ke cikin garken Laban. Sai ya ware waɗanda suke nasa, bai kuwa haɗa su da garken Laban ba. 41 A kowane lokacin da ƙarfafan suke barbara Yakubu yakan sa tsabgogin a magudana a gaban idanun garken, domin su yi barbara a tsakanin tsabgogin. 42 Amma ga marasa ƙarfi na garken, ba ya sa musu. Don haka marasa ƙarfin ne na Laban, ƙarfafan kuwa na Yakubu. 43 Ta haka mutumin ya zama riƙaƙƙen mai arziki, yana da manya manyan garkuna da barori mata da maza, da raƙuma, da jakuna.

Farawa 31

Yakubu ya Gudu daga wurin Laban

1 Yakubu ya ji 'ya'yan Laban suna cewa, “Yakubu ya kwashe dukan abin da yake na mahaifinmu, daga cikin dukan abin da yake na mahaifinmu kuma ya sami dukiyarsa.” 2 Yakubu kuma ya ga ba shi da farin jini a wurin Laban kamar dā. 3 Ubangiji ya ce wa Yakubu, “Ka koma ƙasar kakanninka da danginka, ni kuwa ina tare da kai.” 4 Saboda haka Yakubu ya aika a kirawo Rahila da Lai'atu zuwa cikin saura inda garkensa yake, 5 ya ce musu, “Na ga ba ni da sauran farin jini wurin mahaifinku kamar dā. Amma Allah na mahaifina yana tare da ni. 6 Kun sani na yi wa mahaifinku barantaka da dukan ƙarfina, 7 duk da haka mahaifinku ya cuce ni, ya yi ta sassauya ladana har sau goma, amma Allah bai ba shi ikon zambatata ba. 8 In ya ce, ‘Dabbare-dabbare, su ne ladanka,’ duk garken sai ya haifi dabbare-dabbare, in kuma ya ce ‘masu sofane ne ladanka,’ sai garken duka ya haifi masu sofane. 9 Ta haka Allah ya kwashe dukiyar mahaifinku ya ba ni. 10 “A lokacin ɗaukar cikin garke, cikin mafarki na ta da idanuna, na kuwa gani cikin mafarkin, bunsuran da suke hawan garke, masu sofane, da dabbare-dabbare da roɗi-roɗi ne. 11 Sai mala'ikan Allah ya ce mini a cikin mafarki, ‘Yakubu,’ sai na ce, ‘Ga ni.’ 12 Ya kuwa ce, ‘Ta da idanunka ka gani, dukan bunsuran da ke hawan awaki masu sofane ne, dabbare-dabbare da roɗi-roɗi, gama na ga dukan abin da Laban yake yi maka. 13 Ni ne Allah na Betel, inda ka zuba wa dutsen mai, ka kafa shi al'amudi, ka kuma rantse mini. Yanzu fa tashi ka fita daga cikin ƙasar nan, ka koma ƙasar haihuwarka.’ ” 14 Rahila da Lai'atu suka amsa masa, “Akwai wani rabo, ko gādon da ya rage mana a cikin gidan mahaifinmu? 15 Ba ga shi ma, sai kamar baƙi yake ɗaukarmu ba? Gama ya sayar da mu, yana kuwa morar kuɗin da aka bayar dominmu. 16 Dukan dukiyar da Allah ya kwashe daga wurin mahaifinmu, tamu ce da 'ya'yanmu, yanzu fa, kome Allah ya faɗa maka, sai ka yi.” 17 Sai Yakubu ya tashi, ya ɗauki 'ya'yansa, da matansa a bisa raƙumansa, 18 ya kora shanunsa duka, da dukan bisashen da ya samu, da shanu da suke nasa, waɗanda ya samu a Fadan-aram a ƙasar Mesofotamiya, zuwa ƙasar Kan'ana wurin mahaifinsa Ishaku. 19 Amma a sa'an nan Laban ya riga ya tafi ya yi wa tumakinsa sausaya, sai Rahila ta sace gumakan gidan mahaifinta. 20 Yakubu kuwa ya yaudari Laban Ba'aramiye da bai sanar da shi zai gudu ba. 21 Ya gudu da dukan abin da yake da shi, ya tashi ya haye Yufiretis, ya miƙe zuwa ƙasar Gileyad ta tuddai.

Laban ya Bi Sawun Yakubu

22 Sa'ad da aka sanar da Laban, cewa, Yakubu ya gudu da kwana uku, 23 sai ya ɗauki danginsa tare da shi, ya bi sawunsa har kwana bakwai, yana biye da shi kurkusa har zuwa ƙasar Gileyad ta tuddai. 24 Amma Allah ya zo wurin Laban Ba'aramiye cikin mafarki da dad dare, ya ce masa, “Ka kula fa, kada ka ce wa Yakubu kome, ko nagari ko mugu.” 25 Sai Laban ya ci wa Yakubu. A yanzu Yakubu ya riga ya kafa alfarwarsa a ƙasa ta tuddai, Laban da danginsa kuma suka yi zango a ƙasar Gileyad ta tuddai. 26 Laban ya ce wa Yakubu, “Me ka yi ke nan, da ka cuce ni, ka gudu da 'ya'yan matana kamar kwason yaƙi? 27 Me ya sa ka gudu a ɓoye? Ka cuce ni, ba ka kuwa faɗa mini ba, ai, da na sallame ka da farin ciki, da waƙe-waƙe, da kiɗa, da garaya. 28 Don me ba ka bari na sumbaci 'ya'yana mata da maza na yi bankwana da su ba? Kai! Ka yi aikin wauta. 29 Ina da iko in yi maka lahani, amma Allah na mahaifinka, ya yi magana da ni a daren jiya, yana cewa, ‘Ka kula fa kada ka ce wa Yakubu kome, ko nagari ko mugu.’ 30 Amma yanzu, ka gudu domin kana kewar gidan mahaifinka ƙwarai, amma don me ka sace mini gumakana?” 31 Yakubu ya amsa wa Laban, ya ce, “Domin na ji tsoro ne gama na yi zaton za ka ƙwace 'ya'yanka mata ƙarfi da yaji. 32 Ga duk wanda ka iske gumaka a wurinsa, a kashe shi. Yanzu a nan gaban danginmu, ka nuna abin da nake da shi wanda yake naka, ka ɗauka.” Ashe, Yakubu bai sani Rahila ce ta sace su ba. 33 Laban ya shiga alfarwar Yakubu, da ta Lai'atu, da na kuyangin nan biyu, amma bai same su ba. Sai ya fita daga alfarwar Lai'atu, ya shiga ta Rahila. 34 Ashe, Rahila ta kwashe gumakan ta zuba su cikin sirdin raƙumi, ta zauna a kansu. Laban ya wawaka alfarwar duka, amma bai same su ba. 35 Sai ta ce wa mahaifinta, “Kada ubangijina ya yi fushi da ban iya tashi ba, don ina al'adar mata ne.” Ya kuwa bincike, amma bai sami gumakan ba. 36 Yakubu ya husata, ya yi wa Laban faɗa, ya ce wa Laban, “Wane laifi na yi, mene ne zunubina da ka tsananta bina? 37 Ko da yake ka wawaka dukan kayayyakina, me ka samu na gidanka a ciki? A tabbatar a nan yau a gaban dangina da danginka, su yanke shari'a tsakanina da kai. 38 Waɗannan shekaru ashirin da na yi tare da kai, tumakinka da awakinka ba su yi ɓari ba, ban kuwa ci ragunan garkenka ba. 39 Wanda namomin jeji suka yayyaga ban kawo maka ba, ni da kaina na ɗauki hasararsu. Ka kuma nemi abin da aka sace da rana ko da dare daga hannuna. 40 Abin da na zama ke nan, da rana na sha zafin rana, da dare kuwa na sha sanyi, ga rashin barci. 41 A waɗannan shekaru ashirin da nake cikin gidanka, na yi maka barantaka shekara goma sha huɗu domin 'ya'yanka mata biyu, shekara shida kuma domin garkenka, ka kuwa sauya ladana har sau goma. 42 Da ba domin Allah na mahaifina da Ibrahim, da martabar Ishaku na wajena ba, hakika da yanzu ka sallame ni hannu wofi. Allah ya ga wahalata da aikin hannuwana, ya kuwa tsauta maka a daren jiya.”

Yarjejeniya Tsakanin Yakubu da Laban

43 Sa'an nan Laban ya amsa ya ce wa Yakubu, “'Ya'ya mata, 'ya'yana ne, 'ya'yansu kuma nawa ne, garkunan, garkunana ne, dukan abin da kake gani nawa ne. Amma me zan yi a wannan rana ta yau ga waɗannan 'ya'ya mata nawa, ko kuma ga 'ya'yan da suka haifa? 44 Zo mana mu ƙulla alkawari, da ni da kai, bari ya zama shaida tsakanina da kai.” 45 Saboda haka Yakubu ya ɗauki dutse ya kafa shi al'amudi. 46 Yakubu ya ce wa iyalinsa, “Ku tattara duwatsu,” sai suka ɗauki duwatsu, suka tsiba, suka kuwa ci abinci kusa da tsibin. 47 Laban ya sa masa suna Yegar-sahaduta, amma Yakubu ya kira shi Galeyed. 48 Laban ya ce, “Wannan tsibi shaida ce tsakanina da kai yau.” Saboda haka ya sa wa wurin suna Galeyed. 49 Laban kuma ya kira wurin Mizfa, gama ya ce, “Ubangiji ya kiyaye tsakanina da kai sa'ad da muka rabu da juna. 50 Idan ka wulakanta 'ya'yana mata, ko kuma ka auri wata mata banda 'ya'yana mata, ko da yake babu kowa tare da mu, ka tuna, Allah shi ne mashaidi tsakanina da kai.” 51 Sai Laban ya ce wa Yakubu, “Dubi wannan tsibi da al'amudi, wanda na kafa tsakanina da kai. 52 Wannan tsibi, shaida ce, al'amudin kuma shaida ce ba zan zarce wannan tsibi zuwa wurinka ba, kai kuma ba za ka zarce wannan tsibi da wannan al'amudi zuwa wurina don cutarwa ba. 53 Allah na Ibrahim da Nahor, Allah na mahaifinsu, ya shara'anta tsakaninmu.” Saboda haka Yakubu ya rantse da martabar mahaifinsa Ishaku. 54 Yakubu kuwa ya miƙa hadaya a bisa dutsen, ya kirawo iyalinsa su ci abinci, suka kuwa ci abinci suka zauna dukan dare a bisa dutsen. 55 Da sassafe, Laban ya tashi ya sumbaci jikokinsa, da 'ya'yansa mata, ya sa musu albarka. Sa'an nan ya tashi ya koma gida.

Farawa 32

Yakubu ya yi Shirin Saduwa da Isuwa

1 Yakubu ya yi tafiyarsa, mala'ikun Allah kuma suka gamu da shi. 2 Sa'ad da Yakubu ya gan su ya ce, “Waɗannan rundunar Allah ce!” Saboda haka ya sa wa wannan wuri suna Mahanayim. 3 Yakubu kuwa ya aiki jakadu a gabansa zuwa wurin Isuwa ɗan'uwansa a cikin ƙasar Seyir a karkarar Edom, 4 yana umartarsu da cewa, “Haka za ku faɗa wa shugabana Isuwa, ‘Ga abin da baranka Yakubu ya ce, “Na yi baƙunta a ƙasar Laban, na zauna har wa yau. 5 Ina da takarkarai, da jakai, da garkuna, da barori mata da maza, na kuwa aika a faɗa wa shugabana domin in sami tagomashi a idonka.” ’ ” 6 Jakadun kuwa suka komo wurin Yakubu, suka ce, “Mun je wurin ɗan'uwanka Isuwa, yana kuwa zuwa ya tarye ka da mutum arbaminya tare da shi.” 7 Yakubu fa ya tsorata ƙwarai, ya damu, sai ya karkasa mutanen da suke tare da shi, da garkunan tumaki da awaki, da na shanu, da raƙuma cikin ƙungiya biyu, 8 yana tunani cewa, “In Isuwa ya zo ya hallaka ƙungiya guda, ƙungiyar da ta ragu sai ta tsira.” 9 Sai Yakubu ya ce, “Ya Allah na kakana Ibrahim, da mahaifina Ishaku, Ubangiji, wanda ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuwa yi maka alheri,’ 10 ban cancanci ayyukanka na ƙauna da irin amincin da ka gwada wa baranka ba, gama da sandana kaɗai na haye Kogin Urdun, ga shi yanzu kuwa na zama ƙungiya biyu. 11 Ka cece ni ina roƙonka daga hannun ɗan'uwana, wato, daga hannun Isuwa, gama ina jin tsoronsa, kada ya zo ya karkashe mu duka, 'ya'ya da iyaye. 12 Gama ka riga ka ce, ‘Zan yi maka alheri, in kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar yashin teku, waɗanda ba su lasaftuwa saboda yawansu.’ ” 13 Ya yi zango a nan a wannan dare, ya kuwa bai wa ɗan'uwansa Isuwa kyauta daga cikin abin da yake da shi, 14 awakai metan da bunsurai ashirin, tumaki metan da raguna ashirin, 15 raƙuman tatsa talatin tare da 'yan taguwoyi, shanu arba'in da bijimai goma, jakai mata ashirin da jakai maza goma. 16 Waɗannan ya sa su a hannun barorinsa ƙungiya ƙungiya, ya ce wa barorinsa, “Ku yi gaba, ku ba da rata tsakanin ƙungiya da ƙungiya.” 17 Ya umarci na kan gaba, ya ce, “Sa'ad da Isuwa ɗan'uwana ya gamu da ku, ya tambaye ku cewa, ‘Ku mutanen wane ne? Ina za ku? Waɗannan da suke gabanku na wane ne?’ 18 Sa'an nan sai ku ce, ‘Na Yakubu baranka ne, kyauta ce zuwa ga shugabana Isuwa, ga shi nan ma biye da mu.’ ” 19 Da haka nan ya umarci na biyu da na uku da dukan waɗanda suke korar garkunan, ya ce, “Sai ku faɗa wa Isuwa daidai haka nan. 20 Ku kuma ce, ‘Ga shi ma, Yakubu ɗan'uwanka yana biye da mu.’ ” Gama, cikin tunaninsa ya ce, “Ya yiwu in gamshe shi da kyautar da ta riga ni gaba, daga baya in ga fuskarsa, watakila ya karɓe ni.” 21 Saboda haka kyautar ta yi gaba, shi kansa kuwa a daren, ya sauka a zango.

Yakubu ya Yi Kokawa a Feniyel

22 A wannan dare kuwa ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da kuyanginsa biyu da 'ya'yansa goma sha ɗaya ya haye mashigin Jabbok. 23 Ya ɗauke su ya haye da su rafi, haka kuma ya yi da dukan abin da yake da shi. 24 Aka bar Yakubu shi kaɗai. Sai wani mutum ya kama shi da kokawa har wayewar gari. 25 Sa'ad da mutumin ya ga bai rinjayi Yakubu ba sai ya taɓa kwarin kwatangwalonsa, sai gaɓar kwatangwalon Yakubu ta gulle a lokacin da yake kokawa da shi. 26 Sa'an nan sai mutumin ya ce, “Ka bar ni in tafi, gama gari na wayewa.” Amma Yakubu ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.” 27 Sai ya ce masa, “Yaya sunanka?” Ya ce, “Yakubu.” 28 Sai ya ce, “Ba za a ƙara kiranka da suna Yakubu ba, amma za a kira ka Isra'ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.” 29 Sa'an nan Yakubu ya tambaye shi, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma ya ce, “Don me kake tambayar sunana?” A nan mutumin ya sa masa albarka. 30 Saboda haka Yakubu ya sa wa wurin suna Feniyel, yana cewa, “Gama na ga Allah fuska da fuska, duk da haka ban mutu ba.” 31 Rana ta yi sama a sa'ad da Yakubu ya wuce Feniyel domin yana ɗingishi saboda kwatangwalonsa. 32 Saboda haka, har wa yau, Isra'ilawa ba sā cin jijiyar kwatangwalo wadda take a kwarin kwatangwalo, domin an taɓi kwarin kwatangwalon Yakubu ta jijiyar kwatangwalo.

Farawa 33

Yakubu ya Sadu da Isuwa

1 Yakubu ya ɗaga ido ya duba ke nan, sai ga Isuwa na zuwa da mutum arbaminya tare da shi. Sai ya raba wa Lai'atu da Rahila 'ya'yan, tare da kuyangin nan biyu. 2 Ya sa kuyangin da 'ya'yansu a gaba, sa'an nan Lai'atu sa'an nan Rahila da Yusufu a ƙarshen duka. 3 Shi kansa ya wuce gabansu, ya yi ta sunkuyar da kansa ƙasa sau bakwai, har sa'ad da ya kai kusa da ɗan'uwansa. 4 Amma Isuwa ya sheƙa ya tarye shi, ya rungume shi, ya faɗa a wuyansa, ya sumbace shi, suka kuwa yi kuka. 5 Sa'ad da Isuwa ya ta da idonsa ya ga mata da 'ya'ya, ya ce, “Suwane ne waɗannan tare da kai?” Yakubu ya ce, “Su ne 'ya'ya waɗanda Allah cikin alherinsa ya ba baranka.” 6 Sai kuyangin suka matso kusa, su da 'ya'yansu, suka sunkuya ƙasa. 7 Haka nan kuma Lai'atu da 'ya'yanta suka matso, suka sunkuya ƙasa, a ƙarewa Yusufu da Rahila suka matso kusa, su kuma suka sunkuya ƙasa. 8 Isuwa kuwa ya ce, “Ina manufarka da duk waɗannan ƙungiyoyi da na gamu da su?” Yakubu ya amsa, ya ce, “Ina neman tagomashi ne a idon shugabana.” 9 Amma Isuwa ya ce, “Ina da abin da ya ishe ni, ɗan'uwana, riƙe abin da kake da shi don kanka.” 10 Yakubu ya ce, “A'a, ina roƙonka, in dai na sami tagomashi a idonka, to, sai ka karɓi kyautar da yake hannuna, gama hakika ganin fuskarka, kamar ganin fuskar Allah ne, bisa ga yadda ka karɓe ni. 11 Ina roƙonka, ka karɓi kyautar da na kawo maka, gama Allah ya yi mini alheri matuƙa, gama ina da abin da ya ishe ni.” Da haka Yakubu ya i masa, Isuwa kuwa ya karɓa. 12 Sa'an nan Isuwa ya ce, “Bari mu ci gaba da tafiyarmu, ni kuwa in wuce gabanka.” 13 Amma Yakubu ya ce masa, “Shugabana, ai, ka sani 'ya'yan ba su da ƙarfi, ga kuma bisashe da shanun tatsa, ina jin tausayinsu ƙwarai da gaske. Idan kuwa aka tsananta korarsu kwana ɗaya, garkunan za su mutu duka. 14 Bari shugabana ya wuce gaban baransa, ni zan biyo a hankali bisa ga saurin shanun da yake gabana, da kuma bisa ga saurin yaran, har in isa wurin shugaba a Seyir.” 15 Sai Isuwa ya ce, “Bari in bar waɗansu daga cikin mutanen da suke tare da ni, a wurinka.” Amma Yakubu ya ce, “Ka kyauta ƙwarai, amma ba na bukatar haka, ya shugaba.” 16 A ran nan Isuwa ya koma a kan hanyarsa zuwa Seyir. 17 Yakubu ya kama hanya zuwa Sukkot, ya kuwa gina wa kansa gida, ya yi wa shanunsa garke. Saboda haka aka sa wa wurin suna Sukkot. 18 Yakubu kuwa ya kai birnin Shalem wanda yake ƙasar Kan'ana lafiya, a kan hanyarsa daga Fadan-aram, ya kuwa yi zango a ƙofar birnin. 19 Ya kuma sayi yankin saura inda ya kafa alfarwarsa daga 'ya'yan Hamor, mahaifin Shekem, a bakin azurfa ɗari. 20 A wurin ya gina bagade ya sa masa suna El-Elohe-Isra-el.

Farawa 34

An Yi wa Dinatu Faɗe

1 Yanzu fa Dinatu 'yar Lai'atu, wadda ta haifa wa Yakubu, ta fita ta ziyarci waɗansu matan ƙasar, 2 sai Shekem, ɗan Hamor Bahiwiye, yariman ƙasar, da ya gan ta, ya kama ta, ya kwana da ita, ya ɓata ta. 3 Ransa kuwa ya zaƙu da son Dinatu 'yar Yakubu. Ya ƙaunaci budurwar, ya kalallame ta da maganganu masu daɗi. 4 Sai Shekem ya yi magana da mahaifinsa, Hamor, ya ce, “Ka auro mini wannan budurwa ta zama matata.” 5 Yakubu kuwa ya ji an ɓata 'yarsa, Dinatu, amma 'ya'yansa maza suna tare da garken cikin saura, saboda haka Yakubu ya yi shiru har kafin su komo. 6 Sai Hamor mahaifin Shekem ya fita ya je wurin Yakubu, ya yi magana da shi. 7 'Ya'yan Yakubu, maza, kuwa sa'ad da suka komo daga saura, da suka ji yadda aka yi, sai suka hasala, abin ya ba su haushi kwarai, don Shekem ya yi aikin wauta ga Isra'ila da ya kwana da 'yar Yakubu. Gama irin wannan abu, bai kamata a yi shi ba. 8 Amma Hamor ya yi magana da su, ya ce, “Zuciyar ɗana Shekem tana begen 'yarku, ina roƙonku, ku ba shi ita aure. 9 Ku yi aurayya da mu. Ku ba mu 'yan matanku, ku kuma ku auri 'yan matanmu. 10 Sai ku zauna tare da mu, ƙasar kuma tana gabanku. Ku zauna a cikinta ku yi sana'a, ku sami dukiya.” 11 Shekem kuma ya ce wa mahaifin Dinatu da 'yan'uwanta, “Bari in sami tagomashi a idanunku, dukan abin da kuka ce kuwa, sai in yi. 12 Ku fada mini ko nawa ne dukiyar auren da sadakin, zan kuwa bayar bisa ga yadda kuka faɗa mini, in dai kawai ku ba ni budurwar ta zama matata.” 13 'Ya'yan Yakubu, maza, suka amsa wa Shekem da mahaifinsa Hamor a ha'ince, domin ya ɓata 'yar'uwarsu Dinatu. 14 Suka ce musu, “Ba za mu iya yin wannan abu ba, mu aurar da 'yar'uwarmu ga marasa kaciya, gama wannan abin kunya ne a gare mu. 15 Ta wannan hali ne kaɗai za mu yarda, wato, idan za ku zama kamarmu, ku yi wa dukan mazajenku kaciya. 16 Sa'an nan za mu ba ku auren 'ya'yanmu mata, mu kuma mu auro wa kanmu 'ya'yanku mata. Sai kuwa mu zauna tare da ku, mu zama jama'a ɗaya. 17 Amma idan ba ku saurare mu kun yi kaciya ba, sai mu ɗauki 'yarmu, mu kama hanyarmu.” 18 Hamor da ɗansa Shekem suka yi na'am da sharuɗan. 19 Saurayin kuwa bai yi jinkirin aikata batun ba, gama yana jin daɗin 'yar Yakubu. Shekem kuwa shi ne aka fi darajantawa a cikin gidan. 20 Hamor kuwa da ɗansa Shekem, suka je dandali a bakin ƙofar birni, suka yi wa mutanen birninsu magana, suka ce, 21 “Waɗannan mutane suna abuta da mu, ai, sai su zauna a ƙasar a sake, gama ga shi akwai isasshen fili a ƙasar dominsu. Bari mu auri 'ya'yansu mata, mu kuma mu aurar musu da 'ya'yanmu mata. 22 Ga sharaɗin da mutanen za su yarda su zauna tare da mu, mu zama jama'a ɗaya, wato, kowane namiji a cikinmu ya yi kaciya kamar yadda su suke da kaciya. 23 Da shanunsu, da dukiyarsu da dukan dabbobinsu, ashe, ba za su zama namu ba? Bari dai kurum mu yarda da su, su zauna tare da mu.” 24 Duk jama'ar birnin suka yarda da maganar Hamor da ɗansa Shekem. Aka kuwa yi wa kowane namiji kaciya. 25 A rana ta uku, sa'ad da jikunansu suka yi tsami, biyu daga cikin 'ya'yan Yakubu, Saminu da Lawi, 'yan'uwan Dinatu, suka ɗauki takubansu suka fāɗa wa birnin ba labari, suka karkashe mazajen duka. 26 Suka kashe Hamor da ɗansa Shekem da takobi, suka ɗauko Dinatu daga gidan Shekem suka yi tafiyarsu. 27 'Ya'yan Yakubu kuwa suka tarar da kisassun, suka washe birnin, saboda sun ɓata 'yar'uwarsu. 28 Suka kwashe garkunan awaki da tumaki, da garkunan shanu da jakunansu da dukan abin da yake cikin birnin da na cikin saura, 29 dukan dukiyarsu, da 'yan ƙananansu, da matansu, wato, dukan abin da yake cikin gidajen, suka kwashe. 30 Sai Yakubu ya ce wa Saminu da Lawi, “Kun jawo mini wahala. Kun sa na zama abin ƙi ga Kan'aniyawa da Ferizziyawa mazaunan ƙasar. Mutanena kima ne, in suka haɗa kai suka fāɗa mini, za su hallaka ni, da ni da gidana.” 31 Amma 'ya'yansa suka ce, “Zai mai da ƙanwarmu kamar karuwa?”

Farawa 35

Allah ya Sa wa Yakubu Albarka a Betel

1 Allah ya ce wa Yakubu, “Tashi, ka hau zuwa Betel, ka zauna can. Can za ka gina bagade ga Allah wanda ya bayyana gare ka sa'ad da kake guje wa ɗan'uwanka Isuwa.” 2 Sai Yakubu ya ce wa iyalin gidansa da dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku kawar da gumakan da suke wurinku, ku tsarkake kanku, ku sāke rigunanku, 3 sa'an nan mu tashi mu haura zuwa Betel, domin in kafa bagade ga Allah wanda ya taimake ni a kwanakin ƙuncina, wanda kuwa yake tare da ni duk inda na tafi.” 4 Saboda haka, suka bai wa Yakubu dukan gumakan da suke da su, da zobban kunnuwansu. Sai Yakubu ya ɓoye su a ƙarƙashin itacen oak wanda yake kusa da Shekem. 5 Da suna cikin tafiya, razana daga Allah ta fāɗa wa biranen da suke kewaye da su, har ba wanda ya iya bin 'ya'yan Yakubu. 6 Sai Yakubu ya zo Luz, wato, Betel, wadda take cikin Kan'ana, shi da dukan mutanen da suke tare da shi. 7 A nan ya gina bagade, ya sa wa wurin suna El-betel, domin a nan Allah ya bayyana kansa gare shi sa'ad da yake guje wa ɗan'uwansa. 8 Can Debora, ungozomar Rifkatu ta rasu, aka kuwa binne ta a gangaren Betel, a ƙarƙashin itacen oak, don haka ana kiran wurin, Allon-bakut. 9 Allah kuma ya sāke bayyana ga Yakubu a lokacin da ya komo daga Fadan-aram, ya sa masa albarka. 10 Allah kuwa ya ce masa, “Sunanka Yakubu ne, amma nan gaba ba za a ƙara kiran sunanka Yakubu ba, sai Isra'ila.” Don haka aka kira sunansa Isra'ila. 11 Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka hayayyafa ka riɓaɓɓanya, al'umma da tattaruwar al'ummai za su bumbunto daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga cikinka. 12 Na ba ka ƙasar da na ba Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba da ita ga zuriyarka a bayanka.” 13 Sa'an nan Allah ya tashi Sama ya bar shi a wurin da ya yi masa magana. 14 Sai Yakubu ya kafa al'amudin dutse a inda Allah ya yi masa magana, ya zuba masa sadaka ta sha, ya kuma zuba mai a bisansa. 15 Yakubu ya kira sunan wurin da Allah ya yi magana da shi, Betel.

Rasuwar Rahila

16 Da suka tashi daga Betel, tun suna da 'yar rata da Efrata, sai lokaci ya yi da Rahila za ta haihu, amma ta sha wahala kafin ta haihu. 17 Sa'ad da take cikin naƙudarta, sai ungozoma ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.” 18 Da tana suma, sai ta sa masa suna Ben-oni, amma mahaifinsa ya sa masa suna Biliyaminu. 19 Ta haka fa Rahila ta rasu, aka kuwa binne ta a bakin hanya zuwa Efrata, wato, Baitalami. 20 Yakubu ya kafa al'amudi bisa kabarinta, al'amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau. 21 Isra'ila ya ci gaba da tafiyarsa, ya kuwa kafa alfarwarsa daura da hasumiyar Eder.

'Ya'yan Yakubu Maza

22 A lokacin da Isra'ila ke zaune a ƙasar, Ra'ubainu ya je ya kwana da Bilha kwarkwarar mahaifinsa, Isra'ila kuwa ya sami labari. 'Ya'yan Isra'ila, maza, su goma sha biyu ne. 23 'Ya'yan Lai'atu, su ne Ra'ubainu ɗan farin Yakubu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza, da Issaka, da Zabaluna. 24 'Ya'yan Rahila, su ne Yusufu da Biliyaminu. 25 'Ya'yan Bilha, kuyangar Rahila, su ne Dan da Naftali. 26 'Ya'yan Zilfa, kuyangar Lai'atu, su ne Gad da Ashiru. Waɗannan su ne 'ya'yan Yakubu da aka haifa masa a Fadan-aram.

Rasuwar Ishaku

27 Yakubu kuma ya zo wurin mahaifinsa a Mamre, a Kiriyat-arba, wato, Hebron ke nan, inda Ibrahim da Ishaku suka yi baƙunci. 28 Yanzu kuwa kwanakin Ishaku shekara ce ɗari da tamanin. 29 Sai Ishaku ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya rasu, aka kuwa kai shi ga jama'arsa waɗanda suka riga shi, da kyakkyawan tsufa cike da kwanaki, 'ya'yansa Isuwa da Yakubu suka binne shi.

Farawa 36

Zuriyar Isuwa

1 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa, wato, Edom. 2 Isuwa ya auri matansa daga cikin Kan'aniyawa, wato, Ada 'yar Elon Bahitte, da Oholibama 'yar Ana ɗan Zibeyon Bahiwiye, 3 da Basemat, 'yar Isma'ilu, 'yar'uwar Nebayot. 4 Ada ta haifa wa Isuwa, Elifaz, Basemat kuma ta haifi Reyuwel. 5 Oholibama ta haifi Yewush, da Yalam, da Kora. Waɗannan su ne 'ya'yan Isuwa waɗanda aka haifa masa a ƙasar Kan'ana. 6 Isuwa ya kwashi matansa, da 'ya'yansa mata da maza, da dukan jama'ar gidansa, da shanunsa, da dabbobinsa duka, da dukan dukiyarsa da ya samu a ƙasar Kan'ana, ya kuwa tafi wata ƙasa nesa da ɗan'uwansa Yakubu. 7 Gama abin mallakarsu ya yi yawa har ba zai yiwu su zama tare ba, ƙasar baƙuntarsu kuwa ba ta wadace su ba saboda yawan dabbobinsu. 8 Saboda haka Isuwa ya zauna a ƙasar Seyir ta tuddai. Isuwa shi ne Edom. 9 Waɗannan su ne zuriyar Isuwa, kakan Edomawa, a ƙasar Seyir ta tuddai. 10 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Isuwa, maza, wato, Elifaz ɗan Ada matar Isuwa, Reyuwel ɗan Basemat matar Isuwa. 11 'Ya'yan Elifaz su ne Teman, da Omar, da Zeho, da Gatam, da Kenaz. 12 Timna kuwa ƙwarƙwarar Elifaz ɗan Isuwa ce, ta haifa wa Elifaz Amalek. Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Ada, matar Isuwa. 13 Waɗannan su ne 'ya'yan Reyuwel, maza, Nahat, da Zera, da Shamma, da Mizza. Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Basemat, matar Isuwa. 14 Waɗannan su ne 'ya'yan Oholibama matar Isuwa 'yar Ana ɗan Zibeyon. Ta haifi wa Isuwa Yewush, da Yalam, da Kora. 15 Waɗannan su ne shugabanni na zuriyar Isuwa. Ga 'ya'yan Elifaz, maza, ɗan farin Isuwa, shugaba Teman, da Omar, da Zeho, da Kenaz, 16 da Kora, da Gatam, da Amalek, su ne shugabannin Elifaz cikin ƙasar Edom, su ne 'ya'yan Ada. 17 Waɗannan su ne 'ya'yan Reyuwel, maza, ɗan Isuwa. Shugaba Nahat, da Zera, da Shamma, da Mizza, waɗannan su ne shugabannin Reyuwel na cikin ƙasar Edom, su ne 'ya'ya maza na Basemat, matar Isuwa. 18 Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Oholibama matar Isuwa, shugaba Yewush, da Yalam, da Kora, waɗannan su ne shugabanni waɗanda Oholibama matar Isuwa, 'yar Ana ta haifa. 19 Waɗannan su ne 'ya'yan Isuwa, maza, wato, Edom, da shugabanninsu.

Zuriyar Seyir

20 Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Seyir Bahore, mazaunan ƙasar Lotan, da Shobal, da Zibeyon, da Ana, 21 da Dishon, da Ezer, da Dishan. Waɗannan su ne shugabannin Horiyawa, 'ya'yan Seyir, maza, a ƙasar Edom. 22 'Ya'yan Lotan, maza, su ne Hori da Hemam, 'yar'uwarsa Timna ce. 23 Waɗannan su ne 'ya'yan Shobal, maza, Alwan, da Manahat, da Ebal, da Sheho, da Onam. 24 Waɗannan su ne 'ya'yan Zibeyon, maza, Aiya da Ana. Shi ne Ana wanda ya sami maɓuɓɓugan ruwan zafi a cikin jeji, a sa'ad da yake kiwon jakunan mahaifinsa Zibeyon. 25 Waɗannan su ne 'ya'yan Ana, Dishon da Oholibama 'yar Ana. 26 Waɗannan su ne 'ya'yan Dishon, maza, Hemdan da Eshban, da Yitran, da Keran. 27 Waɗannan su ne 'ya'yan Ezer, maza, Bilha, da Zayawan, da Akan. 28 Waɗannan su ne 'ya'yan Dishan, maza, Uz da Aran. 29 Waɗannan su ne shugabannin Horiyawa, shugaba Lotan, da Shobal, da Zibeyon, da Ana, 30 da Dishon, da Ezer, da Dishan, waɗannan su ne shugabannin Horiyawa bisa ga shugabancinsu a ƙasar Seyir.

Sarakunan Edom

31 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi sarauta a ƙasar Edom, kafin wani sarki ya taɓa yin mulkin Isra'ilawa. 32 Bela ɗan Beyor ya yi sarautar Edom, sunan birninsa kuwa Dinhaba. 33 Bela ya rasu, sai Yobab ɗan Zera daga Bozara ya ci sarauta a bayansa. 34 Ɗan Yobab ya rasu, sai Husham na ƙasar Temanawa ya ci sarauta a bayansa. 35 Da Husham ya rasu, sai Hadad ɗan Bedad wanda ya ci Madayana a ƙasar Mowab, ya ci sarauta a bayansa, sunan birninsa kuwa Awit ne. 36 Da Hadad ya rasu, sai Samla na Masreka ya ci sarauta a bayansa. 37 Da Samla ya rasu, sai Shawul na Rehobot ta Yufiretis ya ci sarauta a bayansa. 38 Da Shawul ya rasu, sai Ba'al-hanan ɗan Akbor ya ci sarauta a bayansa. 39 Da Ba'al-hanan ɗan Akbor ya rasu, sai Hadad ya ci sarauta a bayansa, sunan birninsa Fau, sunan matarsa kuwa Mehetebel 'yar Matred, 'yar Mezahab. 40 Waɗannan su ne sunayen sarakunan Isuwa bisa ga dangoginsu da bisa ga wurin zamansu. Ga sunayensu, sarki Timna, da Alwa, da Yetet, 41 da Oholibama, da Ila, da Finon, 42 da Kenaz, da Teman, da Mibzar, 43 da Magdiyel, da Iram. Waɗannan su ne sarakunan Edom, (wato, Isuwa ne kakan Edomawa) bisa ga wuraren zamansu a ƙasar mallakarsu.

Farawa 37

1 Yakubu ya zauna a ƙasar Kan'ana inda mahaifinsa ya yi baƙunci. 2 Wannan shi ne tarihin zuriyar Yakubu.

Yusufu da 'Yan'uwansa

Yusufu yana da shekara goma sha bakwai sa'ad da ya zama makiyayin garke tare da 'yan'uwansa, ɗan ƙanƙanen yaro ne a tsakanin 'ya'ya maza na Bilha da Zilfa matan mahaifinsa. Sai Yusufu ya kawo labarin munanan abubuwa da 'yan'uwansa suke yi a wurin mahaifinsa, 3 Isra'ila kuwa ya fi ƙaunar Yusufu da ko wannensu, domin shi ɗan tsufansa ne. Sai ya yi masa riga mai ado. 4 Amma sa'ad da 'yan'uwansa suka gane mahaifinsu yana ƙaunarsa fiye da dukansu, suka ƙi jininsa, ba su iya maganar alheri da shi. 5 Yusufu ya yi mafarki. Sa'ad da ya faɗa wa 'yan'uwansa, suka ƙara ƙin jininsa. 6 Ya ce musu, “Ku ji irin mafarkin da na yi. 7 Ga shi, muna ɗaurin dammuna cikin gona, ga kuwa damina ya tashi tsaye kyam, ga kuma dammunanku suka taru kewaye da shi, suka sunkuya wa damina.” 8 'Yan'uwansa suka ce masa, “Ashe, lalle ne kai za ka sarauce mu? Ko kuwa, ashe lalle ne kai za ka mallake mu?” Sai suka daɗa ƙin jininsa domin mafarkansa da maganganunsa. 9 Shi kuwa sai ya sāke yin wani mafarki, ya faɗa wa 'yan'uwansa, ya ce, “Ga shi kuma na sāke yin wani mafarki, na ga rana, da wata, da taurari goma sha ɗaya suna sunkuya mini.” 10 Amma sa'ad da ya faɗa wa mahaifinsa da 'yan'uwansa, sai mahaifinsa ya tsauta masa, ya ce, “Wane irin mafarki ne wannan da ka yi? Lalle ne, da ni da mahaifiyarka da 'yan'uwanka za mu sunkuya a gabanka har ƙasa?” 11 'Yan'uwansa suka ji kishinsa, amma mahaifinsa ya riƙe al'amarin cikin zuciyarsa.

An Sayar da Yusufu zuwa Masar

12 Wata rana, da 'yan'uwansa suka tafi kiwon garken mahaifinsu a Shekem, 13 Isra'ila ya ce wa Yusufu, “Ashe, ba 'yan'uwanka suna kiwon garken a Shekem ba? Zo in aike ka wurinsu.” Sai ya ce masa, “Ga ni.” 14 Mahaifinsa ya ce, “Tafi yanzu, ka dubo lafiyar 'yan'uwanka da ta garken, ka kawo mini labarinsu.” Saboda haka, ya aike shi daga kwarin Hebron. Da Yusufu ya isa Shekem, 15 wani mutum ya same shi yana hange-hange cikin karkara. Sai mutumin ya tambaye shi ya ce, “Me kake nema?” 16 Yusufu ya ce, “Ina neman 'yan'uwana ne. Ina roƙonka ka faɗa mini idan ka san inda suke kiwon garkuna.” 17 Mutumin ya ce, “Sun riga sun tashi daga nan, gama na ji sun ce, ‘Bari mu tafi Dotan.’ ” Saboda haka, Yusufu ya bi sawun 'yan'uwansa, ya kuwa same su a Dotan. 18 Da suka hango shi daga nesa, kafin ya zo kusa da su, sai suka ƙulla su kashe shi. 19 Suka ce wa juna, “Ga mai mafarkin nan can yana zuwa. 20 Ku zo mu kashe shi yanzu, mu jefa shi cikin ɗaya daga cikin rijiyoyin nan, sa'an nan mu ce, wata muguwar dabbar jeji ce ta kashe shi, sa'an nan mu ga yadda mafarkinsa zai zama.” 21 Amma sa'ad da Ra'ubainu ya ji, ya yi ƙoƙari ya cece shi daga hannunsu, yana cewa, “Kada mu raba shi da ransa. 22 Kada mu kashe shi, mu dai jefa shi cikin rijiyar nan a jeji, amma kada mu yi masa lahani.” Ya yi haka da nufin ya cece shi daga hannunsu, ya mayar da shi ga mahaifinsu. 23 Don haka, sa'ad da Yusufu ya zo wurin 'yan'uwansa, suka tuɓe masa rigarsa, rigan nan mai ado wadda take wuyansa. 24 Suka ɗauke shi suka jefa shi cikin rijiyar. Rijiyar kuwa wofi ce, ba ruwa a ciki. 25 Suka zauna su ci abinci, da suka ɗaga ido suka duba, sai ga ayarin Isma'ilawa suna zuwa daga Gileyad, da raƙumansu ɗauke da ƙāro, da man ƙanshi na wartsakewa, da mur, suna gangarawa kan hanyarsu zuwa Masar. 26 Yahuza ya ce wa 'yan'uwansa, “Wace riba ke nan, in mun kashe ɗan'uwanmu, muka ɓoye jininsa? 27 Ku zo mu sayar da shi ga Isma'ilawa, kada mu bar hannunmu ya taɓa shi, gama shi ɗan'uwanmu ne, shi kuma jikinmu ne.” 'Yan'uwansa suka yarda da shi. 28 Da Madayanawa, fatake, suna wucewa, sai suka jawo Yusufu suka fitar da shi daga cikin rijiyar suka sayar wa Isma'ilawa a bakin azurfa ashirin, aka kuwa tafi da Yusufu zuwa Masar. 29 Sa'ad da Ra'ubainu ya koma a wajen rijiya, da bai ga Yusufu a cikin rijiyar ba, sai ya kyakkece tufafinsa, 30 ya koma wurin 'yan'uwansa, ya ce, “Saurayin ba ya nan, ni kuwa, ina zan sa kaina?” 31 Suka ɗauki rigar Yusufu, suka yanka akuya, suka tsoma rigar cikin jinin. 32 Suka kuma ɗauki rigan nan mai ado, suka kawo ta ga mahaifinsu, suka ce, “Ga abar da muka samu, duba ka gani, ta ɗanka ce, ko kuwa?” 33 Da ya gane ita ce, ya ce, “Rigar ɗana ce, wani mugun naman jeji ne ya cinye shi, ba shakka an yayyage Yusufu.” 34 Sai Yakubu ya kyakkece rigunansa, ya yi ɗamara da majayi, ya yi kukan ɗansa har kwanaki masu yawa. 35 Dukan 'ya'yansa mata da maza suka tashi domin su ta'azantar da shi, amma ya ƙi ta'azantuwa, yana cewa, “A'a, a Lahira zan tafi wurin ɗana, ina baƙin ciki.” Haka mahaifinsu ya yi kuka dominsa. 36 A lokacin kuwa, ashe, Madayanawa sun riga sun sayar da shi a Masar ga Fotifar, sarkin yaƙin Fir'auna, shugaba na masu tsaron fādar Fir'auna.

Farawa 38

Yahuza da Tamar

1 Ya zama fa a wannan lokaci, Yahuza ya bar 'yan'uwansa ya gangara, ya zauna wurin wani Ba'adullame mai suna Hira. 2 A can, sai Yahuza ya ga 'yar wani Bakan'ane mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya shiga wurinta, 3 ta yi ciki, ta haifi ɗa namiji, ya kuwa raɗa masa suna Er. 4 Sai ta sāke yin ciki, ta kuma haifi ɗa, ta raɗa masa suna Onan. 5 Har yanzu kuma ta sāke haihuwar ɗa, ta raɗa masa suna Shela. A Kezib ta haifi Shela. 6 Yahuza kuwa ya auro wa ɗan farinsa, Er, mata, sunanta Tamar. 7 Amma Er, ɗan farin Yahuza mugu ne a gaban Ubangiji. Sai Ubangiji ya kashe shi. 8 Sa'an nan Yahuza ya ce wa, Onan, “Shiga wurin matar ɗan'uwanka, ka yi mata wajibin ɗan'uwan miji, ka samar wa ɗan'uwanka zuriya.” 9 Amma Onan ya sani zuriyar ba za ta zama tasa ba, saboda haka duk lokacin da ya shiga wurin matar ɗan'uwansa, sai ya zubar da maniyyi a ƙasa don kada ya ba ɗan'uwansa zuriya. 10 Amma abin nan da ya yi, mugun abu ne a gaban Ubangiji, shi ma Ubangiji ya kashe shi. 11 Yahuza kuwa ya ce wa Tamar surukarsa, “Yi zaman gwauranci a gidan mahaifinki, har ɗana Shela ya yi girma,” gama yana jin tsoro kada shi kuma ya mutu kamar 'yan'uwansa. Saboda haka Tamar ta tafi ta zauna a gidan mahaifinta. 12 A kwana a tashi, ga matar Yahuza, 'yar Shuwa ta rasu. Da Yahuza ya gama karɓar ta'aziyya, sai ya haura Timna wurin masu sausayar tumakinsa, da shi da abokinsa Hira Ba'adullame. 13 Sa'ad da aka faɗa wa Tamar, aka ce, “Surukinki zai haura zuwa Timna ya yi wa tumakinsa sausaya,” 14 sai ta tuɓe tufafinta na takaba, ta yi lulluɓi ta lulluɓe kanta, ta zauna a ƙofar Enayim a hanyar Timna, gama ta ga Shela ya yi girma, amma ba a ba da ita gare shi ba. 15 Da Yahuza ya gan ta, ya yi tsammani wata karuwa ce, gama ta rufe fuskarta. 16 Sai ya je wurinta a gefen hanyar, ya ce, “Zo, mu kwana mana,” gama bai san ita surukarsa ba ce. Sai ta ce, “Me za ka ba ni, da za ka kwana da ni?” 17 Ya amsa, ya ce, “Zan aiko miki da ɗan akuya daga cikin garken.” Ta ce, “Ko ka ba ni jingina, kafin ka aiko?” 18 Ya ce, “Wane alkawari zan yi miki?” Ta amsa, ta ce, “Ba ni hatiminka da ɗamararka da sandan da yake a hannunka.” Ya kuwa ba ta su, ya kwana da ita. Sai ta yi ciki. 19 Ta tashi ta yi tafiyarta. Da ta cire lulluɓinta ta sa tufafinta na takaba. 20 Sa'ad da Yahuza ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa Ba'adullame don ya karɓi jinginar daga hannun matar, bai same ta ba. 21 Ya tambayi mutanen wurin, ya ce, “Ina karuwan nan wadda take zaune a Enayim a bakin hanya?” Sai suka ce, “Ba wata karuwar da ta taɓa zama nan.” 22 Ya koma wurin Yahuza ya ce, “Ban same ta ba, mutanen wurin kuma suka ce, ‘Ba wata karuwa da ta zo nan.’ ” 23 Yahuza ya amsa, ya ce, “Bari ta riƙe abubuwan su zama nata, don kada a yi mana dariya, gama ga shi, na aike da ɗan akuya, amma ba ka same ta ba.” 24 Bayan misalin wata uku, aka faɗa wa Yahuza, “Tamar surukarka ta yi lalata, har ma tana da ciki.” Sai Yahuza ya ce, “A fito da ita, a ƙone ta.” 25 Za a fito da ita ke nan sai ta aika wa surukinta, ta ce, “Wanda yake da waɗannan kaya shi ya yi mini ciki.” Ta kuma ce, “Ka shaida, ina roƙonka, ko na wane ne wannan hatimi, da abin ɗamarar, da sanda.” 26 Sai Yahuza ya shaida su, ya ce, “Ta fi ni gaskiya, tun da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Daga nan bai ƙara kwana da ita ba. 27 Sa'ad da lokaci ya yi da za ta haihu, ashe, cikin tagwaye ne. 28 Da tana cikin naƙuda, sai hannun wani ya fara fitowa, ungozoma kuwa ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, tana cewa, “Wannan shi ya fara fitowa.” 29 Amma da ya janye hannunsa, ga ɗan'uwansa ya fito, sai ta ce, “A'a, ta haka za ka keta ka fito!” Saboda haka aka raɗa masa suna Feresa. 30 Daga baya ɗan'uwansa ya fito da jan zare a hannunsa, aka kuwa sa masa suna Zera.

Farawa 39

Yusufu da Matar Fotifar

1 Aka kuwa gangara da Yusufu zuwa Masar. Sai Fotifar Bamasare sarkin yaƙin Fir'auna, shugaban masu tsaron fāda ya saye shi daga hannun Isma'ilawa, waɗanda suka gangaro da shi zuwa can. 2 Ubangiji yana tare da Yusufu, har ya zama mutum ne mai galaba a gidan maigidansa Fotifar, Bamasaren. 3 Maigidansa kuwa ya ga Ubangiji yana tare da shi, Ubangiji kuma yakan sa albarka ga aikin hannuwansa duka. 4 Don haka Yusufu ya sami tagomashi a wurinsa, ya zama mai yi masa hidima. Fotifar kuma ya shugabantar da shi a bisa gidansa, da bisa dukan abin da yake da shi. 5 Ubangiji ya sa wa gidan Bamasaren albarka sabili da Yusufu tun daga lokacin da Fotifar Bamasaren ya shugabatar da shi a bisa gidansa da dukan dukiyarsa. Albarkar Ubangiji na bisa dukan abin da yake da shi, na gida da na jeji. 6 Ya bar dukan abin da yake da shi a hannun Yusufu. Tun da ya same shi, ba ruwansa da kome, sai dai abincin da zai ci. Yusufu fa kyakkyawa ne mai kyan gani. 7 Ya zamana fa, wata rana, sai matar maigidansa ta sa idonta kan Yusufu, ta ce, “Ka kwana da ni.” 8 Amma ya ƙi, ya kuwa faɗa wa matar maigidansa, ya ce, “Ga shi, tun da maigida ya same ni, maigidana ba ruwansa da kome na cikin gida, ya kuwa riga ya sa dukan abin da yake da shi cikin hannuna. 9 Bai fi ni iko cikin gidan nan ba, ba kuma abin da ya hana mini sai ke kaɗai, domin ke matarsa ce. Ƙaƙa fa zan aikata wannan babbar mugunta, in yi wa Allah zunubi?” 10 Ko da yake ta yi ta yi wa Yusufu magana yau da gobe, amma bai biye mata ya kwana da ita ko su zauna tare ba. 11 Amma wata rana, sa'ad da ya shiga cikin gida ya yi aikinsa, mazajen gidan kuma ba wanda yake gidan, 12 sai ta kama rigarsa, tana cewa, “Ka kwana da ni.” Amma ya bar rigarsa a hannunta ya gudu ya fita. 13 Da ta ga ya bar rigarsa a hannunta ya gudu, ya fita waje, 14 sai ta yi kira ga mutanen gidan, ta ce musu, “Ku duba ku gani, ya kawo mana Ba'ibrane ya ci mutuncinmu. Ya zo wurina don ya kwana da ni, sai na yi ihu da ƙarfi. 15 Da ya ji na ta da murya na yi ihu, ya kuwa gudu ya bar rigarsa, ya fita waje.” 16 Ta ajiye rigar a wurinta har maigidansa ya komo. 17 Sai ta mayar masa da magana, ta ce, “Baran nan, Ba'ibrane wanda ka kawo cikinmu, ya shigo wurina don ya ci mutuncina, 18 amma nan da nan da na ta da murya na yi ihu, sai ya gudu ya bar rigarsa a hannuna, ya gudu zuwa waje.” 19 Sa'ad da maigidan Yusufu ya ji abin da matarsa ta faɗa masa, “Ka ji yadda baranka ya yi da ni ke nan,” sai ya husata. 20 Maigidan Yusufu ya ɗauke shi ya māka shi a kurkuku, inda 'yan sarƙa na sarki suke tsare, can ya zauna a kurkuku. 21 Amma Ubangiji yana tare da Yusufu, ya kuwa nuna masa madawwamiyar ƙauna, ya sa ya sami farin jini a wurin yarin kurkukun. 22 Yarin kurkuku ya shugabantar da Yusufu bisa dukan 'yan sarƙa da suke a kurkuku, dukan abin da ake yi a wurin kuma shi yake yi. 23 Yarin kurkukun, ba ruwansa da dukan abin da Yusufu yake kula da shi, domin Ubangiji yana tare da shi, dukan abin da ya yi kuwa Ubangiji yakan sa wa abin albarka.

Farawa 40

Yusufu ya Fassara Mafarkan 'Yan Kurkuku

1 Bayan waɗannan al'amura, sai mai shayarwa da mai tuya na Sarkin Masar suka yi wa maigidansu Sarkin Masar laifi. 2 Fir'auna ya yi fushi da ma'aikatan nan nasa biyu, wato, shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya. 3 Ya ba da su a sa su kurkuku, cikin gidan shugaban masu tsaron fāda, wato, kurkuku inda Yusufu yake a tsare. 4 Shugaban 'yan tsaron ya danƙa su ga Yusufu don ya hidimta musu, sun kuwa jima a kurkukun har an daɗe. 5 Suka yi mafarki, su biyu ɗin, a dare ɗaya, da shi mai shayarwar da mai tuyar na gidan Sarkin Masar, waɗanda aka sa a kurkuku, kowanne kuwa da nasa mafarkin da kuma tasa irin fassarar mafarkin. 6 Da Yusufu ya zo wurinsu da safe, ya ga sun damu. 7 Sai ya tambaye su ya ce, “Me ya sa fuskokinku suke a yamutse yau?” 8 Suka ce masa, “Mafarkai muka yi, ba kuma wanda zai fassara mana su.” Sai Yusufu ya ce musu, “Ashe, ba a wurin Allah fassarori suke ba? Ku faɗa mini su, ina roƙonku.” 9 Saboda haka, shugaban masu shayarwa ya faɗa wa Yusufu mafarkinsa, ya ce masa, “A mafarkina ga kurangar inabi a gabana. 10 A kurangar akwai rassa uku. Sai ta yi toho, ta huda nan da nan, ta kuma yi nonna, har suka nuna suka zama inabi. 11 Finjalin Fir'auna na hannuna, sai na ɗauki 'ya'yan inabi na matse su cikin finjalin Fir'auna, na sa finjalin a hannun Fir'auna.” 12 Yusufu ya ce masa, “Wannan ita ce fassararsa, rassan nan uku, kwana uku ne, 13 bayan kwana uku Fir'auna zai ɗaukaka ka, ya komar da kai matsayinka, za ka kuma sa finjalin Fir'auna a hannunsa kamar dā lokacin da kake mai hidimar shayarwarsa. 14 Amma ka tuna da ni sa'ad da abin ya tabbata gare ka, sai ka yi mini alheri, ka ambace ni a wurin Fir'auna, har da za a fisshe ni daga wannan gida. 15 Gama ni, hakika sato ni aka yi daga ƙasar Ibraniyawa. A nan kuma ban yi wani abin da zai isa a sa ni a kurkuku ba.” 16 Sa'ad da shugaban masu tuya ya ga fassarar tana da kyau, sai ya ce wa Yusufu, “Ni ma cikin nawa mafarki, na ga kwanduna uku na waina a bisa kaina. 17 A kwandon da yake bisa ɗin akwai toye-toye iri iri domin Fir'auna, amma ga tsuntsaye suna ta ci daga cikin kwandon da yake bisa duka, wato, wanda yake bisa kaina ɗin.” 18 Yusufu ya amsa, “Wannan ita ce fassararsa, kwandunan uku, kwana uku ne, 19 bayan kwana uku Fir'auna zai falle kanka ya rataye ka a bisa itace, tsuntsaye kuwa za su ci naman jikinka.” 20 A rana ta uku, wadda take ranar haihuwar Fir'auna, Fir'auna ya yi wa dukan bayinsa biki, sai ya kawo shugaban masu shayarwa da shugaban masu tuya a gaban fādawansa. 21 Ya komar da shugaban masu shayarwa a matsayinsa na shayarwa, ya kuwa miƙa finjali a hannun Fir'auna, 22 amma ya rataye shugaban masu tuya kamar yadda Yusufu ya fassara musu. 23 Duk da haka shugaban masu shayarwar bai tuna da Yusufu ba, amma ya manta da shi.

Farawa 41

Yusufu ya Fassara wa Fir'auna Mafarkansa

1 Bayan shekaru biyu cif, Fir'auna ma ya yi mafarki, ga shi, yana tsaye a bakin kogin Nilu, 2 sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul suka fito daga Nilu, suka yi kiwo cikin iwa. 3 Ga kuma waɗansu shanu bakwai munana ramammu suka fito daga cikin Nilu a bayansu, suka tsaya kusa da waɗancan shanu a bakin Nilu. 4 Sai shanun nan munana ramammu suka cinye shanun nan bakwai masu sheƙi, masu ƙibar. Sai Fir'auna ya farka. 5 Barci kuma ya kwashe shi, ya sāke yin mafarki a karo na biyu, sai zangarku bakwai masu kauri kyawawa suna girma a kara guda. 6 Ga shi kuma, a bayansu waɗansu zangarku bakwai suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta ƙeƙasar. 7 Sai siraran zangarkun suka haɗiye zangarkun nan bakwai masu kauri kyawawa. Sai Fir'auna ya farka, ashe, mafarki ne. 8 Saboda haka da safe, hankalinsa ya tashi, sai ya aika aka kirawo dukan bokayen Masar da dukan masu hikimar Masar, Fir'auna kuwa ya faɗa musu mafarkansa, amma ba wanda ya iya fassara masa su. 9 Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir'auna, “Yau, na tuna da laifofina. 10 Sa'ad da ka yi fushi da barorinka, ka sa ni da shugaban masu tuya cikin kurkukun da yake a cikin gidan shugaban masu tsaron fāda, 11 muka yi mafarki dare ɗaya, ni da shi, kowane mutum da irin tasa fassarar mafarkin. 12 Akwai wani Ba'ibrane, ɗan saurayi, tare da mu, bawan shugaban masu tsaron fāda, sa'ad da muka faɗa masa sai ya fassara mana mafarkanmu, ya yi wa ko wannenmu fassara bisa kan mafarkinsa. 13 Yadda ya fassara mana haka kuwa ya zama, aka komar da ni matsayina, mai tuya kuwa aka rataye shi.” 14 Sai Fir'auna ya aika a kirawo Yusufu, da gaggawa suka fito da shi daga cikin kurkuku. Da Yusufu ya yi aski, ya sāke tufafinsa ya zo gaban Fir'auna. 15 Fir'auna kuwa ya ce wa Yusufu, “Na yi mafarkin da ba wanda ya san fassararsa, amma na ji an ce, wai kai, in ka ji mafarkin kana iya fassara shi.” 16 Yusufu ya amsa wa Fir'auna ya ce, “Ba a gare ni ba, Allah zai amsa wa Fir'auna da kyakkyawar amsa.” 17 Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Ga shi, a cikin mafarkina ina tsaye a bakin Kogin Nilu, 18 ga shanu bakwai, masu sheƙi masu ƙiba suka fito daga cikin Nilu suna kiwo cikin iwa. 19 Sai waɗansu shanu bakwai ƙanjamammu, munana, ramammu, irin waɗanda ban taɓa ganinsu a ƙasar Masar ba, suka fito bayansu. 20 Sai ramammun, munanan shanun suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba na farko, 21 amma da suka haɗiye su, ba wanda zai iya sani sun haɗiye su, gama suna nan a ramammunsu kamar yadda suke a dā. Sai na farka. 22 Har yanzu kuma, a cikin mafarkina ga zangarku masu kauri kyawawa guda bakwai, suna girma a kara guda, 23 zangarku bakwai kuma busassu sirara waɗanda iskar gabas ta ƙeƙasar, suka fito a bayansu. 24 Siraran zangarkun kuwa suka haɗiye zangarkun nan bakwai kyawawa masu kauri. Na faɗa wa bokaye, amma ba wanda ya iya yi mini fassararsa.” 25 Yusufu ya ce wa Fir'auna, “Mafarkin Fir'auna ɗaya ne, Allah ya bayyana wa Fir'auna abin da yake shirin aikatawa. 26 Waɗannan shanu bakwai, shekaru bakwai ne, kyawawan zangarkun nan bakwai kuma shekaru bakwai ne, mafarkin ɗaya ne. 27 Ramammun shanun nan bakwai da suka fito a bayansu shekaru bakwai ne, busassun zangarkun nan bakwai waɗanda iskar gabas ta ƙeƙasar kuwa, shekaru bakwai ne na yunwa. 28 Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir'auna, Allah ya nuna wa Fir'auna abin da yake shirin aikatawa. 29 Za a yi shekara bakwai cike da ƙoshi a ƙasar Masar duka, 30 amma a bayansu za a yi shekara bakwai na yunwa, amma za a manta da dukan ƙoshin nan a ƙasar Masar, yunwar kuwa za ta game dukan ƙasar. 31 Zai kuwa zama kamar ba a taɓa yin ƙoshi a ƙasar ba, saboda tsananin yunwar. 32 Maimaitawar mafarkin nan na Fir'auna kuwa, ya nuna cewa, Allah ya riga ya ƙaddara al'amarin, hakika kuwa Allah zai tabbatar da shi ba da jimawa ba. 33 “Yanzu fa bari Fir'auna ya zaɓi mutum mai basira, mai hikima, ya sa shi bisa ƙasar Masar. 34 Bari Fir'auna ya ci gaba da naɗa shugabanni bisa ƙasa, don su tattara humushin amfanin ƙasar Masar na shekarun nan bakwai na ƙoshi. 35 Bari kuma su tattara dukan abinci a shekarun nan bakwai masu zuwa na albarka, su tsiba a ƙarƙashin ikon Fir'auna saboda abinci cikin birane, su kuma lura da shi. 36 Wannan abinci zai zama ajiya domin ƙasar, kariyar shekaru bakwai na yunwa, waɗanda za a yi cikin ƙasar Masar, domin kada ƙasar ta ƙare saboda yunwar.”

An Naɗa Yusufu Mai Mulki a Masar

37 Fir'auna da fādawansa duka sun yarda da wannan shawara. 38 Sai Fir'auna ya ce wa fādawansa, “Mā iya samun mutum irin wannan, wanda Ruhun Allah yake cikinsa?” 39 Domin haka Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Tun da yake Allah ya nuna maka waɗannan abu duka, ba wani mai basira da hikima kamarka, 40 za ka shugabanci gidana, bisa ga cewarka za a mallaki jama'ata, sai dai da sarauta kaɗai nake gaba da kai.” 41 Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Ga shi, na sa ka bisa dukan ƙasar Masar.” 42 Sai Fir'auna ya cire zobensa mai hatimi daga hannunsa ya sa a hannun Yusufu, ya sa masa rigunan lilin masu kyau, ya rataya masa sarƙar zinariya a wuya, 43 ya kuma sa shi ya hau karusarsa ta biyu, suka yi ta shela a gabansa, “Ku ba da hanya.” Ta haka fa ya sa ya zama mai mulki bisa dukan ƙasar Masar. 44 Har yanzu dai Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Ni ne Fir'auna, ba mutumin da zai ɗaga hannu ko ƙafa cikin dukan ƙasar Masar idan ba da izninka ba.” 45 Fir'auna kuwa ya sa wa Yusufu suna, Zafenat-faneya. Ya kuma aurar masa da Asenat 'yar Fotifera, firist na On. Yusufu kuwa ya fita rangadin ƙasar Masar. 46 Yusufu yana da shekara talatin lokacin da ya kama aiki a wurin Fir'auna, Sarkin Masar. Yusufu kuwa ya fita daga gaban Fir'auna ya ratsa dukan ƙasar Masar. 47 A cikin shekaru bakwai ɗin nan na ƙoshi, ƙasa ta ba da amfani mai yawan gaske, 48 sai ya tattara dukan abinci na shekarun nan bakwai da aka yi na ƙoshi a ƙasar Masar, ya kuwa tanada abinci cikin birane, a kowane birni ya tanada abinci daga karkarar da take kewaye da shi. 49 Sai Yusufu ya tsiba tsaba kamar yashin teku, har ya daina aunawa domin ba ta aunuwa saboda yawa. 50 Kafin kuwa shekarun nan na yunwa, an haifa wa Yusufu 'ya'ya biyu maza, waɗanda Asenat 'yar Fotifera, firist na On ta haifa masa. 51 Yusufu ya raɗa wa ɗan farin suna, Manassa, yana cewa, “Gama Allah ya sa ni in manta da dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.” 52 Na biyun kuma ya raɗa masa suna, Ifraimu, yana cewa, “Gama Allah ya wadata ni a cikin ƙasar wulakancina.” 53 Shekarun nan bakwai na ƙoshi da aka yi cikin ƙasar Masar sun cika, 54 aka fara shekaru bakwai na yunwa kamar yadda Yusufu ya faɗa. Sai aka yi yunwa cikin sauran ƙasashe duka, amma a ƙasar Masar akwai abinci. 55 Sa'ad da yunwa ta game dukan ƙasar, mutanen suka yi wa Fir'auna kuka domin abinci, sai Fir'auna ya faɗa wa Masarawa duka, ya ce, “Ku tafi wurin Yusufu, abin da duk ya faɗa muku, sai ku yi.” 56 Domin haka sa'ad da yunwar ta bazu ko'ina a ƙasar, Yusufu ya buɗe taskokin ajiya, ya yi ta sayar wa Masarawa, gama yunwa ta tsananta a ƙasar. 57 Duniya duka kuwa ta zo Masar wurin Yusufu, ta sayi hatsi saboda yunwa ta tsananta a duniya duka.

Farawa 42

'Yan'uwan Yusufu sun Zo Masar Sayen Abinci

1 A sa'ad da Yakubu ya ji akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa 'ya'yansa maza, “Me ya sa kuke zuba wa juna ido? 2 Ga shi kuwa, na ji akwai hatsi a Masar, ku gangara ku sayo mana hatsi a can domin mu rayu, kada mu mutu.” 3 Don haka 'yan'uwan Yusufu su goma suka gangara su sayo hatsi a Masar. 4 Amma Yakubu bai aiki Biliyaminu ɗan'uwan Yusufu tare da 'yan'uwansa ba, gama ya ce, “Kada wata ɓarna ta same shi.” 5 Haka nan 'ya'yan Isra'ila maza suka zo su sayi hatsi tare da sauran matafiya, gama ana yunwa a ƙasar Kan'ana. 6 Yanzu fa, Yusufu shi ne mai mulkin ƙasar, shi ne kuwa mai sayar wa jama'ar ƙasar duka. 'Yan'uwan Yusufu suka zo suka sunkuya har ƙasa a gabansa. 7 Da Yusufu ya ga 'yan'uwansa, ya gane da su, amma ya mai da su kamar baƙi, ya yi musu magana da gautsi ya ce, “Daga ina kuka fito?” Suka ce, “Daga ƙasar Kan'ana muka zo sayen abinci.” 8 Yusufu kuwa ya gane da 'yan'uwansa amma su ba su gane shi ba. 9 Sai Yusufu ya tuna da mafarkan da ya yi a kansu, ya ce musu, “Ku magewaya ne, zuwa kuka yi domin ku leƙi asirin ƙasar.” 10 Suka ce masa, “A'a, shugabanmu, domin sayen abinci bayinka suka zo. 11 Mu duka 'ya'yan mutum guda ne, amintattu kuma, bayinka ba magewaya ba ne.” 12 Yusufu ya ce musu, “A'a! Ku dai kun zo ku ga inda ƙasarmu yake da rashin ƙarfi.” 13 Suka ce, “Mu bayinka, 'yan'uwan juna ne, mu goma sha biyu muke maza, 'ya'yan mutum guda a ƙasar Kan'ana, ga shi kuwa autanmu yana tare da mahaifinmu a yanzu, ɗayan kuwa ya rasu.” 14 Amma Yusufu ya ce musu, “Ai, kamar dai yadda na faɗa muku, magewaya ne ku. 15 Ta haka za a jarraba ku, da ran Fir'auna, ba za ku fita daga nan wurin ba, sai autanku ya zo nan. 16 Ku aiki ɗaya daga cikinku ya kawo ɗan'uwanku, amma ku, za a tsare ku, don a tabbatar da maganarku, ko akwai gaskiya cikinku, idan ba haka ba kuwa, da ran Fir'auna, lalle ku magewaya ne.” 17 Sai ya tura su cikin waƙafi har kwana uku. 18 A kan rana ta uku, Yusufu ya ce musu, “Abin da za ku yi in bar ku da rai ke nan, gama ina tsoron Allah, 19 sai ku bar ɗan'uwanku ɗaya a tsare a inda aka kulle ku. Idan amintattu ne ku, sauran kuwa su tafi su kai hatsi ga iyalanku mayunwata, 20 sa'an nan su kawo mini autanku. Ta haka za a tabbatar da maganarku, har a bar ku da rai.” Haka kuwa suka yi. 21 Sai suka ce wa junansu, “A ainihin gaskiya, muna da laifi dangane da ɗan'uwanmu, da yake mun ga wahalar da yake sha, sa'ad da kuma ya roƙe mu mu taimake shi, amma ba mu saurara ba, domin haka wannan wahala ta sauko mana.” 22 Sai Ra'ubainu ya amsa musu, “Ashe, dā ma ban faɗa muku kada ku cuci yaron ba? Amma ba ku saurara ba. To, ga shi fa, ana neman hakkinsa yanzu.” 23 Ba su sani ba, ashe, Yusufu yana jinsu, domin akwai tafinta a tsakaninsu. 24 Ya juya waje ɗaya ya yi kuka, sai ya sāke komawa wurinsu ya yi magana da su. Ya ɗauki Saminu daga cikinsu ya ɗaure shi a kan idonsu.

'Yan'uwan Yusufu suka Komo Kan'ana

25 Yusufu ya umarta a cika tayakan da hatsi, a kuma mayar wa kowa da kuɗinsa cikin taikinsa, a kuma ba su guzuri don hanya. Haka kuwa aka yi musu. 26 Suka labta wa jakunansu hatsi, suka tashi. 27 Da ɗaya daga cikinsu ya buɗe taikinsa domin ya ba jakinsa tauna a zango, sai ya ga kuɗinsa a bakin taikinsa. 28 Ya ce wa 'yan'uwansa, “An mayar mini da kuɗina, ga shi nan a taiki!” Zuciyarsu ta karai sai suka juya suna duban juna, suna makyarkyata suna cewa, “Me ke nan da Allah ya yi mana?” 29 Sa'ad da suka zo wurin mahaifinsu Yakubu a ƙasar Kan'ana, suka faɗa masa dukan abin da ya same su, suna cewa, 30 “Mutumin, shugaban ƙasar, ya yi mana magana da gautsi, ya ɗauke mu a magewayan ƙasa. 31 Amma muka ce masa, ‘Mu amintattu ne, mu ba magewaya ba ne. 32 Mu sha biyu ne 'yan'uwan juna, 'ya'ya maza na mahaifinmu, ɗayan ya rasu, autan kuwa yana tare da mahaifinmu a yanzu haka a ƙasar Kan'ana.’ 33 “Sai mutumin, shugaban ƙasar, ya ce mana, ‘Ta haka zan sani ko ku amintattu ne, ku bar ɗan'uwanku ɗaya tare da ni, ku ɗauki hatsi domin iyalanku mayunwata, ku yi tafiyarku. 34 Ku kawo mini autanku, da haka zan sani ku ba magewaya ba ne, amma amintattu ne, zan kuma ba ku ɗan'uwanku, ku yi ta ciniki a ƙasar.’ ” 35 Da zazzagewar tayakansu ga ƙunshin kuɗin ko wannensu a cikin taikinsa. Sa'ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshin kuɗinsu, suka razana. 36 Sai Yakubu mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashi, ga shi, ba Yusufu, Saminu ba shi, wai kuma yanzu za ku ɗauki Biliyaminu, ga dai irin abubuwan da suka faɗo mini.” 37 Ra'ubainu kuwa ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe 'ya'yana biyu maza idan ban komo da shi ba, ka sa shi a hannuna, zan kuwa komo maka da shi.” 38 Amma ya ce, “Ɗana ba zai gangara tare da ku ba, ga ɗan'uwansa ya rasu, shi kaɗai kuwa ya ragu. Zai yiwu a kashe shi a hanya. Na tsufa ƙwarai ba zan iya ɗaukar wannan baƙin ciki ba, zai kashe ni.”

Farawa 43

'Yan'uwan Yusufu sun Sāke Komawa Masar da Biliyaminu

1 A halin yanzu, yunwa ta tsananta a ƙasar. 2 Sa'ad da suka cinye hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ɗan abinci.” 3 Amma Yahuza ya ce masa, “Mutumin fa, ya yi mana faɗakarwa sosai, ya ce, ‘Idan ba tare da autanku kuka zo ba, ba za ku ga fuskata ba.’ 4 In za ka yarda ka aiki ɗan'uwanmu tare da mu, sai mu gangara mu sayo muku abinci. 5 Amma idan ba haka ba, ba za mu tafi ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku ga fuskata ba idan ba ku zo tare da ɗan'uwanku ba.’ ” 6 Sai Isra'ila ya ce, “Don me kuka cuce ni, da kuka faɗa wa mutumin nan, kuna da wani ɗan'uwa?” 7 Suka amsa, “Ai, mutumin ne ya yi ta tambayar labarinmu da na danginmu, yana cewa, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna kuma da wani ɗan'uwa?’ Abin da muka faɗa masa amsoshi ne na waɗannan tambayoyi. Ta ƙaƙa za mu iya sani zai ce, ‘Ku zo da ɗan'uwanku?’ ” 8 Sai Yahuza ya ce wa Isra'ila, mahaifinsu, “Ka sa saurayin a hannuna, mu tashi mu tafi, mu sami abinci mu rayu, kada mu mutu, da mu da kai da ƙanananmu. 9 Na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. Idan ban komo maka da shi, in kawo shi a gabanka ba, bari alhakin ya zauna a kaina har abada, 10 gama da ba don mun yi jinkiri ba, da yanzu, ai, mun yi sawu biyu.” 11 Mahaifinsu, Isra'ila ya ce musu, “In tilas haka zai zama, sai ku yi wannan, ku ɗiba daga cikin zaɓaɓɓu, mafiya kyau na albarkar ƙasar a cikin tayakanku, ku kai wa mutumin tsaraba, da ɗan man shafawa na ƙanshi da 'yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta, da ɓaure. 12 Ku ɗauki kuɗi riɓi biyu a hannunku, ku kuma ɗauki kuɗin da aka mayar muku a tayakanku, kila kuskure ne aka yi. 13 Ku kuma ɗauki ɗan'uwanku, ku tashi ku sāke komawa wurin mutumin. 14 Allah Maɗaukaki ya ba ku tagomashi a gun mutumin, har da zai sakar muku da ɗaya ɗan'uwan nan naku tare da Biliyaminu kuma. Ni kuwa idan na yi rashi, na rasa ke nan.” 15 Sai mutane suka ɗauki tsarabar, suka kuma ɗauki riɓin kuɗin a hannunsu tare da Biliyaminu. Suka tashi suka gangara zuwa Masar, suka shiga wurin Yusufu. 16 Sa'ad da Yusufu ya ga Biliyaminu tare da su, ya faɗa wa mai hidimar gidansa, ya ce, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.” 17 Mutumin kuwa ya yi kamar yadda Yusufu ya faɗa masa, ya shigo da mutanen a gidan Yusufu. 18 Mutanen suka tsorata sabili da an kawo su a cikin gidan Yusufu, sai suka ce, “Ai, saboda kuɗin da aka mayar mana cikin tayakanmu a zuwanmu na farko, shi ya sa aka shigar da mu, domin ya nemi hujja a kanmu, ya fāɗa mana, ya maishe mu bayi, ya kuma ƙwace jakunanmu.” 19 Sai suka hau wurin mai hidimar gidan Yusufu, suka yi magana da shi a ƙofar gida, 20 suka ce, “Ya shugaba, mun zo a karo na farko sayen abinci, 21 amma da muka isa zango muka buɗe tayakanmu sai ga kuɗin ko wannenmu cif cif bakin taikinsa, don haka ga su a hannunmu, mun sāke komowa da su, 22 ga waɗansu kuɗin kuma mun riƙo a hannunmu, mun gangaro mu ƙara sayen abinci. Ba mu san wanda ya sa kuɗin nan namu a tayakanmu ba.” 23 Ya amsa ya ce, “Salama na tare da ku, kada ku ji tsoro, Allahnku da Allah na mahaifinku ne kaɗai ya sa muku dukiyar cikin tayakanku. Na karɓi kuɗinku.” Sai ya fito musu da Saminu. 24 Da mutumin ya kawo su gidan Yusufu, ya ba su ruwa, suka kuwa wanke ƙafafunsu, sa'an nan kuma ya bai wa jakunansu tauna, 25 sai suka shirya tsarabar, domin Yusufu yana zuwa da tsakar rana, saboda sun ji, wai zai ci abinci a nan. 26 Sa'ad da Yusufu ya koma gida, suka kawo tsarabar da suka riƙo masa cikin gida, suka sunkuya har ƙasa a gabansa. 27 Ya tambayi lafiyarsu ya ce, “Mahaifinku yana lafiya, tsohon nan da kuka yi magana a kansa? Yana nan da rai?” 28 Sai suka amsa, “Bawanka, mahaifinmu yana lafiya, har yanzu yana da rai.” Suka sunkuya suka yi masa mubaya'a. 29 Sai ya ɗaga idanunsa, ya ga ɗan'uwansa Biliyaminu, ɗan da mahaifiyarsa ta haifa, ya ce, “Wannan shi ne auta naku, wanda kuka yi mini magana a kansa? Allah ya yi maka alheri, ɗana!” 30 Da Yusufu ya ji kamar zai yi kuka sabili da zuciyarsa tana begen ɗan'uwansa, sai ya gaggauta ya nemi wurin yin kuka. Ya shiga ɗakinsa, a can ya yi kuka. 31 Sa'an nan ya wanke fuskarsa, ya fito ya ɗaure, ya umarta a kawo abinci. 32 Aka hidimta masa shi kaɗai, su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sukan ci abinci tare da Ibraniyawa ba, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa. 33 Aka zaunar da 'yan'uwan Yusufu a gaban Yusufu bisa ga shekarunsu na haihuwa, daga babba zuwa ƙarami. 'Yan'uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki. 34 Daga teburin da yake a gabansa aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Biliyaminu ya yi biyar ɗin na ko wannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.

Farawa 44

Finjalin Yusufu a Taikin Biliyaminu

1 Yusufu ya umarci mai hidimar gidansa, ya ce, “Cika tayakan mutanen nan da abinci iyakar yadda za su iya ɗauka, ka kuma sa kuɗin kowanne a bakin taikinsa, 2 ka sa finjalina na azurfa a bakin taikin autan, tare da kuɗinsa na hatsin.” Sai ya yi kamar yadda Yusufu ya faɗa masa. 3 Gari na wayewa aka sallami mutanen da jakunansu. 4 Tun ba su riga suka yi nisa da garin ba, Yusufu ya ce wa mai hidimar gidansa, “Tashi, ka bi mutanen, in ka iske su ka ce musu, 5 ‘Don me kuka rama alheri da mugunta? Don me kuka sace mini finjalina na azurfa? Da shi ne maigidana ke sha, da shi ne kuma yake yin istihara. Kun yi kuskure da kuka yi haka.’ ” 6 Lokacin da ya iske su sai ya yi musu waɗannan maganganu. 7 Suka ce masa, “Don me shugabana zai faɗi irin waɗannan maganganu? Allah ya sawwaƙe da bayinka za su aikata irin wannan! 8 Ga shi, kuɗin da muka samu a bakin tayakanmu, mun komo maka da su tun daga ƙasar Kan'ana, ta yaya fa, za mu saci azurfa ko zinariya daga gidan maigidanka? 9 Daga cikinmu barorinka, duk wanda aka sami abin a wurinsa, bari ya mutu, mu kuwa mu zama bayinka, ranka ya daɗe.” 10 Ya ce, “Bari ya zama kamar yadda kuka faɗa, shi wanda aka sami abin a wurinsa zai zama bawana, sauranku kuwa za ku tafi lafiya.” 11 Nan da nan kowa ya saukar da taikinsa ƙasa, kowa kuwa ya buɗe taikinsa. 12 Ya bincika, ya fara daga babba zuwa ƙarami, sai aka iske finjalin a cikin taikin Biliyaminu. 13 Suka kyakkece rigunansu, ko wannensu kuwa ya yi wa jakinsa labtu suka koma birnin. 14 Sa'ad da Yahuza da 'yan'uwansa suka zo gidan Yusufu, suka iske yana nan har yanzu, sai suka fāɗi ƙasa a gabansa. 15 Yusufu ya ce musu, “Wane abu ke nan kuka aikata? Ba ku sani ba, mutum kamata yakan yi istihara?” 16 Sai Yahuza ya amsa, “Me za mu ce wa shugabana? Wace magana za mu yi? Ko kuwa, ta yaya za mu baratar da kanmu? Allah ne ya tona laifin bayinka, ga mu, mu bayin shugabana ne, da mu da shi wanda aka sami finjalin a wurinsa.” 17 Amma Yusufu ya ce, “Allah ya sawwaƙe mini da in yi haka! Sai shi wanda aka sami finjalin a hannunsa, shi zai zama bawana, amma ku, ku yi tafiyarku lafiya zuwa wurin mahaifinku.” 44 .18 Yahuza ya yi G�d� domin Biliyaminu Yahuza ya yi G�d� domin Biliyaminu 18 Yahuza ya je wurin Yusufu ya ce, “Ya shugabana, ina roƙonka, ka bar bawanka ya yi magana a kunnuwanka, kada kuma ka bar fushinka ya yi ƙuna bisa bawanka, gama daidai da Fir'auna kake. 19 Ranka ya daɗe, ka tambaye mu, ka ce, ‘Kuna da mahaifi ko ɗan'uwa?’ 20 Sai muka amsa, ranka ya daɗe, muka ce, ‘Muna da mahaifi, tsoho, da ɗan tsufansa, auta, wanda ɗan'uwansa ya rasu, shi kaɗai ya ragu daga cikin mahaifiyarsa, mahaifinsa kuwa yana ƙaunarsa.’ 21 Sai ka ce wa barorinka, ‘Ku kawo shi wurina, don in gan shi.’ 22 Ranka ya daɗe, muka kuwa ce, ‘Saurayin ba zai iya rabuwa da mahaifinsa ba, gama in ya rabu da mahaifinsa, mahaifinsa zai mutu.’ 23 Sai ka amsa wa barorinka, ka ce, ‘In ba autanku ya zo tare da ku ba, ba za ku ƙara ganin fuskata ba.’ 24 “Sa'ad da muka koma a wurin baranka, mahaifinmu, muka mayar masa da dukan abin da ka ce. 25 Don haka sa'ad da mahaifinmu ya ce, ‘Koma, ku sayo mana ɗan abinci,’ 26 sai muka ce, ‘Ba za mu iya gangarawa ba, amma idan autanmu zai tafi tare da mu, za mu gangara, gama ba dama mu ga fuskar mutumin sai ko autanmu yana tare da mu.’ 27 Sa'an nan baranka, mahaifinmu, ya ce mana, ‘Kun sani 'ya'ya biyu matata ta haifa mini, 28 ɗayan ya bar ni, na kuwa ɗauka, hakika an yayyage shi kaca kaca, gama ban ƙara ganinsa ba. 29 In kuka ɗauke wannan kuma daga gare ni, mai yiwuwa ne a kashe shi, to, za ku sa baƙin ciki ya ishe ni, da tsufana, har ya kashe ni.’ 30-31 “Domin haka kuwa, yanzu, idan na koma wurin baranka, mahaifina, ba tare da saurayin ba, in har bai ga yaron tare da ni ba, zai mutu, gama ransa ya shaƙu da saurayin, barorinka kuwa za su sa baranka, mahaifinmu, ya mutu cikin baƙin ciki, da tsufansa. 32 Gama ni baranka na ɗauki lamunin saurayin wurin mahaifinsa da cewa, ‘In ban komo maka da shi ba, sai alhakinsa ya zauna a kaina a gaban mahaifina dukan raina.’ 33 Domin haka fa, ina roƙonka, bari ni baranka in zama bawa gare ka, shugabana, a maimakon saurayin a bar saurayin ya koma tare da 'yan'uwansa. 34 Gama yaya zan iya komawa wurin mahaifina, in saurayin ba ya tare da ni? Ina jin tsoron ganin ɓarnar da za ta auko wa mahaifina.”

Farawa 45

Yusufu ya Bayyana Kansa ga 'Yan'uwansa

1 Yusufu ya kasa daurewa a gaban dukan waɗanda suke a tsaye kusa da shi, sai ya ta da murya ya ce, “Kowa ya ba mu wuri.” Saboda haka ba mutumin da ya tsaya a wurin sa'ad da Yusufu ya bayyana kansa ga 'yan'uwansa. 2 Ya yi kuka da ƙarfi, har Masarawa suka ji, labarin kuwa ya kai gidan Fir'auna. 3 Yusufu kuwa ya ce wa 'yan'uwansa, “Ni ne Yusufu. Mahaifina yana da rai har yanzu?” Amma 'yan'uwansa ba su iya ba shi amsa ba, gama sun firgita a gabansa. 4 Yusufu ya ce wa 'yan'uwansa. “Ku matso kusa da ni, ina roƙonku.” Suka matso kusa. Sai ya ce, “Ni ne ɗan'uwanku, Yusufu, wanda kuka sayar zuwa Masar. 5 Yanzu fa, kada ku damu ko kuwa ku ji haushin kanku domin kun sayar da ni a nan, gama Allah ne ya aike ni a gabanku don in ceci rai. 6 Gama shekara biyu ke nan da ake yunwa a ƙasar, amma da sauran shekara biyar masu zuwa da ba za a yi noma ko girbi ba. 7 Allah kuwa ya aike ni a gabanku, domin in cetar muku da ringi a duniya, in kuma rayar muku kuɓutattu masu yawa. 8 Don haka, ba ku kuka aiko ni nan ba, amma Allah ne, shi ne kuwa ya sa in zama uba ga Fir'auna, da shugaban gidansa duka, mai mulki kuma bisa ƙasar Masar duka. 9 “Ku gaggauta, ku hau zuwa wurin mahaifina ku ce masa, ‘Ga abin da Yusufu ɗanka ya ce, “Allah ya maishe ni shugaban Masar duka, ka gangaro wurina kada ka yi wata wata. 10 Za ka zauna a ƙasar Goshen, za ka zauna kusa da ni, kai da 'ya'yanka da jikokinka, da garkunan awaki da na tumaki, da garkunanka na shanu, da dukan abin da kake da shi. 11 A nan zan cishe ka, gama akwai sauran shekara biyar masu zuwa na yunwa, don kada ka tsiyace, kai da iyalinka, da duk wanda yake tare da kai.” ’ 12 Yanzu, da idanunku kun gani, idanun ɗan'uwana Biliyaminu kuma sun gani, cewa, bakina ne yake magana da ku. 13 Ku faɗa wa mahaifina dukan darajar da nake da ita a Masar da dukan abin da kuka gani. Ku gaggauta ku gangaro mini da mahaifina a nan.” 14 Sai Yusufu ya rungumi ɗan'uwansa Biliyaminu ya yi ta kuka, Biliyaminu ma ya yi kuka a bisa kafaɗun Yusufu. 15 Ya sumbaci 'yan'uwansa duka, ya yi kuka bisansu, bayan wannan sai 'yan'uwansa suka yi taɗi da shi. 16 Sa'ad da labari ya kai gidan Fir'auna cewa, “'Yan'uwan Yusufu sun zo,” abin ya yi wa Fir'auna da fādawansa daɗi ƙwarai. 17 Sai Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Ka faɗa wa 'yan'uwanka su yi wannan, ‘Ku yi wa dabbobinku laftu ku koma a ƙasar Kan'ana. 18 Ku ɗauko mahaifinku da iyalanku, ku zo wurina, ni kuwa zan ba ku yankin ƙasa mafificiya a Masar, za ku ci moriyar ƙasar.’ 19 Ka kuma umarce su ka ce, ‘Ku ɗauki kekunan shanu daga ƙasar Masar domin 'yan ƙanananku da matanku, ku ɗauko mahaifinku, ku zo. 20 Kada ku damu da kayayyakinku, gama abin da yake mafi kyau duka a ƙasar Masar naku ne.’ ” 21 Haka kuwa 'ya'yan Isra'ila suka yi. Yusufu kuma ya ba su kekunan shanu bisa ga umarnin Fir'auna, ya ba su guzuri don hanya. 22 Ga kowane ɗayansu ya ba da rigar ado, amma ga Biliyaminu ya ba da azurfa ɗari uku, da rigunan ado biyar. 23 Ga mahaifinsa kuwa ya aika da jakai goma ɗauke da kyawawan abubuwa na Masar, da jakai mata goma ɗauke da tsaba, da kuma abinci da guzurin hanya saboda mahaifinsa. 24 Ya sallami 'yan'uwansa. Da suna shirin tashi, sai ya ce musu, “Kada ku yi faɗa a hanya.” 25 Suka haura daga Masar, suka zo ƙasar Kan'ana zuwa wurin Yakubu mahaifinsu. 26 Suka ce masa, “Har yanzu Yusufu yana nan da rai, shi ne kuwa mai mulki bisa ƙasar Masar duka.” Sai gabansa ya fāɗi, domin bai gaskata su ba. 27 Amma sa'ad da suka faɗa masa jawaban Yusufu duka, waɗanda ya faɗa musu, sa'ad da kuma ya ga kekunan shanun da Yusufu ya aiko don a ɗauke shi, sai ruhun mahaifinsu Yakubu ya farfaɗo. 28 Isra'ila ya ce, “I, ya isa, ɗana Yusufu yana da rai har yanzu. Zan tafi in gan shi kafin in mutu.”

Farawa 46

Yakubu da Iyalinsa suka Tafi Masar

1 Isra'ila ya kama tafiyarsa da dukan abin da yake da shi. Ya zo Biyer-sheba, ya kuwa ba da hadayu ga Allah na mahaifinsa Ishaku. 2 Sai Allah ya yi magana cikin wahayin dare, ya ce, “Yakubu.” Ya amsa ya ce, “Na'am.” 3 Sai ya ce, “Ni ne Allah, Allah na mahaifinka, kada ka ji tsoron zuwa Masar, gama a can zan maishe ka babbar al'umma. 4 Ni kuwa zan gangara tare da kai zuwa Masar, ni kuma zan sāke haurowa tare da kai. Lokacin mutuwarka za ka mutu a hannun Yusufu.” 5 Sai Yakubu ya tashi daga Biyer-sheba, 'ya'yan Isra'ila maza kuwa suka ɗauki mahaifinsu Yakubu, da 'yan ƙananansu da matansu a cikin kekunan shanun da Fir'auna ya aika a ɗauko su. 6 Suka kuma kora shanunsu, suka ɗauki kayayyakinsu waɗanda suka samu a ƙasar Kan'ana, suka iso Masar, Yakubu da zuriyarsa duka, 7 'ya'yansa maza da jikokinsa maza tare da shi, 'ya'yansa mata, da jikokinsa mata, ya kawo zuriyarsa dukka zuwa ƙasar Masar. 8 Waɗannan su ne sunayen 'ya'ya maza na Isra'ila, wato, Yakubu, waɗanda suka iso Masar. Ra'ubainu, ɗan farin Yakubu. 9 'Ya'yan Ra'ubainu, maza kuwa, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi. 10 'Ya'yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Ohad, da Yakin, da Zohar, da Shawul ɗan wata Bakan'aniya. 11 'Ya'yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari. 12 'Ya'yan Yahuza, maza, su ne Er, da Onan, da Shela, da Feresa, da Zera, (amma Er da Onan suka rasu a ƙasar Kan'ana). 'Ya'yan Feresa, maza kuwa, su ne Hesruna da Hamul. 13 'Ya'yan Issaka, maza, su ne Tola, da Fuwa, da Yashub, da Shimron. 14 'Ya'yan Zabaluna, maza, su ne Sered, da Elon, da Yaleyel, 15 (waɗannan su ne 'ya'yan Lai'atu, maza, waɗanda ta haifa wa Yakubu cikin Fadan-aram, da 'ya tasa kuma Dinatu, 'ya'yansa mata da maza duka, mutum talatin da uku ne). 16 'Ya'yan Gad, maza, su ne Zifiyon, da Haggi, da Shuni, da Ezbon, da Eri, da Arodi, da Areli. 17 'Ya'yan Ashiru, maza, su ne Yimna, da Yishuwa, da Yishwi, da Beriya, da Sera, 'yar'uwarsu. 'Ya'yan Beriya, maza kuma, su ne Eber da Malkiyel. 18 Waɗannan su goma sha shida, su ne zuriyar Yakubu, maza, na wajen Zilfa, wadda Laban ya bai wa Lai'atu, 'yarsa. 19 'Ya'ya maza, na Rahila, matar Yakubu, su ne Yusufu da Biliyaminu. 20 Asenat 'yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusufu Manassa da Ifraimu a ƙasar Masar. 21 'Ya'yan Biliyaminu, maza, su ne Bela, da Beker, da Ashbel, da Gera, da Na'aman, da Ahiram, da Rosh, da Muffim, da Huffim, da Adar. 22 Waɗannan su goma sha huɗu su ne zuriyar Yakubu, maza, na wajen Rahila. 23 Hushim shi ne ɗan Dan. 24 'Ya'yan Naftali, maza, su ne Yazeyel, da Guni, da Yezer, da Shallum. 25 Waɗannan su bakwai, su ne zuriyar Yakubu, maza, na wajen Bilha, wadda Laban ya bai wa 'yarsa Rahila. 26 Mutanen Yakubu dukka da suka shiga Masar, waɗanda suke zuriyarsa ne, banda matan 'ya'yansa, su mutum sittin da shida ne. 27 'Ya'yan Yusufu, maza, waɗanda aka haifa masa a Masar su biyu ne. Dukkan mutane na gidan Yakubu da suka zo Masar su saba'in.

Yakubu da Iyalinsa a Masar

28 Isra'ila kuwa ya aiki Yahuza ya yi gaba zuwa wurin Yusufu ya faɗa masa ya sadu da shi a nuna masa Goshen. Da suka zo ƙasar Goshen, 29 sai Yusufu ya kintsa karusarsa ya haura zuwa Goshen don ya taryi Isra'ila, mahaifinsa. Nan da nan da isowarsa wurinsa, ya rungume shi, ya jima yana ta kuka a kafaɗarsa. 30 Isra'ila ya ce wa Yusufu, “To, bari in mutu yanzu, tun da na ga fuskarka na sani kuma kana da rai har yanzu.” 31 Yusufu ya ce wa 'yan'uwansa da iyalin gidan mahaifinsa, “Zan tafi in faɗa wa Fir'auna, in ce masa, ‘'Yan'uwana da iyalin gidan mahaifina, waɗanda dā suke a ƙasar Kan'ana, sun zo wurina, 32 mutanen kuwa makiyaya ne, sun kuwa zo da garkunansu na awaki da na tumaki, da garkunansu na shanu, da dukkan abin da suke da shi.’ 33 To, sa'ad da Fir'auna zai kira ku, ya tambaye ku, ‘Mece ce sana'arku?’ 34 Sai ku ce, ‘Ranka ya daɗe, mu makiyayan shanu ne tun muna 'yan yara har zuwa yau, da mu da kakanninmu,’ don ku sami wurin zama a ƙasar Goshen, gama kowane makiyayi abin ƙyama ne ga Masarawa.”

Farawa 47

1 Yusufu ya shiga ya yi magana da Fir'auna, ya ce, “Mahaifina da 'yan'uwana, da garkunansu na awaki da na tumaki, da garkunan shanu, da dukan abin da suka mallaka, sun zo daga ƙasar Kan'ana, yanzu suna ƙasar Goshen.” 2 Daga cikin 'yan'uwansa kuma ya ɗauki mutum biyar ya gabatar da su a gaban Fir'auna. 3 Sai Fir'auna ya ce wa 'yan'uwan nan nasa, “Mece ce sana'arku?” Suka amsa wa Fir'auna, suka ce, “Ranka ya daɗe, mu makiyaya ne, kamar yadda iyayenmu suke.” 4 Suka kuma ce wa Fir'auna, “Ranka ya daɗe, mun zo baƙunci ne cikin ƙasar, gama ba wurin kiwo domin garkunan bayinka, gama yunwa ta tsananta a ƙasar Kan'ana. Yanzu muna roƙonka, ka yarda wa bayinka su zauna a ƙasar Goshen.” 5 Fir'auna ya ce wa Yusufu, “Mahaifinka da 'yan'uwanka sun zo wurinka. 6 Ƙasar Masar tana gabanka. Ka zaunar da mahaifinka da 'yan'uwanka a ƙasa mai kyau, bari su zauna a ƙasar Goshen. In kuma ka san da waɗansu waɗanda suka dace a cikinsu, ka sa su su lura da shanuna.” 7 Yusufu kuwa ya shigo da Yakubu mahaifinsa, ya tsai da shi a gaban Fir'auna, Yakubu kuwa ya sa wa Fir'auna albarka. 8 Fir'auna kuma ya ce wa Yakubu, “Nawa ne shekarun haihuwarka?” 9 Yakubu ya ce wa Fir'auna, “Shekaruna na zaman baƙuncina, shekara ce ɗari da talatin, shekaruna kima ne cike kuma da wahala, ba su kuwa kai yawan shekarun kakannina ba, cikin baƙuncinsu.” 10 Yakubu kuwa ya sa wa Fir'auna albarka, sa'an nan ya fita daga gaban Fir'auna. 11 Sai Yusufu ya zaunar da mahaifinsa da 'yan'uwansa, ya kuwa ba su mahalli a ƙasar Masar, cikin ƙasa mafi kyau a ƙasar Remesse, kamar yadda Fir'auna ya umarta. 12 Yusufu ya bai wa mahaifinsa da 'yan'uwansa da dukan iyalin gidan mahaifinsa abinci, bisa ga yawan 'ya'yansu.

Hidimar Yusufu a Lokacin Yunwa

13 A yanzu cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwar ta tsananta ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan'ana suka matsu saboda yunwar. 14 Yusufu kuwa ya ƙwalƙwale dukan kuɗin da yake akwai a ƙasar Masar da a ƙasar Kan'ana, domin hatsin da suka saya. Yusufu kuma ya kawo kuɗin cikin gidan Fir'auna. 15 Sa'ad da aka kashe kuɗin da yake a Masar duka da na ƙasar Kan'ana, Masarawa duka suka zo wurin Yusufu, suka ce, “Ka ba mu abinci, don me za mu mutu a kan idonka? Gama kuɗinmu sun ƙare.” 16 Yusufu ya amsa, ya ce, “Ku ba da shanunku, ni kuwa zan ba ku abinci a madadin shanunku in kuɗinku sun ƙare.” 17 Saboda haka suka kai wa Yusufu dabbobinsu, sai Yusufu ya ba su abinci madadin dawakai da garkunan awaki da na tumaki, da garkunan shanu da na jakai, ya tallafe su da abinci a madadin dabbobinsu duka a wannan shekara. 18 Sa'ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biyu, suka ce masa, “Ranka ya daɗe. Ba za mu ɓoye wa shugabanmu ba cewa, kuɗinmu duka mun kashe, garkunan dabbobin kuma sun zama naka. Banda jikunanmu da gonakunmu, ba kuwa abin da ya rage mana. 19 Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakunmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir'auna, ka kuma ba mu iri domin mu rayu, kada mu mutu don kuma kada ƙasar ta zama kango.” 20 Ta haka Yusufu ya saya wa Fir'auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da saurukansu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama halaliyar Fir'auna. 21 Yusufu ya mai da jama'ar bayi daga wannan kan iyaka na Masar zuwa wancan. 22 Sai gonakin firistoci ne kaɗai bai saya ba, gama firistocin suna da rabo wanda Fir'auna ya yanka musu, da rabon da Fir'auna yake ba su suke zaman gari, sabili da haka ba su sayar da gonakinsu ba. 23 Yusufu ya ce wa jama'ar, “Ga shi, a yau na saya wa Fir'auna ku da gonakinku. Yanzu fa, ga iri dominku, za ku shuka gonakin. 24 Da haka za ku ba da kashi ɗaya cikin biyar ga Fir'auna, kashi huɗu cikin biyar kuwa ya zama naku din iri na shuka a gonakinku, don kuma abincinku, da na iyalan gidanku, da na 'yan ƙanananku.” 25 Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ko ya gamshe ka, ya shugaba, mā zama bayin Fir'auna.” 26 Sai Yusufu ya kafa doka daga wannan rana har wa yau game da ƙasar Masar wadda ta ce, Fir'auna zai sami kashi ɗaya daga cikin biyar, sai dai gonakin firistoci kaɗai ne ba su zama na Fir'auna ba.

Wasiyyar Yakubu

27 Ta haka fa Isra'ila ya yi zamansa a ƙasar Masar a ƙasar Goshen, suka kuwa sami mahalli a cikinta suka hayayyafa suka riɓaɓɓanya ƙwarai. 28 Yakubu kuma ya zauna a ƙasar Masar shekara goma sha bakwai, don haka kwanakin Yakubu, wato, shekarun ransa, shekara ce ɗari da arba'in da bakwai. 29 A sa'ad da lokaci ya gabato da Isra'ila zai mutu, ya kira ɗansa Yusufu ya ce masa, “Idan zan sami tagomashi a idonka, ka sa hannunka a ƙarƙashin cinyata, ka ɗau alkawari za ka aikata mini aminci da gaskiya. Kada ka binne ni a Masar, 30 amma bari in kwanta tare da kakannina, ka ɗauke ni daga Masar, ka binne ni a makabartarsu.” Ya amsa ya ce, “Zan aikata yadda ka faɗa.” 31 Sai Yakubu ya ce, “Rantse mini.” Sai Yusufu ya rantse masa. Sa'an nan sai Isra'ila ya mai da kai bisa kan gadonsa.

Farawa 48

Yakubu ya Sa wa Ifraimu da Manassa Albarka

1 Ya zama fa bayan waɗannan al'amura, aka faɗa wa Yusufu, “Ga mahaifinka yana ciwo.” Sai ya ɗauki 'ya'yansa biyu maza, Manassa da Ifraimu ya tafi ya gai da mahaifinsa. 2 Sa'ad da aka ce wa Yakubu, “Ɗanka Yusufu ya zo wurinka,” sai Yakubu ya ƙoƙarta ya tashi zaune a kan gadon. 3 Yakubu ya ce wa Yusufu, “Allah Maɗaukaki ya bayyana gare ni a Luz a ƙasar Kan'ana ya sa mini albarka, 4 ya ce mini, ‘Ga shi, zan sa ka hayayyafa, in riɓaɓɓanya ka, zan maishe ka ƙungiyar al'ummai, zan kuwa ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka ta zama madawwamiyar mallaka.’ 5 Yanzu fa, a kan waɗannan 'ya'yanka maza biyu da aka haifa a Masar kafin zuwana, su nawa ne, Ifraimu da Manassa za su zama nawa, kamar yadda su Ra'ubainu da Saminu suke. 6 'Ya'ya waɗanda za a haifa a bayansu za su zama naka, za a kira su da sunan 'yan'uwansu cikin gādonsu. 7 Sa'ad da nake zuwa daga Mesofotamiya, sai Rahila ta rasu a hannuna a ƙasar Kan'ana a kan hanya, ga shi kuwa, da sauran tazara kafin a kai Efrata. Na kuwa binne ta a Efrata,” wato, Baitalami. 8 Sa'ad da Isra'ila ya ga 'ya'yan Yusufu, maza, ya ce, “Suwane ne waɗannan?” 9 Sai Yusufu ya ce wa mahaifinsa, “'Ya'yana ne maza waɗanda Allah ya ba ni a nan.” Sai ya ce, “Kawo su gare ni, ina roƙonka, domin in sa musu albarka.” 10 Yanzu fa, idanun Isra'ila sun dushe saboda yawan shekaru, har ba ya iya gani. Sai Yusufu ya kawo su kusa da shi, ya sumbace su ya rungume su. 11 Isra'ila ya ce wa Yusufu, “Ban yi zaton zan ga fuskarka ba, ga shi kuwa, Allah ya sa na gani har da na 'ya'yanka.” 12 Yusufu ya kawar da su daga gwiwoyin Isra'ila, ya sunkuyar da fuskarsa har ƙasa a gabansa. 13 Yusufu ya ɗauki su biyu ɗin, Ifraimu a hannunsa na dama zuwa hannun hagun Isra'ila, Manassa kuma a hannunsa na hagu zuwa dama na Isra'ila, ya kawo su kusa da shi. 14 Isra'ila ya miƙa hannunsa na dama, ya ɗora bisa kan Ifraimu wanda yake ƙarami, hannunsa na hagu kuma bisa kan Manassa, yana harɗe da hannuwansa, gama Manassa shi ne ɗan fari. 15 Sai ya sa wa Yusufu albarka, ya ce, “Allah na Ibrahim da Ishaku, Iyayena da suka yi tafiyarsu a gabansa, Allah da ya bi da ni Dukan raina har wa yau, ya sa musu albarka. 16 Mala'ikan da ya fanshe ni Daga dukan mugunta, Ya sa wa samarin albarka, Bari a dinga ambatarsu da sunana, Da sunan Ibrahim da na Ishaku iyayena, Bari kuma su riɓaɓɓanya, su zama taron jama'a a tsakiyar duniya.” 17 Sa'ad da Yusufu ya ga mahaifinsa ya ɗora hannun damansa a bisa kan Ifraimu, ransa bai so ba, ya ɗauke hannun mahaifinsa, domin ya kawar da shi daga kan Ifraimu zuwa kan Manassa. 18 Sai Yusufu ya ce wa mahaifinsa, “Ba haka ba ne baba, gama wannan ne ɗan fari. Sa hannunka na dama a bisa kansa.” 19 Amma mahaifinsa ya ƙi, ya ce, “Na sani, ɗana, na sani, shi ma zai zama al'umma, zai ƙasaita, duk da haka ƙanensa zai fi shi ƙasaita, zuriyarsa kuwa za ta zama taron al'ummai.” 20 Ya sa musu albarka a wannan rana, yana cewa, “Ta gare ku Isra'ila za su sa albarka da cewa, ‘Allah ya maishe ku kamar Ifraimu da Manassa.’ ” Da haka ya sa Ifraimu gaba da Manassa. 21 Isra'ila ya ce wa Yusufu, “Ga shi, ina bakin mutuwa, amma Allah zai kasance tare da kai, zai kuma sāke komar da kai ƙasar kakanninka. 22 Ni ne nake ba ka Shekem, kashi ɗaya fiye da 'yan'uwanka, wanda na ƙwace da takobina da bakana daga hannun Amoriyawa.”

Farawa 49

Faɗar Yakubu a kan 'Ya'yansa

1 Yakubu ya kirawo 'ya'yansa maza, ya ce, “Ku tattaru wuri ɗaya don in faɗa muku abin da zai same ku a cikin kwanaki masu zuwa. 2 “Ku taru ku ji, ya ku 'ya'yan Yakubu, maza, Ku kuma kasa kunne ga Isra'ila mahaifinku. 3 “Ra'ubainu, kai ɗan farina ne, ƙarfina, Ɗan balagata, isasshe kuma, mafi ƙarfi duka cikin 'ya'yana. 4 Kamar ambaliyar ruwa mai fushi kake, Amma ba za ka zama mafi daraja ba, Domin ka hau gadon mahaifinka, Sa'an nan ka ƙazantar da shi. 5 “Saminu da Lawi 'yan'uwa ne, Suka mori takubansu cikin ta da hankali. 6 Ba zan shiga shawararsu ta asiri ba, Ba kuwa zan sa hannu cikin taronsu ba, Gama cikin fushinsu suka kashe mutane, Cikin gangancinsu kuma suka gurgunta bijimai. 7 La'ananne ne fushinsu domin mai tsanani ne, Da hasalarsu kuma, gama bala'i ce. Zan warwatsa su cikin dukan ƙasar Yakubu, In ɗaiɗaitar su su cikin Isra'ilawa. 8 “Yahuza, 'yan'uwanka za su yabe ka, Za ka shaƙe wuyan maƙiyanka, 'Yan'uwanka za su rusuna a gabanka. 9 Yahuza ɗan zaki ne, Ya kashe ganima sa'an nan ya komo wurin ɓuyarsa. Yahuza kamar zaki yake, Yakan kwanta a miƙe, Ba mai ƙarfin halin da zai tsokane shi. 10 Yana riƙe da sandan mulkinsa, Ya sa shi a tsakanin ƙafafunsa, Har Shilo ya zo. Zai mallaki dukan jama'o'i. 11 Zai ɗaure aholakinsa a kurangar inabi, A kuranga mafi kyau, Zai wanke tufafinsa da ruwan inabi, Ruwan inabi ja wur kamar jini. 12 Idanunsa za su yi ja wur saboda shan ruwan inabi, Haƙoransa kuma su yi fari fat saboda shan madara. 13 “Zabaluna zai zauna a gefen teku, Zai zama tashar jiragen ruwa, Kan iyakarsa kuma zai kai har Sidon. 14 “Issaka alfadari ne ƙaƙƙarfa, Ya kwanta a miƙe tsakanin jakunkunan shimfiɗa. 15 Saboda ya ga wurin hutawa ne mai kyau, Ƙasar kuma mai kyau ce, Sai ya sunkuyar da kafaɗunsa domin ɗaukar kaya, Ya zama bawa, yana yin aiki mai wuya. 16 “Dan zai zama mai mulki ga mutanensa Kamar ɗaya daga cikin kabilan Isra'ila. 17 Dan zai zama maciji a gefen hanya, Zai zama kububuwa a gefen turba, Mai saran diddigen doki Don mahayin ya fāɗi da baya. 18 “Ina zuba ido ga cetonka, ya Ubangiji. 19 “Gad, 'yan fashi za su kai masa hari, Shi kuwa zai runtume su. 20 “Ashiru, ƙasarsa za ta ba da amfani mai yawa, Zai kuma yi tanadin abincin da ya dace da sarki. 21 “Naftali sakakkiyar barewa ce, Mai haihuwar kyawawan 'ya'ya. 22 “Yusufu jakin jeji ne, Jakin jeji a gefen maɓuɓɓuga Aholakan jeji a gefen tuddai. 23 Maharba suka tasar masa ba tausayi Suka fafare shi da kwari da baka. 24 Duk da haka bakunansu sun kakkarye. Damatsansu sun yayyage Ta wurin ikon Allah Mai Girma na Yakubu, Makiyayi, Dutse na Isra'ila. 25 Ta wurin Allah na mahaifinka wanda zai taimake ka, Ta wurin Allah Mai Iko Dukka wanda zai sa maka albarka Albarkun ruwan sama daga bisa, Da na zurfafa daga ƙarƙashin ƙasa, Da albarkun mama da na mahaifa. 26 Albarkun hatsi da na gari Albarkun daɗaɗɗun duwatsu, Abubuwan jin daɗi na madawwaman tuddai, Allah ya sa su zauna a kan Yusufu, Da a goshin wanda aka raba shi da 'yan'uwansa. 27 “Biliyaminu kyarkeci ne mai kisa, Da safe yakan cinye abin da ya kaso, Da maraice kuma yakan raba abin da ya kamo.” 28 Waɗannan duka su ne kabilan Isra'ila goma sha biyu, wannan kuma shi ne abin da mahaifinsu ya faɗa musu sa'ad da yake sa musu albarka. Ya sa wa ko wannensu albarka da irin albarkar da ta cancance shi.

Rasuwar Yakubu da Jana'izarsa

29 Yakubu ya umarce su, ya ce musu, “Ga shi, lokacin mutuwa ya gabato da za a kai ni wurin jama'ata da suka riga ni. Sai ku binne ni tare da kakannina a cikin kogon da yake a saurar Efron Bahitte, 30 a cikin kogon da yake a Makfela, gabashin Mamre, a ƙasar Kan'ana, wanda Ibrahim ya saya duk da saurar, daga wurin Efron Bahitte, ya zama mallakarsa don makabarta. 31 A can aka binne Ibrahim da Saratu matarsa. A can kuma suka binne Ishaku da Rifkatu matarsa. A can kuma na binne Lai'atu. 32 Da saurar da kogon da yake cikinta, an saye su daga Hittiyawa.” 33 Sa'ad da Yakubu ya gama yi wa 'ya'yansa maza wasiyya, sai ya hau da ƙafafunsa bisa kan gado, Ya ja numfashinsa na ƙarshe, aka kuwa kai shi ga jama'arsa waɗanda suka riga shi.

Farawa 50

1 Yusufu kuwa ya fāɗa a kan mahaifinsa, ya yi kuka a kansa, ya sumbace shi. 2 Sai Yusufu ya umarci barorinsa masu magani, su shafe gawar mahaifinsa da maganin hana ruɓa. Saboda haka masu maganin suka shafe Isra'ila da maganin hana ruɓa. 3 Suka ɗauki kwana arba'in cif suna yin wannan, gama kwanakin da ake bukata ke nan don shafewa da maganin hana ruɓa. Masarawa kuwa suka yi masa makoki na kwana saba'in. 4 Sa'ad da kwanakin makokin suka wuce, Yusufu ya yi magana da iyalin gidan Fir'auna, ya ce, “Idan fa yanzu na sami tagomashi a wurinku, ku yi magana, ina roƙonku a gaban Fir'auna, ku ce masa, 5 ‘Sa'ad da mahaifina yake bakin mutuwa, ya sa ni in yi masa alkawari, cewa, zan binne shi a kabarin da ya haƙa wa kansa a ƙasar Kan'ana.’ Don haka in ya yarda ya bar ni in je in binne mahaifina, sa'an nan in komo.” 6 Fir'auna ya amsa, ya ce, “Ka haura ka binne mahaifinka, kamar yadda ya rantsar da kai.” 7 Saboda haka, Yusufu ya haura ya binne mahaifinsa, tare da shi kuma dukan barorin Fir'auna suka haura, da dattawan gidan Fir'auna, da dukan dattawan ƙasar Masar, 8 da kuma dukan iyalin gidan Yusufu, da 'yan'uwansa, da iyalin gidan mahaifinsa. Sai 'yan ƙananansu, da garkunan awaki da na tumaki, da garkunan shanunsu, aka bari a ƙasar Goshen. 9 Da karusai da mahayan dawakai kuma suka tafi tare da shi. Babbar ƙungiya ce ƙwarai. 10 Sa'ad da suka kai farfajiyar masussukar Atad, wanda yake wajen Urdun, a nan ne fa suka yi makoki, da babban makoki da baƙin ciki mai zafi. Aka kuwa yi kwana bakwai ana makokin mahaifinsa. 11 Sa'ad da Ka'aniyawa mazaunan ƙasar, suka ga makokin da aka yi a farfajiyar masussukar Atad, sai suka ce, “Wannan makoki mai zafi ne ga Masarawa.” Don haka aka sa wa wurin suna Abel-mizrayim, wanda yake wajen Urdun. 12 Haka 'ya'yansa suka yi masa kamar yadda ya umarta, 13 gama 'ya'yansa suka ɗauke shi zuwa ƙasar Kan'ana, suka kuwa binne shi a kogon da yake saurar Makfela a gabashin Mamre, wanda Ibrahim ya saya, duk da saurar, daga wurin Efron Bahitte, ya zama mallakarsa don makabarta. 14 Bayan da Yusufu ya binne mahaifinsa, ya koma Masar tare da 'yan'uwansa da dukan waɗanda suka tafi tare da shi don jana'izar mahaifinsa.

Yusufu ya Tabbatar wa 'Yan'uwansa ba zai Rama Ba

15 Sa'ad da 'yan'uwan Yusufu suka ga mahaifinsu ya rasu, suka ce, “Mai yiwuwa ne Yusufu zai ƙi jininmu, ya sāka mana dukan muguntar da muka yi masa.” 16 Saboda haka suka aika wa Yusufu da jawabi, suka ce, “Mahaifinka ya ba da wannan umarni kafin rasuwarsa, 17 ya ce, ‘Ku faɗa wa Yusufu, ina roƙonsa, ya gafarta laifin 'yan'uwansa da zunubansu, gama sun yi masa mugunta.’ Yanzu fa, muna roƙonka, ka gafarta laifofin bayin Allah na mahaifinka.” Yusufu ya yi kuka sa'ad da suka yi magana da shi. 18 'Yan'uwansa kuma suka zo suka fāɗi a gabansa, suka ce, “Ga shi, mu barorinka ne.” 19 Amma Yusufu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ni ba a matsayin Allah nake ba. 20 A nufinku mugunta ce kuka yi mini, amma Allah ya maishe ta alheri, don a rayar da jama'a masu yawa waɗanda suke da rai a yau. 21 Don haka kada ku ji tsoro, zan tanada muku, ku da ƙanananku.” Ta haka ya ta'azantar da su, ya yi musu magana ta kwantar da zuciya.

Rasuwar Yusufu

22 Haka fa Yusufu ya zauna a Masar, shi da iyalin gidan mahaifinsa. Yusufu kuwa ya yi shekara ɗari da goma a duniya. 23 Yusufu fa ya ga 'ya'yan Ifraimu har tsara ta uku, aka kuma haifi 'ya'yan Makir ɗan Manassa, aka karɓe su cikin iyalin Yusufu. 24 Yusufu kuwa ya ce wa 'yan'uwansa, “Ina gab da mutuwa, amma lalle Allah zai ziyarce ku, zai kuwa haurar da ku daga wannan ƙasa zuwa ƙasar da ya rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.” 25 Sa'an nan Yusufu ya rantse wa 'ya'yan Isra'ila da cewa, “Hakika Allah zai ziyarce ku, ku kuma sai ku haura da ƙasusuwana daga nan.” 26 Yusufu ya rasu yana da shekara ɗari da goma. Sai suka shafe shi da maganin hana ruɓa. Aka kuwa sa shi a akwatin gawa cikin Masar.

Fitowa 1

Wahalar Isra'ilawa a Masar

1 Waɗannan su ne sunayen 'ya'ya maza na Isra'ila, waɗanda suka tafi Masar tare da Yakubu, kowanne da iyalinsa. 2 Su ne Ra'ubainu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza, 3 da Issaka, da Zabaluna, da Biliyaminu, 4 da Dan, da Naftali, da Gad, da Ashiru. 5 Zuriyar Yakubu duka mutum saba'in ne, Yusufu kuwa, an riga an kai shi Masar. 6 Ana nan sai Yusufu ya rasu, shi da dukan 'yan'uwansa na wannan tsara. 7 Amma 'ya'yan Isra'ila suka hayayyafa, suka ƙaru ƙwarai, suka riɓaɓɓanya, suka ƙasaita ƙwarai da gaske, har suka cika ƙasar. 8 A wannan lokaci kuwa aka yi wani sabon sarki a Masar wanda bai san Yusufu ba. 9 Sai ya ce wa mutanensa, “Duba, jama'ar Isra'ila sun cika yawa sun fi ƙarfinmu. 10 Zo, mu san irin dabarar da za mu yi musu, don kada su riɓaɓɓanya, domin in aka faɗa mana da yaƙi, kada su haɗa kai da maƙiyanmu, su yaƙe mu, su tsere daga ƙasar.” 11 Suka kuwa naɗa musu shugabannin aikin gandu domin su wahalshe su da mawuyacin aiki. Aka sa su su gina wa Fir'auna biranen ajiya, wato, Fitom da Ramases. 12 Amma ko da yake Masarawa sun ƙara tsananta musu, duk da haka sai suka ƙara ƙaruwa, suna ta yaɗuwa. Masarawa kuwa suka tsorata saboda Isra'ilawa. 13 Suka kuma tilasta wa Isra'ilawa su yi ta aiki mai tsanani. 14 Suka baƙanta musu rai da aiki mai tsanani na kwaɓa, da yin tubali, da kowane irin aiki a saura. A cikin ayyukansu duka suka tsananta musu. 15 Sarkin Masar ya ce wa ungozomar Ibraniyawa, Shifra da Fu'a, 16 “Sa'ad da kuke yi wa matan Ibraniyawa hidimarku ta ungozomai, in kuka gan su durƙushe, in jariri ne suka haifa, sai ku yi masa sanadin mutuwa, in kuma jaririya ce, ku bar ta da rai.” 17 Amma da yake ungozomar masu tsoron Allah ne, ba su yi yadda Sarkin Masar ya umarce su ba, amma suka bar 'ya'ya maza da rai. 18 Don haka Sarkin Masar ya kirawo ungozomar, ya ce musu, “Me ya sa kuka bar 'ya'ya maza da rai?” 19 Ungozomar suka ce wa Fir'auna, “Domin matan Ibraniyawa ba kamar matan Masarawa ba ne, gama su masu ƙwazo ne, sukan haihu tun ungozomar ba su kai wurinsu ba.” 20 Allah kuwa ya yi wa ungozomar nan alheri. Mutanen suka riɓanya, suka ƙasaita ƙwarai. 21 Allah kuma ya ba ungozomar nan zuriya domin sun ji tsoronsa. 22 Fir'auna kuwa ya umarci dukan mutanensa ya ce, “Duk jaririn da aka haifa wa Ibraniyawa, sai ku jefa shi cikin Kogin Nilu, amma idan jaririya ce, ku bar ta da rai.”

Fitowa 2

Haihuwar Musa

1 Sai wani mutum, Balawe, ya auro 'yar Lawi. 2 Matar kuwa ta yi ciki, ta haifi ɗa. Sa'ad da ta ga jaririn kyakkyawa ne, sai ta ɓoye shi har wata uku. 3 Da ta ga ba za ta iya ƙara ɓoye shi ba, sai ta saƙa kwando da iwa, ta yaɓe shi da katsi, ta sa jaririn a ciki, ta ajiye shi cikin kyauro a bakin Kogin Nilu. 4 Ga 'yar'uwarsa kuma a tsaye daga nesa don ta san abin da zai same shi. 5 Gimbiya, wato, 'yar Fir'auna, ta gangaro don ta yi wanka a Kogin Nilu, barorinta 'yan mata suna biye da ita a gaɓar Kogin Nilu. Da ta ga kwando a cikin kyauro, ta aiki baranyarta ta ɗauko mata shi. 6 Sa'ad da ta tuɗe kwandon ta ga jariri yana kuka. Sai ta ji tausayinsa, ta ce, “Wannan ɗaya daga cikin 'ya'yan Ibraniyawa ne.” 7 'Yar'uwar jaririn kuwa ta ce wa Gimbiya, “In tafi in kirawo miki wata daga cikin matan Ibraniyawa da za ta yi miki renon ɗan?” 8 Sai Gimbiya ta ce mata, “Je ki.” Yarinyar kuwa ta tafi ta kirawo mahaifiyar jaririn. 9 Da ta zo, sai Gimbiya ta ce mata, “Dauki wannan jariri, ki yi mini renonsa, zan biya ki ladanki.” Matar kuwa ta ɗauki jaririn ta yi renonsa. 10 Da jaririn ya yi girma sai ta kai shi wurin Gimbiyar. Yaro kuwa ya zama tallafinta. Ta raɗa masa suna Musa, gama ta ce, “Domin na tsamo shi daga cikin ruwa.”

Musa ya Gudu zuwa Madayana

11 Ana nan wata rana, sa'ad da Musa ya yi girma, ya tafi wurin mutanensa, sai ya ga yadda suke shan wahala. Ya kuma ga wani Bamasare yana d�kan Ba'ibrane, ɗaya daga cikin 'yan'uwansa. 12 Da ya waiwaya, bai ga kowa ba, sai ya kashe Bamasaren, ya turbuɗe shi cikin yashi. 13 Kashegari da ya sāke fita, sai ya ga waɗansu Ibraniyawa biyu suna faɗa da juna. Ya ce wa wanda yake ƙwaran ɗan'uwansa, “Me ya sa kake bugun ɗan'uwanka?” 14 Ya amsa, ya ce, “Wa ya naɗa ka sarki ko alƙali a bisanmu? So kake ka kashe ni kamar yadda ka kashe Bamasaren?” Sai Musa ya tsorata, ya ce, “Assha, ashe, an san al'amarin!” 15 Da Fir'auna ya ji, sai ya nema ya kashe Musa. Amma Musa ya gudu daga gaban Fir'auna, ya tafi, ya zauna a ƙasar Madayana. Da ya kai, sai ya zauna a bakin wata rijiya. 16 Ana nan waɗansu 'yan mata bakwai, 'ya'yan firist na Madayana suka zo su cika komaye da ruwa don su shayar da garken mahaifinsu. 17 Sai makiyaya suka zo, suka kore su, amma Musa ya tashi ya taimake su, ya kuma shayar da garkensu. 18 Lokacin da suka koma wurin mahaifinsu, Reyuwel, wato, Yetro, ya ce musu, “Yaya aka yi yau, kuka komo da sauri haka?” 19 Sai suka ce, “Wani Bamasare ne ya cece mu daga hannun makiyaya, har ya ɗebo ruwa, ya shayar da garkenmu.” 20 Reyuwel kuwa ya ce wa 'ya'yansa mata, “A ina yake? Me ya sa ba ku zo da shi ba? Ku kirawo shi, ya zo, ya ci abinci.” 21 Musa kuwa ya yarda ya zauna tare da Reyuwel. Sai ya aurar wa Musa da 'yarsa Ziffora. 22 Ita kuwa ta haifa masa ɗa, ya raɗa masa suna Gershom, gama ya ce, “Baƙo ne ni, a baƙuwar ƙasa.” 23 Ana nan, a kwana a tashi, sai Sarkin Masar ya rasu. Jama'ar Isra'ila suka yi nishi, suka yi kuka kuma saboda bautarsu, kukansu na neman gudunmawa ya kai gun Allah. 24 Allah kuwa ya ji nishinsu, sai ya tuna da alkawarinsa da ya yi wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. 25 Allah ya dubi jama'ar Isra'ila, ya kuwa kula da su.

Fitowa 3

Allah ya Kira Musa

1 Wata rana, sa'ad da Musa yake kiwon garken surukinsa, Yetro, firist na Madayana, sai ya kai garken yammacin jeji, har ya zo Horeb, wato, dutsen Allah. 2 A can mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi cikin harshen wuta daga cikin kurmi. Da Musa ya duba, sai ga kurmin yana cin wuta, amma duk da haka bai ƙone ba. 3 Musa kuwa ya ce, “Bari in ratse, in ga wannan abin banmamaki da ya sa kurmin bai ƙone ba.” 4 Sa'ad da Ubangiji ya ga ya ratse don ya duba, sai Allah ya kira shi daga cikin kurmin, ya ce, “Musa, Musa.” Musa ya ce, “Ga ni.” 5 Allah kuwa ya ce, “Kada ka matso kusa, ka cire takalminka, gama wurin da kake tsaye, tsattsarka ne.” 6 Ya kuma ce, “Ni ne Allah na kakanninka, wato, Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.” Sai Musa ya ɓoye fuskarsa, gama yana jin tsoro ya dubi Allah. 7 Ubangiji kuwa ya ce, “Na ga wahalar jama'ata waɗanda suke a Masar, na kuma ji kukansu da suke yi a kan shugabanninsu. Na san wahalarsu, 8 don haka na sauko in cece su daga hannun Masarawa, in fito da su daga cikin wannan ƙasa zuwa kyakkyawar ƙasa mai ba da yalwar abinci, wato, ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. 9 Yanzu fa, ga shi, kukan jama'ar Isra'ila ya zo gare ni. Na kuma ga wahalar da Masarawa suke ba su. 10 Zo, in aike ka wurin Fir'auna domin ka fito da jama'ata, wato, Isra'ilawa, daga cikin Masar.” 11 Amma Musa ya ce wa Allah, “Wane ni in tafi gaban Fir'auna in fito da Isra'ilawa daga cikin Masar?” 12 Sai Allah ya ce, “Zan kasance tare da kai, wannan kuwa zai zama alama a gare ka, cewa, ni ne na aike ka. Sa'ad da ka fito da jama'ar daga Masar, za ku bauta wa Allah a bisa dutsen nan.” 13 Sai Musa ya ce wa Allah, “Idan na je wurin Isra'ilawa na ce musu, ‘Allah na ubanninku ya aiko ni gare ku,’ idan sun ce mini, ‘Yaya sunansa?’ Me zan faɗa musu?” 14 Allah kuwa ya ce wa Musa, “NI INA NAN YADDA NAKE,” ya kuma ce, “Haka za ka faɗa wa Isra'ilawa, ‘NI NE ya aiko ni gare ku.’ ” 15 Allah kuma ya sāke ce wa Musa, “Faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Ubangiji Allah na kakanninku, wato, na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu ya aiko ni gare ku.’ Wannan shi ne sunana har abada. Da wannan suna za a tuna da ni a dukkan zamanai. 16 Tafi, ka tattara dattawan Isra'ila, ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah na kakanninku ya bayyana gare ni, wato, na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, ya ce, sosai ya ziyarce ku, ya kuma ga abin da ake yi muku a Masar. 17 Ya yi alkawari cewa, zai fisshe ku daga wahalar Masar zuwa ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. Ƙasa wadda take mai ba da yalwar abinci.’ 18 Za su kasa kunne ga muryarka. Sa'an nan kai da dattawan Isra'ila za ku tafi gaban Sarkin Masar ku ce masa, ‘Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya gamu da mu. Yanzu fa, muna roƙonka, ka yarda mana mu yi tafiyar kwana uku a cikin jeji mu miƙa masa hadaya.’ 19 Amma na sani Sarkin Masar ba zai bar ku ku fita ba, sai an yi masa tilas. 20 Domin haka zan miƙa hannuna in bugi Masar da dukan mu'ujizaina waɗanda zan aikata cikinta, sa'an nan zai bar ku ku fita. 21 “Zan sa wannan jama'a su yi farin jini a idanun Masarawa, sa'ad da kuka fita kuma, ba za ku fita hannu wofi ba. 22 Amma kowace mace za ta roƙi maƙwabciyarta da wadda take cikin gidanta kayan ado na azurfa, da na zinariya, da tufafi, za ku sa wa 'ya'yanku mata da maza. Da haka za ku washe Masarawa.”

Fitowa 4

1 Musa kuwa ya amsa ya ce, “Ai, ba za su gaskata ni ba, ba kuma za su kasa kunne ga maganata ba, gama za su ce, ‘Ubangiji bai bayyana gare ka ba.’ ” 2 Amma Ubangiji ya ce masa, “Mene ne wannan a hannunka?” Ya ce, “Sanda ne.” 3 Ubangiji ya ce, “Jefa shi ƙasa.” Sai ya jefa shi ƙasa, sandan ya zama maciji, Musa kuwa ya yi gudunsa. 4 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka ka kama wutsiyarsa.” Ya miƙa hannunsa ya kama shi, ya zama sanda kuma a hannunsa. 5 Sai Ubangiji ya ce, “Ta haka za su gaskata Ubangiji Allah na kakanninsu ne, wato, na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, ya bayyana gare ka.” 6 Sai Ubangiji ya sāke ce masa, “Sa hannunka cikin ƙirjinka.” Sa'ad da ya fitar da shi, ga hannunsa a kuturce fari fat. 7 Allah kuma ya ce masa, “Mai da hannunka cikin ƙirjinka.” Sai ya mai da hannunsa cikin ƙirjinsa. Sa'ad da ya fitar da shi, ga hannun ya koma kamar sauran jikinsa. 8 Ubangiji kuma ya ce, “Idan kuma ba su gaskata ka ba, ba su kuma kula da mu'ujiza ta fari ba, ya yiwu su gaskata ta biyun. 9 Idan ba su gaskata mu'ujizan nan biyu ba, ba su kuma kula da maganarka ba, sai ka ɗibi ruwa daga Kogin Nilu, ka zuba bisa busasshiyar ƙasa. Ruwan zai zama jini a bisa busasshiyar ƙasa.” 10 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangijina, ni ba mai lafazi ba ne, ban taɓa zama ba, ko a yanzu ma, bayan da ka yi magana da bawanka, gama ni mai nauyin baki ne, mai nauyin harshe kuma.” 11 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Wa ya yi bakin ɗan adam? Wa ya yi bebe ko kurma, ko mai gani ko makaho? Ko ba ni Ubangiji ba ne? 12 Yanzu fa, tafi, zan kasance tare da bakinka, in koya maka abin da za ka faɗa.” 13 Amma Musa ya ce, “Ya Ubangijina, in ka yarda, ka aiki wani.” 14 Ubangiji kuwa ya hasala da Musa, ya ce, “Haruna ɗan'uwanka Balawe ba ya nan ne? Lalle na san shi ya iya magana, ga shi nan ma, yana fitowa ya tarye ka. Sa'ad da ya gan ka kuwa zai yi murna cikin zuciyarsa. 15 Sai ka yi magana da shi. Ka kuma sa masa maganata a baka, zan kuwa kasance tare da bakinka da bakinsa. Zan kuma sanar da ku abin da za ku yi. 16 Shi zai yi maka magana da jama'a, zai zama bakinka, kai kuwa za ka zama kamar Allah a gare shi. 17 Za ka riƙe wannan sanda a hannunka, da shi za ka aikata mu'ujizan.”

Musa ya Koma Masar

18 Musa ya koma wurin Yetro, surukinsa, ya ce masa, “Ina roƙonka, ka bar ni in koma wurin 'yan'uwana a Masar, in ga ko a raye suke har yanzu.” Sai Yetro ya ce wa Musa, “Ka tafi lafiya.” 19 Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa a Madayana, ya koma Masar, gama dukan waɗanda suke neman ransa sun rasu. 20 Saboda haka Musa ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa maza, ya haushe su bisa kan jaki, ya koma ƙasar Masar, yana riƙe da sandan Allah a hannunsa. 21 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Sa'ad da ka koma Masar, sai ka kula, ka aikata a gaban Fir'auna dukan mu'ujizan da na sa cikin ikonka. Amma zan taurara zuciyarsa, don kada ya bar jama'a su fita. 22 Za ka ce wa Fir'auna, Ubangiji ya ce, ‘Isra'ila ɗan fārina ne. 23 Na ce maka ka bar ɗana ya tafi domin ya bauta mini, amma in ka ƙi ka bar shi ya tafi, yanzu zan kashe ɗan fārinka.’ ” 24 Ya zama kuwa sa'ad da Musa yake masauki a kan hanya sai Ubangiji ya gamu da shi, ya nema ya kashe shi. 25 Sai Ziffora ta ɗauki ƙanƙara ta yanke loɓar ɗanta, ta taɓa gaban Musa da shi, ta ce, “Kai angon jini kake a gare ni.” 26 Sa'an nan Ubangiji ya ƙyale shi. Ta kuma ce, “Kai angon jini ne,” saboda kaciyar. 27 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Tafi, ka taryi Musa cikin jeji.” Ya kuwa tafi ya tarar da shi a dutsen Allah, ya sumbace shi. 28 Sa'an nan Musa ya faɗa wa Haruna abubuwan da Ubangiji ya aike shi ya yi, da dukan mu'ujizan da ya umarce shi ya aikata. 29 Sai Musa da Haruna suka tafi suka tattara dukan dattawan Isra'ila. 30 Haruna dai ya hurta wa dattawan al'amuran da Ubangiji ya faɗa wa Musa. Ya kuma aikata mu'ujizan a idanunsu. 31 Dattawan kuwa suka gaskata. Sa'ad da suka ji Ubangiji ya ziyarci Isra'ilawa, ya kuma ga wahalarsu, sai suka sunkuya, suka yi masa sujada.

Fitowa 5

Musa da Haruna sun Tafi gaban Fir'auna

1 Bayan wannan Musa da Haruna suka tafi gaban Fir'auna, suka ce, “Ga abin da Ubangjiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Bar jama'ata su tafi domin su yi mini idi cikin jeji.’ ” 2 Amma Fir'auna ya ce, “Wane ne Ubangiji, har da zan ji maganarsa, in bar Isra'ilawa su tafi? Ai, ban san Ubangiji ɗin nan ba, balle in bar Isra'ilawa su tafi.” 3 Sai suka ce, “Allahn Ibraniyawa ya gamu da mu, muna roƙonka, ka bar mu mu yi tafiyar kwana uku cikin jeji domin mu yi wa Ubangiji Allahnmu hadaya, don kada ya aukar mana da annoba ko takobi.” 4 Amma Sarkin Masar ya ce wa Musa da Haruna, “Me ya sa kuke hana jama'ar yin aikinsu? Ku tafi wurin aikin gandunku.” 5 Ya kuwa ci gaba ya ce, “Ga jama'ar ƙasar sun yi yawa, yanzu kuna so ku hana su yin aikinsu.” 6 A ran nan fa Fir'auna ya umarci shugbannin aikin gandu da manyan jama'a, ya ce, 7 “Nan gaba kada ku ƙara ba mutanen nan budu na yin tubali kamar dā. Ku sa su, su tafi, su tara budu da kansu. 8 Duk da haka, kada su kāsa cika yawan tubalin da aka ƙayyade musu da fari. Ai, su ragwaye ne, shi ya sa suke kuka, suna cewa, ‘A bar mu, mu tafi mu miƙa wa Allahnmu hadaya.’ 9 Ku sa mutanen su yi aiki mai tsanani har da ba za su sami damar kasa kunne ga maganganun ƙarya ba.” 10 Sai shugabannin aikin gandu da manyan jama'a suka tafi suka faɗa wa jama'a cewa, “Ga abin da Fir'auna ya ce, ‘Ba zan ba ku budu ba. 11 Ku je, ku da kanku, ku nemi budu inda duk za ku iya samowa, amma daɗai, ba za a sawwaƙe muku aikinku ba.’ ” 12 Sai jama'a suka watsu ko'ina cikin ƙasar Masar, suna tattara budu. 13 Shugabannin aikin gandun suka matsa musu, suna cewa, “Sai ku cika aikinku na kowace rana daidai yadda kuke yi a dā lokacin da ake ba ku budu.” 14 Aka kuwa bulali manya waɗanda suke Isra'ilawa waɗanda shugabannin aikin gandu na Fir'auna suka sa a bisa Isra'ilawa, ana cewa, “Me ya sa jiya da yau ba ku cika yawan tubalin da aka ƙayyade, kamar dā ba?” 15 Manyan Isra'ilawa kuwa suka tafi suka yi kuka a gaban Fir'auna, suka ce, “Me ya sa ka yi wa bayinka haka? 16 Ba a ba mu budu, amma ana ce mana mu yi tubali. Ga shi ma, d�kan bayinka suke yi. Ai, jama'arka ne suke da laifin.” 17 Fir'auna kuwa ya ce musu, “Ku ragwaye ne ƙwarai, shi ya sa kuke cewa, a bar ku ku tafi, ku miƙa wa Ubangiji hadaya. 18 Ku tafi, ku kama aiki, ba za a ba ku budu ba, duk da haka za ku cika yawan tubali da aka sa muku.” 19 Manyan Isra'ilawa suka ga lalle sun shiga uku, da yake aka ce dole su cika yawan tubali da aka yanka musu kowace rana. 20 Da suka fita daga gaban Fir'auna, sai suka sadu da Musa da Haruna, suna jiransu. 21 Suka ce wa Musa da Haruna, “Allah ya duba, ya hukunta ku, gama kun sa mun yi baƙin jini a wurin Fir'auna da barorinsa, har suka ɗauki takobi don su kashe mu.”

Addu'ar Musa

22 Sai Musa ya koma wurin Ubangiji, ya ce, “Ya Ubangijina, me ya sa ka jawo wa wannan jama'a masifa? Me ya sa ka aike ni? 23 Gama tun da na tafi wurin Fir'auna, na yi masa magana da sunanka, ya mugunta wa wannan jama'a, kai kuwa ba ka ceci jama'arka ba ko kaɗan!”

Fitowa 6

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Yanzun nan, za ka ga abin da zan yi da Fir'auna. Gama zan tilasta shi ya bar su su fita, har ma ya iza ƙyeyarsu don su bar ƙasarsa!”

An Sāke Kiran Musa

2 Allah kuma ya yi magana da Musa, ya ce, “Ni ne Ubangiji. 3 Na bayyana ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu a kan ni Allah Maɗaukaki ne, amma sunan nan nawa, Yahweh, ban sanasshe su ba. 4 Na kuma yi musu alkawari zan ba su ƙasar Kan'ana, inda suka yi zaman baƙunci. 5 Yanzu na ji nishin Isra'ilawa, waɗanda Masarawa suka bautar, na kuwa tuna da alkawarina. 6 Sai ka faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Ni Ubangiji zan 'yantar da ku daga wulakancin nan da Masarawa suke yi muku. Zan kuɓutar da ku daga bautar Masarawa. Da ƙarfi zan aikata hukuntaina masu iko don in cece ku. 7 Zan tallafe ku, ku zama jama'ata, ni kuwa in zama Allahnku. A sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya 'yanto ku daga wulakancin Masarawa. 8 Sa'an nan zan kawo ku cikin ƙasar da na rantse zan bai wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. Zan ba ku ita ta zama mallakarku. Ni ne Ubangiji.’ ” 9 Sai Musa ya faɗa wa Isra'ilawa wannan magana, amma ba su kasa kunne gare shi ba, saboda ɓacin rai da tsananin bauta. 10 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 11 “Tafi gaban Fir'auna, Sarkin Masar, ka faɗa masa ya bar Isra'ilawa su fita ƙasa tasa.” 12 Amma Musa ya amsa wa Ubangiji ya ce, “Duba, tun da yake Isra'ilawa ba su kasa kunne gare ni ba, yaya Fir'auna zai kasa kunne gare ni, ni mutum mai nauyin baki?” 13 Ubangiji kuma ya yi magana da Musa da Haruna, su tafi wurin Isra'ilawa da wurin Fir'auna, Sarkin Masar, su ba su umarni, su kuma fito da Isra'ilawa daga cikin ƙasar Masar.

Asalin Musa da Haruna

14 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu. 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, ɗan farin Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi. Waɗannan su ne iyalan kabilar Ra'ubainu. 15 'Ya'yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Ohad, da Yakin, da Zohar, da Shawul ɗan Bakan'aniya, waɗannan su ne iyalan kabilar Saminu. 16 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Lawi bisa ga iyalansu, Gershon, da Kohat, da Merari. Lawi ya rayu shekara ɗari da talatin da bakwai. 17 'Ya'yan Gershon, maza kuwa, su ne Libni, da Shimai bisa ga iyalansu. 18 'Ya'ya maza na Kohat kuwa, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel. Kohat ya rayu shekara ɗari da talatin da uku. 19 'Ya'ya maza na Merari, su ne Mali, da Mushi. Waɗannan su ne kabilar Lawi bisa ga zuriyarsu. 20 Amram ya auri Yokabed 'yar'uwar mahaifinsa, ta kuwa haifa masa Haruna da Musa. Amram ya rayu shekara ɗari da talatin da bakwai. 21 'Ya'yan Izhara, su ne Kora, da Nefeg, da Zikri. 22 'Ya'ya maza na Uzziyel, su ne Mishayel, da Elzafan, da Zitri. 23 Haruna ya auri Elisheba, 'yar Amminadab 'yar'uwar Nashon. Sai ta haifa masa Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar. 24 'Ya'ya maza na Kora, su ne Assir, da Elkana, da Abiyasaf. Waɗannan su ne iyalin Kora. 25 Ele'azara, ɗan Haruna, ya auri ɗaya daga cikin 'ya'ya mata na Futiyel. Ita kuwa ta haifa masa Finehas. Waɗannan su ne shugabannin iyalan kabilar Lawi bisa ga kabilansu. 26 Wannan Haruna ne da Musa, waɗanda Ubangiji ya yi musu magana su fito da Isra'ilawa daga cikin ƙasar Masar, ƙungiya ƙungiya. 27 Su ne waɗanda suka yi magana da Sarkin Masar ya bar Isra'ilawa su fita daga Masar. Musa da Haruna ne suka yi wannan.

Umarnin Ubangiji ga Musa da Haruna

28 Wata rana Ubangiji ya yi magana da Musa a ƙasar Masar ya ce, 29 “Ni ne Ubangiji, sai ka faɗa wa Fir'auna, Sarkin Masar, dukan abin da na faɗa maka.” 30 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ni mai nauyin baki ne, yaya Fir'auna zai kasa kunne gare ni?”

Fitowa 7

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, zan maishe ka kamar Allah ga Fir'auna. Ɗan'uwanka, Haruna kuwa, zai zama manzonka. 2 Kai za ka faɗa wa Haruna, ɗan'uwanka, dukan abin da na umarce ka, shi kuwa zai faɗa wa Fir'auna ya bar Isra'ilawa su fita ƙasa tasa. 3 Amma zan taurare zuciyar Fir'auna don in aikata alamu da mu'ujizai cikin ƙasar Masar. 4 Amma Fir'auna ba zai kasa kunne gare ku ba, don haka zan miƙa hannuna a bisa Masar, zan fitar da rundunar jama'ata, wato, Isra'ilawa, daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu iko. 5 Masarawa kuma za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na miƙa hannuna gāba da Masar, don in fito da Isra'ilawa daga tsakiyarsu.” 6 Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. 7 Musa yana da shekara tamanin, Haruna kuwa yana da shekara tamanin da uku sa'ad da suka yi magana da Fir'auna.

Sandan Haruna

8 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, 9 “Idan Fir'auna ya ce muku, ‘Aikata waɗansu al'ajabai don ku nuna isarku,’ sai ka faɗa wa Haruna ya ɗauki sandansa, ya jefa shi ƙasa a gaban Fir'auna. Sandan kuwa zai zama maciji.” 10 Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir'auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa a gaban Fir'auna. Da sandan ya fāɗi, sai ya zama maciji. 11 Fir'auna kuwa ya kirawo shahararrun malamai, da masu sihiri, su kuma su yi haka ta wurin sihirinsu na Masarawa. 12 Ko wannensu ya jefa sandansa ƙasa, sai sandunan suka zama macizai. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu. 13 Duk da haka zuciyar Fir'auna ta taurare kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

Annobar Jini

14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir'auna yana da taurin zuciya, ga shi, ya ƙi sakin jama'ar. 15 Ka tafi wurinsa da safe daidai lokacin da ya fita zai tafi Kogin Nilu. Ka jira don ka sadu da shi a bakin Nilu. Ka kuma ɗauki sandan nan wanda ya juye ya zama maciji. 16 Za ka faɗa wa Fir'auna cewa, ‘Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya aike ni gare ka da cewa, ka saki jama'ar Ubangiji domin su yi masa hidima a jeji. Amma ga shi, har yanzu ba ka yi biyayya ba. 17 Ubangiji ya ce, za ka sani shi ne Ubangiji ta wurin abin da zan aikata. Zan bugi ruwan Nilu da sandan da yake hannuna, ruwan kuwa zai rikiɗe ya zama jini. 18 Kifayen da suke cikin Nilu za su mutu. Nilu kuwa zai yi ɗoyi, har da Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’ ” 19 Ubangiji kuma ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya ɗauki sandansa ya miƙa shi a bisa ruwayen Masar, da kogunansu, da rafuffukansu, da fadamunsu, da dukan tafkunansu don ruwansu ya zama jini. Jini zai kasance ko'ina a ƙasar Masar, i, har ma cikin randuna. 20 Musa da Haruna kuwa suka yi daidai kamar yadda Ubangiji ya umarta. Sai Haruna ya ta da sandansa sama ya bugi ruwan Nilu a gaban Fir'auna da fādawansa. Dukan ruwan Nilu kuwa ya rikiɗe jini. 21 Kifayen da suke cikin Nilu suka mutu. Nilu kuwa ya yi ɗoyi, har Masarawa ba su iya shan ruwansa ba. Ko'ina kuma a ƙasar Masar akwai jini. 22 Masu sihiri kuma na Masar suka yi haka, su ma, ta wurin sihirinsu, don haka zuciyar Fir'auna ta daɗa taurarewa, ya kuwa ƙi jin Musa da Haruna kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa. 23 Sai ya juya, ya koma fādarsa, bai ko kula da abin da aka yi ba. 24 Dukan Masarawa suka tattone ramummuka a bakin Nilu, suna neman ruwan sha, gama ba su iya shan ruwan Nilu ba. 25 Kwana bakwai suka cika bayan da Ubangiji ya bugi Kogin Nilu.

Fitowa 8

Annobar Kwaɗi

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tafi wurin Fir'auna, ka ce masa, ‘Ubangiji ya ce ka saki jama'arsa domin su yi masa sujada. 2 Idan ka ƙi sakinsu, zai hore ka da kwaɗi. 3 Nilu zai cika da kwaɗi, za su tashi, su shiga cikin fādarka, da ɗakin kwanciyarka, da gadonka, har da gidajen fadawanka da jama'arka. Za su kuma shiga matuyanka da kwanon tuwonka, 4 har ma za su hau bisa kanka, da jama'arka, da dukan fādawanka.’ ” 5 Sai Ubangiji ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya miƙa sandansa a bisa koguna, da rufuffuka, da tafkuna don ya sa kwaɗi su fito, su rufe ƙasar Masar. 6 Haruna ya miƙa sandansa a bisa ruwayen Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka rufe ƙasar Masar. 7 Masu sihiri kuma suka sa kwaɗi su fito a bisa ƙasar Masar ta wurin sihirinsu. 8 Sai Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna, ya ce su roƙi Ubangiji ya kawar masa da kwaɗin, shi da mutanensa, sa'an nan zai saki jama'ar, su tafi su miƙa wa Ubangiji hadaya. 9 Musa ya ce wa Fir'auna, “In ka yarda, a wane lokaci ne kake so in roƙa maka, kai da barorinka da jama'arka domin a kawar da kwaɗin daga gidajenku, a hallakar muku da su, sai dai na cikin Kogin Nilu za a bari?” 10 Fir'auna ya ce, “Gobe ne.” Musa kuwa ya ce, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani allah kamar Ubangiji Allahnmu. 11 Kwaɗin za su rabu da ku, da kai, da gidanka, da fādawanka, da jama'arka, sai na cikin Nilu kaɗai za a bari.” 12 Da Musa da Haruna suka fita daga gaban Fir'auna, sai Musa ya roƙi Ubangiji ya kawar da kwaɗin nan da suka azabta wa Fir'auna. 13 Ubangiji kuwa ya karɓi addu'ar Musa, sai kwaɗin da suke cikin gida da waɗanda suke kewaye da gida, da waɗanda suke cikin saura suka mutu. 14 Aka tsiba su tsibi tsibi. Suka sa ƙasar ta yi ɗoyi. 15 Da Fir'auna ya ga an kawar masa da kwaɗin, sai ya taurare zuciyarsa, ya ƙi jinsu kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

Annobar Kwarkwata

16 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa ya faɗa wa Haruna ya miƙa hannunsa ya bugi ƙurar ƙasar, ta zama kwarkwata a ƙasar Masar. 17 Haka kuwa suka yi. Haruna ya miƙa sandansa ya bugi ƙurar ƙasa, sai ta zama kwarkwata a bisa 'yan adam, da bisa dabbobi. Dukan ƙurar ta zama kwarkwata ko'ina cikin ƙasar Masar. 18 Masu sihiri suka ƙokarta su sa kwarkwata ta bayyana ta wurin sihirinsu, amma ba su iya ba. Kwarkwata kuma ta yayyaɓe 'yan adam da dabbobi. 19 Sai masu sihiri suka ce wa Fir'auna, “Ai, wannan aikin Allah ne.” Amma zuciyar Fir'auna ta taurare, har da bai kasa kunne ga Musa da Haruna ba, kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.

Annobar Ƙudaje

20 Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe ka sami Fir'auna a daidai lokacin da ya fita za shi rafi, ka ce masa, ‘Ni Ubangiji na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada. 21 In kuwa ka ƙi sakin jama'ata, sai in koro maka ƙudaje, da kai da fādawanka, da jama'arka, da gidajen Masarawa, har ma duk da ƙasa inda suke takawa. 22 A wannan rana fa zan keɓe ƙasar Goshen inda jama'ata suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, ta haka ne za ka sani ni Ubangiji ina nan a duniya. 23 Zan sa iyaka tsakanin jama'ata da jama'arka. Gobe ne wannan mu'ujiza za ta auku.’ ” 24 Haka kuwa Ubangiji ya aikata. Ƙudaje masu yawa suka shiga gidan Fir'auna, da gidan fādawansa, da ko'ina a ƙasar Masar. Ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje. 25 Sa'an nan Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna, ya ce, “Tafi, ku yi wa Allahnku hadaya a ƙasar nan.” 26 Amma Musa ya ce, “Ba zai kyautu a yi haka ba, gama irin dabbobin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu hadaya da su, haramu ne ga Masarawa. Idan fa muka miƙa hadaya da waɗannan dabbobi da suke haramu a idon Masarawa za su jajjefe mu da duwatsu. 27 Za mu yi tafiya kwana uku a jeji kafin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu kamar yadda ya umarce mu.” 28 Sai Firauna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, ku miƙa wa Ubangiji Allahnku hadaya a jeji, sai dai kada ku tafi da nisa. Ku kuma yi mini addu'a.” 29 Musa kuwa ya ce, “Nan da nan da tashina daga gabanka, zan yi addu'a ga Ubangiji, ƙudajen kuwa za su rabu da kai, da fādawanka, da jama'arka gobe, kada ka sāke yin ruɗi, ka ƙi barin jama'ar su tafi, su miƙa wa Ubangiji hadaya.” 30 Musa ya fita daga wurin Fir'auna, ya roƙi Ubangiji. 31 Ubangiji kuwa ya aikata bisa ga roƙon Musa. Ƙudajen suka rabu da Fir'auna, da fādawansa, da jama'arsa. Ko ƙuda ɗaya bai ragu ba. 32 Duk da haka Fir'auna ya taurare zuciyarsa a wannan lokaci kuma, ya ƙi sakin jama'ar.

Fitowa 9

Mutuwar Dabbobi

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je ka wurin Fir'auna, ka faɗa masa cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Ibraniyawa, na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada. 2 Amma idan ka ƙi sakinsu, wato, kana ta riƙonsu, 3 to, hannuna zai auka wa dabbobinka cikin sauruka, da dawakai, da jakai, da raƙuma, da shanu, da tumaki, da awaki, da annoba mai tsanani. 4 Zan raba tsakanin dabbobin Isra'ilawa, da na Masarawa. Ko ɗaya daga cikin dabbobin Isra'ilawa ba zai mutu ba. Na riga na sa lokacin. 5 Gobe ne zan aikata al'amarin nan a ƙasar.’ ” 6 Kashegari kuwa Ubangiji ya aikata al'amarin. Dukan dabbobin Masarawa suka mutu, na Isra'ilawa kuwa, ko ɗaya bai mutu ba. 7 Sai Fir'auna ya aika, ya tambaya, ashe, ko dabba guda daga cikin na Isra'ilawa ba ta mutu ba? Duk da haka zuciyar Fir'auna ta taurare, bai kuwa saki jama'ar ba.

Marurai

8 Ubangiji kuma ya ce wa Musa da Haruna, “Dibi tokar matoya cike da tafin hannuwanku, Musa kuwa zai watsa ta sama a gaban Fir'auna. 9 Tokar za ta zama kamar ƙura a dukan ƙasar Masar, ta zama marurai, suna kuwa fitowa a jikin mutum da dabba a dukan ƙasar Masar.” 10 Sa'an nan suka ɗauko toka daga matoya, suka tsaya a gaban Fir'auna. Da Musa ya watsa ta sama, sai ta zama marurai suna ta fitowa a jikin mutum da dabba. 11 Amma masu sihirin suka kāsa tsayawa a gaban Musa saboda maruran, gama suka kamu da maruran kamar sauran Masarawa. 12 Ubangiji kuma ya taurare zuciyar Fir'auna har ya ƙi jin Musa da Haruna kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa wa Musa.

Ƙanƙara

13 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Tashi da sassafe, ka je ka sami Fir'auna, ka ce masa, ‘Ni Ubangiji Allah na Ibraniyawa, na ce ka saki jama'ata domin su yi mini sujada. 14 A wannan karo, ni da kaina zan kawo maka, da fādawanka, da jama'arka annoba, domin ka sani babu mai kama da ni a dukan duniya. 15 Gama da ni kaina na miƙa dantsena na buge ka da jama'arka da annoba, ai, da an hallakar da ku a duniya ƙaƙaf. 16 Amma na bar ka ka rayu domin in nuna maka ikona, domin kuma sunana ya zama abin darajantawa a dukan duniya. 17 Har yanzu kana fariya a kan jama'ata, ba ka sake su ba. 18 Gobe war haka zan sa a yi ƙanƙara mai tsananin gaske irin wadda Masar ba ta taɓa gani ba tun kafawarta, har zuwa yanzu. 19 Yanzu fa, sai ka ba da umarni a lura da awaki, da dukan abin da yake naku wanda yake a saura, gama duk mutum ko dabba wanda ya ragu a saura, wato, wanda ba a kawo shi gida ba, zai mutu sa'ad da ƙanƙarar ta zo.’ ” 20 Akwai waɗansu daga cikin fādawan Fir'auna waɗanda suka tsorata saboda abin da Ubangiji ya faɗa, sai suka kawo bayinsu da dabbobinsu cikin gida. 21 Amma waɗanda ba su kula da abin da Ubangiji ya faɗa ba, suka bar bayinsu da dabbobinsu a waje cikin saura. 22 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama don a yi ƙanƙara a bisa mutum da dabba da bisa dukan itatuwan saura a dukan ƙasar Masar.” 23 Sai Musa ya miƙa sandansa sama, Ubangiji kuwa ya aiko da tsawa da ƙanƙara, wuta kuwa ta bi ƙasar. Ubangiji ya sa aka yi ƙanƙara a bisa ƙasar Masar. 24 Ƙanƙarar tana faɗowa, wuta kuma tana tartsatsi a cikin ƙanƙara. Aka yi ƙanƙara mai tsananin gaske irin wadda ba a taɓa yi ba cikin dukan ƙasar Masar tun lokacin da ta zama al'umma. 25 Ƙanƙarar ta bugi ko'ina a Masar. Dukan abin da yake cikin saura, mutum duk da dabba, da tsire-tsire duka, ƙanƙara ta buge su. Duk itatuwan da suke a saura aka ragargaza su. 26 Sai dai a ƙasar Goshen inda Isra'ilawa suke, ba a yi ƙanƙara ba. 27 Fir'auna ya aika, aka kirawo Musa da Haruna, ya ce musu, “Lalle a wannan karo na yi laifi, Ubangiji shi ne da gaskiya. Ni da jama'ata muke da kuskure. 28 Ku roƙi Ubangiji ya tsai da tsawar da ƙanƙarar. Ni kuwa na yi alkawari zan bar ku ku tafi, ba za ku ƙara tsayawa a nan ba.” 29 Musa ya ce masa, “Da fitata daga cikin birnin, zan yi addu'a ga Ubangiji, walƙiya kuwa za ta tsaya, ƙanƙara kuma ta daina, don ku sani duniya ta Ubangiji ce. 30 Amma dai na sani, da kai da fādawanka, har wa yau ba ku ji tsoron Ubangiji Allah ba tukuna.” 31 Rama da sha'ir suka lalace, gama sha'ir ya riga ya nuna, rama kuwa tana huda. 32 Amma alkama da maiwa ba su lalace ba, gama kakarsu ba ta yi ba tukuna. 33 Sai Musa ya fita daga wurin Fir'auna ya rabu da birnin. Ya yi addu'a ga Ubangiji sai walƙiya da ƙanƙara suka tsaya, kwararowar ruwa kuma ta ɗauke. 34 Da Fir'auna ya ga an ɗauke ruwa, da ƙanƙara, da kuma walƙiya, sai ya sāke yin zunubi, ya taurare zuciyarsa, da shi da fādawansa. 35 Zuciyar Fir'auna ta taurare, har ya ƙi sakin Isra'ilawa kamar yadda Ubangiji ya riga ya faɗa ta bakin Musa.

Fitowa 10

Fara

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Je ka wurin Fir'auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da ta fādawansa domin in aikata waɗannan mu'ujizai nawa a tsakiyarsu, 2 domin kuma ka sanar da 'ya'yanka da jikokinka yadda na shashantar da Masarawa, na kuma aikata waɗannan mu'ujizai a tsakiyarsu. Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.” 3 Saboda haka Musa da Haruna suka tafi gaban Fir'auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi yarda ka ba da kanka a gare ni? Saki jama'ata don su tafi su yi mini sujada. 4 In kuwa ka ƙi yarda ka bar jama'ata su tafi, to, gobe zan aiko da fara cikin ƙasarka, 5 za ta rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za ta cinye sauran abin da ya kuɓuta daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a ƙasar. 6 Za su cika fādarka, da dukan gidajen fādawanka, da na dukan Masarawa. Iyayenka da kakanninka ba su taɓa ganin irin farar nan ba, tun daga ran da suke ƙasar, har wa yau.’ ” Sai ya juya ya fita daga gaban Fir'auna. 7 Fādawan Fir'auna kuwa suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai riƙa jawo mana masifa? Ka saki mutanen, su fita su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Ashe, har yanzu ba ka sani Masar ta lalace ba?” 8 Aka komar da Musa da Haruna gaban Fir'auna. Sai Fir'auna ya ce musu, “Ku tafi ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?” 9 Musa ya amsa, “Da samarinmu, da tsofaffinmu za mu tafi, da 'ya'yanmu mata da maza za su fita tare da mu, da kuma garkunanmu da shanunmu, gama wajibi ne mu yi idi a gaban Ubangiji.” 10 Fir'auna ya ce musu, “To, Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba, gama kuna da niyyar mugunta a zuciyarku. 11 Sai dai ku mazaje, ku tafi ku bauta wa Ubangiji, gama abin da kuke so ke nan.” To, aka kore su daga gaban Fir'auna. 12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa ƙasar Masar domin fara ta zo. Farar kuwa za ta rufe ƙasar Masar, ta cinye duk tsire-tsire da ganyayen da suke cikin ƙasar, da iyakar abin da ƙanƙara ta rage.” 13 Sai Musa ya miƙa sandansa bisa ƙasar Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a ƙasar dukan yini da dukan dare, har safiya. Iskar gabas ɗin kuwa ta kawo farar. 14 Farar ta mamaye ƙasar Masar, ta rufe dukan ƙasar. Ba a taɓa ganin fara ta taru da yawa kamar haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin kamar haka ba. 15 Ta rufe dukan fuskar ƙasa har ƙasar ta yi duhu. Ta cinye kowane tsiro na ƙasar da dukan 'ya'yan itatuwa waɗanda ƙanƙara ta rage. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar. 16 Fir'auna ya aika da gaggawa a kira Musa da Haruna. Ya ce musu, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku. 17 Amma ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma roƙar mini Ubangiji Allahnku ya ɗauke mini wannan mutuwa.” 18 Sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna, ya tafi ya roƙi Ubangiji. 19 Ubangiji kuwa ya sa iska mai ƙarfi ta huro daga wajen yamma, ta kwashi farar, ta zuba ta a Bahar Maliya. Ko fara guda ba ta ragu a cikin iyakar Masar ba. 20 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, Fir'auna kuwa ya ƙi sakin Isra'ilawa.

Duhu

21 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama, domin a yi duhu cikin ƙasar Masar, irin duhun da za a iya taɓawa.” 22 Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuwa yi duhu baƙi ƙirin har kwana uku a dukan ƙasar Masar. 23 Mutum bai iya ganin ɗan'uwansa ba, ba kuma mutumin da ya iya fita gidansa har kwana uku. Amma akwai haske inda Isra'ilawa suke zaune. 24 Fir'auna ya kirawo Musa da Haruna ya ce musu, “Ku tafi ku bauta wa Ubangiji, sai dai ku bar tumakinku, da awakinku, da shanunku a nan, amma ku ku tafi da 'ya'yanku.” 25 Musa kuwa ya ce, “In haka ne, kai ka ba mu abin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu hadayu da su. 26 Don haka sai mu tafi da dabbobinmu, ko kofato ba za a bari a baya ba, gama daga cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.” 27 Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna har bai yarda ya sake su ba. 28 Fir'auna ma ya ce wa Musa, “Tafi, ka ba ni wuri, ka mai da hankali fa, kada in ƙara ganinka, gama ran da na sāke ganinka ran nan kā mutu.” 29 Sai Musa ya amsa ya ce, “Haka nan ne kuwa, ba zan ƙara ganin fuskarka ba.”

Fitowa 11

Musa ya Hurta Mutuwar 'Ya'yan Fari

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yanzu dai zan ƙara bugun Fir'auna da Masarawa sau ɗayan nan kawai da annoba. Bayan wannan zai sake ku. Sa'ad da ya bar ku ku tafi, zai iza ƙyeyarku. 2 Sai ka faɗa wa jama'a, kowane mutum da kowace mace su roƙi kayan ado na azurfa da na zinariya daga wurin maƙwabtansu.” 3 Ubangiji kuwa ya sa jama'a su yi farin jini a idanun Masarawa. Musa kuwa ya zama babban mutum a ƙasar Masar a gaban fādawan Fir'auna da kuma gaban jama'ar. 4 Musa ya ce wa Fir'auna, “Ga abin da Ubangiji ya faɗa, ‘A wajen tsakar dare zan ratsa cikin Masar. 5 Kowane ɗan farin da yake ƙasar Masar zai rasu, daga ɗan farin Fir'auna wanda zai hau gadon sarautarsa, har zuwa ɗan farin kuyanga wadda take niƙa, da dukan ɗan farin shanu. 6 Za a kuwa yi kuka mai zafi ko'ina a ƙasar Masar irin wanda ba a taɓa yi ba, ba kuma za a ƙara yi ba. 7 Amma ko kare ba zai yi wa wani mutum ko dabba na Isra'ila haushi ba, domin ku sani Ubangiji zai bambanta tsakanin Masarawa da Isra'ilawa.’ 8 Sa'an nan dukan fādawanka za su zo wurina su fāɗi a gabana suna cewa, ‘Ka fita, kai da dukan jama'arka!’ Sa'an nan zan fita.” Daga nan sai Musa ya fita daga gaban Fir'auna a husace. 9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Fir'auna ba zai kasa kunne gare ka ba, sai na ƙara aikata waɗansu mu'ujizai cikin ƙasar Masar.” 10 Musa da Haruna suka aikata dukan waɗannan mu'ujizai a gaban Fir'auna. Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, bai kuwa saki Isra'ilawa daga ƙasarsa ba.

Fitowa 12

Idin Ketarewa

1 Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna cikin ƙasar Masar, 2 wannan wata zai zama wata na farko a shekara a gare su. 3 A faɗa wa dukan taron Isra'ilawa cewa, “A rana ta goma ga watan nan, kowane namiji ya ɗauki ɗan rago ko ɗan akuya daga cikin garke domin iyalinsa, dabba ɗaya domin kowane gida. 4 Idan da wanda iyalinsa ba za su iya cinye dabba guda ɗungum ba, saboda iyalin kima ne, to, sai su haɗa kai da maƙwabtansu, su ɗauki dabba guda gwargwadon yawansu. 5 Tilas ne dabbar ta kasance lafiyayyiya ƙalau, bana ɗaya. Za ku kamo daga cikin tumakinku ko awaki. 6 Za ku turke dabbar har rana ta goma sha huɗu ga wata, wato, sa'ad da dukan taron jama'ar Isra'ila za su yanka ragunansu da maraice. 7 Sa'an nan ku ɗibi jinin, ku sa a dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar gidajen da za a ci naman dabbobin. 8 A daren nan za ku gasa naman, ku ci da abinci marar yisti, da ganyaye masu ɗaci. 9 Kada ku ci shi ɗanye ko daffaffe da ruwa, amma a gasa shi, da kan, da ƙafafun, da kayan cikin. 10 Kada ku bar kome ya kai gobe, abin da ya kai gobe kuwa, sai ku ƙone shi. 11 Ga yadda za ku ci shi, da ɗamara a gindinku, da takalma a ƙafafunku, da sanda a hannunku, da gaggawa kuma za ku ci shi. Idin Ƙetarewa ne ga Ubangiji. 12 A daren nan zan ratsa ƙasar Masar, in bugi kowane ɗan fari na ƙasar, na mutum da na dabba. Zan hukunta gumakan Masar duka, gama ni ne Ubangiji. 13 Jinin da yake bisa gidajenku zai nuna inda kuke. Sa'ad da na ga jinin zan tsallake ku, ba kuma wani bala'in da zai same ku, ya hallaka ku, a lokacin da zan bugi ƙasar Masar. 14 Ranar nan za ta zama ranar tunawa a gare ku, za ku kiyaye ta, ranar idi ga Ubangiji. Dukan zamananku za ku kiyaye ta, idi ga Ubangiji har abada. 15 “Za ku yi kwana bakwai kuna cin abinci marar yisti. A rana ta fari za ku fitar da yisti daga cikin gidajenku, gama duk wanda ya ci abin da aka sa wa yisti tun daga rana ta fari har zuwa ta bakwai za a fitar da shi daga cikin Isra'ila. 16 A kan rana ta fari za ku yi tsattsarkan taro, haka kuma za ku yi a rana ta bakwai. A cikin waɗannan ranaku ba za a yi kowane aiki ba, sai na abin da kowa zai ci. 17 Za ku kiyaye idin abinci marar yisti, gama a wannan rana na fitar da rundunarku daga ƙasar Masar. Ku kiyaye wannan rana dukan zamananku. Wannan farilla ce ta har abada. 18 Za ku ci abinci marar yisti da maraice a kan rana ta goma sha huɗu ga wata na fari, har zuwa rana ta ashirin da ɗaya ga watan da maraice. 19 Amma kada a iske yisti a gidajenku har kwana bakwai, gama idan wani ya ci abin da aka sa wa yisti za a fitar da shi daga cikin taron jama'ar Isra'ila, ko shi baƙo ne ko kuwa haifaffen ƙasar. 20 Dukan abin da yake da yisti ba za ku ci shi ba, wato, sai abinci marar yisti ne kaɗai za ku ci a dukan gidajenku.” 21 Musa ya kirayi dattawan Isra'ila duka, ya ce musu, “Gaggauta, ku zaɓa wa kanku ɗan tunkiya ko akuya bisa ga iyalanku, ku yanka domin Idin Ƙetarewa. 22 Ku ɗauki tuntun ezob, ku tsoma cikin jinin da yake a kasko, ku yarfa wa dogaran ƙofa duka biyu, da bisa kan ƙofar. Kada kowa ya fita daga gidansa sai da safe. 23 Gama Ubangiji zai ratsa don ya kashe Masarawa, sa'ad da ya ga jinin a bisa kan ƙofar, da dogaran ƙofa duka biyu sai ya wuce ƙofar, ba zai bar mai hallakarwa ya shiga gidanku, ya kashe ku ba. 24 Za ku kiyaye waɗannan ka'idodi, ku riƙe su farilla, ku da 'ya'yanku har abada. 25 Sa'ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji zai ba ku kamar yadda ya alkawarta, wajibi ne ku kiyaye wannan farilla. 26 Sa'ad da 'ya'yanku suka tambaye ku, ‘Ina ma'anar wannan farilla?’ 27 Za ku ce, ‘Hadaya ce ta Idin Ƙetarewa ga Ubangiji, domin ya tsallake gidajen Isra'ilawa a Masar, lokacin da ya kashe Masarawa, amma bai taɓa gidajenmu ba.’ ” Sai jama'ar suka durƙusa suka yi sujada. 28 Isra'ilawa suka tafi suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna.

Mutuwar 'Ya'yan Fari

29 Da tsakar dare sai Ubangiji ya karkashe dukan 'ya'yan fari maza a ƙasar Masar, tun daga ɗan farin Fir'auna, wato, magajinsa, har zuwa ɗan farin ɗan sarka da yake a kurkuku, har da dukan 'ya'yan fari maza na dabbobi. 30 Da dare Fir'auna ya tashi, shi da dukan fādawansa, da dukan Masarawa, suka yi kuka mai tsanani a Masar, gama ba gidan da ba a yi mutuwa ba. 31 Sai Fir'auna ya sa aka kirawo masa Musa da Haruna da daren, ya ce musu, “Tashi, ku da jama'arku, ku fita daga cikin jama'ata. Tafi, ku bauta wa Ubangiji kamar yadda kuka ce. 32 Kwashi garkunanku na tumaki da awaki, da na shanu, ku yi tafiyarku kamar yadda kuka ce, amma ku sa mini albarka.” 33 Masarawa suka iza mutanen su gaggauta, su fita ƙasar, gama suka ce, “Ƙarewa za mu yi idan ba ku tafi ba.” 34 Sai jama'ar suka ɗauki ƙullun da ba a sa masa yisti ba, da ƙorensu na aikin ƙullun, suka ƙunshe a mayafansu, suka saɓa a kafaɗunsu. 35 Isra'ilawa kuwa suka yi yadda Musa ya faɗa musu, suka roƙi Masarawa kayan adonsu na azurfa da na zinariya, da kuma tufafi. 36 Ubangiji ya sa jama'a su yi farin jini a wurin Masarawa, saboda haka Masarawa suka ba su abin da suka roƙa. Ta haka suka washe Masarawa.

Isra'ilawa sun Fita Masar

37 Isra'ilawa mutum wajen zambar ɗari shida maza (600,000 ), banda iyalansu, suka kama tafiya daga Ramases zuwa Sukkot. 38 Babban taron tattarmuka kuma suka tafi tare da su, da garkunan tumaki da awaki, da na shanu tinjim. 39 Suka toya abinci marar yisti da ƙullun da suka fita da shi daga Masar, gama ba su sa yisti cikin ƙullun ba domin an iza ƙyeyarsu, ba su sami damar dakatawa ba, ba su kuwa shirya wa kansu guzuri ba. 40 Zaman da Isra'ilawa suka yi a Masar shekara ce arbaminya da talatin. 41 A ranar da shekara arbaminya da talatin ɗin nan suka cika, a ran nan ne dukan rundunar Ubangiji suka fita daga ƙasar Masar. 42 Daren nan da Ubangiji ya sa don ya fito da Isra'ilawa daga ƙasar Masar, daren ne wanda wajibi ne Isra'ilwa su kiyaye don su girmama Ubangiji dukan zamanansu.

Ka'idodin Idin Ƙetarewa

43 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, “Wannan ita ce ka'idar Idin Ƙetarewa, baƙo ba zai ci ba. 44 Amma kowane bawa da aka saya da kuɗi ya iya ci, in dai an yi masa kaciya. 45 Amma da baƙo da wanda aka yi ijararsa ba zai ci shi ba. 46 A gidan da aka shirya, nan za a ci, kada a fitar da naman waje, kada kuma a karye ƙashinsa. 47 Dukan taron jama'ar Isra'ila za su kiyaye Idin Ƙetarewa. 48 Idan baƙon da yake zaune tare da ku yana so ya yi Idin Ƙetarewa ga Ubangiji tare da ku, to, sai a yi wa kowane namiji da yake a gidansa kaciya sa'an nan ya iya shiga idin, shi kuma ya zama ɗan ƙasa. Daɗai, marar kaciya ba zai ci ba. 49 Wannan ka'ida ta shafi ɗan ƙasa daidai da baƙon da yake baƙunci tsakaninku.” 50 Isra'ilawa suka yi na'am da shi, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa da Haruna. 51 A wannan rana ce Ubangiji ya fitar da Isra'ilawa runduna runduna daga ƙasar Masar.

Fitowa 13

Keɓewar 'Ya'yan Fari

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Keɓe mini 'ya'yan fari maza duka. Kowane ɗan fari wanda ya fara buɗe mahaifa cikin Isra'ilawa nawa ne, ko na mutum ko na dabba.”

Idin Abinci Marar Yisti

3 Musa ya ce wa jama'a, “Ku kiyaye wannan rana da kuka fito daga Masar, daga gidan bauta, gama da hannu mai ƙarfi Ubangiji ya fitar da ku daga wurin. Daɗai, ba za ku ci abinci mai yisti ba. 4 A wannan rana kuka fita, wato, a watan Abib. 5 Sai ku kiyaye wannan farilla a wannan wata sa'ad da Ubangiji ya kai ku ƙasar Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, wadda ya rantse wa kakanninku zai ba ku, wato, ƙasar da take ba da yalwar abinci. 6 Sai ku riƙa cin abinci marar yisti har kwana bakwai, amma a rana ta bakwai za ku yi idi ga Ubangiji. 7 Abinci marar yisti za a ci har kwana bakwai. Kada a ga wani da abinci mai yisti, ko kuma yisti ɗin kansa, a ko'ina a wurarenku. 8 A wannan rana kowa zai sanar wa ɗansa cewa, abubuwan nan da muke yi, muna yi ne don tunawa da abin da Ubangiji ya yi mana sa'ad da ya fitar da mu daga Masar. 9 Zai zama matuni kamar alama a hannunku, da abin tunawa a goshinku, domin shari'ar Ubangiji ta zama a bakinku, gama da hannu mai ƙarfi Ubangiji ya fisshe ku daga Masar. 10 Sai ku kiyaye farillar nan kowace shekara a lokacinta.”

'Ya'yan Fari

11 “Sa'ad da Ubangiji ya kai ku ƙasar Kan'aniyawa wadda zai ba ku kamar yadda ya rantse muku, ku da kakanninku, 12 sai ku miƙa kowane ɗan fari ga Ubangiji. Kowane ɗan farin dabbarku na Ubangiji ne. 13 Amma a fanshi kowane ɗan farin jakinku da ɗan rago. Idan kuwa ba za ku fanshe shi ba, sai ku karye wuyansa. Kowane ɗan farin 'ya'yanku, sai ku fanshe shi. 14 In wata rana 'ya'yanku suka tambaye ku cewa, ‘Ina ma'anar wannan?’ Sai ku ce musu, ‘Da iko Ubangiji ya fisshe mu daga Masar, daga gidan bauta. 15 Gama sa'ad da Fir'auna ya taurare zuciyarsa, bai yarda ya sallame mu ba, Ubangiji kuwa ya kashe dukan 'ya'yan farin ƙasar Masar, na mutum da na dabba gaba ɗaya. Domin haka muke yin hadaya ga Ubangiji da 'ya'yan fari, maza, da suka fara buɗe mahaifa, amma mukan fanshi dukan 'ya'yan farinmu, maza.’ 16 Al'amarin nan kuwa zai zama matuni kamar alama a hannunku ko a goshinku, gama da iko Ubangiji ya fisshe mu daga Masar.”

Al'amudin Gizagizai da na Wuta

17 Da Fir'auna ya bar jama'a su tafi, Allah bai bi da su ta hanyar ƙasar Filistiyawa ba, ko da yake wannan hanya ta fi kusa, gama Allah ya ce, “Don kada jama'a su sāke tunaninsu sa'ad da suka ga yaƙi, su koma Masar.” 18 Amma Allah ya kewaya da jama'a ta hanyar jeji, wajen Bahar Maliya. Isra'ilawa kuwa suka fita daga ƙasar Masar da shirin yaƙi. 19 Musa ya kuma ɗauki ƙasusuwan Yusufu, gama Yusufu ya riga ya rantsar da Isra'ilawa su kwashe ƙasusuwansa daga Masar sa'ad da Allah ya ziyarce su. 20 Sai suka ci gaba da tafiya daga Sukkot suka yi zango a Etam a gefen jejin. 21 Da rana Ubangiji yakan yi musu jagora da al'amudin girgije, da dare kuwa da al'amudin wuta, don ya ba su haske domin su iya tafiya dare da rana. 22 Al'amudan nan biyu kuwa, na girgijen da na wutar, ba su daina yi wa jama'a jagora ba.

Fitowa 14

Hayen Bahar Maliya

1 Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Faɗa wa Isra'ilawa su juya su yi zango a gaban Fi-hahirot tsakanin Migdol da bahar, a gaban Ba'alzefon. Sai ku yi zango gab da bahar. 3 Gama Fir'auna zai ce, ‘Aha, Isra'ilawa sun rikice cikin ƙasar, hamada kuwa ta cinye su.’ 4 Zan taurare zuciyar Fir'auna, zai kuwa bi ku, ni Ubangiji zan nuna ɗaukakata a bisa Fir'auna da dukan rundunansa. Masarawa kuwa za su sani ni ne Ubangiji.” Haka kuwa Isra'ilawa suka yi. 5 Da aka faɗa wa Sarkin Masar jama'a sun gudu, sai shi da fādawansa suka sāke tunaninsu game da jama'ar, suka ce, “Me muka yi ke nan, da muka bar Isra'ilawa su fita daga cikin bautarmu?” 6 Ya kuwa shirya karusarsa, ya ɗauki rundunarsa tare da shi. 7 Ya kuma ɗauki zaɓaɓɓun karusai ɗari shida da sauran karusan Masar duka waɗanda shugabanni suke bi da su. 8 Ubangiji ya taurare zuciyar Fir'auna, Sarkin Masar, sai ya bi Isra'ilawa sa'ad da suka fita gabagaɗi. 9 Masarawa kuwa, da dukan dawakan Fir'auna, da karusai, da mahayan dawakansa, da askarawansa, suka bi su, suka ci musu a inda suka yi zango a bakin bahar, kusa da Fi-hahirot wanda ya fuskanci Ba'alzefon. 10 Da Fir'auna ya matso, Isra'ilawa kuwa suka ɗaga idanunsu suka ga Masarawa tafe, sun tasar musu, sai suka firgita ƙwarai, suka yi kuka ga Ubangiji. 11 Suka ce wa Musa, “Don ba makabarta a Masar, shi ya sa ka fito da mu, mu mutu a jeji? Me ke nan ka yi mana da ka fito da mu daga Masar? 12 Ashe, ba abin da muka faɗa maka tun a Masar ke nan ba cewa, ‘Ka rabu da mu, mu bauta wa Masarawa?’ Gama gwamma mu bauta wa Masarawa da mu mutu a jeji.” 13 Sai Musa ya ce wa jama'a, “Kada ku tsorata, ku tsaya cik, ku ga ceton Ubangiji, wanda zai yi muku yau, gama Masarawan nan da kuke gani yau, ba za ku ƙara ganinsu ba faufau. 14 Ubangiji zai yi yaƙi dominku, sai dai ku tsaya kurum!” 15 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Me ya sa kake yi mini kuka? Faɗa wa Isra'ilawa su ci gaba. 16 Ɗaga sandanka, ka miƙa hannunka a bisa bahar, ka raba shi, domin Isra'ilawa su taka busasshiyar ƙasa cikin bahar, su haye. 17 Ni kuwa zan taurare zukatan Masarawa domin su bi su. Ta haka zan ci nasara bisa Fir'auna da rundunansa, da karusansa, da mahayan dawakansa. 18 Masarawa kuwa za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na sami nasara bisa kan Fir'auna, da karusansa, da mahayan dawakansa.” 19 Mala'ikan Allah kuwa wanda yake tafiya a gaban rundunar Isra'ila ya tashi ya koma bayansu, haka kuma al'amudin girgijen ya tashi daga gabansu ya tsaya a bayansu. 20 Ya shiga tsakanin sansanin Masarawa da zangon Isra'ilawa. Girgije mai duhu na tsakaninsu, amma ya haskaka wajen Isra'ilawa har gari ya waye, ba wanda ya kusaci wani. 21 Da Musa ya miƙa hannunsa bisa bahar, sai Ubangiji ya sa iskar gabas mai ƙarfi ta tsaga bahar, ta tura ta baya, ta yi ta hurawa dukan dare har bahar ta bushe, ruwan kuwa ya dāre. 22 Isra'ilawa kuwa suka bi ta tsakiyar bahar, a busasshiyar ƙasa. Ruwan ya zama musu katanga dama da hagu. 23 Masarawa kuwa suka bi su har tsakiyar bahar, da dawakan Fir'auna duka, da karusansa, da mahayan dawakansa. 24 Da asubahin fāri, Ubangiji, daga cikin al'amudin wuta da na girgije, ya duba rundunar Masarawa, ya gigitar da su. 25 Kafafun karusansu suka fara kwaɓewa, da ƙyar ake jansu. Daga nan Masarawa suka ce, “Mu guje wa Isra'ilawa, gama Ubangiji yana yaƙi dominsu gāba da Masarawa.” 26 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka bisa bahar domin ruwa ya koma bisa kan Masarawa, da bisa karusansu, da mahayan dawakansu.” 27 Gari na wayewa sai Musa ya miƙa hannunsa bisa bahar, ruwan kuwa ya koma kamar yadda yake a dā. Da Masarawa suka yi ƙoƙarin tserewa, sai ruwan ya rufe su. Ubangiji kuwa ya hallaka su a tsakiyar bahar. 28 Ruwan ya komo ya rufe dukan karusai, da mahayan dawakai, da dukan rundunar Fir'auna waɗanda suka bi ta cikin bahar, ba ko ɗaya da ya ragu. 29 Amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busasshiyar ƙasa a tsakiyar bahar, ruwa kuwa ya yi musu katanga dama da hagu. 30 A wannan rana, Ubangiji ya ceci Isra'ilawa daga hannun Masarawa. Isra'ilawa kuwa suka ga gawawwakin Masarawa a bakin bahar. 31 Isra'ilawa suka ga gawurtaccen aikin da Ubangiji ya yi gāba da Masarawa. Isra'ilawa kuwa suka ji tsoron Ubangiji, suka gaskata Ubangiji da bawansa Musa.

Fitowa 15

Waƙar Musa

1 Musa da jama'ar Isra'ila suka raira wannan waƙa ga Ubangiji suka ce, “Zan raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara, Dawakai da mahayansu ya jefar cikin bahar. 2 Ubangiji ne ƙarfina da mafakata, Shi ne wanda ya cece ni. Wannan ne Allahna, zan yabe shi, Allah na kakana, zan ɗaukaka shi. 3 Ubangiji mayaƙi ne, Yahweh ne sunansa. 4 “Karusan Fir'auna da rundunarsa, ya jefar cikin bahar, Zaɓaɓɓun jarumawansa ya nutsar da su cikin Bahar Maliya. 5 Rigyawa ta rufe su, Suka nutse cikin zurfi kamar dutse. 6 Ya Ubangiji dantsen damanka, mai iko ne, Ya Ubangiji, dantsen damanka ya ragargaza magabta. 7 Cikin girman ɗaukakarka, ka kā da maƙiyanka, ka aika da hasalarka, Ka cinye su kamar ciyawa. 8 Da hucin numfashin hancinka ruwa ya tattaru, Rigyawa ta tsaya kamar tudu, Zurfafan ruwa suka daskare a tsakiyar bahar. 9 Magabcin ya ce, ‘Zan bi, in kama su, in raba ganima, Muradina a kansu zai biya, zan zare takobina, hannuna zai hallaka su.’ 10 Ka hura iskarka, bahar ta rufe su, suka nutse kamar darma cikin manyan ruwaye. 11 “Ya Ubangiji, wane ne kamarka a cikin alloli? Wa yake kamarka a cikin ɗaukaka da tsarki? Mai banrazana cikin mafifitan ayyuka, mai aikata mu'ujizai. 12 Ka miƙa dantsen damanka, ƙasa ta haɗiye su. 13 Da tabbatacciyar ƙaunarka, ka bi da jama'arka da ka fansa, Ka bi da su da ƙarfinka zuwa tsattsarkan mazauninka. 14 Al'ummai suka ji suka yi rawar jiki, Tsoro ya kama mazaunan Filistiya. 15 Sarakunan Edom suka tsorata, Shugabannin Mowab suna rawar jiki, Dukan mazaunan Kan'ana sun narke. 16 Tsoro da razana sun aukar musu, Ta wurin ikonka suka tsaya cik kamar dutse, Har jama'arka, ya Ubangiji, suka haye, I, jama'arka, ya Ubangiji, suka haye, 17 Za ka kawo su, ka dasa su a kan dutsen nan naka, Wurin, ya Ubangiji, da ka maishe shi tsattsarkan mazauninka, Tsattsarkan wurinka, ya Ubangiji, wanda ka kafa da ikonka. 18 Ubangiji zai yi mulki har abada abadin.” 19 Gama sa'ad da dawakan Fir'auna, da karusansa, da mahayan dawakansa suka shiga bahar, Ubangiji ya komar da ruwan bahar a bisansu, amma Isra'ilawa suka yi tafiya a busassiyar ƙasa ta tsakiyar bahar. 20 Sai Maryamu, annabiya, 'yar'uwar Haruna, ta ɗauki kuru cikin hannunta. Mata duka suka fita, suka bi ta da kuwaru suna ta rawa. 21 Maryamu tana raira musu waƙa tana cewa, “Raira waƙa ga Ubangiji, gama ya ci gawurtacciyar nasara, Doki da mahayinsa, ya jefar cikin bahar.”

Maɓuɓɓugan Ruwan Ɗaci

22 Musa kuwa ya bi da Isra'ilawa daga Bahar Maliya, suka shiga jejin Sur. Suka yi tafiya kwana uku cikin jejin, ba su sami ruwa ba. 23 Sa'ad da suka zo Mara, sun kasa shan ruwan Mara saboda ɗacinsa, don haka aka sa masa suna Mara. 24 Sai mutanen suka yi wa Musa gunaguni suna cewa, “Me za mu sha?” 25 Musa ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya nuna masa wani itace. Sa'an nan Musa ya karyi itacen, ya jefa cikin ruwa, ruwan kuwa ya zama mai daɗi. A nan ne Ubangiji ya kafa musu dokoki da ka'idodi, a nan ne kuma ya gwada su. 26 Ya ce, “In za ku himmantu ku yi biyayya da ni, ni da nake Ubangiji Allahnku, sai ku aikata abin da yake daidai a gare ni, ku kuma kiyaye umarnaina da dokokina duka, to, ba zan sa muku cuce-cuce irin waɗanda na sa wa Masarawa ba, gama ni ne Ubangiji da nake warkar da ku.” 27 Daga nan suka je Elim inda akwai maɓuɓɓugan ruwa goma sha biyu, da itatuwan giginya saba'in. A nan suka yi zango a bakin ruwa.

Fitowa 16

Manna da Makware

1 Taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga Elim suka shiga jejin Sin wanda yake tsakanin Elim da Sina'i, a rana ta goma sha biyar ga watan biyu bayan fitowarsu daga ƙasar Masar. 2 Sai dukan taron jama'ar Isra'ilawa suka yi wa Musa da Haruna gunaguni cikin jejin, suka ce musu, 3 “Da ma mun mutu ta ikon Ubangiji a ƙasar Masar lokacin da muka zauna kusa da tukwanen nama, muka ci abinci muka ƙoshi. Ga shi, kun fito da mu zuwa cikin jeji don ku kashe dukan wannan taro da yunwa.” 4 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ga shi, zan sauko muku da abinci daga sama. A kowace rana jama'a za su fita su tattara abin da zai ishe su a yini, da haka zan gwada su, ko za su kiyaye maganata, ko babu. 5 A kan rana ta shida, sai su ninka abin da suka saba tattarawa na kowace rana, su shirya shi.” 6 Musa da Haruna kuwa suka ce wa Isra'ilawa, “Da yamma za ku sani Ubangiji ne ya fisshe ku daga ƙasar Masar. 7 Da safe za ku ga ɗaukakar Ubangiji, gama ya ji gunagunin da kuka yi a kansa, gama wane, mu, da za ku yi gunaguni a kanmu?” 8 Musa ya kuma ce, “Da yamma Ubangiji zai ba ku nama ku ci, da safe kuwa zai ƙosar da ku da abinci, gama Ubangiji ya riga ya ji irin gunagunin da kuka yi a kansa. Ai, gunagunin ba a kanmu yake ba, wane mu? A kan Ubangiji ne kuka yi.” 9 Musa ya ce wa Haruna, “Faɗa wa taron jama'ar Isra'ila, su matso nan a gaban Ubangiji, gama ya ji gunaguninsu.” 10 Sa'ad da Haruna yake magana da taron jama'ar, suka duba wajen jeji, sai ga ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a cikin girgije. 11 Ubangiji kuwa ya yi magana da Musa ya ce, 12 “Na ji gunagunin Isra'ilawa, amma ka faɗa musu cewa, ‘A tsakanin faɗuwar rana da almuru, za ku ci nama, da safe za ku kuma ƙoshi da abinci. Sa'an nan za ku sani, ni Ubangiji Allahnku ne.’ ” 13 Da maraice makware suka zo suka rufe zangon, da safe kuma raɓa ta kewaye zangon. 14 Sa'ad da raɓar ta kaɗe, sai ga wani abu tsaki-tsaki mai laushi, fari, kamar hazo a ƙasa. 15 Sa'ad da Isra'ilawa suka gan shi, suka ce wa junansu, “Manna,” wato, “Mece ce wannan?” Gama ba su san irinta ba. Musa kuwa ya ce musu, “Wannan ita ce abincin da Ubangiji ya ba ku, ku ci. 16 Abin da Ubangiji ya umarta ke nan, ko wannenku ya tattara wadda ta ishe shi ci, kowa ya sami mudu daidai bisa ga yawan mutanen da suke cikin kowace alfarwa.” 17 Isra'ilawa suka yi haka nan, suka tattara, waɗansu suka zarce, waɗansu kuma ba su kai ba. 18 Amma da aka auna da mudu, ta waɗanda suka zarce ba ta yi saura ba, ta waɗanda ba su kai ba, ba ta gaza ba. Kowane mutum ya tattara daidai cinsa. 19 Musa ya ce musu, “Kada wani ya ci, ya bar saura har safiya.” 20 Amma waɗansu ba su kasa kunne ga Musa ba, suka bar saura, har ta kwana, kashegari kuwa ta yi tsutsotsi, ta ruɓe, sai Musa ya yi fushi da su. 21 Kowace safiya sukan tattara ta, kowa gwargwadon cinsa, amma da rana ta yi zafi sai manna ɗin ta narke. 22 A kan rana ta shida suka tattara biyu ɗin abin da suka saba, kowane mutum mudu biyu biyu. Sai shugabannin taron suka zo suka faɗa wa Musa. 23 Shi kuwa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya umarta, ‘Gobe ranar hutawa ce ta saduda, Asabar ce, tsattsarka ga Ubangiji. Ku toya abin da za ku toya, ku kuma dafa abin da za ku dafa. Abin da kuka ci kuka rage, ku ajiye don gobe.’ ” 24 Suka ajiye har gobe kamar yadda Musa ya umarta, amma ba ta yi ɗoyi ba, ba ta kuwa yi tsutsotsi ba. 25 Sai Musa ya ce, “Ita za ku ci yau, gama yau Asabar ce ga Ubangiji. Yau ba za ku same ta a saura ba. 26 Kwana shida za ku tattara ta, amma a rana ta bakwai wadda take asabar, ba za a iske kome ba.” 27 Amma a rana ta bakwai ɗin waɗansu mutane suka tafi don su tattara, ba su kuwa sami kome ba. 28 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe za ku ƙi kiyaye dokokina da umarnaina? 29 Lura fa, Ubangiji ne ya ba ku ranar Asabar, domin haka a rana ta shida yakan ba ku abinci na kwana biyu. Kowanne ya yi zamansa a inda yake. Kada kowa ya bar inda yake a rana ta bakwai ɗin.” 30 Sai jama'a suka huta a rana ta bakwai. 31 Isra'ilawa kuwa suka sa wa wannan abinci suna, Manna. Manna wata irin tsaba ce kamar farin riɗi. Ɗanɗanarta kuwa kamar waina ce da aka yi da zuma. 32 Sai Musa ya ce, “Ubangiji ya umarta a cika mudu da ita, a adana ta dukan zamananku domin kowane zamani a ga irin abincin da ya ciyar da ku cikin jeji lokacin da ya fito da ku daga ƙasar Masar.” 33 Sai Musa ya ce wa Haruna, “Ɗauki tukunya, ka zuba mudu guda na manna a ciki, ka ajiye a gaban Ubangiji, a adana har dukan zamananku.” 34 Kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa, haka Haruna ya ajiye ta a gaban akwatin alkawari don kiyayewa. 35 Shekara arba'in Isra'ilawa suka yi suna cin manna, har suka kai ƙasar da take da mutane, suka ci manna, har zuwa kan iyakar ƙasar Kan'ana. 36 Mudu ɗaya humushin garwa ɗaya ta gari.

Fitowa 17

Ruwa daga Dutse

1 Dukan taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga jejin Sin, suna tafiya daga zango zuwa zango bisa ga umarnin Ubangiji. Suka yi zango a Refidim, amma ba ruwan da jama'a za su sha. 2 Domin haka jama'a suka zargi Musa suka ce, “Ba mu ruwa, mu sha.” Musa ya amsa musu ya ce, “Don me kuke zargina? Don me kuke gwada Ubangiji?” 3 Amma jama'a suna fama da ƙishirwa, suka yi wa Musa gunaguni. Suka ce, “Don me ka fito da mu daga Masar? Ashe, don ka kashe mu ne, da mu, da 'ya'yanmu, da dabbobinmu da ƙishi?” 4 Sai Musa ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Me zan yi wa jama'ar nan? Ga shi, saura kaɗan su jajjefe ni da duwatsu.” 5 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ɗauki waɗansu dattawa daga cikin jama'ar Isra'ila, ka wuce a gaban jama'ar. Ka kuma ɗauki sandanka wanda ka bugi Nilu da shi, ka tafi. 6 Zan tsaya a dutsen Horeb can a gabanka. Za ka bugi dutsen, ruwa kuwa zai fito domin jama'a su sha.” Musa kuma ya yi haka nan a gaban dattawan Isra'ila. 7 Sai aka sa wa wurin suna, “Masaha” da “Meriba,” saboda Isra'ilawa suka yi husuma, suka kuma jarraba Ubangiji suna cewa, “Ubangiji yana tare da mu, ko babu?”

Yaƙi da Amalekawa

8 Amalekawa suka zo su yi yaƙi da Isra'ilawa a Refidim. 9 Sai Musa ya ce wa Joshuwa, “Zaɓo mana mutane, ka fita ka yi yaƙi da Amalekawa gobe. Zan tsaya a bisa dutsen da sandan mu'ujiza a hannuna.” 10 Joshuwa kuwa ya yi yadda Musa ya faɗa masa, ya fita ya yi yaƙi da Amalekawa. Musa, da Haruna, da Hur kuma suka hau kan dutsen. 11 Muddin hannun Musa na miƙe, sai Isra'ilawa su yi ta cin nasara, amma da zarar hannunsa ya sauka, sai Amalekawa su yi ta cin nasara. 12 Sa'ad da hannuwan Musa suka gaji, Haruna da Hur suka ɗauki dutse suka ajiye wa Musa, ya zauna a kai, su kuwa suka tsaya a gefen damansa da hagunsa suna tallabe da hannunsa sama, suka tallabe su har faɗuwar rana. 13 Joshuwa kuwa ya ragargaza rundunar Amalekawa da takobi. 14 Ubangiji ya ce wa Musa, “Rubuta wannan a littafi domin a tuna da shi, ka kuma faɗa wa Joshuwa zan shafe Amalekawa ɗungum.” 15 Sai Musa ya gina bagade ya sa masa suna, Yahweh Nissi, wato, Ubangiji ne tutarmu. 16 Ya ce, “Ubangiji ya tabbata zai yaƙi Amalekawa har abada.”

Fitowa 18

Yetro ya Ziyarci Musa

1 Yetro, firist na Madayana, surukin Musa, ya ji dukan abin da Allah ya yi wa jama'arsa, wato, Musa da Isra'ilawa, yadda Ubangiji ya fito da su daga Masar. 2 Ya kawo Ziffora matar Musa, wadda Musa ya aika da ita gida. 3 Yetro kuma ya kawo 'ya'yanta biyu maza, Gershom da Eliyezer tare da ita. Gama Musa ya ce, “Ni baƙo ne a baƙuwar ƙasa.” Saboda haka ne ya raɗa wa ɗaya daga cikin 'ya'yansa, suna, Gershom. 4 Ya kuma ce, “Allah na ubanan shi ne ya taimake ni, ya cece ni daga takobin Fir'auna,” saboda haka ya raɗa wa ɗayan, suna, Eliyezer. 5 Sai Yetro ya kawo wa Musa 'ya'yansa maza da matarsa a cikin jeji inda suka yi zango kusa da dutsen Allah. 6 Aka faɗa wa Musa, “Ga surukinka, Yetro, yana zuwa wurinka da matarka da 'ya'yanta biyu tare da ita.” 7 Musa kuwa ya fita ya marabce shi, ya sunkuya, ya sumbace shi. Suka gaisa, suka tambayi lafiyar juna, sa'an nan suka shiga alfarwa. 8 Sai Musa ya faɗa wa surukinsa dukan abin da Ubangiji ya yi da Fir'auna da Masarawa saboda Isra'ilawa, ya kuma faɗa masa dukan wahalar da suka sha a kan hanya, da yadda Ubangiji ya cece su. 9 Yetro kuwa ya yi murna saboda alherin da Ubangiji ya yi wa Isra'ilawa da yadda ya cece su daga hannun Masarawa. 10 Yetro kuma ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya cece ku daga hannun Masarawa da Fir'auna, wanda kuma ya ceci jama'arsa daga bautar Masarawa. 11 Yanzu na sani Ubangiji yake gāba da sauran alloli duka, gama ya ceci Isra'ilawa daga tsanantawar da Masarawa suka yi musu.” 12 Yetro, surukin Musa kuwa, ya miƙa hadaya ta ƙonawa da sadaka ga Allah. Sai Haruna ya zo tare da dattawan Isra'ila duka don su ci abinci tare da surukin Musa a gaban Allah. 13 Kashegari da Musa ya zauna garin yi wa jama'ar shari'a, mutane suka kekkewaye shi tun dage safiya har zuwa yamma. 14 Da surukin Musa ya ga yadda Musa yake fama da jama'a, sai ya ce, “Mene ne wannan da kake yi wa jama'a? Don me kake zaune kai kaɗai, mutane kuwa na tsattsaye kewaye da kai, tun daga safe har zuwa maraice?” 15 Sai Musa ya ce wa surukinsa, “Mutane suna zuwa wurina ne domin su san faɗar Allah. 16 A sa'ad da suke da wata matsala sukan zo wurina, ni kuwa nakan daidaita tsakanin mutum da maƙwabcinsa, nakan kuma koya musu dokokin Allah da umarnansa.” 17 Amma surukin Musa ya ce, “Abin nan da kake yi ba daidai ba ne. 18 Kai da jama'ar nan da take tare da kai za ku rafke, saboda abin da kake yi ya fi ƙarfinka, kai kaɗai ba za ka iya ba. 19 Yanzu sai ka saurari maganata, zan ba ka shawara, Allah kuwa ya kasance tare da kai. Za ka wakilci jama'a a gaban Allah, ka kai matsalolinsu gare shi. 20 Ka koya musu dokokin da umarnan, ka nuna musu hanyar da ya kamata su yi. 21 Ka kuma zaɓa daga cikin jama'a isassun mutane, masu tsoron Allah, amintattu, waɗanda suke ƙyamar cin hanci. Ka naɗa su shugabannin jama'a na dubu dubu da na ɗari ɗari, da na hamsin hamsin, da na goma goma. 22 Za su yi wa mutane shari'a koyaushe, amma kowace babbar matsala sai su kawo maka, ƙaramar matsala kuwa su yanke da kansu. Da haka za su ɗauki nauyin jama'a tare da kai don ya yi maka sauƙi. 23 In ka bi wannan shawara, in kuma Allah ya umarce ka da yin haka, za ka iya ɗaukar nawayar jama'ar. Mutane duka kuwa za su yi zamansu lafiya.” 24 Musa kuwa ya saurari maganar surukinsa, ya yi abin da ya ce duka. 25 Sai Musa ya zaɓi isassun mutane daga cikin Isra'ilawa ya naɗa su shugabannin jama'a na dubu dubu, da na ɗari ɗari, da na hamsin hamsin, da na goma goma. 26 Suka yi ta yi wa jama'a duka shari'a kullayaumin, amma matsaloli masu wuya sukan kawo wa Musa, ƙananan kuwa sukan yanke da kansu. 27 Sa'an nan Musa ya sallami surukinsa, ya koma garinsu.

Fitowa 19

Isra'ilawa a Dutsen Sina'i

1 Isra'ilawa sun kai jejin Sina'i a farkon watan uku bayan fitowarsu daga ƙasar Masar. 2 Da suka tashi daga Refidim, suka shiga jejin Sina'i, sai suka yi zango gaban dutsen. 3 Musa kuwa ya hau bisa dutsen don ya sadu da Allah. Ubangiji ya kira shi daga kan dutsen, ya ce, “Abin da za ka faɗa wa gidan Yakubu, wato, Isra'ilawa ke nan, 4 ‘Kun dai ga abin da na yi da Masarawa, da yadda na ɗauke ku kamar yadda gaggafa yake ɗaukar 'yan tsakinta, na kawo ku gare ni. 5 Yanzu fa, in za ku yi biyayya da ni, ku kuma kiyaye maganata, za ku zama mutanena. Dukan duniya tawa ce, amma ku za ku zama zaɓaɓɓiyar jama'ata, 6 za ku zama daular firistoci da al'umma keɓaɓɓiya a gare ni.’ Waɗannan su ne zantuttukan da za ka faɗa wa Isra'ilawa.” 7 Sa'an nan Musa ya je ya kira taron dattawan jama'a, ya bayyana musu dukan zantuttukan da Ubangiji ya umarce shi. 8 Dukan jama'a kuwa suka amsa masa baki ɗaya, suka ce, “Dukan abin da Ubangiji ya faɗa za mu aikata.” Musa kuwa ya mayar wa Ubangiji da amsar da jama'ar suka bayar. 9 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ga shi, ni da kaina, ina zuwa a gare ka cikin duhun girgije, domin jama'a su ji sa'ad da nake magana da kai, domin su amince da kai tutur.” Musa kuwa ya mayar wa Ubangiji da amsar da jama'ar suka bayar. 10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je ka wurin jama'a ka tsarkake su yau da kuma gobe, su kuma wanke tufafinsu. 11 Su shirya saboda rana ta uku, gama a kan rana ta uku zan sauko a bisa dutsen Sina'i a gabansu duka. 12 Sai ka yi wa jama'a iyaka kewaye da dutsen, ka faɗa musu cewa, ‘Ku yi hankali kada ku hau dutsen ko ku taɓa shi. Duk wanda ya taɓa dutsen za a kashe shi, 13 za a jajjefe shi da duwatsu ko a harbe shi da kibiya, kada kowa ya taɓa dutsen da hannu. Wannan kuwa ya shafi mutane duk da dabbobi, tilas ne a kashe su.’ Sa'ad da aka busa ƙahon rago, sai mutane su taru a gindin dutsen.” 14 Da Musa ya gangaro daga dutsen zuwa wurin mutane, ya tsarkake su. Su kuwa suka wanke tufafinsu. 15 Sai Musa ya ce musu, “Ku shirya saboda rana ta uku, kada ku kusaci mace.” 16 A safiyar rana ta uku aka yi tsawa, da walƙiyoyi, da girgije mai duhu a bisa dutsen, aka tsananta busar ƙaho, sai dukan jama'ar da take cikin zango suka yi rawar jiki. 17 Musa kuwa ya fito da jama'a daga zango ya shugabance su, su sadu da Allah, suka tsattsaya a gindin dutsen. 18 Ga shi, hayaƙi ya tunnuƙe dutsen Sina'i duka, saboda Ubangiji ya sauko a bisa dutsen da wuta. Hayaƙi kuwa ya tunnuƙe, ya yi sama kamar na wurin narka ma'adinai, dutsen duka ya girgiza ƙwarai. 19 Da busar ƙaho ta ƙara tsananta, sai Musa ya yi magana, Ubangiji kuwa ya amsa masa da tsawa. 20 Ubangiji ya sauko bisa dutsen Sina'i bisa ƙwanƙolin dutsen. Ya kirawo Musa zuwa ƙwanƙolin dutsen, Musa kuwa ya hau. 21 Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, ka faɗakar da jama'ar, don kada su ƙetare kan iyakar, su zo garin a kalli Ubangiji, da yawa daga cikinsu kuwa su mutu. 22 Ko firistocin da za su kusato Ubangiji, sai su tsarkake kansu, don kada in hukunta su.” 23 Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutanen ba za su iya hawan dutsen Sina'i ba, gama kai da kanka ka umarce mu cewa, ‘Ku sa iyaka kewaye da dutsen, ku tsarkake shi.’ ” 24 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Sauka, ka hau tare da Haruna. Amma kada ka bar firistoci da jama'a su ƙetare kan iyakar su hau zuwa wurina, don kada in hukunta su.” 25 Sai Musa ya sauka wurin jama'a ya faɗa musu.

Fitowa 20

Dokoki Goma

1 Allah ya faɗi dukan waɗannan zantuttuka, ya ce, 2 “Ni ne Ubangiji Allahnka wanda ya fisshe ka daga ƙasar Masar, daga gidan bauta. 3 “Kada ka kasance da waɗansu alloli sai ni. 4 “Kada ka yi wa kanka wani gunki ko kuwa wata siffa ta wani abu a sama a bisa, ko a duniya a ƙasa, ko kuma a ruwa a ƙarƙarshin ƙasa. 5 Kada ka rusuna musu, kada kuwa ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, mai kishi ne. Nakan hukunta 'ya'ya har tsara ta uku da ta huɗu na waɗanda suke ƙina. 6 Amma nakan gwada madawwamiyar ƙaunata ga dubban tsararraki da suke ƙaunata, masu kiyaye dokokina. 7 “Kada ka kama sunan Ubangiji Allahnka a banza, gama zan hukunta duk wanda ya kama sunana a banza. 8 “Tuna da rana Asabar, ka kiyaye ta da tsarki. 9 Za ku yi dukan ayyukanku cikin kwana shida, 10 amma rana ta bakwai keɓaɓɓiya ce ga Ubangiji Allahnka. A ranar ba za ka yi kowane irin aiki ba, ko kai, ko 'ya'yanka, ko barorinka, ko dabbobinka, ko kuwa baƙon da yake zaune tare da ku. 11 Gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama, da duniya, da teku, da dukan abin da yake cikinsu, amma a rana ta bakwai ya huta. Soboda haka Ubangiji yakeɓe ranar Asabar, ya tsarkake ta. 12 “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, domin ka yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka. 13 “Kada ka yi kisankai. 14 “Kada ka yi zina. 15 “Kada ka yi sata. 16 “Kada ka ɓāta sunan maƙwabcinka. 17 “Kada ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka. Kada kuma ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka, ko barorinsa mata da maza, ko sansa, ko jakinsa, ko kowane abin da yake nasa.”

Jama'a suka Tsorata

18 Da jama'a suka ji tsawar hadiri, da ƙarar ƙaho mai tsanani suka kuma ga walƙiya, da dutsen yana hayaƙi, sai suka ji tsoro suka yi rawar jiki, suka tsaya nesa. 19 Suka ce wa Musa, “Kai, ka yi magana da mu, za mu ji, amma kada Allah ya yi magana da mu don kada mu mutu.” 20 Musa kuwa ya ce wa jama'a, “Kada ku ji tsoro, gama Allah ya zo ne don ya jarraba ku, don ku riƙa girmama shi, don kuma kada ku yi zunubi.” 21 Sai jama'a suka tsattsaya nesa, Musa kuwa ya matsa kusa da girgije mai duhu inda Allah yake.

Dokoki a kan Bagadai

22 Ubangiji ya ce wa Musa, “Haka za ka faɗa wa Isra'ilawa, ‘Ku da kanku kun ji na yi magana da ku daga sama. 23 Banda ni, kada ku yi wa kanku allolin azurfa da na zinariya. 24 Za ku gina mini bagade na ƙasa. A kansa za ku miƙa mini hadayu na ƙonawa da na salama da tumakinku da shanunku. A duk inda na sa a tuna da sunana zan zo wurinku in sa muku albarka. 25 Idan kuwa za ku gina mini bagade na dutse, kada ku gina mini da sassaƙaƙƙun duwatsu, gama idan guduma ta taɓa duwatsun sun haramtu. 26 Kada ku yi wa bagadena matakai domin kada tsiraicinku ya bayyana a bisansu sa'ad da kuke hawansu.’ ”

Fitowa 21

Yadda za a Yi da Bayi

1 “Waɗannan su ne ka'idodin da za a ba Isra'ilawa. 2 Idan ka sayi bawa Ba'ibrane, zai yi bauta shekara shida, a shekara ta bakwai kuwa, a 'yantar da shi kyauta. 3 Idan yana shi kaɗai aka saye shi, sai ya fita shi kaɗai, idan kuwa yana da aure sa'ad da aka saye shi, sai matarsa ta fita tare da shi. 4 Idan kuwa ubangijinsa ne ya auro masa matar, ta kuwa haifa masa 'ya'ya mata ko maza, to, matar da 'ya'yanta za su zama na ubangijinsa, amma shi kaɗai zai fita. 5 Amma idan hakika bawa ya hurta ya ce, yana ƙaunar ubangijinsa, da matarsa, da 'ya'yansa, ba ya son 'yancin, 6 to, sai ubangijinsa ya kawo shi a gaban Allah a ƙofa ko a madogarar ƙofa, sa'an nan ubangijinsa ya huda kunnensa da abin hudawa. Zai bauta wa ubangijinsa muddin ransa. 7 “Idan mutum ya sayar da 'yarsa kamar baiwa, ba za a 'yanta ta kamar bawa ba. 8 Idan ba ta gamshi maigidanta wanda ya maishe ta kamar ɗaya daga cikin matansa ba, sai ya yarda a fanshe ta. Amma ba shi da iko ya sayar da ita ga baƙi, tun da yake bai kyauta mata ba. 9 Idan ya ba da ita ga ɗansa ne sai ya maishe ta kamar 'yarsa. 10 In mutumin ya auri wata kuma, ba zai hana wa baiwar abinci da sutura ba, ba kuma zai ƙi kwana da ita ba. 11 Idan kuwa bai cika mata wajiban nan uku ba, sai ta fita abinta, ba zai karɓi kome ba.”

Dokoki game da Nuna Ƙarfi da Yaji

12 “Duk wanda ya bugi mutum har ya kashe shi, lalle, shi ma sai a kashe shi. 13 In ba da nufi ya kashe shi ba, amma tsautsayi ne, to, sai mutumin ya tsere zuwa inda zan nuna muku. 14 Amma idan mutum ya fāɗa wa ɗan'uwansa da niyyar kisankai, lalle, sai a kashe shi ko da ya gudu zuwa bagadena. 15 “Wanda ya bugi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lalle, kashe shi za a yi. 16 “Wanda ya saci mutum, ya sayar, ko kuwa a iske shi a hannunsa, lalle kashe shi za a yi. 17 “Wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lalle kashe shi za a yi. 18 “Idan mutane suka yi faɗa, ɗayan ya jefa ɗayan da dutse, ko ya naushe shi amma bai mutu ba, sai dai ya yi ta jiyya, 19 idan mutumin ya sāke tashi ya yi tafiya ko da yana dogarawa da sanda, wanda ya buge shi zai kuɓuta, sai dai zai biya diyyar lokacin da ya ɓāta masa, ya kuma lura da shi har ya warke sarai. 20 “In mutum ya d�ki bawansa ko baiwarsa da sanda har ya mutu a hannunsa, lalle ne a hukunta shi. 21 Amma idan bawan ya rayu kwana ɗaya ko biyu, to, kada a hukunta shi, gama bawan dukiyarsa ne. 22 “Idan mutum biyu na faɗa, har suka yi wa mace mai ciki rauni, har ya sa ta yi ɓari, amma wani lahani bai same ta ba, za a ci wa wanda ya yi mata raunin tara bisa ga yadda mijinta ya yanka zai biya, in dai abin da ya yanka ya yi daidai da abin da alƙalai suka tsara. 23 Amma in wani lahani ya auku, to, sai a hukunta rai a maimakon rai, 24 ido a maimakon ido, haƙori a maimakon haƙori, hannu a maimakon hannu, ƙafa a maimakon ƙafa, 25 ƙuna a maimakon ƙuna, rauni a maimakon rauni, ƙujewa a maimakon ƙujewa. 26 “Idan mutum ya bugi bawansa ko baiwarsa a ido har idon ya lalace, sai ya 'yanta bawan ko baiwar a maimakon idon. 27 Idan ya fangare haƙorin bawansa ko na baiwarsa, sai ya 'yanta bawan ko baiwar a maimakon haƙorin.”

Hakkin Masu Abu

28 “Idan sa ya kashe ko mace ko namiji, to, lalle ne a jajjefi san da duwatsu, kada kuma a ci namansa, mai san kuwa zai kuɓuta. 29 Amma idan san ya saba fafarar mutane, aka kuma yi wa mai shi kashedi, amma bai kula ba, har san ya kashe ko mace ko namiji, sai a jajjefi san duk da mai shi. 30 Idan an yanka masa diyya, sai ya biya iyakar abin da aka yanka masa don ya fanshi ransa. 31 Haka kuma za a yi idan san ya kashe ɗan wani ko 'yar wani. 32 Idan san ya kashe bawa ko baiwa, sai mai san ya biya wa ubangijin bawan, ko baiwar, shekel talatin a kuma jajjefi san. 33 “Idan mutum ya bar rami a buɗe, ko ya haƙa rami bai rufe ba, in sa ko jaki ya fāɗa ciki, 34 mai ramin zai biya mai san ko mai jakin, mushen ya zama nasa. 35 Idan san wani ya yi wa na wani rauni har ya mutu, sai ya sayar da san da yake da rai a raba kuɗin. Haka kuma za su raba mushen. 36 Amma idan dā ma an sani san mafaɗaci ne, mai san kuwa bai kula da shi ba, sai ya biya, wato, ya ba da sa a maimakon mushen. Mushen kuwa zai zama nasa.”

Fitowa 22

Dokokin Biya

1 “Idan mutum ya saci sa ko tunkiya, ya yanka ko ya sayar, zai biya shanu biyar a maimakon sa, tumaki huɗu maimakon tunkiya. 2 In aka iske ɓarawo yana cikin ƙoƙarin shiga ya yi sata, aka buge shi har ya mutu, to, ba za a nemi alhakin jininsa ga kowa ba, 3 sai dai ko in gari ya riga ya waye. Dole ɓarawon ya yi cikakkiyar ramuwa, in kuwa ba shi da abin biya, a sayar da shi a biya abin da ya satar. 4 In kuwa aka iske dabbar da ya satar a hannunsa da rai, ko sa, ko jaki, ko tunkiya, lalle ne ya biya riɓi biyu. 5 “In mutum ya kai dabbarsa kiwo a saura ko a garka, ya bar ta, ta yi ɓarna a gonar wani, ko a gonar inabin wani, sai a sa mai dabbar ya biya tara daga amfanin gonarsa mafi kyau duka. 6 “Idan wuta ta tashi a jeji ta ƙone tarin hatsi, ko hatsin da yake tsaye, ko gona, wanda ya sa wutar lalle ya biya cikakkiyar ramuwa. 7 “Idan mutum ya ba amininsa amanar kuɗi, ko amanar kadara, amma aka sace, in aka sami ɓarawon, a sa shi ya biya ninki biyu. 8 In kuwa ba a sami ɓarawon ba, sai a kawo maigidan a gaban Allah don a tabbatar babu hannunsa a cikin dukiyar amininsa. 9 “A kowane laifi na cin amana, ko sa ne, ko jaki, ko tunkiya, ko tufa, ko kowane ɓataccen abu, da abin da aka samu a hannun wani, in akwai jayayya, za a kawo mutumin nan a gaban Allah. Wanda Allah ya ce shi ne da laifi, sai ya biya wa ɗayan ninki biyu. 10 “In mutum ya bai wa amininsa amanar jaki, ko sa, ko tunkiya ko kowace irin dabba, amma dabbar ta mutu, ko ta yi rauni, ko ta ɓace, in ba shaida, 11 rantsuwa ce za ta raba tsakaninsu don a tabbatar babu hannunsa a dukiyar amininsa, mai dukiyar kuwa ya yarda da rantsuwar. Wanda aka bai wa amanar ba zai biya ba. 12 In dai sacewa aka yi, sai ya biya mai shi. 13 Idan kuwa naman jeji ne ya kashe ta, zai nuna gawar don shida. Ba zai yi ramuwar abin da naman jeji ya kashe ba. 14 “Idan mutum ya yi aron wani abu a wurin maƙwabcinsa, in abin ya yi rauni ko ya mutu, sa'ad da mai abin ba ya nan, lalle ne ya yi ramuwa. 15 Amma in mai abin yana wurin, wanda ya yi aro ba zai yi ramuwa ba. Idan kuwa jingina ce aka yi, kuɗin jinginar ne ramuwar.”

Dokokin Addini da na Inganta Halin Kirki

16 “Idan mutum ya rarrashi budurwa wadda ba a tashinta, har ya ɓata ta, sai ya biya sadaki, ya aure ta. 17 Amma idan mahaifinta bai yarda ya ba da ita gare shi ba, sai mutumin ya ba da sadaki daidai da abin da akan biya domin budurwa. 18 “Kada a bar mace mai sihiri ta rayu. 19 “Duk wanda ya kwana da dabba, lalle kashe shi za a yi. 20 “Wanda ya miƙa hadaya ga wani allah, ba ga Ubangiji ba, sai a hallaka shi ɗungum. 21 “Kada ku wulakanta baƙo ko ku zalunce shi, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar. 22 Kada ku ci zalun marayu da gwauraye. 23 In kun tsananta musu, ba shakka za su yi kuka gare ni, ni kuma, hakika zan ji kukansu. 24 Zan husata, in sa a kashe ku cikin yaƙi, matanku, su ma, su zama gwauraye, 'ya'yanku kuwa su zama marayu. 25 “Idan kun ranta wa jama'ata matalauta da suke tsakaninku kuɗi, ba za ku zama musu kamar masu ba da rance da ruwa ba. Kada ku nemi ruwan kuɗin daga gare su. 26 In har wani ya karɓi rigar amininsa jingina, lalle ne ya mayar masa da ita kafin faɗuwar rana. 27 Gama wannan ne kaɗai mayafinsa, da shi zai rufe huntancinsa. Da me zai rufa ya yi barci? Zan amsa masa kuwa in ya yi kuka gare ni, gama cike nake da juyayi. 28 “Kada ku saɓi Allah, kada kuma ku zagi mai mulkin jama'arku. 29 “Kada ku yi jinkirin fitar da zakar amfanin gonarku ta hatsi da ta abin matsewa. “'Ya'yan farinku, maza, kuma za ku ba ni su. 30 Haka kuma za ku yi da 'ya'yan farin shanunku, da na awakinku, da na tumakinku. Ɗan farin zai yi kwana bakwai tare da uwar, amma a rana ta takwas za ku ba ni shi. 31 “Za ku zama keɓaɓɓun mutane a gare ni. Kada ku ci dabbar da naman jeji ya yayyage shi, sai ku jefa wa karnuka.”

Fitowa 23

Adalci da Aikata Gaskiya

1 Kada ku baza rahoton ƙarya. Kada wani ya haɗa baki da mugu ya zama munafukin mashaidi. 2 Kada ku yi mugunta domin galibin mutane na yi, kada kuwa ku yi shaidar zur a gaban shari'a don ku faranta zuciyar yawancin mutane, domin kada ku sa a kauce wa adalci. 3 Kada ku yi wa matalauci sonkai a gaban shari'a. 4 “Idan wani ya iske san maƙiyinsa ko jakinsa ya ɓace, sai ya komar masa da shi. 5 Idan wani ya ga kaya ya danne jakin maƙiyinsa kada ya tafi ya bar shi da shi, sai ya taimaka a ɗaga masa. 6 “Kada ku rasa yin adalci ga matalauci a wurin shari'a. 7 Ku yi nesa da ƙage. Kada ku kashe marar laifi da kuma adali, gama ba zan baratar da mugu ba. 8 Kada ku ci hanci, gama cin hanci yakan makantar da masu mulki, yakan kuma karkatar da manufar masu gaskiya. 9 “Kada ku wulakanta baƙo, kun dai san halin baƙunci, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar.”

Shekara ta Bakwai da Rana ta Bakwai

10 “Za ku nomi gonakinku shekara shida, kuna tattara amfaninsu. 11 Amma a shekara ta bakwai, ku bar su su huta kurum, ba za ku girbi kome daga ciki ba, domin mutanenku matalauta su ci abin da ya ragu, namomin jeji kuma su ci. Haka kuma za ku yi da gonakinku na inabi da na zaitun. 12 “Cikin kwana shida za ku yi aikinku, amma a kan rana ta bakwai sai ku huta, don shanunku da jakunanku su kuma su huta, don bayinku da baƙinku su wartsake. 13 Ku kula da dukan abin da na faɗa muku. Kada a ji bakinku na roƙon kome ga waɗansu alloli.”

Ƙayyadaddun Idodi Uku

14 “Sau uku a shekara za ku yi mini idi. 15 Wajibi ne ku yi idin abinci marar yisti, kamar yadda na umarce ku. Za ku ci abinci marar yisti kwana bakwai lokacin da aka ayyana a watan Abib, gama a wannan wata ne kuka fito daga Masar. Kada wani ya zo wurina hannu wofi. 16 Ku kuma yi idin nunan fari na amfanin gonakinku da kaka. Sa'an nan kuma za ku yi idin gama tattara amfanin gonakinku a ƙarshen shekara. 17 Sau uku a shekara mazaje za su gabatar da kansu a gaban Ubangiji. 18 “Kada ku miƙa jinin hadayata tare da abinci mai yisti. Kada kuma ku ajiye kitsen abin da aka yanka a lokacin idina, ya kwana. 19 “Wajibi ne ku kawo mafi kyau daga cikin nunan fari na amfanin gonakinku a gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya cikin madarar uwarsa.”

Mala'ikan Ubangiji zai Bi da Isra'ilawa

20 “Ni da kaina zan aiki mala'ika a gabanku don ya kiyaye ku a sa'ad da kuke tafiya, ya kuma kai ku inda na shirya muku. 21 Ku nuna masa bangirma, ku kasa kunne ga maganarsa. Kada ku tayar masa, gama ba zai gafarta muku laifofinku ba, gama shi wakilina ne. 22 Idan kun kasa kunne a hankali ga maganarsa, kuka aikata dukan abin da na faɗa, sai in zama maƙiyin maƙiyanku da magabcin magabtanku. 23 Mala'ikana zai wuce gabanku, ya bi da ku inda Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Kan'aniyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa suke, zan kuma hallakar da su ƙaƙaf. 24 Ba za ku rusuna wa allolinsu ba, balle fa ku bauta musu, kada ku yi yadda suke yi. Sai ku hallaka allolinsu ɗungum, ku farfashe keɓaɓɓun duwatsunsu. 25 Za ku bauta wa Ubangiji Allahnku, ni kuwa zan yalwata abincinku da ruwan shanku, in kuma kawar muku da ciwo. 26 A ƙasarku, mace ba za ta yi ɓari ba, ba kuma za a sami marar haihuwa ba. Zan ba ku tsawon rai. 27 “Zan aiki razanata a gabanku, in sa mutanen da za ku gamu da su su ruɗe. Zan sa maƙiyanku duka su ba ku baya, su sheƙa a guje. 28 Zan aiki zirnako a gabanku, su kore muku Hiwiyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa. 29 Ba a shekara guda zan kore muku su ba, don kada ƙasar ta zama kufai har namomin jeji su fi ƙarfinku. 30 Da kaɗan da kaɗan zan kore muku su, har yawanku ya kai yadda za ku mallaki ƙasar. 31 Zan yanka muku kan iyaka daga Bahar Maliya zuwa tekun Filistiyawa, daga jeji kuma zuwa Kogin Yufiretis. Gama zan ba da mazaunan ƙasar a hannunku, za ku kore su daga gabanku. 32 Kada ku ƙulla alkawari da su, ko da allolinsu. 33 Kada su zauna cikin ƙasarku domin kada su sa ku ku yi mini zunubi, ku bauta wa allolinsu, har abin kuwa ya zamar muku tarko.”

Fitowa 24

Tabbatar da Alkawari

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku zo wurina, kai, da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawa saba'in na Isra'ila. Ku yi sujada daga nesa kaɗan. 2 Musa ne kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama'a su hau tare da shi.” 3 Musa ya tafi, ya faɗa wa jama'a dukan dokokin Ubangiji da ka'idodinsa, sai dukan jama'a suka amsa gaba ɗaya, suka ce, “Za mu kiyaye dukan dokokin da Ubangiji ya ba mu.” 4 Musa kuwa ya rubuta dukan dokokin Ubangiji. Kashegari da sassafe ya gina bagade a gindin dutsen, da kuma ginshiƙai goma sha biyu bisa ga yawan kabilai goma sha biyu na Isra'ila. 5 Ya kuma sa samarin Isra'ila su miƙa hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta salama, da bijimai ga Ubangiji. 6 Sai Musa ya zuba rabin jinin a tasa, sauran rabin jinin kuwa ya yayyafa a kan bagade. 7 Ya kuma ɗauki Littafin Alkawari, ya karanta wa jama'a, sai suka ce, “Za mu yi dukan abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi biyayya.” 8 Musa kuwa ya ɗauki jinin ya watsa wa jama'ar. Sa'an nan ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, wanda yake a cikin dokokin nan duka.” 9 Musa ya haura tare da Haruna, da Nadab, da Abihu, da dattawan nan saba'in na Isra'ila. 10 Suka ga Allah na Isra'ila. Wurin da yake a ƙarƙashin tafin ƙafafunsa yana kama da daɓen da aka yi da dutsen yakutu, garau kamar sararin sama. 11 Amma Ubangiji bai yi wa dattawan Isra'ila wani abu ba, ko da yake suka ga zatin Allah. Su kuma suka ci suka sha a gaban Allah.

Musa a bisa Dutsen Sina'i

12 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka hawo zuwa wurina a bisa dutsen, ka zauna har in ba ka allunan dutse da suke da dokoki da farillan da na rubuta don a koya musu.” 13 Sai Musa ya tashi, shi da baransa Joshuwa, suka tafi, suka hau dutsen Allah. 14 Ya ce wa dattawan, “Ku dakata a nan har mu komo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai ya je wurinsu.” Sa'an nan Musa ya hau bisa dutsen. 15 Da hawan Musa bisa dutsen, girgije ya rufe kan dutsen. 16 Ɗaukakar Ubangiji kuma ta zauna bisa Dutsen Sina'i. Girgijen ya lulluɓe dutsen har kwana shida, a rana ta bakwai kuwa Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen. 17 Isra'ilawa suka ga ɗaukakar Ubangiji kamar wuta mai cinyewa a bisa ƙwanƙolin dutsen. 18 Sai Musa ya shiga girgijen, ya hau bisa dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba'in da dare arba'in.

Fitowa 25

Sadakoki domin Yin Wuri Mai Tsarki

1 Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Faɗa wa Isra'ilawa su karɓo mini kaya daga dukan wanda ya yi niyyar bayarwa. 3 Ga irin sadakokin da za ku karɓa, zinariya, da azurfa, da tagulla, 4 da ulu mai launin shuɗi, da mai launin shunayya, da mai launin ja, da lilin mai laushi, da gashin akuya, 5 da jemammun fatun raguna, da fatun awaki, da itacen ƙirya, 6 da mai domin fitila, da kayan yaji domin man keɓewa, da turaren ƙonawa, 7 da onis, da duwatsun da za a mammanne a falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 8 Za su yi tsattsarkan wuri domina, don in zauna tare da su. 9 Za ku yi mazaunina da kayayyakinsa duka, bisa ga irin fasalin da zan nuna maka.”

Akwatin Alkawari

10 “Sai ku yi akwatin alkawari da itacen maje, tsawonsa ya zama kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa ya zama kamu ɗaya da rabi. 11 Ku dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje. Ku yi wa gyaffansa ado da gurun zinariya. 12 Za ku yi wa akwatin ƙawanya huɗu na zinariya ku liƙa a kowace kusurwar akwatin, wato, ƙawanya biyu a kowane gefe na tsawon. 13 Za ku kuma yi sanduna da itacen ƙirya, ku dalaye su da zinariya. 14 Ku sa sandunan a kafar kowace ƙawanya da take gyaffan akwatin saboda ɗaukarsa. 15 Za a bar sandunan cikin ƙawanen akwatin, kada a zare su. 16 A kuma sa allunan da suke da dokokin da zan ba ka a cikin akwatin. 17 “Za ku yi wa akwatin murfi da zinariya tsantsa, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi. 18 Za ku yi siffofin kerubobi biyu da ƙerarriyar zinariya, ku sa a gefen nan biyu na murfin. 19 Siffar kerub ɗaya a kowane gefe. Ku yi su ta yadda za su zama ɗaya da murfin. 20 Fikafikan kerubobin za su miƙe bisa domin su inuwantar da murfin, za su fuskanci juna, suna duba murfin. 21 Za ku sa murfin bisa akwatin. A cikin akwatin kuwa za ku sa allunan da suke da dokokin da zan ba ka. 22 A nan zan zo in sadu da kai, in yi magana da kai, wato, tsakanin kerubobi biyu da suke bisa akwatin alkawari. Zan ba ka umarnaina duka don Isra'ilawa.”

Teburin Gurasar Ajiyewa ga Ubangiji

23 “Ku yi tebur da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu, fāɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa kuma kamu ɗaya da rabi. 24 Ku dalaye shi da zinariya tsantsa, ku kuma yi masa ado kewaye da gurun zinariya. 25 Za ku yi wa tebur ɗin dajiya mai fāɗin tafin hannu, ku kuma yi wa dajiyar ado da gurun zinariya. 26 Za ku yi ƙawanya huɗu da zinariya, ku sa a kusurwa huɗu na ƙafafun teburin. 27 Ƙawanen za su kasance kusa da dajiyar don su riƙe sandunan ɗaukar teburin. 28 Ku yi sanduna da itacen ƙirya, sa'an nan ku dalaye su da zinariya. Da su za a riƙa ɗaukar teburin. 29 Da zinariya tsantsa kuma za ku yi farantansa, da kwanonin tuya, da butocinsa, da kwanoninsa domin yin hadayu na sha. 30 Kullum za ku riƙa ajiye gurasar da kuke kawo mini a bisa teburin.”

Alkuki

31 “Ku kuma yi alkuki da zinariya tsantsa. Ku yi gindinsa da gorar jikinsa da ƙerarriyar zinariya. Ƙoƙuna, da mahaɗai, da furanninsa a haɗe da shi za ku yi su. 32 Alkukin ya kasance da rassa shida, rassa uku a kowane gefe. 33 A kowane reshe na alkuki za a yi ƙoƙuna uku masu kamar tohon almond. Ya kasance kuma da mahaɗai da furanni. 34 Za a yi wa gorar alkukin ƙoƙuna huɗu masu kamar tohon almond, da mahaɗai da furanni. 35 A gindin kowane reshe biyu za a yi mahaɗi ɗaya. 36 Da mahaɗai da rassan za su kasance a haɗe da alkukin. Da ƙerarriyar zinariya za a yi su. 37 Ku kuma yi fitilu bakwai, ku sa su a bisa alkukin ta yadda za su haskaka wajen da suka fuskanta. 38 Ku kuma yi hantsuka da farantai da zinariya tsantsa. 39 Da zinariya tsantsa na talanti ɗaya za ku yi alkukin da waɗannan abubuwa duka. 40 Sai ku lura, ku yi waɗannan abubuwa duka bisa ga fasalin da aka nuna maka a bisa dutsen.”

Fitowa 26

Alfarwa, wato, wurin da Allah zai Zauna

1 “Alfarwar kanta, za ku yi ta da labule goma na lilin mai laushi ninki biyu, da ulu mai launi shuɗi, da launi shunayya da launi ja. Waɗannan labule za a yi musu zānen siffofin kerubobi, aikin gwani. 2 Tsawon kowane labule zai zama kamu ashirin da takwas, fāɗinsa kuwa kamu huɗu. Labulen su zama daidai wa daida. 3 Labule biyar biyar, za a harhaɗa, a ɗinka. 4 Ku kuma yi wa labulen nan biyu hantuna na shuɗi a karbunsu na bisa. 5 Za ku yi wa kowane labule hantuna hamsin. Hantunan labulen nan biyu su yi daura da juna. 6 Za ku yi maɗauri guda hamsin da zinariya don a haɗa hantuna na labulen nan domin alfarwa ta zama ɗaya. 7 “Ku yi labule goma sha ɗaya da gashin awaki, da za ku rufe alfarwar da shi. 8 Tsawon kowanne zai zama kamu talatin, fāɗinsa kamu huɗu. Labulen za su zama daidai wa daida. 9 Za ku harhaɗa biyar ku ɗinka. Haka kuma za ku yi da sauran shidan. Ku ninka na shida riɓi biyu, ku yi labulen ƙofar alfarwa da shi. 10 Za ku kuma sa hantuna hamsin a karbun labulen daga bisa. Haka nan kuma za a sa hantuna hamsin a karbun ɗayan. 11 Sa'an nan ku yi maɗauri hamsin da tagulla, ku ɗaura hantunan da su don ku haɗa alfarwar ta zama ɗaya. 12 Ragowar rabin labulen da yake a bisa alfarwar, sai a bar shi yana reto a bayan alfarwar. 13 Kamu ɗayan da ya ragu a kowane gefe na tsawon, sai a bar shi yana reto a kowane gefe domin ya rufe alfarwar. 14 Za ku yi abin rufe alfarwa da fatun raguna da aka rina ja, za ku kuma yi wani abin rufewa da fatun da aka jeme. 15 “Za ku yi alfarwar da katakon itacen ƙirya. Za ku kakkafa su a tsaye. 16 Tsawon kowane katako zai zama kamu goma, fāɗinsa kamu ɗaya da rabi. 17 Za a fiƙe kan kowane katako. Haka za ku yi da dukan katakan. 18 Za ku shirya katakan alfarwa kamar haka, katakai ashirin wajen gefen kudu. 19 Ku kuma yi kwasfa arba'in da azurfa da za a sa wa katakan nan ashirin. Za a sa kawunan katakan da aka fiƙe a cikin kwasfa. 20 Za ku kuma kafa katakai ashirin wajen gefen arewa na alfarwar. 21 Haka kuma za ku yi kwasfa arba'in da azurfa dominsu. Kwasfa biyu domin kowane katako. 22 A wajen yamma ga alfarwa kuma ku kafa katakai shida. 23 Ku kuma sa katakai biyu a kowace kusurwa ta yamma a alfarwa. 24 Katakan nan kuwa, sai a haɗa su daga ƙasa zuwa sama, a ɗaure. Haka za a yi da katakan kusurwar nan biyu. Za su zama na kusurwa biyu. 25 Za a sami katakai takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida, kowane katako yana da kwasfa biyu. 26 “Sai ku yi sanduna da itacen ƙirya. Sanduna biyar domin katakai na gefe ɗaya. 27 Biyar kuma domin katakai na wancan gefe. Har yanzu kuma biyar domin katakai na gefen yamma. 28 Sandan da yake tsakiyar katakan zai bi daga wannan gefe zuwa ƙarshen wancan gefe. 29 Za ku dalaye katakan da zinariya, ku kuma yi musu ƙawanen zinariya inda za a sa sandunan. Za ku dalaye sanduna kuma da zinariya. 30 Ta haka za ku yi alfarwar bisa ga fasalin da aka nuna maka a bisa dutsen. 31 “Za ku yi labule da lallausan zaren lilin, mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. A yi shi da gwaninta, a zana siffofin kerubobi a kansa. 32 Ku rataye shi a bisa dirkoki huɗu nan itacen ƙirya waɗanda aka dalaye da zinariya, da maratayansu na zinariya waɗanda aka sa cikin kwasfa huɗu na azurfa. 33 Za ku sa labulen a ƙarƙashin maɗauran, sa'an nan ku shigar da akwatin alkawari a bayan labulen. Labulen zai raba tsakanin Wuri Mai Tsarki da Wuri Mafi Tsarki. 34 Ku sa murfin a bisa akwatin alkawari a Wuri Mafi Tsarki. 35 Sai ku sa teburin a gaban labulen wajen arewa, ku kuma sa alkukin a kudancin alfarwar daura da teburin. 36 Haka nan kuma za ku yi wa ƙofar alfarwa makari da lallausan zaren lilin mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi, aikin mai gwaninta. 37 Ku yi dirkoki biyar da itacen ƙirya saboda makarin, ku dalaye su da zinariya. Ku kuma yi maratayansu da zinariya. Ku yi wa waɗannan dirkoki kwasfa biyar da tagulla.”

Fitowa 27

Bagade

1 “Za ku yi bagaden da itacen ƙirya, mai tsawo kamu biyar, da fāɗi kamu biyar, tsayinsa kamu uku. Bagaden zai zama murabba'i. 2 A yi masa zankaye a kusurwoyinsa. Za ku haɗa zankayen da jikin bagaden. Za ku dalaye bagaden duka da tagulla. 3 Za ku ƙera kwanoni domin tokar bagade, da manyan cokula da daruna, da cokula masu yatsotsi, da kuma farantai domin wuta. Za ku ƙera dukan kayayyakin bagaden da tagulla. 4 Za ku kuma yi wa bagaden raga da tagulla, sa'an nan ku sa wa ragar ƙawane a kusurwoyinta huɗu. 5 Za ku sa ragar a cikin bagaden a tsakiya. 6 Ku yi wa bagaden sanduna da itacen ƙirya, sa'an nan ku dalaye su da tagulla. 7 Za a zura sandunan a ƙawanen da suke gyaffan bagade don ɗaukarsa. 8 Za ku yi bagaden da katakai, sa'an nan ku roɓe cikinsa. Ku yi shi bisa ga fasalin da na nuna maka bisa dutsen.

Farfajiyar Alfarwar

9 “Za ku yi wa alfarwa farfajiya. A kudancin farfajiyar, sai ku rataye labule mai tsawo kamu ɗari wanda aka saƙa da lallausan zaren lilin. 10 Za ku yi masa dirkoki guda ashirin, da kwasfansu guda ashirin da tagulla, amma ku yi wa dirkokin maratayai da maɗaurai da azurfa. 11 A wajen arewa kuma, sai ku rataya labule mai tsawon kamu ɗari. Ku yi masa dirkoki da kwasfansu guda ashirin da tagulla, amma ku yi wa dirkokin maratayai da maɗaurai da azurfa. 12 Fāɗin labulen a wajen yamma na farfajiyar, zai zama kamu hamsin. A yi wa labulen dirkoki goma, a kuma yi wa dirkokin kwasfa goma. 13 Fāɗin labulen wajen gabas na farfajiyar zai zama kamu hamsin. 14 Labulen ƙofa na gefe ɗaya zai zama kamu goma sha biyar, da dirkoki uku tare da kwasfansu uku. 15 Haka kuma labulen ƙofa na wancan gefe zai zama kamu goma sha biyar, da dirkoki uku tare da kwasfansu uku. 16 Za a saƙa labule mai kamu ashirin da lallausan zaren lilin mai launi shuɗi, da shunayya, da mulufi domin ƙofar farfajiyar. Za a sa wa ƙofar dirkoki huɗu tare da kwasfansu huɗu. 17 Za a yi wa dukan dirkokin da suke kewaye da farfajiyar maɗaurai da maratayai na azurfa, da kwasfa ta tagulla. 18 Tsawon farfajiyar zai zama kamu ɗari, fāɗinta kamu hamsin, tsayinta kamu biyar. Za a saƙa labulenta da lallausan zaren lilin, a kuma yi kwasfanta da tagulla. 19 Da tagulla kuma za a yi turakun alfarwar, da turakun farfajiyar, da dukan kayayyakin da za a yi amfani da su a cikin alfarwar.”

Kulawa da Fitila

20 “Sai a umarci Isra'ilawa su kawo tsabtataccen man zaitun tatacce domin fitilar. Za a kunna fitilar ta yi ta ci koyaushe. 21 Za a ajiye ta a cikin alfarwar a gaban labule na wurin shaida. Haruna da 'ya'yansa za su lura da ita daga safiya har maraice. Wannan zai zama ka'ida har abada ga Isra'ilawa.”

Fitowa 28

Tufafin Firistoci

1 “Daga cikin 'ya'ya maza na Isra'ila sai ka kirawo ɗan'uwanka Haruna tare da 'ya'yansa, Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar, su zama firistoci masu yi mini aiki. 2 A ɗinka wa Haruna ɗan'uwanka, tufafi masu tsarki domin daraja da kwarjini. 3 Ka kuma yi magana da gwanayen sana'a duka waɗanda na ba su fasaha, don su ɗinka wa Haruna tufafi, gama za a keɓe shi ya zama firist ɗina. 4 Waɗannan su ne irin tufafin da za su ɗinka, ƙyallen maƙalawa a ƙirji, da falmaran, da taguwa, da zilaika, da rawani, da abin ɗamara. Za su yi wa ɗan'uwanka, Haruna, da 'ya'yansa tufafi tsarkaka, don su zama firistoci masu yi mini aiki. 5 Sai su yi amfani da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. 6 “Za su yi falmaran da zinariya, da shuɗi, da shunayya da mulufi, da lallausan zaren lilin, aikin gwani. 7 Za a yi mata kafaɗa biyu, sa'an nan a haɗa su a karbunsu. 8 Za a yi mata abin ɗamara da irin kayan da aka yi falmaran, wato, da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. Za a yi mata saƙar gwaninta. 9 A kuma ɗauki duwatsu biyu masu daraja, a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a kai. 10 Sunaye shida a kowane dutse bi da bi bisa ga haihuwarsu. 11 Za a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a bisa duwatsun nan kamar yadda mai yin aiki da lu'ulu'u yakan zana hatimai. Za a sa kowane dutse a cikin tsaiko na zinariya. 12 A sa duwatsun a kafaɗun falmaran don a riƙa tunawa da 'ya'yan Isra'ila. Haruna zai rataya sunayensu a kafaɗunsa a gaban Ubangiji domin a tuna da su. 13 Za ku yi tsaiko biyu na zinariya, 14 ku kuma yi tukakkun sarƙoki biyu na zinariya tsantsa. Za ku ɗaura wa tsaikunan nan tukakkun sarƙoƙi. 15 “Ku kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji don neman nufin Allah. Sai a saƙa shi da gwaninta kamar yadda aka saƙa falmaran ɗin. A saƙa shi da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. 16 Ƙyallen maƙalawa a ƙirji zai zama murabba'i, a ninke shi biyu tsawonsa da fāɗinsa su zama kamu ɗaya ɗaya. 17 Sai a yi jeri huɗu na duwatsun a kanta. A jeri na fari, a sa yakutu, da tofaz, da zumurrudu. 18 A jeri na biyu, a sa turkos, da saffir, da daimon. 19 A jeri na uku, a sa yakinta, da idon mage, da ametis. 20 A jeri na huɗu, a sa beril, da onis, da yasfa. Za a sa su cikin tsaiko na zinariya. 21 A bisa duwatsun nan goma sha biyu, sai a zana sunayen 'ya'yan Isra'ila bisa ga kabilansu goma sha biyu. Za a zana sunayen kamar hatimi. 22 Ku kuma yi wa ƙyallen maƙalawa a ƙirji tukakkun sarƙoƙi na zinariya tsantsa. 23 Za ku yi ƙawanya biyu na zinariya, ku sa su a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 24 Ku sa tukakkun sarkoƙin nan biyu na zinariya a cikin ƙawanya biyu na zinariya da suke a gyaffan ƙyallen maƙalawa a ƙirji, a haɗa su daga gaba a kafaɗun falmaran. 25 Za ku kuma sa sauran bakunan sarƙoƙin nan biyu a cikin tsaikuna, sa'an nan a sa shi a gaban kafaɗun falmaran. 26 Ku kuma yi waɗansu ƙawane na zinariya, a sa su a sauran kusurwoyi na ƙyallen maƙalawa a ƙirji, a gefe na ciki da yake manne da falmaran. 27 Ku kuma yi waɗansu ƙawanya biyu na zinariya, a sa su a ƙashiyar kafaɗu biyu na falmaran daga gaba, a sama da abin ɗamarar nan. 28 Za su ɗaure ƙyallen maƙalawa a ƙirji a ƙawanensa haɗe da ƙawanen falmaran da shuɗiyar igiya domin ƙyallen maƙalawa a ƙirji ya zauna bisa abin ɗamarar falmaran, don kuma kada ya yi sako-sako a bisa falmaran. 29 Duk sa'ad da Haruna zai shiga Wuri Mai Tsarki, zai ɗauki sunayen 'ya'yan Isra'ila a gaban Ubangiji kullum, a kan ƙyallen maƙalawa domin nemar musu nufin Allah. 30 Za ku kuma sa Urim da Tummin a kan ƙyallen maƙalawar domin su kasance a zuciyar Haruna sa'ad da ya shiga gaban Ubangiji. Haka kuwa kullum Haruna zai riƙa kai kokekoken Isra'ilawa a gaban Ubangiji. 31 “Sai ku yi taguwar falmaran da shuɗi duka. 32 Za a yanke wuya a tsakiyarta don sawa. A yi wa wuyan shafi, sa'an nan a yi wa wuyan basitsa, wato, cin wuya, domin kada ya kece. 33 Za a yi wa karbun taguwar ado da fasalin 'ya'yan rumman masu launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. A sa ƙararrawa ta zinariya a tsakankaninsu. 34 Za a jera su bi da bi, wato, 'ya'yan rumman na biye da ƙararrawar zinariya. 35 Sai Haruna ya sa taguwar sa'ad da yake aiki. Za a ji ƙarar ƙararrawar a lokacin da yake shiga da lokacin da yake fita Wuri Mai Tsarki a gaban Ubangiji don kada ya mutu. 36 “Sai kuma a yi allo na zinariya tsantsa, a zana rubutu irin na hatimi a kansa haka, ‘MAI TSARKI GA UBANGIJI.’ 37 Sai a ɗaura shi da shuɗiyar igiya a rawanin daga gaba. 38 Haruna kuwa zai sa shi bisa goshinsa, ta haka zai ɗauki kurakuran da ya yiwu Isra'ilawa sun yi cikin miƙa sadakokinsu masu tsarki. Kullum Haruna zai riƙa sa shi bisa goshinsa don su zama karɓaɓɓu ga Ubangiji. 39 “Ku saƙa zilaika da lallausan zaren lilin. Ku yi rawani da lallausan zaren lilin, ku kuma saƙa abin ɗamara mai ado. 40 “Za a yi wa 'ya'yan Haruna, maza, zilaiku, da abubuwan ɗamara, da huluna don daraja da kwarjini. 41 Ka sa wa Haruna, ɗan'uwanka, da 'ya'yansa maza, sa'an nan ka zuba musu mai, ka keɓe su, ka tsarkake su domin su zama firistoci masu yi mini aiki. 42 Sai kuma ku yi musu mukurai na lilin don su rufe tsiraicinsu daga kwankwaso zuwa cinya. 43 Haruna da 'ya'yansa maza za su sa su sa'ad da suke shiga alfarwa ta sujada ko kuwa sa'ad da suka kusaci bagade domin su yi aiki cikin Wuri Mai Tsarki domin kada su yi laifin da zai zama sanadin mutuwarsu. Wannan zai zama doka ga Haruna da zuriyarsa har abada.”

Fitowa 29

Keɓewar Haruna da 'Ya'yansa Maza

1 “Abin da za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa ke nan don ka keɓe su su zama firistoci masu yi mini aiki. Za ka ɗauki ɗan bijimi da raguna biyu marasa lahani, 2 da abinci marar yisti, da waina wadda aka cuɗe da mai, wadda aka yi da garin alkama mai laushi. 3 Ka sa waɗannan abu cikin kwando, sa'an nan ka kawo su cikin kwandon, ka kuma kawo ɗan bijimin da raguna biyu ɗin. 4 “Ka kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar alfarwar ta sujada, ka yi musu wanka. 5 Sa'an nan ka kawo tufafin, ka sa wa Haruna zilaikar, da taguwar falmaran, da falmaran ɗin, da ƙyallen maƙalawa a ƙirji, sa'an nan ka ɗaura masa ɗamarar falmaran wadda aka yi mata saƙar gwaninta. 6 Za ka naɗa masa rawanin, sa'an nan ka ɗora kambi mai tsarki a bisa rawanin. 7 Ka kuma ɗauki man keɓewa, ka zuba masa a ka domin ka keɓe shi. 8 “Sa'an nan ka kawo 'ya'yansa maza, ka sa musu zilaikun. 9 Ka kuma ɗaura musu ɗamara, ka sa musu hulunan. Aikin firist kuwa zai zama nasu har abada bisa ga dokar. Haka za ka keɓe Haruna da 'ya'yansa maza. 10 “A kuma kawo bijimin a ƙofar alfarwa ta sujada. Haruna da 'ya'yansa maza za su ɗora hannuwansu a kan bijimin. 11 Za ka yanka bijimin a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada. 12 Za ka ɗibi jinin bijimin ka sa a bisa zankayen bagaden da yatsanka. Sauran jinin kuwa ka zuba a gindin bagaden. 13 Ka cire dukan kitsen da yake rufe da kayan cikin, da kitsen da yake manne da hanta, da wanda yake manne a ƙoda biyu ɗin. Ka ƙone su a bisa bagaden. 14 Amma naman bijimin da fatarsa, da tarosonsa, za ka ƙone da wuta a bayan zango, wannan hadaya ce don zunubi. 15 “Sai a kawo rago ɗaya, Haruna kuwa da 'ya'yansa maza su ɗora hannuwansu a bisa ragon. 16 Sa'an nan ka yanka ragon, ka ɗibi jininsa, ka yayyafa shi kewaye a kan bagaden. 17 Ka kuma yanyanka rago gunduwa-gunduwa, ka wanke kayan cikinsa, da ƙafafunsa, ka haɗa su da gunduwoyin, da kan. 18 Sa'an nan ka ƙone ragon duka a bisa bagaden don ya ba da ƙanshi. Wannan hadaya ta ƙonawa ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, wato, hadayar da aka ƙone da wuta. 19 “A kuma kawo ɗayan ragon, Haruna kuma da 'ya'yansa maza su ɗora hannuwansu a bisa ragon. 20 Sa'an nan ka yanka ragon, ka ɗibi jininsa ka shafa bisa leɓatun kunnen Haruna na dama, da bisa leɓatun kunnuwan 'ya'yansa maza na dama, da a kan manyan yatsotsin hannuwansu na dama, da kuma a kan manyan yatsotsin ƙafafunsu na dama. Sauran jinin kuwa, sai ka yayyafa shi a kewaye a kan bagaden. 21 Ka ɗiba daga cikin jinin da yake bisa bagaden, da man keɓewa, ka yayyafa wa Haruna da tufafinsa, da bisa 'ya'yansa maza, da tufafinsu don a tsarkake Haruna, da 'ya'yansa maza, da tufafinsu. 22 “Sai ka ɗebe kitsen ragon, ka yanke wutsiyarsa mai kitse, ka kuma ɗebe kitsen da yake rufe da kayan ciki, da dunƙulen kitsen da yake a bisa hanta, da ƙoda biyu ɗin da kitsensu, da cinyar dama, gama ragon na keɓewa ne. 23 Daga cikin kwandon abinci marar yisti da yake a gaban Ubangiji, sai ka ɗauki malmala ɗaya, da waina ɗaya da aka yi da mai, da ƙosai ɗaya. 24 Za ka sa waɗannan duka a hannun Haruna da na 'ya'yansa maza. Sai su kaɗa su domin hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. 25 Sa'an nan za ka karɓe su daga hannunsu, ka ƙone su a bisa bagaden kamar hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Ita hadaya ce ta ƙonawa da wuta ga Ubangiji. 26 “Za ka ɗauki ƙirjin ragon da aka yanka don keɓewar Haruna, ka kaɗa shi don hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. Wannan ƙirji zai zama rabonka. 27 Za ka tsarkake ƙirji na hadaya ta kaɗawa, da cinya ta hadaya ta ɗagawa da za a kaɗa a kuma ɗaga na ragon keɓewa, wanda yake na Haruna da wanda yake na 'ya'yansa maza. 28 Wannan zai zama rabon Haruna da na 'ya'yansa maza daga wurin Isra'ilawa. Gama wannan hadaya ta ɗagawa ce daga cikin hadayu na salama da Isra'ilawa za su miƙa wa Ubangiji. 29 “Keɓaɓɓun tufafin nan na Haruna za su zama na 'ya'yansa maza bayan rasuwarsa. Da tufafin nan ne za a zuba musu mai, a keɓe su. 30 Ɗan da ya gāje shi a matsayin firist shi ne zai sa su har kwana bakwai, lokacin da ya shiga alfarwa ta sujada, domin ya yi aiki a Wuri Mai Tsarki. 31 “Sai ka ɗauki naman ragon keɓewa, ka dafa shi a wuri mai tsarki. 32 Haruna da 'ya'yansa maza za su ci naman da abinci da yake a cikin kwandon a ƙofar alfarwa ta sujada. 33 Za su ci abubuwan nan da aka yi kafara da su a lokacin tsarkakewarsu da keɓewarsu. Ba wanda zai ci, sai su kaɗai, gama abubuwan nan tsarkaka ne. 34 Amma idan naman keɓewar ko abincin ya ragu har safiya, sai ka ƙone abin da ya ragu, kada a ci, gama tsattsarka ne. 35 “Haka nan za ka yi wa Haruna da 'ya'yansa maza bisa ga dukan abin da na umarce ka. Kwana bakwai za ka ɗauka domin keɓewarsu. 36 A kowace rana za ka miƙa bijimi na hadaya domin zunubi ta yin kafara. Za ka tsarkake bagaden lokacin da ka yi kafara dominsa. Ka zuba masa mai, ka keɓe shi. 37 Kwana bakwai za ka ɗauka na yin kafara don bagaden, ka keɓe shi, haka kuwa bagaden zai zama mafi tsarki. Duk abin da ya taɓa bagaden zai tsarkaka.”

Hadayu na Yau da Kullum

38 “Wannan shi ne abin da za a miƙa a bisa bagaden kullum, 'yan raguna biyu bana ɗaya ɗaya. 39 Za a miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya kuma da maraice. 40 Haɗe da rago na fari, za a miƙa mudun gari mai laushi garwaye da rubu'in moɗa na tataccen mai, da rubu'in moɗa na ruwan inabi domin hadaya ta sha. 41 Ɗaya ragon kuma a miƙa shi da maraice. Za a miƙa shi tare da hadaya ta gari, da hadaya ta sha kamar wadda aka yi da safe ɗin domin ta ba da ƙanshi mai daɗi, gama hadaya ce wadda aka ƙone da wuta ga Ubangiji. 42 Wannan hadaya ta ƙonawa za a riƙa yinta dukan zamananku a bakin ƙofar alfarwa ta sujada a gaban Ubangiji, inda ni zan sadu da kai in yi magana da kai. 43 Nan ne zan sadu da Isra'ilawa in tsarkake wurin da ɗaukakata. 44 Zan tsarkake alfarwa ta sujada da bagaden, zan kuma tsarkake Haruna da 'ya'yansa maza don su zama firistoci masu yi mini aiki. 45 Zan zauna tare da Isra'ilawa, in zama Allahnsu. 46 Za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu wanda ya fisshe su daga Masar don in zauna tare da su. Ni ne Ubangiji Allahnsu.”

Fitowa 30

Bagaden Ƙona Turare

1 “Za ku yi bagaden ƙona turare. Za ku yi shi da itacen ƙirya. 2 Tsawonsa da fāɗinsa kamu guda guda ne, zai zama murabba'i, amma tsayinsa ya zama kamu biyu. Za a haɗa zankayensa su zama ɗaya da shi. 3 Za ku dalaye shi, da bisansa, da gyaffansa, da zankayensa da zinariya tsantsa. Ku kuma yi masa dajiyar zinariya. 4 Za ku yi masa ƙawanya biyu na zinariya a ƙarƙashin dajiyar gefe da gefe, daura da juna. Ƙawanen za su zama inda za a zura sandunan ɗaukarsa. 5 Za ku yi sandunan da itacen ƙirya, ku dalaye su da zinariya. 6 Sai ku ajiye bagaden a gaban labulen akwatin alkawari da murfin akwati inda zan sadu da kai. 7 Haruna kuwa zai ƙona turare mai ƙanshi a bisansa kowace safiya lokacin da yake gyarta fitilun. 8 Zai kuma ƙona turaren sa'ad da ya kunna fitilun da almuru. Za a riƙa ƙona turare kullum a gaban Ubangiji dukan zamananku. 9 Ba za a ƙona wani irin turare dabam ba a bisansa, ba kuma za a miƙa hadaya ta ƙonawa, ko ta gari, ko ta sha, a bisansa ba. 10 Sau ɗaya a shekara Haruna zai yi kafara a bisa zankayensa. Zai yi kafara a bisansa da jinin hadaya don zunubi ta yin kafara. Za a riƙa yin wannan dukan zamananku, gama bagaden mai tsarki ne ga Ubangiji.”

Kuɗin Haikali

11 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, 12 “A sa'ad da za ku ƙidaya Isra'ilawa, sai ko wannensu ya biya fansar kansa ga Ubangiji domin kada annoba ta buge su lokacin da za ku ƙidaya su. 13 Dukan wanda aka lasafta shi cikin ƙidayar kuwa zai biya kuɗi bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. Tilas kowanne ya biya wannan, gama sadaka ce ga Ubangiji. 14 Duk wanda aka lasafta shi cikin ƙidayar tun daga mai shekara ashirin ko fi, zai ba da wannan sadaka ga Ubangiji. 15 Lokacin da kuke ba da wannan sadaka ga Ubangiji saboda kafarar rayukanku, mai samu ba zai zarce ba, matalauci kuma ba zai ba da abin da ya gaza abin da aka ƙayyade ba. 16 Za ku karɓi kuɗin nan na kafara daga wurin Isra'ilawa, ku ajiye shi domin aiki a alfarwa ta sujada. Zai zama abin tunawa ga Isra'ilawa a gaban Ubangiji, don su yi kafarar kansu.”

Daron Tagulla na Wanke Hannu

17 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, 18 “Sai ku yi daro da tagulla don wanka. Ku yi masa gammo da tagulla, ku ajiye shi tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, ku zuba ruwa a ciki. 19 A wurin ne Haruna da 'ya'yansa maza za su wanke hannuwansu da ƙafafunsu. 20 Sa'ad da suke shiga cikin alfarwa ta sujada ko sa'ad da suke kusatar bagade don su miƙa hadaya ta ƙonawa da wuta ga Ubangiji, sai su yi wanka don kada a kashe su. 21 Su wanke hannuwansu da ƙafafunsu don kada su mutu. Yin wannan zai zama musu da zuriyarsu farilla dukan zamanansu.”

Man Keɓewa da Turare

22 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 23 “Ɗauki kayan yaji masu kyan gaske, ruwan mur na shekel ɗari biyar, da kirfa mai daɗin ƙanshi na shekel ɗari biyu da hamsin, da turaren wuta mai ƙanshi na shekel ɗari biyu da hamsin, 24 da kashiya na shekel ɗari biyar bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi, da moɗa ɗaya na man zaitun. 25 Da waɗannan za ku yi man keɓewa mai tsarki yadda mai yin turare yake yi, zai zama man keɓewa mai tsarki. 26 Za a shafa wa alfarwa ta sujada da akwatin alkawari wannan mai. 27 A kuma shafa wa teburin da kayayyakinsa, da alkukin da kayayyakinsa, da bagaden ƙona turare, 28 da bagaden hadaya ta ƙonawa da kayayyakinsa, da daron da gammonsa. 29 Ta haka za a tsarkake su domin su zama masu tsarki sosai. Duk abin da ya taɓa su zai tsarkaka. 30 Za ka zuba wa Haruna da ya'yansa maza mai, ka keɓe su domin su zama firistocina masu yi mini aiki. 31 Sai ka faɗa wa Isra'ilawa cewa, ‘Wannan mai, mai tsarki ne a gare ni domin keɓewa a dukan zamananku. 32 Ba za a shafa wa kowa ba, ba kuma za a yi wani mai irinsa ba, gama man tsattsarka ne, saboda haka zai kasance tsattsarka a gare ku. 33 Duk wanda ya yi wani irinsa ko kuwa ya shafa wa wani, za a raba shi da jama'arsa.’ ” 34 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ɗauki kayan yaji masu ƙanshi, su stakte, da onika, da galbanum tare da lubban. Su zama daidai wa daida. 35 Da waɗannan za a yi turare yadda mai yin turare yake yi, a sa masa gishiri, ya zama tsabtatacce, tsarkakakke. 36 A ɗauki kaɗan daga ciki, a niƙa, sa'an nan a ɗiba daga ciki, a ajiye a gaban akwatin alkawari a cikin alfarwa ta sujada a inda zan sadu da kai. Wannan turare zai zama muku mafi tsarki. 37 Irin turaren nan da za ku yi, ba za ku yi wa kanku irinsa ba. Zai zama abu mai tsarki a gare ku, gama na Ubangiji ne. 38 Duk wanda ya yi irin turaren nan don amfanin kansa, za a raba shi da jama'arsa.”

Fitowa 31

Waɗanda za su Yi alfarwa ta Sujada

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 2 “Ga shi, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza. 3 Na cika shi da Ruhuna, da hikima, da basira, da ilimi, da fasaha, 4 don ya yi fasalin abubuwa na zinariya, da azurfa, da tagulla, 5 da yankan duwatsu masu tamani na jerawa, da sassaƙa itace, da kowane irin aikin fasaha. 6 Ga shi kuma, ni da kaina, na sa Oholiyab ɗan Ahisamak na kabilar Dan tare da shi, na kuma sa hikima a zukatan masu hikima, don su yi dukan abin da na umarce ka 7 a kan alfarwar ta sujada da akwatin alkawari, da murfin da yake bisansa, da dukan kayayyakin da suke cikin alfarwar, 8 da teburin da kayayyakinsa, da alkuki na zinariya tsantsa tare da dukan kayayyakinsa, da bagaden ƙona turare, 9 da bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayayyakinsa, da daron da gammonsa, 10 da saƙaƙƙun tufafi, wato, da tsarkakakkun tufafin Haruna da na 'ya'yansa maza domin aikin firistoci, 11 da man keɓewa, da turaren nan mai ƙanshi domin Wuri Mai Tsarki. Za su yi su duka kamar yadda na umarce ka.”

Ranar Hutawa

12 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 13 “Faɗa wa Isra'ilawa, ‘Sai ku kiyaye Asabar domin shaida tsakanina da ku da zuriyarku har abada, domin ku sani ni ne Ubangiji wanda yakeɓe ku. 14 Ku kiyaye ranar Asabar gama tsattsarkar rana ce a gare ku. Duk wanda ya tozarta ta, za a kashe shi, duk wanda ya yi aiki kuma a cikinta za a raba shi da jama'arsa. 15 A kwana shida za a yi aiki, amma rana ta bakwai ranar hutawa ce tsattsarka ta saduda ga Ubangiji, don haka duk wanda ya yi kowane irin aiki a cikinta za a kashe shi. 16 Domin wannan fa Isra'ilawa za su kiyaye ranar Asabar, su kiyaye ta dukan zamanansu, gama madawwamin alkawari ne. 17 Ranar za ta zama dawwamammiyar shaida tsakanina da Isra'ilawa, cewa, a kwana shida ni Ubangiji na yi sama da ƙasa, amma a rana ta bakwai na ajiye aiki, na huta.’ ” 18 Sa'ad da ya gama magana da Musa a kan Dutsen Sina'i, sai ya ba shi alluna biyu na shaida, allunan duwatsu rubatattu da yatsan Allah.

Fitowa 32

Ɗan Maraƙin Zinariya

1 Da mutane suka ga Musa ya yi jinkirin saukowa daga dutsen, sai suka taru wurin Haruna, suka ce masa, “Tashi, ka yi mana allahn da zai shugabance mu, gama ba mu san abin da ya faru da Musa ɗin wanda ya fisshe mu daga ƙasar Masar ba.” 2 Haruna ya ce musu, “Ku tuttuɓe zobban zinariya waɗanda suke kunnuwan matanku, da na 'ya'yanku maza da mata, ku kawo mini.” 3 Sai jama'a duka suka tuttuɓe zobban zinariya da suke a kunnuwansu, suka kawo wa Haruna. 4 Ya karɓi zobban a hannunsu, sai ya narkar da su, ya sassaƙa shi da kurfi, ya siffata ɗan maraƙi. Da jama'a suka gani, sai suka ce, “Allahnku ke nan, ya Isra'ila, wanda ya fisshe ku daga Masar.” 5 Sa'ad da Haruna ya gani, ya gina bagade a gaban siffar maraƙin, ya yi shela, ya ce, “Gobe akwai idi ga Ubangiji.” 6 Kashegari da sassafe, suka tashi, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama. Jama'ar kuma suka zauna su ci su sha, suka kuma tashi suna rawa. 7 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Sauka, gama jama'arka da ka fito da su daga ƙasar Masar sun ƙazantar da kansu. 8 Sun yi saurin kaucewa daga hanyar da na umarce su. Sun yi wa kansu ɗan maraƙi na zubi, sun yi masa sujada, sun miƙa masa hadaya, sun kuma ce, ‘Ya Isra'ila, wannan shi ne allahn da ya fisshe ka daga ƙasar Masar.’ ” 9 Ya kuma ce wa Musa, “Na ga jama'ar nan suna da taurinkai. 10 Yanzu dai, ka bar ni kawai fushina ya yi ƙuna a kansu, ya cinye su, amma kai zan maishe ka babbar al'umma.” 11 Amma Musa ya roƙi Ubangiji Allahnsa, ya ce, “Ya Ubangiji, me ya sa ka husata da mutanenka waɗanda ka fisshe su da ƙarfin ikonka mai girma daga ƙasar Masar? 12 Don me za ka sa Masarawa su ce, ‘Ai, don ƙeta ce ya fitar da su, don ya kashe su cikin duwatsu, ya shafe su sarai daga duniya?’ Ka janye zafin fushinka, kada kuma ka jawo wa jama'arka masifa. 13 Ka tuna da bayinka Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, waɗanda kai da kanka ka rantse musu, ka ce, ‘Zan riɓaɓɓanya zuriyarku kamar taurarin sama, in kuma ba ku wannan ƙasa duka da na alkawarta zan bayar ga zuriyarku. Za su kuwa gāje ta har abada.’ ” 14 Ubangiji kuwa ya huce, ya janye niyyarsa ta jawo masifa a kan jama'arsa. 15 Musa ya sauko daga kan dutsen da allunan dutsen nan biyu na shaida a hannunsa. Allunan rubutattu ne ciki da baya. 16 Allunan kuwa aikin Allah ne, rubutun kuma na Allah ne da ya zāna a kan allunan. 17 A sa'ad da Joshuwa ya ji hayaniyar jama'ar, sai ya ce wa Musa, “Akwai hargowar yaƙi a zangon.” 18 Musa kuwa ya ce, “Ai, wannan ba hargowar nasara ba ce, ba kuma ta waɗanda yaƙi ya ci ba ce, amma hayaniyar waƙa nake ji.” 19 Yana kusato zango, sai ya ga siffar ɗan maraƙi, mutane na ta rawa. Musa kuwa ya harzuƙa, ya watsar da allunan da suke hannunsa a gindin dutsen, suka farfashe. 20 Ya ɗauki siffar ɗan maraƙin da suka yi, ya ƙone ta, ya niƙe, ta zama gari, ya barbaɗa a ruwa, ya sa Isra'ilawa su sha. 21 Musa ya ce wa Haruna, “Me waɗannan mutane suka yi maka, da ka jawo musu babban zunubi?” 22 Haruna kuwa ya amsa, ya ce, “Ya shugabana, kada ka ji haushina, ka san jama'ar nan sarai da irin halinsu na son aikata mugunta. 23 Sun ce mini, ‘Yi mana allahn da zai shugabance mu, gama Musa, mutumin da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya same shi ba.’ 24 Ni kuwa sai na ce musu, ‘Bari duk wanda yake da zinariya ya tuɓe.’ Waɗanda suke da ita, suka tuɓe, suka kawo mini, ni kuwa na zuba su cikin wuta, daga nan wannan maraƙi ya fito.” 25 Musa ya ga jama'ar sun sangarce, domin Haruna ya sa su sangarce, ya bar su su bauta wa gunki har suka zama abin kunya a gaban magabtansu. 26 Musa ya tsaya a ƙofar zango, ya ce, “Duk wanda yake wajen Ubangiji ya zo wurina.” Sai Lawiyawa suka tattaru a wurinsa. 27 Ya ce musu, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Kowane mutum ya rataya takobinsa, ya kai ya kawo daga ƙofa zuwa ƙofa cikin zango duka, kowa ya kashe ɗan'uwansa, kowa ya kashe zumunsa, kowa ya kashe maƙwabcinsa.’ ” 28 Lawiyawa kuwa suka yi yadda Musa ya faɗa. A ranan nan aka kashe mutum wajen talata (3,000 ). 29 Sai Musa ya ce, “Yau kun ba da kanku ga Ubangiji, gama kowane mutum ya kashe ɗansa da ɗan'uwansa, ta haka kuka jawo wa kanku albarka yau.” 30 Kashegari, Musa ya ce wa mutane, “Kun aikata babban zunubi. Yanzu kuwa zan tafi wurin Ubangiji, watakila zan iya yin kafara domin zunubanku.” 31 Musa ya koma wurin Ubangiji, ya ce, “Kaito, mutanen nan sun aikata zunubi mai girma, sun yi wa kansu gunkin zinariya. 32 Amma ina roƙonka ka gafarta zunubansu, in kuwa ba haka ba, ina roƙonka ka shafe sunana daga cikin littafin da ka rubuta.” 33 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Ai, dukan wanda ya yi mini zunubi, shi ne zan shafe sunansa daga cikin littafina. 34 Yanzu fa, sai ka tafi, ka bi da mutanen zuwa wurin da zan faɗa maka, ga shi, mala'ikana zai wuce gabanka. Duk da haka a ranar da zan waiwaye ku, zan hukunta su saboda zunubinsu.” 35 Sai Ubangiji ya aika wa mutanen da annoba saboda ɗan maraƙin da suka sa Haruna ya yi musu.

Fitowa 33

An Ba da Umarni a Kama Tafiya

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Tashi, ka kama hanya, kai da jama'ar da ka fisshe su daga ƙasar Masar, zuwa ƙasar da na rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, na ce, ‘Ga zuriyarka zan ba da ita.’ 2 Zan kuwa aiki mala'ika a gabanka. Zan kuma kori Kan'aniyawa da Amoriyawa, da Hittiyawa, da Farizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. 3 Ka kama hanya zuwa ƙasa mai yalwar abinci, amma fa ba zan tafi tare da ku ba, gama ku mutane ne masu taurin kai, domin kada in hallaka ku a hanya.” 4 Da jama'ar suka ji wannan mugun labari, sai suka yi nadama. Ba wanda ya sa kayan ado. 5 Gama Ubangiji ya ce wa Musa, “Faɗa wa Isra'ilawa, ‘Ku mutane ne masu taurin kai. In na yi tafiya tare da ku, nan da nan zan hallaka ku. Domin haka fa, yanzu, ku tuɓe kayan adonku, domin in san abin da zan yi da ku.’ ” 6 Domin haka Isra'ilawa suka tuɓe kayan adonsu tun daga dutsen Horeb har zuwa gaba.

Alfarwa ta Sujada

7 Musa ya ɗauki alfarwa, ya kafa ta a bayan zango, nesa da zango. Ya kuwa sa mata suna, Alfarwa ta Sujada. Duk wanda yake neman Ubangiji, sai ya tafi alfarwa ta sujada, wanda yake a bayan zango. 8 Duk sa'ad da Musa ya tafi wurin alfarwar, jama'a duka sukan tashi tsaye, kowa ya tsaya a ƙofar alfarwarsa, ya kallaci Musa, har ya shiga alfarwar. 9 Sa'ad da Musa ya shiga alfarwar, al'amudin girgije ya sauko ya tsaya bisa ƙofar alfarwar, Ubangiji kuma ya yi magana da Musa. 10 A sa'ad da jama'a suka ga al'amudin girgijen nan na tsaye a ƙofar alfarwar, sai jama'ar duka su tashi su yi sujada, kowa a ƙofar alfarwarsa. 11 Ta haka Ubangiji ya riƙa yin magana da Musa baki da baki, kamar yadda mutum yakan yi magana da amininsa. Sa'ad da Musa ya koma cikin zango kuma, baransa, Joshuwa, ɗan Num, saurayi, ba zai fita daga cikin alfarwar ba.

Alkawarin Zatin Ubangiji

12 Musa ya ce wa Ubangiji, “Ga shi, ka faɗa mini cewa, ‘Ka fito da mutanen nan,’ amma ba ka sanar da ni wanda zai tafi tare da ni ba. Ga shi kuma, ka ce, ‘Na san ka, na san sunanka, ka kuma sami tagomashi a gare ni.’ 13 Yanzu ina roƙonka idan na sami tagomashi a gare ka, ka nuna mini hanyoyinka domin in san ka, in kuma sami tagomashi a wurinka, ka kuma tuna, wannan al'umma jama'arka ce.” 14 Ubangiji kuwa ya ce, “Zan tafi tare da kai, zan kuma hutashe ka.” 15 Musa kuwa ya ce masa, “In ba za ka tafi tare da mu ba, to, kada ka ɗaga mu daga nan. 16 Yaya zan sani ko na sami tagomashi a wurinka, ni da jama'arka, in ba ka tafi tare da mu ba? Yaya ni da jama'arka, za a bambanta mu da sauran jama'ar da suke a duniya?” 17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Zan yi yadda ka ce, gama ka sami tagomashi a wurina, na san ka, na kuma san sunanka.” 18 Musa kuwa ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini kanka.” 19 Sai Ubangiji ya ce masa, “Zan wuce a gabanka, Ni Ubangiji zan yi shelar sunana a gabanka, zan kuma yi alheri ga wanda nā yi wa alheri, in nuna jinƙai ga wanda nā yi wa jinƙai.” 20 Ya kuma ce, “Ba za ka iya ganin fuskata ba, gama mutum ba zai gan ni ba, ya rayu.” 21 Ubangiji ya ce, “Ga wani wuri kusa da ni inda za ka tsaya bisa dutsen. 22 A sa'ad da zatina yake wucewa, zan sa ka a tsaguwar dutsen, in rufe ka da hannuna har in wuce, 23 sa'an nan in ɗauke hannuna, za ka kuwa ga bayana, amma ba za ka ga fuskata ba.”

Fitowa 34

Allunan Dutse na Biyu

1 Ubangiji ya ce wa Musa, “Sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farkon, ni kuwa in rubuta kalmomin da suke cikin alluna na farko da ka farfasa. 2 Da safe ka shirya, ka zo Dutsen Sina'i ka gabatar da kanka gare ni a kan dutsen. 3 Kada wani mutum ya zo tare da kai, kada a ga kowane mutum a ko'ina a kan dutsen, kada a bar garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu su yi kiwo kusa da dutsen.” 4 Sai Musa ya sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ya tashi da sassafe, ya hau Dutsen Sina'i, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya riƙe allunan nan biyu na dutse a hannunsa. 5 Ubangiji kuwa ya sauko cikin girgije ya tsaya tare da shi a can, ya yi shelar sunansa. 6 Ya kuma gifta a gaban Musa, ya ce, “Ni ne Ubangiji, Ubangiji Allah mai jinƙai, mai alheri, mai jinkirin fushi, mai yawan ƙauna, mai gaskiya. 7 Ni ne mai nuna ƙauna ga dubbai, mai gafarta mugunta, da laifi, da zunubi, wanda ba zai kuɓutar da mai mugunta ba, amma saboda laifin iyaye nakan hukunta 'ya'ya da jikoki har tsara ta uku da ta huɗu.” 8 Sai Musa ya hanzarta, ya sunkuyar da kansa ƙasa, ya yi sujada. 9 Ya ce, “Idan na sami tagomashi a gare ka, ya Ubangiji, ina roƙonka, ka yi tafiya tare da mu, ko da yake jama'a masu taurinkai ne, ka gafarta laifinmu, da zunubinmu, ka sa mu zama abin gādonka.”

Sabunta Alkawari

10 Allah kuwa ya ce, “Ga shi, na yi alkawari, cewa, a gaban dukan jama'a zan aikata al'ajabai irin waɗanda ba a taɓa aikatawa a duniya ba, ko cikin wata al'umma. Dukan mutanen da kuke zaune tare da su za su ga aikina, gama zan aikata abin bantsoro a cikinku. 11 Ku kiyaye abin da na umarce ku a wannan rana. Ga shi, zan kora muku Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. 12 Ku fa kula da kanku, kada ku kuskura, ku ƙulla alkawari da mazaunan ƙasar inda za ku tafi, don kada su zama muku alƙalai. 13 Sai ku rurrushe bagadansu, ku farfashe al'amudansu, ku sassare gumakansu. 14 “Ba za ku yi wa wani allah sujada ba, sai dai ni, gama sunana Mai Kishi, gama ni Allah mai kishi ne. 15 Kada ku ƙulla alkawari da mazaunan ƙasar don kada sa'ad da suke shagulgulan bidi'arsu ga allolinsu, suna miƙa musu hadaya, waninsu ya gayyace ku ku ci abin hadayarsa. 16 Kada kuma ku auro wa 'ya'yanku maza 'yan matansu 'ya'ya matansu kuma su yi shagulgulan bidi'ar allolinsu, har su sa 'ya'yanku su bi allolinsu. 17 “Kada ku yi wa kanku alloli na zubi. 18 “Sai ku kiyaye idin abinci marar yisti har kwana bakwai a ƙayyadadden lokacinsa a watan Abib, gama a watan Abib kuka fito Masar. A lokacin za ku ci abinci marar yisti kamar yadda na umarce ku. 19 “Kowane ɗan farin mutum, ko na dabba nawa ne, duk da 'ya'yan farin dabbobinku, wato, ɗan farin saniya da na tunkiya. 20 Ɗan farin jaki kuwa za ku fansa da ɗan rago, in kuwa ba za ku fansa da ɗan rago ba, sai ku karya wuyansa. Za ku fanshi kowane ɗan fari. Kada a sami wanda ya zo gabana hannu wofi. 21 “Cikin kwana shida za ku yi aiki, amma a kan rana ta bakwai sai ku huta, ko lokacin noma ne, ko lokacin girbi sai ku huta. 22 “Ku kuma kiyaye idin mako, wato, idin girbin nunan fari na alkama, da idin gama tattara amfanin gonaki a ƙarshen shekara. 23 “Sau uku cikin shekara mazajenku duka za su hallara a gabana, ni Ubangiji Allah na Isra'ila. 24 Gama zan kori al'ummai daga gabanku, in fāɗaɗa kan iyakarku. Ba wanda zai yi ƙyashin ƙasarku a lokatan nan uku na shekara da kukan hallara a gaban Ubangiji Allahnku. 25 “Ba za ku miƙa jinin hadayata tare da abinci mai yisti ba, kada kuma a bar hadaya ta Idin Ƙetarewa ta kwana. 26 “Sai ku kawo nunan farin amfanin gonarku a cikin gidan Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya da madarar uwarsa.” 27 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, “Rubuta waɗannan kalmomi, gama daidai suke da kalmomin alkawarin da yake tsakanina, da kai, da Isra'ila.” 28 Musa kuwa yana tare da Ubangiji yini arba'in da dare arba'in, bai ci ba, bai sha ba. Sai ya rubuta kalmomin alkawarin a kan allunan, wato, dokokin nan goma.

Musa ya Sauko daga Dutsen

29 Sa'ad da Musa ya sauko daga Dutsen Sina'i da alluna biyu na alkawarin a hannunsa, ashe, bai sani ba, amma fuskarsa tana annuri saboda zaman da ya yi a gaban Ubangiji. 30 Sa'ad da Haruna da dukan jama'ar Isra'ila suka ga fuskar Musa tana annuri, suka ji tsoro su kusace shi. 31 Sai Musa ya kirawo Haruna tare da shugabannin jama'ar duka, suka zo wurinsa, shi kuwa ya yi magana da su. 32 Daga nan jama'ar Isra'ila duka suka matsa kusa, Musa kuwa ya ba su dukan dokoki waɗanda Ubangiji ya ba shi a bisa Dutsen Sina'i. 33 Da Musa ya gama magana da su, sai ya lulluɓe fuskarsa. 34 Amma duk lokacin da ya je gaban Ubangiji domin ya yi magana da shi, sai ya kware lulluɓin, har lokacin da ya fito. Idan ya fito, sai ya faɗa wa jama'ar Isra'ila abin da aka umarce shi. 35 Jama'ar Isra'ila kuwa sukan ga fuskar Musa tana annuri. Sa'an nan Musa ya sāke lulluɓe fuskarsa, har lokacin da ya shiga don ya yi magana da Ubangiji.

Fitowa 35

Ka'idodin Ranar Hutawa

1 Sai Musa ya tattara dukan taron jama'ar Isra'ila, ya ce musu, “Waɗannan su ne abubuwan da Ubangiji ya umarce ku ku yi. 2 Cikin kwana shida za a yi aiki, amma rana ta bakwai Asabar ce tsattsarka ta Ubangiji ta hutawa sosai. Duk wanda ya yi kowane irin aiki a cikinta, sai a kashe shi. 3 Ba za ku hura wuta a ranar Asabar a wuraren zamanku ba.”

Sadaka domin Yin Alfarwa ta Sujada

4 Musa kuma ya ce wa taron jama'ar Isra'ila duka, “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta, 5 ku karɓi sadaka daga cikinku saboda Ubangiji. Duk wanda ya yi niyya, bari ya kawo wa Ubangiji sadaka ta zinariya, da azurfa, da tagulla, 6 da zane na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin, da gashin awaki, 7 da fatun raguna da aka rina suka zama ja, da fatun awaki, da itacen ƙirya, 8 da man fitila, da kayan yaji domin man keɓewa da turaren ƙonawa, 9 da duwatsu masu tamani, da duwatsun da za a mammanne a falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji.”

Kayayyakin Alfarwa ta Sujada

10 “Bari dukan wanda yake da fasaha a cikinku ya zo, ya yi aikin da Ubangiji ya umarta a yi, 11 wato, aikin alfarwa ta sujada, da alfarwarta da murfinta, da maratayai, da katakanta da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta, 12 da akwati da sandunansa, da murfinsa, da labulen ƙofar. 13 Da tebur da sandunansa, da kayayyakinsa duka, da gurasar ajiyewa, 14 da alkuki don haske, da kayayyakinsa, da fitilunsa, da man fitila, 15 da bagaden turaren ƙonawa da sandunansa, da man keɓewa mai ƙanshi, da turaren ƙonawa, da labulen ƙofar alfarwa ta sujada, 16 da bagaden ƙona hadaya da ragarsa ta tagulla da sandunansa, da kayayyakinsa duka, da daro da gammonsa, 17 da labulen farfajiya da dirkokinsa da kwasfansu, da labulen ƙofar farfajiyar, 18 da turakun alfarwa, da turakun farfajiyar, da igiyoyinsu, 19 da saƙaƙƙun tufafi na yin aiki a Wuri Mai Tsarki, da tsarkakakkun tufafin Haruna firist, da tufafin 'ya'yansa maza na aikin firist.”

Jama'a sun Kawo Sadaka

20 Sa'an nan dukan taron jama'ar Isra'ila suka tashi daga wurin Musa. 21 Duk wanda ya yi niyya, da wanda ruhunsa ya iza shi ya kawo wa Ubangiji sadaka don yin alfarwa ta sujada, da dukan ayyukansa, da tsarkakakkun tufafi. 22 Sai dukan mata da maza waɗanda suke da niyya, suka kawo kayayyakin ƙawanya, wato, da 'yan kunne, da ƙawane, da mundaye, da kayayyakin zinariya iri iri. Kowane mutum ya ba da sadaka ta zinariya ga Ubangiji. 23 Kowane mutum da aka iske shi yana da shuɗi, ko shunayya, ko mulufi, ko lallausan lilin, ko gashin awaki, ko fatun raguna da aka rina suka zama ja, ko fatun awaki, ya kawo su. 24 Kowane ne wanda ya iya, ya ba da sadaka ta azurfa, da ta tagulla ga Ubangiji. Duka kuma wanda aka iske shi yana da itacen ƙirya wanda zai yi amfani a cikin aikin, ya kawo shi. 25 Dukan mata masu hikima suka kaɗa zare da hannuwansu, suka kawo zaren da suka kaɗa na shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin. 26 Sai kuma dukan mata masu hikima, waɗanda zuciyarsu ta iza su, suka kaɗa zare da gashin awaki. 27 Su shugabanni suka kawo duwatsu masu daraja da za a jera a kan falmaran da ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 28 Suka kuma kawo kayan yaji, da man fitila, da man keɓewa, da turaren ƙonawa. 29 Sai dukan mata da maza na Isra'ilawa waɗanda zuciyarsu ta iza su, suka kawo kowane irin abu domin yin aikin da Ubangiji ya umarci Musa. Suka kawo sadaka ta yardar rai ga Ubangiji.

Waɗanda suka yi Aikin Alfarwa ta Sujada

30 Sai Musa ya ce wa Isra'ilawa, “Ga shi, Ubangiji ya zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza. 31 Ya cika shi da ruhu na hikima, da basira, da sani, da fasaha na iya yin kowane irin aiki. 32 Domin ƙirƙiro zāne-zāne na gwaninta, waɗanda za a yi da zinariya, da azurfa, da tagulla. 33 Haka kuma wajen sassaƙar duwatsu na jerawa, da sassaƙar itace, da kowane irin aiki na gwaninta. 34 Ubangiji ya ba Bezalel, da Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, hikimar koya wa waɗansu sana'a. 35 Gama ya cika su da hikima ta yin kowane irin aiki na sassaƙa da na zāne-zāne, da na yin ɗinke-ɗinke da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin, da na yin saƙa. Sun iya yin kowane irin aiki da yin zāne-zāne.

Fitowa 36

1 “Da Bezalel da Oholiyab, da kowane mutum mai hikima, waɗanda Ubangiji ya ba su hikima da basira na sanin yin kowane irin aiki, za su shirya Wuri Mai Tsarki kamar yadda Ubangiji ya umarta.”

Jama'a sun Kawo Sadaka Mai Yawa

2 Sai Musa ya kirayi Bezalel, da Oholiyab, da kowane mutum mai hikima wanda Ubangiji ya ba shi hikima a zuciya, da duk wanda zuciyarsa ta iza shi ya zo, ya yi aikin. 3 Su kuwa suka karɓa daga wurin Musa dukan sadaka ta yardar rai da Isra'ilawa suka kawo don yin aikin alfarwa ta sujada. Jama'a suka yi ta kawo masa sadaka ta yardar rai kowace safiya. 4 Sai masu hikima da suke yin aiki na alfarwa ta sujada suka ɗan dakatar da aiki suka tafi wurin Musa. 5 Suka ce masa, “Jama'a suna ta kawo sadaka fiye da abin da ake bukata domin aikin da Ubangiji ya umarta a yi.” 6 Sai Musa ya umarce su su yi shela a zango cewa, “Kada wata mace ko wani namiji ya sāke kawo sadaka don aikin alfarwa ta sujada.” Sai jama'a suka daina kawowa. 7 Gama abin da aka kawo ya isa yin aikin, har da ragi.

Yin Alfarwa ta Sujada

8 Sai dukan mutane masu gwaninta daga cikin ma'aikatan, suka yi alfarwa da labule goma. An yi labulen da lallausan zaren lilin na shuɗi, da shunayya, da mulufi. Aka yi wa labulen zānen kerubobi na gwaninta. 9 Tsawon kowane labule kamu ashirin da takwas, fāɗinsa kuma kamu huɗu ne. Dukan labulen girmansu ɗaya ne. 10 Ya ɗinɗinke labule biyar a harhaɗe, haka kuma ya yi da sauran labule biyar. 11 Sai ya sa shuɗɗan hantuna a karbun labule na fari da na biyu. 12 Ya sa hantuna hamsin a karbun labule na fari, haka kuma ya sa na biyun. Dukan hantunan suna daura da juna. 13 Ya kuma yi maɗauri hamsin na zinariya, ya harhaɗa labule da juna da maɗauran domin alfarwa ta zama ɗaya. 14 Ya kuma yi labule goma sha ɗaya da gashin awaki domin ya rufe alfarwa. 15 Tsawon kowane labule kamu talatin, fāɗinsa kuma kamu huɗu ne. Labule goma sha ɗayan nan girmansu ɗaya ne. 16 Ya harhaɗa labule biyar wuri ɗaya, shida kuma ya harhaɗa su wuri ɗaya. 17 Sai ya yi hantuna hamsin, ya sa a karbu na bisa na labule na farin, haka kuma ya sa hantuna hamsin a karbun sama na labule na biyu. 18 Ya kuma yi maɗaurai da tagulla waɗanda zai harhaɗa hantuna da su don alfarwa ta zama ɗaya. 19 Ya yi wa alfarwa murfi da fatun raguna da aka rina ja, ya kuma yi wani abin rufewa da fatuna da aka jeme. 20 Ya kuma yi katakan alfarwa da itacen ƙirya. 21 Tsawon kowane katako kamu goma ne, kaurinsa kuma kamu ɗaya da rabi ne. 22 Kowane katako an fiƙe bakinsa biyu don a harhaɗa su tare, haka ya yi da dukan katakan alfarwa. 23 Yadda ya yi da katakan alfarwa ke nan, ya kafa katakai ashirin a fuskar kudu. 24 Sai ya yi kwasfa arba'in da azurfa domin katakai ashirin. Kowane katako yana da kwasfa biyu saboda bakinsa biyu da aka fiƙe. 25 A fuska ta biyu ta wajen arewa ta alfarwa, ya kafa katakai ashirin. 26 Ya kuma yi kwasfa arba'in na azurfa. Kowane katako yana da kwasfa biyu. 27 Ya yi katakai shida a bayan alfarwa a fuskar yamma. 28 Ya kuma yi katakai biyu don kusurwar baya ta alfarwa. 29 Aka haɗa katakai daga ƙasa har zuwa sama inda aka haɗa su a ƙawanya ta fari, haka ya yi da su a kusurwoyin nan biyu. 30 Akwai katako takwas da kwasfansu na azurfa guda goma sha shida. Kowane katako yana da kwasfa biyu. 31 Sai ya yi sanduna na itacen ƙirya, sanduna biyar domin katakan gefe ɗaya na alfarwa, 32 sanduna biyar kuma domin katakan ɗaya gefen na alfarwa, biyar kuma domin katakan da yake baya na alfarwa wajen yamma. 33 Ya sa sandan da yake a tsakiya ya wuce daga wannan gefe zuwa wancan gefe. 34 Ya dalaye katakai da zinariya. Ya yi musu ƙawane na zinariya inda za a sarƙafa sandunan. Ya kuma dalaye sandunan da zinariya. 35 Ya kuma yi labule da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin, ya kuma yi wa labulen zānen kerubobi na gwaninta. 36 Ya yi wa labulen dirkoki huɗu da itacen ƙirya. Sai ya dalaye su da zinariya. Ya kuma yi musu maratayai da zinariya. Ya yi wa dirkokin nan kwasfa huɗu da azurfa. 37 Ya yi wa ƙofar alfarwa labulen da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan zaren lilin. Ya yi wa labulen ado. 38 Ya haɗa labulen da dirkokinsa biyar, da maratayansu. Ya dalaye kawunansu da maɗauransu da zinariya, amma ya dalaye kwasfansu guda biyar da tagulla.

Fitowa 37

Yin Akwatin Alkawari

1 Bezalel ya yi akwati da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kamu ɗaya da rabi, tsayinsa kamu ɗaya da rabi. 2 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa ciki da waje, ya kuma yi masa dajiya da zinariya kewaye da shi. 3 Ya sa masa ƙawanya huɗu na zinariya a kan kusurwoyinsa huɗu, ƙawane biyu a wannan gefe, biyu kuma a wancan gefe. 4 Ya kuma yi sandunan da itacen ƙirya, ya dalaye su da zinariya. 5 Sai ya zura sandunan cikin ƙawanen da ke a gyaffan akwatin don ɗaukarsa. 6 Ya yi murfin da zinariya tsantsa, tsawonsa kamu biyu da rabi, fāɗinsa kuma kamu ɗaya da rabi. 7 Ya kuma ƙera siffofin kerubobi biyu da zinariya, ya maƙala su a gefe biyu na murfin. 8 Kerub ɗaya a wannan gefe, ɗaya kuma a wancan gefe. Ya yi su a haɗe da murfin a gefe biyu na murfin. 9 Kerubobin suka buɗe fikafikansu sama, suka inuwantar da murfin da fikafikansu. Fuskokinsu kuma na duban juna, suna kuma fuskantar murfin.

Yin Tebur

10 Sai kuma ya yi tebur da itacen ƙirya, tsawsonsa kamu biyu, fāɗinsa kamu ɗaya, tsayinsa kamu ɗaya da rabi. 11 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, ya yi masa dajiya da zinariya. 12 Ya yi masa dajiya mai fāɗin tafin hannu kewaye da shi, ya kuma yi wata dajiya da zinariya kewaye da ita. 13 Ya yi wa tebur ɗin ƙawane huɗu na zinariya, ya manna ƙawane a kusurwoyi huɗu na ƙafafunsa. 14 Ƙawanen suna kusa da dajiyar inda za a zura sanduna na ɗaukar teburin. 15 Ya yi sanduna da itacen ƙirya don ɗaukar teburin. Sa'an nan ya dalaye su da zinariya. 16 Ya yi kayan teburin da zinariya tsantsa, wato, farantansa, da kwanonin tuya, da kwanoninsa, da butoci domin yin hadaya ta sha.

Yin Alkuki

17 Ya yi alkuki da zinariya tsantsa. An yi gindinsa da gorar jikinsa da ƙerarriyar zinariya. Ƙoƙunan alkukin da mahaɗansa, da furanninsa, a haɗe aka yi su da alkukin. 18 Akwai rassan fitila guda shida, uku a wannan gefe, uku kuma a wancan. 19 A kowane reshe na alkukin akwai ƙoƙuna uku masu kamar tohon almond, akwai kuma mahaɗai da furanni. 20 A bisa alkukin kuma akwai ƙoƙuna guda huɗu da aka yi su kamar tohon almond, da mahaɗai, da furanni. 21 Akwai mahaɗi kuma a ƙarƙashin kowane reshe biyu biyu na dukan rassan guda shida, a miƙe daga alkukin. 22 An ƙera mahaɗai da rassan alkuki a haɗe. Da ƙerarriyar zinariya aka yi alkukin da dukan kome nasa a haɗe. 23 Da zinariya tsantsa ya yi fitilu bakwai, da hantsuka da farantansa. 24 Da zinariya tsantsa na talanti ɗaya ya yi alkukin da kayayyakinsa duka.

Yin Bagaden Ƙona Turare

25 Ya yi bagaden ƙona turare da itacen ƙirya, tsawonsa kamu ɗaya, fāɗinsa kamu ɗaya, shi murabba'i ne, tsayinsa kuma kamu biyu ne, zankayensa kuwa a haɗe suke da shi. 26 Ya dalaye shi da zinariya tsantsa, da bisansa, da kewayen gyaffansa, da zankayensa. Ya kewaye shi kuma da dajiya ta zinariya. 27 Ya sa masa ƙawane biyu na zinariya a gyaffansa a ƙarkashin dajiya daura da juna don a zura sandunan ɗaukarsa. 28 Ya kuma yi sanduna biyu da itacen ƙirya, sa'an nan ya dalaye su da zinariya.

Yin Man Keɓewa da Turare

29 Ya yi tsattsarkan mai na keɓewa da kuma turare mai ƙanshi yadda mai yin turare yakan yi.

Fitowa 38

Bagaden Ƙona Hadaya

1 Ya kuma yi bagaden ƙona hadaya da itacen ƙirya, tsawonsa kamu biyar, fāɗinsa kamu biyar, murabba'i ke nan, tsayinsa kuwa kamu uku. 2 Ya yi masa zankaye a kusurwoyinsa huɗu. Zankayen a haɗe suke da shi. Ya dalaye bagaden da tagulla. 3 Da tagulla ya yi duk kayayyakin bagaden, da kwanoni, da babban cokali, da daruna, da cokula masu yatsotsi, da farantan wuta. 4 Ya yi wa bagaden raga da tagulla, ya sa ta a tsakiya. 5 Ya sa ƙawane huɗu a kusurwoyi huɗu na ragar tagulla don zura sanduna. 6 Ya kuma yi sanduna da itacen ƙirya, ya dalaye su da tagulla. 7 Sai ya zura sandunan cikin ƙawane na gyaffan bagaden don ɗaukarsa. Ya yi bagaden da itace sa'an nan ya robe cikinsa.

Yin Daron Wanka

8 Ya yi daron wanka da tagulla, da gammonsa na tagulla, daga madubai na mata masu yin aiki a ƙofar alfarwa ta sujada.

Farfajiyar Alfarwa ta Sujada

9 Ya kuma yi farfajiya. Ya yi labulenta na gefen kudu da lallausan zaren lilin, tsawonsu kamu ɗari ne. 10 Da tagulla aka yi dirkokinsa ashirin, da kwasfan dirkoki guda ashirin, amma da azurfa aka yi maratayan dirkoki da maɗaurai. 11 Tsawon labule na wajen gefen arewa kamu ɗari ne. An yi dirkokinsa guda ashirin da kwasfansu ashirin da tagulla, amma an yi maratayan dirkoki da maɗaurai da azurfa. 12 Labule na gefen yamma kamu hamsin ne, dirkokinsa kuwa guda goma ne, da kwasfansu guda goma. An yi maratayan dirkoki, da maɗaurai da azurfa. 13 Tsawon gefen gabas kamu hamsin ne. 14 Labule na gefe ɗaya na ƙofar, kamu goma sha biyar ne, da dirkokinsu guda uku da kwasfan dirkoki guda uku. 15 Akwai kuma labule mai kamu goma sha biyar a gefe biyu na ƙofar farfajiyar. Labulen yana da dirkoki guda uku da kwasfan dirkoki guda uku. 16 Duk labulen da yake kewaye da farfajiya an yi shi da lallausan zaren lilin. 17 An yi kwasfan dirkoki duka da tagulla, amma maratayan dirkoki da maɗauransu an yi su da azurfa. An dalaye kawunansu da azurfa. Dirkokin farfajiya duka suna da maɗaurai na azurfa. 18 An yi wa labulen ƙofar farfajiya ado na ɗinki da na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin. Tsawonsa kamu ashirin, tsayinsa kamu biyar daidai da labulen farfajiya. 19 An yi dirkokin labulen guda huɗu, da kwasfan dirkoki guda huɗu da tagulla, amma da azurfa aka yi maratayan dirkokin. An dalaye kawunansu da maɗauransu da azurfa. 20 An yi turakun alfarwa ta sujada da na farfajiya duka da tagulla.

Ƙarafan da aka yi Amfani da Su

21 Wannan shi ne lissafin abubuwan da aka yi alfarwa ta sujada da su, yadda aka lasafta bisa ga umarnin Musa domin aikin Lawiyawa a ƙarƙashin jagorar Itamar, ɗan Haruna firist. 22 Sai Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuza, ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa. 23 Tare da shi kuma ga Oholiyab ɗan Ahisamak na kabilar Dan, gwani ne cikin aikin zāne-zāne, da ɗinki na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan zaren lilin. 24 Dukan zinariya da aka yi aikace-aikacen da ita na alfarwa ta sujada sadaka ce talanti ashirin da tara ne da shekel ɗari bakwai da talatin bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 25 Azurfar da aka samu daga ƙidayar taron jama'a talanti ɗari ne, da shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai da saba'in da biyar (1,775 ) bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 26 Kowane mutum da aka ƙidaya ya ba da rabin shekel. Duk mai shekara ashirin ko fi an ƙidaya shi, aka sami maza dubu ɗari shida da dubu uku da ɗari biyar da hamsin (603,550 ). 27 An mori azurfa talanti ɗari don yin kwasfa na alfarwa, da kwasfa na labule. An yi kwasfa ɗari da azurfa talanti ɗari, wato, kwasfa ɗaya talanti ɗaya ke nan. 28 An yi maratayan dirkoki da azurfa shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai da saba'in da biyar (1,775 ), sa'an nan an dalaye kawunansu, an kuma yi musu maɗaurai. 29 Tagullar da aka bayar kuwa, talanti saba'in da shekel dubu biyu da ɗari huɗu (2,400 ). 30 Da tagullar ce ya yi kwasfan ƙofar alfarwa ta sujada, da bagade, da ragarsa, da dukan kayayyakin bagaden. 31 Da tagullar kuma aka yi kwasfan farfajiya, da kwasfan ƙofar farfajiya, da dukan turakun alfarwar da na farfajiyar.

Fitowa 39

Yin Tufafin Firistoci

1 An yi wa firistoci tufafi masu kyau na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, domin yin aiki a Wuri Mai Tsarki. Suka yi wa Haruna tsarkakan tufafi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 2 Ya yi falmaran da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin. 3 An kuma buga zinariya fake-fake, suka yanyanka ta zare-zare don su yi saƙa da ita tare da zane na shuɗi, da na shunayya, da na mulufi, da na lallausan lilin, aikin gwani mai fasaha. 4 Suka yi wa falmaran kafaɗu, sa'an nan suka haɗa su a gefenta biyu na sama. 5 Gwanin masaƙi ya saƙa abin ɗamarar falmaran. Da irin kayan da aka saƙa falmaran ne aka saƙa abin ɗamarar, wato, da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da zaren lallausan lilin kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 6 Sai aka gyaggyarta duwatsu masu daraja aka jera su cikin tsaiko na zinariya. Aka zana sunayen 'ya'yan Isra'ila a kan duwatsun kamar yadda akan yi hatimi. 7 Aka sa su a kan kafaɗun falmaran don su zama duwatsun tunawa da Isra'ila kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 8 Aka kuma yi ƙyallen maƙalawa a ƙirji da gwaninta kamar yadda aka yi wa falmaran aiki da zinariya, da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin. 9 Ƙyallen maƙalawa a ƙirji murabba'i ne, aka ninka shi biyu, tsawonsa da fāɗinsa kamu ɗaya ɗaya ne. 10 Sai suka sa jeri huɗu na duwatsu masu daraja a bisansa. A jeri na fari aka sa yakutu, da tofaz, da zumurrudu. 11 A jeri na biyu aka sa turkos, da saffir, da daimon. 12 A jeri na uku aka sa yakinta, da idon mage, da ametis. 13 A jeri na huɗu aka sa beril, da onis, da yasfa. Aka sa su cikin tsaiko na zinariya. 14 An zana sunayen 'ya'yan Isra'ila goma sha biyu a kan duwatsu masu daraja kamar yadda akan yi hatimi. 15 Sai suka yi tukakkun sarƙoƙi na zinariya tsantsa a kan ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 16 Suka yi tsaiko biyu na zinariya da ƙawane biyu na zinariya. Sai suka sa ƙawanen nan biyu a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 17 Suka kuma zura sarƙoƙin nan biyu na zinariya a ƙawanen nan biyu na zinariya na gyaffan ƙyallen maƙalawa a ƙirji. 18 Sai suka maƙala waɗancan bakin sarƙoƙin zinariya a tsaikon nan biyu, sa'an nan suka rataya su a kafaɗun falmaran daga gaba. 19 Suka kuma yi ƙawane biyu na zinariya, suka sa su a gefe biyu na ƙyallen maƙalawa a ƙirji daga ciki kusa da falmaran. 20 Suka yi waɗansu ƙawane biyu na zinariya, suka maƙala su daga ƙasa a gaban kafaɗu biyu na falmaran kusa da mahaɗin a bisa abin ɗamarar falmaran. 21 Sai suka ɗaure ƙawanen ƙyallen maƙalawa a ƙirjin a ƙawanen falmaran da shuɗiyar igiya don ƙyallen maƙalawa a ƙirji ya kwanta lif a bisa kan abin ɗamarar falmaran don kada ya kwance daga falmaran, sun yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 22 Ya kuma saƙa taguwa ta falmaran da shuɗi duka. 23 An yi wa taguwar wuyan wundi kamar sulke, aka daje wuyan don kada ya kece. 24 A karbun taguwar, suka yi fasalin 'ya'yan rumman da shuɗi, da shunayya, da mulufi, da lallausan lilin. 25 Suka kuma yi ƙararrawa da zinariya tsantsa, suka sa su a tsakankanin fasalin 'ya'yan rumman kewaye da karbun taguwa. 26 An jera su bi da bi, wato, fasalin rumman yana biye da ƙararrawa. Haka aka jera su kewaye da karbun taguwar yin aiki, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 27 Suka saƙa zilaika da lallausan zaren lilin don Haruna da 'ya'yansa. 28 Suka kuma yi rawani, da huluna, da mukurai da lallausan lilin. 29 Sun kuma yi abin ɗamara da lallausan lilin mai launin shuɗi, da shunayya, da mulufi. Aka yi mata ɗinkin ado kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 30 Suka yi allo tsattsarka da zinariya tsantsa suka zāna rubutu irin na hatimi a kansa haka, “MAI TSARKI GA UBANGIJI.” 31 Suka ɗaura shi da shuɗiyar igiya a gaban rawanin kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Ƙarewar Aikin

32 Haka kuwa aka gama dukan aiki na alfarwa ta sujada. Isra'ilawa suka yi shi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 33 Sai suka kawo wa Musa alfarwa da dukan kayayyakinta, wato, da maratayanta, da katakanta, da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta, 34 da murfi na fatun raguna da na awaki, da labulen, 35 da akwatin alkawari da sandunansa, da murfinsa, 36 da tebur, da kayayyakinsa duka, da gurasar ajiyewa, 37 da alkuki na zinariya tsantsa da fitilunsa da dukan kayayyakinsa, da man fitila, 38 da bagade na zinariya, da man keɓewa, da turare mai ƙanshi, da labulen ƙofar alfarwar, 39 da bagade na tagulla da ragarsa ta tagulla, da sandunansa da dukan kayayyakinsa, da daro da gammonsa, 40 da labulen farfajiya da dirkokinta, da kwasfanta, da labulen ƙofarta, da igiyoyinta, da turakunta, da dukan kayayyakin yin aiki a alfarwa ta sujada, 41 da tufafin ado na aiki a Wuri Mai Tsarki, wato, tsarkakan tufafin Haruna firist, da tufafin 'ya'yansa maza don su yi aikin firistoci. 42 Isra'ilawa sun yi dukan aiki kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 43 Da Musa ya duba dukan aikin, ga shi kuwa, sun yi shi daidai, kamar yadda Ubangiji ya umarta, sai Musa ya sa musu albarka.

Fitowa 40

Kafawar Alfarwa ta Sujada da Keɓewarta

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, 2 “A kan rana ta fari ga wata na fari za ka kafa alfarwa ta sujada. 3 Sai ka sa akwatin alkawari a cikinta sa'an nan ka kāre shi da labule. 4 Ka shigar da tebur ɗin, ka shirya kayayyakinsa daidai. Ka kuma shigar da alkukin, ka sa fitilu a bisansa. 5 Ka ajiye bagade na zinariya na ƙona turare a gaban akwatin alkawari, sa'an nan ka rataya labulen ƙofar alfarwa. 6 Ka ajiye bagade na yin hadaya ta ƙonawa a gaban ƙofar alfarwa ta sujada, 7 ka kuma ajiye daro tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, sa'an nan ka zuba ruwa a ciki. 8 Sai ka yi farfajiya ka kewaye wurin sa'an nan ka rataya labulen ƙofar farfajiyar. 9 “Ka ɗauki man keɓewa, ka shafa wa alfarwa da dukan abin da yake cikinta, domin ka tsarkake ta da kayayyakinta duka, za ta kuwa zama tsarkakakkiya. 10 Ka shafa wa bagade na ƙona hadaya da kayayyakinsa duka man domin ka tsarkake shi, bagaden kuma zai zama mafi tsarki. 11 Ka kuma shafa wa daron da gammonsa man keɓewa, da haka za ka tsarkake shi. 12 “Ka kuma kawo Haruna da 'ya'yansa maza a ƙofar alfarwa ta sujada, ka yi musu wanka da ruwa. 13 Sa'an nan ka sa wa Haruna tufafi tsarkaka ka shafa masa man domin ka tsarkake shi ya yi mini aiki na firist. 14 Sai ka kawo 'ya'yan Haruna maza, ka kuma sa musu taguwoyi. 15 Sa'an nan ka shafa musu mai kamar yadda ka shafa wa mahaifinsu domin su yi mini aiki a matsayin firistoci. Shafa musu man zai sa su zama firistoci din din din dukan zamanansu.” 16 Haka kuwa Musa ya yi dukan abin da Ubangiji ya umarce shi. 17 A rana ta fari ga wata na fari a shekara ta biyu, aka kafa alfarwa. 18 Sai musa ya kafa alfarwa, ya kafa kwasfanta, ya jera katakanta, ya sa mata sandunanta, ya kakkafa dirkokinta. 19 Sa'an nan ya shimfiɗa murfi a bisa alfarwa ya rufe alfarwar kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 20 Sai ya ɗauki dokoki goma ɗin, ya sa a akwatin, ya kuma zura sandunan a ƙawanen akwatin, sa'an nan ya sa murfin a bisansa. 21 Ya kawo akwatin a cikin alfarwa, sa'an nan ya sa labulen don kāre akwatin alkawari, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 22 Musa ya sa teburin cikin alfarwa ta sujada, a wajen gefen arewa na alfarwa, a gaban labulen. 23 Sa'an nan ya jera gurasa daki-daki a bisa teburin a gaban Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 24 Ya kuma sa alkukin a cikin alfarwa ta sujada daura da teburin a wajen gefen kudu na alfarwa. 25 Ya kunna fitilun a gaban Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 26 Ya kuma sa bagade na zinariya a cikin alfarwa ta sujada daga gaban labulen. 27 Sai ya ƙona turare mai ƙanshi a bisansa kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 28 Ya sa labule a ƙofar alfarwa. 29 Ya kuma sa bagade na ƙona hadaya a ƙofar alfarwa ta sujada, sa'an nan ya miƙa hadaya ta ƙonawa da ta gari kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 30 Ya kuma sa daro a tsakanin alfarwa ta sujada da bagaden, sa'an nan ya zuba ruwa a ciki don wanka. 31 A cikinsa Musa da Haruna da 'ya'yansa maza sukan wanke hannuwansu da ƙafafunsu, 32 sa'ad da suke shiga cikin alfarwa ta sujada, da sa'ad da sukan kusaci bagaden kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 33 Ya kuma yi farfajiya kewaye da alfarwa da bagaden, ya sa labulen ƙofar farfajiyar. Da haka Musa ya gama aikin.

Saukowar Girgije a bisa Alfarwa ta Sujada

34 Sa'an nan girgije ya rufe alfarwa ta sujada, ɗaukakar Ubangiji kuma ta cika alfarwa. 35 Musa kuwa bai iya shiga alfarwa ta sujada ba domin girgijen yana zaune a bisanta, ɗaukakar Ubangiji kuma ta cika alfarwa. 36 Cikin tafiyar Isra'ilawa duka, sukan kama tafiyarsu ne a duk sa'ad da girgijen ya tashi daga kan alfarwa. 37 Idan girgijen bai tashi ba, su kuma ba za su tashi ba, sai a ranar da ya tashi. 38 Gama a cikin tafiyarsu duka, girgijen Ubangiji yana kan alfarwa da rana, da dare kuwa wuta ke cikinsa domin dukan Isra'ilawa su gani.

Littafin Firistoci 1

Hadaya ta Ƙonawa

1 Ubangiji ya kirawo Musa, ya yi masa magana daga cikin alfarwa ta sujada, ya ce 2 ya ba Isra'ilawa ka'idodin nan. Sa'ad da kowane mutum a cikinsu zai kawo sadaka ga Ubangiji, sai ya kawo sadakarsa daga cikin garkunansa na shanu, da na tumaki, da na awaki. 3 Idan sadakarsa ta hadayar ƙonawa ce daga cikin garken shanu, sai ya ba da namiji marar lahani, zai miƙa shi a ƙofar alfarwa ta sujada domin sadakar ta zama abar karɓa a gaban Ubangiji. 4 Sai ya ɗibiya hannunsa a kan kan hadaya ta ƙonawar, za a karɓa masa, a kuwa yi masa gafara. 5 Sa'an nan zai yanka ɗan bijimin a gaban Ubangiji. 'Ya'yan Haruna maza, firistoci, za su miƙa jinin a bagaden da yake a ƙofar alfarwa ta sujada za su kuma yayyafa jinin a kewaye da shi. 6 Sai mai hadayar ya feɗe dabbar, ya yanyanka ta gunduwa-gunduwa. 7 Sa'an nan 'ya'yan Haruna maza, firistoci, za su hura wuta a bisa bagaden, su jera itace daidai a wutar. 8 Su ɗibiya gunduwoyin, da kan, da kitsen bisa itacen da yake cikin wutar da take a kan bagaden. 9 Amma mai hadayar zai wanke kayan ciki da ƙafafu da ruwa, sa'an nan firist ya ƙone duka a kan bagaden, hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 10 Idan hadayarsa ta ƙonawa daga cikin garken tumaki ko kuwa na awaki ne, sai ya ba da namiji marar lahani. 11 Zai yanka shi a arewacin bagaden a gaban Ubangiji. 'Ya'yan Haruna, firistoci, za su yayyafa jinin a kewaye da bagaden. 12 Mai hadayar kuma zai yanyanka shi gunduwa-gunduwa, da kansa, da kitsensa. Firist zai jera su a bisa itacen da yake cikin wutar da take a bagaden. 13 Amma mai hadayar zai wanke kayan ciki da ƙafafu da ruwa, sa'an nan firist ya miƙa duka, ya ƙone a bisa bagaden, gama hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 14 Idan kuma hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji daga cikin tsuntsaye ne, sai ya kawo kurciyoyi, ko 'yan tattabarai. 15 Firist ɗin zai kawo tsuntsun a bagaden, ya murɗe wuyan tsuntsun, sa'an nan ya ƙone kan a bisa bagaden. Za a tsiyaye jini a gefen bagaden. 16 Amma zai ɗauki kururun da gashin ya zubar da su a gefen bagaden a wajen gabas a wurin zuba toka. 17 Zai tsaga shi biyu a tsaka, amma ba zai raba shi ba. Firist ɗin zai ɗibiya shi a bisa itacen da yake bisa bagaden, ya ƙone shi, gama hadaya ta ƙonawa ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

Littafin Firistoci 2

Hadaya ta Gari

1 A sa'ad da mutum ya kawo hadaya ta gari ga Ubangiji, sai ya kawo gari mai laushi, ya zuba masa mai da lubban. 2 Zai kuma kawo hadayarsa a wurin 'ya'yan Haruna maza, firistoci. Zai ɗibi tāfi guda na lallausan garin da aka zuba wa mai da dukan lubban. Firist kuwa zai ƙona wannan a kan bagaden don tunawa, gama hadaya ta ƙonawa ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 3 Ragowar garin hadayar kuwa, zai zama na Haruna da 'ya'yansa maza, gama hadaya ce ta ƙonawa mafi tsarki ga Ubangiji. 4 Sa'ad da aka kawo hadaya ta gari da aka toya cikin tanda, sai a yi shi da gari mai laushi marar yisti kwaɓaɓɓe da mai, a shafa masa mai, a toya, ko kuwa a soya ƙosai. 5 Idan kuwa hadayar ta gari ce da aka toya cikin kaskon tuya, sai a yi abinci da gari mai laushi wanda ba a sa masa yisti ba, wanda aka kwaɓa da mai. 6 Za a gutsuttsura shi, a zuba masa mai, hadayar gari ke nan. 7 Idan kuma hadayar ta gari ce wadda aka dafa cikin tukunya, ita kuma, sai a yi ta da gari mai laushi da mai. 8 Za a kawo hadaya ta gari da aka yi da abubuwan nan ga Ubangiji. Sa'ad da aka kai wa firist, sai ya kawo ta a bagaden. 9 Firist zai ɗauki kashi na tunawa daga hadaya ta garin, ya ƙona shi bisa bagaden, hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 10 Ragowar hadayar garin zai zama na Haruna da 'ya'yansa maza, gama hadayar ƙonawa ce mafi tsarki ga Ubangiji. 11 A kowace hadaya ta gari da za a kawo wa Ubangiji, ba za a sa yisti ba, gama ba za a yi hadayar ƙonawa ga Ubangiji da yisti, ko da zuma ba. 12 Amma a iya kawo su kamar hadayar nunan fari ga Ubangiji, sai dai ba za a ƙona su a kan bagade ba, kamar hadaya ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi. 13 Sai a sa gishiri a kowace hadaya ta gari, kada a rasa sa gishirin alkawarin Allah a hadaya ta gari. A sa gishiri a dukan hadayu. 14 Idan za a yi hadaya ta gari daga cikin nunan fari ga Ubangiji, sai a miƙa hadaya ta nunan fari da ɗanyen hatsi wanda aka gasa aka ɓarza. 15 Za a zuba masa mai, a barbaɗa masa lubban, gama hadaya ce ta gari. 16 Firist kuwa zai ƙone wani kashi daga cikin ɓarzajjen hatsin a gauraye da man, da dukan lubban don tunawa, gama hadaya ce ta ƙonawa ga Ubangiji.

Littafin Firistoci 3

Hadaya ta Salama

1 Idan mutum zai kawo hadayarsa ta salama daga garken shanu, sai ya kawo mace ko namiji marar lahani ga Ubangiji. 2 Zai ɗibiya hannunsa a kan kan hadayarsa, ya yanka a bakin ƙofar alfarwa ta sujada. 'Ya'yan Haruna maza kuwa, firistoci, za su yayyafa wa bagaden jinin kewaye da shi. 3 Daga hadaya ta salama sai a miƙa waɗannan hadayu na ƙonawa ga Ubangiji, wato, kitsen da yake rufe da kayan ciki, da wanda yake bisana, 4 da ƙoda biyu, da kitsen da yake bisansu a wajen kwiɓi, da matsarmamar da zai cire tare ƙodojin. 5 'Ya'yan Haruna, maza kuwa, za su ƙone su tare da hadayar ƙonawa da take bisa itacen da yake cikin wutar bagade, hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 6 Idan kuwa hadayarsa ta salama ga Ubangiji daga garken tumaki, ko na awaki ce, sai ya ba da dabbar, mace ko namiji, marar lahani. 7 Idan ɗan rago ne ya bayar don hadaya, sai ya miƙa shi a gaban Ubangiji. 8 Zai ɗibiya hannunsa a kan kan hadayarsa, ya yanka a gaban alfarwa ta sujada. 'Ya'yan Haruna, maza kuwa, za su yayyafa wa bagaden jinin kewaye da shi. 9 Daga cikin hadaya ta salama sai a miƙa waɗannan hadayu na ƙonawa ga Ubangiji, wato, kitsensa da wutsiyarsa duka mai kitse. Zai yanke ta gab da ƙashin gadon baya, da kitsen da ya rufe kayan ciki kuwa, da wanda yake bisansa, 10 da ƙoda biyu, da kitsen da yake bisansu a wajen kwiɓi, da matsarmamar da zai cire tare da ƙodojin. 11 Firist kuwa zai ƙone su a bisa bagaden kamar hadayar abincin da akan ƙone da wuta ga Ubangiji. 12 Idan ya kawo akuya don hadayarsa, sai ya miƙa ta a gaban Ubangiji. 13 Zai ɗibiya hannunsa a bisa kanta, ya yanka ta a gaban alfarwa ta sujada. 'Ya'yan Haruna, maza, za su yayyafa wa bagaden jinin kewaye da shi. 14 Sa'an nan mai hadayar zai ba da kitsen da yake rufe da kayan cikin, da wanda yake bisansa, 15 da ƙodoji biyu, da kitsen da yake bisansu wajen kwiɓi, da matsarmama don a miƙa su hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. 16 Firist kuwa zai ƙone su a bisa bagaden kamar hadayar abincin da akan ƙone don ya yi ƙanshi mai daɗi. Dukan kitse na Ubangiji ne. 17 Ba za a ci kitse ko jinin ba a wuraren zamanku. Wannan doka madawwamiya ce.

Littafin Firistoci 4

Hadayu domin Zunubi

1 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, 2 ya faɗa wa mutanen Isra'ila, in wani ya yi zunubi, ba da gangan ba, har ya karya ɗaya daga cikin dokokin Ubangiji, sai ya bi ka'idodin nan. 3 Idan keɓaɓɓen firist ne ya yi zunubi, ya jawo wa jama'a laifi, sai ya ba da ɗan bijimi marar lahani ga Ubangiji don yin hadaya saboda zunubin da ya aikata. 4 Zai kawo ɗan bijimin a ƙofar alfarwa ta sujada a gaban Ubangiji, ya ɗibiya hannunsa a kan kan bijimin, ya yanka shi a gaban Ubangiji. 5 Shi kuma keɓaɓɓen firist ɗin ya ɗibi jinin bijimin ya kai shi a alfarwa ta sujada. 6 Ya tsoma yatsansa cikin jinin, ya yayyafa jinin sau bakwai a gaban Ubangiji a wajen labulen Wuri Mai Tsarki. 7 Zai kuma ɗiba daga cikin jinin, ya sa a bisa zankayen bagaden ƙona turaren da suke cikin alfarwar a gaban Ubangiji. Sauran jinin bijimin kuwa zai zuba shi a gindin bagaden ƙona hadaya wanda yake a ƙofar alfarwa ta sujada. 8 Zai ɗebe dukan kitsen ɗan bijimi na yin hadaya don zunubi, da kitsen da yake rufe da kayan cikin, da wanda yake bisansa, 9 da ƙodoji biyu da kitsen da yake bisansu wajen kwiɓi, da matsarmama. 10 Zai cire su daidai kamar yadda akan cire na bijimin hadaya ta salama. Sai firist ɗin ya ƙone su a kan bagaden ƙona hadaya. 11 Amma fatar ɗan bijimin, da namansa, da kansa, da ƙafafunsa, da kayan cikinsa, da tarosonsa, 12 da sauran bijimin duka zai kai su waje bayan zango a wuri mai tsabta inda ake zubar da toka, nan zai ƙone su da wuta a inda ake zubar da tokar. 13 Idan taron jama'ar Isra'ila sun yi zunubi, ba da gangan ba, har sun aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, amma ba su farga da laifinsu ba, duk da haka sun yi laifi. 14 Amma sa'ad da zunubin da suka aikata ya sanu, taron jama'a za su ba da ɗan bijimi na yin hadaya don zunubi. Za a kawo shi a gaban alfarwa ta sujada. 15 Sai dattawan jama'a su ɗibiya hannunsu a kan kan bijimin a gaban Ubangiji, sa'an nan a yanka bijimin a gaban Ubangiji. 16 Sai keɓaɓɓen firist ya ɗibi jinin bijimin, ya kai cikin alfarwa ta sujada. 17 Sa'an nan ya tsoma yatsansa a cikin jinin ya yayyafa shi sau bakwai a gaban Ubangiji, a gaban labulen. 18 Sai ya ɗiba daga cikin jinin ya shafa wa zankayen bagaden da suke cikin alfarwa ta sujada a gaban Ubangiji, sauran jinin kuwa sai ya zuba a gindin bagaden ƙona hadaya wanda yake a ƙofar alfarwa ta sujada. 19 Zai kwashe kitsensa duka, ya ƙone shi bisa bagaden. 20 Sai ya yi da ɗan bijimin kamar yadda ya yi da ɗan bijimi na hadaya don zunubin firist. Ta haka firist zai yi kafara domin jama'a, za a kuwa gafarta musu. 21 Zai kai bijimin a bayan zango, ya ƙone shi kamar yadda ya yi da na farin, gama hadaya ce don zunubin taron jama'ar. 22 Idan shugaba ya yi zunubi, ba da gangan ba, har ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji Allahnsa ya umarta kada a yi, to, ya yi laifi. 23 Idan aka sanar da shi zunubin da ya yi, sai ya kawo bunsuru marar lahani don yin hadaya. 24 Zai ɗibiya hannunsa a kan kan bunsurun, ya yanka a wurin da ake yanka hadaya ta ƙonawa a gaban Ubangiji, gama hadaya ce don zunubi. 25 Sai firist ya ɗibi jinin hadaya don zunubi da yatsansa ya shafa wa zankayen bagaden ƙona hadaya, sa'an nan ya zuba sauran jinin a gindin bagaden. 26 Firist ɗin zai ƙona kitsen duka a bisa bagaden kamar yadda akan yi da kitsen hadaya ta salama, ta haka firist zai yi kafara domin zunubin shugaban, za a kuwa gafarta masa. 27 In wani daga cikin talakawa ya yi zunubi, ba da gangan ba, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, to, ya yi laifi. 28 Sa'ad da aka sanar da shi zunubin da ya aikata, sai ya kawo akuya marar lahani don yin hadaya saboda zunubinsa. 29 Zai ɗibiya hannunsa a kan kan hadaya don zunubi, ya yanka hadayar a wurin hadaya ta ƙonawa. 30 Firist zai ɗibi jinin da yatsansa ya shafa wa zankayen bagaden ƙona kadaya, sa'an nan ya zuba sauran jinin a gindin bagaden. 31 Za a ɗebe kitsenta duka kamar yadda akan ɗebe kitsen hadaya ta salama. Firist zai ƙona shi a kan bagaden don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Ta haka firist zai yi kafara dominsa, za a kuwa gafarta masa. 32 Idan kuwa daga cikin 'yan tumaki zai ba da hadayarsa, sai ya kawo 'yar tunkiya marar lahani. 33 Zai ɗibiya hannunsa a kan kan abin yin hadaya don zunubin, sa'an nan ya yanka a wurin da akan yanka hadaya ta ƙonawa. 34 Sai firist ya ɗibi jinin abin yin hadaya don zunubi da yatsansa ya shafa wa zankayen bagaden ƙona hadaya, sauran jinin kuwa ya zuba a gindin bagaden. 35 Zai kuma ɗebe kitsenta duka kamar yadda a kan ɗebe na ragon hadaya ta salama. Firist zai ƙone shi a bisa bagaden a bisa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ta haka firist zai yi masa kafara saboda zunubin da ya aikata, za a kuwa gafarta masa.

Littafin Firistoci 5

Hadayu domin Laifi

1 Laifi ne idan mutum ya aikata kowane ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa. Idan mutum ya ji ana shelar neman mai laifi, amma ya ƙi fitowa ya ba da shaida, ko da yake ya gani, ko kuma ya san abin da ya faru, ya yi laifi, alhaki yana kansa. 2 Ko kuma idan mutum ya taɓa kowane abu da yake haram ko mushen haramtacciyar dabba ta jeji ko ta gida, ko mushen haramtaccen abin da yake rarrafe, zai zama da laifi, ko da bai sani ba. 3 Ko kuma idan ya taɓa kowace irin ƙazantar mutum wadda akan ƙazantu da ita, ba da saninsa ba, amma in daga baya ya sani, to, laifi ya kama shi. 4 Ko kuma idan mutum ya yi rantsuwa da garaje da bakinsa, cewa, zai yi mugunta, ko nagarta, ko kowace irin rantsuwa ta garaje da mutane sukan yi, to, laifi ya kama shi bayan da ya gane da rantsuwarsa. 5 In mutum ya aikata ɗaya daga cikin waɗannan laifofi, sai ya hurta laifin da ya yi. 6 Ya kuma kawo hadaya ga Ubangiji don laifin da ya yi. Sai ya kawo 'yar tunkiya ko akuya domin hadaya don zunubi. Firist zai yi kafara don laifin mutumin. 7 Amma idan 'yar tunkiyar ta fi ƙarfinsa, sai ya kawo kurciyoyi biyu ko 'yan tattabarai biyu don yin hadaya ga Ubangiji saboda laifin da ya yi. Ɗaya za ta zama ta yin hadaya don laifi, ɗayan kuwa don yin hadaya ta ƙonawa. 8 Zai kawo su wurin firist. Da fari firist zai miƙa hadaya don laifi. Zai karye wuyanta, amma ba zai tsinke kan ba. 9 Zai yayyafa jinin hadaya don laifi a gefen bagaden, sauran jinin kuwa zai tsiyaye a gindin bagade, gama hadaya ce don laifi. 10 Sa'an nan zai miƙa ta biyun don hadaya ta ƙonawa bisa ga yadda aka ƙayyade. Firist ɗin zai yi kafara saboda laifin da mutumin ya yi, za a kuwa gafarta masa. 11 Amma idan har kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai biyu sun fi ƙarfinsa don yin hadaya saboda laifinsa, sai ya kawo humushin garwar gari mai laushi don yin hadaya saboda laifinsa. Ba zai zuba mai ko lubban a garin ba, gama hadaya ce don laifi. 12 Zai kai wa firist garin, firist zai ɗibi garin cike da tafin hannunsa, wannan shi ne kashi na tunawa. Zai ƙone shi bisa bagaden kamar hadaya na ƙonawa ga Ubangiji, gama hadaya ce don laifi. 13 Ta haka firist zai yi kafara don laifin da mutumin ya aikata daga cikin abubuwan nan, za a kuwa gafarta masa. Sauran garin zai zama na firist kamar yadda yakan zama nasa a hadaya ta gari. 14 Sai Ubangiji ya ba Musa ka'idodin nan. 15 Idan mutum ya ci amana, ya kuwa yi laifi ba da gangan ba, a kan tsarkakakkun abubuwa na Ubangiji, sai ya kawo rago marar lahani daga garken tumaki ga Ubangiji saboda yin hadaya don laifinsa. Za a kimanta ragon da tamanin kuɗi bisa ga ma'aunin azurfar da ake aiki da shi. 16 Zai kuma biya diyya saboda abu mai tsarki da ya yi laifi a kansa. Zai kuma ƙara humushi a kai, sa'an nan ya ba firist. Firist kuwa zai yi kafara dominsa da ragon hadaya don laifi. Za a kuwa gafarta masa. 17 Idan wani ya yi laifi, ya aikata ɗaya daga cikin abubuwan da Ubangiji ya umarta kada a yi, to, laifi ya kama shi ko da bai sani ba. Alhakin laifin yana kansa. 18 Sai ya kai wa firist rago marar lahani daga cikin garke. Za a kimanta tamanin rago daidai da tamanin hadaya don laifi. Firist kuwa zai yi kafara don kuskuren da mutumin ya yi ba da saninsa ba, za a gafarta masa. 19 Hadaya ce don laifi, gama ya yi wa Ubangiji laifi.

Littafin Firistoci 6

1 Ubangiji kuma ya ba Musa ka'idodin nan. 2 Idan wani mutum ya yi laifi na cin amana gāba da Ubangiji, wato, ya yaudari maƙwabcinsa a kan ajiya, ko jingina, ko ƙwace, ko ya zalunce shi, 3 ko ya yi tsintuwa, amma ya yi m�su har ya rantse da ƙarya, duk dai irin abubuwan da akan aikata na laifi, 4 sa'ad da mutum ya yi laifi, ya kuwa tabbata mai laifi ne, sai ya mayar da abin da ya ƙwace, ko abin da ya samu ta hanyar zalunci, ko abin da aka ba shi ajiya, ko abin da ya tsinta, 5 ko kowane abu da ya rantse a kansa da ƙarya. Zai mayar wa mai abin da abinsa a yadda yake, har ya ƙara da humushin tamanin abin. A ranar da zai yi hadaya don laifinsa, a ranar ce zai mayar wa mai abin da abinsa. 6 Zai kuwa kai wa firist rago marar lahani daga garken tumaki don yin hadaya ga Ubangiji saboda laifinsa. Za a kimanta tamanin ragon daidai da tamanin hadaya don laifi. 7 Firist kuwa zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji, za a kuwa gafarta masa irin laifin da ya yi.

Hadayun da za a Ƙone Ƙurmus

8 Ubangiji kuma ya umarci Musa, 9 ya ba Haruna da 'ya'yansa maza ka'idodin hadayu na ƙonawa. Hadaya ta ƙonawa za ta kwana bisa bagaden, wutar bagaden kuma ta kwana tana ci har safe. 10 Firist zai sa rigarsa ta lilin, ya ɗaura mukurunsa na lilin, sa'an nan ya kwashe tokar hadaya ta ƙonawa daga bagaden, ya zuba a gefensa. 11 Firist ɗin kuma zai tuɓe rigunansa, ya sa waɗansu, sa'an nan ya kwashe tokar ya kai bayan zango ya zuba a wani wuri mai tsabta. 12 Sai a bar wutar bagaden ta yi ta ci, kada a kashe ta. Firist ɗin ya yi ta iza wutar kowace safiya, ya shimfiɗa hadaya ta ƙonawa a jere a bisa wutar, ya kuma ƙone kitsen hadaya ta salama a bisanta. 13 Sai wuta ta yi ta ci a bisa bagaden kullum, kada ta mutu.

Hadaya ta Gari

14 Wannan ita ce dokar hadaya ta gari. 'Ya'yan Haruna, maza, za su miƙata a gaban Ubangiji daga gaban bagaden. 15 Ɗaya daga cikinsu zai ɗibi lallausan garin hadayar wanda aka zuba masa mai da lubban cike da tafin hannunsa. Zai ƙona wannan a bisa bagaden, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji don tunawa. 16 Haruna da 'ya'yansa maza za su ci ragowar garin. Za a ci shi ba tare da yisti ba a wuri mai tsarki na farfajiyar alfarwa ta sujada. 17 Ba za a sa masa yisti a toya shi ba. Wannan Ubangiji ne ya ba su ya zama rabonsu daga cikin hadayun da ake ƙonawa da wuta, abu ne mafi tsarki, kamar hadaya don zunubi da laifi. 18 Kowane ɗa namiji cikin 'ya'yan Haruna zai iya ci daga cikin hadayun Ubangiji waɗanda akan yi da wuta. Wannan madawwamiyar doka ce cikin zamananku duka. Duk wanda ya taɓa hadayu zai tsarkaka. 19 Sai Ubangiji ya ba Musa waɗannan ka'idodi, 20 domin keɓe firist, wato, zuriyar Haruna. A ranar da za a keɓe shi zai kawo humushin garwar gari mai laushi (kamar yadda akan kawo na hadaya ta gari), za a miƙa rabinsa da safe, rabin kuma da maraice. 21 Za a shirya shi da mai a kwanon tuya. A kwaɓa shi sosai, a toya shi dunƙule dunƙule kamar hadaya ta gari, sa'an nan a kawo shi a miƙa shi don ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. 22 Wanda aka keɓe daga zuriyar Haruna, shi ne zai miƙa wannan hadaya ga Ubangiji. Za a ƙone ta duka. Wannan farilla ce har abada. 23 Kowace hadaya ta gari ta firist, za a ƙone ta ɗungum, ba za a ci ba.

Hadayu don Zunubi

24 Sai Ubangiji ya umarci Musa 25 ya ba Haruna da 'ya'yansa maza waɗannan ka'idodi domin hadaya don zunubi. A inda ake yanka hadaya ta ƙonawa, a nan ne za a yanka hadaya don zunubi a gaban Ubangiji, hadaya ce mai tsarki. 26 Firist wanda ya miƙa hadaya don zunubi zai ci daga ciki a wuri mai tsarki a cikin farfajiyar alfarwa ta sujada. 27 Duk wanda ya taɓa naman zai tsarkaka, in kuma jinin ya ɗiga a riga, sai a wanke rigar a wuri mai tsarki. 28 Sai a fasa tukunyar ƙasa wadda aka dafa naman a ciki, amma in a cikin tukunyar tagulla aka dafa, sai a kankare ta a ɗauraye da ruwa. 29 Kowane namiji a cikin firistoci zai iya cin naman, gama abu ne mafi tsarki. 30 Amma ba za a ci naman hadaya don zunubi ba wanda aka shigar da jininsa a alfarwa ta sujada domin yin kafara a Wuri Mai Tsarki. Sai a ƙone shi da wuta.

Littafin Firistoci 7

Hadaya don Laifi

1 Waɗannan su ne ka'idodin hadaya don ramuwa, hadaya ce tsattsarka. 2 Za a yanka dabbar hadayar a arewa da bagaden inda akan yanka hadaya don ƙonawa. Sai a yayyafa jinin a kan bagaden da kewayensa. 3 Za a miƙa kitsen abin hadaya duka, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, 4 da ƙodoji biyu da kitsen da yake bisansu wajen kwiɓi, da matsarmama wadda za a cire tare da ƙodojin. 5 Firist zai ƙone su a bisa bagaden, gama hadaya ce da akan ƙone da wuta ga Ubangiji, hadaya ce don laifi. 6 Kowane namiji a cikin firistoci zai iya ci. Sai a wuri mai tsarki za a ci, gama tsattsarkan abu ne. 7 Hadaya don laifi kamar hadaya don zunubi take, saboda haka ka'idar yinsu iri ɗaya ce. Firist wanda ya yi kafarar, zai ɗauki abin da ya ragu. 8 Firist kuma wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ta wani mutum, zai ɗauki fatar abin da aka yi hadayar da shi. 9 Kowace hadaya ta gari da aka toya cikin tanda, da duk wadda aka yi a tukunya ko a kaskon tuya, za su zama na firist wanda ya miƙa hadaya. 10 Kowace hadaya ta gari kuma wadda aka kwaɓa da mai, ko wadda ba a kwaɓa ba, za ta zama rabon 'ya'yan Haruna, maza duka, kowa da kowa.

Hadaya don Zumunta

11 Waɗannan su ne ka'idodin hadaya ta salama wadda za a miƙa wa Ubangiji. 12 Idan domin godiya mutum ya miƙa hadaya, sai ya miƙa ta tare da abinci marar yisti, wadda aka kwaɓa da mai, da wadda aka shafa wa mai, da kuma ƙosai. 13 Tare da hadayarsa ta salama don godiya, sai ya kawo dunƙulen abincin da aka sa masa yisti. 14 Daga cikin wannan zai miƙa waina ɗaya daga kowace hadaya don hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji. Wannan zai zama na firist wanda ya yayyafa jinin hadaya ta salama. 15 Za a ci naman hadayarsa ta salama da aka miƙa don godiya a ranar da aka miƙa ta. Kada a bar naman ya kai safe. 16 Amma idan hadayarsa ta cika wa'adi ce, ko ta yardar rai ce, sai a ci ta a ranar da aka miƙa ta, kashegari kuma a ci abin da ya ragu. 17 Amma idan ba a cinye naman hadayar ba har ya kai kwana uku, kada a ci, sai a ƙone shi da wuta. 18 Idan aka ci naman hadayarsa ta salama a rana ta uku, ba za a karɓi wanda ya ba da hadayar har ya sami fa'idar hadayar ba, naman zai zama abin ƙyama, duk wanda ya ci ya yi laifi. 19 Kada a ci naman da ya taɓa wani abu marar tsarki, sai a ƙone shi da wuta. Duk wanda yake da tsarki zai iya cin nama. 20 Amma wanda ya ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji lokacin da ba shi da tsarki, za a raba shi da mutenensa. 21 Idan wani mutum ya taɓa abu marar tsarki, ko mutum ne, ko dabba ce, ko wani abu na banƙyama, ya kuma ci naman hadaya ta salama ga Ubangiji, za a raba wannan mutum da mutanensa. 22 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 23 ya faɗa wa mutanen Isra'ila cewa, kada su ci kitsen sa, ko na tunkiya, ko na akuya. 24 Kitsen dabbar da ta mutu mushe, da kitsen dabbar da namomin jeji suka yayyaga, za a iya yin wani amfani da shi, amma kada a kuskura a ci. 25 Duk mutumin da ya ci kitsen dabbar da aka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, za a raba shi da mutanensa. 26 Ko kaɗan, ba za a yi abinci da jini ba, ko na tsuntsu, ko na dabba, a inda suke duka. 27 Duk mutumin da ya karya wannan doka za a raba shi da mutanensa. 28 Ubangiji kuma ya ba Musa waɗannan ka'idodi 29 don mutanen Isra'ila, cewa, wanda zai miƙa hadayarsa ta salama ga Ubangiji, sai ya kawo hadayarsa ga Ubangiji daga cikin hadayu na salama. 30 Sai shi kansa ya kawo hadayar da za a ƙona. Zai kawo kitsen da ƙirjin. Za a yi hadaya ta kaɗawa da ƙirjin a gaban Ubangiji. 31 Firist zai ƙone kitsen a bisa bagaden, amma ƙirjin zai zama rabon Haruna da 'ya'yansa maza. 32 Za a ba firist cinya ta dama, don hadaya ta ɗagawa daga cikin hadayu na salama. 33 Cinyar ƙafar dama za ta zama rabon ɗan Haruna wanda ya miƙa jinin da kitsen hadaya ta salama. 34 Gama Ubangiji ya ba Haruna da 'ya'yansa maza, ƙirjin da aka kaɗa da cinyar da aka ɗaga, su zama rabonsu daga cikin hadayu na salama na Isra'ilawa. Ya ba Haruna, firist, da 'ya'yansa maza, su zama rabonsu har abada daga cikin hadayu na Isra'ilawa. 35 Wannan shi ne rabon da aka keɓe wa Haruna da 'ya'yansa maza, daga cikin hadayun da ake yi da wuta ga Ubangiji, tun a ranar da aka keɓe su firistoci na Ubangiji. 36 Ubangiji ya umarci Isra'ilawa su ba firistoci wannan a ranar da aka keɓe su. Wannan hakkinsu ne a dukan zamanansu. 37 Waɗannan su ne ka'idodin hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta gari, da hadaya don zunubi, da hadaya don laifi, da hadaya don keɓewa, da hadaya ta salama. 38 Waɗannan su ne umarnan da Ubangiji ya ba Musa a Dutsen Sina'i, can cikin hamada, a ranar da ya faɗa wa Isra'ilawa su kawo hadayunsu gare shi.

Littafin Firistoci 8

Keɓewar Haruna da 'Ya'yansa Maza

1 Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Ɗauki Haruna da 'ya'yansa maza, da rigunan, da man keɓewa, da bijimi na yin hadaya don zunubi, da raguna biyu, da kwandon abinci marar yisti. 3 Ka kuma tattara jama'a duka a ƙofar alfarwa ta sujada.” 4 Musa kuwa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Jama'ar kuwa suka tattaru a ƙofar alfarwa ta sujada. 5 Musa ya faɗa wa taron jama'ar cewa “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya umarta a yi.” 6 Sai Musa ya fito da Haruna da 'ya'yansa maza, ya yi musu wanka. 7 Ya sa wa Haruna zilaika, ya ɗaura masa ɗamara, ya sa masa taguwa, ya kuma sa masa falmaran, ya ɗaura masa ɗamarar falmaran wadda aka yi mata saƙar gwaninta. 8 Ya maƙala masa ƙyallen maƙalawa a ƙirji, sa'an nan ya sa Urim da Tummin, a kan ƙyallen. 9 Sai ya naɗa masa rawani, daga gaban rawanin ya sa allon zinariya, wato, kambi tsattsarka, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 10 Sai Musa ya ɗauki man keɓewa ya shafa wa alfarwa ta sujada da dukan abin da yake cikinta, da haka ya tsarkake su. 11 Ya yayyafa wa bagaden mai sau bakwai, ya kuma shafa wa bagaden da dukan kayayyakinsa, da daron da gammonsa, don ya tsarkake su. 12 Ya zuba man keɓewa a kan Haruna, ya keɓe shi. 13 Sai Musa kuma ya kawo 'ya'yan Haruna, maza, ya sa musu zilaiku, ya ɗaura musu ɗamaru, ya sa musu huluna kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 14 Sa'an nan ya kawo bijimi na yin hadaya don zunubi, Haruna da 'ya'yansa maza, suka ɗibiya hannuwansu a kan kan bijimin. 15 Sai Musa ya yanka shi, ya ɗibi jinin a yatsansa ya shafa wa zankayen bagaden a kewaye, ya tsarkake bagaden, ya zuba jinin a gindin bagaden, ya keɓe shi don ya yi kafara dominsa. 16 Sai ya ɗauki dukan kitsen da yake bisa kayan ciki da matsarmama, da ƙodoji biyu da kitsensu, ya ƙone su bisa bagaden. 17 Amma ya ƙone naman bijimin da fatarsa da tarosonsa a bayan zangon kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 18 Sa'an nan ya kawo rago na yin hadaya ta ƙonawa. Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan kan ragon. 19 Sai ya yanka ragon, ya yayyafa jinin a bisa bagaden da kewayensa. 20 Da aka yanyanka ragon gunduwa gunduwa, sai Musa ya ƙone kan, da gunduwoyin, da kitsen. 21 Sa'ad da kuma aka wanke kayan ciki da ƙafafu da ruwa, sai ya ƙone ragon duka a bisa bagaden, hadaya ce ta ƙonawa mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 22 Musa ya kawo ɗayan ragon keɓewa, sai Haruna da 'ya'yansa maza suka ɗibiya hannuwansu a kan kan ragon. 23 Musa kuwa ya yanka shi, ya ɗibi jinin, ya sa a leɓatun kunnen dama na Haruna, da bisa babban yatsansa na hannun dama, da babban yatsa na ƙafar dama. 24 Sai aka kawo 'ya'yan Haruna, maza, Musa kuma ya sa jinin a leɓatun kunnensu na dama, da manyan yatsotsi na hannuwansu na dama, da manyan yatsotsin ƙafafu na dama. Sa'an nan ya yayyafa jinin kewaye da bagaden. 25 Ya kuma ɗauki kitsen, da wutsiya mai kitse, da dukan kitsen da yake bisa kayan ciki, da matsarmama da ƙodoji biyu da kitsensu, da cinyar dama. 26 Daga cikin kwandon abinci marar yisti da yake a gaban Ubangiji, ya ɗauki waina guda marar yisti, da waina guda da aka yi da mai, da ƙosai guda. Sai ya ɗibiya su a bisa kitsen da cinyar dama. 27 Ya sa waɗannan abubuwa duka a tafin hannuwan Haruna da na 'ya'yansa maza, ya miƙa abubuwan nan domin hadayar kaɗawa ga Ubangiji. 28 Sa'an nan ya karɓe su daga tafin hannuwansu, ya ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a bisa bagaden don hadayar keɓewa, hadaya ce da aka yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 29 Ya kuma ɗauki ƙirjin, ya kaɗa shi don hadayar kaɗawa ga Ubangiji. Wannan shi ne rabon Musa daga cikin ragon keɓewar, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 30 Sa'an nan Musa ya ɗiba daga cikin man keɓewa da jinin da yake bisa bagaden, ya yayyafa wa Haruna da rigunansa, da 'ya'yansa maza da rigunansu. Da haka ya tsarkake Haruna da rigunansa, da 'ya'yansa maza da rigunansu. 31 Sai Musa ya ce wa Haruna da 'ya'yansa maza, “Ku dafa naman a ƙofar alfarwa ta sujada, ku ci shi a wurin, da abincin da yake a cikin kwandon hadayar keɓewa, kamar yadda Ubangiji ya umarta, cewa, Haruna da 'ya'yansa maza za su ci shi. 32 Sauran abin da ya ragu daga naman da abincin, sai ku ƙone su. 33 Ba za ku fita daga cikin alfarwa ta sujada ba har kwana bakwai, wato, sai kwanakin keɓewarku sun cika, gama keɓewarku za ta ɗauki kwana bakwai. 34 Abin da aka yi a wannan rana haka Ubangiji ya umarta a yi domin kafararku. 35 A ƙofar alfarwa ta sujada za ku zauna dare da rana har kwana bakwai, kuna kiyaye umarnin Ubangiji don kada ku mutu, gama haka Ubangiji ya umarta.” 36 Sai Haruna da 'ya'yansa maza suka yi dukan abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

Littafin Firistoci 9

Haruna ya Miƙa Hadayu

1 A kan rana ta takwas, Musa ya kirawo Haruna, da 'ya'yansa maza, da dattawan Isra'ila. 2 Sai ya ce wa Haruna, “Kawo ɗan maraƙi marar lahani na yin hadaya don zunubi, da rago marar lahani don hadaya ta ƙonawa, ka miƙa su ga Ubangiji. 3 Ka faɗa wa Isra'ilawa su ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi, da ɗan maraƙi bana ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya marasa lahani, don hadaya ta ƙonawa, 4 da bijimi da rago don hadayun salama, a yi hadaya da su ga Ubangiji, da hadaya ta gari da aka kwaɓa da mai, gama yau Ubangiji zai bayyana a gare ku.” 5 Sai suka kawo abin da Musa ya umarce su a gaban alfarwa ta sujada. Dukan taron jama'a suka matso kusa, suka tsaya a gaban Ubangiji. 6 Musa kuma ya ce, “Ubangiji ya umarce ku ku yi dukan wanna, domin ɗaukakar Ubangiji za ta bayyana gare ku.” 7 Sa'an nan Musa ya ce wa Haruna, “Matsa kusa da bagaden, ka miƙa hadayarka don zunubi, da hadayarka ta ƙonawa, ka yi kafara don kanka da kuma don jama'a. Ka kuma kawo hadayar jama'a, ka yi kafara dominsu kamar yadda Ubangiji ya umarta.” 8 Sai Haruna ya matsa kusa da bagaden, ya yanka ɗan maraƙi na yin hadaya don zunubi saboda kansa. 9 'Ya'yansa maza kuma suka miƙa masa jinin, sai ya tsoma yatsansa a cikin jinin, ya shafa a zankayen bagaden, ya kuma zuba jinin a gindin bagaden. 10 Amma kitsen, da ƙadojin, da kitsen da yake rufe da hanta na hadaya don zunubi, ya ƙone su a bisa bagaden kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 11 Naman da fatar kuwa ya ƙone su a bayan zangon. 12 Haruna ya yanka hadaya ta ƙonawa, 'ya'yansa maza kuma suka miƙa masa jinin, sai ya yayyafa a bagaden da kewayensa. 13 Suka kuma miƙa masa hadaya ta ƙonawa gunduwa gunduwa tare da kan, sai ya ƙone su bisa bagaden. 14 Ya kuma wanke kayan ciki, da ƙafafu, sa'an nan ya ƙone su tare da hadaya ta ƙonawa a bisa bagaden. 15 Haruna kuma ya miƙa hadayar jama'a. Ya ɗauki bunsuru na yin hadaya don zunubi jama'ar, ya yanka, ya miƙa shi hadaya don zunubi kamar yadda aka yi da na farin. 16 Ya kuma miƙa hadaya ta ƙonawa, ya yi kamar yadda aka faɗa. 17 Ya kuma kawo hadaya ta gari, ya ɗibi garin cike da tafin hannunsa, ya ƙone shi a bisa bagaden tare da hadaya ta ƙonawa ta safiya. 18 Sai kuma ya yanka bijima da rago don yin hadayun salama domin jama'ar. 'Ya'yansa maza suka miƙa masa jinin, sai ya yayyafa jinin a bisa bagaden da kewayensa. 19 Suka cire kitsen bijimin, da na ragon, da wutsiya mai kitse, da kitsen da yake rufe da kayan ciki, da ƙodoji, da matsarmama. 20 Sai Haruna ya aza kitsen a bisa ƙirjin dabbobin ya ƙone kitsen a bisa bagaden. 21 Amma ya yi hadaya ta kaɗawa da ƙirjin da cinyoyi na dama ga Ubangiji, kamar yadda Musa ya umarta. 22 Sai Haruna ya ta da hannuwansa wajen jama'a, ya sa musu albarka sa'an nan ya sauka daga wurin yin hadaya don zunubi, da hadaya ta ƙonawa, da hadayun salama. 23 Musa da Haruna suka shiga alfarwa ta sujada. Da suka fita, sai suka sa wa jama'a albarka. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta bayyana ga jama'a duka. 24 Wuta kuma ta fito daga wurin Ubangiji, ta ƙone hadaya ta ƙonawa da kitsen a bisa bagaden. Da jama'a duka suka gani, suka yi ihu, suka fāɗi rubda ciki suka yi sujada.

Littafin Firistoci 10

Zunubin Nadab da Abihu

1 'Ya'yan Haruna, maza, Nadab da Abihu kuwa ko wannensu ya ɗauki faranti ya sa wuta, ya zuba turare a kai, ya miƙa haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji, ba irin wadda Ubangiji ya umarta ba. 2 Sai wuta ta fito daga wurin Ubangiji ta kashe su, suka mutu a gaban Ubangiji. 3 Musa kuwa ya ce wa Haruna, “Wannan ita ce ma'anar abin da Ubangiji yake cewa, ‘Dukan waɗanda suke bauta mini, dole su nuna ladabi ga tsarkina, zan kuma bayyana ɗaukakata ga jama'ata.’ ” Haruna kuwa ya yi tsit. 4 Musa ya kirawo Mishayel da Elzafan 'ya'ya maza na Uzziyel, kawun Haruna, ya ce musu, “Ku zo nan, ku ɗauki gawawwakin 'yan'uwanku daga gaban wuri mai tsarki zuwa bayan zango.” 5 Sai suka zo, suka kama rigunan matattun suka ɗauke su zuwa bayan zango kamar yadda Musa ya faɗa.

Nawayar Aikin Firist

6 Musa kuma ya ce wa Haruna, da 'ya'yansa maza, wato, Ele'azara da Itamar, “Kada ku bar gashin kanku barkatai, kada kuma ku kyakketa rigunanku don kada ku mutu, don kada Ubangiji ya yi fushi da taron jama'a duka, amma 'yan'uwanku, wato, dukan Isra'ilawa, suna iya kuka saboda waɗanda Ubangiji ya ƙone. 7 Kada kuwa ku fita daga cikin alfarwa ta sujada don kada ku mutu, gama an shafa muku man keɓewa na Ubangiji.” Sai suka yi yadda Musa ya faɗa.

Dokoki don Firistoci

8 Ubangiji kuma ya yi magana da Haruna ya ce, 9 “Kada kai da 'ya'yanka maza ku sha ruwan inabi, ko abin sha mai ƙarfi sa'ad da za ku shiga alfarwa ta sujada don kada ku mutu. Wannan doka ce a dukan zamananku. 10 Sai ku bambanta tsakanin abu mai tsarki da marar tsarki, da tsakanin abin da yake halal da abin da yake haram. 11 Ku kuma koya wa mutanen Isra'ila dukan dokokin da Ubangiji ya ba su ta hannun Musa.” 12 Musa kuwa ya ce wa Haruna da 'ya'yansa maza, waɗanda suka ragu, wato, Ele'azara da Itamar, “Ku ɗauki ragowar hadaya ta gari wadda aka yi hadaya ta ƙonawa da ita ga Ubangiji, ku ci ba tare da yisti ba a gefen bagaden, gama tsattsarka ne. 13 Za ku ci shi a wuri mai tsarki gama naka rabo ke nan da na 'ya'yanka maza daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji, gama haka Ubangiji ya umarce ni. 14 Amma ƙirjin da aka yi hadayar ta kaɗawa da shi da cinyar da aka miƙa, za ka ci su a kowane tsabtataccen wuri, da kai da 'ya'yanka mata da maza, gama wannan ne rabon da aka ba ku, daga hadayun salama na Isra'ilwa. 15 Za su kawo cinyar hadayar ɗagawa da ƙirjin hadayar kaɗawa tare da kitsen hadayun ƙonawa domin a yi hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. Wannan zai zama rabonka da na 'ya'yanka har abada kamar yadda Ubangiji ya umarta.” 16 Da Musa ya nemi bunsurun hadaya don zunubi sai ya tarar an ƙone shi. Ya kuwa yi fushi da Ele'azara da Itamar, 'ya'yan Haruna, maza, waɗanda suka ragu, ya ce, 17 “Don me ba ku ci hadaya don zunubi a wuri mai tsarki ba, da yake tsattsarkan abu ne wanda aka ba ku domin ku kawar da laifin taron jama'a, domin kuma ku yi kafara dominsu a gaban Ubangiji? 18 Ga shi, ba a shigar da jinin can cikin Wuri Mai Tsarki ba. Ga shi kuwa, ya kamata ku ci kamar yadda na umarta amma ba ku yi ba.” 19 Sai Haruna ya ce wa Musa, “Ga shi, yau suka miƙa hadayarsu don zunubi, da ta ƙonawa a gaban Ubangiji, ga kuma irin waɗannan abubuwa da suka same ni, da a ce na ci hadaya don zunubi yau, da zai yi kyau ke nan a gaban Ubangiji?” 20 Da Musa ya ji wannan, sai ya yi na'am da shi.

Littafin Firistoci 11

Dabbobin da suke Halal da na Haram

1 Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan ka'idodi 2 domin Isra'ilawa. Za ku ci kowace irin dabbar da take a duniya, 3 wadda take da rababben kofato, wadda kuma take yin tuƙa. 4 Ko daga cikin masu tuƙar ko masu rababben kofaton ba za ku ci waɗannan ba. Raƙumi yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato, haram ne a gare ku. 5 Rema tana tuƙa, amma ba ta da rababben kofato, haram ce a gare ku. 6 Zomo yana tuƙa, amma ba shi da rababben kofato, haram ne a gare ku. 7 Alade yana da rababben kofato, amma ba ya tuƙa, haram ne a gare ku. 8 Ba za ku ci namansu ba, ba kuwa za ku taɓa mushensu ba, gama haram ne a gare ku. 9 Kwa iya cin waɗannan abubuwa da suke cikin ruwa, kowane abu da yake da ƙege da kamɓori da yake cikin tekuna ko koguna. 10 Amma kowace irin halittar da take cikin tekuna da koguna da ba ta da ƙege da kamɓori, abar ƙyama ce a gare ku. 11 Namansu kuma zai zama abin ƙyama a gare ku, ba za ku ci ba. Mushensu kuma abin ƙyama ne. 12 Kowane irin abu da yake cikin ruwa da ba shi da ƙege da kamɓori, abin ƙyama ne a gare ku. 13 Za ku ji ƙyamar waɗannan irin tsuntsaye, ba za ku ci su ba, gama abin ƙyama ne su, wato, gaggafa, da mikiya, da ungulun kwakwa, 14 da shirwa, da buga zabi, da irinsu, 15 da kowane irin hankaka, 16 da jimina, da mujiya, da shaho, da irinsu, 17 da ƙururu, da babba da jaka, da zarɓe, 18 da kazar ruwa, da kwasakwasa, da ungulu, 19 da shamuwa, da jinjimi da irinsa, da burtu, da jemage. 20 Dukan ƙwarin da yake da fikafikai ƙazantattu ne, 21 sai dai waɗanda suke da cinyoyin da suke sa su iya tsalle. 22 Za ku iya cin fara, da gyare, da ƙwanso da irinsu. 23 Amma sauran ƙananan ƙwari duka masu fikafikai, suna kuma jan ciki, abin ƙyama ne a gare ku. 24 Duk wanda ya taɓa mushen waɗannan dabbobi, zai ƙazantu har faɗuwar rana. 25 Duk wanda kuma ya ɗauki mushensu dole ne ya wanke tufafinsa, amma zai ƙazantu har zuwa maraice. 26 Kowace dabba wadda ba ta da rababben kofato, ba ta kuma tuƙa, haram ce a gare ku. Duk wanda ya taɓa su zai ƙazantu. 27 Duk abin da yake tafiya a kan daginsa daga cikin dabbobin da suke da ƙafa huɗu, haram ne a gare ku. Duk wanda ya taɓa mushensu zai ƙazantu har zuwa maraice. 28 Wanda kuma ya ɗauki mushensu, sai ya wanke tufafinsa, ya zama ƙazantacce har zuwa maraice. 29 Waɗannan ƙananan dabbobi da suke rarrafe a ƙasa haram ne a gare ku, wato, murɗiya, da ɓera, da gafiya da irinsa, 30 da tsaka, da hawainiya, da ƙadangare, da guza, da damo. 31 Duk wanda ya taɓa su ko ya taɓa mushensu, zai zama ƙazantacce har zuwa maraice. 32 Duk abin da mushensu ya fāɗa a kai zai ƙazantu. Ko a kan itace ne, ko a bisa tufafi, ko a fata, ko a buhu, ko cikin kowane irin abu da ake amfani da shi, to, tilas a sa shi cikin ruwa, zai zama ƙazantacce har zuwa maraice, sa'an nan zai tsarkaka. 33 Idan wani daga cikinsu ya fāɗa cikin kasko, to, kaskon da abin da yake cikinsa za su ƙazantu, sai a fasa kaskon. 34 Kowane irin abinci da yake cikinsa kuma da yake da ruwa a cikinsa, zai haramtu. Kowane irin abin sha da yake cikinsa kuma, zai haramtu. 35 Kowane irin abu da mushensu ya fāɗa a kai, zai haramtu, ko randa ce, ko murhu, sai a farfasa, sun ƙazantu, haram ne a gare ku. 36 Duk da haka maɓuɓɓuga, ko tafkin ruwa ba za su haramtu ba, amma duk wanda ya taɓa mushensu ya ƙazantu. 37 Idan kuma kowane ɓangare na mushen ya fāɗa a kan kowane iri da za a shuka, ba zai haramta shi ba. 38 Amma idan an zuba ruwa a kan irin, mushen kuwa ya fāɗa kan irin, zai haramta a gare ku. 39 Idan kuma wata dabbar da kuke ci ta mutu, wanda duk ya taɓa mushenta zai ƙazantu har zuwa maraice. 40 Wanda kuwa ya ci mushen sai ya wanke tufafinsa, ya ƙazantu har zuwa maraice. Haka kuma shi wanda ya ɗauki mushen zai wanke tufafinsa ya kuma ƙazantu har zuwa maraice. 41 Ba za ku ci ƙananan dabbobin da suke motsi a bisa ƙasa ba, 42 duk waɗanda suke jan ciki, da waɗanda suke da ƙafa huɗu, da waɗanda suke da ƙafafu da yawa. 43 Kada ku ƙazantar da kanku da cin waɗannan abubuwa. 44 Ni ne Ubangiji Allahnku, domin haka dole ku tsarkake kanku, ku tsarkaka, gama ni mai tsarki ne. 45 Ni ne Ubangiji wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku. Sai ku zama tsarkakakku, gama ni mai tsarki ne. 46 Wannan ita ce dokar da ta shafi kowace dabba, da kowane tsuntsu, da kowace irin halitta wadda take tafiya cikin ruwa da kowace irin halitta da take a tudu. 47 Dole ku lura ku bambanta tsakanin masu tsarki, da marasa tsarki, da tsakanin dabbobin da za a ci, da waɗanda ba za a ci ba.

Littafin Firistoci 12

Tsarkakewar Mata bayan Haihuwa

1 Ubangiji ya ba Musa ka'idodin nan domin jama'ar Isra'ila. 2 Idan mace ta yi ciki, ta haifi ɗa namiji, to, za ta zama marar tsarki har kwana bakwai, kamar cikin kwanakin hailarta. 3 A kan rana ta takwas za a yi wa jaririn kaciya. 4 Sa'an nan kuma sai ta ci gaba da zama cikin jinin har kwana talatin da uku. A lokacin ba za ta taɓa kowane tsattsarkan abu ba, ba za ta shiga wurin yin sujada ba, har kwanakin tsarkakewarta su cike. 5 Amma idan 'ya mace ce ta haifa, za ta zama marar tsarki mako biyu kamar a kwanakin hailarta. Za ta ci gaba da zama cikin jinin har kwana sittin da shida. 6 Sa'ad da kwanakin tsarkakewarta na haihuwar ɗa ko 'ya suka cika, sai ta kai wa firist ɗan rago bana ɗaya, a ƙofar alfarwa ta sujada don hadaya ta ƙonawa, da ɗan tattabara, ko kurciya na yin hadaya don zunubi. 7 Sai ya miƙa ga Ubangiji, ya yi kafara dominta, za ta kuwa tsarkaka. Wannan shi ne abin da ya wajaba ta haifi ɗa ko 'ya. 8 Amma idan ɗan rago ya fi ƙarfinta, sai ta kawo kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai biyu, ɗaya don hadaya ta ƙonawa, ɗayan kuwa don yin hadaya don zunubi. Firist kuwa zai yi kafara dominta, za ta kuwa tsarkaka.

Littafin Firistoci 13

Dokoki a kan Kuturta

1 Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan ka'idodi. 2 Idan mutum yana da kumburi a fatar jikinsa, ko ɓamɓaroki ko tabo, har ya zama kamar cutar kuturta, sai a kai shi wurin Haruna, firist, ko ɗaya daga cikin zuriyarsa, firistoci. 3 Firist ɗin zai dudduba cutar da take a fatar jikin mutumin. Idan gashin da yake wurin cutar ya rikiɗa ya zama fari, zurfin cutar kuma ya zarce fatar jikinsa, wannan cuta kuturta ce. Firist ɗin da ya dudduba shi zai hurta, cewa, mutumin marar tsarki ne. 4 Amma idan tabon fari ne, zurfinsa kuwa bai zarce fatar ba, gashin kuma da yake cikinsa bai rikiɗa ya zama fari ba, sai firist ya kulle mai ciwon har kwana bakwai. 5 A rana ta bakwai firist zai ƙara dudduba shi, in ya ga cutar ba ta yaɗu a fatar jikin mutumin ba, sai ya sāke kulle shi waɗansu kwana bakwai kuma. 6 A rana ta bakwai sai firist ya sāke dubansa, idan ciwon ya dushe, cutar kuma ba ta yaɗuwa a fatar jikin mutumin, firist zai hurta, cewa, mutumin tsattsarka ne, ɓamɓaroki ne kawai, sai ya wanke tufafinsa. 7 Amma idan ɓamɓaroki ya yaɗu a cikin fatar jikin mutumin bayan da ya nuna kansa ga firist don tsarkakewa, sai ya sāke zuwa gaban firist. 8 Firist zai duba shi, idan ɓamɓaroki ya yaɗu a fatar, sai firist ya hurta, cewa, mutumin marar tsarki ne, ba ɓamɓaroki ba ne, kuturta ce. 9 Sa'ad da cutar kuturta ta kama mutum, sai a kai shi wurin firist. 10 Firist kuwa ya dudduba shi, in akwai kumburi a fatar jikin mutum wanda ya rikiɗar da gashin wurin ya zama fari, in kuma akwai sabon miki a kumburin, 11 to, kuturta ce da ta daɗe a fatar jikinsa. Firist kuwa zai hurta, cewa, mutumin marar tsarki ne, ba za a kulle shi ba, gama ya tabbata marar tsarki ne. 12 Idan kuturtar ta faso a fatar jikin mutum har ta rufe fatar jikin mutumin daga kai zuwa ƙafa a iyakar ganin firist, 13 firist ɗin zai duba shi, in kuturtar ta rufe jikin duka, zai hurta, cewa, mutumin tsarkakakke ne daga cutar, gama kuturtar ta rikiɗa, ta yi fari fat, don haka ya tsarkaka. 14 Amma a ranar da aka ga sabon miki a jikinsa zai zama marar tsarki. 15 Sai firist ya dudduba sabon mikin ya hurta, cewa, mutumin marar tsarki ne, sabon miki fa marar tsarki ne, gama kuturta ce. 16 Idan kuma sabon mikin ya juya, ya rikiɗa ya zama fari, zai tafi wurin firist. 17 Firist ɗin zai dudduba shi, idan cutar ta rikiɗa ta zama fara, sai firist ya hurta, cewa, mutumin tsarkakakke ne, gama ya tsarkaka. 18 Amma idan akwai wanda yake da ƙurjin da ya warke, 19 idan kuma akwai tabo jaja-jaja, da fari-farin tabo, sai a nuna wa firist. 20 Firist zai dudduba shi, idan zurfin kumburin ko tabon rikiɗa fari, sai firist ya hurta, cewa, mutumin marar tsarki ne, cutar kuturta ce ta faso a ƙurjin. 21 Amma idan firist ya dudduba shi ya ga gashin wurin bai yi fari ba, zurfin ƙurjin kuma bai zarce fatar ba, amma ya dushe, sai firist ɗin ya kulle shi kwana bakwai. 22 Amma idan ƙurjin ya bazu a fatar jikin, sai firist ya hurta, cewa, shi mutumin marar tsarki ne, kuturta ce. 23 Amma idan tabon ya tsaya wuri ɗaya, bai bazu ba, tabon miki ke nan, sai firist ya hurta, cewa, shi mutumin tsarkakakke ne. 24 Ko kuma idan mutum ya ƙuna a fatar jiki, naman wurin ƙunar kuwa ya yi tabo jaja-jaja, da fari-fari, ko fari, 25 sai firist ya dudduba shi, in gashin wurin tabo ya zarce fatar, to, kuturta ce ta faso a cikin ƙunar, sai firist ya hurta, cewa, shi mutumin marar tsarki ne, cutar kuturta ce. 26 Amma idan firist ya dudduba tabon, ya ga gashin tabon bai zama fari ba, zurfin tabon kuma bai zarce fatar ba, amma ya dushe, firist zai kulle shi kwana bakwai. 27 A kan rana ta bakwai, zai sāke dubansa, idan tabon yana bazuwa cikin fatar, sai firist ya hurta, cewa, shi mutumin marar tsarki ne, kuturta ce. 28 Amma idan tabon ya tsaya a wuri ɗaya, bai bazu a fatar jikin ba, ya kuma dushe, to, kumburi ne na ƙunar, firist zai hurta, cewa, shi mutumin tsarkakakke ne, gama tabon ƙuna ne. 29 Sa'ad da mace ko namiji na da cuta a kai, ko a gemu, 30 sai firist ya dudduba cutar, in ya ga zurfin cutar ya zarce fatar, gashin kuma da yake wurin ya zama rawaya, siriri kuma, firist zai hurta, cewa, shi mutumin marar tsarki ne, miki ne, ciwon da za a iya ɗauka ne. 31 Amma idan firist ya duba mikin, ya ga zurfinsa bai zarce fatar ba, ba kuma baƙin gashi a ciki, sai firist ya kulle mai miki har kwana bakwai. 32 A rana ta bakwai kuma firist zai duba cutar, idan mikin bai bazu ba, babu kuma rawayan gashi a cikinsa, zurfin mikin kuwa bai zarce fatar ba, 33 zai aske kansa, amma ba zai aske mikin ba, sai firist ya sāke kulle mai mikin har waɗansu kwana bakwai. 34 A rana ta bakwai firist zai dudduba mikin, idan mikin bai bazu ba, zurfinsa kuma bai zarce fatar ba, sai firist ya hurta, cewa, shi mutumin tsarkakakke ne, sai mutumin ya wanke tufafinsa, ya tsarkaka ke nan. 35 Amma idan mikin ya bazu bayan tsarkakewarsa, 36 sai firist ya dudduba shi, idan mikin ya bazu a fatar, ba lalle ne ya nemi rawayan gashi ba, shi mutumin marar tsarki ne. 37 Amma idan a ganinsa mikin bai yaɗu ba, baƙin gashi ya tsiro ya kuma yi tsawo a wurin, mikin ya warke ke nan, mutumin ya tsarkaka, firist kuwa zai hurta, cewa, shi mutumin tsarkakakke ne. 38 Idan a fatar jikin mace ko namiji akwai fararen tabbai, 39 sai firist ya dudduba, idan tabban toka-toka ne, mawanki ne ya faso a fatar, shi tsarkakakke ne. 40 Idan gashin kan mutum ya zube, ya zama mai sanƙo ke nan, amma shi tsattsarka ne. 41 Idan gashin goshin mutum ya zube, ya yi sanƙo ke nan, amma shi tsattsarka ne. 42 Idan a sanƙon ko a gaban goshi akwai tabon cuta jaja-jaja da fari-fari, to, kuturta ce ta faso a sanƙonsa ko gaban goshinsa. 43 Firist kuwa zai dudduba shi, idan an ga kumburin jaja-jaja da fari-fari ne a sanƙon kansa, ko a gabansa kamar alamar kuturta a fata jikinsa, 44 to, kuturu ne shi, marar tsarki. Firist zai hurta, cewa, shi mutumin marar tsarki ne, cutar kuturta tana kansa. 45 Mai kuturta zai sa yagaggun tufafinsa, ya bar gashin kansa ba gyara, sa'an nan ya rufe leɓensa na sama, ya ta da murya, ya riƙa cewa, “Marar tsarki, marar tsarki.” 46 Muddin yana da cutar, zai zama marar tsarki. Zai zauna shi kaɗai a bayan zango. 47 Idan ana tsammani akwai cutar kuturta a rigar ulu ko ta lilin, 48 ko a tariyar zaren, ko a waɗari, ko a lilin, ko a ulu, ko a cikin fata, ko cikin kowane abu da aka yi da fata, 49 idan cutar ta zama kore-kore, ko jaja-jaja a rigar, ko a fatar, ko a tariyar zaren, ko a waɗarin, ko a kan abin da aka yi da fata, wannan cuta kuturta ce, sai a nuna wa firist. 50 Firist zai dudduba cutar, ya ajiye abin da yake da cutar har kwana bakwai. 51 A rana ta bakwai ɗin zai sāke dudduba cutar, idan cutar ta yaɗu a rigar, ko a tariyar zaren, ko a waɗarin, ko a fatar, komenene za a yi da fata, wannan cuta muguwar kuturta ce, abin zai zama marar tsarki. 52 Zai ƙone rigar, ko tariyar zaren, ko waɗari na ulu ko na lilin, ko abin da dai aka yi da fata wanda yake da cutar, gama muguwar kuturta ce. 53 Amma idan firist ya dudduba ya ga cutar ba ta yaɗu a rigar, ko a tariyar zaren, ko a waɗarin, ko a abin da aka yi da fata ba, 54 sai firist ya umarta a wanke abin da yake da cutar, ya sāke ajiye shi har kwana bakwai kuma. 55 Firist kuma zai sāke duban abin da yake da cutar bayan da aka wanke shi, idan ya ga launin cutar bai sāke ba, ko da cutar ba ta yaɗu ba, abin ya zama marar tsarki ne nan, sai a ƙone shi da wuta, ko tabon cutar yana cikin abin ne, ko a waje. 56 Amma idan firist ɗin ya duba ya ga tabon ya dushe bayan da aka wanke shi, sai ya kece wurin daga fatar, ko tariyar zaren, ko waɗarin. 57 Idan tabon ya sāke bayyana kuma a rigar, ko a tariyar zaren, ko a waɗarin, ko a kan abin da aka yi da fata, ya yaɗu, sai a ƙone abin da yake da kuturtar. 58 Amma da rigar, ko a tariyar zaren, ko a waɗarin, ko kowane abu da aka yi da fata, wanda cutar ta wanku daga shi sa'ad da aka wanke, sai a sāke wanke shi, ya kuwa zama tsarkakakke ke nan. 59 Wannan ita ce dokar da za a bi a kan cutar kuturtar rigar ulu ko ta lilin, ko cutar kuturta ta tariyar zaren, ko ta waɗarin, ko kuma ta kan kowane abu da aka yi da fata, don a tabbatar tsattsarka ne, ko marar tsarki ne.

Littafin Firistoci 14

1 Ubangiji ya ba Musa 2 waɗannan ka'idodi da za a bi a ranar tsarkakewar mai kuturta. Sai a kawo shi ga firist. 3 Firist ɗin zai fita zuwa bayan zango ya dudduba shi. Idan kuturun ya warke daga cutar kuturtar, 4 firist ɗin zai umarta a kawo tsuntsaye biyu masu rai, masu tsabta, da itacen al'ul, da jan alharini, da ɗaɗɗoya domin aikin tsarkakewa. 5 Sai firist ya umarta a yanka tsuntsu ɗaya a kaskon da yake cike da ruwa mai gudu. 6 Ya kuma ɗauki ɗayan tsuntsu, da itacen al'ul, da jan alharini, da ɗaɗɗoya, ya tsoma su cikin jinin tsuntsun da aka yanka a ruwan kaskon. 7 Sai ya yayyafa jinin sau bakwai a kan wanda za a tsarkake daga kuturtar, sa'an nan ya hurta, cewa, mutumin ya tsarkaka, ya kuma saki tsuntsu mai ran ya tafi cikin saura. 8 Shi kuwa wanda za a tsarkake, sai ya wanke tufafinsa, ya aske dukan gashinsa, ya yi wanka da ruwa, zai kuwa tsarkaka. Bayan wannan zai shiga zango, amma kada ya shiga cikin alfarwarsa har kwana bakwai. 9 A kan rana ta bakwai zai aske dukan gashin kansa, da gemunsa, da gashin girarsa, da duk gashin jikinsa. Sai kuma ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai kuwa tsarkaka. 10 A rana ta takwas zai kawo 'yan raguna biyu bana ɗaya ɗaya marasa lahani da 'yar tunkiya bana ɗaya marar lahani, da hadaya ta gari rabin garwar gari mai laushi karɓaɓɓe da man zaitun, da rabin moɗa na mai. 11 Firist ɗin da zai tsarkake mutumin zai kawo wanda za a tsarkake da waɗannan abubuwa a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada. 12 Firist ɗin zai ɗauki ɗan rago ɗaya ya miƙa shi hadaya don diyyar laifi, da rabin moɗa na mai, ya miƙa su don hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. 13 Sa'an nan zai yanka ɗan rago a inda ake yanka hadaya don zunubi da hadaya ta ƙonawa. Tilas ya yi haka domin hadaya ta laifi rabon firist ne kamar hadaya domin zunubi. Hadaya ce mafi tsarki. 14 Firist zai ɗibi jinin hadaya don laifi ya shafa a leɓatun kunnen dama, da bisa babban yatsan hannun dama, da na ƙafar dama na wanda za a tsarkake ɗin. 15 Firist kuwa zai ɗibi man, ya zuba shi a tafin hannunsa na hagu. 16 Ya kuma tsoma yatsan hannunsa na dama a cikin man da ka a tafin hannunsa na hagu, ya yayyafa man da yatsansa sau bakwai a gaban Ubangiji. 17 Sauran man da ya ragu a tafin hannunsa, sai ya shafa shi a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da bisa babban yatsan hannunsa na dama, da na ƙafar dama. Wato, za a shafa man a inda aka shafa jinin hadaya don laifin. 18 Sauran man kuma da ya ragu cikin tafin hannunsa, firist ɗin zai shafa a kan wanda za a tsarkake. Firist zai yi kafara dominsa gaban Ubangiji. 19 Sai firist ya miƙa hadaya don zunubi domin ya yi kafara, don rashin tsarkin mutumin. Daga baya ya yanka hadaya ta ƙonawa. 20 Firist kuma zai miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta gari a bisa bagaden. Da haka zai yi kafara dominsa, shi kuwa zai tsarkaka. 21 Amma idan matalauci ne, har ba zai iya samun waɗannan abubuwa ba, sai ya kawo ɗan rago ɗaya domin hadaya don laifi, a yi hadaya ta kaɗawa, a yi kafara dominsa. Ya kuma kawo humushin garwa na gari mai laushi kwaɓaɓɓe da man zaitun don yin hadaya ta gari, da rabin moɗa na mai, 22 da kuma kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai biyu yadda dai ya iya. Ɗayan domin hadaya don zunubi, ɗayan kuma don hadaya ta ƙonawa. 23 A rana ta takwas zai kawo su wurin firist don tsarkakewarsa a ƙofar alfarwa ta sujada a gaban Ubangiji. 24 Sai firist ya ɗauki ɗan rago da man zaitun, ya miƙa su hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji. 25 Sa'an nan ya yanka ɗan ragon don laifi, ya ɗibi jinin hadaya don laifin, ya shafa a leɓatun kunnen dama na mutumin da za a tsarkake, da a babban yatsan hannunsa na dama, da ƙafarsa ta dama. 26 Firist ɗin kuma zai ɗibi man ya zuba cikin tafin hannunsa na hagu. 27 Sai ya yayyafa man da yake cikin tafin hannunsa na hagu sau bakwai a gaban Ubangiji da yatsansa na hannun dama. 28 Ya kuma shafa man da ya ragu cikin hannunsa a leɓatun kunnen dama na wanda za a tsarkake, da a babban yatsan hannun damansa, da kuma a babban yatsan ƙafar damansa, a inda aka shafa jinin hadaya don laifin. 29 Sauran man da yake cikin tafin hannunsa zai zuba a bisa wanda ake tsarkakewar, ya yi kafara dominsa a gaban Ubangiji. 30 Sai mutumin ya ba da kurciyoyi, ko 'yan tattabarai yadda ya iya, 31 ɗaya domin hadaya don zunubi, ɗaya kuma don hadaya ta ƙonawa tare da hadaya ta gari. Firist ɗin kuma zai yi kafara a gaban Ubangiji domin wanda ake tsarkakewar. 32 Wannan ita ce doka a kan mai ciwon kuturta wanda ba shi da isasshen abin bayarwa don yin hadayun tsarkakewarsa. 33 Sai kuma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, 34 “Sa'ad da kuka shiga ƙasar Kan'ana wadda nake ba ku ku mallaka, zan sa kuturta ta yaɗu a gidajenku.” Sa'an nan Ubangiji ya ba su waɗannan ka'idodi. 35 Mutumin da ya ga kuturta a gidansa, tilas ye je ya faɗa wa firist. 36 Firist kuwa ya umarta a fitar da dukan abin da yake cikin gidan kafin ya tafi ya dudduba tabo, domin kada kome da yake cikin gidan ya ƙazantu. Bayan haka sai firist ya shiga, ya duba gidan. 37 Zai dudduba tabon, idan akwai alamar tabon a bangayen gida kore-kore, ko jaja-jaja, idan an ga tabon ya yi zurfi cikin bangon, 38 sai firist ɗin ya fita daga cikin gidan zuwa ƙofa, ya rufe gidan har kwana bakwai. 39 A kan rana ta bakwai, sai firist ɗin ya komo, ya duba. Idan tabon ya yaɗu a jikin bangayen gidan, 40 sai ya umarta a ciccire duwatsun da suke da cutar, a zuba a wuri marar tsarki can bayan birnin, 41 ya sa a kankare jikin gidan duka. Shafen da suka kankare kuwa, sai su zubar da shi a wuri marar tsarki can bayan birnin. 42 Sa'an nan sai su kwaso waɗansu duwatsu, su sa su a wuraren da suka ciccire waɗancan. Sai a kawo laka a shafe gidan. 43 Idan cutar ta sāke ɓulla a cikin gidan bayan da aka ciccire duwatsun, aka kuma kankare gidan, aka yi masa shafe, 44 sai firist ya je ya duba, idan cutar ya yaɗu a gidan, to, muguwar kuturta ce, gidan marar tsarki ne. 45 Sai a rushe gidan, a kwashe duwatsun gidan, da katakansa, da shafensa duka a zubar bayan birni a wuri marar tsarki. 46 Duk wanda ya shiga gidan bayan da an rufe shi, zai ƙazantu har maraice. 47 Wanda kuma ya kwana cikin gidan, sai ya wanke tufafinsa, haka kuma wanda ya ci abinci cikin gidan, zai wanke tufafinsa. 48 Amma idan firist ɗin ya zo, ya dudduba, ya ga tabon bai yaɗu a gidan ba, bayan da an yi wa gidan shafe, sai firist ya hurta, cewa, gidan tsattsarka ne domin tabon ya warke. 49 Don tsarkakewar gidan, sai maigida ya kawo 'yan tsuntsaye biyu, da itacen al'ul, da jan alharini, da ɗaɗɗoya. 50 Sai a yanka tsuntsu ɗaya a kasko cike da ruwa mai gudu. 51 Zai ɗauki itacen al'ul, da ɗaɗɗoya, da jan alharini, da ɗayan tsuntsu mai ran, ya tsoma su cikin jinin tsuntsun da aka yanka a ruwan kaskon, ya yayyafa wa gidan sau bakwai. 52 Da haka zai tsarkake gidan da jini tsuntsun, da ruwa mai gudu, da tsuntsu mai ran, da itacen al'ul, da ɗaɗɗoya, da jan alharini. 53 Sa'an nan ya saki tsuntsu mai ran daga birni ya tafi saura. Ta haka zai yi kafara domin gidan, gidan kuwa zai tsarkaka. 54 Waɗannan su ne dokoki a kan cuce-cucen da akan ɗauka, da 55 kuturta a tufafi ko a jikin gida, 56 da kumburi, da ɓamɓaroki, ko tabo, 57 don a tabbatar lokacin da suke tsarkakakku da lokacin da ba su da tsarki.

Littafin Firistoci 15

Ƙazanturwar Namiji ko Mace

1 Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan ka'idodi 2 domin jama'ar Isra'ila. Duk lokacin da wani namiji yake ɗiga daga al'aurarsa, ƙazantacce ne. 3 Ko al'aurar tana ɗiga ko ta daina shi dai ƙazantacce ne. 4 Kowane gado da mai ɗigan ya kwanta a kai ya ƙazantu, da kowane abu da ya zauna a kai ya ƙazantu. 5 Duk wanda ya taɓa gadonsa, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 6 Duk wanda kuma ya zauna a kan kowane abu da mai ɗigar ya zauna a kai, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 7 Wanda kuma ya taɓa jikin mai ɗigar, sai ya wanke tufafinsa ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 8 Idan mai ɗigar yo tofar da yau a kan wanda yake da tsabta, sai mutumin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 9 Kowane sirdi da mai ɗigar ya zauna a kai zai ƙazantu. 10 Duk wanda ya taɓa kowane abu da yake ƙarƙashin sirdin zai ƙazantu har maraice, duk kuma wanda ya ɗauki wannan abu, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 11 Duk wanda kuma mai ɗigar ya taɓa da hannunsa da bai wanke ba, sai wanda aka taɓa ɗin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 12 Kaskon da mai ɗigar ya taɓa, sai a fasa shi, amma idan akushi ne sai a wanke shi da ruwa. 13 Sa'ad da mai ɗigar ya warke, sai ya ƙidaya ranaku bakwai don tsarkakewarsa, ya wanke tufafinsa, ya yi wanka a ruwa mai gudu, zai tsarkaka. 14 A kan rana ta takwas zai kawo kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai biyu a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada, ya ba firist. 15 Sai firist ya yi hadaya da su, ɗaya don hadayar zunubi, ɗaya kuma don hadaya ta ƙonawa. Firist ɗin zai yi kafara dominsa a gaban Ubangiji domin ɗigarsa. 16 Idan maniyyin mutum ya zubo, sai ya wanke jikinsa duka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 17 Kowace riga ko fatar da maniyyin ya taɓa, sai a wanke da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 18 Idan mutum ya kwana da mace, sai su yi wanka da ruwa, sun ƙazantu har maraice. 19 Sa'ad da mace take haila irin ta ka'ida, za ta ƙazantu har kwana bakwai, duk wanda ya taɓa ta kuwa zai ƙazantu har maraice. 20 Duk abin da ta kwana a kai a lokacin rashin tsarkinta zai ƙazantu, haka kuma abin da ta zauna a kai zai ƙazantu. 21 Wanda kuma ya taɓa gadonta, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 22 Haka kuma duk wanda ya taɓa kowane abu da ta zauna a kai, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 23 Ko gado ne, ko kuma kowane abu da ta zauna a kai, sa'ad da wani ya taɓa shi zai ƙazantu har maraice. 24 Idan kuma wani ya kwana da ita, rashin tsarkinta zai shafe shi. Zai zama marar tsarki har kwana bakwai. Kowane gado da ya kwanta a kai zai ƙazantu. 25 Idan zubar jinin hailar macen ya yi kwanaki da yawa, ko kuwa kwanakin hailarta sun zarce ka'ida, a duk kwanakin zubar jininta za ta lizima cikin rashin tsarki daidai kamar lokacin hailarta. 26 Kowane gado da ta kwanta a kai a kwanakin zubar jininta, zai zama ƙazantacce, daidai kamar lokacin hailarta. Kowane abu da ta zauna a kai zai ƙazantu kamar a lokacin hailarta. 27 Wanda duk ya taɓa waɗannan abubuwa zai ƙazantu, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, zai ƙazantu har maraice. 28 Bayan da hailarta ta tsaya, za ta ƙidaya kwanaki bakwai, bayan haka za ta tsarkaka. 29 A rana ta takwas sai ta kawo 'yan kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai, a wurin firist a ƙofar alfarwa ta sujada. 30 Firist ɗin zai miƙa ɗaya hadaya don zunubi, ɗayan kuma don hadaya ta ƙonawa. Firist zai yi kafara dominta a gaban Ubangiji saboda rashin tsarkinta. 31 Ta haka za ka tsarkake jama'ar Isra'ila daga rashin tsarkinsu, domin kada su mutu saboda rashin tsarkinsu ta wurin ƙazantar da alfarwata wadda take tsakiyarsu. 32 Waɗannan su ne ka'idodi a kan wanda yake ɗiga, da wanda yake zubar da maniyyi, ƙazantacce ne. 33 Haka kuma wadda take haila, da kowane namiji ko mace, da take ɗiga, da namijin da ya kwana da mace marar tsarki.

Littafin Firistoci 16

Ranar Kafara

1 Sai Ubangiji ya yi magana da Musa bayan rasuwar 'ya'yan Haruna, maza biyu, sa'ad da suka hura wuta marar tsarki a gaban Ubangiji, suka mutu. 2 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Faɗa wa ɗan'uwanka Haruna kada ya riƙa shiga Wuri Mafi Tsarki bayan labule koyaushe, wato, a gaban murfi wanda yake bisa akwatin alkawari, domin kada ya mutu, gama zan bayyana a cikin girgije a kan murfin. 3 Amma sai Haruna ya shiga Wuri Mafi Tsarki bayan da ya kawo ɗan bijimi domin yin hadaya don zunubi, da rago don yin hadaya ta ƙonawa.” 4 Sa'an nan Ubangiji ya ba Musa ka'idodin nan. Sai Haruna ya sa zilaika ta lilin tsattsarka, ya ɗaura mukuru na lilin, ya yi ɗamara da abin ɗamara na lilin, ya naɗa rawani na lilin, waɗannan su ne tsattsarkar sutura. Zai yi wanka da ruwa, sa'an nan ya sa su. 5 Zai karɓi bunsuru biyu daga taron jama'ar Isra'ila domin yin hadaya don zunubi, da rago ɗaya don yin hadaya ta ƙonawa. 6 Haruna zai miƙa bijimi na yin hadaya don zunubi saboda kansa. Zai yi kafara don kansa da gidansa. 7 Zai kuma kawo bunsuran nan biyu a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada. 8 Sa'an nan ya jefa kuri'a kan bunsuran nan biyu. Kuri'a ɗaya don Ubangiji, ɗaya kuma domin Azazel. 9 A wanda kuri'ar Ubangiji ta faɗa a kansa, sai Haruna ya miƙa shi hadaya don zunubi ga Ubangiji. 10 Amma a wanda kuri'ar Azazel ta faɗa a kansa, sai a miƙa shi da rai a gaban Ubangiji, a yi kafara da shi, a kora shi can cikin jeji domin Azazel. 11 Haruna kuma zai miƙa bijimi na yin hadaya don zunubin kansa, ya yi kafara don kansa da gidansa. Zai yanka bijimi na yin hadaya don zunubin kansa. 12 Zai ɗauki faranti cike da garwashin wuta daga bagaden da yake a gaban Ubangiji, ya kuma cika hannunsa biyu da turare mai ƙanshi, ya shigar da shi bayan labulen. 13 Zai zuba turaren a wuta a gaban Ubangiji, domin hayaƙi ya tunnuke ya rufe murfi wanda yake a kan akwatin alkawari, don kada ya mutu. 14 Sai ya ɗibi jinin bijimin, ya yayyafa da yatsansa a gefen gabas na murfin, zai kuma yayyafa jinin a gaban murfin sau bakwai. 15 Sai kuma ya yanka bunsuru na yin hadaya don zunubin jama'ar ya shigar da jinin bayan labulen. Zai sa jinin kamar yadda ya yi da jinin bijimin, ya yayyafa shi a kan murfin, da gaban murfin. 16 Da haka zai yi kafara domin Wuri Mai Tsarki saboda ƙazantar mutanen Isra'ila, da laifofinsu, da dukan zunubansu. Haka kuma zai yi wa alfarwa ta sujada, wadda take a wurinsu, a tsakiyar ƙazantarsu. 17 Kada kowa ya kasance cikin alfarwar sujada lokacin da Haruna ya shiga Wuri Mafi Tsarki domin ya yi kafara don kansa, da gidansa, da dukan taron jama'ar Isra'ila, sai lokacin da ya fita. 18 Sa'an nan zai fita ya tafi wurin bagade wanda yake gaban Ubangiji don ya yi kafara dominsa. Zai ɗibi jinin bijimin da na bunsurun, ya shafa wa zankayen bagaden a kewaye. 19 Zai kuma yayyafa jinin da yatsansa har sau bakwai a kan bagaden, ya tsabtace shi, ya tsarkake shi daga ƙazantar jama'ar Isra'ila. 20 A sa'ad da ya gama yin kafara don Wuri Mai Tsarki, da alfarwa ta sujada, da bagaden, sai ya miƙa bunsuru ɗin mai rai. 21 Haruna zai ɗibiya hannuwansa duka biyu a kan kan bunsurun mai rai, ya hurta muguntar Isra'ilawa duka a bisa bunsurun, da dukan laifofinsu, da dukan zunubansu. Zai ɗibiya su a kan kan bunsurun, ya kora shi cikin jeji ta hannun wanda aka shirya zai kora shi. 22 Bunsurun zai ɗauki muguntarsu duka a kansa zuwa jeji. Mutumin kuwa zai sake shi can a jeji. 23 Sa'an nan Haruna zai shiga alfarwa ta sujada, ya tuɓe tufafinsa na lilin waɗanda ya sa sa'ad da ya shiga Wuri Mafi Tsarki, ya ajiye su a nan. 24 Zai kuma yi wanka da ruwa a wuri mai tsarki, sa'an nan ya sa tufafinsa, ya je, ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa, da hadaya ta ƙonawa don jama'a, domin ya yi kafara don kansa da jama'a. 25 Zai ƙone kitsen hadaya don zunubi a bisa bagaden. 26 Shi wanda ya kore bunsurun Azazel, sai ya wanke tufafinsa ya yi wanka da ruwa, bayan haka yana iya komawa cikin zango. 27 Bijimin da bunsurun da aka yi hadaya don zunubi da su, waɗanda aka yi kafara da jininsu a Wuri Mafi Tsarki, sai a kai su bayan zangon, a ƙone fatunsu, da namansu, da tarosonsu. 28 Shi wanda ya ƙone su, zai wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, bayan haka ya iya komawa zangon. 29 Waɗannan za su zama farillai a gare su har abada. A rana ta goma ga watan bakwai za su ƙasƙantar da kansu, ba za su yi kowane irin aiki ba, ko ɗan ƙasa, ko baƙon da yake cikinsu. 30 Gama a wannan rana za a yi kafara dominsu, domin a tsarkake su daga dukan zunubansu, su zama tsarkakakku a gaban Ubangiji. 31 Wannan rana muhimmiya ce don hutawa a gare su. Za su ƙasƙantar da kansu, wannan farilla ce har abada. 32 Firist kuma da aka naɗa ya zama firist a madadin mahaifinsa, zai yi kafara yana saye da tufafin lilin masu tsarki. 33 Zai yi kafara domin Wuri Mai Tsarki, da alfarwa ta sujada, da bagaden. Sa'an nan kuma ya yi kafara domin firistocin, da dukan taron jama'ar. 34 Wannan zai zama dawwamammiyar farilla a gare su. Za a riƙa yin kafara domin jama'ar Isra'ila saboda zunubansu duka sau ɗaya a shekara. Sai Musa ya aikata kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

Littafin Firistoci 17

Wuri Ɗaya domin Yin Hadaya

1 Ubangiji ya umarce Musa, 2 ya faɗa wa Haruna da 'ya'yansa maza, da dukan mutanen Isra'ila waɗannan ka'idodi. 3 Idan Ba'isra'ile ya yanka sa, ko ɗan rago, ko akuya a cikin zango, ko a bayan zango, 4 bai kuwa kawo shi a ƙofar alfarwa ta sujada don ya miƙa shi sadaka ga Ubangiji a gaban alfarwa ta sujada ba, alhakin jinin da ya zubar yana bisa kansa, za a fitar da wannan mutum daga cikin jama'arsa. 5 Manufar wannan umarni ce domin Isra'ilawa su riƙa kawo hadayunsu, waɗanda sukan yi a filin saura ga Ubangiji a wurin firist a ƙofar alfarwa ta sujada. Sai su yanka hadayu na salama ga Ubangiji. 6 Sai firist ya yayyafa jinin a kan bagaden Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada. Zai ƙone kitsen don ya ba da ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. 7 Kada kuma su ƙara yin hadayunsu ga gumaka masu siffar bunsurai waɗanda suka bauta wa. Wannan doka ce ta har abada a gare su har dukan zamanansu. 8 Kowane Ba'isra'ile, ko baƙon da yake baƙunta a cikinsu, wanda ya miƙa hadaya ta ƙonawa ko sadaka, 9 amma bai kawo ta a ƙofar alfarwa ta sujada, ya miƙa ta ga Ubangiji ba, sai a fitar da wannan mutum daga cikin jama'a.

An Hana Cin Jini

10 Idan wani Ba'isra'ile, ko baƙon da yake baƙunta a cikinsu ya ci jini, Ubangiji zai yi gāba da wannan mutum da ya ci jinin ya fitar da shi daga cikin jama'a. 11 Gama ran nama yana cikin jinin, Ubangiji kuwa ya ba su shi a bisa bagade domin a yi wa rayukansu kafara, gama da jini ake kafara saboda akwai rai a cikinsa. 12 Saboda haka Ubangiji ya faɗa wa mutanen Isra'ila, cewa, kada wani daga cikinsu, ko baƙon da yake baƙunta a cikinsu, ya ci jini. 13 Idan kowane Ba'isra'ile, ko baƙon da yake baƙunta a cikinsu ya tafi farauta, ya kama nama, ko tsuntsu da ake ci, sai ya zub da jininsa, ya rufe da ƙasa. 14 Gama ran dukan nama yana cikin jininsa, saboda haka Ubangiji ya faɗa wa mutanen Isra'ila, cewa, faufau ba za su ci jinin kowace dabba ba, gama ran kowace dabba yana cikin jininta. Duk wanda kuwa ya ci shi, za a raba shi da jama'a. 15 Duk wanda ya ci mushe, ko abin da namomin jeji suka yayyaga, ko shi Ba'isra'ile ne, ko baƙo ne, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, ya ƙazantu har maraice, sa'an nan zai tsarkaka. 16 Amma idan bai wanke su ba, bai kuwa yi wanka ba, alhakinsa yana kansa.

Littafin Firistoci 18

An Haramta yin Lalata

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa 2 ya faɗa wa mutanen Isra'ila cewa, “Ni ne Ubangiji Allahnku. 3 Kada ku yi kamar yadda suke yi a kasar Masar inda kuka fito. Kada ma ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan'ana inda nake kai ku. Kada ku kiyaye dokokinsu. 4 Amma ku bi ka'idodina, ku yi tafiya a cikinsu, gama ni ne Ubangiji Allahnku. 5 Domin haka sai ku kiyaye dokokina da ka'idodina waɗanda ta wurin kiyaye su mutum zai rayu. Ni ne Ubangiji.” 6 Ubangiji ya ba da waɗannan ka'idodi kuma. Kada kowane mutum ya kusaci 'yar'uwarsa don ya kwana da ita. Ya ce, “Ni ne Ubangiji.” 7 Kada ya ƙasƙantar da mahaifinsa, wato, kada ya kwana da mahaifiyarsa, kada ya ƙasƙantar da mahaifiyarsa. 8 Kada ya kwana da matar mahaifinsa, gama ita matar mahaifinsa ce. 9 Kada ya kwana da 'yar'uwansa, 'yar mahaifinsa, ko 'yar mahaifiyarsa, ko a gida ɗaya aka haife ta da shi, ko a wani gida dabam. 10 Kada ya kwana da jikanyarsa gama zai zama ƙasƙanci a gare shi. 11 Kada ya kwana da 'yar matar mahaifinsa, wadda mahaifinsa ya haifa, tun da yake ita 'yar'uwarsa ce. 12 Kada ya kwana da bābarsa gama 'yar'uwar mahaifinsa ce. 13 Kada ya kwana da innarsa, gama ita 'yar'uwar mahaifiyarsa ce. 14 Kada ya kwana da matar ɗan'uwan mahaifinsa, gama ita ma bābarsa ce. 15 Kada ya kwana da matar ɗansa, gama ita surukarsa ce. 16 Kada ya kwana da matar ɗan'uwansa, gama ita matar ɗan'uwansa ce. 17 In ya kwana da mace, kada kuma ya kwana da 'yarta, ko jikanyarta, wannan duk haramun ne, gama su danginsa ne na kusa. 18 Muddin matarsa tana da rai, ba zai auro ƙanwarta ta zama kishiyarta ba. 19 Kada ya kwana da mace a lokacin hailarta, gama ba ta da tsarki. 20 Kada ya kwana da matar maƙwabcinsa don kada ya ƙazantar da kansa. 21 Kada ya ba da ɗaya daga cikin 'ya'yansa don a miƙa wa Molek, gama yin haka zai ƙasƙantar da sunan Allah. Shi Ubangiji ne. 22 Kada ya yi luɗu, gama Allah yana ƙin wannan. 23 Kada wani ko wata su kwana da dabba don kada su wofintar da kansu. 24 Kada su ƙazantar da kansu da irin waɗannan abubuwa, gama da irin waɗannan abubuwa ne al'umman da Ubangiji yake kora a gabansu suka ƙazantar da kansu. 25 Har ƙasar ma ta ƙazantu, don haka Ubangiji ya hukunta muguntarta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta. 26 Amma su sai su kiyaye dokokin Ubangiji da ka'idodinsa. Kada su aikata ko ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa na banƙyama, ko haifaffe na gida, ko baƙon da yake baƙunta a cikinsu. 27 Gama mazaunan ƙasar da suka riga su, sun aikata dukan abubuwa masu banƙyaman nan, don haka ƙasar ta ƙazantu. 28 Kada kuma ƙasar ta amayar da su idan sun ƙazantar da ita, kamar yadda ta amayar da al'ummar da ta riga su zama a cikinta. 29 Duk wanda ya aikata abu ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa masu banƙyaman nan za a raba shi da jama'a. 30 Ubangiji kuma ya ce, “Don haka sai ku kiyaye umarnina, kada ku kiyaye dokoki na banƙyama waɗanda aka kiyaye kafin ku zo, kada ku ƙazantu da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Littafin Firistoci 19

Dokoki a kan Tsarki da Yin Adalci

1 Ubangiji ya ce wa Musa 2 ya faɗa wa dukan taron jama'ar Isra'ila cewa, “Ku zama tsarkakakku, gama ni Ubangiji Allahnku mai tsarki ne. 3 Sai ko wannenku ya girmama mahaifiyarsa da mahaifinsa, ya kuma kiyaye lokatan sujada. Ni ne Ubangiji Allahnku. 4 “Kada ku juya ku bi gumaka, ko kuma ku yi wa kanku gumaka na zubi. Ni ne Ubangiji Allahnku. 5 “Sa'ad da za ku miƙa hadaya ta salama ga Ubangiji, ku miƙa ta domin a karɓe ku. 6 A cinye ta a ranar da kuka miƙa ta ko kuwa kashegari. Abin da ya ragu har kwana na uku, sai a ƙone da wuta, 7 gama ta zama abar ƙyama, idan aka ci ta a rana ta uku, ba za ta zama abar karɓa ba. 8 Wanda ya ci ta a rana ta uku ɗin, zai zama da laifi, domin ya tozartar da abu mai tsarki na Ubangiji, sai a raba wannan mutum da jama'a. 9 “Sa'ad da kuke girbin amfanin ƙasarku, kada ku girbe gefen gonakinku, kada kuma ku yi kala bayan da kuka gama girbi. 10 Kada ku girbe kalar gonar inabinku, kada kuma ku tattara 'ya'yan inabinku da suka kakkaɓe, sai ku bar wa matalauta, da baƙo. Ni ne Ubangiji Allahnku. 11 “Kada ku yi sata, ko ku cuci wani, ko ku yi ƙarya. 12 Kada ku yi alkawari da sunana idan dai ba ku da niyyar cika shi, wannan zai jawo wa sunana ƙasƙanci. Ni ne Ubangiji Allahnku. 13 “Kada ku zalunci kowa ko ku yi masa ƙwace. Kada kuma ku bar lokacin biyan hakkin ma'aikaci ya kai har gobe. 14 Kada ku zagi kurma, kada kuma ku sa wa makaho abin tuntuɓe, amma ku ji tsoron Ubangiji Allahnku. Ni ne Ubangiji. 15 “Ku yi gaskiya da adalci cikin shari'a, kada ku ma ku yi wa matalauci son zuciya, ko ku goyi bayan mawadaci. 16 Kada ku yi ta yaɗa ƙarya game da wani. Sa'ad da wani yake cikin shari'ar kuɓutar da ransa, ku yi magana muddin dai shaidarku za ta taimake shi. Ni ne Ubangiji. 17 “Kada wani ya riƙe ɗan'uwansa da ƙiyayya a zuciyarsa, amma ya daidaita rashin jituwa da shi, don kada ya yi zunubi saboda shi. 18 Kada ya ɗaukar wa kansa fansa a kan wani ko yo yi ta ƙinsa, amma ya ƙaunaci sauran mutane kamar yadda yake ƙaunar kansa. Ni ne Ubangiji. 19 “Sai ku kiyaye dokokina. Kada ku bar dabbobinku su yi barbara da waɗansu iri dabam. Kada ku shuka iri biyu a gonakinku. Kada ku sa tufar da aka yi da ƙyalle iri biyu. 20 “Idan mutum ya kwana da mace wadda take baiwa, wadda kuma wani yake tashinta, tun ba a fanshe ta ba, ko kuwa ba a 'yanta ta ba, sai a bincike, amma ba za a kashe su ba, domin ita ba 'yantacciya ba ce. 21 Amma ya kawo rago na yin hadaya don laifinsa ga Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada. 22 Sai firist ya yi kafara da ragon hadaya don laifi saboda laifin mutumin a gaban Ubangiji. Za a kuwa gafarta masa zunubin da ya yi. 23 “Sa'ad da kuka shiga ƙasar, kuka dasa itatuwa iri iri masu ba da 'ya'ya na ci, 'ya'yan itatuwan za su zama ƙazantattu a gare ku har shekara uku. A cikin shekarun nan uku ba za ku ci su ba. 24 A shekara ta huɗu 'ya'yan itatuwan za su tsarkaka. Hadaya ce ta yabo ga Ubangiji. 25 Amma a shekara ta biyar, sai ku ci 'ya'yan itatuwan domin su ba ku amfani a yalwace. Ni ne Ubangiji Allahnku. 26 “Kada ku ci kowane abu da jininsa, kada kuma ku yi duba, ko sihiri. 27 Kada ku yi wa goshinku da gemunku kwakkwafe saboda matattu, 28 ko ku tsattsaga jikinku, ko kuwa ku yi wa kanku jarfa. Ni ne Ubangiji. 29 “Kada ku ƙasƙantar da 'ya'yanku mata ta wurin sa su su zama karuwan masujadai, idan kuka yi haka, za ku juya ga gumaka, ƙasar za ta cika da lalata. 30 Sai ku kiyaye lokatan sujada, ku kuma darajanta alfarwata mai tsarki. Ni ne Ubangiji. 31 “Kada ku tafi wurin masu mabiya, kada kuma ku nemi shawarar bokaye, domin kada su sa ku ku ƙazantu. Ni ne Ubangiji Allahnku. 32 “Ku girmama tsofaffi ku darajanta su, gama kuna tsorona. Ni ne Ubangiji. 33 “Idan baƙo ya baƙunce ku a ƙasarku, kada ku cuce shi. 34 Amma ku ɗauke shi tankar ɗan ƙasa, ku ƙaunace shi kamar kanku, gama dā ku ma baƙi ne a ƙasar Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku. 35 “Kada ku cuci wani wajen yin amfani da kowane irin ma'auni na ƙarya, wato, awon tsawo, ko na nauyi, ko na ruwa. 36 Sai ma'auninku na awon nauyi, da mudun awo, da mudun awon abin da yake ruwa ruwa, su zama na gaskiya. Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar. 37 Sai ku kiyaye, ku aikata dokokina da umarnaina duka. Ni ne Ubangiji.”

Littafin Firistoci 20

Hukunci a kan Rashin Biyayya

1 Ubangiji ya faɗa wa Musa, 2 ya ce wa mutanen Isra'ila, “Duk Ba'isra'ile da kowane baƙo da yake zaune cikin Isra'ila, wanda ya ba da ɗaya daga cikin 'ya'yansa ga Molek, lalle ne a kashe shi. Mutanen ƙasar za su jajjefe shi da duwatsu. 3 Ni kaina zan yi gāba da wannan mutum, in raba shi da jama'arsa domin ya ba Molek ɗaya daga cikin 'ya'yansa, gama ya ƙazantar da alfarwa ta sujada, ya ƙasƙantar da sunana mai tsarki. 4 Idan kuwa mutanen ƙasar ba su kashe mutumin nan, wanda ya ba Molek ɗaya daga cikin 'ya'yansa ba, 5 ni kaina zan yi gāba da mutumin nan da iyalinsa, da waɗanda suka yarda suka bi Molek tare da shi. Ba zan ƙara ce da su mutanena ba. 6 “Duk wanda yake sha'ani da masu mabiya, ko da bokaye zan yi gāba da wannan mutum, in raba shi da jama'arsa. 7 Sai ku kiyaye kanku da tsarki, gama ni ne Ubangiji Allahnku. 8 Ku kuma kiyaye dokokina, ku aikata su, gama ni ne Ubangiji wanda yakeɓe ku. 9 “Dukan wanda ya zagi mahaifinsa, ko mahaifiyarsa za a kashe shi, gama ya zagi mahaifinsa da mahaifiyarsa. Alhakin jininsa yana wuyansa. 10 “Idan mutum ya yi zina, sai a kashe dukansu biyu, wato, shi da mazinaciyar. 11 Mutumin kuma da ya kwana da matar mahaifinsa, ya ƙasƙantar da mahaifinsa ke nan, su biyu ɗin za a kashe su. Alhakin jininsu yana wuyansu. 12 Duk wanda ya kwana da matar ɗansa, za a kashe su duka biyu ɗin, gama sun yi abin da yake haram. Alhakin jininsu yana wuyansu. 13 Duk mutumin da ya kwana da namiji kamar yadda namiji yake kwana da mace, su biyu ɗin, sun yi aikin ƙazanta, za a kashe su. Alhakin jininsu yana wuyansu. 14 Duk mutumin da ya auri 'ya tare da mahaifiyarta, wannan mugun abu ne, shi da su biyu ɗin, sai a ƙone su da wuta, don kada mugun abu ya kasance a cikinku. 15 Idan mutum ya kwana da dabba, sai a kashe shi, a kuma kashe dabbar. 16 In kuma mace ta yi ƙoƙari har ta kwana da dabba, sai a kashe matar tare da dabbar, alhakin jininsu yana wuyansu. 17 “Idan mutum ya auri ƙanwarsa ko kuma 'yar mahaifinsa, sai a ƙasƙantar da su a bainar jama'a, a kuwa kore su daga cikin jama'a. Ya kwana da ƙanwarsa ke nan, tilas su sha hukuncin laifinsu. 18 Idan mutum ya kwana da mace a lokacin hailarta, duka biyunsu za a kore su daga cikin jama'arsu, gama sun karya ka'idodi a kan rashi tsarki. 19 “Idan mutum ya kwana da bābarsa ko innarsa, za a hukunta duka biyunsu saboda abin ƙyama da suka yi. 20 Idan kuma mutum ya kwana da matar kawunsa, ya ƙasƙantar da kawunsa, sai su ɗauki alhakin laifinsu, za su mutu ba haihuwa. 21 Idan mutum ya auri matar ɗan'uwansa, ya yi mugun abu, za su mutu ba haihuwa, gama ya ƙasƙantar da ɗan'uwansa. 22 “Sai fa ku kiyaye dokokina duka, da ka'idodina duka, ku kuma aikata su domin kada ƙasar da nake kai ku ta amayar da ku. 23 Kada ku bi al'adun waɗannan al'ummai, waɗanda nake kora a gabanku, gama sun aikata waɗannan al'amura, don haka nake ƙyamarsu. 24 Amma ni na faɗa muku, za ku gāji ƙasarsu, zan kuwa ba ku ita, ku mallake ta, ƙasar da take da yalwar abinci. Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya keɓe ku daga sauran al'ummai. 25 Domin haka sai ku bambanta tsakanin halattattun dabbobi da haramtattun dabbobi, da tsakanin haramtattun tsuntsaye da halattattun tsuntsaye. Kada ku ƙazantar da kanku da haramtattun dabbobi, ko da tsuntsaye, ko da kowane abu mai rarrafe bisa ƙasa, waɗanda na ware su, su zama haramtattu a gare ku. 26 Sai ku zama tsarkakakku a gare ni, gama ni Ubangiji Mai Tsarki ne, na kuwa keɓe ku daga sauran al'umman duniya don ku zama nawa. 27 “Namiji ko mace da ke da mabiya ko maita, sai a kashe. Za ku jajjefe su da duwatsu, alhakin jininsu yana kansu.”

Littafin Firistoci 21

Tsarkin Firistoci

1 Ubangiji kuma ya umarce Musa, ya faɗa wa 'ya'yan Haruna, maza, firistoci cewa, “Kada ko wannensu ya ƙazantar da kansa ta wurin gawar mutanensa, 2 sai dai gawar iyalinsa na kurkusa, wato, gawar mahaifiyarsa, da ta mahaifinsa, da ta ɗansa, da ta 'yarsa, da ta ɗan'uwansa, 3 da ta 'yar'uwarsa, budurwa, da take kusa da shi, wadda ba ta yi aure ba tukuna. Saboda su ya iya ƙazantar da kansa. 4 Kada ya ƙazantar da kansa saboda dangantakar aure cikin mutanensa. 5 “Kada su aske kansu ƙwal, ko su kwakkwafe gemunsu, ko su tsattsaga jikinsu. 6 Sai su kasance da tsarki, kada su ƙasƙantar da sunana domin su ne masu kawo hadaya ta ci, masu ƙone hadayu da wuta gare ni, don haka sai su kasance da tsarki. 7 Kada firist ya auri karuwa, ko wadda mijinta ya sake ta, gama shi tsattsarka ne gare ni. 8 Dole jama'a su gan su da tsarki, gama suna miƙa hadaya ta ci gare ni. Ni ne Ubangiji, ni mai tsarki ne, na kuwa tsarkake mutanena. 9 'Yar firist wadda ta ɓata kanta da yin aikin karuwanci, ta ƙasƙantar da mahaifinta, sai a ƙone ta da wuta. 10 “Firist wanda yake babba cikin 'yan'uwansa da aka zuba masa man keɓewa, aka kuma keɓe shi ya riƙa sa tufafin firist, kada ya bar gashin kansa buzu-buzu, ko kuwa ya kyakketa tufafinsa. 11 Kada ya kusaci gawa, ko gawar mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa don kada ya ƙazantu. 12 An keɓe shi domina, kada ya ƙazantar da kansa, kada kuwa ya ɓata alfarwa ta sujada ta wurin shiga gidan da gawa take, ko ta mahaifinsa, ko ta mahaifiyarsa ce. 13 Sai ya auri budurwa. 14 Kada ya auri mace wadda mijinta ya rasu, ko sakakkiya, ko karuwa, amma ya auri budurwa daga cikin kabilarsa, 15 domin kada ya ƙazantar da 'ya'yansa waɗanda ya kamata su zama tsarkakakku. Ni ne Ubangiji, na kuwa keɓe shi ya zama babban firist.” 16 Sai Ubangiji ya umarce Musa 17 ya faɗa wa Haruna cewa, “Kada ko ɗaya daga cikin zuriyarka, da yake da lahani ya kusato garin ya miƙa hadaya ta ci gare ni har abada. 18 Duk mutumin da yake da lahani na makanta, ko gurguntaka, ka rauni a fuska, ko gaɓar da ta fi wata, 19 ko tauyayye a ƙafa ko a hannu, 20 ko mai ƙusumbi, ko wada, ko mai lahani a ido, ko cuta mai sa ƙaiƙayi, ko kirci, ko dandaƙaƙƙe, ba zai kusato garin ya miƙa hadaya ba. 21 Duk mutumin da yake cikin zuriyar Haruna firist, wanda yake da lahani, ba zai kusato garin ya miƙa hadaya ta ci gare ni ba. 22 Amma zai iya ci daga cikin tsattsarkan abincin da aka miƙa mini, da abinci mafi tsarki. 23 Sai dai ba zai kusaci labulen, ko ya tafi kusa da bagaden ba, domin yana da lahani, don kada ya ɓata wuraren yin sujada, gama ni ne Ubangiji, ni kuwa na tsarkake su.” 24 Haka nan kuwa Musa ya faɗa wa Haruna, da 'ya'yan Haruna, maza, da dukan Isra'ilawa.

Littafin Firistoci 22

Hadayu suna da Tsarki

1 Ubangiji kuma ya umarci Musa 2 ya faɗa wa Haruna, da shi da 'ya'yansa cewa, “Ku lura da tsarkakakkun abubuwa waɗanda Isra'ilawa suka keɓe domina, don kada ku ƙasƙantar da sunana mai tsarki. Ni ne Ubangiji. 3 Idan kowanne daga cikin dukan zuriyarku ya kusaci tsarkakakkun abubuwa, waɗanda Isra'ilawa suka keɓe domina, lokacin da yake ƙazantacce, wannan mutum ba zai ƙara kasancewa a gabana ba, wannan kuwa zai zama har dukan lokatai masu zuwa. Ni ne Ubangiji. 4 “Daga cikin zuriyar Haruna wanda yake kuturu, ko mai ɗiga, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwa ba, sai lokacin da ya tsarkaka. Duk wanda ya taɓa wani abu marar tsarki na mamaci, ko wanda maniyyinsa yake ɗiga, 5 da duk kuma wanda ya taɓa wani abu mai rarrafe wanda yake ƙazantarwa, ko kuwa wani mutum mai ƙazanta, 6 duk mutumin da ya taɓa kowane irin abu haka, zai ƙazantu har maraice, ba kuwa zai ci daga cikin tsarkakakkun abubuwan nan ba, sai ya yi wanka da ruwa tukuna. 7 To, sa'ad da rana ta faɗi mutumin zai tsarkaka, bayan wannan ya iya cin tsarkakakkun abubuwan nan, gama ko dā ma abincinsa ne. 8 Kada ya ci abin da ya mutu mushe, ko abin da namomin jeji suka yayyaga, don kada ya ƙazantar da kansa. Ni ne Ubangiji. 9 “Domin haka sai su kiyaye umarnaina don kada su yi zunubi su mutu ta wurin karya tsarkakakkun ka'idodina. Ni ne Ubangiji, ni na sa su tsarkaka. 10 “Duk wanda ba daga cikin iyalin firistoci ba, ko da yake zama tare da su ne, ko kuwa an ɗauke shi yana yi musu aiki, ba zai ci daga cikin tsarkakakkun hadayun ba. 11 Amma idan firist ya sayi bawa da kuɗinsa, bawan ya zama dukiyarsa, bawan zai iya ci, haifaffun gidansa kuma za su iya cin tsattsarkan abincin. 12 Idan kuwa 'yar firist ta auri wani wanda ba firist ba, to, kada ta ci daga cikin tsarkakakkun hadayu. 13 Amma idan 'yar firist ɗin gwauruwa ce, ko sakakkiya, ba ta kuma da ɗa, ta kuwa koma gidan mahaifinta, sai ta ci daga cikin abincin mahaifinta kamar cikin kwanakin ƙuruciyarta. Amma wani dabam ba zai ci ba. 14 “Idan kuwa har wani mutum dabam ya ci daga cikin tsarkakakken abin ba da saninsa ba, to, sai ya maido abin ga firist, da ƙarin humushin tamanin abin. 15 Firist ba zai ƙasƙantar da tsarkakakkun abubuwan nan da jama'ar Isra'ila suke miƙawa ba, 16 da zai bar mutumin da bai cancanta ya ci ba, wannan zai jawo masa hukunci. Ni ne Ubangiji. Ni na tsarkake hadayun.” 17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 18 ya yi magana da Haruna da 'ya'yansa maza, da dukan Isra'ilawa ya ce musu, “Sa'ad da duk Ba'isra'ile ko baƙon da yake zaune a Isra'ila, ya kawo hadaya ta ƙonawa, ko ta wa'adi ce, ko ta yardar rai, dole ne dabbar ta zama marar lahani. 19 Dabbar ta kasance namiji marar lahani idan ana so ta karɓu. 20 Kada ku yi hadaya da abin da yake da lahani, gama Ubangiji ba zai karɓa ba. 21 Idan kuwa wani ya kawo hadaya ta salama ga Ubangiji don cika wa'adi, ko don hadaya ta yardar rai, daga cikin garken shanu, ko na tumaki, da na awaki, sai ya zama cikakke, marar lahani, don ya karɓu. 22 Dabbobi makafi, ko naƙasassu, ko mai gundumi, ko mai ɗiga, ko mai susa, ko mai kirci, kada ku miƙa wa Ubangiji, kada kuma ku yi hadaya ta ƙonawa a bagaden Ubangiji da su. 23 Kwa iya ba da dabba, marar cikakkiyar halitta don hadaya ta yardar rai, amma ba za ku bayar don hadaya ta cika wa'adi ba, ba za a karɓa ba. 24 Kowace dabba kuma da lunsayinta yake da ƙujewa, ko dandaƙewa, ko yagewa, ko yankewa, ba za ku miƙa ta hadaya ga Ubangiji ba, ba kuwa za ku yi hadaya da ita a ƙasarku ba. 25 “Ba kuma za ku karɓi irin dabbobin nan daga hannun baƙo don ku miƙa su hadaya ga Ubangiji ba, marasa tsarki ne tun da yake suna da lahani, ba za a karɓa ba.” 26 Ubangiji ya yi magana da Musa, ya ce, 27 “Sa'ad da kuma aka haifi ɗan maraƙi, ko ɗan rago, ko ɗan akuya, zai yi kwana bakwai tare da uwarsa. A rana ta takwas zuwa gaba, sai a karɓe shi don yin hadaya ta ƙonewa ga Ubangiji. 28 Ba za ku yanka uwar dabbar tare da ɗanta rana ɗaya ba, ko uwar saniya ce, ko ta tunkiya ce. 29 Sa'ad da za ku miƙa hadaya ta godiya ga Ubangiji, sai ku miƙa ta yadda za a karɓa. 30 A ranar ce za a cinye, kada a bar kome ya kai gobe. Ni ne Ubangiji. 31 “Ku yi biyayya da umarnina. Ni ne Ubangiji. 32 Kada ku jawo wa sunana mar tsarki ƙasƙanci, amma sai mutanen Isra'ila su gane, ni mai tsarki ne. Ni ne Ubangiji na kuwa tsarkake ku, 33 na kuma fisshe ku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji.”

Littafin Firistoci 23

Ƙayyadaddun Idodi

1 Ubangiji ya ba Musa 2 waɗannan ka'idodi domin ƙayyadaddun idodi sa'a da Isra'ilawa za su taru domin yin sujada. 3 Cikin kwanaki shida za a yi aiki, amma a rana ta bakwai za a huta ɗungum, gama ranar Asabar ce, tsattsarka. Ko kaɗan ba za a yi aiki a ranar ba a duk inda suke, amma ku yi taruwa ta sujada gama ranar Asabar ta Ubangiji ce. 4 Su yi waɗannan idodi a ƙayyadaddun lokatai.

Idin Ƙetarewa da na Abinci Marar Yisti

5 Da maraice a rana ta goma sha huɗu ga watan fari, ita ce ranar Idin Ƙetarewa ta Ubangiji. 6 Sa'an nan kuma sha biyar ga watan za a yi bikin idin abinci marar yisti na Ubangiji. Za su ci abinci marar yisti har kwana bakwai. 7 Za su yi muhimmin taro a rana ta fari. Ba za su yi aiki mai wuya a ranar ba. 8 A kwana bakwai ɗin za su riƙa miƙa hadaya ta ƙonawa kowace rana ga Ubangiji. Za su kuma yi muhimmin taro a rana ta bakwai ɗin. Ba za su yi aiki mai wuya ba. 9 Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa, 10 lokacin da suka shiga ƙasar da Ubangiji yake ba su, sai su kawo wa firist dami na fari na amfanin gonakinsu. 11 Firist ɗin zai kaɗa damin hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, don a karɓe su. Firist zai kaɗa hadayar a kashegarin Asabar. 12 A ranar da suka miƙa hadaya ta kaɗawa, za su kuma miƙa wa Ubangiji hadaya ta ƙonawa da ɗan rago bana ɗaya marar lahani. 13 Tare da wannan hadaya kuma, za su miƙa hadaya ta gari, humushi biyu na garwar gari mai laushi kwaɓaɓɓe da man zaitun. Za a miƙa shi hadaya ta ƙonawa don ya ba da ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Za su kuma miƙa hadaya ta sha da ruwan inabi kwalaba ɗaya. 14 Kada su ci sabon hatsin, wanda aka tuma, ko ɗanyensa, ko wanda aka yi gurasa da shi sai sun kawo hadayarsu ta sabon hatsi ga Allah. Za su kiyaye wannan ka'ida, da su da dukan zuriyarsu, har dukan zamanai masu zuwa.

Idin Girbi

15 Za su ƙidaya mako bakwai daga kashegarin Asabar da suka kawo damin hadaya ta kaɗawa domin miƙa wa Ubangiji. 16 Kwana hamsin za su ƙirga zuwe kashegarin Asabar ta bakwai ɗin. Sa'an nan sai su kawo hadaya ta sabon hatsi ga Ubangiji. 17 Za su kawo malmala biyu na abinci da za a kaɗa daga inda suke domin a miƙa su ga Ubangiji. Za a yi malmalan da rabin garwar gari mai laushi. Za a sa wa garin yisti, sa'an nan a toya. Hadaya ta 'ya'yan fari ke nan ga Ubangiji. 18 Za su kuma miƙa 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya marasa lahani, da bijimi ɗaya, da raguna biyu tare da abincin. Za a yi hadaya ta ƙonawa da su ga Ubangiji, tare da hadayarsu ta gari, da hadayarsu ta sha, wato, hadaya ta ƙonawa da wuta, hadaya ce mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 19 Za su miƙa hadaya ta zunubi da bunsuru ɗaya, da 'yan raguna biyu bana ɗaya ɗaya don hadaya ta salama. 20 Firist zai kaɗa su tare da abinci na nunan fari domin hadaya ta kaɗawa, da 'yan ragunan nan biyu a gaban Ubangiji. Za su zama tsarkakakku ga Ubangiji domin a ba firist. 21 A ranar fa za su yi shela don a yi muhimmin taro. Ba za su yi aiki mai wuya ba. Wannan doka ce gare su har abada a inda suke duka. 22 Sa'ad da suka girbe amfanin gonakinsu, ba za su girbe har da gyaffan gonakinsu ba, ba kuma za su yi kalar amfanin gonakinsu ba. Za su bar wa matalauta da baƙi. Shi ne Ubangiji Allahnsu.

Idin Sabuwar Shekara

23 Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa, 24 ya ce wa Isra'ilawa su mai da rana ta fari ga wata na bakwai ta zama ranar hutu musamman, sa'ad da za su ji busar ƙaho, sai su taru domin yin sujada. 25 Ba za su yi aiki mai wuya ba. Za su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.

Ranar Kafara

26 Ubangiji ya yi magana da Musa, cewa, 27 rana ta goma ga watan bakwai za ta zama rana ta yin kafara da lokacin yin muhimmin taro. Kada su ci abinci a ranar, su taru su yi sujada, su miƙa hadaya taƙonawa ga Ubangiji. 28 Ba za su yi aiki a wannan rana ba, gama rana ce ta yin kafara dominsu. 29 Duk wanda ya ci abinci a wannan rana ba za a lasafta shi ɗaya daga cikin jama'ar Allah ba. 30 Duk kuma wanda ya yi aiki a wannan rana, Ubangiji kansa zai kashe shi. 31 Wannan ka'ida ta shafi dukan zuriyarsu a duk inda suke. 32 Daga faɗuwar ranar tara ga watan, har zuwa faɗuwar ranar goma ga watan, su kiyaye wannan ta zama ranar hutu musamman. A wannan lokaci ba wanda zai ci abinci.

Idin Bukkoki

33 Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa, 34 a rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi Idin Bukkoki kwana bakwai saboda Ubangiji. 35 Za a yi muhimmin taro na sujada a rana ta fari. Ba za su yi aiki ba. 36 A kwana bakwai ɗin za su riƙa miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. A rana ta takwas kuma sai su yi muhimmin taro na sujada, su miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Rana ce ta yin sujada, kada su yi aiki. 37 Waɗannan su ne ƙayyadaddun idodi na Ubangiji da za su riƙa yi domin sujada. Za su miƙa hadayu ga Ubangiji, wato, hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta gari, da ta sadakoki, da hadayu na sha. Za a miƙa kowace hadaya a ranarta. 38 Waɗannan idodi ƙari ne a kan lokatan sujada da aka saba, hadayun kuma ƙari ne a kan kyautan da aka saba bayarwa, kamar su hadaya don cika wa'adi, da hadaya ta yardar rai da suke bayarwa ga Ubangiji. 39 A rana ta goma sha biyar ga watan bakwai, bayan da sun gama tattara amfanin gonakinsu, sai su yi idi ga Ubangiji har kwana bakwai. Rana ta fari, da rana ta takwas za su zama muhimman ranakun hutawa. 40 A ranar sai su ɗibi 'ya'yan itatuwa masu kyau, da rassan dabino, da kauraran rassan itatuwa masu ganye, da itacen wardi na rafi, sa'an nan su nuna bangirma gaban Ubangiji Allahnsu har kwana bakwai. 41 Za su yi idin nan ga Ubangiji har kwana bakwai. Wannan ka'ida ce a gare su har abada. 42 Za su zauna cikin bukkoki har kwana bakwai. Duk 'yan ƙasa waɗanda suke Isra'ilawa za su zauna cikin bukkoki. 43 Don zuriyarsu ta sani Ubangiji ya sa Isra'ilawa su zauna cikin bukkoki, sa'ad da ya fito da su daga ƙasar Masar. Shi ne Ubangiji Allahnsu. 44 Haka kuwa Musa ya sanar wa mutanen Isra'ila da ƙayyadaddun idodin Ubangiji.

Littafin Firistoci 24

Kulawa da Fitila

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa 2 ya umarce Isra'ilawa, su kawo masa tsabtataccen man zaitun da aka matse domin fitilar. Fitilar za ta riƙa ci kullum. 3 Za a ajiye ta a gaban labulen shaida a alfarwa ta sujada. Kullum Haruna zai riƙa lura da ita daga maraice har safiya a gaban Ubangiji. Wannan zai zama muku farilla har abada a dukan zamananku. 4 Kullum sai ya shirya fitilun a bisa alkuki na zinariya tsantsa a gaban Ubangiji.

Gurasar da aka Miƙa ga Allah

5 Ɗauki lallausan gari a toya gurasa goma sha biyu. A ki kowace gurasa da humushi biyu na garwar gari. 6 A ajiye su bisa tebur na zinariya tsantsa jeri biyu, shida a kowane jeri. 7 Sai a sa lubban tsantsa a kowane jeri don a haɗa da abincin da za a ƙone domin hadaya ta tunawa ga Ubangiji. 8 Kullum a kowace ranar Asabar, Haruna zai kintsa su a gaban Ubangiji domin Isra'ilawa saboda madawwamin alkawarin. 9 Wannan abinci zai zama rabon Haruna da na 'ya'yansa maza, za su ci a wuri mai tsarki, tun da yake a gare shi rabo ne mai tsarki daga cikin hadayun da akan ƙone da wuta ga Ubangiji. Wannan farilla ce har abada.

Hukunci a kan Saɓo da Biyan Diyya

10 Ɗan wata mace Ba'isra'iliya wanda mahaifinsa Bamasare ne, ya fita, ya yi faɗa da wani Ba'isra'ile a cikin zangon. 11 Sai ɗan Ba'isra'iliyar ya saɓi sunan Allah. Aka kai shi wurin Musa. Sunan mahaifiyar kuwar Shelomit 'yar Dibri na kabilar Dan. 12 Musa kuwa ya kulle shi a gidan tsaro kafin Ubangiji ya faɗa musu abin da za su yi da shi. 13 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 14 “Fito da wanda ya yi saɓon nan daga cikin zangon. Ka kuma sa dukan waɗanda suka ji shi su sa hannuwansu a bisa kansa. Taron jama'ar kuwa su jajjefe shi da duwatsu. 15 Sa'an nan ka faɗa wa Isra'ilawa, cewa, duk wanda ya saɓi Allah zai ɗauki alhakin zunubinsa, 16 za a kuwa kashe shi. Duk Ba'isra'ile ko baƙon da yake zaune cikin Isra'ilawa wanda ya saɓi Allah, sai taron jama'a su jajjefe shi da duwatsu ya mutu. 17 “Duk wanda ya kashe mutum, shi ma sai a kashe shi. 18 Wanda ya kashe dabba kuma ya yi ramuwa, rai maimakon rai. 19 “Idan mutum ya yi wa wani rauni, kowane irin rauni ne ya yi masa, shi kuma haka za a yi masa. 20 Idan ya karya masa ƙashi ne, sai a karya nasa ƙashin, idan ya cire wa wani ido, sai a ƙwaƙule nasa, idan haƙori ya ɓalle, sai a ɓalle nasa. Duk irin raunin da ya ji wa wani haka za a yi masa. 21 Wanda ya kashe dabba ya yi ramuwa, wanda kuwa ya kashe mutum sai a kashe shi. 22 Irin shari'ar da za a yi wa baƙo, ita za a yi wa ɗan gari, gama ni ne Ubangiji Allahnku.” 23 Sai Musa ya yi magana da Isra'ilawa, suka kuwa fito masa da mutumin da ya yi saɓon a bayan zangon. Suka jajjefe shi da duwatsu. Haka Isra'ilawa suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Littafin Firistoci 25

Bikin Kewayowar Shekaru

1 Ubangiji kuwa ya yi wa Musa magana a kan Dutsen Sina'i, ya ce 2 ya faɗa wa Isra'ilawa ka'idodin nan. Sa'ad da suka shiga ƙasar da Ubangiji yake ba su, ƙasar za ta kiyaye shekara ta bakwai ga Ubangiji. 3 Shekara shida za su yi, suna ta noman gonakinsu, suna kuma ta aske gonakin inabinsu, suna tattara amfaninsu. 4 Amma shekara ta bakwai ta Ubangiji ce, shekara ce ta hutawa ga ƙasar. Kada su nomi gonakinsu, ko kuwa su aske inabinsu. 5 Kada su girbe gyauron gonakinsu da na inabin da ba su yi wa aski ba. Za ta zama shekarar hutawa ta musamman ga ƙasar. 6 A shekarar nan ɗin ƙasar za ta tanada musu abinci, da su da bayinsu mata, da maza, da barorinsu na ijara, da baƙon da yake zaune tare da su, 7 har da dabbobinsu na gida da na jeji. Duk albarkar da ƙasar za ta bayar, za ta zama abinci.

Murnar Shekara ta Hamsin

8 Sai su ƙidaya shekara bakwai har sau bakwai. Shekarar nan bakwai sau bakwai su ne shekara arba'in da tara a gare su. 9 A ranar kafara, goma ga wata na bakwai za su busa ƙahon rago da ƙarfi cikin ƙasarsu duka. 10 Shekara ta hamsin kuwa za su keɓe ta, su yi shelar 'yanci cikin ƙasar duka ga dukan mazaunanta. Za ta zama shekarar murna a gare su. Kowa zai koma mahallinsa, ko wannensu kuma wurin danginsa. 11 Shekarar nan ta hamsin za ta zama shekara ta murna a gare su. A cikinta ba za su yi shuka, ko su girbe gyauro ba, ba kuwa za su tattara 'ya'yan inabin da ba su yi wa aski ba. 12 Shekara ce ta murna, za ta zama keɓaɓɓiya a gare su. Za su ci albarkar da gonakin suka bayar. 13 Ubangiji ya ce, “A wannan shekara ta hamsin ta murna kowa zai koma mahallinsa. 14 In ka sayar, ko ka sayi gona a wurin ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, kada ku cuci juna. 15 Idan za ka yi sayayya a wurin maƙwabcinka, sai ka lura da yawan shekarun da za ka mora kafin shekara ta hamsin ta murna ta kewayo. 16 Idan shekarun sun ragu da yawa kafin shekara ta hamsin ta murna ta kewayo, sai ka saya da tsada. Idan kuwa shekarun sun ragu kima ne, sai ka saya da araha, gama yana sayar maka bisa ga yawan shekarun da za ka mora ne. 17 Kada ku cuci juna fa, amma ku ji tsoron Allahnku, gama ni ne Ubangiji Allahnku.”

Matsalolin Shekarar Murna

18 “Domin haka sai ku kiyaye farillaina, da ka'idodina. Ku aikata su domin ku zauna a ƙasar lami lafiya. 19 Ƙasar za ta ba da amfani, za ku ci, ku ƙoshi, ku zauna lafiya. 20 “Idan kuwa kun tambaya abin da za ku ci a shekara ta bakwai, idan ba za ku yi shuka ba, ba kuwa za ku tattara amfanin gona ba, 21 ku sani zan sa muku albarka a shekara ta shida don ta ba da isasshen amfanin da zai kai ku shekara uku. 22 Sa'ad da za ku yi shuka a shekara ta takwas, shi ne za ku yi ta ci, har shekara ta tara lokacin da za ku yi girbi.”

Fansar Mallaka

23 “Kada a sayar da gona din din din, gama ƙasar tawa ce, ku kuwa baƙi na da kuke baƙunci a wurina. 24 “Amma kuna iya jinginar da gonar da kuka mallaka. 25 Idan ɗan'uwanka ya talauce, har ya jinginar maka da mahallinsa, sai danginsa na kusa ya fanshi abin da ɗan'uwansa ya jinginar. 26 Idan mutumin ba shi da wanda zai fansa, idan shi kansa ya arzuta, ya sami abin da ya isa yin fansa, 27 to, sai ya lasafta yawan shekarun da ya jinginar da abin, sa'an nan ya biya jinginar daidai da shekarun da suka haura kafin shekara ta hamsin ta murna ta kewayo, shi ya koma kan mahallinsa. 28 Amma idan ba shi da isasshen abin da zai fanshi abinsa, to, sai wanda ya karɓi jinginar ya ci gaba da riƙon abin da aka jinginar masa ɗin har shekara ta hamsin ta murna, a lokacin ne zai mayar wa mai shi, mai shi ɗin kuwa ya koma a kan mahallinsa. 29 “Haka nan kuma idan mutum ya jinginar da gida a cikin birni mai garu, yana da izini ya fanshi abinsa a ƙarshen shekara guda. 30 Idan kuwa bai fanshi gidan a ƙarshen shekara guda ba, sai gidan nan da yake cikin birni mai garu ya zama mallakar wanda ya karɓi jinginar, da na zuriyarsa duka har abada. Ba za a mayar wa maigidan da gidan a shekara ta hamsin ta murna ba. 31 Amma gidajen da suke cikin ƙauyuka da ba su cikin garu, sai a lasafta su daidai da gonakin da suke cikin ƙasar, ana iya fansarsu, za a kuma mayar wa masu su a shekara ta hamsin ta murna. 32 Amma a kan biranen Lawiyawa, da gidajen da suke cikin biranen da suka mallaka, Lawiyawa suna da izini su fanshe su a kowane lokaci. 33 Amma idan wani daga cikin Lawiyawa bai fanshi gidansa ba, a shekara ta hamsin ta murna sai a mayar masa da gidan nan na cikin birnin da suka mallaka, gama gidajen da suke cikin biranen Lawiyawa su ne nasu rabo a cikin Isra'ilawa. 34 Ba za a jinginar da hurumin biranensu ba, gama wannan shi ne abin mallakarsu har abada.”

Ba da Rance ga Matalauci

35 “Idan ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, ya talauce, ya kasa riƙon kansa, sai ka riƙe shi kamar baƙon da yake baƙunci a wurinka. 36 Kada ka ba shi rance da ruwa, amma ka ji tsoron Allah ka bar ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, ya zauna tare da kai. 37 Kada ka ranta masa kuɗi da ruwa, kada kuma ka ba shi abinci don sumun riba. 38 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fanshe ku daga ƙasar Masar don in ba ku ƙasar Kan'ana, in zama Allahnku.”

'Yantar da Bayi

39 “Idan kuwa ɗan'uwanka, Ba'isra'ile, ya talauce har ya sayar da kansa gare ka, to, kada ka bautar da shi kamar bawa. 40 Amma ya zauna tare da kai kamar bara na ijara, ko kuwa kamar wanda yake baƙunci. Sai ya yi aiki tare da kai har shekara ta hamsin ta murna ta kewayo. 41 Sa'an nan shi da iyalinsa su rabu da kai, ya koma wurin danginsa da mahallin kakanninsa. 42 Gama su bayina ne, waɗanda na fanshe su daga ƙasar Masar, ba za a sayar da su kamar yadda ake sayar da bayi ba. 43 Kada ka mallake shi da tsanani, amma ka ji tsoron Allahnka. 44 Amma a kan bayi mata da maza da kuke so ku samu, kwa iya sayensu daga al'ummar da take kewaye da ku. 45 Kwa iya sayen bayi daga baƙin da suke baƙunci a wurinku, su da iyalinsu waɗanda aka haifa a ƙasarku. Kwa iya sayensu su zama dukiyarku. 46 Kwa iya barinsu ga 'ya'yanku maza a bayanku su gāda, su zama abin mallakarsu har abada. Kwa iya bautar da su, amma 'yan'uwanku, Isra'ilawa, ba za ku mallaki juna da tsanani ba. 47 “Idan baƙo ne ko mai aikin ijara da yake zaune tare da ku ya arzuta, ɗan'uwanku kuwa wanda yake kusa da shi ya talauce, har ya sayar da kansa ga baƙon, ko mai aikin ijarar da yake tare da ku, ko kuwa ga wani daga cikin iyalin baƙon, 48 bayan da ya sayar da kansa ana iya fansarsa. Wani daga cikin 'yan'uwansa ya iya fansarsa. 49 Ko kawunsa, ko ɗan kawunsa, ko wani daga cikin danginsa na kusa ya iya fansarsa. Idan kuma shi kansa ya arzuta ya iya fansar kansa. 50 Sai ya sa wanda ya saye shi ya lasafta tun daga shekarar da ya sayar da kansa, har zuwa shekara ta hamsin ta murna. Ƙuɗin da za a fanshe shi zai zama daidai da yawan shekarun da suka ragu kafin shekara ta murna. Sai a ɗauke shi kamar bara na ijara. 51 Idan shekarun sun ragu da yawa, sai ya fanshi kansa bisa ga adadin kuɗin da aka saye shi. 52 Amma idan shekarun sun ragu kaɗan kafin shekara ta hamsin ta murna, sai ya lasafta, ya biya don fansarsa bisa ga yawan shekarun. 53 Sai baƙon ya mai da shi kamar bara mai aikin ijara, shekara a kan shekara. Amma kada ya tsananta masa. 54 Idan ba a fanshe shi ta waɗannan hanyoyi ba, sai a shekara ta hamsin ta murna, a sake shi, shi da 'ya'yansa. 55 Gama a gare ni Isra'ilawa bayi ne waɗanda na fisshe su daga ƙasar Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Littafin Firistoci 26

Fa'idodin Biyayya

1 Ubangiji ya ce, “Kada ku yi wa kanku gumaka, ko ku kafa sassaƙaƙƙiyar siffa, ko al'amudi. Kada kuma ku kafa wata siffa ta dutse a ƙasarku da za ku durƙusa mata, gama ni ne Ubangiji Allahnku. 2 Sai ku kiyaye lokatan sujadata, ku girmama alfarwa ta sujada. Ni ne Ubangiji. 3 “Idan kun bi dokokina, kun kiyaye umarnaina, kun aikata su, 4 sa'an nan zan ba da ruwan sama a lokacinsa, ƙasar kuwa za ta ba da albarkarta, itatuwan gonaki kuma za su ba da 'ya'yansu. 5 Za ku yi ta girbi, har lokacin tattara 'ya'yan inabi, za ku kuma yi ta tattara 'ya'yan inabi har zuwa lokacin shuka. Za ku ci abincinku, ku ƙoshi, ku yi zamanku a ƙasarku lafiya. 6 “Zan ba da salama cikin ƙasar. Za ku kwanta, ba abin da zai razana ku. Zan kawar da mugayen dabbobi daga ƙasar. Ba za a ƙara yin yaƙi a ƙasarku ba. 7 Za ku runtumi maƙiyanku, za su kuwa fāɗi ta kaifin takobi a gabanku. 8 Mutum biyar ɗinku za su runtumi mutum ɗari, mutum ɗari ɗinku za su runtumi mutum dubu goma. Maƙiyanku kuwa za su fāɗi a gabanku ta kaifin takobi. 9 Zan dube ku da idon rahama, in sa muku albarka, in riɓaɓɓanya ku. Zan tabbatar muku da alkawarina. 10 Za ku girbi amfani mai yawa har kun zubar da s�nā tukuna kafin ku sami wurin ajiye sabo. 11 Zan kafa wurin zamana a tsakiyarku, ba kuwa zan gaji da ku ba. 12 Zan yi tafiya tare daku, in zama Allahnku, ku kuma ku zama mutanena. 13 Ni ne Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, don kada ku zama bayinsu. Na karya ikonsu da yake danne ku, na bar ku ku yi tafiya a sake.”

Hukuncin Rashin Biyayya

14 “Amma idan ba za ku kasa kunne gare ni ba, to, za ku sha hukunci. 15 Idan kuma kuka yi watsi da dokokina, ba ku kuwa kula da ka'idodina ba, har kuka ƙi kiyaye umarnaina, kuka karya alkawarina, 16 to, zan hukunta ku. Zan aukar muku da bala'i, da cuce-cuce da ba su warkuwa, da zazzaɓin da zai lalatar muku da ido, rai zai zama muku da wahala. Za ku yi shuka a banza gama maƙiyanku ne za su ci. 17 Zan yi gāba da ku in sa maƙiyanku su ɗibge ku, waɗanda suke ƙinku za su mallake ku. Za ku yi ta gudu ba mai korarku. 18 “Amma idan duk da haka ba ku kasa kunne gare ni ba, sai in tsananta hukuncinku har sau bakwai saboda zunubanku. 19 Zan karya ikonku wanda kuke fariya da shi, in hana ruwan sama, ƙasa kuma ta zama kamar tagulla. 20 Za ku ɓarnatar da ƙarfinku a banza gama ƙasarku ba za ta ba da amfaninta ba, itatuwan ƙasar kuma ba za su ba da 'ya'ya ba. 21 “Idan har yanzu kuka tayar mini, ba ku kasa kunne gare ni ba, sai in ƙara yawan hukuncinku har sau bakwai, saboda zunubanku. 22 Zan kuwa turo muku mugayen namomin jeji waɗanda za su kashe 'ya'yanku, su hallakar da dabbobinku, su sa ku zama kaɗan, har ba mai gilmayya a hanyoyinku. 23 “Idan wannan hukunci bai sa kun juyo gare ni ba, amma kuka ci gaba da tayar mini, 24 sai in hau ku da hukunci, har ya fi na dā riɓi bakwai saboda zunubanku. 25 Zan sa a kawo muku yaƙi saboda karya alkawarina da kuka yi. Idan kuwa kun tattaru a cikin biranenku, sai in aukar muku da masifa, in bashe ku ga maƙiyanku. 26 Zan katse abincinku, mata goma za su dafa abincinku a murhu ɗaya, su rarraba muku shi da ma'auni. Za ku ci, amma ba za ku ƙoshi ba. 27 “Amma idan duk da haka ba ku kasa kunne gare ni ba, amma kuka ci gaba da tayar mini, 28 sai ni ma in tayar muku da fushi, in hukunta ku har riɓi bakwai, saboda zunubanku. 29 Za ku ci naman 'ya'yanku mata da na 'ya'yanku maza. 30 Zan lalatar da masujadanku, in rurrushe bagaden ƙona turarenku, in jefar da gawawwakinku a kan gumakanku, raina kuwa zai ji ƙyamarku. 31 Zan sa biranenku su zama kangwaye, in mai da wuraren yin sujada kufai, ba zan shaƙi ƙanshin turarenku ba. 32 Ni zan lalatar da ƙasar har maƙiyanku da suke zaune a ciki za su yi mamaki. 33 Zan sa a kawo muku yaƙi a warwatsa ku a baƙin ƙasashe, ƙasarku za ta zama kufai, biranenku kuwa za su lalace. 34 Sa'an nan ƙasar za ta ji daɗin hutunta muddin tana zaune kango. Sa'ad da kuke a ƙasar maƙiyanku, ƙasar za ta huta, taji daɗin hutunta. 35 Muddin tana zaune kufai za ta sami hutawa, hutawa asabatan da ba ta samu ba a lokacin da kuke zaune cikinta. 36 “Amma ga waɗanda suka ragu, zan sa fargaba a zuciyarsu sa'ad da suke a ƙasar maƙiyansu. Ko motsin ganye kawai ma zai razanar da su su sheƙa a guje kamar waɗanda ake fafara da takobi, ga shi kuwa, ba mai korarsu, za sukuwa fāɗi. 37 Za su yi karo da juna kamar waɗanda suke tsere wa takobi, ko da yake ba wanda yake korarsu. Ba za su sami ikon tsaya wa maƙiyansu ba. 38 Za ku mutu a cikin al'ummai. Ƙasar maƙiyanku za ta haɗiye ku. 39 Sauranku da kuka ragu za ku lalace a ƙasashen maƙiyanku saboda muguntarku da ta kakanninku, za ku lalace kamarsu. 40 “Amma za su hurta muguntarsu da ta kakanninsu, da cin amana da suka yi mini, da kuma tayarwa da suka yi mini, 41 haka kuma ni na tayar musu, na kai su ƙasar maƙiyansu. Amma idan sun ƙasƙantar da kangararriyar zuciyarsu, suka tuba, suka bar muguntarsu, 42 sa'an nan zan tuna da alkawarina wanda na yi wa Yakubu, da Ishaku, da Ibrahim, zan kuwa tuna da ƙasar. 43 Amma za su fita daga ƙasar, ƙasar kuwa za ta ji daɗin hutunta muddin ba su ciki, tana zaman kango. Amma za su tuba saboda sun ƙi kula da ka'idodina, suka yi watsi da dokokina. 44 Duk da haka, sa'ad da suke a ƙasar maƙiyansu ba zan wulakanta su ba, ba kuwa zan ji ƙyamarsu, har da zan karya alkawarina da su ba, gama ni ne Ubangiji Allahnsu. 45 Amma saboda su zan tuna da alkawarin da na yi da kakanninsu waɗanda na fisshe su daga ƙasar Masar a idon al'ummai domin in zama Allahnsu. Ni ne Ubangiji.” 46 Waɗannan su ne dokoki, da ka'idodi, da umarnai waɗanda Ubangiji ya yi tsakaninsa da Isra'ilawa ta hannun Musa a bisa Dutsen Sina'i.

Littafin Firistoci 27

Ka'idodin Keɓewa

1 Ubangiji ya ba Musa 2 waɗannan ka'idodi domin Isra'ilawa. Idan an ba da mutum ga Ubangiji don cikar babban wa'adi za a iya fansarsa ta wurin biya waɗannan kuɗi. da aka ƙayyade za su biya bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. Masu biya Abin da za su biya Maza masu shekara 20-60 Shekel hamsin Mata masu shekara 20-60 Shekel talatin Maza masu shekara 5-20 Shekel ashirin Mata masu shekara 5-20 Shekel goma Maza masu wata guda zuwa shekara 5 Shekel biyar Mata masu wata guda zuwa shekara 5 Shekel uku Tsohon da ya fi shekara 60 Shekel goma sha biyar Tsohuwar da ta fi shekara 60 Shekel goma 8 Idan mutumin ya cika talauci har ya kasa biyan tamanin da aka kimanta, sai ya kawo mutumin da aka yi wa'adi a kansa a gaban firist, firist ɗin zai kimanta tamaninsa daidai da ƙarfin wanda ya yi wa'adin. 9 Idan kuwa dabba ce irin wadda mutane kan miƙa hadaya ga Ubangiji, dukan irin wannan da mutum yakan bayar ga Ubangiji zai zama tsattsarka. 10 Ba zai musaya shi da wani abu ba, ba zai musaya mai kyau da marar kyau, ko marar kyau da mai kyau ba. Idan kuwa ya musaya dabba da dabba, sai duka biyu, abar da aka musaya, da wadda aka musayar, za su zama tsarkakakku. 11 Idan kuwa dabbar marar tsarki ce, irin wadda ba a miƙa ta hadaya ga Ubangiji, sai mutumin ya kai dabbar a wurin firist. 12 Firist ɗin zai kimanta tamanin dabbar daidai darajarta, kamar yadda firist ya kimanta, haka zai zama. 13 Amma idan mutumin yana so ya fansa, sai ya yi ƙarin humushin tamanin da aka kimanta. 14 Idan mutum ya keɓe gidansa ga Ubangiji, sai firist ya kimanta tamanin gidan daidai darajarsa, ko gidan mai tsada ne, ko mai araha ne. Yadda shi firist ya kimanta tamaninsa, haka zai zama. 15 Idan shi wanda ya keɓe gida nasa yana so ya fansa, sai ya ƙara kashi ɗaya daga cikin biyar na tamanin da aka kimanta, gidan kuwa zai zama nasa. 16 Idan mutum ya keɓe wa Ubangiji wani sashi daga cikin gonarsa ta gādo, sai ka kimanta tamanin gonar daidai da yawan irin da zai rafa. Gonar da za a yafa iri wajen garwa ashirin na sha'ir tamaninta zai zama wajen shekel hamsin. 17 Idan ya keɓe gonarsa daga shekara ta hamsin ta murna, ba za a rage kome daga cikin tamanin gonar da aka kimanta ba. 18 Amma idan ya keɓe ta bayan shekara ta hamsin ta murna, sai firist ya kimanta yawan kuɗin bisa ga yawan shekarun da suka ragu kafin shekara ta hamsin ta murna ta kewayo. Sai a rage kuɗin tamanin gonar. 19 Idan shi wanda ya keɓe gonar yana so ya fanshe ta, to, sai ya ƙara kashi ɗaya daga cikin biyar na tamanin kuɗin gonar, gonar kuwa za ta zama tasa. 20 Amma idan ba ya so ya fanshi gonar, ko kuwa ya riga ya sayar wa wani da gonar, faufau, ba zai sāke fansarta ba. 21 Sa'ad da aka mayar da gonar a shekara ta hamsin ta murna, za ta zama tsattsarka ta ubangiji kamar gonar da aka keɓe. Firist ne zai mallaka ta. 22 Idan kuwa ya keɓe wa Ubangiji gonar da ya saya, wadda ba ta gādo ba, 23 sai firist ya kimanta tamaninta har zuwa shekara ta hamsin ta murna. Shi mutumin zai ba da yawan abin da aka kimanta a ranar, abu mai tsarki ne ga Ubangiji. 24 A cikin shekara ta hamsin ta murna, sai a mayar da gonar ga wanda aka saye ta a hannunsa, wanda gonarsa ce ta gādo. 25 Sai a kimanta tamanin kowane abu bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 26 Kowane ɗan fari na dabba na Ubangiji ne, kada wani ya fanshi sa ko tunkiya, gama na Ubangiji ne. 27 Idan dabbar marar tsarki ce, sai mai ita ya kimanta tamanin kuɗinta, ya ƙara da humushin kuɗin, ya saya. Idan ba a fansa ba, sai a sayar bisa ga tamaninta. 28 Amma iyakar abin da mutum ya ba Ubangiji ɗungum daga cikin abubuwan da yake da su, ko mutum ko dabba, ko gonarsa ta gādo, ba za a sayar ko a fansar ba, gama kowane abu da aka keɓe mafi tsarki ne ga Ubangiji. 29 Ko da mutum ne aka ba Ubangiji ɗungum, ba za a fanshe shi ba, sai a kashe shi. 30 Dukan ushirin amfanin ƙasar, ko na hatsi ne, ko na 'ya'yan itatuwa ne, na Ubangiji ne, gama tsattsarka ne ga Ubangiji. 31 Idan wani yana so ya fanshi ushiri na kowane iri, sai ya ƙara humushin tamanin ushirin. 32 Dukan ushiri na shanu, da na tumaki da awaki, duk dai dabbar da ta zama ta goma bisa ga ƙirgar makiyayan, keɓaɓɓiya ce, ta Ubangiji ce. 33 Ba ruwan kowa da kyanta ko rashin kyanta. Kada kuma a musaya ta. Idan kuwa an musaya ta, sai dai su zama tsarkakakku ga Ubangiji, ita da abar da aka yi musayar. Ba za a fanshe su ba. 34 Waɗannan su ne umarnan da Ubangiji ya ba Musa a kan Dutsen Sina'i saboda isra'ilawa.

Littafin Ƙidaya 1

Ƙidaya ta Farko a Jejin Sina'i

1 A rana ta fari ga wata na biyu a shekara ta biyu bayan da Isra'ilawa suka bar Masar, Ubangiji ya yi magana da Musa a cikin alfarwa ta sujada a jejin Sina'i. Ya ce, 2 “Da kai da Haruna ku ƙidaya Isra'ilawa, bisa ga kabilansu da iyalansu. Ku tsara sunayen dukan mazaje 3 daga mai shekara ashirin zuwa sama waɗanda suka isa zuwa yaƙi. 4 Ku roƙi shugaban kowace kabila ya taimake ku.” 5-15 Waɗannan su ne mutanen da aka zaɓa. Kabila Shugaban Kabila Ra'ubainu Elizur ɗan Shedeyur Saminu Shelumiyel ɗan Zurishaddai Yahuza Nashon ɗan Amminadab Issaka Netanel ɗan Zuwar Zabaluna Eliyab ɗan Helon Ifraimu Elishama ɗan Ammihud Manassa Gamaliyel ɗan Fedazur Biliyaminu Abidan ɗan Gideyoni Dan Ahiyezer ɗan Ammishaddai Ashiru Fagiyel ɗan Okran Gad Eliyasaf ɗan Deyuwel Naftali Ahira ɗan Enan 16 Waɗannan shugabannin kabilai waɗanda suke manya cikin kabilansu, an zaɓe su daga cikin jama'a domin wannan aiki. 17 Musa da Haruna suka ɗauki waɗannan mutane goma sha biyu, 18 suka kuma kira dukan jama'a wuri ɗaya a ran ɗaya ga watan biyu. Dukan mutanen kuwa aka rubuta su bisa ga kabilansu da iyalansu, da kuma sunayen dukan mazaje masu shekara ashirin ko fi, duk aka ƙidaya su aka rubuta, 19 kamar yadda Ubangiji ya umarta. Musa ya rubuta jama'a a jeji ta Sina'i. masu shekara ashirin ko fi da suka isa yaƙi aka rubuta su suna suna, bisa ga kabilansu da iyalansu, aka fara da kabilar Ra'ubainu, babban ɗan Yakubu. Ga yadda jimillarsu take. Kabila Jimilla Ra'ubainu (46,500 ) Dubu arba'in da shida da ɗari biyar. Saminu (59,300 ) Dubu hamsin da tara da ɗari uku. Gad (45,650 ) Dubu arba'in da biyar da ɗari shida da hamsin. Yahuza (74,600 ) Dubu saba'in da huɗu da ɗari shida. Issaka (54,400 ) Dubu hamsin da huɗu da ɗari huɗu. Zabaluna (57,400 ) Dubu hamsin da bakwai da ɗari huɗu. Ifraimu (40,500 ) Dubu arba'in da ɗari biyar. Manassa (32,200 ) Dubu talatin da biyu da ɗari biyu. Biliyaminu (35,400 ) Dubu talatin da biyar da ɗari huɗu. Dan (62,700 ) Dubu sittin da biyu da ɗari bakwai. Ashiru (41,500 ) Dubu arba'in da ɗaya da ɗari biyar. Naftali (53,400 ) Dubu hamsin da uku da ɗari huɗu. Jimilla duka (603,550 ) dubu ɗari shida da uku da ɗari biyar da hamsin.

An Ba Lawiyawa Ikon Alfarwa

47 Amma ba a rubuta Lawiyawa tare da sauran kabilai ba, 48 gama Ubangiji ya ce wa Musa, 49 “Sa'ad da kake ƙidaya Isra'ilawa, kada ka haɗa da kabilar Lawi. 50 A maimakon haka, sai ka sa Lawiyawa su zama masu lura da alfarwa ta sujada da kayayyakinta. Za su ɗauki alfarwar da kayayyakinta, su yi aikinta, a zango kuma sai su sauka kewaye da ita. 51 Sa'ad da kuka tashi tafiya, Lawiyawa za su kwankwance alfarwar, su ne kuma za su kafa ta, su ɗaɗɗaure, idan suka sauka a sabon wuri. Idan wani dabam ya zo kusa da alfarwar za a kashe shi. 52 Sauran Isra'ilawa za su sauka ƙungiya ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa a ƙarƙashin tutarsa. 53 Amma Lawiyawa za su sauka kewaye da alfarwa ta sujada don su yi tsaronta, domin kada wani dabam ya matsa kusa har ya sa in yi fushi in bugi jama'ar Isra'ila.” 54 Sai Isra'ilawa suka aikata kowane abu da Ubangiji ya umarci Musa.

Littafin Ƙidaya 2

Zango da Shugabannin Kabilai

1 Ubangiji ya ba Musa da Haruna waɗannan umarnai. 2 Duk sa'ad da Isra'ilawa suka yi zango, kowane mutum zai sauka a inda tutar ƙungiyar kabilarsa take. Zangon zai kasance a kewaye da alfarwa ta sujada. kabilar Yahuza za su sauka su kafa tutarsu a sashin gabas a ƙarƙashin jagorancin shugabanninsu, kamar haka, Kabila Shugaba Jimilla Yahuza Nashon ɗan Amminadab 74,600 Issaka Netanel ɗan Zuwar 54,400 Zabaluna Eliyab ɗan Helon 57,400 Jimilla duka, (186,400 ) dubu ɗari da tamanin da shida da ɗari huɗu. Ƙungiyoyin kabilar Yahuza su ne za su fara tafiya. kabilar Ra'ubainu za su sauka su kafa tutarsu a sashin kudu a ƙarƙashin jagorancin shugabanninsu, kamar haka, Kabila Shugaba Jimilla Ra'ubainu Elizur ɗan Shedeyur 46,500 Saminu Shelumiyel ɗan Zurishaddai 59,300 Gad Eliyasaf ɗan Deyuwel 45,650 Jimilla duka, (151,450 ) duba ɗari da hamsin da ɗaya, da ɗari huɗu da hamsin. Ƙungiyoyin kabilar Ra'ubainu za su bi bayan na Yahuza. 17 Sa'an nan Lawiyawa ɗauke da alfarwa ta sujada za su kasance a tsakanin ƙungiyoyi biyu na farko da biyun da suke daga ƙarshe. Kowace ƙungiya za ta yi tafiya kamar yadda aka dokace ta ta zauna a zango, wato kowacce ta yi tafiya a ƙarƙashin tutarta a matsayinta. kabilar Ifraimu za su sauka su kafa tutarsu a sashin yamma a ƙarƙashin jagorancin shugabanninsu, kamar haka, Kabilar Shugaba Jimilla Ifraimu Elishama ɗan Ammihud 40,500 Manassa Gamaliyel ɗan Fedazur 32,200 Biliyaminu Abidan ɗan Gideyoni 35,400 Jimilla duka, (108,100 ) dubu ɗari da takwas, da ɗari ɗaya daidai. Ƙungiyoyin Ifraimu za su zama na uku a jerin. 25-31 Ƙungiyoyin kabilar Dan za su sauka su kafa tutarsu a sashin arewa a ƙarƙashin jagorancin shugabanninsu, kamar haka, Kabila Shugaba Jimilla Dan Ahiyezer ɗan Ammishaddai 62,700 Ashiru Fagiyel ɗan Okran 41,500 Naftali Ahira ɗan Enan 53,400 Jimilla duka, (157,600 ) duba ɗari da hamsin da bakwai, da ɗari shida. Ƙungiyoyin Dan za su bi daga bayan duka. 32 Jimillar yawan Isra'ilawa da aka rubuta su a yadda suke ƙungiya ƙungiya, su dubu ɗari shida da uku da ɗari biyar da hamsin ne (603,550 ). 33 Amma kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa, ba a rubuta Lawiyawa haɗe da sauran Isra'ilawa ba. 34 Saboda haka Isra'ilawa suka yi dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa. Kowa ya yi zango a ƙarƙashin tutarsa, kowa kuma ya yi tafiya cikin jerin kabilarsa.

Littafin Ƙidaya 3

Yawan Lawiyawa da Aikinsu

1 Waɗannan su ne zuriyar Haruna da Musa lokacin da Ubangiji ya yi magana da Musa a bisa Dutsen Sina'i. 2 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Haruna, maza, Nadab ɗan fari, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar. 3 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Haruna, maza, da aka naɗa firistoci domin su yi aikin firist. 4 Amma Nadab da Abihu sun mutu a gaban Ubangiji a jejin Sina'i, a sa'ad da suka ƙona turare da haramtacciyar wuta. Sun mutu, ba su da 'ya'ya, saboda haka Ele'azara da Itamar suka yi aikin firist su kaɗai a zamanin mahaifinsu Haruna. 5 Ubangiji ya ce wa Musa, 6 “Kawo kabilar Lawiyawa kusa, ka sa su su yi aiki tare da Haruna, firist. 7 Sai su yi wa firistoci da dukan jama'a aiki a gaban alfarwa ta sujada. 8 Su za su lura da kayayyakin alfarwa ta sujada su kuma yi wa Isra'ilawa aiki. 9 Abin da Lawiyawa za su yi, shi ne su yi wa Haruna da 'ya'yansa aiki. 10 Ka sa Haruna da 'ya'yansa maza, su kula da aikinsu na firist, idan kuwa wani mutum dabam ya yi ƙoƙarin yin wannan aiki, to, za a kashe shi.” 11 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 12 “Ga shi, na ɗauki Lawiyawa daga cikin Isra'ilawa a maimakon kowane ɗan farin da ya buɗe mahaifa daga cikin mutanen Isra'ila. Lawiyawa za su zama nawa. 13 Gama 'yan fari duka nawa ne, tun daga ranar da na kashe 'ya'yan fari na ƙasar Masar, na keɓe wa kaina duk ɗan fari na Isra'ila, na mutum da na dabba. Za su zama nawa, ni ne Ubangiji.” 14 Ubangiji ya yi magana da Musa a jejin Sina'i, ya ce masa 15 ya ƙidaya mazaje na kabilar Lawi bisa ga gidajen kakanninsu da iyalansu, tun daga mai wata ɗaya zuwa gaba. 16 Haka Musa ya ƙidaya su bisa ga maganar Ubangiji, kamar yadda ya umarce shi. 17 Waɗannan su ne 'ya'yan Lawi, maza, bisa ga sunayensu, da Gershon, da Kohat, da Merari. 18 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Gershon, maza, bisa ga iyalansu, Libni da Shimai. 19 Ga 'ya'yan Kohat, maza, bisa ga iyalansu, da Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel. 20 Ga kuma 'ya'yan Merari, maza, bisa ga iyalansu, da Mali da Mushi. Waɗannan su ne iyalan Lawi bisa ga gidajen kakanninsu. 21 Iyalin Libnawa, da na Shimaiyawa su ne iyalan Gershon. 22 Jimillarsa tun daga ɗa namiji mai wata ɗaya zuwa gaba, mutum dubu bakwai ne da ɗari biyar (7,500 ). 23 Iyalan Gershonawa za su yi zango a bayan alfarwar daga yamma. 24 Eliyasaf, ɗan Layel, shi ne shugaban gidan kakanninsa, Gershonawa. 25 'Ya'yan Gershon, maza, su ne da aikin lura da alfarwa ta sujada da murfinta na ciki da na waje, da labulen ƙofar, 26 da labulen farfajiya da yake kewaye da alfarwar, da bagade, da labulen ƙofar farfajiyar. Su za su lura da dukan aikin da ya shafi waɗannan abubuwa. 27 Iyalan Kohat su ne iyalin Amramawa, da na Izharawa, da na Hebronawa, da na Uzziyelawa. Waɗannan su ne iyalan Kohatawa. 28 Lissafin mazaje duka, tun daga mai wata ɗaya zuwa gaba, su dubu takwas ne da ɗari shida (8,600 ). 29 Iyalan 'ya'yan Kohat za su kafa zangonsu a kudancin alfarwar. 30 Elizafan ɗan Uzziyel shi ne shugaban gidan kakanninsa, Kohatawa. 31 Aikinsu shi ne lura da akwatin alkawari, da tebur, da alkuki, da bagadai, da kayayyakin Wuri Mai Tsarki waɗanda firistoci suke aiki da su, da labule, da dukan aikin da ya shafi waɗannan abubuwa. 32 Ele'azara, ɗan Haruna, firist, shi zai shugabanci shugabannin Lawiyawa, shi ne kuma zai lura da waɗanda suke aiki a Wuri Mai Tsarki. 33 Iyalan Merari su ne iyalin Maliyawa, da na Mushiyawa. Waɗannan su ne iyalan Merari. 34 Yawan mazajensu duka da aka ƙidaya tun daga mai wata ɗaya zuwa gaba, mutum dubu shida ne da ɗari biyu (6,200 ). 35 Shugaban gidan kakannin iyalan Merari kuwa shi ne Zuriyel, ɗan Abihail. Za su kafa zangonsu a arewacin alfarwar. 36 Aikin da aka danƙa wa 'ya'yan Merari shi ne lura da katakan alfarwar, da sanduna, da dirkoki, da kwasfa, da sauran abubuwa duka, da duk ayyukan da suka shafi waɗannan, 37 da kuma dirkoki na farfajiyar da ta kewaye wurin, da kwasfa da turaku da igiyoyinsu. 38 Waɗanda za su yi zango a gaban alfarwa ta sujada daga gabas, su ne Musa, da Haruna da 'ya'yansa maza, waɗanda aka danƙa musu tafiyar da aikin Wuri Mai Tsarki, da dukan aikin da za a yi wa Isra'ilawa. Banda su, duk wanda ya je kusa da wurin sai a kashe shi. 39 Dukan Lawiyawa waɗanda Musa da Haruna suka ƙidaya bisa ga iyalansu, bisa ga umarnin Ubangiji, tun daga mai wata ɗaya zuwa gaba, mazaje dubu ashirin da dubu biyu ne (22,000 ).

An Fanshi 'Ya'yan Fari Maza

40 Sai kuma Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙidaya dukan 'ya'yan fari maza na Isra'ilawa, tun daga wata ɗaya zuwa mai gaba, ka rubuta sunayensu. 41 Za ka keɓe mini Lawiyawa a maimakon 'ya'yan fari maza na Isra'ilawa. Dabbobin Lawiyawa za su zama nawa a maimakon dukan 'ya'yan farin dabbobin Isra'ilawa. Ni ne Ubangiji.” 42 Sai Musa ya ƙidaya 'ya'yan fari maza na Isra'ilawa, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 43 Jimillar 'ya'yan fari maza da aka ƙidaya bisa ga sunayensu tun daga mai wata ɗaya zuwa gaba, mutum dubu ashirin da biyu, da ɗari biyu da saba'in da uku ne (22,273 ). 44 Ubangiji kuma ya yi magana da Musa, ya ce, 45 “Ka keɓe Lawiyawa a maimakon dukan 'ya'yan fari na Isra'ilawa. Dabbobin Lawiyawa kuma za su zama a maimakon 'ya'yan farin dabbobin Isra'ilawa. Lawiyawa kuwa za su zama nawa. Ni ne Ubangiji. 46 'Ya'yan fari maza na Isra'ilawa sun fi Lawiyawa da mutum ɗari biyu da saba'in da uku. Sai a fanshi wannan ragowa. 47 Ka karɓi shekel biyar a kan kowane mutum, bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 48 Sai ka ba da kuɗin fansar ga Haruna da 'ya'yansa maza.” 49 Musa kuwa ya karɓi kuɗin fansar waɗanda suka haura yawan Lawiyawa. 50 Kuɗin da ya karɓa daga 'ya'yan fari na Isra'ilawa da suka haura yawan Lawiyawa shekel dubu ɗaya da ɗari uku da sittin da biyar (1,365 ) bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 51 Musa kuwa ya ba Haruna da 'ya'yansa maza kuɗin fansa bisa ga maganar Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Littafin Ƙidaya 4

Ayyukan da aka Danƙa wa Iyalin Kohat

1 Ubangiji ya faɗa wa Musa da Haruna, 2 su ƙidaya 'ya'yan Kohat, maza, daga cikin 'ya'yan Lawi bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu, 3 su ƙidaya daga mai shekara talatin zuwa hamsin, wato waɗanda suka isa su yi aiki a alfarwa ta sujada. 4 Wannan shi ne aikin 'ya'yan Kohat, maza, a cikin alfarwa ta sujada a kan abubuwa mafi tsarki. 5 Sa'ad da za a tashi daga zango, sai Haruna, tare da 'ya'yansa maza, su shiga cikin alfarwa, su kwance labulen kāriya, su rufe akwatin alkawari da shi. 6 Sa'an nan kuma su rufe shi da fatun awaki, su kuma shimfiɗa shuɗin zane a bisansa, su zura masa sandunansa. 7 Sai su shimfiɗa shuɗin zane a kan tebur na gurasar ajiyewa, sa'an nan su d�biya faranta, da cokula, da kwanonin, da butocin hadaya ta sha, da gurasar ajiyewa. 8 Sa'an nan su rufe su da jan zane, a kuma rufe su da fatun awaki, sa'an nan su zura masa sandunansa. 9 Su kuma ɗauki shuɗin zane su rufe alkuki, da fitilunsa, da hantsukansa, da farantansa, da dukan kwanonin man da akan zuba masa. 10 Sai su sa alkukin da dukan kayayyakinsa a cikin fatar awaki su naɗe, su sarƙafa shi asandan ɗaukarsa. 11 A rufe bagaden zinariya da shuɗin zane, a kuma rufe shi da fatun awaki, sa'an nan a zura sandunan ɗaukarsa. 12 Su ɗauki dukan kwanonin da ake amfani da su a Wuri Mai Tsarki, su sa su cikin shuɗin zane, sa'an nan su rufe su da fatun awaki, a sarƙafa su a sanda don a ɗauka. 13 Za su kwashe tokar da take cikin bagaden, su rufe bagaden da shunayyan zane. 14 Sa'an nan su sa dukan kayayyakin bagaden a kansa waɗanda ake aiki da su a wurin, wato su farantai don wuta, da cokula masu yatsotsi, da manyan cokula, da daruna da dai dukan kayayyakin bagaden. Su kuma rufe bagaden da fatun awaki, sa'an nan su zura sandunan ɗaukarsa. 15 Sa'ad da Haruna da 'ya'yansa maza suka gama kintsa Wuri Mai Tsarki da kayayyakinsa duka a lokacin tashi, sai 'ya'yan Kohat, maza, su zo su ɗauke kayayyakin, amma kada su taɓa abubuwan nan masu tsarki domin kada su mutu. Waɗannan su ne ayyukan 'ya'yan Kohat a duk lokacin da za a naɗe alfarwa ta sujada. 16 Ele'azara kuwa, ɗan Haruna, firist, shi ne zai lura da man fitila, da turare, da hadayar gari ta kullum, da man keɓewa, ya kuma kula da dukan alfarwar, da duk abin da ke cikinta, da Wuri Mai Tsarki, da kayayyakinsa. 17 Sai Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna, 18 “Kada ku bar zuriyar Kohat 19 ta hallaka ta wurin kusatar waɗannan tsarkakakkun abubuwa. Maganin abin, shi ne sai Haruna da 'ya'yansa maza, su shiga, su nuna wa kowannensu irin aikin da zai yi, da kayan da zai ɗauka. 20 Amma idan Kohatawa suka shiga alfarwar suka tarar firistoci suna shisshirya tsarkakakkun abubuwa don tashi, har dai in sun gani, to za su mutu.”

Ayyukan Gershonawa

21 Ubangiji ya kuma faɗa wa Musa, 22 ya ƙidaya 'ya'yan Gershon, maza, bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu 23 ya rubuta su tun daga mai shekara talatin, har zuwa mai shekara hamsin, duk wanda ya isa yin aikin da zai yi a alfarwa ta sujada. 24 Wannan shi ne aikin da iyalan Gershonawa za su yi wajen ɗaukar kaya. 25 Za su ɗauki alfarwa ta sujada, da labule na ciki da na waje, da murfi na fatun tumaki wanda yake a bisa alfarwar, da kuma labulen ƙofar alfarwa ta sujada, 26 da labulen farfajiya, da labulen ƙofar farfajiya wadda ta kewaye alfarwar da bagaden, da igiyoyinsu, da duk kayayyakinsu na yin aiki. Sai su yi dukan abin da ya kamata a yi da su. 27 Haruna ne da 'ya'yansa maza za su nuna wa 'ya'yan Gershonawa irin aikin da za su yi, da kayayyakin da za su ɗauka. Sai a faɗa musu dukan abin da za su yi, da dukan abinda za su ɗauka. 28 Wannan shi ne aikin da iyalan Gershonawa za su yi a alfarwa ta sujada. Itamar ɗan Haruna, firist, shi zai shugabance su cikin aikin da za su yi.

Ayyukan Merariyawa

29 Ubangiji kuma ya faɗa wa Musa ya ƙidaya Merariyawa bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu, 30 ya rubuta su tun daga mai shekara talatin, har zuwa mai shekara hamsin, duk wanda ya isa yin aikin da zai yi a alfarwa ta sujada. 31 Wannan shi ne abin da aka umarce su su riƙa ɗauka na wajen aikinsu a alfarwa ta sujada, katakan alfarwar, da sandunanta, da dirkokinta, da kwasfanta, 32 da dirkokin farfajiya wadda take kewaye da alfarwar, da kwasfansu, da turakunsu, da igiyoyi, da dukan kayayyakinsu. Sai ya faɗa wa kowa kayan da zai ɗauka. 33 Wannan shi ne aikin iyalan 'ya'yan Merari, maza. Aikinsu ke nan duka a alfarwa ta sujada. Itamar ɗan Haruna, firist, shi ne zai shugabance su.

Yawan Lawiyawa

34-48 Musa da Haruna da shugabannin taron jama'a kuwa suka ƙidaya iyalan Lawiyawa uku, wato Kohatawa, da Gershonawa da Merariyawa bisa ga iyalansu da gidajen kakanninsu, aka rubuta dukan mazaje daga mai shekara talatin zuwa mai shekara hamsin, waɗanda za su iya aiki a alfarwa ta sujada, kamar haka, Kohat dubu biyu da ɗari bakwai da hamsin (2,750 ), Gershon dubu biyu da ɗari shida da talatin (2,630 ), Merari dubu uku da ɗari biyu (3,200 ), Jimilla duka, dubu takwas da ɗari biyar da tamanin (8,580 ). 49 Aka ba kowannensu aikinsa da ɗaukar kaya bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa. Haka kuwa aka ƙidaya su kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Littafin Ƙidaya 5

Ƙazantattun Mutane

1 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Ka umarci Isra'ilawa su fitar da kuturu, da mai ɗiga, da wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, daga cikin zango. 3 Su fitar da mace ko namiji daga cikin zango, don kada su ƙazantar da zangonku inda nake zaune.” 4 Sai Isra'ilawa suka fitar da su daga cikin zango kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Musa. Haka mutanen Isra'ila suka yi.

Biyan Diyya saboda Ɓarna

5 Ubangiji kuma ya ba Musa 6 waɗannan ka'idodi domin Isra'ilawa. Idan wani ya aikata rashin gaskiya ga Ubangiji, ta wurin saɓa wa wani, 7 sai ya hurta zunubinsa, sa'an nan ya biya cikakkiyar diyyar abin da ƙarin humushin abin, ya ba mutumin da ya yi wa laifin. 8 Idan wanda ya yi wa laifin ya rasu, ba shi kuma da wani dangi na kusa wanda za a ba diyyar, sai a kai diyyar gaban Ubangiji domin firist, tare da ragon hadaya, don yin kafarar da za a yi masa. 9 Dukan sadakoki na tsarkakakkun abubuwa na Isra'ilawa waɗanda sukan kawo wa firist, za su zama nasa. 10 Kowane firist zai adana sadakokin da aka ba shi.

Matsalar Miji mai Kishi

11 Ubangiji kuma ya umarci Musa faɗa wa Isra'ilawa waɗannan ka'idodi. Idan mutum yana shayin matarsa kan tana yi masa rashin aminci, har ta ƙazantar da kanta ta wurin kwana da wani mutum, amma mijin bai tabbatar ba, domin ta yi abin a asirce, ba kuwa mai shaida, ba a kuma kama ta tana cikin yi ba, ko kuma mijin ya yi shayinta ko da ba ta aikata irin wannan laifi ba, 15 duk da haka sai mutum ya kawo matarsa a gaban firist, ya kawo kuma hadayar da ake bukata, wato humushin garwar garin sha'ir, amma kada ya zuba mai ko kayan ƙanshi, gama hadaya ce domin kishi, domin a bayyana gaskiya a fili. 16 Sai firist ya kawo ta kusa, ya tsai da ita a gaban Ubangiji. 17 Ya ɗebo ruwa mai tsarki a cikin kasko, ya kuma ɗauki ƙurar ƙasar da take a alfarwa ta alkawari ya zuba a ruwan. 18 Sa'an nan firist zai kwance gashin kanta, ya sa hadaya ta gari don tunawa a hannuwanta, hadayar gari ce ta kishi. Ya riƙe ruwan nan mai ɗaci da yake kawo la'ana a hannunsa. 19 Sa'an nan zai sa ta ta yi rantsuwa, ya ce mata, “Idan wani mutum bai kwana da ke ba, to, bari ki kuɓuta daga la'anar da ruwan nan mai ɗaci zai kawo. 20 Amma idan kin kwana da wani mutum wanda ba mijinki ba ne, 21 bari Ubangiji ya sa sunanki ya la'antu cikin jama'arki, ya sa cinyarki ta shanye, cikinki kuma ya kumbure. 22 Bari ruwan nan ya shiga cikinki, ya sa cikinki ya kumbure, cinyarki kuma ta shanye.” Sai matar ta amsa, ta ce, “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka.” 23 Firist ɗin zai rubuta waɗannan la'anoni a cikin littafi sa'an nan ya wanke rubutun da ruwan nan mai ɗaci. 24 Ya sa matar ta shanye ruwa wanda yake kawo la'ana, sai ruwan ya shiga cikinta, ya zama la'ana mai ɗaci. 25 Firist kuma zai karɓi hadaya ta gari don kishi a hannun matar, ya kaɗa ta a gaban Ubangiji. Sa'an nan ya kai wurin bagade. 26 Sai ya ɗibi garin hadaya cike da tafin hannu don yin hadayar tunawa, ya ƙone shi a bisa bagaden, bayan wannan ya sa matar ta sha ruwan. 27 Bayan da ya sa ta ta sha ruwan, idan ta ƙazantar da kanta, ta kuwa ci amanar mijinta, ruwan nan mai kawo la'ana zai shiga cikinta ya zama la'ana mai ɗaci, cikinta zai kumbure, cinyarta ta shanye, matar kuwa za ta zama la'ananniya cikin jama'arta. 28 Amma idan matar ba ta ƙazantar da kanta ba, ita tsattsarka ce, za ta kuɓuta, har ta haifi 'ya'ya. 29 Wannan ita ce dokar kishi idan mutum yana shayin matarsa, wai wani yana kwana da ita. 30 Matar kuwa za ta tsaya a gaban Ubangiji, firist kuwa zai yi da ita bisa ga wannan doka duka. 31 Mijin zai kuɓuta daga muguntar, amma matar za ta ɗauki muguntarta, idan ta yi laifin.

Littafin Ƙidaya 6

Ka'idodin Zama Keɓaɓɓe

1 Ubangiji kuma ya umarci Musa 2 ya faɗa wa Isra'ilawa, cewa idan mace ko namiji ya ɗau wa'adi na musamman na zama keɓaɓɓe domin ya keɓe kansa ga Ubangiji, 3 sai ya keɓe kansa daga ruwan inabin da yake sa maye da ruwan inabi mai tsami. Kada kuma ya sha ruwan inabi mai tsami da yake sa maye da kowane irin abin sha da aka yi da 'ya'yan inabi mai tsami. Kada kuma ya ci ɗanyu ko busassun 'ya'yan inabi. 4 A dukan kwanakin nan da ya keɓe kansa, kada ya ci kowane irin abu da aka yi da kurangar inabi, ko da ƙwayar inabi ko da ɓawonsa. 5 A dukan kwanakin wa'adinsa na keɓewa, kada aska ta taɓa kansa, sai kwanakin keɓewar kansa ga Ubangiji sun cika. Zai zama mai tsarki, zai kuma bar sumarsa ta yi tsawo. 6 A dukan kwanakin da ya keɓe kansa ga Ubangiji, kada ya kusaci gawa. 7 Ko ta mahaifinsa ce, ko ta mahaifiyarsa, ko ta ɗan'uwansa, ko ta 'yar'uwarsa, ba zai ƙazantar da kansa ba, tun da yake ya keɓe kansa ga Allahnsa. 8 Shi tsattsarka ne ga Ubangiji dukan kwanakin da ya keɓe kansa. 9 Idan farat ɗaya wani mutum ya rasu kusa da shi, to, keɓewarsa ta ƙazantu, sai ya aske kansa a ranar tsarkakewarsa a kan rana ta bakwai. 10 A rana ta takwas kuwa zai kawo wa firist 'yan kurciyoyi biyu, ko 'yan tattabarai biyu a bakin ƙofar alfarwa ta sujada. 11 Sai firist ya miƙa ɗaya don hadayar zunubi, ɗaya kuma don hadayar ƙonawa, ya yi kafara dominsa, gama ya yi zunubi saboda gawa. A wannan rana zai sāke keɓe kansa. 12 Sai ya sāke keɓe kansa ga Ubangiji daidai da kwanakin da ya ɗauka a dā. Zai kawo ɗan rago bana ɗaya na yin hadaya don laifi. Kwanakin da ya yi a dā ba su cikin lissafi domin keɓewarsa ta dā ta ƙazantu. 13 Wannan ita ce ka'idar zama keɓaɓɓe a ranar da keɓewarsa ta cika. Za a kai shi ƙofar alfarwa ta sujada, 14 ya miƙa wa Ubangiji hadayarsa ta ɗan rago bana ɗaya mara lahani don yin hadaya ta ƙonawa, da 'yar tunkiya bana ɗaya marar lahani ta yin hadaya don zunubi, da rago marar lahani don yin hadaya ta salama, 15 da kwandon abinci marar yisti da aka yi da lallausan gari kwaɓaɓɓe da mai, da ƙosai wanda aka yayyafa masa mai, da hadaya ta gari, da hadayu na sha. 16 Sai firist ɗin ya kai su gaban Ubangiji, ya miƙa hadaya don zunubi, da hadaya ta ƙonawa. 17 Ya kuma miƙa rago don hadaya ta salama ga Ubangiji tare da kwandon abinci, da ƙosai. Firist ɗin kuma zai miƙa hadaya ta gari, da hadaya ta sha. 18 Sai kuma keɓaɓɓen ya aske sumarsa a ƙofar alfarwa ta sujada, sa'an nan ya kwashe sumar, ya zuba cikin wutar da take ƙarƙashin hadaya ta salama. 19 Firist ɗin zai ɗauki dafaffiyar kafaɗar ragon, da malmala guda marar yisti daga cikin kwando, da ƙosai guda, ya sa su a tafin hannun keɓaɓɓen bayan da keɓaɓɓen ya riga ya aske sumarsa. 20 Firist ɗin zai haɗa su don yin hadayar kaɗawa a gaban Ubangiji. Za su zama rabo mai tsarki na firist tare da ƙirjin da aka kaɗa da cinyar da aka yi hadayar ɗagawa da ita. Bayan haka keɓaɓɓen ya iya shan ruwan inabi. 21 Wannan ita ce ka'ida a kan keɓaɓɓe wanda ya ɗau wa'adi. Hadayarsa ga Ubangiji za ta zama bisa ga keɓewarsa, banda kuma abin da ya iya bayarwa. Sai ya cika wa'adin da ya ɗauka bisa ga ka'idar keɓewarsa.

Albarkar da Firist zai Sa wa Jama'a

22 Ubangiji ya umarci Musa 23 ya faɗa wa Haruna da 'ya'yansa maza, su sa wa Isra'ilawa albarka haka, su ce musu, 24 “Ubangiji ya sa muku albarka, ya kiyaye ku. 25 Ubangiji ya sa fuskarsa ta haskaka ku, ya yi muku alheri. 26 Ubangiji ya dube ku da idon rahama, ya ba ku salama.” 27 Idan suka sa wa jama'a wannan albarka sa'ad da suke addu'a ga Ubangiji domin Isra'ilawa, Ubangiji zai sa musu albarka.

Littafin Ƙidaya 7

Hadayun Keɓe Bagade

1 A ranar da Musa ya gama kafa alfarwa ta sujada, ya shafa mata mai, ya tsarkake ta, da dukan kayayyakinta, ya kuma shafa wa bagaden mai, ya tsarkake shi da dukan kayayyakinsa. 2 Sai shugabannin Isra'ila, wato shugabannin gidajen kakanninsu, su ne shugabannin kabilansu, waɗanda suka shugabanci waɗannan da aka ƙidaya, 3 suka kawo hadayarsu a gaban Ubangiji, karusai shida rufaffu, da takarkarai goma sha biyu. Shugabanni biyu suka ba da karusa ɗaya, kowannensu kuwa ya ba da takarkari ɗaya, da suka gama miƙa su, 4 sai Ubangiji ya ce wa Musa, 5 “Karɓi waɗannan daga gare su domin a yi aiki da su a alfarwa ta sujada. Ka ba da su ga Lawiyawa, a ba kowane mutum bisa ga aikinsa.” 6 Musa kuwa ya karɓi karusan, da takarkaran, ya ba Lawiyawa. 7 Ya ba 'ya'ya maza na Gershon karusai biyu da takarkarai huɗu bisa ga aikinsu. 8 Ya kuwa ba 'ya'ya maza na Merari karusai huɗu da takarkarai takwas bisa ga aikinsu, a hannun Itamar ɗan Haruna, firist. 9 Amma bai ba 'ya'ya maza na Kohat kome ba, domin aikinsu shi ne lura da kayayyaki masu tsarki waɗanda ake ɗauka a kafaɗa. 10 Sai shugabanni suka miƙa hadayu domin keɓewar bagade a ranar da aka zuba masa mai. Suka fara miƙa sadakokinsu a bagaden, 11 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, “Bari shugabannin su kawo hadayunsa domin keɓewar bagade, har kwana sha biyu, kowa a ranarsa.” miƙa hadayunsu bi da bi kamar haka, Kabila Shugaba Yahuza Nashon ɗan Amminadab Issaka Netanel ɗan Zuwar Zabaluna Eliyab ɗan Helon Ra'ubainu Elizur ɗan Shedeyur Saminu Shelumiyel ɗan Zurishaddai Gad Eliyasaf ɗan Deyuwel Ifraimu Elishama ɗan Ammihud Manassa Gamaliyel ɗan Fedazur Biliyaminu Abidan ɗan Gideyoni Dan Ahiyezer ɗan Ammishaddai Ashiru Fagiyel ɗan Okran Naftali Ahira ɗan Enan Hadayun da kowannensu ya kawo duk daidai da juna suke, farantin azurfa na shekel ɗari da talatin, da kwanon azurfa na shekel saba'in, bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi, duka suna cike da garin da aka kwaɓa da mai domin hadaya ta gari, cokali na zinariya guda na shekel goma, cike da kayan ƙanshi, da ɗan bijimi guda, da rago ɗaya, da ɗan rago bana ɗaya domin hadaya ta ƙonawa, da akuya guda domin hadaya ta zunubi, da bijimai biyu, da raguna biyar, da awaki biyar, da 'yan raguna biyar bana ɗaya ɗaya, domin hadaya ta salama. 84-88 Ga jimillar hadayun da shugabanni goma sha biyu suka kawo domin keɓewar bagaden: farantan azurfa goma sha biyu da kwanonin azurfa goma sha biyu, duka nauyinsu shekel dubu biyu da ɗari huɗu cokulan zinariya goma sha biyu, nauyinsu duka shekel ɗari da ashirin cike da kayan ƙanshi bijimai goma sha biyu, da raguna goma sha biyu, da 'yan raguna goma sha biyu bana ɗaya ɗaya, da kuma hadaya ta gari da za a haɗa da waɗannan domin hadaya ta ƙonawa awaki goma sha biyu domin hadaya don zunubi bijimai ashirin da huɗu, da raguna sittin, da awaki sittin, da 'yan raguna bana ɗaya ɗaya guda sittin domin hadaya ta salama. 89 Duk lokacin da Musa ya shiga alfarwa ta sujada domin ya yi magana da Ubangiji, sai ya ji Ubangiji yana magana da shi daga bisa murfin akwatin alkawari, a tsakanin kerubobi masu fikafikai biyu.

Littafin Ƙidaya 8

Haruna ya Kakkafa Fitilu

1 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa ya 2 faɗa wa Haruna cewa, “Sa'ad da za ka kakkafa fitilun nan bakwai, sai ka kakkafa su yadda za su haskaka sashin gaba.” 3 Haka kuwa Haruna ya yi. Ya kakkafa fitilun yadda za su haskaka a gaban alkukin, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 4 Da zinariya aka ƙera alkukin tun daga samansa har gindinsa, bisa ga fasalin da Ubangiji ya nuna wa Musa.

Keɓewar Lawiyawa

5 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, 6 “Keɓe Lawiyawa daga cikin Isra'ilawa ka tsarkake su. 7 Ga yadda za ka tsarkake su. Ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa. Su aske jikunansu duka, su kuma a wanke tufafinsu, sa'an nan za su tsarkaka. 8 Su kuma ɗauki maraƙi tare da lallausan garin hadaya kwaɓaɓɓe da mai. Kai kuma ka ɗauki wani maraƙi na yin hadaya don zunubi. 9 Sa'an nan ka gabatar da Lawiyawa a gaban alfarwa ta sujada, ka kira taron Isra'ilawa duka. 10 Sa'ad da ka gabatar da Lawiyawa a gaban Ubangiji, sai Isra'ilawa su ɗibiya hannuwansu bisa Lawiyawa. 11 Haruna kuma zai gabatar da Lawiyawan a gaban Ubangiji kamar hadaya ta kaɗawa daga Isra'ilawa domin su zama masu yi wa Ubangiji aiki. 12 Sa'an nan Lawiyawa za su ɗibiya hannuwansu a bisa kawunan maruƙan. Za ka yi hadaya domin zunubi da maraƙi ɗaya, ɗaya kuma ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji domin ka yi kafara saboda Lawiyawa. 13 “Za ka keɓe Lawiyawa su zama kamar hadaya ta kaɗawa gare ni, ka sa Haruna da 'ya'yansa maza su lura da su. 14 Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga cikin Isra'ilawa su zama nawa. 15 Bayan da ka tsarkake su, ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, za su cancanta su yi aiki a alfarwa ta sujada. 16 Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra'ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato dukan 'ya'yan farin Isra'ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa. 17 A ranar da na kashe 'ya'yan fari na ƙasar Masar, na keɓe wa kaina dukan 'ya'yan fari na Isra'ilawa, na mutum, da na dabba. 18 Na kuwa keɓe wa kaina Lawiyawa a maimakon dukan 'ya'yan fari na Isra'ilawa. 19 Daga cikin Isra'ilawa kuwa na ba da Lawiyawa ga Haruna da 'ya'yansa maza don su yi wa Isra'ilawa hidima a alfarwa ta sujada, su kuma yi kafara dominsu don kada annoba ta sami Isra'ilawa sa'ad da suka kusaci alfarwa ta sujada.” 20 Musa da Haruna kuwa da dukan taron Isra'ilawa suka yi wa Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarce Musa, haka kuwa Isra'ilawa suka yi musu. 21 Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka wanke tufafinsu. Haruna kuwa ya keɓe su, suka zama kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji, ya kuma yi kafara dominsu don ya tsarkake su. 22 Bayan haka Lawiyawa suka shiga alfarwa ta sujada don su yi aiki a gaban Haruna da 'ya'yansa maza, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa a kan Lawiyawa, haka kuwa suka yi musu.

Adadin yawan Shekarun Aikin Lawiyawa

23 Ubangiji ya kuma ce wa Musa, 24 “Wannan ita ce ka'idar aikin Lawiyawa, tun daga mai shekara ashirin da biyar zuwa gaba, zai shiga yin aiki a alfarwa ta sujada. 25 Amma daga shekara hamsin, sai su huta daga aiki alfarwa ta sujada. 26 Amma su taimaki 'yan'uwansu da tafiyar da ayyuka a cikin alfarwa ta sujada, sai dai ba za su ɗauki nauyin gudanar da aikin ba. Haka za ka shirya wa Lawiyawa aikinsu.”

Littafin Ƙidaya 9

Idin Ƙetarewa na Biyu

1 Sai Ubangiji ya yi wa Musa magana a jejin Sina'i a watan farko na shekara ta biyu bayan fitarsu daga ƙasar Masar, ya ce, 2 “Sai Isra'ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa a ƙayyadadden lokacinsa. 3 A rana ta goma sha huɗu ga wannan wata, da maraice za su kiyaye shi a ƙayyadadden lokacinsa bisa ga dokokinsa da ka'idodinsa duka.” 4 Musa kuwa ya faɗa wa Isra'ilawa su kiyaye Idin Ƙetarewa. 5 Sai suka kiyaye Idin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu ga watan farko da maraice a cikin jejin Sina'i bisa ga dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa. Haka kuwa Isra'ilawa suka yi. 6 Akwai waɗansu mutane da suka ƙazantu ta wurin taɓa gawar wani mutum, don haka ba su iya kiyaye Idin Ƙetarewar a ranar ba. Sai suka zo wurin Musa da Haruna a ranar, 7 suka ce masa, “Ai, mun ƙazantu saboda mun taɓa gawa. Me ya sa aka hana mu mu ba da hadaya ga Ubangiji tare da sauran 'yan'uwanmu a ƙayyadadden lokacin yinta?” 8 Sai Musa ya ce musu, “Dakata, har na ji abin da Ubangiji zai umarta a kanku.” 9 Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa 10 ya faɗa wa Isra'ilawa ya ce, “Idan wani mutum na cikinku, ko na cikin zuriyarku, ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ko kuwa ya yi tafiya mai nisa, duk da haka zai kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji. 11 Za su kiyaye shi da maraice a watan biyu yana da kwana goma sha huɗu. Za su ci shi da abinci marar yisti da ganyaye masu ɗaci. 12 Kada su bar kome daga cikinsa ya kai gobe, kada kuwa a fasa ƙashinsa, sai su yi shi bisa ga dukan umarnin Idin Ƙetarewa. 13 Amma mutumin da yake da tsarki, bai kuma yi tafiya ba, ya kuwa ƙi kiyaye Idin Ƙetarewa, sai a raba wannan mutum da jama'arsa, gama bai miƙa hadayar Ubangiji a ƙayyadadden lokacin yinta ba. Wannan mutum zai ɗauki alhakin zunubinsa. 14 “Idan baƙo yana zaune a wurinku, shi ma sai ya kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji bisa ga umarnai da ka'idodi na Idin Ƙetarewa. Ka'ida ɗaya ce ga baƙo da ɗan gari.”

Girgijen Wuta

15-16 A ranar da aka kafa alfarwa ta sujada, sai girgije ya sauko ya rufe ta. Da maraice kuwa girgijen yana kamar wuta. 17 A duk lokacin da aka gusar da girgijen, sai Isra'ilawa su kama hanya. A inda girgijen ya tsaya, nan kuma Isra'ilawa za su kafa zango. 18 Da umarnin Ubangiji Isra'ilawa suke tashi, da umarninsa kuma suke sauka. Muddin girgijen yana bisa alfarwar, sukan yi ta zamansu a zangon. 19 Ko da girgije ya daɗe a bisa alfarwar Isra'ilawa ba sukan tashi ba, sukan bi umarnin Ubangiji. 20 Wani lokaci girgijen yakan yi 'yan kwanaki ne kawai bisa alfarwar. Tashinsu da zamansu sun danganta ga umarnin Ubangiji. 21 Wani lokaci girgijen yakan zauna a bisa alfarwar daga maraice zuwa safiya ne kawai, sa'an nan ya tashi, su kuma sai su tashi. Amma idan girgijen ya yini, ya kwana, sa'an nan ya tashi, su kuma sai su tashi. 22 Ko kwana biyu ne girgijen ya yi, yana zaune a bisa alfarwar ko wata guda, ko fi, sai Isra'ilawa su yi ta zamansu a zangon, ba za su tashi ba. Amma in ya tashi, sai su kuma su tashi. 23 Da umarnin Ubangiji suke sauka, da umarninsa kuma suke tashi, suna bin faɗarsa, yadda ya umarci Musa.

Littafin Ƙidaya 10

Kakaki na Azurfa

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 2 “Ka ƙera kakaki biyu na azurfa don ka riƙa kirawo taron jama'a, don kuma ka riƙa sanashe su lokacin tashi daga zangon. 3 Lokacin da aka busa kakaki biyu ɗin gaba ɗaya, sai taron jama'a duka su tattaru a wurinka a ƙofar alfarwa ta sujada. 4 Amma idan ɗaya kaɗai aka busa, sai shugabannin Isra'ila su tattaru a wurinka. 5 Sa'ad da kuka yi busar faɗakarwa, waɗanda suke zaune a gabashin zangon za su tashi. 6 Sa'ad da kuma kuka yi busar faɗakarwa ta biyu, waɗanda suke a kudancin zangon za su tashi. Sai a yi busar faɗakarwa a kowane lokaci da za su tashi. 7 Amma idan za a kira jama'a ne sai a yi busa da ƙarfi amma banda faɗakarwa. 8 'Ya'yan Haruna, maza, firistoci, su ne za su busa kakakin. “Kakakin za su zama muku ka'ida ta din din din cikin dukan zamananku. 9 Sa'ad da kuka tafi yaƙi a ƙasarku gāba da maƙiyanku da suke matsa muku lamba, sai ku yi busar faɗakarwan nan da kakakin, Ubangiji Allahnku zai tuna da ku, ya cece ku daga maƙiyanku. 10 A ranar murnarku, da lokacin ƙayyadaddun idodinku, da tsayawar watanninku, za ku busa kakakin a lokacin yin hadayunku na ƙonawa, da hadayunku na salama. Za su zama sanadin tunawa da ku a gaban Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Tashin Isra'ilawa daga Sina'i

11 A rana ta ashirin ga watan biyu a shekara ta biyu, sai aka gusar da girgijen daga kan alfarwa ta sujada. 12 Isra'ilawa kuwa suka tashi daki-daki daga jejin Sina'i. Girgijen kuma ya tsaya a jejin Faran. 13 Suka fara tafiyarsu bisa ga umarnin da Ubangiji ya yi wa Musa. 14 Tutar zangon kabilar mutanen Yahuza ta fara tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Nashon, ɗan Amminadab, shi ne shugaban rundunarsu. 15 Shugaban rundunar kabilar mutanen Issaka Netanel ne, ɗan Zuwar. 16 Shugaban rundunar kabilar mutanen Zabaluna Eliyab ne, ɗan Helon. 17 Sa'an nan aka kwankwance alfarwar, sai 'ya'yan Gershon, da 'ya'yan Merari masu ɗaukar alfarwar suka kama hanya. 18 Tutar zangon kabilar mutanen Ra'ubainu ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Elizur ne, ɗan Shedeyur. 19 Shugaban rundunar kabilar mutanen Saminu kuwa Shelumiyel ne, ɗan Zurishaddai. 20 Shugaban rundunar kabilar mutanen Gad Eliyasaf ne, ɗan Deyuwel. 21 Daganan sai Kohatawa masu ɗauke da kayayyaki masu tsarki suka tashi. Kafin su isa masaukin, an riga an kafa alfarwar. 22 Tutar zangon mutanen Ifraimu ta tashi, ƙungiyoyinsu na biye. Shugaban rundunarsu Elishama ne, ɗan Ammihud. 23 Shugaban rundunar kabilar mutanen Manassa Gamaliyel ne, ɗan Fedazur. 24 Shugaban rundunar kabilar mutanen Biliyaminu Abidan ne, ɗan Gideyoni. 25 A ƙarshe sai ƙungiyar mutanen Dan da take bayan dukan zangon, ta tashi, ƙungiyoyinsu suna biye. Shugaban rundunarsu Ahiyezer ne, ɗan Ammishaddai. 26 Shugaban rundunar kabilar mutanen Ashiru Fagiyel ne, ɗan Okran. 27 Shugaban rundunar kabilar mutanen Naftali Ahira ne, ɗan Enan. 28 Wannan shi ne tsarin tafiyar Isra'ilawa bisa ga rundunansu sa'ad da sukan tashi. 29 Sai Musa ya ce wa Hobab ɗan Reyuwel Bamadayane, surukinsa, “Muna kan hanya zuwa wurin da Ubangiji ya ce zai ba mu, ka zo tare da mu, za mu yi maka alheri, gama Ubangiji ya alkawarta zai yi wa Isra'ila alheri.” 30 Amma ya ce masa, “Ba zan tafi ba, zan koma ƙasata da wurin dangina.” 31 Musa kuwa ya ce masa, “Ina roƙonka kada ka rabu da mu, gama ka san jejin da muke zango, kai za ka zama idonmu. 32 Idan ka tafi tare da mu, kowane irin alheri da Ubangiji zai yi mana, mu kuma haka za mu yi maka.”

Mutanen suka Kama Hanya

33 Sai suka tashi daga dutsen Ubangiji, wato Sina'i, suka yi tafiya kwana uku. Akwatin alkawarin Ubangiji kuwa ya wuce gabansu don ya nemar musu masauki. 34 A duk lokacin da suka tashi daga zango, sai girgijen Ubangiji ya inuwantar da su da rana. 35 Duk kuma lokacin da akwatin zai tashi, sai Musa ya ce, “Ka tashi, ya Ubangiji, ka sa maƙiyanka su warwatse, ka sa waɗanda suke ƙinka su gudu gabanka.” 36 Sa'ad da akwatin ya sauka kuma, Musa yakan ce, “Ka komo, ya Ubangiji, a wurin dubun dubbai na iyalan Isra'ila.”

Littafin Ƙidaya 11

Ubangiji zai Ba su Nama

1 Da Ubangiji ya ji gunagunin da mutanen suke yi saboda wahalarsu, sai ya husata ƙwarai, wutarsa ta yi ta ci a cikinsu har ta ƙone wani gefe na zangon. 2 Sai mutanen suka yi ta yi wa Musa kuka, Musa kuwa ya yi addu'a ga Ubangiji, wutar kuwa ta mutu. 3 Aka sa wa wurin suna Tabera, wato matoya, domin wutar Ubangiji ta yi ƙuna a cikinsu. 4 Tattarmukan da suke cikinsu kuwa suka faye kwaɗayin nama, har Isra'ilawa ma da kansu suka fara gunaguni suna cewa, “Wa zai ba mu nama mu ci? 5 Mun tuna da kifin da muka ci kyauta a Masar, da su kakamba, wato wani irin kayan lambu ne mai yaɗuwa, da guna, da sāfa, da albasa, da tafarnuwa. 6 Yanzu ranmu ya yi yaushi, ba wani abu, sai dai wannan manna muke gani.” 7 Manna kuwa kamar tsabar riɗi take, kamanninta kuwa kamar na ƙāro ne. 8 Mutane sukan fita su tattara ta, su niƙa, ko kuwa su daka, su dafa, su yi waina da ita. Dandanar wainar tana kamar wadda aka yi da mai. 9 Manna takan zubo tare da raɓa da dad dare a zangon. 10 Musa ya ji mutanen suna ta gunaguni ko'ina a cikin iyalansu, kowane mutum a ƙofar alfarwarsa. Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai. 11 Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Don me ka wahalar da bawanka? Me ya sa ban sami tagomashi a gare ka ba, da ka jibga wahalar dukan mutanen nan a kaina? 12 Ni na ɗauki cikinsu? Ko kuwa ni ne na haife su, har da za ka ce mini, ‘Ka ɗauke su a ƙirjinka, kamar yadda mai reno yake rungume jariri, zuwa ƙasa wadda ka rantse za ka bai wa kakanninsu?’ 13 A ina zan samo nama da zan ba wannan jama'a duka? Gama suna ta gunaguni a gabana, suna cewa, ‘Ba mu nama mu ci.’ 14 Ba zan iya ɗaukar nawayar mutanen nan ni kaɗai ba, gama nauyin ya fi ƙarfina. 15 Idan haka za ka yi da ni, ina roƙonka ka kashe ni, idan na sami tagomashi a gare ka, don kada in rayu in ga wannan baƙin ciki.” 16 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Tattaro mini mutum saba'in daga cikin dattawan Isra'ila waɗanda aka sani su ne dattawa da shugabannin jama'ar, ka kawo su a alfarwa ta sujada, ka sa su tsaya tare da kai. 17 Ni kuwa zan sauko, in yi magana da kai a can. Zan ɗiba daga cikin ruhun da yake cikinka, in ba su. Su kuma za su ɗauki nawayar jama'ar tare da kai, domin kada ka ɗauki nawayar kai kaɗai. 18 Ka ce wa jama'ar, su tsarkake kansu don gobe, za su ci nama, gama Ubangiji ya ji gunagunin da suka yi, da suka ce, ‘Wa zai ba mu nama mu ci? Ai, zama cikin Masar ya fi mana.’ Domin haka Ubangiji zai ba su nama, za su kuwa ci. 19 Ba ma don kwana ɗaya, ko biyu, ko biyar, ko goma, ko ashirin kaɗai za su ci ba. 20 Amma har wata guda cur. Za su ci har ya gundure su, ya zama musu abin ƙyama saboda sun ƙi Ubangiji wanda ke tare da su, suka yi gunaguni a gabansa, suna cewa, ‘Me ya sa ma, muka fito Masar?’ ” 21 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Mutum dubu ɗari shida (600,000 ) ne suke tafe tare da ni, ga shi kuwa, ka ce za ka ba su nama, za su ci har wata guda cur. 22 Za a yanyanka musu garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu, don su ishe su? Ko kuwa za a tattara musu dukan kifayen teku don su ishe su?” 23 Sai Ubangiji ya amsa wa Musa, “Ikon Ubangiji ya gaza ne? Yanzu za ka gani ko maganata gaskiya ce, ko ba gaskiya ba ce.”

Shugabanni sun yi Annabci

24 Musa kuwa ya fita, ya faɗa wa jama'a maganar Ubangiji, ya kuma tattara dattawa saba'in daga cikin jama'ar, ya sa su tsaya kewaye da alfarwar. 25 Sa'an nan Ubangiji ya sauko cikin girgije, ya yi masa magana, ya kuma sa ruhun da yake kansa, ya zama a kan dattawan nan saba'in. Sa'ad da ruhun ya zauna a kansu sai suka yi annabci, amma daga wannan kuma ba su ƙara yi ba. 26 Akwai mutum biyu da suka ragu a zangon, sunan ɗayan Eldad, ɗayan kuwa Medad. Ruhun kuma ya zauna a kansu gama suna cikin dattawan nan da aka lasafta, amma ba su fita zuwa alfarwa ba, sai suka yi annabci a zangon. 27 Sai wani saurayi ya sheƙa a guje ya faɗa wa Musa, ya ce, “Ga Eldad da Medad suna nan suna annabci a cikin zangon.” 28 Joshuwa ɗan Nun, mai yi wa Musa barantaka, ɗaya daga cikin zaɓaɓɓun, ya ce, “Ya shugabana, Musa, ka hana su.” 29 Amma Musa ya ce masa, “Kishi kake yi domina? Da ma jama'ar Ubangiji duka annabawa ne, har ma ya sa Ruhunsa a cikinsu!” 30 Sai Musa da dattawan Isra'ila suka koma zango.

Ubangiji ya Aiko da Makware

31 Sai iska ta huro daga wurin Ubangiji, ta koro makware daga teku, ta bar su birjik kusa da zango, misalin nisan tafiyar yini guda ta kowace fuska. Tsayin tashinsu daga ƙasa misalin kamu biyu ne. 32 Sai mutane suka tashi suka yi ta tattara makware dukan wannan yini, da dukan dare, har kashegari duka. Wanda ya tattara kaɗan, ya tara garwa metan. Suka shanya abinsu kewaye da zangon. 33 Tun suna cikin cin naman, sai Ubangiji ya husata da mutanensa, ya bugi jama'a da annoba mai zafi. 34 Don haka aka sa wa wurin suna Kibrot-hata'awa, wato makabarta, gama a can ne aka binne mutanen nan makwaɗaita. 35 Daga Kibrot-hata'awa mutanen suka yi tafiya zuwa Hazerot, a can suka sauka.

Littafin Ƙidaya 12

Aka Hukunta Maryamu

1 Sai Maryamu da Haruna suka zargi Musa saboda mace, Bahabashiya, wadda ya aura. 2 Suka ce, “Da Musa kaɗai ne, Ubangiji ya yi magana, bai yi magana da mu kuma ba?” Ubangiji kuwa ya ji. 3 (Musa dai mai tawali'u ne ƙwarai, fiye da kowane mutum a duniya.) 4 Farat ɗaya sai Ubangijiya ce wa Musa, da Haruna, da Maryamu, “Ku uku, ku tafi zuwa alfarwa ta sujada.” Sai su uku suka tafi. 5 Ubangiji kuwa ya zo cikin al'amudin girgije, ya tsaya a ƙofar alfarwar, ya yi kira, “Haruna! Maryamu!” Su biyu fa suka gusa gaba. 6 Ya ce, “Ku ji abin da zan faɗa! Idan akwai annabawa a cikinku, nakan bayyana gare su cikin wahayi, in kuma yi magana da su ta cikin mafarki. 7 Ba haka nake magana da bawana Musa ba, na sa shi ya lura da dukkan jama'ata Isra'ila. 8 Nakan yi magana da shi fuska da fuska a sarari, ba a duhunce ba. Yakan kuma ga zatina. Me ya sa ba ku ji tsoron zargin bawana Musa ba?” 9 Ubangiji kuwa ya husata da su, ya rabu da su. 10 Sa'ad da al'amudin girgijen ya tashi daga kan alfarwar, sai ga Maryamu ta kuturce, fari fat kamar auduga. Da Haruna ya juya wajen Maryamu, ya ga ta zama kuturwa. 11 Sai ya ce wa Musa, “Ya shugabana, ina roƙonka, kada ka hukunta mu saboda wannan zunubi, mun yi aikin wauta. 12 Na roƙe ka kada ka bari ta zama kamar matacce wanda rabin jikinsa ruɓaɓɓe ne a lokacin da aka haife shi.” 13 Sai Musa ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ya Allah, ka warkar da ita.” 14 Amma ubangiji ya ce wa Musa, “Da a ce mahaifinta ne ya tofa mata yau a fuskarta, ba za ta ji kunya har kwana bakwai ba? Bari a fitar da ita a bayan zangon kwana bakwai, bayan haka a shigar da ita.” 15 Aka fitar da Maryamu a bayan zangon har kwana bakwai. Jama'ar kuwa ba su ci gaba da tafiya ba, sai da aka shigar da Maryamu a zangon. 16 Bayan wannan jama'a suka tashi daga Hazerot suka sauka a jejin Faran.

Littafin Ƙidaya 13

'Yan Leƙen Asirin Ƙasa

1 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 2 “Ka aiki mutane su leƙi asirin ƙasar Kan'ana wadda nake ba Isra'ilawa. Daga kowace kabila na kakanninsu, ka zaɓi mutum guda wanda yake shugaba a cikinsu.” kuwa ya yi biyayya, daga jejin Faran ya aika da waɗannan shugabanni, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ra'ubainu. Shafat ɗan Hori, daga kabilar Saminu. Kalibu ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuza. Igal ɗan Yusufu, daga kabilar Issaka. Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Ifraimu. Falti ɗan Rafu, daga kabilar Biliyaminu. Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zabaluna. Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manassa. Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan. Setur ɗan Maikel, daga kabilar Ashiru. Nabi ɗan Wofsi, daga kabilar Naftali. Geyuwel ɗan Maci, daga kabilar Gad. 16 Waɗannan su ne mutanen da Musa ya aika su leƙo asirin ƙasar. Amma Musa ya ba Hosheya, ɗan Nun, suna Joshuwa. 17 Sa'ad da Musa ya aike su leƙen asirin ƙasar Kan'ana, ya ce musu, “Ku haura, ku bi ta Negeb har zuwa ƙasar tuddai, 18 ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanenta ƙarfafa ne, ko raunana ne, ko su kima ne, ko kuwa suna da yawa, 19 ko ƙasa tasu mai ni'ima ce, ko babu, ko biranensu marasa garu ne, ko masu garu ne, 20 ko ƙasar tana da wadata, ko matalauciya ce, ko ƙasar kurmi ce, ko fili. Ku yi jaruntaka, ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Gama lokacin farkon nunan inabi ne.) 21 Sai suka haura, suka leƙo asirin ƙasar tun daga jejin Zin har zuwa Rehob kusa da Hamat. 22 Suka haura ta wajen Negeb, suka isa Hebron inda Ahimaniyawa, da Sheshaiyawa, da Talmaiyawa, zuriyar ƙarfafan mutanen da ake kira Anakawa suke zaune. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.) 23 Da suka isa Kwarin Eshkol, sai suka datse reshe guda na nonon inabi da 'ya'ya cunkus. Suka rataya a sanda, mutum biyu suka ɗauka a kafaɗunsu. Suka kuma kawo rumman da ɓaure. 24 Aka kira wurin Kwarin Eshkol, wato “Nonon inabi,” saboda nonon inabi wanda 'yan leƙen ƙasa suka yanko a wurin. 25 Bayan sun yi kwana arba'in suna leƙen asirin ƙasar, sai suka komo. 26 Suka zo wurin Musa, da Haruna, da dukan taron jama'ar Isra'ila a jejin Faran a Kadesh. Suka faɗa musu labarin tafiyarsu, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar da suka kawo. 27 Suka ce wa Musa, “Mun tafi ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana da yalwar abinci, ga kuma amfanin ƙasar. 28 Amma mazaunan ƙasar ƙarfafa ne, biranenta kuma manya ne, masu garu, banda wannan kuma, mun ga Anakawa a can. 29 Amalekawa suna zaune a Negeb, Hittiyawa kuwa, da Yebusiyawa, da Amoriyawa suna zaune a ƙasar tuddai, Kan'aniyawa suna zaune kusa da teku, da kuma kusa da Kogin Urdun.” 30 Amma Kalibu ya sa mutane su yi shiru a gaban Musa, ya ce, “Bari mu tafi nan da nan mu mallaki ƙasar, gama za mu iya cinta.” 31 Sai mutanen da suka tafi tare da shi suka amsa suka ce, “Ba za mu iya haurawa, mu kara da mutanen ba, gama sun fi mu ƙarfi.” 32 Haka suka kawo wa 'yan'uwansu, Isra'ilawa, mugun rahoton ƙasa wadda suka leƙi asirinta, suka ƙara da cewa, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zaune a cikinta, dukan mutane kuma da muka gani a cikinta ƙatti ne. 33 Mun kuma ga manyan mutane a can, wato mutanen Anakawa da suka fito daga Nefilawa. Sai muka ga kanmu kamar fara ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

Littafin Ƙidaya 14

Mutane suka yi Yaji

1 Sai dukan taron jama'a suka yi kuka da babbar murya dukan dare saboda wahala. 2 Dukan Isra'ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, suke ce, “Da ma mun mutu a ƙasar Masar, ko kuwa a wannan jeji. 3 Me ya sa Ubangiji ya kawo mu a wannan ƙasa, mu mutu da takobi? Matanmu da ƙanananmu za su zama ganima. Ba zai fi mana kyau, mu koma Masar ba?” 4 Sai suka ce wa juna, “Bari mu shugabantar da wani, mu koma Masar.” 5 Sa'an nan Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban dukan taron jama'ar Isra'ilawa. 6 Sai Joshuwa, ɗan Nun, da Kalibu, ɗan Yefunne waɗanda ke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu. 7 Suka ce wa dukan taron jama'ar Isra'ilawa, “Ƙasar da muka ratsa ta don mu leƙi asirinta, ƙasa ce mai kyau ƙwarai da gaske. 8 Idan Ubangiji yana jin daɗinmu zai kai mu a wannan ƙasa da take cike da yalwar abinci, ya ba mu ita. 9 Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji, kada kuwa ku ji tsoron mutanen ƙasar. Za mu ci su ba wuya, Ubangiji kuma zai lalatar da gumakansu da ke kāre su. Ubangiji kuwa yana tare da mu, kada ku ji tsoronsu.” 10 Amma taron jama'a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan mutanen Isra'ila daga cikin alfarwa ta sujada. 11 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su raina ni? Har yaushe za su ƙi gaskata ni, ko da yake na aikata alamu a tsakiyarsu? 12 Zan kashe su da annoba, in raba su da gādonsu. Zan yi wata al'umma da kai, wadda za ta fi su girma da iko.” 13 Amma Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji, gama ka fitar da mutanen daga cikinsu da ƙarfin ikonka. 14 Za su kuwa faɗa wa mutanen wannan ƙasa, gama sun riga sun ji, kai, ya Ubangiji, kana cikin tsakiyar jama'ar nan wadda kake bayyana kanka gare ta fuska da fuska. Girgijenka kuma yana tsaye a kansu, kakan kuma yi musu jagora da al'amudin wuta. 15 Idan kuwa ka kashe jama'ar nan gaba ɗaya, sai al'umman da suka ji labarinka, su ce, 16 ‘Domin Ubangiji ya kāsa kai jama'ar nan zuwa cikin ƙasar da ya rantse zai ba su, don haka ya kashe su a cikin jeji.’ 17 Yanzu fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka sa ikonka ya zama da girma kamar yadda ka alkawarta cewa, 18 ‘Ubangiji mai jinkirin fushi ne, mai yawan ƙauna, kana gafarta mugunta da laifi, amma ba za ka ƙyale mai laifi ba, gama kakan ɗora wa 'ya'ya alhakin muguntar iyaye, har tsara ta uku da ta huɗu.’ 19 Ina roƙonka ka gafarta muguntar wannan jama'a saboda ƙaunarka mai girma, kamar yadda kake gafarta musu tun daga Masar har zuwa yanzu.” 20 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda maganarka na gafarta. 21 Amma, hakika, na rantse da zatina, kamar yadda ɗaukakata za ta cika duniya duka, 22 dukan mutanen da suka ga ɗaukakata da alamuna waɗanda na aikata a Masar, da kuma a jejin, suka kuwa jarraba ni har sau goma, ba su kuma yi biyayya da maganata ba, 23 ba za su ga ƙasar da na rantse zan ba kakanninsu ba. Duk waɗanda suka raina ni, ba za su ga ƙasar ba, 24 sai dai bawana Kalibu da yake ruhunsa dabam ne, gama ya bi ni sosai. 25 Yanzu fa, tun da yake Amalekawa da Kan'aniyawa suna zaune a kwarin, gobe sai ku juya ku nufi wajen jejin ta hanyar Bahar Maliya.”

Ubangiji ya Hukunta Jama'ar saboda Gunaguni

26 Ubangiji kuma ya ce wa Musa da Haruna, 27 “Har yaushe wannan mugun taron jama'a zai yi ta gunaguni a kaina? Na ji gunagunin da Isra'ilawa suka yi a kaina. 28 Sai ka faɗa musu cewa, ‘Ni Ubangiji na rantse da zatina, abin da kuka sanar da ni zan yi muku. 29 Gawawwakin waɗanda suka yi gunaguni a kaina za su fādi cikin jejin nan. Dukan waɗanda aka ƙidaya, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba, 30 ba wanda zai shiga ƙasar da na rantse ta zama wurin zamanku, sai Kalibu, ɗan Yefunne, da Joshuwa ɗan Nun. 31 Amma 'yan ƙanananku, waɗanda kuka ce za su zama ganima, su ne zan kai su cikin ƙasar, za su san ƙasar da kuka raina. 32 Amma ku, gawawwakinku za su fāɗi a jejin. 33 'Ya'yanku za su yi yawo a jeji shekara arba'in, za su sha wahala saboda rashin bangaskiyarku, har mutuminku na ƙarshe ya mutu a jejin. 34 Bisa ga kwanakin nan arba'in da kuka leƙi asirin ƙasar, haka za ku ɗauki alhakin zunubanku shekara arba'in, gama kowane kwana a maimakon shekara yake. Ta haka za ku sani ban ji daɗin abin da kuka yi ba. 35 Ni Ubangiji na faɗa, hakika, haka zan yi da wannan mugun taron jama'a da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su ƙare ƙaƙaf a wannan jeji, a nan za su mutu.’ ” 36 Mutanen da Musa ya aika su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama'a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, 37 mutanen nan da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta kashe su a gaban Ubangiji. 38 Sai dai Joshuwa, ɗan Nun, da Kalibu, ɗan Yefunne, kaɗai ne ba za su mutu ba daga cikin waɗanda suka tafi leƙen asirin ƙasar.

Ƙoƙarin Cin Ƙasar na Farko ya Kāsa

39 Da Musa ya faɗa wa Isra'ilawa abin da Ubangiji ya ce, sai jama'a suka yi baƙin ciki ƙwarai. 40 Suka tashi da sassafe, suka hau kan tudu, suna cewa, “Ga shi, a shirye muke mu tafi wurin da Ubangiji ya ambata, gama mun yi kuskure.” 41 Amma Musa ya ce, “Me ya sa kuke karya umarnin Ubangiji? Yin haka ba zai kawo nasara ba. 42 Kada ku haura domin kada ku sha ɗibga a gaban maƙiyanku, gama Ubangiji ba ya tare da ku. 43 Gama akwai Amalekawa da Kan'aniyawa a gabanku, za su kashe ku da takobi domin kun bar bin Ubangiji, don haka Ubangiji ba zai kasance tare da ku ba.” 44 Amma sai suka yi izgili, suka haura kan tudun, amma akwatin alkawari da Musa ba su bar zangon ba. 45 Sai Amalekawa da Kan'aniyawa, mazauna a kan tudun, suka gangaro, suka ci su, suka runtume su har Harma, wato hallakarwa.

Littafin Ƙidaya 15

Ka'idodin Yin Hadayu

1 Ubangiji ya ba Musa 2 waɗannan ka'idodi domin Isra'ilawa su kiyaye su a ƙasar da zai ba su. 3 Sa'ad da za su yi hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji daga cikin garken shanu, ko na tumaki da awaki, ko hadaya ta ƙonawa ce, ko ta cika wa'adi ce, ko ta yardar rai ce, ko ta ƙayyadaddun idodinsu ce, don a ba da ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, 4 sai shi wanda ya kawo hadayar ga Ubangiji, ya kuma kawo hadaya ta gari, humushin garwa guda kwaɓaɓɓe da rubu'in moɗa na mai. 5 Ya kuma shirya hadaya ta sha, rubu'in moɗa ta ruwan inabi domin kowane ɗan rago na hadaya ta ƙonawa. 6 Idan kuwa da rago ne, a shirya hadaya ta gari humushi biyu na garwa, a kwaɓa da sulusin moɗa na mai. 7 Za a kuma miƙa hadaya ta sha da sulusin moɗa na ruwan inabi, don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. 8 Idan kuwa da bijimi ne za a yi hadaya ta ƙonawar, ko sadaka domin cika wa'adi, ko ta salama ga Ubangiji, 9 sai a miƙa hadaya ta gari tare da bijimin, humushi uku na garwar gari kwaɓaɓɓe da rabin moɗa na mai. 10 Za a kuma miƙa hadaya ta sha da rabin moɗa na ruwan inabi. Hadaya ce da akan yi da wuta, mai yin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. 11 Haka za a yi da kowane bijimi, ko rago, ko ɗan rago, ko bunsuru. 12 Bisa ga yawan abin da aka shirya, haka za a yi da kowannensu bisa ga adadinsu. 13 Haka dukan waɗanda suke 'yan ƙasa za su yi in za su ba da hadayar da akan yi da wuta don yin ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. 14 Idan baƙon da yake baƙunci a cikinsu ko kowanene da ke tare da su a dukan zamanansu, yana so ya ba da hadayar da akan yi da wuta don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji, sai ya yi kamar yadda suke yi. 15 Ka'ida ɗaya ce domin taron jama'a da kuma baƙin da ke zaune tare da su. Ka'ida ce madawwamiya a dukan zamanansu. Kamar yadda suke a gaban Ubangiji, haka kuma baƙon da yake baƙunci a cikinsu yake. 16 Ka'ida ɗaya ce umarni kuma ɗaya ne domin su da baƙin da suke baƙunci a cikinsu. 17 Ubangiji ya ba Musa 18 waɗannan ka'idodi domin Isra'ilawa su kiyaye a ƙasar da zai ba su. 19 Sa'ad da suke cin amfaninta, sai su miƙa hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji. 20 Daga cikin ɓarzajjen hatsinsu na nunan fari sai su yi wainar da za su ɗaga don yin hadaya da amfanin masussuka. 21 Daga cikin ɓarzajjen hatsinsu na nunan fari, sai su miƙa wa Ubangiji hadaya ta ɗagawa a dukan zamanansu. 22 Amma idan sun yi kuskure, ba su kiyaye dukan umarnan nan waɗanda Ubangiji ya faɗa wa Musa ba, 23 wato duk dai abin da ubangiji ya umarta ta bakin Musa tun daga ranar da Ubangiji ya ba da umarnan, har zuwa dukan zamanansu, 24 idan jama'a sun yi kuskure da rashin sani, sai su miƙa maraƙi don yin hadaya ta ƙonawa don a yi ƙanshi mai daɗi ga Ubangiji. Su kuma ba da hadaya ta gari, da hadaya ta sha tare da maraƙin bisa ga ka'idar. Za su kuma miƙa bunsuru ɗaya na yin hadaya don zunubi. 25 Firist kuwa zai yi kafara domin dukan jama'ar Isra'ilawa, za a kuwa gafarta musu kuskuren, domin sun kawo hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi ga Ubangiji saboda kuskurensu. 26 Za a gafarta wa dukan taron jama'ar Isra'ilawa da baƙon da yake baƙunci a cikinsu, kuskuren da suka yi. 27 Idan bisa ga kuskure wani mutum ya yi zunubi, sai ya ba da 'yar akuya bana ɗaya ta yin hadaya don zunubi. 28 Firist kuwa zai yi kafara a gaban Ubangiji saboda mutumin da ya yi kuskuren, gama ya yi zunubi ba da saninsa ba, za a kuwa gafarta masa. 29 Ka'idarsu ɗaya ce a kan wanda ya yi kuskure, ko Ba'isra'ile ne, ko baƙon da yake baƙunci a cikinsu. 30 Amma mutumin da ya yi laifi da gangan, ko shi ɗan ƙasa ne, ko kuma baƙo ne, ya sāɓi Ubangiji, sai a kashe shi, 31 gama ya raina maganar Ubangiji, ya karya umarninsa. Hakika za a kashe mutumin nan, alhakin zunubinsa, yana wuyansa.

Jajjefewar Wanda ya Ɓata Ranar Asabar

32 Sa'ad da Isra'ilawa suke jeji, sai aka iske wani yana tattara itace a ranar Asabar. 33 Sai suka kai shi wurin Musa, da Haruna, da dukan taron jama'a. 34 Aka sa shi a gidan waƙafi domin ba a bayyana abin da za a yi da shi ba tukuna. 35 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “A kashe mutumin, dukan taron jama'a za su jajjefe shi da duwatsu a bayan zangon.” 36 Dukan taron jama'a suka kai shi bayan zangon, suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.

Dokoki a kan Tuntayen Riguna

37 Ubangiji ya umarci Musa ya ce, 38 “Ka faɗa wa Isra'ilawa su yi wa shafin rigunansu tuntaye a dukan zamananku. A kan kowane tuntu, su sa shuɗin zare. 39 Tuntu zai zama musu abin dubawa don su riƙa tunawa da dukan umarnan Ubangiji su aikata su, don kada su bi son zuciyarsu, da sha'awar idanunsu yadda suka taɓa yi. 40 Da haka za su riƙa tunawa, su aikata dukan umarnaina su zama tsarkakakku gare ni. 41 Gama ni ne Ubangiji Allahnku, na fisshe ku daga ƙasar Masar domin in zama Allahnku. Ni ne Ubangiji Allahnku.”

Littafin Ƙidaya 16

Tayarwar Kora, da Datan, da Abiram

1-2 Sai Kora, ɗan Izhara, na kabilar Lawi, iyalin Kohat, ya yi ƙarfin hali ya tayar wa Musa. Waɗansu uku kuma daga kabilar Ra'ubainu suka haɗa kai da shi, su ne Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab, da On, ɗan Felet, da waɗansu Isra'ilawa su ɗari biyu da hamsin, sanannun shugabanni da jama'a suka zaɓa. 3 Suka taru a gaban Musa da Haruna, suka ce musu, “Kun cika izgili, gama dukan taron jama'a na Ubangiji ne, Ubangiji kuwa yana tare da su. Me ya sa kai Musa ka aza kanka shugaba a kan taron jama'ar Ubangiji?” 4 Da Musa ya ji wannan, sai ya fāɗi rubda ciki ya yi addu'a. 5 Sa'an nan ya ce wa Kora da ƙungiyarsa, “Da safe Ubangiji zai nuna mana wanda yake nasa, zai sa wanda yake nasa, wato wanda ya zaɓa, ya sadu da shi a bagade. 6 Kai, Kora da ƙungiyarka duka, gobe, sai ku ɗauki farantan ƙona turare. 7 Ku zuba wuta a ciki, ku kuma zuba musu turaren wuta a gaban Ubangiji. Sa'an nan ne za mu ga wanda Ubangiji ya zaɓa tsakaninmu. Ku Lawiyawa ku ne kuka fi fiffiƙewa!” 8 Musa ya ci gaba da magana da Kora. “Ku Lawiyawa ku kasa kunne! 9 Kuna ganin wannan ƙaramar magana ce, wato cewa Allah na Isra'ila ya keɓe ku daga cikin jama'ar Isra'ila domin ya kawo ku kusa da shi, ku yi aiki a alfarwar sujada ta Ubangiji, ku kuma tsaya a gaban jama'a don ku yi musu aiki? 10 Ya yarda ka zo kusa da shi, kai da dukan 'yan'uwanka Lawiyawa, a yanzu kuwa sai ƙoƙari kuke ku karɓi aikin firist! 11 Kai da ƙungiyarka kun haɗa kai kuna yi wa Haruna gunaguni, amma wane ne Haruna? A zahiri tawaye ne kuke wa Ubangiji!” 12 Musa kuwa ya aika a kirawo Datan da Abiram, 'ya'yan Eliyab, amma suka ce, “Ba za mu zo ba! 13 Kana jin ƙaramin abu ne da ka fitar da mu daga cikin ƙasar mai yalwar abinci, don ka kashe mu a jeji? So kake kuma ka mai da kanka sarki a bisanmu? 14 Banda wannan kuma, ga shi, ba ka kai mu zuwa cikin ƙasa mai yalwar abinci ba, ba ka ba mu gonaki da gonakin inabi domin mu gāda ba, yanzu kuwa kana so ka ruɗe mu, to, ba za mu zo ba sam!” 15 Musa kuwa ya husata ƙawarai da gaske, ya ce wa Ubangiji, “Kada ka karɓi hadayarsu. Ban ƙwace ko jakinsu ba, ban kuwa cuce su ba.” 16 Musa ya ce wa Kora, “Kai da ƙungiyarka duka ku hallara a gaban Ubangiji gobe, da kai, da su, da Haruna. 17 Sa'an nan kowane ɗayanku ya ɗauki farantinsa na ƙona turare, ya zuba turaren wuta a ciki, ya kawo a gaban Ubangiji, wato farantan ƙona turare guda ɗari biyu da hamsin ke nan. Kai kuma da Haruna kowannenku ya kawo nasa faranti.” 18 Sai kowannensu ya ɗauki farantinsa, ya zuba wuta a ciki, sa'an nan ya zuba turaren wuta, suka tsaitsaya a bakin ƙofar alfarwa ta sujada tare da Musa da Haruna. 19 Sai Kora ya tara dukan taron jama'a a bakin alfarwa ta sujada, ya zuga su su tayar wa Musa, da Haruna. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana ga dukan taron jama'ar. 20 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna, 21 “Ku ware kanku daga cikin taron jama'ar nan, ni kuwa in hallaka su nan take.” 22 Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki, suka ce, “Ya Allah, Allahn ruhohin 'yan adam duka, za ka yi fushi da dukan taron jama'a saboda zunubin mutum ɗaya?” 23 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 24 “Ka faɗa wa jama'a su tashi, su nisanci alfarwar Kora, da ta Datan, da ta Abiram.” 25 Musa kuwa ya tashi ya tafi wurin Datan, da Abiram Dattawan Isra'ilawa suka bi Musa. 26 Sai ya ce wa jama'ar, “Ina roƙonku, ku ƙaurace wa alfarwan waɗannan mugayen mutane, kada ku taɓa kowane abu da yake nasu, domin kada a shafe ku saboda zunubansu.” 27 Sai jama'a suka tashi daga inda Kora, da Datan, da Abiram suke zama. Datan da Abiram kuwa suka fito suka tsaya a ƙofar alfarwansu tare da matansu da 'ya'yansu, da 'yan ƙananansu. 28 Sai Musa ya ce, “Da haka za ku sani Ubangiji ne ya aiko ni, in yi waɗannan ayyuka, ba da nufin kaina na yi su ba. 29 Idan mutanen nan sun mutu kamar yadda mutane ke mutuwa, idan abin da yakan sami kowa shi ne ya same su, to, ba Ubangiji ne ya aiko ni ba. 30 Amma idan Ubangiji ya aikata wani abu sabo, ya sa ƙasa ta buɗe bakinta, ta haɗiye su da dukan abin da suke da shi, suka gangara zuwa cikin lahira a raye, sa'an nan za ku sani mutanen nan sun raina Ubangiji.” 31 Musa ya rufe bakinsa ke nan, sai wurin da Datan da Abiram suke tsaye, ƙasar ta dāre 32 ta haɗiye su tare da iyalansu, da dukan mutanen Kora, da dukan mallakarsu. 33 Haka fa, su da dukan abin da yake nasu suka gangara zuwa lahira da rai. 34 Sai Isra'ilawa duka waɗanda suke kewaye da su suka gudu saboda kururuwansu, suka ce. “Mu mā gudu, kada kuma ƙasa ta haɗiye mu.” 35 Wuta kuma ta fito daga wurin Ubangiji ta cinye mutum ɗari biyu da hamsin ɗin nan da suke miƙa hadaya da turare. 36 Ubangiji ya ce wa Musa, 37 “Ka faɗa wa Ele'azara, ɗan Haruna firist, ya kawar da farantan ƙona turare daga wurin da wutar ta cinye, ka watsar da gawayin daga farantan a wani wuri gama farantan tsarkakakku ne. 38 Waɗannan farantan ƙona turaren sun zama tsarkakakku sa'ad da aka miƙa su a bagaden Ubangiji. Sai ka ɗauki farantan mutanen da suka yi zunubin da ya jawo musu mutuwa, ka ƙera murfin bagade da su, gama an miƙa su a gaban Ubangiji, ta haka za su zama gargaɗi ga jama'ar Isra'ila.” 39 Sai Ele'azara, firist, ya ɗauki farantan tagullar waɗanda mutanen da aka hallaka suka kawo. Aka ƙera murfin bagade da su. 40 Zai zama abin tunawa ga Isra'ilawa domin kada wanda ba firist ba, ba kuwa a cikin zuriyar Haruna ba, ya guso don ya ƙona turare a gaban Ubangiji, domin kada ya zama kamar Kora da ƙungiyarsa. Haka Ubangiji ya faɗa wa Ele'azara ta bakin Musa.

Haruna ya Ceci Jama'a

41 Kashegari dukan taron Isra'ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, suna cewa, “Ku ne sanadin mutuwar jama'ar Ubangiji.” 42 Da taron jama'ar suka haɗa kai gāba da Musa da Haruna, sai suka fuskanci alfarwa ta sujada. Ga girgije yana rufe da alfarwar, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta bayyana. 43 Sai Musa da Haruna suka tafi wajen ƙofar alfarwa ta sujada. 44 Ubangiji kuwa ya yi magana da Musa, ya ce, 45 “Ku nisanci wannan taro, gama yanzun nan zan hallaka su.” Sai suka fāɗi rubda ciki. 46 Sa'an nan Musa ya ce wa Haruna, “Ɗauki farantin turare, ka cika shi da wuta daga bagade, ka zuba turaren wuta a ciki, ka tafi da sauri wurin taron, ka yi kafara dominsu, gama fushin Ubangiji ya riga ya sauko, an fara annoba.” 47 Sai Haruna ya ɗauko farantin turaren, ya yi yadda Musa ya ce. Ya sheƙa a guje a tsakiyar taron jama'a. Amma an riga an fara annobar a cikin jama'a. Sai ya zuba turare, ya yi kafara domin jama'a. 48 Ya kuwa tsaya a tsakanin matattu da masu rai, annobar kuwa ta tsaya. 49 Waɗanda annoba ta kashe mutum dubu goma sha huɗu ne da ɗari bakwai (14,700 ), banda waɗanda suka mutu a sanadin Kora. 50 Sai Haruna ya koma wurin Musa a ƙofar alfarwa ta sujada, gama annobar ta ƙare.

Littafin Ƙidaya 17

Sandan Haruna

1 Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce, 2 “Ka faɗa wa Isra'ilawa su ba ka sanduna, sanda guda daga kowane shugaban gidan kakanninsu, sanduna goma sha biyu ke nan. Ka rubuta sunan kowane mutum a sandansa. 3 Ka rubuta sunan Haruna a kan sandan Lawi, gama akwai sanda guda domin kowane gidan kakanninsu. 4 Sai ka ajiye su a alfarwa ta sujada a gaban akwatin alkawari, inda nakan sadu da kai. 5 Mutumin da sandansa ya yi toho, shi ne na zaɓa, da haka zan sa gunagunin da Isra'ilawa suke yi a kaina ya ƙare.” 6 Musa kuwa ya yi magana da Isra'ilawa. Sai dukan shugabanninsu suka ba shi sanda ɗaya ɗaya, sanda ɗaya daga kowane shugaba bisa ga gidajen kakanninsu, sanduna goma sha biyu ke nan. Sandan Haruna yana cikin sandunan. 7 Sai Musa ya ajiye sandunan a gaban Ubangiji cikin alfarwa ta sujada. 8 Kashegari Musa ya shiga alfarwar, sai ga shi, sandan Haruna na gidan Lawiyawa ya huda, ya yi toho, ya yi furanni, ya kuma yi 'ya'yan almon nunannu, wato wani irin itace ne mai kama da na yazawa. 9 Musa kuwa ya fito wa Isra'ilawa da dukan sandunan da aka ajiye a gaban Ubangiji. Suka duba, kowanne ya ɗauki sandansa. 10 Ubangiji ya ce wa Musa, “Mayar da sandan Haruna a akwatin alkawari, alama ce ga masu tawaye ta cewa za su mutu idan ba su daina gunaguninsu ba.” 11 Haka kuwa Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. 12 Isra'ilawa suka ce wa Musa, “Ba shakka, mun hallaka. Mun lalace, dukanmu mun lalace. 13 Duk wanda ya kusaci alfarwa ta sujada ta Ubangiji, zai mutu. Ashe, dukanmu za mu mutu ke nan!”

Littafin Ƙidaya 18

Ayyukan Lawiyawa da Firistoci

1 Sai Ubangiji ya ce wa Haruna, “Kai da 'ya'yanka, da gidan mahaifinka za ku ɗauki hakkin abin da ya shafi alfarwa ta sujada. Kai da 'ya'yanka kuma za ku ɗauki hakkin aikinku wanda ya shafi firistoci. 2 Ka kawo 'yan'uwanka tare da kai, wato kabilar Lawi, kakanka, don su yi muku aiki sa'ad da kai da 'ya'yanka kuke gaban alfarwa ta sujada. 3 Za su taimake ku, su kuma yi dukan ayyukan alfarwa. Amma fa, ba za su kusaci kayayyakin Wuri Mai Tsarki, ko bagade ba, don kada su, har da ku, ku mutu. 4 Za su haɗa kai da ku su lura da alfarwa ta sujada da dukan aikace-aikace na cikin alfarwar. Kada wani dabam ya kusace ku. 5 Ku lura da ayyukan Wuri Mai Tsarki da na bagade don kada hasala ta sāke fāɗa wa Isra'ilawa. 6 Ga shi, ni na ɗauki 'yan'uwanku, Lawiyawa, daga cikin mutanen Isra'ila. Kyauta suke a gare ku, waɗanda aka bayar ga Ubangiji don su lura da alfarwa ta sujada. 7 Da kai, da 'ya'yanka za ku yi aikin firist da duk abin da ya shafi bagade da aiki na bayan labule. Ku ne za ku yi wannan aiki. Na ba ku aikin firist ya zama naku. Duk wani dabam wanda ya zo kuwa, za a kashe shi.”

Rabon Firistoci

8 Ubangiji ya kuma ce wa Haruna, “Na ba ka aikin lura da hadayuna na ɗagawa, wato sadakokin Isra'ilawa, na ba ka su su zama rabonka da na 'ya'yanka har abada. 9 Abin da ya ragu daga cikin hadaya mafi tsarki da ake miƙa mini zai zama rabonka da na 'ya'yanka, wato daga kowace hadaya, da hadaya ta gari, da hadaya don zunubi, da hadaya don laifi. 10 A wuri mai tsarki za ku ci shi, kowane namiji ya iya ci. Abu mai tsarki ne a gare ka. 11 “Har yanzu kuma duk sadakokin da Isra'ilawa ke bayarwa don hadaya ta ɗagawa da ta kaɗawa, na ba ka, kai da 'ya'yanka mata da maza, a kowane lokaci. Duk wanda yake da tsarki a gidanka zai iya ci. 12 “Duk mai mafi kyau, da ruwan inabi mafi kyau duka, da hatsi mafi kyau duka na nunan fari, waɗanda suke bayarwa ga Ubangiji, na ba ku. 13 Nunan fari na dukan amfanin gonarsu wanda suke kawowa ga Ubangiji, zai zama naka. Duk wanda yake da tsarki a gidanka zai iya cinsa. 14 “Iyakar abin da aka keɓe wa Ubangiji a Isra'ila zai zama naka. 15 “Dukan haihuwar fari, ko ta mutum ko ta dabba da sukan bayar ga Ubangiji zai zama naka. Amma ka fanshi kowace haihuwar fari ta mutum, ko ta dabbar da take haram. 16 Sai ka fanshe su suna 'yan wata ɗaya a bakin shekel biyar biyar, bisa ga ma'aunin kuɗin da ake aiki da shi. 17 Haihuwar fari ta saniya, ko ta tunkiya, ko ta akuya, ba za ka fanshe su ba, gama su halal ne. Sai kayayyafa jininsu a kan bagade, kitsensu kuma ka ƙone a kan bagaden ƙona hadayu, zai zama turare mai ƙanshi, mai daɗi ga Ubangiji. 18 Naman kuwa zai zama naka, duk da ƙirji na kaɗawa da cinyar dama da aka miƙa su hadaya ta kaɗawa. 19 “Duk hadayu na ɗagawa na tsarkakakkun abubuwan da Isra'ilawa suka miƙa wa Ubangiji, na ba ka, da kai da 'ya'yanka mata da maza a kowane lokaci. Wannan alkawarin gishiri ne na Ubangiji dominka da zuriyarka.” 20 Ubangiji kuma ya ce wa Haruna, “Ba za ka gāji kome a ƙasar Isra'ilawa ba, ba ka da wani rabo a cikinta. Ni ne rabonka da gādonka a cikin Isra'ilawa.”

Rabon Lawiyawa

21 Ubangiji ya ce, “Na ba Lawiyawa kowace zaka ta Isra'ilawa gādo saboda aikinsu da suke ya a alfarwa ta sujada. 22 Nan gaba kada Isra'ilawa su zo kusa da alfarwa ta sujada don kada su yi zunubi, su mutu. 23 Gama Lawiyawa ne kaɗai za su yi aikin alfarwa ta sujada, wannan alhakinsu ne. Wajibi ne kuma ga zuriyarsu a kowane lokaci. Lawiyawa ba su da gādo tare da Isra'ilawa. 24 Gama ni Ubangiji na ba su zaka da Isra'ilawa suke kawo mini ta hadaya ta ɗagawa ta zama gādonsu. Saboda haka ne, na ce ba su da gādo tare da Isra'ilawa.”

Zaka

25 Ubangiji ya ce wa Musa, 26 “Har yanzu ka faɗa wa Lawiyawa, cewa sa'ad da suka karɓi zaka daga Isra'ilawa wadda na ba su gādo, sai su fitar da zaka daga cikin zakar, su miƙa wa Ubangiji hadaya ta ɗagawa. 27 Za a lasafta hadayarku ta ɗagawa kamar hatsinku ne da kuka sussuka a masussuka, da kuma kamar cikakken amfanin ruwan inabin da kuka samu a wurin matsewar inabinku. 28 Haka za ku miƙa hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji daga cikin dukan zakar da kuke karɓa daga wurin Isra'ilawa. Daga ciki za ku ba da hadaya ta ɗagawa ga Ubangiji ta hannun Haruna, firist. 29 Daga dukan kyautar da ake kawo muku, za ku ba Ubangiji hadaya ta ɗagawa daga mafi kyau da kuke samu. 30 Domin haka kuwa sai ka ce musu, ‘Sa'ad da kuka ɗaga mafi kyau daga cikinta duka, sai ragowar ta zama ta Lawiyawa kamar abin da ya fito daga masussuka, da wurin matsewar inabinsu. 31 Za ku iya cinta ko'ina da kuka ga dama, ku da iyalan gidajenku, gama ladanku ke nan saboda aikin da kuke yi a alfarwa ta sujada. 32 Ba kuwa za ta zama muku sanadin zunubi ba, in dai har kuka ɗaga mafi kyau duka. Ba za ku ɓata tsarkakakkun abubuwa na Isra'ilawa ba, don kada ku mutu.’ ”

Littafin Ƙidaya 19

Tsarkakewar Marasa Tsarki

1 Ubangiji ya yi magana da Musa da Haruna, ya ce, 2 “Wannan ita ce ka'ida wadda Ubangiji ya umarta. Ka faɗa wa Isra'ilawa su kawo maka jar karsana, marar lahani, wadda ba ta da wani aibi, wadda ba a taɓa aza mata karkiya ba. 3 Sai ka ba Ele'azara firist ita, sa'an nan a kai ta bayan sansani, a yanka ta gabansa. 4 Ele'azara, firist, kuwa zai ɗibi jininta da yatsansa, ya yayyafa sau bakwai a wajen alfarwar ta sujada. 5 Sai a ƙone karsanar a idonsa, za a ƙone fatarta, da naman, da jinin, tare da tarosonta. 6 Firist zai ɗauki itacen al'ul, da ɗaɗɗoya, da mulufi, ya jefa a wutar da take ƙone karsanar. 7 Sai firist ɗin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, sa'an nan ya shiga zangon. Firist ɗin zai ƙazantu har zuwa maraice. 8 Shi kuma wanda ya ƙone karsanar, sai ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, shi ma zai ƙazantu har zuwa maraice. 9 Mutumin da yake da tsarki shi zai tara tokar karsanar, ya ajiye a wuri mai tsabta a bayan zangon. Za a adana tokar domin jama'ar Isra'ila, za a riƙa zubawa a ruwa don tsarkakewar zunubi. 10 Shi kuma wanda ya tara tokar karsanar, sai ya wanke tufafinsa zai ƙazantu har maraice. Wannan ka'ida ce ta har abada ga Isra'ilawa da baƙin da ke zama tare da su.”

Taɓa Gawa

11 “Duk wanda ya taɓa gawa zai ƙazantu har kwana bakwai. 12 A rana ta uku da ta bakwai zai tsarkake kansa da ruwa, zai kuwa tsarkaka, amma in a rana ta uku da ta bakwai bai tsarkake kansa ba, to, ba zai tsarkaka ba. 13 Duk wanda ya taɓa gawa, bai kuwa tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da alfarwa ta sujada ta Ubangiji, ba za a lasafta shi cikin mutanen Allah ba, domin ba a yayyafa masa ruwan tsarkakewa ba. 14 “Wannan ita ce ka'ida a kan wanda ya rasu a alfarwa, duk wanda ya shiga alfarwar, da duk wanda yake cikin alfarwar zai ƙazantu har kwana bakwai. 15 Kowace buɗaɗɗiyarsa kuma wadda ba a rufe ba, za ta ƙazantu. 16 Wanda duk yake cikin saura ya taɓa wanda aka kashe da tokobi, ko gawa, ko ƙashin mutum, ko kabari zai ƙazantu har kwana bakwai. 17 “Don a tsarkake ƙazantar, sai a ɗiba daga cikin tokar hadaya don zunubi a cikinsa, sa'an nan a zuba ruwa mai gudu. 18 Tsarkakakken mutum zai ɗauki ɗaɗɗoya ya tsoma a ruwan, ya yayyafa wa alfarwar, da bisa kan dukan kayayyakin da suke ciki, da a kan mutanen da suke a wurin, da kan wanda ya taɓa ƙashin, ko ya taɓa wanda aka kashe, ko ya taɓa gawa, ko kabari. 19 A kan rana ta uku da ta bakwai kuma, wanda yake da tsarki zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, ya tsarkake shi. Sai mutumin ya wanke tufafinsa, ya yi wanka da ruwa, da maraice kuwa zai tsarkaka. 20 “Amma mutumin da ba shi da tsarki, bai kuwa tsarkake kansa ba, ba za a lasafta shi cikin jama'ar Allah ba, tun da yake ya ƙazantar da alfarwa ta sujada ta Ubangiji, gama ba a yayyafa masa ruwan da akan yayyafa wa marasa tsarki ba. 21 Wannan zai zama musu ka'ida har abada. Wanda ya yayyafa ruwan tsarkakewa, sai ya wanke tufafinsa, wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa zai zama marar tsarki har maraice. 22 Duk abin da mutumin da ba shi da tsarki ya taɓa zai ƙazantu, duk wanda kuma ya taɓa abin da marar tsarkin ya taɓa zai ƙazantu har maraice.”

Littafin Ƙidaya 20

Ruwa daga cikin Dutse

1 Sai dukan taron jama'ar Isra'ilawa suka zo jejin Zin a watan fari, suka sauka a Kadesh. A nan ne Maryamu ta rasu, a nan kuma aka binne ta. 2 Da jama'a suka rasa ruwa, sai suka taru suka tayar wa Musa da Haruna. 3 Suka ce wa Musa, “Da ma mun mutu kamar yadda 'yan'uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji. 4 Don me ka fito da taron jama'ar Ubangiji zuwa cikin wannan jeji don mu mutu a nan, mu da dabbobinmu? 5 Don me kuma ka sa muka fito daga masar, ka kawo mu a wannan mugun wuri inda babu hatsi, ko ɓaure, ko inabi, ko rumman, ko ruwan da za a sha ma?” 6 Sai Musa da Haruna suka bar taron jama'a, suka tafi ƙofar alfarwa ta sujada, suka fāɗi rubda ciki. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta bayyana a gare su. 7 Ubangiji ya ce wa Musa, 8 “Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan'uwanka, ku tara jama'a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama'a da garkunansu ruwan sha.” 9 Musa kuwa ya ɗauki sanda daga gaban Ubangiji kamar yadda ya umarce shi. 10 Sai Musa da Haruna suka sa jama'a su taru a gaban dutsen, sa'an nan Musa ya ce musu, “Ku kasa kunne, ku 'yan tawaye, za mu fito muku da ruwa daga cikin dutsen nan?” 11 Musa kuwa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa, sai ruwa mai yawa ya yi ta kwararowa. Taron jama'a tare da garkunansu suka sha. 12 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna, “Tun da ya ke ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra'ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama'ar nan a ƙasar da na ba su ba.” 13 Wannan ya faru ne a Meriba inda mutanen Isra'ila suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda shi kuma ya nuna musu shi mai tsarki ne.

Sarkin Edom ya Hana Isra'ilawa Wucewa

14 Sai Musa ya aika manzanni daga Kadesh zuwa wurin Sarkin Edom, su ce masa, “In ji ɗan'uwanka, Isra'ila, ka dai san dukan wahalar da ta same mu, 15 yadda kakanninmu suka gangara zuwa Masar, suka zauna a can da daɗewa, da yadda Masarawa suka wahalshe mu, mu da kakanninmu. 16 Sa'ad da muka yi kuka ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya aiko mala'ikansa, ya fisshe mu daga Masar. Ga mu nan a Kadesh, garin da yake kan iyakar ƙasarka. 17 Ka yarda mana mu ratsa ƙasarka, ba za mu bi ta cikin gona, ko gonar inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba. Mu dai za mu bi gwadaben sarki, ba za mu kauce dama ko hagu ba, har mu wuce ƙasarka.” 18 Amma Edomawa suka ce masa, “Ba za ku ratsa ta ƙasarmu ba! Idan kuwa kun ce za ku gwada, za mu fita mu ci ku da yaƙi.” 19 Amma mutanen Isra'ila suka amsa musu suka ce, “Ai, za mu bi gwadabe ne kawai, idan kuwa mu da dabbobinmu mun sha ruwanku, sai mu biya, mu dai, a yardar mana mu wuce kawai.” 20 Amma Edomawa suka sāke cewa, “Ba mu yarda ba.” Sai suka fito da runduna mai yawa su yi yaƙi da su. 21 Da haka Edomawa suka hana Isra'ilawa ratsa ƙasarsu. Sai Isra'ilawa suka kauce musu.

Haruna ya Rasu

22-23 Sai taron jama'ar Isra'ila suka kama tafiya daga Kadesh, suka je Dutsen Hor, a kan iyakar ƙasar Edom. Ubangiji kuwa ya ce wa Musa da Haruna a can, 24 “Haruna ba zai shiga ƙasar da na alkawarta zan ba Isra'ila ba, zai mutu, gama ku biyun nan kuka tayar wa umarnina a Meriba. 25 Ka kawo Haruna da ɗansa, Ele'azara, bisa Dutsen Hor. 26 Ka tuɓe wa Haruna rigunansa na firist, ka sa wa ɗansa, Ele'azara. Haruna zai mutu can.” 27 Musa kuwa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau bisa Dutsen Hor a idon dukan taron jama'a. 28 Sai Musa ya tuɓe wa Haruna rigunansa na firist ya sa wa Ele'azara ɗan Haruna. Haruna kuwa ya rasu a kan dutsen. Sa'an nan Musa da Ele'azara suka sauko daga kan dutsen. 29 Sa'ad da dukan jama'a suka ga Haruna ya rasu, sai duka suka yi makoki dominsa har kwana talatin.

Littafin Ƙidaya 21

An ci Kan'aniyawa da Yaƙi

1 Da Sarkin Arad, Bakan'ane, wanda yake zaune a Negeb, ya ji Isra'ilawa suna zuwa ta hanyar Atarim, sai ya fita ya yi yaƙi da Isra'ilawa, ya kama waɗansu daga cikinsu. 2 Sai Isra'ilawa suka yi wa'adi ga Ubangiji, suka ce, “In hakika, za ka ba da mutanen nan a hannunmu, lalle za mu hallaka biranensu ƙaƙaf.” 3 Ubangiji kuwa ya ji wa'adin Isra'ilawa, ya kuwa ba su Kan'aniyawa, suka hallaka su da biranensu ƙaƙaf. Don haka aka sa wa wurin suna Horma, wato hallakarwa.

Macijin da aka Yi da Tagulla

4 Isra'ilawa suka kama hanya daga Dutsen Hor zuwa Bahar Maliya don su kauce wa ƙasar Edom. Sai jama'a suka ƙosa da hanyar. 5 Suka yi wa Allah gunaguni, da Musa kuma, suka ce, “Me ya sa kuka fitar da mu daga Masar, kuka kawo mu cikin jeji mu mutu? Gama ba abinci, ba ruwa, mu kuwa mun gundura da wannan abinci marar amfani.” 6 Sai Ubangiji ya aiko macizai masu zafin dafi a cikin jama'a, suka sassari Isra'ilawa, da yawa kuwa suka mutu. 7 Jama'a kuwa suka zo wurin Musa, suka ce, “Mun yi zunubi gama mun yi wa Ubangiji gunaguni, mun kuma yi maka. Ka roƙi Ubangiji ya kawar mana da macizan.” Musa kuwa ya yi roƙo domin jama'ar. 8 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ƙera maciji da tagulla, ka sarƙafa shi a bisa dirka, duk wanda maciji ya sare shi, idan ya dubi maciji na tagullar, zai rayu.” 9 Musa kuwa ya yi maciji na tagulla, ya sarƙafa shi a bisa dirka, idan kuwa maciji ya sari mutum, in ya dubi macijin tagullar, zai warke.

Tafiya zuwa Kwarin Mowabawa

10 Sai mutanen Isra'ila suka kama hanya, suka yi zango a Obot. 11 Suka kama hanya daga Obot, suka yi zango a kufafen Abarim a cikin jeji daura da Mowab wajen gabas. 12 Daga can suka tashi suka sauka a Kwarin Zered. 13 Daga can kuma suka tashi suka sauka hayin Kogin Arnon, wanda yake cikin jeji wanda ya nausa zuwa iyakar Amoriyawa. Gama Arnon shi ne kan iyakar Mowabawa da Amoriyawa. 14 Saboda haka aka faɗa a Littafin Yaƙoƙi na Ubangiji cewa, “Waheb ta cikin yankin Sufa, da kwaruruka na Kogin Arnon, 15 da gangaren kwaruruka, wanda ya nausa zuwa garin Ar, ya kuma dangana da kan iyakar Mowab.” 16 Daga can suka ci gaba da tafiya zuwa Biyer, wato rijiya wadda Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tattara mutane wuri ɗaya, zan kuwa ba su ruwa.” 17 Sai Isra'ilawa suka raira waƙa, suka ce, “Rijiya, ki ɓuɓɓugo da ruwa Mu kuwa za mu raira waƙa mu gaishe ta! 18 Rijiyar da hakimai suka haƙa, Shugabannin jama'a suka haƙa, Da sandan sarauta, Da kuma sandunansu.” Daga cikin jejin suka tafi har zuwa Mattana. 19 Daga Mattana suka tafi Nahaliyel suka tafi Bamot. 20 Daga Bamot kuma suka tafi kwarin da yake a ƙasar Mowab wajen ƙwanƙolin Dutsen Fisga wanda yake fuskantar hamada.

Mutanen Isra'ila sun Ci Sihon

21 Mutanen suka aiki manzanni zuwa wurin Sihon, Sarkin Amoriyawa, suka ce masa, 22 “Ka yarda mana mu ratsa ta ƙasarka, ba za mu ratsa ta cikin gonaki, ko cikin gonakin inabi ba, ba kuwa za mu sha ruwan rijiyarka ba, gwadaben sarki za mu bi sosai, har mu fita daga karkararka.” 23 Amma Sihon bai yarda wa Isra'ilawa su ratsa ta karkararsa ba. Sai ya tattara mazajensa, suka fita don su yi yaƙi da Isra'ilawa a jejin. Suka tafi Yahaza suka yi yaƙi da Isra'ilawa. 24 Isra'ilawa kuwa suka karkashe su da takobi, suka mallaki ƙasarsa tun daga Kogin Arnon zuwa Kogin Yabbok, har zuwa kan iyakar Ammonawa, gama Yahaza ita ce kan iyakar Ammonawa. 25 Isra'ilawa kuwa suka ci dukan waɗannan birane, suka zauna a biranen Amoriyawa, wato a Heshbon da ƙauyukanta duka. 26 Gama Heshbon ita ce birnin Sihon, Sarkin Amoriyawa, wanda ya yi yaƙi da Sarkin Mowab na dā. Ya ƙwace ƙasarsa duka daga hannunsa har zuwa Kogin Arnon. 27 Domin haka mawaƙa sukan ce, “Ku zo Heshbon, bārin sarki Sihon! Muna so mu ga an sāke gina an kuma fanso shi. 28 Gama sojojin Sihon sun shiga kamar wuta, A wannan birni na Heshbon, Sun cinye Ar ta Mowab, Ta murƙushe tuddan Arnon. 29 Kaitonku, ku mutanen Mowab! Ku masu sujada ga Kemosh kun lalace! Gumakanku sun sa mutane su zama 'yan gudun hijira, Mata kuwa, Sihon, Sarkin Amoriyawa ya kama su. 30 Amma yanzu an hallaka zuriyarsu, Tun daga Heshbon har zuwa Dibon, Har da Nofa kusa da Medeba.”

Isra'ilawa sun Ci Og

31 Haka fa Isra'ilawa suka zauna a ƙasar Amoriyawa. 32 Sai Musa ya aika a leƙo asirin ƙasar Yazar. Suka tafi suka ci ƙauyukanta, suka kori Amoriyawan da suke can. 33 Suka juya suka haura ta hanyar Bashan. Sai Og, Sarkin Bashan, da dukan jama'arsa suka fita, suka yi yaƙi da su a Edirai. 34 Ubangiji kuwa ya ce wa Musa, “Kada ka ji tsoronsa, gama na bashe shi a hannunka duk da jama'arsa, da ƙasarsa. Za ka yi masa yadda ka yi wa Sihon, Sarkin Amoriyawa wanda ya zauna a Heshbon.” 35 Haka fa suka kashe shi, shi da 'ya'yansa maza, da dukan jama'arsa, har ba wanda ya tsira, suka kuwa mallaki ƙasarsa.

Littafin Ƙidaya 22

Balak ya Sa a Kirawo masa Bal'amu

1 Isra'ilawa suka kama tafiya, suka yi zango a filayen Mowab a hayin Urdun daura da Yariko. 2 Balak ɗan Ziffor ya ga abin da Isra'ilawa suka yi wa Amoriyawa. 3 Sai Mowabawa suka firgita ƙwarai saboda yawan mutanen. Tsoron Isra'ilawa ya kama su. 4 Mowabawa kuwa suka ce wa dattawan Madayanawa, “Yanzun nan wannan taro zai lashe dukan abin da yake kewaye da mu kamar yadda sā yakan lashe ciyawar saura.” Don haka Balak ɗan Ziffor wanda yake sarautar Mowab a lokacin, 5 ya aiki manzanni zuwa wurin Bal'amu ɗan Beyor a Fetor, a ƙasar danginsa, wadda take kusa da kogin, su kirawo shi, su ce, “Ga mutane sun fito daga ƙasar Masar, sun mamaye ƙasar, ga shi, suna zaune daura da ni. 6 Ina roƙonka, ka zo yanzu, ka la'anta mini mutanen nan, gama sun fi ƙarfina, ko ya yiwu in ci su, in kore su daga ƙasar, gama na sani duk wanda ka sa wa albarka zai albarkatu, wanda kuwa ka la'anta, zai la'antu.” 7 Dattawan Mowab da na Madayana suka ɗauki kafin alkalami suka tafi wurin Bal'amu suka faɗa masa saƙon Balak. 8 Ya ce musu, “Ku kwana a nan, ni kuwa zan shaida muku abin da Ubangiji zai faɗa mini.” Sai dattawan Mowab suka zauna wurin Bal'amu. 9 Allah kuwa ya zo wurin Bal'amu ya ce masa, “Suwane ne mutanen da suke tare da kai?” 10 Sai Bal'amu ya ce wa Allah, “Ai, Balak ne ɗan Ziffor, Sarkin Mowab, ya aiko ya ce mini, 11 ‘Ga jama'a sun fito daga Masar, sun mamaye ƙasar, ka zo, ka la'anta mini su, watakila zan iya yin yaƙi da su, in kore su!’ ” 12 Allah kuwa ya ce wa Bal'amu, “Ba za ka tafi tare da su ba, ba kuwa za ka la'anta su ba, gama albarkatattu ne su.” 13 Da safe Bal'amu ya tashi, ya ce wa dattawan Balak, “Ku koma ƙasarku, gama Ubangiji bai yarda mini in tafi tare da ku ba.” 14 Domin haka dattawan Mowab suka tashi, suka koma wurin Balak, suka ce masa, “Bal'amu bai yarda ya biyo mu ba.” 15 Sai Balak ya sāke aiken dattawa da yawa masu daraja fiye da na dā. 16 Suka je wurin Bal'amu, suka ce masa, “Ga abin da Balak ɗan Ziffor ya ce, ‘Kada ka bar wani abu ya hana ka zuwa wurina, 17 gama zan ɗaukaka ka ƙwarai, kome kuwa ka faɗa mini in yi, zan yi, ka zo ka la'anta mini wannan jama'a.’ ” 18 Amma Bal'amu ya amsa ya ce wa barorin Balak, “Ko da a ce Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan yi wani abu ko kaɗan saɓanin umarnin Ubangiji Allahna ba. 19 Amma ina roƙonku ku kwana a nan yau har in san abin da Ubangiji zai faɗa mini.” 20 Sal Allah ya je wurin Bal'amu da dare, ya ce masa, “Idan mutanen nan sun zo kiranka ne, sai ka tashi, ka tafi tare da su, amma abin da na umarce ka kaɗai za ka yi.”

Mala'ika da Jakar Bal'amu

21 Da safe sai Bal'amu ya tashi ya yi wa jakarsa shimfiɗa, ya tafi tare da dattawan Mowab. 22 Allah kuwa ya husata don ya tafi, mala'ikan Ubangiji ya tsaya a hanya ya tarye shi. Shi kuwa yana tafe a bisa jakarsa tare da barorinsa biyu. 23 Da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji yana tsaye kan hanya da takobi zare a hannunsa, sai ta kauce daga hanya, ta shiga saura. Bal'amu kuwa ya buge ta don ya komar da ita a hanyar. 24 Sai mala'ikan Ubangiji ya je, ya tsaya a inda hanyar ta yi matsatsi a tsakanin bangayen gonakin inabi. 25 Sa'ad da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji, ta matsa a jikin bango, ta goge ƙafar Bal'amu ga bangon, sai ya sāke bugunta. 26 Mala'ikan Ubangiji kuma ya sha kanta, ya tsaya a ƙunƙuntaccen wuri inda ba wurin juyawa zuwa dama ko hagu. 27 Da jakar ta ga mala'ikan Ubangiji, sai ta kwanta a ƙafafun Bal'amu. Sai Bal'amu ya husata, ya bugi jakar da sandansa. 28 Ubangiji kuwa ya buɗe bakin jakar, ta ce wa Bal'amu, “Me na yi maka, da ka buge ni har sau uku?” 29 Bal'amu ya ce mata, “Domin kin shashantar da ni, da a ce ina da takobi a hannuna, da na kashe ki.” 30 Sai jakar ta ce wa Bal'amu, “Ba ni ce jakarka ba wadda kake ta hawa dukan lokacin nan har zuwa yau? Na taɓa yi maka haka?” Ya ce, “A'a.” 31 Ubangiji kuwa ya buɗe idanun Bal'amu, ya ga mala'ikan Ubangiji yana tsaye a hanya da takobi zāre a hannunsa. Sai ya sunkuyar da kansa, ya fāɗi rubda ciki. 32 Mala'ikan Ubangiji kuwa ya ce masa, “Me ya sa ka bugi jakarka har sau uku? Na fito ne don inhana ka, gama hanyarka ba daidai ba ce a gabana. 33 Jakar ta gan ni, ta kauce mini har sau uku. Da ba ta kakuce mini ba, lalle da na kashe ka, in bar ta da rai.” 34 Sai Bal'amu ya ce wa mala'ikan Ubangiji, “Na yi zunubi, gama ban sa ka tsaya a hanya don ka tarye ni ba. Yanzu fa, idan ka ga mugun abu ne, to, sai in koma.” 35 Ubangiji kuwa ya ce wa Bal'amu, “Tafi tare da mutanen, amma abin da na faɗa maka shi kaɗai za ka faɗa.” Sai Bal'amu ya tafi tare da dattawan Balak.

Balak ya Marabci Bal'amu

36 Sa'ad da Balak ya ji Bal'amu ya zo, sai ya fito ya tarye shi a Ar, wato wani birni a bakin Kogin Arnon, a kan iyakar Mowab. 37 Sai Balak ya ce wa Bal'amu, “Ashe, ban aika a kirawo ka ba? Me ya sa ba ka zo wurina ba, sai yanzu? Ko ban isa in ɗaukaka ka ba ne?” 38 Bal'amu ya amsa wa Balak ya ce, “To, ai, ga shi, na zo yanzu! Ina da wani ikon yin wata magana ne? Maganar da Allah ya sa a bakina, ita zan faɗa, tilas.” 39 Sai Bal'amu ya tafi tare da Balak suka je Kiriyat-huzot. 40 Can ya yi hadaya da shanu da tumaki, ya kuwa aika wa Bal'amu da dattawan da suke tare da shi. 41 Kashegari, sai Balak ya ɗauki Bal'amu ya kai shi kan Bamotba'al, daga can ya ga rubu'in mutanen.

Littafin Ƙidaya 23

1 Sai Bal'amu ya ce wa Balak, “Ka gina mini bagadai guda bakwai a nan, ka kawo mini bijimai bakwai da raguna bakwai.” 2 Balak ya yi yadda Bal'amu ya faɗa masa. Balak da Bal'amu suka miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade. 3 Sai Bal'amu ya ce wa Balak, “Tsaya kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa zan tafi can, in ga ko Ubangiji zai sadu da ni. Duk abin da ya bayyana mini, zan faɗa maka.” Ya kuwa tafi wani faƙo a kan tudu.

Bal'amu ya sa wa Isra'ila Albarka

4 Da Ubangiji ya sadu da Bal'amu, sai Bal'amu ya ce wa Ubangiji, “Na riga na shirya bagadai bakwai, na kuwa miƙa bijimi guda da rago guda a kan kowane bagade.” 5 Ubangiji kuwa ya sa magana a bakin Bal'amu ya ce, “Koma wurin Balak, ka faɗa masa abin da na faɗa maka.” 6 Sai ya koma wurin Balak, ya same shi da dukan dattawan Mowab suna tsaye kusa da hadayarsa ta ƙonawa. 7 Bal'amu kuwa ya faɗi jawabinsa, ya ce “Tun daga Aram Balak ya kawo ni, Shi Sarkin Mowab ne daga gabashin duwatsu. ‘Zo, la'anta mini Yakubu, Zo, ka tsine wa Isra'ila!’ 8 Ƙaƙa zan iya la'anta wanda Allah bai la'antar ba? Ƙaƙa zan iya tsine wa wanda Ubangiji bai tsine wa ba? 9 Gama daga kan duwatsu na gan su, Daga bisa kan tuddai na hange su, Jama'a ce wadda take zaune ita kaɗai, Sun sani sun sami albarka fiye da sauran al'ummai. 10 Wa zai iya ƙidaya yawan Isra'ilawa da suke kamar ƙura? Yawansu ya fi gaban lasaftawa. Bari ƙarshena ya zama kamar ɗaya daga cikin mutanen Allah, Bari in mutu cikin salama kamar adalai.” 11 Sai Balak ya ce wa Bal'amu, “Me ke nan ka yi mini? Na kawo ka domin ka la'anta abokan gābana, ga shi, sai albarka kake sa musu!” 12 Bal'amu kuwa ya ce, “Ai, ba tilas ne in hurta abin da Ubangiji ya sa a bakina ba?” 13 Sai Balak ya ce masa, “Zo, mu tafi wani wuri inda za ka gan su. Waɗanda suka fi kusa kaɗai ne za ka gani, amma ba za ka iya ganinsu duka ba. Ka la'anta mini su daga can.” 14 Ya kuwa kai shi saurar Zofim a bisa Dutsen Fisga. Sa'an nan ya gina bagadai bakwai, ya miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade. 15 Sai Bal'amu ya ce wa Balak, “Tsaya nan kusa da hadayarka ta ƙonawa, ni kuwa in tafi in sadu da Ubangiji a can.” 16 Ubangiji kuwa ya sadu da Bal'amu ya sa masa magana a baka, ya ce, “Koma wurin Balak ka faɗa masa abin da na faɗa maka.” 17 Sai Bal'amu ya koma wurin Balak ya same shi yana tsaye kusa da hadayarsa ta ƙonawa tare da dattawan Mowab. Balak kuwa ya ce masa, “Me Ubangiji ya faɗa?” 18 Sai Bal'amu ya faɗi jawabinsa, ya ce, “Tashi, Balak, ka ji, Ka kasa kunne gare ni, ya ɗan Ziffor. 19 Allah ba kamar mutum ba ne, da zai yi ƙarya, Ba kuwa ɗan mutum ba ne, da zai tuba. Zai cika dukan abin da ya alkawarta, Ya hurta, ya kuwa cika. 20 Ga shi, an umarce ni in sa albarka. Ya sa albarka, ba zan iya janye ta ba. 21 Bai ga mugunta ga Yakubu ba, Bai kuma ga wahala a Isra'ilawa ba. Ubangiji Allahnsu yana tare da su, Suna sowar murna domin shi sarkinsu ne. 22 Allah ne ya fisshe shi daga Masar, Ya yi yaƙi dominsu kamar kutunkun ɓauna. 23 Ba wata maitar da za ta cuci Yakubu, Ba kuwa sihirin da zai cuci Isra'ilawa. Yanzu za a ce, ‘Duba irin abin da Allah ya yi domin Yakubu, wato Isra'ilawa!’ 24 Ga shi, jama'ar Isra'ila tana kama da ƙaƙƙarfan zaki, Ba zai kwanta ba sai ya cinye ganimarsa. Ya lashe jinin waɗanda ya kashe.” 25 Sai Balak ya ce wa Bal'amu, “Kada ka la'anta su, kada kuma ka sa musu albarka.” 26 Bal'amu kuwa ya amsa wa Balak, ya ce, “Ban faɗa maka ba, duk abin da Ubangiji ya faɗa, shi ne zan yi?” 27 Sai Balak ya ce wa Bal'amu, “In ka yarda ka zo in kai ka wani wuri, watakila Allah zai yarda ka la'anta mini su a can.” 28 Balak kuwa ya kai Bal'amu a ƙwanƙolin Dutsen Feyor wanda yake fuskantar hamada. 29 Sai Bal'amu ya ce wa Balak, “Ka gina mini bagadai bakwai, ka shirya mini bijimai bakwai da raguna bakwai.” 30 Balak ya yi yadda Bal'amu ya faɗa masa. Ya miƙa bijimi da rago a kan kowane bagade.

Littafin Ƙidaya 24

1 Da Bal'amu ya gane Ubangiji yana jin daɗin sa wa Isra'ilawa albarka bai tafi neman shawara kamar dā ba, sai ya fuskanci jeji, 2 ya ta da idanunsa ya ga Isra'ilawa sun yi zango kabila kabila. Sai Ruhun Allah kuwa ya sauko masa. 3 Sai ya yi annabcinsa, ya ce. “Faɗar Bal'amu ɗan Beyor, Faɗar mutumin da idonsa ke a buɗe. 4 Faɗar wanda yake jin faɗar Allah, Shi wanda yake ganin wahayin Maɗaukaki, Yana durƙushe, amma idanunsa a buɗe suke. 5 Alfarwan Isra'ilawa suna da kyan gani! 6 Kamar dogon jerin itatuwan dabino, Kamar gonaki a gefen kogi, Kamar itatuwan aloyes da Ubangiji ya dasa, Kamar kuma itatuwan al'ul a gefen ruwaye. 7 Sojojin Isra'ilawa za su sa al'ummai rawar jiki, Za su yi mulkin jama'a mai yawa Sarkinsu zai fi Agag girma, Za a ɗaukaka mulkinsa. 8 Allah ne ya fisshe su dada Masar, Kamar kutunkun ɓauna yake a gare su, Yakubu zai cinye maƙiyansa, Zai kakkarya ƙasusuwansu, ya mummurɗe kibansu. 9 Al'ummar tana kama da ƙaƙƙarfan zaki Sa'ad da yake barci, ba wanda zai yi ƙarfin hali ya tashe shi. Duk wanda ya sa muku albarka zai sami albarka, Duk wanda ya sa muku la'ana zai sami la'ana.”

Annabcin Bal'amu

10 Sai Balak ya husata da Bal'amu, ya tafa hannunsa ya ce wa Bal'amu, “Na kirawo ka don ka la'anta maƙiyana, amma ga shi, har sau uku kana sa musu albarka. 11 Yanzu sai ka tafi abinka. Hakika, na ce zan ɗaukaka ka, amma ga shi, Ubangiji ya hana maka ɗaukakar.” 12 Sai Bal'amu ya ce wa Balak, “Ashe, ban faɗa wa manzanninka waɗanda ka aiko gare ni ba? 13 Na ce, ‘Ko da Balak zai ba ni gidansa cike da azurfa da zinariya, ba zan iya in zarce maganar Ubangiji ba, in aikata nagarta ko mugunta bisa ga nufin kaina.’ Abin da Ubangiji ya faɗa shi ne zan faɗa.” 14 Bal'amu ya ce wa Balak, “Yanzu fa, zan koma wurin mutanena. Ka zo in sanar maka da abinda mutanen nan za su yi wa mutanenka nan gaba.” 15 Sai ya hurta jawabinsa, ya ce, “Faɗar Bal'amu ɗan Beyor, Faɗar mutumin da idonsa ke buɗe, 16 Faɗar wanda yake jin faɗar Allah, Wanda ya san hikimar Maɗaukaki, Wanda yake ganin wahayin Mai Iko Dukka, Yana durƙurshe, amma idanunsa a buɗe suke. 17 Ina ganinsa, amma ba yanzu ba, Ina hangensa, amma ba kusa ba. Tauraro zai fito daga cikin Yakubu, Kandiri zai fito daga cikin Isra'ila, Zai ragargaje goshin Mowabawa, Zai kakkarya 'ya'yan Shitu duka. 18 Za a mallaki Edom, Hakka kuma za a mallaki Seyir abokiyar gābanta, Isra'ila za ta gwada ƙarfi. 19 Yakubu zai yi mulki, Zai hallaka waɗanda suka ragu cikin birni.” 20 Sai ya dubi Amalek, ya hurta jawabinsa, ya ce, “Amalek na fari ne cikin al'ummai, amm ƙarshensa hallaka ne.” 21 Sai kuma ya dubi Keniyawa, ya hurta jawabinsa, ya ce, “Wurin zamanku mai ƙarƙo ne, Gidajenku kuma suna cikin duwatsu. 22 Duk da haka za a lalatar da Keniyawa. Har yaushe za ku zama bayin Assuriyawa?” 23 Sai kuma ya hurta jawabinsa, ya ce, “Kaito, wa zai rayu sa'ad da Allah ya yi wannan? 24 Jiragen ruwa kuwa za su zo daga Kittim, Za su wahalar da Assuriya da Eber, Su kuma da kansu za su lalace.” 25 Sai Bal'amu ya tashi ya koma garinsu, Balak kuma ya yi tafiyarsa.

Littafin Ƙidaya 25

Isra'ilawa sun yi Sujada ga Ba'al-feyor

1 Sa'ad da Isra'ilawa suka yi zango a Shittim, maza suka fara yin lalata da matan Mowabawa. 2 Waɗannan mata sukan gayyaci mutanen zuwa wajen shagalin tsafinsu. Isra'ilawa kuwa sukan ci abinci, su kuma yi sujada ga gumaka. 3 Ta haka Isra'ilawa suka shiga bautar gumakan Ba'al na Feyor. Sai Ubangiji ya husata da Isra'ilawa. 4 Ya ce wa Musa, “Ɗauki sugabannin jama'a, ka rataye su a rana a gabana don in huce daga fushin da nake yi da Isra'ilawa.” 5 Musa kuwa ya ce wa alƙalan Isra'ilawa, “Kowa ya kashe mutanensa da suka shiga bautar gumakan Ba'al-feyor.” 6 Sai ga wani Ba'isra'ile ya taho da wata mace, Bamadayaniya, ya kai ta alfarwarsa ƙiriƙiri a gaban Musa da dukan taron jama'ar Isra'ila a sa'ad da suke kuka a ƙofar alfarwa ta sujada. 7 Finehas ɗan Ele'azara, wato jikan Haruna, firist, ya gani, sai ya tashi daga cikin taron, ya ɗauki mashi. 8 Ya bi Ba'isra'ilen, har zuwa ƙuryar alfarwar, ya soke dukansu biyu, Ba'isra'ilen da macen, har ya sha zarar macen. Da haka aka tsai da annoba daga Isra'ilawa. 9 Duk da haka annobar ta kashe mutane dubu ashirin da dubu huɗu (24,000 ). 10 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 11 “Finehas ɗan Ele'azara, wato jikan Haruna, firist, ya kawar da fushina daga Isra'ilawa saboda ya yi kishi irin nawa a gabansu, don haka ban shafe Isra'ilawa saboda kishina ba. 12 Domin haka ina yi masa alkawarin da ba zai ƙare ba. 13 Alkawarin zai zama nasa da na zuriyarsa, wato alkawarin zama firist din din din, domin ya yi kishi saboda Allahnsa. Ya kuwa yi kafara domin Isra'ilawa.” 14 Sunan Ba'isra'ilen da aka kashe tare da Bamadayaniyar, Zimri ɗan Salu, shi ne shugaban gidan Saminawa. 15 Sunan Bamadayaniya kuwa, Kozbi, 'yar Zur. Shi ne shugaban mutanen gidan ubansa a Madayana. 16 Ubangiji kuma ya umarci Musa, ya ce, 17 “Ku fāɗa wa Madayanawa ku hallaka su. 18 Gama sun dame ku da makircinsu da suka yaudare ku a kan al'amarin Feyor da na Kozbi 'yar'uwarsu, 'yar shugaban Madayana, wadda aka kashe a ranar da aka yi annoba a Feyor.”

Littafin Ƙidaya 26

Ƙidaya ta Biyu

1 Bayan annobar, sai Ubangiji ya ce wa Musa da Ele'azara, ɗan Haruna, firist, 2 “Ku ƙidaya dukan taron jama'ar Isra'ila tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba bisa ga gidajen ubanninsu. Ku ƙidaya duk wanda ya isa zuwa yaƙi a cikin Isra'ilawa.” 3 Sai Musa da Ele'azara, firist, suka yi musu magana a filayen Mowab daura da Yariko, suka ce, 4 “A ƙidaya mutane tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba kamar yadda Ubangiji ya umarta.” Isra'ilawa waɗanda suka fita daga ƙasar Masar ke nan. 5 Ra'ubainu shi ne ɗan fari na Yakubu. 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, su ne Hanok, da Fallu, 6 da Hesruna, da Karmi. 7 Waɗannan yawansu ya kai dubu arba'in da uku da ɗari bakwai da talatin (43,730 ). 8 Fallu ya haifi Eliyab. 9 'Ya'yan Eliyab, maza su ne Yemuwel, da Datan, da Abiram. Datan da Abiram ne aka zaɓa daga cikin taron jama'ar, suna cikin ƙungiyar Kora wadda ta tayar wa Musa da Haruna, har ma da Ubangiji. 10 Ƙasa kuwa ta buɗe ta haɗiye su tare da Kora. Wuta kuma ta cinye sauran mutanen ƙungiyar, mutum ɗari biyu da hamsin suka mutu. Suka zama abin faɗakarwa. 11 Amma 'ya'yan Kora ba su mutu ba. 12 'Ya'yan Saminu, maza, bisa ga iyalansu, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin, 13 da Zohar, da Shawul. Waɗannan su ne iyalan kabilar Saminu. 14 Yawansu ya kai mutum dubu ashirin da biyu da ɗari biyu (22,200 ). 15 Zuriyar Gad bisa ga iyalansu, su ne Zifiyon, da Haggi, da Shuni, 16 da Ezbon, da Eri, 17 da Arodi, da Areli. 18 Waɗannan su ne iyalan kabilar Gad. Yawan mutanensu ya kai dubu arba'in da ɗari biyar (40,500 ). 19 Kabilar Yahuza ke nan, (Er, da Onan, 'ya'yan Yahuza sun mutu a ƙasar Kan'ana). 20 Sauran 'ya'yansa bisa ga iyalansu su ne, Shela, da Feresa, da Zera, 21 da Hesruna, da Hamul. 22 Waɗannan su ne iyalan kabilar Yahuza. Yawan mutanensu ya kai dubu saba'in da shida da ɗari biyar (76,500 ). 23 Kabilar Issaka ke nan bisa ga iyalansu, da Tola, da Fuwa, 24 da Yashub, da Shimron. 25 Waɗannan su ne iyalan kabilar Issaka. Yawansu ya kai mutum dubu sittin da huɗu da ɗari uku (64,300 ). 26 Kabilar Zabaluna ke nan bisa ga iyalansu, Sered, da Elon, da Yaleyel. 27 Waɗannan su ne iyalan kabilar Zabaluna. Yawansu ya kai mutum dubu sittin da ɗari biyar (60,500 ). 28 Kabilar Yusufu ke nan bisa ga iyalansu, wato Manassa da Ifraimu. 29 Kabilar Manassa, su ne Makir ɗan Manassa. Makir ya haifi Gileyad wanda ya zama tushen zuriyar Gileyad. 30 'Ya'yan Gileyad, maza su ne Abiyezer, da Helek, 31 da Asriyel, da Shekem, 32 da Shemida, da Hefer. 33 Zelofehad, ɗan Hefer, ba shi da 'ya'ya maza, sai dai 'ya'ya mata. Sunayen 'ya'yansa mata su ne Mala, da Nowa, da Hogla, da Milka, da Tirza. 34 Waɗannan su ne iyalan kabilar Manassa. Yawansu ya kai mutum dubu hamsin da biyu da ɗari bakwai (52,700 ). 35 Waɗannan su ne kabilar Ifraimu bisa ga iyalansu, Shutela, da Beker, da Tahat. 36 Iyalin Eran suna lasafta kansu, daga zuriyar Shutela ne. 37 Waɗannan su ne iyalan kabilar Ifraimu. Yawansu ya kai dubu talatin da biyu da ɗari biyar (32,500 ). 38 Kabilar Biliyaminu ke nan bisa ga iyalansu, Bela, da Ashbel, da Ahiram, 39 da Shuffim, da Huffim. 40 Iyalin Adar da na Na'aman suna lasafta kansu, su daga zuriyar Bela ne. 41 Waɗannan su ne 'ya'yan Biliyaminu bisa ga iyalansu. Yawansu ya kai mutum dubu arba'in da biyar da ɗari shida (45,600 ). 42 Waɗannan su ne kabilar Dan bisa ga iyalansu, Hushim. Waɗannan su ne iyalan kabilar Dan. 43 Yawansu ya kai dubu sittin da huɗu da ɗari huɗu (64,400 ). 44 Kabilar Ashiru ke nan bisa ga iyalansu, Yimna, da Yishwi, da Beriya. 45 Iyalin Beriya kuwa su Eber, da Malkiyel, suna lasafta kansu a zuriyar Beriya. 46 Sunan 'yar Ashiru Sera. 47 Waɗannan su ne iyalan kabilar Ashiru. Yawansu ya kai mutum dubu hamsin da uku da ɗari huɗu (53,400 ). 48 Kabilar Naftali ke nan bisa ga iyalansu, Yezeyel, da Guni, 49 da Yezer, da Shallum. 50 Waɗannan su ne iyalan kabilar Naftali. Yawansu ya kai mutum dubu arba'in da biyar da ɗari huɗu (45,400 ). 51 Jimillar Isra'ilawa maza waɗanda aka ƙidaya, dubu ɗari shida da dubu ɗaya da ɗari bakwai da talatin (601,730 ).

An Raba Ƙasa ta Hanyar Kuri'a

52 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, 53 “A raba wa waɗannan mutane gādon ƙasar bisa ga yawan kowace kabila. 54 Za ka ba babbar kabila babban rabo, ka ba ƙaramar kabila ƙaramin rabo. Kowace kabila za a ba ta gādo bisa ga yawanta. 55 Amma za a rarraba musu gādon ƙasar kabila kabila ta hanyar kuri'a. 56 Za a rarraba gādo tsakanin manya da ƙananan kabilai ta hanyar kuri'a.”

Kabilar Lawi

57 Waɗannan su ne Lawiyawan da aka ƙidaya bisa ga iyalansu, Gershon, da Kohat, da Merari. 58 Sauran iyalin Lawiyawa daga zuriyar Libni ne, da Hebron, da Mali, da Mushi, da Kora. Kohat shi ne mahaifin Amram, 59 wanda ya auri Yokabed 'yar Lawi wadda aka haifa masa a Masar. Yokabed ta haifa wa Amram, Haruna, da Musa, da Maryamu, 'yar'uwarsu. 60 Haruna yana da 'ya'ya huɗu maza, Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar. 61 Amma Nadab da Abihu sun mutu saboda sun miƙa hadaya da haramtacciyar wuta a gaban Ubangiji. 62 Mazan da aka ƙidaya daga mai wata guda zuwa gaba sun kai dubu ashirin da dubu uku (23,000 ). Ba a haɗa jimillarsu tare da ta sauran Isra'ilawa ba, da yake ba a ba su gādo tare da su ba.

Joshuwa da Kalibu kaɗai suka Ragu

63 Waɗannan su ne Isra'ilawa waɗanda Musa da Ele'azara, firist, suka ƙidaya a filayen Mowab wajen Kogin Urdun daura da Yariko. 64 Amma a cikin waɗannan da aka ƙidaya, ba wanda ya ragu daga Isra'ilawa waɗanda Musa da Haruna, firist, suka ƙidaya a jejin Sina'i. 65 Gama Ubangiji ya riga ya yi magana a kansu, cewa lalle za su mutu a jeji. Ba wani mutumin da ya ragu daga cikinsu, sai dai Kalibu ɗan Yefunne, da Joshuwa ɗan Nun.

Littafin Ƙidaya 27

Roƙon 'Ya'yan Zelofehad Mata

1 Sai 'ya'yan Zelofehad, mata, ɗan Hefer ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manassa, ɗan Yusufu, suka tafi ƙofar alfarwa ta sujada. Sunayen 'ya'ya, matan ke nan, Mala, da Nowa, da Hogla, da Milka, da Tirza. 2 Da suka tafi, suka tsaya a gaban Musa da Ele'azara, firist, da gaban shugabanni, da dukan taron jama'a, suka ce, 3 “Mahaifinmu ya rasu cikin jeji. Ba ya cikin ƙungiyar Kora wadda ta tayar wa Ubangiji. Ya rasu saboda alhakin zunubinsa. Ga shi, ba shi da 'ya'ya maza. 4 Don me za a tsame sunan mahaifinmu daga cikin zuriyar iyalinsa saboda ba shi da ɗa? In ka yarda, muna roƙonka ka ba mu gādo tare da 'yan'uwan mahaifinmu.” 5 Musa ya kai maganarsu a gaban Ubangiji. 6 Ubangiji ya ce wa Musa, 7 “Maganar 'ya'yan Zelofehad, mata, daidai ce, saika ba su gādo tare da 'yan'uwan mahaifinsu. Za ka sa gādon mahaifinsu ya zama nasu. 8 Sai kuma ka shaida wa Isra'ilawa, ka ce, ‘Idan mutum ya rasu ba shi da ɗa, sai 'yarsa ta ci gādonsa. 9 Idan kuwa ba shi da 'ya, sai a ba 'yan'uwansa gādonsa. 10 Idan kuma ba shi da 'yan'uwa, sai a ba 'yan'uwan mahaifinsa gādonsa. 11 Idan kuma ba shi da su, sai a ba danginsa na kusa su mallaka, wannan zai zama umarni da ka'ida ga Isra'ilawa kamar yadda ni, Ubangiji na umarce ka.’ ”

An Zaɓi Joshuwa ya Gāji Musa

12 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa kan Dutsen Abarim, ka dubi ƙasa wadda na ba Isra'ilawa. 13 Bayan da ka gan ta, za ka mutu kamar yadda Haruna ya yi, 14 domin ba ku yi biyayya da umarnina ba a jejin Zin. Lokacin da dukan jama'a suka yi mini gunaguni a Meriba, ba ku nuna ikona mai tsarki a gabansu ba.” (Wannan shi ne ruwan Meriba na Kadesh a jejin Zin.) 15 Musa kuwa ya ce wa Ubangiji, 16 “Bari Ubangiji Allah na ruhohin dukan 'yan adam ya shugabantar da mutum a kan taron jama'ar, 17 mutumin da zai shugabance su cikin yaƙi, don kada taron jama'ar Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyaya.” 18 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Joshuwa, ɗan Nun, mutumin da ya dace, ka ɗibiya masa hannuwanka, 19 ka sa shi ya tsaya a gaban Ele'azara, firist, da gaban dukan taron, sa'an nan ka keɓe shi a gabansu. 20 Ka danƙa masa ikonka don taron jama'ar Isra'ila su yi masa biyayya. 21 Zai dogara ga Ele'azara, firist, don ya san nufina, ta wurin amfani da Urim da Tummin. Ta haka ne Ele'azara zai bi da Joshuwa da dukan taron jama'ar Isra'ila cikin al'amuransu.” 22 Musa kuwa ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Joshuwa, ya sa shi ya tsaya a gaban Ele'azara, firist, da gaban dukan taron. 23 Ya ɗibiya hannuwansa a kansa, ya keɓe shi kamar yadda Ubangiji ya umarta.

Littafin Ƙidaya 28

Hadaya na Kullum

1 Sai Ubangiji ya umarce Musa, 2 ya dokaci Isra'ilawa su tabbatar cewa sun miƙa wa Allah hadaya ta abinci tare da hadayun da za a yi da wuta, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji a ƙayyadadden lokaci bisa ga yadda ake bukata. 3 Waɗannan su ne hadayu na abinci da za a miƙa wa Ubangiji, hadaya ta ƙonawa ta kowace rana, raguna biyu 'yan bana ɗaya ɗaya marasa lahani. 4 A miƙa ɗan rago ɗaya da safe, ɗaya kuma da maraice, 5 da kuma mudun lallausan gari, kwaɓaɓɓe da man zaitun mafi kyau har rubu'in moɗa. 6 Hadaya ce ta ƙonawa kullum, wadda aka kafa a Dutsen Sina'i, don daɗin ƙanshi, hadayar da akan yi da wuta ga Ubangiji. 7 Hadaya ta sha za ta zama rubu'in moɗa na ruwan inabi domin kowane ɗan rago. Za a kwarara hadaya ta sha mai gafi ga Ubangiji a bagade. 8 Ɗayan ɗan ragon kuma za a miƙa da maraice, tare da hadaya ta gari kamar ta safe, da hadayarsa ta sha. Za a miƙa shi hadaya ta ƙonawa, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

Hadayu na Ranar Asabar

9 A rana Asabar kuwa za a miƙa 'yan raguna biyu bana ɗaya ɗaya marasa lahani da mudu biyu na lallausan gari, kwaɓaɓɓe da mai, domin yin hadaya ta gari tare da hadayarsa ta sha. 10 Wannan ita ce hadaya ta ƙonawa ta kowace ranar Asabar, banda hadaya ta ƙonawa ta kullum, tare da hadaya ta sha.

Hadayu na Ɗaya ga Wata

11 A farkon kowane wata sai a miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, da 'yan bijimai biyu, da rago ɗaya, da kuma 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya marasa lahani, 12 hadaya ta gari kuma, a kwaɓa gari humushi uku na garwa da man zaitun don kowane bijimi, da gari humushi biyu na garwa don rago, 13 da kuma gari humushin garwa don ɗan rago. Waɗannan su ne hadayu na abinci na ƙonawa, mai daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 14 Hadaya ta sha kuwa za ta zama rabin moɗa na ruwan inabi don kowane bijimi, sulusin moɗa kuma don kowane rago, rubu'in moɗa don kowane ɗan rago. Wannan ita ce ka'idar hadaya ta ƙonawa don tsayawar kowane wata na shekara. 15 A kuma miƙa bunsuru ɗaya na yin hadaya don zunubi ga Ubangiji tare da hadaya ta ƙonawa, da hadayarta ta sha.

Hadayu na Idin Abinci Marar Yisti

16 Za a yi Idin Ƙetarewa ga Ubangiji a rana ta goma sha huɗu ga watan fari. 17 Kashegari kuwa za a fara idin kwana bakwai. A kwanakin nan, sai a riƙa cin abinci marar yisti. 18 Za ku yi tsarkakakken taro a ranar fari ta idin, ba za a yi aiki ba. 19 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da bijimai biyu, da rago ɗaya, da 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya ga Ubangiji. Dukansu su zama marasa lahani. 20 Za a kuma miƙa hadaya ta gari tare da dabbobin, da lallausan gari wanda aka kwaɓa da man zaitun, gari humushi uku na garwa tare da kowane bijimi, da gari humushi biyu tare da kowane rago, 21 gari humushi ɗaya tare da kowane ɗan rago. 22 Za a miƙa bunsuru guda don yin hadaya don zunubi, domin yin kafara. 23 Za a miƙa waɗannan hadayu banda hadaya ta ƙonawa wadda akan miƙa kowace safiya. 24 Haka za a miƙa abinci na hadaya ta ƙonawa kowace rana har kwana bakwai, domin daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Za a kuma riƙa miƙa hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta sha. 25 A rana ta bakwai za a yi tsattsarkan taro, ba za a yi aiki ba.

Hadayun Idin Girbi

26 Za a yi tsattsarkan taro a ranar nunan fari, wato idi na mako bakwai lokacin da za a miƙa wa Ubangiji hadaya da sabon hatsi. A ranar ba za a yi aiki ba. 27 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa, da 'yan bijimai biyu, da rago ɗaya, da 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji. 28 Za a miƙa hadaya ta gāri tare da dabbobin, da lallausan gari wanda aka kwaɓa da mai, gari humushi uku na garwa, za a miƙa tare da kowane bijimi, humushi biyu na garwa don rago, 29 da humushin garwa don kowane ɗan rago. 30 Za a miƙa bunsuru guda saboda yin hadaya don zunubi, domin a yi kafara. 31 Banda hadaya ta ƙonawa ta kullum, sai a miƙa waɗannan tare da hadayarsu ta sha. Dabbobin su zama marasa lahani.

Littafin Ƙidaya 29

Hadayu na Idin Watan Bakwai

1 A rana ta fari ga wata na bakwai za a taru domin yin sujada, ba za a yi aiki a ranar ba. A ranar za a busa ƙahoni. 2 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da bijimi guda, da rago guda, da 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Dabbobin za su zama marasa lahani. 3 Tare da dabbobin za a kuma miƙa hadaya ta lallausan gāri kwaɓaɓɓe da mai. Za a miƙa gāri humushi uku na garwa tare da bijimin, humushi biyu na garwa kuma tare da ragon. 4 Za a miƙa humushin garwa na gāri tare da kowane ɗan rago. 5 Sai kuma a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi domin a yi kafara. 6 Banda waɗannan hadayu kuma, sai a miƙa hadaya ta ƙonawa tare da hadayarta ta gari, da akan yi a tsayawar wata, da kuma hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri, da hadayarsu ta sha. Sai a yi su bisa ga ka'idar yinsu. Hadaya ke nan da akan yi da wuta don daɗin ƙanshi ga Ubangiji.

Hadaya a Ranar Kafara

7 Za a yi tsattsarkan taro a rana ta goma ga watan bakwai domin yin sujada. Ba za a ci abinci ba, ba kuwa za a yi aiki ba. 8 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da bijimi ɗaya, da rago guda, da 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Dabbobin nan su zama marasa lahani. 9 Tare da dabbobin za a miƙa hadaya ta gāri kwaɓaɓɓe da mai. Za a miƙa gāri humushi uku na garwa tare da bijimi, da gāri humushi biyu na garwa tare da ragon, 10 da humushin garwa kuma tare da kowane ɗan rago. 11 Za a kuma miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, banda hadaya don zunubi saboda yin kafara, da hadaya ta ƙonawa ta kullum, tare da hadayarta ta gāri, da hadayarsu ta sha.

Hadayu na Idin Bukkoki

12 A rana ta goma sha biyar ga watan bakwai za a yi tsattsarkan taro domin yin sujada, ba za a yi aiki ba. Su kiyaye idin da girmama Ubangiji har kwana bakwai. 13 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da 'yan bijimai goma sha uku, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Dabbobin nan su zama marasa lahani. 14 Tare da dabbobin za a miƙa hadaya ta lallausan gāri wanda aka kwaɓa da mai. Za a miƙa gāri humushi uku na garwa tare da kowane bijimi, da gāri humushi biyu na garwa tare da kowane rago, 15 da humushin garwa kuma tare da kowane ɗan rago. 16 Za a kuma miƙa bunsuru guda saboda yin hadaya don zunubi. Banda waɗannan hadayu kuma za a riƙa yin hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 17 A rana ta biyu ta idin za a miƙa bijimai goma sha biyu, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dukan dabbobin su zama marasa lahani. 18 Za a kuma miƙa hadaya ta gari da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 19 Za a kuma miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gari, da hadayarsu ta sha. 20 A rana ta uku ta idin za a miƙa bijimai goma sha ɗaya, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dabbobin su zama marasa lahani. 21 Za a kuma miƙa hadaya ta gari da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 22 Za a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 23 A rana ta huɗu ta idin za a miƙa bijimai goma, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dabbobin su zama marasa lahani. 24 Za a kuma miƙa hadaya ta gāri da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 25 Za a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 26 A rana ta biyar ta idin za a miƙa bijimai tara, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dabbobin su zama marasa lahani. 27 Za a kuma miƙa hadaya ta gāri da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 28 Za a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 29 A rana ta shida ta idin za a miƙa bijimai takwas, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dabbobin su zama marasa lahani. 30 Za a kuma miƙa hadaya ta gāri da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 31 Za a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya taƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 32 A rana ta bakwai ta idin za a miƙa bijimai bakwai, da raguna biyu, da 'yan raguna goma sha huɗu bana ɗaya ɗaya. Dabbobin su zama marasa lahani. 33 Za a kuma miƙa hadaya ta gāri da hadayu na sha tare da bijiman, da ragunan, da 'yan ragunan bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 34 Za a kuma miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 35 A rana ta takwas za a taru domin yin sujada. Ba za a yi aiki ba. 36 Za a miƙa hadaya ta ƙonawa da bijimi, da rago, da 'yan raguna bakwai bana ɗaya ɗaya don daɗin ƙanshi ga Ubangiji. Dabbobin su zama marasa lahani. 37 Za a miƙa hadaya ta gāri da hadaya ta sha tare da bijimin, da ragon, da 'yan ragunan, bisa ga adadinsu, da kuma bisa ga ka'idar. 38 Za a miƙa bunsuru guda saboda hadaya don zunubi, duk da hadaya ta ƙonawa ta kullum tare da hadayarta ta gāri da hadayarta ta sha. 39 Waɗannan su ne hadayun da za a miƙa wa Ubangiji a lokacin idodinsu, duk da hadayunsu na wa'adi, da na yardar rai, da na ƙonawa, da na gāri, da na sha, da na salama. 40 Musa kuwa ya faɗa wa jama'ar Isra'ila kome da kome kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.

Littafin Ƙidaya 30

Doka a kan Wa'adodin Mata

1 Musa ya kuma ce wa shugabannin kabilan Isra'ilawa, “Ga abin da Ubangiji ya umarta.” 2 Idan mutum ya yi wa'adi ga Ubangiji, ko kuwa ya rantse zai yi wani abu, ko kuwa ba zai yi wani abu ba, to, kada ya warware maganarsa, amma sai ya aikata abin da bakinsa ya hurta. 3 Idan kuma mace ta yi wa'adi ga Ubangiji, ta kuma ɗaure kanta da rantsuwa tun tana yarinya a gidan mahaifinta, 4 idan mahaifinta ya ji wa'adinta da rantsuwarta wadda ta ɗaure kanta da su, bai ce mata kome ba, to, sai wa'adinta da rantsuwarta su tabbata. 5 Amma idan mahaifinta ya ji, ya nuna rashin yarda, to, wa'adinta da rantsuwarta ba za su tsaya ba, Ubangiji kuwa zai gafarce ta domin mahaifinta bai yardar mata ba. 6 Idan kuwa ta yi aure lokacin da take da wa'adi ko kuwa rantsuwar da ta yi da garaje, 7 idan mijinta ya ji wa'adin ko rantsuwar amma bai ce mata kome ba a ranar da ya ji, to, sai wa'adinta da rantsuwarta su tabbata. 8 Amma idan mijinta bai goyi bayanta a ranar da ya ji ba, to, sai wa'adinta da rantsuwarta su warware, Ubangiji kuwa zai gafarce ta. 9 Mace wadda mijinta ya rasu ko sakakkiya, dole ta cika wa'adin da ta yi, da kowane alkawari, za su tabbata. 10 Idan macen aure ta yi wa'adi ko alkawari ba za ta yi wani abu ba, 11 idan mijinta ya ji, amma bai ce mata kome ba, to, sai wa'adinta da kowace irin rantsuwarta su tabbata. 12 Amma idan mijinta ya hana ta a ranar da ya ji, to, sai ta bari. Mijinta ya hana ta ɗaukar wa'adin, Ubangiji kuwa zai gafarce ta. 13 Mijinta yana da iko ya tabbatar, ko kuwa ya rushe kowane wa'adi da kowane irin alkawarin da ta ɗauka. 14 Idan mijinta ya yi shiru, bai ce mata kome ba, to, dole ta cika kowane abu da ta yi wa'adi da wanda kuma ta ɗauki alkawarinsa. Shirun da ya yi ya yardar mata. 15 Amma idan ya ji, sa'an nan daga baya ya hana ta, to, zai sha hukunci a maimakon matar. 16 Waɗannan su ne dokokin da Ubangiji ya ba Musa a kan wa'adodin matar aure da na wadda ba ta yi aure ba, wato matar da take zaune a gidan mahaifinta.

Littafin Ƙidaya 31

Yaƙin Jihadi da Madayanawa

1 Ubangiji ya ce wa Musa, 2 “Ka ɗaukar wa Isra'ilawa fansa a kan Madayanawa. Bayan ka yi wannan za ka mutu.” 3 Musa kuwa ya ce wa jama'a, “Ku sa mazajen da suke cikinku su yi shiri, su yi ɗamarar yaƙi, don su tafi su yi yaƙi da Madayanawa, su ɗaukar wa ubangiji fansa a kansu. 4 Sai ku aiki mutum dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra'ila zuwa wurin yaƙi.” 5 Aka samo mutum dubu goma sha biyu (12,000 ) shiryayyu don yaƙi, daga cikin dubban Isra'ilawa, mutum dubu ɗaya daga kowace kabila. 6 Musa ya aike su zuwa yaƙi tare da Finehas, ɗan Ele'azara firist, da akwatin alkawari, da ƙahonin kiran yaƙi a hannun Finehas. 7 Suka yi yaƙi da Madayanawa suka kashe musu kowane namiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 8 Suka kashe har da sarakuna biyar na Madayanawa, da Ewi, da Rekem, da Zur, da Hur, da Reba. Suka kuma kashe Bal'amu ɗan Beyor. 9 Isra'ilawa suka kwashi mata da yaran Madayanawa bayi. Suka washe shanunsu, da tumakinsu da dukan dukiyarsu ganima. 10 Suka kuma ƙone dukan biranen zamansu da dukan san saninsu da wuta. 11 Da mutum da dabba sun kwashe su ganima. 12 Suka kawo bayin da ganimar a wurin Musa, da Ele'azara firist, da taron jama'ar Isra'ila a zango a filayen Mowab a Kogin Urdun daura da Yariko.

Sojoji Sun Komo

13 Sai Musa da Ele'azara firist, da shugabannin taron jama'ar Isra'ila suka fita zango su tarye su. 14 Musa kuwa ya husata da shugabannin sojoji waɗanda ke shugabannin dubu dubu da shugabannin ɗari ɗari, waɗanda suka dawo daga wurin yaƙi. 15 Ya tambaye su ya ce, “Don me kuka bar dukan mata da rai? 16 Ku tuna fa, su ne, ta wurin shawarar Bal'amu, suka yaudari Isra'ilawa, suka saɓi Ubangiji cikin maƙidar Feyor, har annoba ta fasu a jama'ar Ubangiji. 17 Yanzu, sai ku kashe dukan yara maza da kowace mace wadda ta san namiji. 18 Amma dukan 'yan mata da ba su san maza ba, sai ku bar wa kanku. 19 A cikinku duk wanda ya kashe mutum ko ya taɓa gawa, sai ya zauna a bayan zango kwana bakwai don ya tsarkake kansa tare da bayin a rana ta uku da ta bakwai. 20 Za ku tsarkake kowace riga, da kowane abu da aka yi da fata, da kowane kaya da aka yi da gashin awaki, da kowane abu da aka yi da itace.” 21 Ele'azara firist kuwa, ya ce wa sojojin da suka tafi yaƙi, “Waɗannan su ne ka'idodin da Ubangiji ya ba Musa. 22 Zinariya, da azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da kuza, da darma, 23 da dukan abin da wuta ba ta ci ba, su ne za ku tsarkake su da wutar tsarkakewa, duk da haka za a kuma tsarkake shi da ruwa. Amma abin da wuta takan ci, sai a tsarkake shi da ruwa kawai. 24 Ku wanke tufafinku a rana ta bakwai don ku tsarkaka, bayan haka ku shiga zangon.”

Raba Ganima

25 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 26 “Da kai, da Ele'azara firist, da shugabannin gidajen kakannin taron jama'a, ku lasafta yawan mutane, da dabbobin da aka kwaso ganima. 27 Ku kasa ganima kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗayan kuwa ku ba taron jama'ar. 28 Sai ka karɓi na Ubangiji daga cikin kashin ganimar da aka baiwa sojojin da suka tafi yaƙi. Ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakai ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar. 29 Ka ba Ele'azara firist. Wannan hadaya ta ɗagawa ce ga Ubangiji. 30 Daga cikin rabin ganimar da aka ba Isra'ilawa, sai ka ɗauki ɗaya ɗaya daga cikin mutum hamsin, da shanu hamsin, da jakai hamsin, da tumaki hamsin, da dukan dabbobin. Ka ba da su ga Lawiyawa waɗanda suke lura da alfarwar sujada ta Ubangiji.” 31 Musa da Ele'azara firist, suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa. 32 Yawan ganimar da sojoji suka kawo ke nan, tumaki dubu ɗari shida da dubu saba'in da dubu biyar (675,000 ), 33 shanu dubu saba'in da dubu biyu (72,000 ), 34 jakai dubu sittin da dubu ɗaya (61,000 ), 35 'yan mata dubu talatin da dubu biyu (32,000 ) waɗanda ba su san namiji ba. 36 Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi ne nan, tumaki dubu ɗari uku da talatin da bakwai da ɗari biyar (337,500 ). 37 Daga ciki aka fitar da tumaki ɗari shida da saba'in da biyar domin Ubangiji. 38 Shanu kuma dubu talatin da dubu shida (36,000 ), daga ciki aka fitar da shanu saba'in da biyu domin Ubangiji. 39 Jakai dubu talatin da ɗari biyar (30,500 ), daga ciki aka fitar da jakai sittin da ɗaya domin Ubangiji. 40 'Yan mata dubu goma sha shida (16,000 ), daga ciki aka fitar da 'yan mata talatin da biyu domin Ubangiji. 41 Sai Musa ya ba Ele'azara firist rabon Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 42 Wannan shi ne kashin da aka ba jama'ar Isra'ila cikin kashin da aka ware daga na waɗanda suka tafi yaƙin. 43 Tumaki dubu ɗari uku da talatin da bakwai da ɗari bayar (337,500 ), 44 shanu dubu talatin da dubu shida (36,000 ), 45 jakai dubu talatin da ɗari biyar (30,500 ), 46 'yan mata dubu goma sha shida (16,000 ). 47 Daga rabin kashi na jama'ar Isra'ila, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na 'yan mata, da na dabbobi, ya ba Lawiyawan da suke lura da alfarwar sujada ta Ubangiji kamar yadda Ubangiji ya umarce shi. 48 Sai shugabannin da suka shugabanci rundunar yaƙin, suka zo wurin Musa. 49 Suka ce masa, “Mu barorinka mun ƙidaya mayaƙan da ke ƙarƙashin ikonmu, ba wanda ya ɓace daga cikinmu. 50 Mun kuwa kawo wa Ubangiji hadaya daga cikin abubuwan da kowannenmu ya samu, kayan ado na zinariya, da mundaye, da ƙawane da 'yan kunne, da duwatsun wuya, don yi wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.” 51 Musa da Ele'azara firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka. 52 Dukan zinariya da shugabanni suka bayar hadaya ga Ubangiji, nauyinta ya kai shekel dubu goma sha shida da ɗari bakwai da hamsin (16,750 ). 53 Kowane soja ya kwashi ganimarsa. 54 Musa da Ele'azara firist kuwa, suka karɓi zinariya da shugabanni suka bayar, suka kai su cikin alfarwa ta sujada don ta zama abin tunawa da jama'ar Isra'ila a gaban Ubangiji.

Littafin Ƙidaya 32

Kabilai a Gabashin Urdun

1 Kabilan Ra'ubainu da Gad suna da dabbobi da yawa ƙwarai. Da suka ga ƙasar Yazar da ta Gileyad wuri ne mai kyau domin shanu, 2 sai suka je wurin Musa da Ele'azara firist, da shugabannin taron jama'ar, 3 suka ce, “Atarot, da Dibon, da Yazar, da Bet-nimra, da Heshbon, da Eleyale, da Simba, da Nebo, da Ba'al-meyon, 4 ƙasar da Ubangiji ya ci da yaƙi a gaban taron jama'a, ƙasa ce mai kyau don dabbobi. Ga shi kuwa, barorinka suna da dabbobi da yawa. 5 Idan mun sami tagomashi a gare ka, ka ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu, kada ka kai mu a wancan hayin Urdun.” 6 Amma Musa ya amsa musu ya ce, “Wato sai 'yan'uwanku su yi ta yaƙi, ku kuwa ku yi zamanku a nan, ko? 7 Don me za ku karya zuciyar jama'ar Isra'ila daga hayewa zuwa ƙasar da Ubangiji ya ba su? 8 Haka iyayenku suka yi sa'ad da na aike su daga Kadesh-barneya don su dubo ƙasar. 9 Gama sa'ad da suka tafi Kwarin Eshkol suka ga ƙasar, suka karya zuciyar jama'a daga shigar ƙasar da Ubangiji ya ba su. 10 Saboda haka Ubangiji ya husata a ranan nan, har ya yi wa'adi ya ce, 11 ‘Hakika ba wani daga cikin mutanen da suka fito daga Masar, tun daga mai shekara ashirin zuwa gaba da zai ga ƙasar da na rantse zan ba Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, domin ba su bi ni sosai ba. 12 Sai dai Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, da Joshuwa ɗan Nun, domin su ne kaɗai suka bi ni sosai.’ 13 Saboda Ubangiji ya husata da isra'ilawa, shi ya sa suka yi ta yawo a jeji har shekara arba'in, wato sai da tsaran nan wadda ta aikata mugunta a gaban Ubangiji ta ƙare. 14 Ga shi, ku kuma da kuke 'ya'yan mugayen mutanen nan, ku da kuke a matsayin iyayenku, kuna so ku ƙara sa Ubangiji ya husata da Isra'ilawa. 15 Gama idan kun ƙi binsa, zai sāke yashe ku a jeji. Ku ne kuwa za ku zama sanadin hallakar mutanen nan duka.” 16 Sai suka zo kusa da shi, suka ce, “Za mu gina garu na dutse don mu kāre dabbobinmu, da birane don 'ya'yanmu a nan. 17 'Ya'yanmu za su zauna a biranen don gudun mazaunan ƙasar, amma mu za mu ɗauki makamai mu tafi tare da sauran Isra'ilawa, har mu kai su wuraren zamansu. 18 Ba kuwa za mu koma gidajenmu ba, sai lokacin da kowane Ba'isra'ile ya sami gādonsa. 19 Gama ba za mu ci gādo tare da su a wancan hayin Urdun ba, domin mun sami gādonmu a wannan hayi na gabashin Urdun.” 20 Sai Musa ya ce musu, “Idan za ku yi haka, wato ku ɗauki makamai, ku tafi yaƙi a gaban Ubangiji, 21 kowane sojanku ya haye Urdun a gaban Ubangiji, har lokacin da Ubangiji ya kori abokan gābansa daga gabansa, 22 har kuma lokacin da aka ci ƙasar a gaban Ubangiji kafin ku koma, to, za ku kuɓuta daga alhakinku a gaban Ubangiji da jama'ar Isra'ila. Wannan ƙasa kuwa za ta zama mallakarku a gaban Ubangiji. 23 Idan kuwa ba ku yi haka ba, kun yi wa Ubangiji laifi, ku tabbata fa alhakin zunubinku zai kama ku. 24 To, sai ku gina wa 'ya'yanku birane, ku gina wa garkunanku garu, amma ku aikata abin da kuka faɗa da bakinku.” 25 Sai Gadawa da Ra'ubainawa suka amsa wa Musa, suka ce, “Barorinka za su yi kamar yadda ka umarta. 26 'Ya'yanmu, da matanmu, da tumakinmu, da shanunmu za su zauna a birane a nan Gileyad. 27 Amma kowane soja a cikinmu zai haye a gaban Ubangiji zuwa yaƙi kamar yadda shugabanmu ya faɗa.” 28 Sai Musa ya yi wa Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan mutanen Isra'ila kashedi a kansu, 29 ya ce, “Idan kowane soja na Gadawa da Ra'ubainawa zai haye Urdun tare da ku don yaƙi har an ci ƙasar dominku, to, sai ku ba su ƙasar Gileyad ta zama mallakarsu. 30 Amma idan ba su haye tare da ku da shirin yaƙi ba, to, sai ku ba su gādo tare da ku a cikin ƙasar Kan'aniyawa.” 31 Gadawa da Ra'ubainawa kuwa suka ce, “Kamar yadda Ubangiji ya ce wa barorinka, haka za mu yi. 32 Za mu haye da shirin yaƙi a gaban Ubangiji zuwa cikin ƙasar Kan'aniyawa, amma za mu sami gādonmu a wannan hayin Urdun.” 33 Sa'an nan Musa ya ba Gadawa, da Ra'ubainawa, da rabin mutanen Manassa, ɗan Yusufu, mulkin Sihon, Sarkina Amoriyawa, da mulin Og, Sarkin Bashan, wato ƙasar da biranenta da karkaransu. 34 Sai Gadawa suka gina Dibon, da Atarot, da Arower, 35 da Atarot-shofan, da Yazar, da Yogbeha, 36 da Bet-nimra, da Bet-aram su zama birane masu garu da shinge don dabbobi. 37 Ra'ubainawa kuwa suka gina Heshbon da Eleyale, da Kiriyatayim, 38 da Nebo, da Ba'al-meyon, da Sibma. 39 Mutanen Makir, ɗan Manassa, suka tafi Gileyad, suka ci ta da yaƙi, suka kori Amoriyawan da suke cikinta. 40 Sai Musa ya ba mutanen Makir, ɗan Manassa, Gileyad, suka zauna ciki. 41 Yayir, ɗan Manassa, ya tafi ya ci ƙauyukansu da yaƙi, suka ba su suna Hawot-yayir. 42 Noba kuma ya tafi ya ci Kenat da ƙauyukanta da yaƙi, ya ba ta suna Noba bisa ga sunansa.

Littafin Ƙidaya 33

Tafe-tafe daga Masar zuwa Mowab

1 Waɗannan su ne wuraren da Isra'ilawa suka yi zango sa'ad da suka fita runduna runduna daga ƙasar Masar ta hannun Musa da Haruna. 2 Bisa ga faɗar Ubangiji, Musa ya rubuta wuraren tashinsu da wuraren saukarsu. Wuraren saukarsu da na tashinsu ke nan. 3 Sun tashi daga Ramases a rana ta goma sha biyar ga watan fari. A kashegarin Idin Ƙetarewa ne suka fita gabagaɗi a gaban dukan Masarawa. 4 Masarawa suna ta binne gawawwakin 'ya'yan farinsu da Ubangiji ya karkashe musu. Banda 'ya'yan farinsu kuma Ubangiji ya hukunta wa allolinsu. 5 Isra'ilawa kuwa suka tashi daga Ramases suka sauka a Sukkot. 6 Suka tashi daga Sukkot suka sauka a Etam wadda take a gefen jejin. 7 Da suka tashi daga Etam, sai suka juya zuwa Fi-hahirot wadda take gaban Ba'al-zefon suka sauka a gaban Migdol. 8 Da suka tashi daga gaban Fi-hahirot sai suka haye teku zuwa cikin jejin. Suka yi tafiya kwana uku a jejin Etam, suka sauka a Mara. 9 Suka tashi daga Mara suka zo Elim inda akwai maɓuɓɓugan ruwa guda goma sha biyu da itacen dabino guda saba'in. Sai suka sauka a can. 10 Suka tashi daga Elim, suka sauka a gefen Bahar Maliya. 11 Da suka tashi daga Bahar Maliya suka sauka a jejin Sin. 12 Suka tashi daga jejin Sin, suka sauka a Dofka. 13 Daga Dofka suka tafi Alush. 14 Suka tashi daga Alush suka sauka a Refidim inda mutane suka rasa ruwan sha. 15 Suka tashi daga Refidim suka sauka a jejin Sina'i. 16 Da suka tashi daga jejin Sina'i, sai suka sauka a Kibrot-hata'awa. 17 Suka tashi daga Kibrot-hata'awa suka sauka a Hazerot. 18 Da suka tashi daga Hazerot, sai suka sauka a Ritma. 19 Suka tashi daga Ritma suka sauka a Rimmon-farez. 20 Suka tashi daga Rimmon-farez, suka sauka a Libna. 21 Da suka tashi daga Libna, sai suka sauka a Rissa. 22 Da suka tashi daga Rissa, suka sauka a Kehelata. 23 Suka tashi daga Kehelata suka sauka a Dutsen Shifer. 24 Suka tashi daga Dutsen Shifer suka sauka a Harada. 25 Da suka tashi daga Harada, suka sauka a Makelot. 26 Suka tashi daga Makelot suka sauka a Tahat. 27 Suka tashi daga Tahat suka sauka a Tara. 28 Suka kama hanya daga Tara suka sauka a Mitka. 29 Suka kuma kama hanya daga Mitka suka sauka a Hashmona. 30 Daga Hashmona suka sauka a Moserot. 31 Da suka tashi daga Moserot suka sauka a Bene-ya'akan. 32 Suka tashi daga Bene-ya'akan suka sauka a Hor-hagidgad. 33 Da suka tashi daga Hor-hagidgad suka sauka a Yotbata. 34 Suka kama hanya daga Yotbata suka sauka a Abrona. 35 Da suka tashi daga Abrona, sai suka sauka a Eziyon-geber. 36 Suka tashi daga Eziyon-geber suka sauka a jejin Zin, wato Kadesh. 37 Da suka kama hanya daga Kadesh suka sauka a Dutsen Hor a kan iyakar ƙasar Edom. 38 Bisa ga umarnin Ubangiji, Haruna firist ya hau Dutsen Hor inda ya rasu a rana ta fari ga watan biyar a shekara ta arba'in ta fitowar jama'ar Isra'ila daga ƙasar Masar. 39 Haruna yana da shekara ɗari da ashirin da uku sa'ad da ya rasu a Dutsen Hor. 40 Sai Sarkin Arad, Bakan'ane wanda yake zaune a Negeb, a ƙasar Kan'ana, ya ji zuwan Isra'ilawa. 41 Isra'ilawa kuma suka tashi daga Dutsen Hor, suka sauka a Zalmona. 42 Daga Zalamona suka sauka a Funon. 43 Da suka tashi daga Funon, sai suka sauka a Obot. 44 Suka kuma kama hanya daga Obot suka sauka a Abarim a karkarar Mowab. 45 Suka tashi daga nan suka sauka a Dibon-gad. 46 Suka tashi daga Dibon-gad suka sauka a Almon-diblatayim. 47 Da suka tashi daga Almon-diblatayim, suka sauka a duwatsun Abarim a gaban Nebo. 48 Daga duwatsun Abarim suka sauka a filayen Mowab kusa da Urdun daura da Yariko. 49 Suka sauka kusa da Urdun, suka kakkafa alfarwansu tun daga Betyeshimot har zuwa Abel-shittim, a filayen Mowab.

Umarni kafin su Haye Urdun

50 Sai Ubangiji ya yi magana da Musa a filayen Mowab kusa da Urdun, daura da Yariko, ya ce 51 ya faɗa wa jama'ar Isra'ila, “Sa'ad da kuka haye Urdun zuwa ƙasar Kan'ana, 52 sai ku kori dukan mazaunan ƙasar daga gabanku ku rurrushe sassaƙaƙƙun duwatsunsu, da siffofinsu na zubi, da masujadansu. 53 Sa'an nan ku mallaki ƙasar, ku zauna a ciki, gama na ba ku ƙasar, ku mallake ta. 54 Za ku rarraba wa kanku gādon ƙasar kabila kabila ta hanyar jefar kuri'a. Za ku ba babbar kabila babban rabo, ƙaramar kabila kuwa ku ba ta ƙaramin rabo. Inda duk kuri'a ta fāɗa wa mutum, nan ne zai zama wurinsa. Bisa ga kabilan kakanninku za ku gāji ƙasar. 55 Amma idan ba ku kori mazaunan ƙasar daga gabanku ba, to, waɗannan da kuka bari cikinta za su zama haki a idanunku, da ƙayayuwa a kwiyaɓunku. Za su yi ta wahalshe ku da yaƙi. 56 Idan ba ku kore su ba, zan lalatar daku kamar yadda na shirya lalatar da su.”

Littafin Ƙidaya 34

Iyakokin Ƙasar

1 Ubangiji ya ba Musa 2 waɗannan umarnai domin jama'ar Isra'ila. Sa'ad da suka shiga ƙasar Kan'ana ga yadda iyakokin ƙasashensu za su zama. 3 Iyakar ƙasarsu daga wajen kudu ta miƙa tun daga wajen jejin Zin, har zuwa iyakar Edom. Iyakarsu kuwa ta wajen kudu za ta fara daga ƙarshen Tekun Gishiri wajen gabas. 4 Sa'an nan kuma za ta nausa ta nufin hawan Akrabbim, ta ƙetare zuwa Zin, ta dangana da kudancin Kadesh-barneya, sa'an nan ta miƙa zuwa Hazar'addar, ta zarce ta bi ta Azemon. 5 Iyakar za ta nausa daga Azemon zuwa rafin Masar, ta fāɗa bahar. 6 Bahar Rum ita ce iyakarsu ta wajen yamma. 7 Iyakarsu a wajen arewa kuwa ita ce tun daga Bahar Rum zuwa Dutsen Hor. 8 Daga Dutsen Hor iyakar za ta bi zuwa Hamat ta tsaya a Zedad. 9 Iyakar za ta miƙa har zuwa Zifron, ta tsaya a Hazar-enan, wannan ita ce iyakarsu a wajen arewa. 10 Iyakarsu a wajen gabas za ta tashi tun daga Haza-enan har zuwa Shefam. 11 Sa'an nan za ta gangara daga Shefam zuwa Ribla wajen gabashin Ayin. Za ta kuma gangara har ta kai Tekun Galili a wajen gabas. 12 Iyakar kuma za ta gangara har zuwa Urdun, ta tsaya a Tekun Gishiri. Wannan ita ce ƙasarsu da iyakokinta kewaye da ita. 13 Sai Musa ya ce wa Isra'ilawa, “Wannan ita ce ƙasar da za ku gāda ta hanyar jefa kuri'a. Ƙasar da Ubangiji ya umarta a ba kabilai tara da rabi. 14 Gama kabilar Ra'ubainu da ta Gad da kuma rabin kabilar Manassa sun riga sun karɓi nasu gādo. 15 Kabilan nan biyu da rabi sun karɓi nasu gādo a wancan hayin Urdun a gabashin Yariko.”

Shugabannin da za su Rarraba Kasa

16 Ubangiji kuma ya ce wa Musa, 17 “Ga sunayen mutanen da za su taimake ka raba gādon ƙasar, Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun. 18 Za ka kuma ɗauki shugaba ɗaya daga kowace kabila don su raba gādon ƙasar. 19 Waɗannan su ne sunayen mutanen, Kalibu ɗan Yefunne daga kabilar Yahuza. 20 Shemuyel ɗan Ammihud daga kabilar Saminu. 21 Elidad ɗan Kislon daga kabilar Biliyaminu. 22 Bukki ɗan Yogli daga kabilar Dan. 23 Na wajen Yusufu, Haniyel ɗan Efod daga kabilar Manassa, 24 da Kemuwel ɗan Shiftan daga kabilar Ifraimu. 25 Elizafan ɗan Farnak daga kabilar Zabaluna. 26 Faltiyel ɗan Azzan daga kabilar Issaka. 27 Ahihud ɗan Shelomi daga kabilar Ashiru. 28 Fedahel ɗan Ammihud daga kabilar Naftali.” 29 Waɗannan su ne mutanen da Ubangiji ya umarta su raba wa jama'ar Isra'ila gādon ƙasar Kan'ana.

Littafin Ƙidaya 35

Biranen Lawiyawa

1 A filayen Mowab a wajen Urdun daura da Yariko, Ubangiji ya yi magana da Musa, ya ce, 2 “Ka umarci jama'ar Isra'ila, ka ce su ba Lawiyawa biranen da za su zauna a ciki daga cikin gādonsu, za su kuma ba Lawiyawa hurumi kewaye da biranen. 3 Biranen za su zama nasu, inda za su zauna, hurumi kuwa domin shanunsu da sauran dukan dabbobinsu. 4 Girman hurumin da za su ba Lawiyawa kewaye da biranen zai zama mai fāɗin kamu dubu kewaye da garun birnin. 5 A bayan birnin za a auna kamu dubu biyu a wajen gabas, kamu dubu biyu a wajen kudu, kamu dubu biyu a wajen yamma, kamu dubu biyu a wajen arewa. Wannan zai zama hurumin mutanen birnin. Birnin kuwa zai kasance a tsakiya. 6 A cikin biranen da za a ba Lawiyawa, shida su zama na mafaka, inda za a yarda wa mai kisankai ya gudu zuwa can. Banda biranen mafaka guda shida, za a kuma ba su birane arba'in da biyu. 7 Wato dukan biranen da za a ba Lawiyawa guda arba'in da takwas ne tare da huruminsu. 8 Isra'ilawa za su ba Lawiyawa biranen nan bisa ga girman mallakarsu. Manyan kabilai za su ba su birane da yawa, amma ƙananan kabilai za su ba su birane kaɗan.”

Biranen Mafaka

9 Ubangiji kuwa ya faɗa wa Musa, 10 ya ce wa jama'ar Isra'ila, “Sa'ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar Kan'ana, 11 sai ku keɓe wa kanku biranen mafaka domin wanda ya yi kisankai da kuskure, ba da niyya ba, ya gudu zuwa can. 12 Biranen za su zamar muku mafaka daga hannun mai bin hakkin jini, don kada a kashe mai kisankai tun bai riga ya tsaya a gaban shari'a ba. 13 Sai ku zaɓi birane shida. 14 Biranen mafaka uku a hayin gabashin Urdun, birane uku kuma a ƙasar Kan'ana. 15 Waɗannan birane shida za su zama wuraren mafaka ga jama'ar Isra'ila, da baƙi, da baren da yake zaune tare da su, domin duk wanda ya kashe wani ba da niyya ba, ya tsere zuwa can. 16 “Amma idan wani ya bugi wani da makami na ƙarfe har ya mutu, ya yi kisankai, sai a kashe shi. 17 Idan kuwa ya jefe shi da dutsen da ya isa a yi kisankai da shi, har ya mutu, ya yi kisankai ke nan, to, sai a kashe shi. 18 Idan kuwa ya buge shi da makami na itace da ya isa a yi kisankai da shi, har kuwa ya mutu, ya yi kisankai ka nan, sai a kashe shi. 19 Sai mai bin hakkin jinin ya kashe mai kisankan sa'ad da ya iske shi. 20 “Idan saboda ƙiyayya ya laɓe, ya soke shi, ko ya jefe shi har ya mutu, 21 ko kuma saboda ƙiyayya ya naushe shi da hannu har ya mutu, sai a kashe shi, gama ya yi kisankai ke nan. Wanda yake bin hakkin jinin, zai kashe wanda ya yi kisankai sa'ad da ya iske shi. 22 “Amma idan bisa ga tsautsayi ya soke shi, ba don ƙiyayya ba, ko kuwa idan ya jefe shi da kowane abu, ba a laɓe ba, 23 ko ya jefe shi da dutsen da ya isa a kashe mutum da shi, ba da saninsa ba, shi kuwa ba maƙiyinsa ba ne, bai kuwa yi niyya ya cuce shi ba, amma ga shi kuwa, ya kashe shi, 24 to, sai taron jama'a su hukunta tsakanin mai kisankan da mai bin hakkin jinin bisa ga waɗannan ka'idodi. 25 Taron jama'a za su ceci mai kisankan daga hannun mai bin hakkin jinin. Su komar da shi a birnin mafaka inda ya je neman mafaka. Zai zauna can sai lokacin da babban firist da aka keɓe da tsattsarkan mai ya rasu. 26 Amma idan a wani lokaci mai kisankan ya fita kan iyakar birnin mafaka inda yake, 27 idan mai bin hakkin jinin ya same shi a bayan iyakar birnin, ya kashe shi, bai yi laifi ba. 28 Gama dole ne mai kisankan ya zauna cikin birnin mafaka inda yake, sai bayan rasuwar babban firist. Bayan rasuwar babban firist, mai kisankan yana iya komawa ƙasarsa.”

Ka'idodin Shaidu da Fansa

29 “Waɗannan ka'idodi sun shafe ku da zuriyarku a duk inda kuke. 30 Duk wanda ya yi kisankai sai a kashe shi bisa ga shaidar shaidu, amma saboda shaidar mutum ɗaya ba za a kashe mutum ba. 31 Kada ku karɓi fansa don ran wanda ya yi kisankai, dole ne a kashe shi. 32 Hakanan kuma kada ku karɓi fansa saboda wanda ya tsere zuwa birnin mafaka don ya koma ya zauna gidansa tun babban firist bai rasu ba. 33 Saboda haka kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zaune a ciki, gama jini yakan ƙazantar da ƙasa. Ba wata kafara da za a yi don ƙasar da aka zubar da jini a cikinta, sai dai da jinin wanda ya zubar da jinin. 34 Kada ku ƙazantar da ƙasar da kuke zaune a ciki, wadda ni kuma nake zaune a ciki, gama ni Ubangiji ina zaune a tsakiyar jama'ar Isra'ila.”

Littafin Ƙidaya 36

Gādon Matan Aure

1 Sai shugabannin gidajen iyalan 'ya'yan Gileyad, ɗan Makir, jikan Manassa, ɗan Yusufu, suka zo suka yi magana da Musa da sauran shugabanni. 2 Suka ce, “Ubangiji ya umarce ka ka raba wa Isra'ilawa gādon ƙasar ta hanyar jefa kuri'a. Ubangiji kuwa ya umarce ka ka ba 'ya'ya mata na Zelofehad, ɗan'uwanmu, gādo. 3 Amma idan suka auri waɗansu daga waɗansu kabilan jama'ar Isra'ila, wato za a ɗebe gādonsu daga gādon kakanninmu a ƙara wa gādon kabilan mutanen da suka aura, wato ka ga an ɗebe daga cikin namu gādo ke nan. 4 Sa'ad da shekara ta hamsin ta murnar Isra'ilawa ta kewayo, za a haɗa gādonsu da na kabilan mutanen da suka aura, da haka za a ɗebe gādonsu daga gādon kabilar kakanninmu.” 5 Musa kuwa ya umarci Isra'ilawa bisa ga faɗar Ubangiji ya ce, “Abin da mutanen kabilar 'ya'yan Yusufu suka faɗa daidai ne. 6 Abin da Ubangiji ya umarta a kan 'ya'ya mata na Zelofehad ke nan, ‘A bar su su auri wanda suka ga dama, amma sai a cikin iyalin kabilar kakansu. 7 Ba za a sāke gādon Isra'ilawa daga wata kabila zuwa wata ba, gama kowane mutum na cikin jama'ar Isra'ila zai riƙe gādonsa na kabilar kakanninsa. 8 Kowace 'ya mace wadda ta ci gādo a wata kabilar Isra'ila, sai ta yi aure a cikin kabilar kakanta domin kowane Ba'isra'ile ya ci gādon kakanninsa. 9 Ta yin haka ba za a sāke gādo daga wata kabila zuwa wata ba, gama kowace kabilar Isra'ila za ta riƙe gādonta.’ ” 10 Sai 'ya'yan Zelofehad mata, wato Mala, da Tirza, da Hogla, da Milka, da Nowa suka yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 11 Suka auri 'ya'yan 'yan'uwan mahaifinsu. 12 Sun yi aure a cikin iyalan 'ya'yan Manassa, ɗan Yusufu. Gādonsu kuwa bai ɓalle daga cikin kabilar iyalin kakansu ba. 13 Waɗannan su ne umarnai da ka'idodi waɗanda Ubangiji ya ba jama'ar Isra'ila ta wurin Musa a filayen Mowab kusa da Urdun daura da Yariko.

Maimaitawar Shari’a 1

Musa ya Jaddada wa Isra'ilawa Alkawarin Ubangiji a Horeb

1 Waɗannan su ne zantuttukan da Musa ya faɗa wa dukan Isra'ilawa a hayin Urdun cikin jejin Araba daura da Suf, tsakanin Faran, da Tofel, da Laban, da Hazerot, da Dizahab. 2 Tafiyar kwana goma sha ɗaya ne daga Horeb zuwa Kadesh-barneya, ta hanyar Dutsen Seyir. 3 A shekara ta arba'in, a rana ta fari ga watan goma sha ɗaya, Musa ya faɗa wa Isra'ilawa dukan abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa musu. 4 A lokacin kuwa ya riga ya ci Sihon, Sarkin Amoriyawa, wanda yake zaune a Heshbon, da Og, Sarkin Bashan, wanda yake zaune a Ashtarot, da Edirai. 5 A hayin Urdun, cikin ƙasar Mowab, Musa ya yi niyya ya fassara waɗannan dokoki. Ya ce, 6 “Ubangiji Allahnmu ya faɗa mana a Horeb, ya ce, ‘Daɗewarku a wannan dutse ta isa. 7 Ku tashi, ku yi gaba zuwa ƙasar duwatsun Amoriyawa, da dukan maƙwabtansu waɗanda suke a Araba. Ku shiga tuddai, da kwaruruka, da Negeb, da bakin bahar, da ƙasar Kan'aniyawa, da Lebanon, har zuwa babban kogi, wato Kogin Yufiretis. 8 Duba, na sa ƙasar a gabanku, sai ku shiga ku mallake ta, ƙasa wadda na rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, cewa zan ba su, su da zuriyarsu a bayansu.’ ”

Sa shugabanni

9 “A wancan lokaci ne na yi magana, na ce, ‘Ba zan iya ɗaukar nawayarku ba, 10 gama Ubangiji ya riɓaɓɓanya ku, har yawanku ya kai kamar taurarin sama. 11 Ubangiji Allah na kakanninku ya riɓa yawanku har sau dubu, ya sa muku albarka yadda ya alkawarta muku! 12 Ƙaƙa ni kaɗai zan iya ɗaukar nawayarku da wahalarku da kuma faɗace-faɗacenku? 13 Ku zaɓi masu hikima, da masu ganewa daga cikin kabilanku, waɗanda suka saba da zaman jama'a, ni kuwa in sa su zama shugabanninku!’ 14 Kuka amsa mini, kuka ce, ‘I, daidai ne kuwa mu bi shawarar nan da ka kawo mana.’ 15 Don haka na ɗauko shugabannin kabilanku masu hikima, waɗanda suka saba da ma'amala da jama'a, na sa su shugabanni a gabanku, waɗansu suka zama shugabanni a kan dubu dubu, waɗansu a kan ɗari ɗari, waɗansu a kan hamsin hamsin, waɗansu kuma a kan goma goma. Na sa su zama shugabanni a kabilanku. 16 “A wannan lokaci kuma na umarci shugabanninku na ce, ‘Ku yi adalci cikin shari'a tsakanin 'yan'uwanku, tsakanin mutum da ɗan'uwansa, ko kuma da baren da yake zaune tare da shi. 17 Kada ku nuna bambanci cikin shari'a, ko babban mutum ne ko talaka, duka biyu za ku ji su. Kada ku ji tsoron fuskar mutum, gama shari'a ta Allah ce. In kuwa shari'a ta fi ƙarfinku, sai ku kawo ta wurina, ni kuwa zan yanke ta.’ 18 A wancan lokaci na umarce ku da dukan abin da ya kamata ku yi.”

An Aiki 'Yan Leƙen Asirin Ƙasa

19 “Sai muka tashi daga Horeb, muka ratsa babban jejin nan mai bantsoro wanda kuka gani a hanyarmu zuwa ƙasar tuddai ta Amoriyawa, kamar yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu, muka zo Kadesh-barneya. 20 Sa'an nan na faɗa muku cewa, ‘Kun iso ƙasar tuddai ta Amoriyawa wadda Ubangiji Allahnmu yake ba mu. 21 Ga ƙasar a gabanku wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku, sai ku haura ku mallake ta yadda Ubangiji Allah na kakanninku ya faɗa muku. Kada ku ji tsoro ko ku firgita.’ 22 “Sa'an nan sai dukanku kuka zo wurina, kuka ce, ‘Bari mu aika da mutane, su je su leƙo mana asirin ƙasar tukuna, domin su shawarce mu ta hanyar da za mu bi, da kuma irin biranen da za mu shiga.’ 23 “Na ga al'amarin ya gamshe ni, saboda haka na ɗauki mutum goma sha biyu daga cikinku, mutum guda daga kowace kabila. 24 Mutanen kuwa suka kama hanya, suka tafi tuddai, suka kuma isa kwarin Eshkol, suka leƙo asirin ƙasar. 25 Da hannunsu suka ɗebo daga cikin amfanin ƙasar, suka gangaro mana da shi. Suka kuma faɗa mana cewa ƙasa wadda Ubangiji Allahnmu yake ba mu, mai kyau ce. 26 “Amma kuka ƙi ku haura, kuka ƙi bin umarnin Ubangiji Allahnku. 27 Sai kuka yi ta gunaguni cikin alfarwanku, kuna cewa, ‘Ai, saboda Ubangiji ya ƙi mu, shi ya sa ya fisshe mu daga ƙasar Masar, don ya bashe mu a hannun Amoriyawa, su hallaka mu. 28 Ta ƙaƙa za mu hau? Gama 'yan'uwanmu sun narkar da zuciyarmu da cewa, mutanen sun fi mu girma, sun kuma fi mu ƙarfi. Biranensu kuma manya manya ne, da gine-gine masu tsayi ƙwarai. Har ma sun ga Anakawa a wurin.’ 29 “Sai na ce muku, ‘Kada ku ji tsoronsu ko ku firgita. 30 Ubangiji Allahnku wanda yake tafiya tare da ku, shi kansa zai yi yaƙi dominku kamar yadda ya yi muku a Masar a kan idonku. 31 Kun ma ga yadda Ubangiji ya bi da ku cikin jeji kamar yadda mutum yakan bi da ɗansa, a dukan tafiyarku har zuwa wannan wuri.’ 32 Amma ko da yake ya yi muku haka duk da haka ba ku dogara ga Ubangiji Allahnku ba. 33 Shi wanda ya bishe ku, ya nuna muku inda za ku yi zango. Da dare yakan nuna muku hanya da wuta, da rana kuma yakan bi da ku da girgije.”

Hukuncin Allah a kan Isra'ilawa

34 “Ubangiji kuwa ya ji maganganunku, sai ya yi fushi, ya rantse, ya ce, 35 ‘Daga cikin mutanen wannan muguwar tsara ba wanda zai ga ƙasan nan mai albarka wadda na rantse zan ba kakanninku, 36 sai dai Kalibu ɗan Yefunne, shi kaɗai ne zai gan ta. Zan ba shi da 'ya'yansa ƙasar da ƙafarsa ta taka, gama shi ne ya bi Ubangiji sosai.’ 37 Ubangiji ma ya yi fushi da ni sabili da ku, ya ce, ‘Har kai ma ba za ka shiga ba. 38 Baranka, Joshuwa ɗan Nun, shi ne zai shiga. Sai ka ƙarfafa masa zuciya gama shi ne zai bi da Isra'ilawa, har su amshi ƙasar, su gāje ta.’ 39 “Sa'an nan Ubangiji ya ce wa dukanmu, ‘Amma 'ya'yanku ƙanana waɗanda ba su san mugunta ko nagarta ba, waɗanda kuke tsammani za a kwashe su ganima, su ne za su shiga ƙasar. Ni Ubangiji zan ba su su mallake ta. 40 Amma ku, sai ku koma cikin jeji ta hanyar Bahar Maliya.’ ”

An Ci Isra'ilawa da Yaƙi a Horma

41 “Sa'an nan kuka amsa mini, kuka ce, ‘Mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi. Za mu tafi mu yi yaƙi bisa ga faɗar Ubangiji Allahnmu.’ Sai kowannenku ya yi ɗamara ya ɗauki makaman yaƙinsa, kuka yi tsammani abu mai sauƙi ne ku shiga ƙasar tuddai. 42 “Amma Ubangiji ya ce mini in faɗa muku, kada ku tafi kada kuma ku yi yaƙi, gama ba ya tare da ku. Maƙiyanku za su kore ku. 43 Haka kuwa na faɗa muku, amma ba ku kasa kunne ba, kuka ƙi yin biyayya da umarnin Ubangiji. Sai kuka yi izgili, kuka hau cikin ƙasar tuddai. 44 Sai Amoriyawa waɗanda suke zaune a ƙasar tuddai suka fito da yawa kamar ƙudan zuma, suka taru a kanku suka bi ku, suka fatattaka ku a Seyir, har zuwa Horma. 45 Sai kuka koma, kuka yi kuka ga Ubangiji, amma Ubangiji bai ji kukanku ba, bai kuma kula da ku ba. 46 Kun kuwa zauna cikin Kadesh kwana da kwanaki, kamar dai yadda kuka yi.”

Maimaitawar Shari’a 2

Shekarun da suka Yi a Jeji

1 “Muka koma cikin jeji ta hanyar Bahar Maliya kamar yadda Ubangiji ya faɗa mini. Muka daɗe muna ta gewaya ƙasar tuddai ta Seyir. 2 “Sai Ubangiji ya ce mini. 3 ‘Ai, kun daɗe kuna ta gewaya waɗannan tuddai. Ku juya, ku nufi arewa. 4 Ka umarci jama'a, su bi yankin ƙasar zuriyar Isuwa, danginku, waɗanda suke zaune a Seyir. Za su ji tsoronku, sai ku yi hankali, 5 kada ku tsokane su, gama ko wurin sa ƙafa a ƙasarsu ba zan ba ku ba, gama na riga na ba Isuwa ƙasar tuddai ta Seyir. 6 Za ku sayi abincin da za ku ci, da ruwan da za ku sha a wurinsu. 7 Gama Ubangiji Allahnku ya sa albarka a kan dukan ayyukan hannuwanku. Ya kuma san tafiye-tafiyenku cikin babban jejin nan. Ubangiji Allahnku yana tare da ku a shekara arba'in ɗin nan, ba ku rasa kome ba.’ 8 “Muka yi gaba, muka bar zuriyar Isuwa 'yan'uwan nan namu waɗanda sike zaune a ƙasar tuddai ta Seyir, muka bar hanyar Araba, da hanyar Elat da Eziyon-geber. Muka juya, muka nufi wajen jejin Mowab. 9 “Sai Ubangiji ya ce mini, ‘Kada ku dami Mowabawa, ko kuwa ku tsokane su, gama ba zan ba ku ƙasarsu ku mallake ta ba. Na riga na bayar da Ar ta zama mallakar zuriyar Lutu.’ ” 10 (Emawa manya ne, masu yawa, dogaye ne kuma kamar Anakawa. Su ne suke zaune a ƙasar a dā. 11 Su ma akan lasafta su Refayawa tare da Anakawa, amma Mowabawa suka ce da su Emawa. 12 Hakanan kuma a dā Horiyawa ne suke zaune a ƙasar Seyir, amma mutanen zuriyar Isuwa suka zo, suka kore su, suka karkashe su, suka zauna a wurin, daidai kamar yadda Isra'ilawa suka yi da ƙasar mallakarsu, wadda Ubangiji ya ba su.) 13 “ ‘Yanzu, ku tashi ku haye rafin Zered da kanku.’ Sai kuwa muka haye. 14 Lokacin da muka tashi daga Kadesh-barneya zuwa lokacin da muka haye rafin Zered, shekara talatin da takwas ne. Duk wannan lokaci dukan waɗanda suka isa yaƙi suka murmutu kamar yadda Ubangiji ya rantse a kansu. 15 Hakika kuwa ikon Ubangiji ya buge su har suka hallaka ƙaƙaf. 16 “Sa'ad da dukan waɗanda suka isa yaƙi suka mutu, 17 sai Ubangiji ya yi mini magana, ya ce, 18 ‘Yau za ku ratsa kan iyakar ƙasar Mowab a Ar. 19 Sa'ad da ku kuka zo kusa da Ammonawa, kada ku dame su, ko ku tsokane su, gama ba zan ba ku abin mallaka daga yankin ƙasar Ammonawa ba, domin na ba da ita ta zama mallaka ga zuriya Lutu.’ ” 20 (Ita ma aka lasafta ta ƙasar Refayawa ce. Dā Refayawa waɗanda Ammonawa suke kira Zuzawa, su ne suka zauna cikinta. 21 Manyan mutane masu yawa dogaye ne kuma kamar Anakawa, amma Ubangiji ya hallakar da su a gabansu, suka kore su, suka zauna a wurinsu, 22 daidai kamar yadda Ubangiji ya yi wa zuriyar Isuwa waɗanda suka zauna a Seyir, sa'ad da ya hallakar da Horiyawa a gabansu. Su kuma suka kore su suka zauna a wurinsu har wa yau. 23 Hakanan kuma ya faru da Awwiyawa mazaunan ƙauyukan da suke kewaye da Gaza, wato su Kaftorawa waɗanda suka zo daga Kaftor, suka hallakar da su, suka zauna a wurinsu.) 24 “Ubangiji ya ce, ‘Ku tashi, ku kama hanya, ku haye kwarin Arnon. Duba, na ba da Sihon Ba'amore, Sarkin Heshbon, da ƙasarsa a hannunku, ku fara mallakar ƙasar, ku yaƙe shi. 25 A wannan rana ce zan fara sa al'ummai ko'ina a duniya su razana, su ji tsoronku. Sa'ad da za su ji labarinku, za su yi rawar jiki, su damu ƙwarai.’ ”

Isra'ilawa sun Ci Sihon

26 “Sa'an nan na aiki manzanni daga jejin Kedemot zuwa Sihon, Sarkin Heshbon, ina neman zaman lafiya, na ce, 27 ‘Ka yardar mini in bi ta cikin ƙasarka. Zan bi ta kan babbar hanya sosai, ba zan ratse dama ko hagu ba. 28 Zan sayi abincin da zan ci, da ruwan da zan sha a wurinku. 29 Kai dai ka yardar mini in bi in wuce kamar yadda zuriyar Isuwa, mazaunan Seyir, da Mowabawa, mazaunan Ar, suka yardar mini. Gama ina so in haye Urdun zuwa ƙasa wadda Ubangiji Allahnmu yake ba mu.’ 30 “Amma Sihon, Sarkin Heshbon, ya ƙi yarda mu wuce, gama Ubangiji Allahnku ya riga ya taurare hankalinsa da zuciyarsa don ya bashe shi a hannunku, kamar yadda yake a yau. 31 “Sai Ubangiji ya ce mini, ‘Duba, na fara ba da Sihon da ƙasarsa a gare ku. Ku fara fāɗa wa ƙasarsa da yaƙi don ku mallake ta.’ 32 Sai Sihon da mutanensa suka fita su gabza yaƙi da mu a Yahaza. 33 Ubangiji Allahnmu ya bashe shi a hannunmu, muka ci nasara a kansa, da 'ya'yansa, da dukan mutanensa. 34 Muka ci dukan garuruwansa, muka hallaka kowane gari, da mata, da maza, da yara, ko ɗaya bai ragu ba. 35 Sai dabbobi ne kaɗai da dukiyar garuruwan da muka ci, su ne muka kwashe ganima. 36 Daga Arower wadda take gefen kwarin kogin Arnon, zuwa Gileyad har ma da garin da yake cikin kwarin, Ubangiji Allahnmu ya ba da dukan kome a gare mu. Ba birnin da ya gagare mu. 37 Amma ba ku kusaci ƙasar Ammonawa ba, wato ƙasar da take a kwarin kogin Yabbok, da garuruwan ƙasar tuddai, da wuraren da Ubangiji Allahnmu ya hana mu.”

Maimaitawar Shari’a 3

Isra'ilawa sun Ci Og na Bashan

1 “Muka ci gaba da tafiyarmu muka nufi Bashan. Sai Og, Sarkin Bashan, tare da dukan jama'arsa suka fito su yi yaƙi da mu a Edirai. 2 Sai Ubangiji ya ce mini, ‘Kada ka ji tsoronsu, gama da shi, da jama'arsa duka, da ƙasarsa, zan bashe su a hannunka. Sai ka yi masa kamar yadda ka yi wa Sihon, Sarkin Amoriyawa, wanda yake zaune a Heshbon.’ 3 “Haka fa Ubangiji Allahnmu ya ba da Og, Sarkin Bashan, da dukan jama'arsa a hannunmu. Muka karkashe su duka, ba wanda muka bari da rai. 4 Muka ƙwace dukan garuruwansa a wannan lokaci. Ko gari guda ɗaya, ba mu bar musu ba, garuruwa sittin, da dukan yankin Argob, da mulkin Og a Bashan. 5 Dukan garuruwan nan masu dogo garu ne, da ƙofofi masu ƙyamaren ƙarfe. Banda waɗannan kuma akwai garuruwa da yawa marasa garu. 6 Muka hallaka su ƙaƙaf kamar yadda muka yi da Sihon, Sarkin Heshbon. Muka hallaka kowane gari, da mata da maza, da yara. 7 Amma muka riƙe dabbobi da dukiyar da muka kwaso daga garuruwan, ganima. 8 “A lokacin ne fa muka ƙwace wannan ƙasa daga hannun sarakunan nan biyu na Amoriyawa, wato ƙasa wadda take a hayin Urdun, daga kwarin kogin Arnon zuwa Dutsen Harmon.” 9 (Sidoniyawa suka kira Harmon, Siriyon, amma Amoriyawa suna ce da shi Senir.) 10 “Wato dukan garuruwa na ƙasar tudu, da dukan ƙasar Gileyad, da ta Bashan har zuwa Salka da Edirai, garuruwa na mulkin Og ke nan cikin ƙasar Bashan.” 11 (Sai Og, Sarkin Bashan, ne kaɗai ya ragu daga cikin Refayawa. Gadonsa na ƙarfe ne. Gadon yana nan a Rabbah ta Ammonawa. Tsawonsa kamu tara, faɗinsa kuma kamu huɗu ne.)

Ra'ubainu da Gad, da Rabin Kabilar Manassa sun Zauna a Gabashin Urdun

12 “Sa'ad da muka mallaki ƙasar a wannan lokaci, sai na ba Ra'ubainawa da Gadawa yankin ƙasar daga Arower wadda take gefen kwarin kogin Arnon, da rabin ƙasar tuddai ta Gileyad tare da garuruwanta. 13 Sauran ƙasar Gileyad, da dukan ƙasar Bashan wadda take ƙarƙashin mulkin Og, wato dukan yankin ƙasar Argob.” (Duk dai yankin ƙasar nan wadda ake kira ƙasar Refayawa.) “Na ba da ita ga rabin kabilar Manassa.” 14 (Yayir na zuriyar Manassa ya karɓi dukan yankin ƙasar Argob a Bashan har zuwa iyakar Geshurawa da Ma'akatiyawa. Sai ya kira ƙauyukan wurin da sunansa, Hawot-yayir.) 15 “Na ba Makir Gileyad. 16 Na ba Ra'ubainawa da Gadawa yankin ƙasar da ta tashi daga Gileyad har zuwa kwarin Arnon, tsakiyar kwarin shi ne iyakar har zuwa kwarin kogin Yabbok wanda ya yi iyaka da Ammonawa. 17 Na kuma ba su Araba, Urdun shi ne iyaka daga Kinneret, har zuwa Tekun Araba, wato Tekun Gishiri, a gangaren gindin Dutsen Fisga wajen gabas. 18 “A wancan lokaci ne na yi muku umarni, na ce, ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku wannan ƙasa, ku mallake ta. Dukan mayaƙanku za su haye da shirin yaƙi a gaban 'yan'uwanku, Isra'ilawa. 19 Amma matanku, da 'ya'yanku, da dabbobinku, na sani kuna da dabbobi da yawa, su ne za ku bari a garuruwan da na ba ku, 20 har lokacin da Ubangiji ya zaunar da 'yan'uwanku kamar yadda ya zamshe ku, su ma su mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba su a hayin Urdun, sa'an nan kowa zai koma ga mallakarsa.’ 21 “A lokacin kuwa na umarci Joshuwa na ce, ‘Ai, da idonka ka ga dukan abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa waɗannan sarakuna biyu. Hakanan kuwa Ubangiji zai yi wa mulkoki waɗanda za ku haye zuwa wurinsu. 22 Kada kuwa ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku ne zai yi yaƙi dominku.’ ”

Ba a Yarda wa Musa ya Shiga Kan'ana Ba

23 “Sa'an nan kuma na roƙi Ubangiji, na ce, 24 ‘Ya Ubangiji Allah, kai ne ka fara nuna wa baranka ɗaukakarka da ikonka. Ba wani Allah a Sama ko a duniya da zai aikata ayyuka na banmamaki irin naka. 25 Ka yarje mini, ina roƙonka in haye in ga wannan kyakkyawar ƙasa a hayin Urdun, ƙasar nan mai kyau ta tuddai, da Lebanon.’ 26 “Amma Ubangiji ya yi fushi da ni saboda ku, don haka bai ji ni ba. Ya ce mini, ‘Ya isa. Kada ma ka sāke yi mini magana a kan wannan al'amari. 27 Ka hau kan ƙwanƙolin Dutsen Fisga, ka dubi gabas, da yamma, da kudu, da arewa. Ka dubi ƙasar da idanunka, gama ba za ka haye Urdun ba. 28 Amma ka umarci Joshuwa, ka ƙarfafa shi. Shi ne zai jagorar jama'ar nan, su haye, shi ne kuma wanda zai rarraba musu gādon ƙasar da za ka gani.’ 29 “Sai muka zauna a kwari daura da Bet-feyor.”

Maimaitawar Shari’a 4

Musa ya Gargaɗi Isra'ilawa su yi Biyayya

1 “Yanzu, ya Isra'ilawa, sai ku kiyaye dokoki da farillai da nake koya muku don ku rayu, ku shiga ku kuma mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na kakanninku yake ba ku. 2 Kada ku ƙara, ko ku rage kome daga cikin abin da na umarce ku, amma ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, waɗanda nake umartarku da su. 3 Idanunku sun ga abin da Ubangiji ya yi a Ba'al-feyor, yadda Ubangiji Allahnku ya hallaka dukan mutane daga cikinku da suka bauta wa Ba'al-feyor. 4 Amma ku da kuka dogara ga Ubangiji Allahnku, a raye kuke har yau. 5 “Ga shi, na koya muku dokoki da farillai, yadda Ubangiji Allah ya umarce ni, don ku kiyaye su a ƙasa wadda kuke shiga ku mallake ta. 6 Ku kiyaye su, ku aikata su, gama yin haka zai tabbatar wa sauran al'ummai, kuna da hikima da ganewa. Sa'ad da al'ummai za su ji waɗannan dokoki, za su ce, ‘Ba shakka, wannan babbar al'umma tana da hikima da ganewa.’ 7 “Gama babu wata babbar al'umma wadda allahnta yake kusa da ita kamar yadda Ubangiji Allahnmu yake kusa da mu sa'ad da muka kira gare shi. 8 Ko kuwa, da akwai wata babbar al'umma wadda take da dokoki da farillai na adalci kamar waɗannan dokoki da na sa a gabanku yau?”

An Tuna wa Isra'ilawa abin da ya Same su a Horeb

9 “Sai ku lura, ku kiyaye kanku sosai, don kada ku manta da abubuwan da kuka gani da idonku kada kuma su fita a ranku dukan kwanakinku. Ku sanar wa 'ya'yanku da jikokinku da su, 10 da yadda kuma a waccan rana kuka tsaya a gaban Ubangiji Allahnku a Horeb, sa'ad da Ubangiji ya ce mini, ‘Ka tattara mini jama'a domin su ji maganata, su koyi tsorona dukan kwanakinsu a duniya, su kuma koya wa 'ya'yansu.’ 11 “Sai kuka matso kusa, kuka tsaya a gindin dutsen sa'ad da dutsen yake cin wuta har zuwa sararin sama, ga kuma girgije baƙi ƙirin yana rufe da dutsen. 12 Ubangiji kuwa ya yi magana da ku ta tsakiyar wuta. Kuka ji hurcin kalmomin, amma ba ku ga siffar kome ba, sai dai murya kaɗai kuka ji. 13 Shi ne ya hurta muku shari'ar da ya umarce ku ku kiyaye, wato dokokin nan goma. Ya rubuta su a allunan dutse guda biyu. 14 Duk da haka Ubangiji ya umarce ni in koya muku dokokin da farillan don ku aikata su a ƙasar da kuke hayewa zuwa ciki don ku mallake ta.”

Faɗakarwa a kan Gumaka

15 “Domin haka, sai ku kula da kanku sosai, gama ba ku ga siffar kome ba sa'ad da Ubangiji Allahnku ya yi magana da ku a Horeb ta tsakiyar wuta. 16 Don kada ku yi mugunta, ku sassaƙa wa kanku wata siffar kowane abu, ko siffar mace ko ta namiji, 17 ko siffar dabbar da take a duniya, ko siffar tsuntsun da yake tashi a sararin sama, 18 ko siffar kowane abu mai jan ciki bisa ƙasa, ko siffar kifin da yake cikin ruwa ƙarƙashin ƙasa. 19 Ku lura fa, sa'ad da kuka dubi sama, kuka ga rana, da wata, da taurari, da dai dukan rundunar sama, don kada fa ku jarabtu, ku yi musu sujada, ko ku bauta musu. Ubangiji Allahnku ya sa waɗannan saboda dukan al'ummai. 20 Amma ku, Ubangiji ya fisshe ku daga gidan bauta mai zafi, wato Masar, don ku zama jama'arsa ta musamman kamar yadda kuke a yau. 21 Amma Ubangiji ya yi fushi da ni sabili da ku, har ya rantse, cewa ba zan haye Urdun in shiga kyakkyawar ƙasar nan wadda yake ba ku abar gādo ba. 22 Gama a nan ƙasar zan mutu, ba zan haye Urdun ba, amma ku za ku haye, ku mallaki wannan kyakkyawar ƙasa. 23 Saboda haka, ku lura fa, kada ku manta da alkawarin da Ubangiji Allahnku ya yi da ku, don haka kada ku sassaƙa wa kanku wata siffar kowane irin kamanni wanda Ubangiji Allahnku ya hana ku. 24 Gama Ubangiji Allahnku wuta ne mai cinyewa, shi kuma mai kishi ne. 25 “Sa'ad da kuka haifi 'ya'ya, kuka sami jikoki, kuka kuma daɗe cikin ƙasar, idan kuka yi abin da yake haram, wato kuka yi gunki na sassaƙa na kowace irin siffa, kuka kuma aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnku har kuka tsokane shi ya yi fushi, 26 to, yau na kira sama da duniya su shaida a kanku, cewa lalle za ku hallaka nan da nan cikin ƙasar da za ku haye Urdun zuwa cikinta don ku mallake ta. Ba za ku daɗe cikinta ba, amma za a shafe ku ƙaƙaf. 27 Ubangiji zai warwatsa ku cikin al'ummai. Za ku ragu kaɗan daga cikin al'ummai inda Ubangiji ya warwatsa ku. 28 Can za ku bauta wa gumaka na itace, da na duwatsu, aikin hannuwan mutum, waɗanda ba su gani, ko ji, ko ci, ko sansana. 29 Amma idan kun nemi Ubangiji Allahnku a can inda kuke, za ku same shi muddin kun neme shi da zuciya ɗaya, da dukan ranku. 30 Sa'ad da wahala ta same ku, waɗannan abubuwa kuma suka auko muku nan gaba, za ku juyo wurin Ubangiji Allahnku, ku yi masa biyayya. 31 Ubangiji Allahnku, Allah mai jinƙai ne. Faufau, ba zai kunyata ku ba, ba kuwa zai hallaka ku ba, ba kuma zai manta da alkawarin da ya rantse wa kakanninku ba. 32 “Ku tambaya mana, ko a kwanakin dā kafin zamaninku, tun ma daga lokacin da Allah ya yi mutum a duniya, ku tantambaya daga wannan kusurwa ta samaniya zuwa waccan, ko wani babban abu irin wannan ya taɓa faruwa, ko kuma an taɓa jin labarin irinsa? 33 Akwai wata jama'a da ta taɓa jin muryar wani allah tana magana ta tsakiyar wuta kamar yadda kuka ji, har suka rayu? 34 Ko kuma, da akwai wani allah wanda ya taɓa ƙoƙarin fitar da al'umma saboda kansa daga cikin tsakiyar wata al'umma ta wurin wahalai, da alamu, da mu'ujizai, da yaƙi, da nuna iko, da babbar razana kamar yadda Ubangiji Allahnku ya yi dominku a ƙasar Masar a kan idonku duka? 35 An nuna muku wannan don ku sani Ubangiji shi ne Allah, banda shi, ba wani kuma. 36 Ya sa ku ji muryarsa daga Sama don ya horar da ku. Ya kuma sa ku ga babbar wutarsa a duniya, kuka kuma ji muryarsa daga cikin wutar. 37 Saboda ya ƙaunaci kakanninku shi ya sa ya zaɓi zuriyarsu a bayansu, shi kansa kuma ya fisshe ku daga Masar da ikonsa mai girma. 38 Ya kori al'ummai a gabanku waɗanda suka fi ku girma da iko, ya kawo ku a ƙasarsu, ya ba ku ita abar gādo kamar yadda yake a yau. 39 Domin haka, yau sai ku sani, ku kuma riƙe a zuciyarku, cewa Ubangiji shi kaɗai ne Allah a sama da duniya. Banda shi, ba wani kuma. 40 Sai ku kiyaye dokokinsa da umarnansa waɗanda na umarce ku da su yau, don zaman lafiyarku da na 'ya'yanku a bayanku, domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku har abada.”

Biranen Mafaka a Hayin Gabashin Urdun

41 Sai Musa ya keɓe birane uku a hayin gabashin Urdun, 42 domin wanda ya yi kisankai ya gudu zuwa can, wato wanda ya kashe mutum ba da niyya ba, babu kuma ƙiyayya tsakaninsu a dā. In ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen zai tsirar da kansa. 43 Biranen su ne, Bezer cikin jeji a kan tudu domin Ra'ubainawa, da Ramot cikin Gileyad domin Gadawa, da Golan cikin Bashan domin Manassawa.

Gabatarwa a kan Maimaita Dokoki

44 Waɗannan su ne dokokin da Musa ya ba Isra'ilawa, 45 su ne kalmomi, da dokoki, da farillai, waɗanda Musa ya faɗa wa jama'ar Isra'ila, bayan da sun fito Masar, 46 a hayin Urdun a kwari daura da Bet-feyor, a ƙasar Sihon, Sarkin Amoriyawa, mazaunan Heshbon, waɗanda Musa da Isra'ilawa suka ci da yaƙi sa'ad da suka fita daga ƙasar Masar. 47 Suka mallaki ƙasar Sihon, da ƙasar Og, Sarkin Bashan, sarakuna biyu na Amoriyawa waɗanda suke a hayin gabashin Urdun. 48 Ƙasar ta kama daga Arower wanda yake a kwarin kogin Arnon zuwa dutsen Siriyon, wato Harmon, 49 da dukan Araba a hayin gabashin Urdun, har zuwa tekun Araba a gindin gangaren Fisga.

Maimaitawar Shari’a 5

Dokoki Goma

1 Musa ya kirawo Isra'ilawa duka, ya ce musu, “Ya ku Isra'ilawa, ku ji dokoki da farillai waɗanda nake muku shelarsu a yau! Sai ku koye su, ku aikata su sosai. 2 Ubangiji Allahnmu ya yi alkawari da mu a Horeb. 3 Ba da kakanninmu ne Ubangiji ya yi wannan alkawari ba, amma da mu ne, mu duka waɗanda suke da rai a yau. 4 Ubangiji ya yi muku magana fuska da fuska bisa dutsen ta tsakiyar wuta. 5 Ni ne na tsaya a tsakanin Ubangiji da ku a lokacin don in faɗa muku maganar Ubangiji, gama kun ji tsoro saboda wutar, ba ku kuma hau dutsen ba. “Ubangiji ya ce, 6 ‘Ni ne Ubangiji Allahnka wanda ya fisshe ka daga ƙasar Masar daga gidan bauta. 7 “ ‘Kada ka kasance da waɗansu gumaka, sai ni. 8 “ ‘Kada ka yi wa kanka gunki, ko wata siffar abin da take a sama a bisa, ko siffar abin da yake a duniya a ƙasa, ko siffar abin da yake a cikin ruwa a ƙarƙashin ƙasa. 9 Kada ka yi musu sujada, ko ka bauta musu, gama ni Ubangiji Allahnka, Allah mai kishi ne, nakan hukunta 'ya'ya, da jikoki saboda laifin iyaye waɗanda suka ƙi ni. 10 Amma nakan nuna ƙauna ga dubbai waɗanda suke ƙaunata, suna kiyaye umarnaina. 11 “ ‘Kada ka rantse da sunan Ubangiji Allahnka a kan ƙarya, gama Ubangiji ba zai kuɓutar da wanda yake rantsewa da sunansa a kan ƙarya ba. 12 “ ‘Ka kiyaye ranar Asabar, ka riƙe ta da tsarki yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka. 13 Kwana shida za ka yi aikinka duka. 14 Amma rana ta bakwai ranar hutu ce ta Ubangiji Allahnka. A cikinta ba za ka yi kowane irin aiki ba, kai da ɗanka, da baranka, da baranyarka, da sanka, da jakinka, da kowace dabbar da kake da ita, da baƙon da yake zaune tare da kai, don barorinka mata da maza su ma su huta kamarka. 15 Ka tuna fa, dā kai bawa ne a ƙasar Masar, amma Ubangiji Allahnka ya fisshe ka da dantse mai iko, mai ƙarfi. Domin haka Ubangiji Allahnka ya umarce ka ka kiyaye ranar Asabar. 16 “ ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka yadda Ubangiji Allahnka ya umarce ka domin ka yi tsawon rai, ka sami zaman lafiya a ƙasar da Ubangiji Allahnka yake ba ka. 17 “ ‘Kada ka yi kisankai. 18 “ ‘Kada ka yi zina. 19 “ ‘Kada ka yi sata. 20 “ ‘Kada ka yi shaidar zur a kan maƙwabcinka. 21 “ ‘Kada ka yi ƙyashin matar maƙwabcinka. Kada kuma ka yi ƙyashin gidan maƙwabcinka, ko gonarsa, ko barorinsa mata ko maza, ko sansa, ko jakinsa, ko kowane abu da yake na maƙwabcinka.’ 22 “Ubangiji ya faɗa wa taron jama'arku waɗannan dokoki da murya mai ƙarfi ta tsakiyar wuta, da girgije, da duhu baƙi ƙirin. Ya rubuta su a bisa alluna biyu na dutse, ya ba ni, ba abin da ya ƙara.”

Mutane suka Ji Tsoro

23 “Sa'ad da kuka ji murya tana fitowa daga duhu, harshen wuta kuma tana ci a bisa dutse, sai shugabannin kabilanku da dattawanku suka zo wurina, 24 suka ce, ‘Ga shi, Ubangiji Allahnmu ya bayyana mana ɗaukakarsa da girmansa, mun kuma ji muryarsa a tsakiyar wutar. Yau mun ga Allah ya yi magana da mutum, duk da haka ya rayu. 25 Don me za mu mutu yanzu? Gama wannan babbar wuta za ta cinye mu. Idan muka ci gaba da jin muryar Ubangiji Allahnmu, za mu mutu. 26 Akwai wani ɗan adam wanda ya taɓa jin muryar Allah, Allah Mai Rai yana magana ta tsakiyar wuta yadda muka ji, har ya rayu? 27 Kai, ka matsa kusa, ka ji dukan abin da Ubangiji Allahnmu zai faɗa, sa'an nan ka mayar mana da dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya faɗa maka. Za mu ji, mu kuma aikata.’ 28 “Ubangiji kuwa ya ji maganarku wadda kuka yi mini, sai ya ce, ‘Na ji maganar da jama'ar nan suka yi maka, abin da suka faɗa daidai ne. 29 Da ma kullum suna da irin wannan zuciya ta tsorona, da za su kiyaye dukan umarnaina, zai zama fa'ida gare su da 'ya'yansu har abada. 30 Tafi, ka faɗa musu su koma cikin alfarwansu. 31 Amma kai ka tsaya nan a wurina don in faɗa maka dukan umarnai, da dokoki, da farillai, waɗanda za ka koya musu su kiyaye a ƙasar da nake ba su, su mallake ta.’ 32 “Sai ku lura ku yi daidai bisa ga abin da Ubangiji Allahnku ya umarce ku, kada ku kauce dama ko hagu. 33 Sai ku bi hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku don ku rayu, ku zauna lafiya, ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku mallaka.”

Maimaitawar Shari’a 6

Babban Umarni

1 “Waɗannan su ne umarnai, da dokoki, da farillai waɗanda Ubangiji Allahnku ya umarce ni in koya muku domin ku kiyaye su a ƙasar da kuke hayewa zuwa ciki don ku mallake ta, 2 don ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku da 'ya'yanku da jikokinku, ku kuma kiyaye dukan dokokinsa da umarnansa, waɗanda nake umartarku dukan kwanakinku don ku yi tsawon rai. 3 Don haka, ku ji, ya Isra'ilawa, ku lura, ku kiyaye su domin zaman lafiyarku, domin kuma ku riɓaɓɓanya ƙwarai a ƙasar da take mai yalwar abinci yadda Ubangiji Allah na kakanninku ya alkawarta muku. 4 “Ku ji, ya Isra'ilawa, Ubangiji shi ne Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne. 5 Sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya, da dukan ranku, da dukan ƙarfinku. 6 Waɗannan kalmomi da na umarce ku da su a yau, za su zauna a zuciyarku. 7 Sai ku koya wa 'ya'yanku su da himma. Za ku haddace su sa'ad da kuke zaune a gida, da sa'ad da kuke tafiya, da sa'ad da kuke kwance, da sa'ad da kuka tashi. 8 Za ku ɗaura su a hannunku da goshinku don alama. 9 Za ku kuma rubuta su a madogaran ƙofofin gidajenku, da ƙofofinku.”

Faɗakarwa a kan Rashin Biyayya

10 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya kai ku ƙasar da ya rantse wa kakanninku Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, zai ba ku manyan birane masu kyau waɗanda ba ku ne kuka gina ba, 11 da gidaje cike da abubuwa masu kyau waɗanda ba ku ne kuka cika su ba, da rijiyoyi waɗanda ba ku ne kuka haƙa ba, da gonakin inabi da itatuwan zaitun waɗanda ba ku ne kuka dasa ba. Sa'ad da kuka ci, kuka ƙoshi, 12 to, kada ku manta da Ubangiji wanda ya fito da ku daga ƙasar Masar, daga gidan bauta. 13 Sai ku ji tsoron Ubangiji Allahnku. Shi ne za ku bauta masa, ku rantse da sunansa. 14 Kada ku bi waɗansu alloli na al'umman da suke kewaye da ku, 15 gama Ubangiji Allahnku wanda yake zaune a tsakiyarku, mai kishi ne, don kada Ubangiji Allahnku ya husata, ya shafe ku daga duniya. 16 “Kada ku gwada Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi a Masaha. 17 Sai ku himmantu ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, da farillansa, da dokokinsa waɗanda ya umarce ku da su. 18 Sai ku yi abin da yake daidai, da abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji saboda lafiyarku, domin kuma ku shiga ku mallaki ƙasa mai kyau wadda Ubangiji ya rantse zai ba kakanninku. 19 Zai kuwa kori maƙiyanku a gabanku kamar yadda ya alkawarta. 20 “Idan nan gaba 'ya'yanku suka tambaye ku ma'anar maganarsa, da dokoki, da farillai, waɗanda Ubangiji Allahnmu ya umarce ku da su, 21 sai ku amsa wa 'ya'yanku, ku ce, ‘Dā mu bayin Fir'auna ne a ƙasar Masar, amma Ubangiji ya fisshe mu daga Masar da dantse mai iko. 22 A idonmu Ubangiji ya aikata manyan alamu masu banmamaki, da mu'ujizai gāba da Masarawa, da Fir'auna, da dukan gidansa. 23 Ya fisshe mu daga wurin, ya bi da mu zuwa ƙasar da ya alkawarta wa kakanninmu zai ba mu. 24 Ubangiji kuwa ya umarce mu mu kiyaye dukan waɗannan umarnai, mu kuma ji tsoron Ubangiji Allahnmu domin amfanin kanmu kullum, domin kuma mu wanzu kamar yadda muke a yau. 25 Idan mun lura, muka kiyaye waɗannan umarnai, muka aikata su kamar yadda Ubangiji Allahnmu ya umarce mu, zai zama adalci a gare mu.’ ”

Maimaitawar Shari’a 7

Tsattsarkar Jama'a ta Ubangiji

1 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya kai ku ƙasar da kuke shiga ku mallake ta, zai korar muku da al'ummai da yawa, su Hittiyawa, da Girgashiyawa, da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, al'umma bakwai ke nan, waɗanda suka fi ku yawa, da kuma ƙarfi. 2 Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannunku, kuka kuma ci nasara a kansu, sai ku hallaka su sarai. Kada ku yi alkawari da su, kada kuma ku yi musu jinƙai. 3 Kada ku yi aurayya da su. Kada ku aurar wa ɗansu da 'yarku, kada kuma ku auro wa ɗanku 'yarsu. 4 Gama za su sa 'ya'yanku su bar bina, su bauta wa gumaka. Wannan zai sa Ubangiji ya husata, ya hallaka ku da sauri. 5 Ga yadda za ku yi da su, za ku rurrushe bagadansu, ku ragargaza al'amudansu, ku sassare ginshiƙansu na tsafi, ku ƙaƙƙone sassaƙaƙƙun siffofinsu. 6 Gama ku jama'a ce tsattsarka ta Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku ya zaɓe ku daga cikin dukan al'ummai don ku zama jama'arsa, abar mulkinsa. 7 “Ubangiji ya ƙaunace ku, ya zaɓe ku, ba don kun fi sauran al'ummai yawa ba, gama ku ne mafiya ƙanƙanta cikin dukan al'ummai. 8 Amma saboda Ubangiji ya ƙaunace ku, yana kuma so ya cika rantsuwar da ya yi wa kakanninku, shi ya sa ya fisshe ku da dantse mai iko ya fanshe ku kuma daga gidan bauta, wato daga ikon Fir'auna, Sarkin Masar. 9 Domin haka sai ku sani Ubangiji Allahnku shi ne Allah, Allah mai aminci, mai cika alkawari, mai nuna ƙauna ga dubban tsararraki waɗanda suke ƙaunarsa, suna kuma kiyaye umarnansa. 10 Amma a fili Ubangiji yakan yi ramuwa a kan maƙiyansa, yakan hallaka su. Ba zai yi jinkirin yin ramuwa a kan maƙiyinsa ba, zai yi ramuwar a fili. 11 Saboda haka, sai ku kiyaye umarnai, da dokoki, da farillai ku aikata su, wato waɗanda nake umartarku da su yau.”

Albarkun Biyayya

12 “Idan za ku saurari waɗannan farillai, ku kiyaye su, sai Ubangiji Allahnku ya cika alkawarin da ya rantse wa kakanninku, ya kuma ƙaunace ku. 13 Ubangiji zai ƙaunace ku, ya sa muku albarka, ya riɓaɓɓanya ku. Zai sa wa 'ya'yanku albarka, ya yalwata amfanin gonarku, da hatsinku, da inabinku, da manku, da garken shanunku, da 'yan ƙananan garkenku a ƙasar da ya rantse wa kakanninku zai ba ku. 14 Za ku fi kowace al'umma samun albarka. Ba za a iske mutum ko mace marar haihuwa a cikinku ba, ko a cikin garkenku. 15 Ubangiji zai kiyaye ku daga dukan cuce-cuce. Ba zai wahalshe ku da mugayen cuce-cuce na Masar ba, waɗanda kuka sani, amma zai wahalar da duk maƙiyanku da waɗannan mugayen cuce-cuce. 16 Sai ku hallaka dukan mutanen da Ubangiji Allahnku ya bashe su a hannunku. Kada ku ji tausayinsu. Kada kuma ku bauta wa gumakansu, don kada su zamar muku tarko. 17 “Ya yiwu ku ce a zuciyarku, ‘Waɗannan al'ummai sun fi mu yawa, ta ƙaƙa za mu iya ƙorarsu?’ 18 Kada ku ji tsoronsu. Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya yi da Fir'auna da dukan Masarawa. 19 Ku tuna kuma da wahalar da kuka gani da idonku, da alamu, da mu'ujizai, da dantse mai iko mai ƙarfi wanda Ubangiji Allahnku ya fito da ku. Hakanan kuma Ubangiji Allahnku zai yi da dukan al'umman nan da kuke jin tsoronsu. 20 Banda wannan kuma Ubangiji Allahnku zai aiko da zirnako a cikinsu su hallaka sauran da suka ragu, suka ɓuya. 21 Kada ku ji tsoronsu, gama Ubangiji Allahnku yana tare da ku, shi Allah ne mai girma, mai banrazana. 22 Ubangiji Allahnku zai kori waɗannan al'ummai a gabanku da kaɗan da kaɗan. Ba za ku hallaka su gaba ɗaya ba, don kada namomin jeji su yaɗu, su dame ku. 23 Ubangiji Allahnku zai bashe su a gare ku, zai firgitar da su har ya hallakar da su. 24 Zai ba da sarkunansu a hannunku, za ku kuwa shafe sunayensu daga duniya. Ba wanda zai iya tasar muku har kun ƙare su. 25 Sai ku ƙone siffofin gumakansu. Kada ku yi ƙyashin azurfa ko zinariya da aka dalaye su da ita. Kada ku kwashe su, don kada su zamar muku tarko, gama Ubangiji Allahnku yana ƙyamarsu. 26 Kada ku kawo abin ƙyama a gidajenku don kada ku zama abin ƙyama kamarsa. Lalle sai ku ƙi shi, ku ji ƙyamarsa, gama haramtacce ne.”

Maimaitawar Shari’a 8

Ƙasar da za ku Mallaka Mai Albarka Ce

1 “Sai ku lura, ku aikata dukan umarnan da na umarce ku da su don ku rayu, ku riɓaɓɓanya, ku shiga ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninku. 2 Ku tuna yadda Ubangiji Allahnku ya bishe ku shekarun nan arba'in a jeji don ya koya muku tawali'u. Ya jarraba ku don ya san zuciyarku, ko za ku kiyaye umarnansa ko babu. 3 Ya koya muku tawali'u, ya bar ku da yunwa, ya ciyar da ku da manna wadda ba ku sani ba, kakanninku kuma ba su sani ba, domin ya sa ku sani, ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, amma mutum yana rayuwa da kowane irin abin da yake fitowa daga wurin Ubangiji. 4 A shekarun nan arba'in tufafinku ba su yayyage ba, ƙafafunku kuma ba su kumbura ba. 5 Kun san wannan a zuciyarku, wato kamar yadda mutum yakan yi wa ɗansa tarbiyya, haka kuma Ubangiji Allahnku yake yi muku tarbiyya. 6 Saboda wannan sai ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ji tsoronsa. 7 Ubangiji Allahnku zai kai ku ƙasa mai kyau. Ƙasa mai rafuffukan ruwa da maɓuɓɓugai, da idanun ruwa masu ɓuɓɓugowa daga cikin kwari da tudu. 8 Ƙasa mai alkama, da sha'ir, da inabi, da ɓaure, da rumman. Ƙasa ce mai itatuwan zaitun da zuma. 9 Ƙasa ce inda za ku ci abinci a yalwace, ba za ku rasa kome ba. Ƙasa ce wadda tama ce duwatsunta, ana kuma haƙar tagulla a tuddanta. 10 Sa'ad da kuka ci, kuka ƙoshi, sai ku yabi Ubangiji Allahnku saboda kyakkyawar ƙasa mai albarka da ya ba ku.”

Faɗakarwa kada a Manta da Ubangiji

11 “Ku kula fa, don kada ku manta da Ubangiji Allahnku, ku ƙi kiyaye umarnansa, da farillansa, da dokokinsa waɗanda na umarce ku da su yau. 12 Sa'ad da kuka ci kuka ƙoshi, kuka gina kyawawan gidaje, kuka zauna ciki, 13 garkunanku na shanu da tumaki suka riɓaɓɓanya, azurfarku, da zinariyarku suka ƙaru, sa'ad da dukan abin da kuke da shi ya haɓaka, 14 to, sai ku lura, kada ku ɗaukaka kanku, har ku manta da Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, wato inda kuka yi bauta. 15 Ubangiji ya bishe ku cikin babban jejin nan mai bantsoro, ƙasa mai macizai masu zafin dafi, da kunamai, da busasshiyar ƙasa wadda ba ta da ruwa. Ubangiji kuwa ya ba ku ruwa daga dutsen ƙanƙara. 16 Ya ciyar da ku da manna a jeji, abin da kakanninku ba su sani ba, domin ya koya muku tawali'u, ya jarraba ku, don ya yi muku alheri daga baya. 17 Kada ku ce a zuciya, ‘Ai, ikona da ƙarfin hannuwana ne suka kawo mini wannan wadata.’ 18 Sai ku tuna da Ubangiji Allahnku, gama shi ne ya ba ku ikon samun wadata domin ya cika alkawarin da ya rantse wa kakanninku kamar yadda yake a yau. 19 Idan kun manta da Ubangiji Allahnku, kuka bi gumaka, kuka bauta musu, kuka yi musu sujada, to, yau ina faɗakar da ku, cewa lalle za ku hallaka 20 kamar al'umman da Ubangiji ya hallakar a gabanku. Haka za ku hallaka domin ba ku kasa kunne ga muryar Ubangiji Allahnku ba.”

Maimaitawar Shari’a 9

Ubangiji zai Hallaka Al'umman Ƙasar Kan'ana

1 “Ku ji, ya Isra'ilawa, yau kuna kan haye Kogin Urdun, don ku kori al'ummai waɗanda suka fi ku yawa, sun kuwa fi ku ƙarfi. Suna da manyan birane masu dogon garu. 2 Mutane ne ƙarfafa, dogaye, zuriyar Anakawa waɗanda kuka riga kuka ji labarinsu. Ai, kun ji akan ce, ‘Wane ne zai iya tsayayya da 'ya'yan Anak?’ 3 Yau za ku sani Ubangiji Allahnku yake muku ja gaba sa'ad da kuke hayewa. Shi wuta ne mai cinyewa, zai hallaka su, ya rinjayar muku su, domin ku kore su, ku hallaka su nan da nan kamar yadda Ubangiji ya alkawarta muku. 4 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya kore su daga gabanku, kada ku ce a ranku, ‘Ai, saboda adalcinmu ne Ubangiji ya kawo mu mu mallaki ƙasar nan.’ Gama saboda muguntar al'umman nan ne Ubangiji ya kore su a gabanku. 5 Ba saboda adalcinku, ko kuma gaskiyarku ne ya sa za ku shiga ƙasar, ku mallake ta ba, amma saboda muguntar waɗannan al'ummai ne, Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku domin kuma ya cika maganar da ya rantse wa kakanninku, wato su Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. 6 Sai ku sani fa, ba saboda adalcinku ne Ubangiji Allahnku yake ba ku kyakkyawar ƙasar nan don ku mallake ta ba, gama ku jama'a ce mai taurinkai.”

Tayarwar Isra'ilawa a Horeb

7 “Tuna fa, kada ku manta da yadda kuka sa Ubangiji Allahnku ya yi fushi a jeji. Tun daga ranar da kuka fita daga Masar har kuka iso wannan wuri kuna ta tayar wa Ubangiji. 8 A Horeb kuka tsokani Ubangiji, Ubangiji kuwa ya yi fushi, har yana so ya hallaka ku. 9 Sa'ad da na hau kan dutsen domin in karɓo allunan dutse, wato allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutsen dare arba'in da yini arba'in ban ci ba, ban sha ba. 10 Ubangiji kuwa ya ba ni allunan nan biyu na dutse da shi kansa ya rubuta. A kansu aka rubuta maganar da Ubangiji ya yi muku daga bisa dutsen a tsakiyar wuta a ranar taron. 11 Bayan dare arba'in da yini arba'in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, wato alluna na alkawarin. 12 “Sa'an nan ya ce mini, ‘Tashi, ka gangara da sauri, gama jama'arka wadda ka fito da ita daga Masar ta aikata mugunta, ta kauce da sauri daga hanyar da na umarce ta ta bi. Ta yi wa kanta gunki na zubi.’ 13 “Ubangiji kuma ya ce mini, ‘Na ga mutanen nan suna da taurinkai. 14 Bari in hallaka su, in shafe sunansu daga duniya, sa'an nan in maishe ka wata al'umma wadda ta fi su iko da kuma yawa.’ 15 “Sai na juya, na gangaro daga dutsen da allunan nan biyu na alkawari a hannuwana, dutsen kuma na cin wuta. 16 Da na duba, sai na ga kun yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, kun yi wa kanku maraƙi na zubi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku ku bi. 17 Sai na ɗauki allunan nan biyu, na jefar da su ƙasa da hannuna, na farfashe su a idonku. 18 Sai na fāɗi ƙasa, na kwanta a gaban Ubangiji dare arba'in da yini arba'in, ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda na yi a dā, saboda dukan zunubin da kuka aikata, kuka yi abin da yake mugu ga Ubangiji, kuka tsokane shi. 19 Gama na ji tsoron zafin fushin Ubangiji da ya yi da ku, har ya so ya hallaka ku. Amma Ubangiji ya ji addu'ata a wannan lokaci. 20 Ubangiji kuma ya husata da Haruna, har ya so ya kashe shi, amma na yi roƙo dominsa a lokacin. 21 Sa'an nan na ɗauki abin zunubin nan, wato siffar maraƙin da kuka yi, na ƙone, na farfashe, na niƙe shi lilis, ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da garin a rafi wanda yake gangarowa daga dutsen. 22 “Kun kuma tsokano Ubangiji ya husata a Tabera, da a Masaha, da a Kibrot-hata'awa. 23 Sa'ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh-barneya, ya ce, ‘Ku hau ku mallaki ƙasar da nake ba ku,’ sai kuka tayar wa umarnin Ubangiji Allahnku, ba ku gaskata shi ba, ba ku kuwa yi biyayya da muryarsa ba. 24 Tun ran da na san ku, ku masu tayar wa Ubangiji ne. 25 “Sai na fāɗi na kwanta a gaban Ubangiji dare arba'in da yini arba'in saboda Ubangiji ya ce zai hallaka ku. 26 Na roƙi Ubangiji, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah, kada ka hallaka jama'arka, abar gādonka wadda ka fanshe ta ta wurin girmanka, waɗanda kuma ka fito da su daga Masar da ikon dantsenka. 27 Ka tuna da bayinka, su Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, kada ka kula da taurinkan jama'ar nan, ko muguntarsu, ko zunubansu 28 Don kada mutanen ƙasar da ka fito da mu su ce, “Ai, saboda Ubangiji ya kāsa ya kai su ƙasar da ya alkawarta musu, saboda kuma ba ya ƙaunarsu, shi ya sa ya fito da su don ya kashe su a jeji.” 29 Amma su mutanenka ne, abin gādonka, waɗanda ka fito da su da ikonka mai girma da dantsenka mai iko.’

Maimaitawar Shari’a 10

Allunan Dutse na Biyu

1 “A lokacin nan kuwa Ubangiji ya ce mini, ‘Ka sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko, ka hau zuwa wurina a bisa dutsen, ka kuma yi akwati na itace. 2 Ni kuma zan rubuta a allunan maganar da take kan alluna na farko waɗanda ka farfashe. Za ka ajiye su cikin akwatin.’ 3 “Sai na yi akwati da itacen ƙirya, na kuma sassaƙa alluna biyu na dutse kamar na farko. Sai na hau dutsen da alluna biyu a hannuna. 4 Ubangiji kuwa ya sāke rubuta dokoki goma a allunan kamar na farko, wato dokoki goma ɗin nan da Ubangiji ya faɗa muku a dutse ta tsakiyar wuta a ranar taron. Sai Ubangiji ya ba ni su. 5 Na sauko daga dutsen, na ajiye allunan cikin akwatin da na yi, a nan suke kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.” 6 (Isra'ilawa suka kama tafiya daga rijiyoyin Bene-ya'akan suka zo Mosera. Nan ne Haruna ya rasu, aka binne shi. Sai ɗansa Ele'azara, ya gāje shi a matsayinsa na firist. 7 Daga nan suka tafi Gudgoda, daga Gudgoda kuma suka tafi Yotbata, ƙasa mai rafuffukan ruwa. 8 A wannan lokaci ne Ubangiji ya keɓe kabilar Lawi domin su riƙa ɗaukar akwatin alkawari na Ubangiji, su kuma tsaya a gaban Ubangiji, su riƙa yi masa aiki, su kuma sa albarka da sunan Ubangiji kamar yadda yake a yau. 9 Domin haka kabilar Lawi ba su da rabo ko gādo tare da 'yan'uwansu, Ubangiji shi ne gādonsu kamar yadda Ubangiji Allahnku ya faɗa musu.) 10 “Na sāke yin dare arba'in da yini arba'in a kan dutsen kamar dā. Ubangiji kuwa ya amsa addu'ata a lokacin kuma, ya janye hallaka ku. 11 Sai Ubangiji ya ce mini, ‘Tashi, ka tafi, ka kama tafiyarka a gaban jama'ar nan domin su je, su shiga, su mallaki ƙasar da na rantse wa kakanninsu, zan ba su.’ ”

Abin da Ubangiji yake So

12 “Yanzu fa, ya Isra'ilawa ga abin da Ubangiji Allahnku yake so a gare ku. Sai ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin hanyoyinsa, ku ƙaunace shi, ku bauta wa Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku. 13 Ku kiyaye umarnan Ubangiji da dokokinsa waɗanda nake umurtarku da su yau don amfanin kanku. 14 Duba, saman sammai, da duniya, da dukan abin da yake cikinta na Ubangiji Allahnku ne. 15 Duk da haka Ubangiji ya ƙaunaci kakanninku ya zaɓi zuriyarsu a bayansu daga cikin dukan sauran al'umma, kamar yadda yake a yau. 16 Saboda haka sai ku kame zukatanku, kada ku ƙara yin taurinkai. 17 Gama Ubangiji Allahnku, Allahn alloli ne, da Ubangijin iyayengiji. Shi Allah mai girma ne, mai iko, mai bantsoro, wanda ba ya son zuciya, ba ya karɓar hanci. 18 Yakan yi wa marayu da gwauraye na gaske shari'a da adalci. Yana ƙaunar baƙo, yakan ba shi abinci da sutura. 19 Sai ku ƙaunaci baƙo, gama dā ku baƙi ne a ƙasar Masar. 20 Sai kuma ku ji tsoron Ubangiji Allahnku, ku bauta masa. Ku manne masa, ku yi rantsuwa da sunansa. 21 Shi ne abin yabonku, shi ne Allahnku, wanda ya yi muku waɗannan al'amura masu girma, masu bantsoro waɗanda kuka gani da idanunku. 22 Kakanninku saba'in ne suka gangara zuwa Masar, amma yanzu Ubangiji Allahnku ya riɓaɓɓanya ku, kuka yi yawa kamar taurarin sama.”

Maimaitawar Shari’a 11

Girman Ubangiji

1 “Sai ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku kiyaye faɗarsa, da dokokinsa da farillansa, da umarnansa kullum. 2 Yau fa ku sani ba da 'ya'yanku nake magana ba, waɗanda ba su sani ba, ba su kuma ga hukuncin Ubangiji Allahnku ba, da girmansa, da ƙarfin ikon dantsensa, 3 da alamunsa, da ayyukan da ya yi a kan Fir'auna Sarkin Masar, da dukan ƙasar, 4 da irin abin da ya yi wa sojojin Masar, da dawakansu, da karusansu, da yadda ya sa ruwan Bahar Maliya ya haɗiye su, a sa'ad da suke bin sawunku, da yadda Ubangiji ya hallaka su ƙaƙaf, 5 da abin da ya yi muku a jeji kafin ku iso wannan wuri, 6 da abin da ya yi wa Datan, da Abiram, 'ya'yan Eliyab, ɗan Ra'ubainu, yadda ƙasa ta buɗe a tsakiyar Isra'ilawa ta haɗiye su da dukan 'ya'yansu, da alfarwansu, da dukan abu mai rai da yake tare da su. 7 Amma idanunku sun ga manyan ayyukan nan da Ubangiji ya aikata.”

Albarkun Ƙasar Alkawari

8 “Don haka fa, sai ku kiyaye dukan umarnan da na umarce ku da su yau domin ku sami ƙarfin da za ku haye, ku shiga, ku ci ƙasar da za ku mallaka, 9 domin kuma ku yi tsawon rai a ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninku da zuriyarsu, ƙasar da take da yalwar abinci. 10 Gama ƙasar da za ku shiga garin ku mallake ta, ba kamar ƙasar Masar take ba inda kuka fito, inda kukan shuka iri sa'an nan ku yi ta zuwa kuna banruwa kamar lambu. 11 Amma ƙasar da za ku haye ku mallaka, ƙasa ce ta tuddai da kwaruruka wadda ruwan sama yake shayar da ita. 12 Ƙasa ce kuma wadda Ubangiji Allahnku yake lura da ita, Ubangiji Allahnku yana dubanta kullum, tun daga farkon shekara har zuwa ƙarshenta. 13 “Idan kun yi biyayya da umarnansa waɗanda ya umarce ku da su yau, kun ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kun bauta masa da zuciya ɗaya da dukan ranku, 14 zai shayar da ƙasarku da ruwa a kan kari, da ruwan bazara da na kaka. Za ku tattara sabon hatsinku da sabon ruwan inabinku, da manku. 15 Zai sa ciyawa ta tsiro a saurukanku domin dabbobinku. Za ku ci ku ƙoshi. 16 Ku lura fa, kada zuciya ta ruɗe ku, har ku kauce, ku bauta wa waɗansu alloli, ku yi musu sujada, 17 don kada Ubangiji ya yi fushi da ku, ya rufe sammai, ku rasa ruwa, ƙasa kuma ta kāsa ba da amfaninta, da haka za ku murmutu nan da nan a kyakkyawar ƙasar da Ubangiji yake ba ku. 18 “Sai ku riƙe zantuttukan nan nawa a zuciyarku da ranku. Za ku ɗaura su alama a hannuwanku, da goshinku. 19 Za ku koya wa 'ya'yanku su, ku yi ta haddace su, sa'ad da kuke zaune a gida, da sa'ad da kuke tafiya, da sa'ad da kuke kwance, da sa'ad da kuka tashi. 20 Za ku rubuta su a madogaran ƙofofin gidajenku, da bisa ƙofofinku, 21 don kwanakinku da kwanakin 'ya'yanku su yi tsawo a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba su muddin samaniya tana bisa duniya. 22 “Idan dai za ku lura, ku kiyaye dukan umarnan nan waɗanda nake umartarku ku kiyaye, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya a dukan hanyoyinsa, ku manne masa, 23 sa'an nan Ubangiji zai kori al'umman nan duka a gabanku. Za ku kori al'umman da suka fi ku yawa da ƙarfi. 24 Duk inda tafin ƙafarku ya taka kuma zai zama naku. Iyakarku za ta kama daga jeji zuwa Lebanon da kuma daga Kogin Yufiretis zuwa Bahar Rum. 25 Ba mutumin da zai iya tsayayya da ku. Ubangiji Allahnku zai sa ƙasar ta firgita, ta ji tsoronku a duk inda kuka sa ƙafa, kamar yadda ya faɗa muku. 26 “Ga shi, yau, na sa albarka da la'ana a gabanku. 27 Za ku sami albarka idan kun yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau. 28 Za ku zama la'anannu idan ba ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku ba, amma kuka kauce daga hanyar da nake umartarku da ita yau, har ku bi waɗansu alloli waɗanda ba ku san su ba. 29 Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya kai ku cikin ƙasar da za ku shiga ku mallake ta, sai ku ɗibiya albarkar a Dutsen Gerizim, ku ɗibiya la'anar kuma a Dutsen Ebal. 30 Duka biyunsu suna hayin Urdun ne, yamma da hanya a ƙasar Kan'aniyawa, mazaunan Araba, kusa da Gilgal, wajen itacen oak na More. 31 Gama za ku haye Urdun, ku shiga ƙasar da za ku mallaka, wadda Ubangiji Allahnku yake ba ku. Sa'ad da kuka mallake ta, kuka zauna a ciki, 32 sai ku lura, ku aikata dukan dokoki da farillai waɗanda nake sawa a gabanku yau.”

Maimaitawar Shari’a 12

A Wuri ɗaya kaɗai za a Yi Sujada

1 “Waɗannan su ne dokoki da farillai da za ku lura ku aikata a ƙasar da Ubangiji Allah na kakanninku ya ba ku, ku mallaka dukan kwanakinku a duniya. 2 Sai ku hallaka dukan wuraren da al'umman da za ku kora sukan bauta wa gumakansu, a bisa duwatsu masu tsawo, da bisa tuddai, da ƙarƙashin kowane itace mai duhu. 3 Sai ku rurrushe bagadansu, ku ragargaje al'amudansu, ku ƙone ginshiƙansu na tsafi, ku kuma sassare siffofin gumakansu, ku shafe sunayensu daga wuraren nan. 4 “Ba haka za ku yi wa Ubangiji Allahnku ba. 5 Amma sai ku nemi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa daga cikin kabilanku duka, inda zai sa sunansa, ya mai da shi wurin zamansa. 6 A can ne za ku tafi, a can ne kuma za ku kai hadayunku na ƙonawa, da sadakokinku, da zakarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na wa'adi, da hadayunku na yardar rai, da 'ya'yan farin garkenku na shanu, da na tumaki, da na awaki. 7 A nan, wato a gaban Ubangiji Allahnku, za ku ci, ku yi murna, ku da iyalanku, a kan dukan abin da Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka da shi. 8 “Kada ku yi kamar yadda muke yi a nan yau, yadda kowa yake yin abin da ya ga dama. 9 Gama ba ku kai wurin hutawa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku gādo ba tukuna. 10 Amma sa'ad da kuka haye Urdun, kuka zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, sa'ad da kuma ya ba ku hutawa daga maƙiyanku waɗanda suke kewaye da ku, kuka sami zaman lafiya, 11 sai ku kai dukan abin da na umarce ku ku kai, wato hadayu na ƙonawa, da sadakokinku, da zakarku, da hadayunku na ɗagawa, da hadayunku na wa'adi da kuka yi wa Ubangiji a wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa ya sa sunansa. 12 Ku yi murna a gaban Ubangiji Allahnku, ku da 'ya'yanku mata da maza, da barorinku mata da maza tare da Lawiyawa waɗanda suke zaune cikinku tun da yake ba su da rabo ko gādo tare da ku. 13 Ku lura, kada ku miƙa hadayunku na ƙonawa ko'ina, 14 amma sai a wurin nan ɗaya wanda Ubangiji zai zaɓa daga cikin kabilanku, nan za ku miƙa hadayunku na ƙonawa, nan ne kuma za ku yi dukan abin da na umarce ku. 15 “Amma kwā iya yanka nama ku ci a garuruwanku duk lokacin da ranku yake so, bisa ga albarkar da Ubangiji yake sa muku. Mai tsarki da marar tsarki za su ci abin da aka yanka kamar barewa da mariri. 16 Amma ba za ku ci jinin ba, sai ku zubar da shi a ƙasa kamar ruwa. 17 Kada ku ci waɗannan a garuruwanku, zakar hatsinku, ko ta inabinku, ko ta manku, ko ta 'ya'yan fari na shanunku da tumakinku, ko hadayunku na wa'adi, da hadayunku na yardar rai, ko hadayarku ta ɗagawa. 18 Amma sai ku ci su a inda Ubangiji Allahnku zai zaɓa, ku da 'ya'yanku mata da maza, da barorinku mata da maza, da Lawiyawa da suke a cikin garuruwanku. Sai ku yi murna a gaban Ubangiji Allah saboda duk abin da kuke yi. 19 Ku lura, kada ku manta da Lawiyawa muddin kuna zaune a ƙasarku. 20 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya fāɗaɗa ƙasarku kamar yadda ya alkawarta muku, sa'an nan ku ce, ‘Ina so in ci nama,’ saboda kuna jin ƙawar nama, to, kuna iya cin nama yadda kuke so. 21 Idan wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa don ya sa sunsansa ya yi muku nisa ƙwarai, to, sai ku yanka daga cikin garken shanunku, ko daga tumaki da awaki, waɗanda Ubangiji ya ba ku, kamar yadda na umarce ku. Za ku iya ci yadda kuke bukata a garuruwanku. 22 Kamar yadda akan ci barewa ko mariri haka za ku ci. Marar tsarki da mai tsarki za su iya cin naman. 23 Sai dai ku lura, kada ku ci jinin, gama jinin shi ne rai, kada ku ci ran tare da naman. 24 Kada ku ci jinin, sai ku zubar a ƙasa kamar ruwa. 25 Kada ku ci shi domin ku sami zaman lafiya, ku da zuriyarku a bayanku, gama za ku riƙa aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji. 26 Amma tsarkakakkun abubuwan da suke wajibanku da hadayunku na wa'adi, su ne za ku ɗauka ku kai wurin da Ubangiji ya zaɓa. 27 Sai ku miƙa nama da jinin hadayunku na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji Allahnku. Za ku zuba jinin sadakokinku a bisa bagaden Ubangiji Allahnku, amma za ku ci naman. 28 Ku lura, ku kasa kunne ga dukan umarnan da nake umartarku da su, don ku sami zaman lafiya, ku da zuriyarku a bayanku har abada, idan kun aikata abin da yake da kyau, daidai ne kuma a gaban Ubangiji Allahnku.”

Faɗakarwa a kan Gumaka

29 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya kawar muku da al'umman nan waɗanda za ku shiga ƙasarsu don ku kore su, sa'ad da kuka kore su, kun zauna a ƙasarsu, 30 to, sai ku lura, kada ku jarabtu ku kwaikwaye su bayan da an riga an shafe su daga gabanku! Kada ku tambayi labarin kome na gumakansu, ku ce, ‘Ƙaƙa waɗannan al'ummai suka bauta wa gumakansu? Mu ma za mu yi kamar yadda suka yi.’ 31 Kada ku yi wa Ubangiji Allahnku haka, gama sun yi wa gumakansu dukan abar ƙyamar da Ubangiji yake ƙi, har sun ƙona wa gumakansu 'ya'yansu mata da maza. 32 “Ku lura, ku aikata dukan abin da na umarce ku da shi, kada ku ƙara, kada ku rage daga cikinsa.

Maimaitawar Shari’a 13

1 “Idan wani annabi, ko mai mafarki ya fito a cikinku, ya yi muku shelar wata alama ko mu'ujiza, 2 idan alamar ko mu'ujizar ta auku, idan kuma ya ce, ‘Bari mu bi gumaka, mu bauta musu,’ gumakan da ba ku san su ba, 3 kada ku saurari maganar annabin nan ko mai mafarkin nan, gama Ubangiji Allahnku yana jarraba ku ne, ya gani, ko kuna ƙaunarsa da zuciya ɗaya da dukan ranku. 4 Sai ku bi Ubangiji Allahnku, ku yi tsoronsa, ku kiyaye umarnansa, ku kasa kunne ga muryarsa, shi ne za ku bauta masa, ku manne masa kuma. 5 Sai a kashe annabin nan, ko mai mafarkin don ya koyar a tayar wa Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, wato inda kuka yi bauta, gama ya yi ƙoƙari ya sa ku ku kauce daga hanyar da Ubangiji Allahnku ya umarce ku ku bi. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. 6 “Idan ɗan'uwanka, wato ɗan mahaifiyarka, ko ɗanka, ko 'yarka, ko ƙaunatacciyar matarka, ko amininka ya rarrashe ka a asirce, yana cewa, ‘Bari mu tafi mu bauta wa gumaka waɗanda ku da ubanninku ba ku san su ba,’ 7 wato gumakan al'umman da suke kewaye da ku, ko suna kusa da ku, ko suna nesa da ku, daga wannan bangon duniya zuwa wancan, 8 kada ku yarda, kada ku saurare shi. Kada kuma ku ji tausayinsa, kada ku haƙura da shi ko ku ɓoye shi. 9 Hannunku ne zai fara jifansa, sa'an nan sauran jama'a su jajjefe shi, har ya mutu. 10 Ku jajjefe shi da duwatsu har ya mutu, saboda ya yi niyyar janye ku daga bin Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar, wato inda kuka yi bauta. 11 Da hakanan dukan Isra'ilawa za su ji, su ji tsoro, har da ba za su ƙara aikata mugun abu irin wannan a cikinku ba. 12-13 “Idan kuka ji akwai 'yan ashararu a wani gari wanda Ubangiji Allahnku ya ba ku ku zauna a ciki, sun fito daga cikinku, suka rikitar da mazaunan garin suna cewa, ‘Ku zo mu bauta wa gumaka,’ waɗanda ba ku san su ba, 14 to, sai ku bincike labarin sosai a hankali. Idan hakika gaskiya ne, mugun abu haka ya faru a cikinku, 15 sai ku karkashe dukan mazaunan garin da takobi, ku kuma karkashe dabbobin da suke cikinsa. Za ku hallaka garin ƙaƙaf. 16 Ku tattara dukan ganimar garin a dandali, ku ƙone garin da dukan ganimar, hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji Allahnku. Garin zai zama kufai har abada, ba za a ƙara gina shi ba. 17 Kada ku ɗauka daga cikin abin da aka haramta don zafin fushin Ubangiji ya huce, ya yi muku jinƙai, ya ji tausayinku, ya kuma riɓaɓɓanya ku ma kamar yadda ya rantse wa kakanninku, 18 in dai za ku yi wa Ubangiji Allahnku biyayya, ku kiyaye dukan umarnansa waɗanda nake umartarku da su yau, ku kuma ku aikata abin da yake daidai ga Ubangiji Allahnku.”

Maimaitawar Shari’a 14

Al'adar Makokin da aka Hana

1 “Ku 'ya'ya ne ga Ubangiji Allahnku, kada ku yi wa jikinku zāne, kada kuma ku yi wa kanku sanƙo saboda wani wanda ya rasu. 2 Gama ku keɓaɓɓun mutane ne na Ubangiji Allahnku. Ubangiji Allahnku kuwa ya zaɓo ku daga cikin dukan al'umman duniya ku zama mutanensa, wato abin gādonsa.”

Halattattun Dabbobi da Haramtattu

3 “Kada ku ci abin da yake haram. 4 Ga dabbobin da za ku ci, da saniya, da tunkiya, da akuya, 5 da mariri, da barewa, da mariya, da mazo, da makwarna, da gada, da ɓauna, da ragon dutse. 6 Za ku iya cin kowace dabbar da take da rababben kofato, wadda kuma take tuƙa. 7 Amma duk da haka cikin waɗanda suke tuƙa, da waɗanda suke da rababben kofato ba za ku ci raƙumi, da zomo, da rema ba, ko da yake suna tuƙa, amma ba su da rababben kofato. Haram ne su a gare ku. 8 Ba kuma za ku ci alade ba, ko da yake yana da rababben kofato, amma ba ya tuƙa. Haram ne shi a gare ku. Kada ku ci naman irin waɗannan dabbobi, ko ku taɓa mushensu. 9 “Daga dukan irin abin da yake zaune a ruwa za ku iya cin duk abin da yake da ƙege da ɓamɓaroki. 10 Kada ku ci duk irin abin da ba shi da ƙege ko ɓamɓaroki, gama haram yake a gare ku. 11 “Kuna iya cin dukan halattattun tsuntsaye. 12 Amma waɗannan tsuntsaye ne ba za ku ci ba, mikiya, da gaggafa, da ungulun kwakwa, 13 da duki, da buga zabi, da kowace irin shirwa, 14 da kowane irin hankaka, 15 da jimina, da ƙururu, da bubuƙuwa, da kowane irin shaho, 16 da mujiya, da babbar mujiya, da ɗuskwi, 17 da kwasakwasa, da ungulu, da dimilmilo, 18 da zalɓe, da kowane irin jinjimi, da katutu, da yaburbura. 19 “Dukan 'yan ƙwari masu fikafikai masu rarrafe haram ne a gare ku, kada ku ci su. 20 Za ku iya cin duk abin da yake da fikafikai in dai shi halattacce ne. 21 “Kada ku ci mushe. Amma mai yiwuwa ne ku ba baren da yake zaune a garuruwanku, ko kuma ku sayar wa baƙo. Gama ku jama'a ce keɓaɓɓiya ga Ubangiji Allahnku. “Kada ku dafa ɗan akuya a madarar uwarsa.”

Dokar Zakar

22 “Ku fitar da zakar dukan amfanin da kuka shuka a gonarku kowace shekara. 23 Ku ci zakar sabon hatsinku, da ruwan inabinku, da manku, da 'yan fari na shanunku, da tumakinku, a gaban Ubangiji Allahnku, a wurin da zai zaɓa ya tabbatar da sunansa, don ku koyi tsoron Ubangiji Allahnku har abada. 24 Idan ya zamana wurin ya yi muku nisa, har ba za ku iya kai zakar a wurin ba, saboda wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa domin ya tabbatar da sunansa ya yi muku nisa sa'ad da Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka, 25 to, sai ku sayar da zakar, ku tafi da kuɗin wurin da Ubangiji Allahnku ya zaɓa, 26 ku kashe kuɗin a kan duk abin da kuke so, ko sa ne, ko tunkiya, ko ruwan inabi, ko abin sha mai gāfi, ko dai duk irin abin da ranku yake so. Nan za ku yi liyafa a gaban Ubangiji Allahnku, ku yi murna tare da iyalan gidanku. 27 “Amma fa, kada ku manta da Balawen da yake garuruwanku gama ba shi da gādo kamarku. 28 A ƙarshen kowace shekara uku, sai ku kawo dukan zakar abin da kuka girbe a wannan shekara, ku ajiye a ƙofofinku. 29 Sa'an nan sai Balawe, da yake shi ba shi da gādo kamarku, da baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske, waɗanda suke zaune a garuruwanku, su zo, su ci, su ƙoshi, domin Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka cikin dukan aikin da hannunku zai yi.”

Maimaitawar Shari’a 15

Shekarar Yafewa

1 “A ƙarshen kowace shekara bakwai dole ku yafe dukan basusuwan da kuke bi. 2 Ga yadda za ku yafe. Sai kowane mai bin bashi ya yafe wa maƙwabcinsa, kada ya karɓi kome a hannun maƙwabcinsa ko ɗan'uwansa, gama an yi shelar yafewa ta Ubangiji. 3 Kana iya matsa wa baƙo ya biya ka, amma sai ka yafe wa danginka bashin da kake binsa. 4 “Ba za a sami matalauci a cikinku ba, da yake Ubangiji Allahnku zai sa muku albarka a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ita gādo, ku mallaka, 5 muddin kun yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku, kuna kiyaye wannan umarni da na umarce ku da shi yau. 6 Ubangiji Allahnku zai sa muku albarka kamar yadda ya alkawarta. Za ku ba al'ummai da yawa rance, amma ba za ku bukaci rance don kanku ba. Za ku mallaki al'ummai da yawa, amma su ba za su mallake ku ba. 7 “Idan akwai wani danginku matalauci, a wani gari na cikin garuruwan ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, to, kada ku taurara zuciyarku, ku ƙi sakin hannu ga danginku matalauci. 8 Amma ku ba shi hannu sake, ku ranta masa abin da yake so gwargwadon bukatarsa. 9 Amma fa, ku lura, kada ku yi tunanin banza a zuciyarku, kuna cewa, ‘Ai, shekara ta bakwai, shekarar yafewa ta yi kusa,’ har ku ɗaure wa danginku matalauci fuska, ku ƙi ba shi kome. Zai yi kuka ga Ubangiji a kanku, abin kuwa zai zama laifi a kanku. 10 Sai ku ba shi hannu sake, ba da ɓacin zuciya ba. Saboda wannan Ubangiji zai sa muku albarka cikin aikinku duka, da abin da kuke niyyar yi. 11 Gama ba za a rasa matalauta a ƙasar ba, saboda haka nake umartarku, cewa ku zama da hannu sake ga 'yan'uwanku, da mabukaci, da matalauci.”

Yadda za a Yi da Bayi

12 “Idan aka sayar muku da Ba'ibrane ko mace ko namiji, to, sai ya bauta muku shekara shida, amma a ta bakwai, sai ku 'yantar da shi. 13 Idan kuma kun 'yantar da shi, kada ku bar shi ya tafi hannu wofi. 14 Sai ku ba shi hannu sake daga cikin tumakinku, da awakinku, da masussukar hatsinku, da wurin matsewar inabinku. Ku ba shi kamar yadda Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka. 15 Ku tuna dā ku bayi ne a ƙasar Masar, amma Ubangiji Allahnku ya 'yantar da ku, domin haka nake ba ku wannan umarni yau. 16 “Amma idan ya ce muku, ‘Ba na so in rabu da ku,’ saboda yana ƙaunarku da iyalinku, tun da yake yana jin daɗin zama tare da ku, 17 to, sai ku ɗauki basilla ku huda kunnensa har ƙyauren ƙofa, zai zama bawanku har abada. Haka kuma za ku yi da baiwarku. 18 Sa'ad da kuka 'yantar da shi kada ku damu, gama shekara shida ya yi muku bauta wadda ta ninka ta ɗan ƙodago. Ubangiji Allahnku kuwa zai sa muku albarka cikin dukan abin da kuke yi.”

Keɓewar 'Ya'yan Fari

19 “Sai ku keɓe wa Ubangiji Allahnku dukan 'yan fari maza waɗanda aka haifa muku daga cikin garkenku na shanu, da na tumaki, da na awaki. Kada ku yi aiki da ɗan farin shanunku, kada kuma ku sausayi ɗan farin tunkiyarku. 20 Ku da iyalanku za ku ci shi kowace shekara a gaban Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji zai zaɓa. 21 Idan yana da wani lahani kamar gurguntaka ko makanta, ko kowane irin mugun lahani, to, kada ku miƙa shi hadaya ga Ubangiji Allahnku. 22 Sai ku ci shi a gida. Mai tsarki da marar tsarki a cikinku za su iya ci, kamar barewa ko mariri. 23 Sai dai kada ku ci jinin, amma ku zubar a ƙasa kamar ruwa.”

Maimaitawar Shari’a 16

Idin Ƙetarewa

1 “Ku kiyaye watan Abib don ku yi Idin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku, gama a watan Abib ne Ubangiji Allahnku ya fito da ku daga Masar da dad dare. 2 Sai ku miƙa hadayar ƙetarewa daga garkenku na tumaki da na shanu ga Ubangiji Allahnku a wurin da Ubangiji ya zaɓa domin ya tabbatar da sunansa. 3 Kada ku ci abinci mai yisti tare da hadayar. Kwana bakwai za ku riƙa cin abinci marar yisti tare da hadayar, gama abincin wahala ne, gama da gaggawa kuka fita daga ƙasar Masar, don haka za ku tuna da ranar da kuka fito daga ƙasar Masar dukan kwanakinku. 4 Kada a iske yisti a ƙasarku duka har kwana bakwai. Kada kuma ku ajiye naman hadayar da kuka miƙa da yamma a rana ta fari ya kwana har safiya. 5 “Kada ku miƙa hadayar ƙetarewa a kowane garin da Ubangiji Allahnku yake ba ku. 6 Amma ku miƙa ta a wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa don ya tabbatar da sunansa. Nan za ku miƙa hadayar ƙetarewa da yamma da faɗuwar rana, daidai da lokacin da kuka fito daga Masar. 7 Sai ku dafa shi, ku ci a inda Ubangiji Allahnku zai zaɓa. Da safe sai ku koma alfarwanku. 8 Kwana shida za ku yi kuna cin abinci marar yisti, amma a rana ta bakwai sai ku yi muhimmin taro saboda Ubangiji Allahnku. Kada ku yi aiki a wannan rana.

Idin Makonni

9 “Sai ku ƙirga mako bakwai, wato ku fara ƙirga mako bakwai ɗin daga lokacin da kuka fara sa lauje don ku yanke hatsinku da yake tsaye. 10 Sa'an nan sai ku yi Idin Makonni domin Ubangiji Allahnku. Za ku ba da sadaka ta yardar rai gwargwadon albarkar da Ubangiji Allahnku ya sa muku. 11 Sai ku yi murna a gaban Ubangiji Allahnku a inda Ubangiji Allahnku ya zaɓa don ya tabbatar da sunansa, ku da 'ya'yanku mata da maza, da barorinku mata da maza, da Balawen da yake zaune a garinku, da baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske, waɗanda suke zaune tare da ku. 12 Ku tuna fa, ku dā bayi ne a Masar, domin haka ku lura, ku kiyaye waɗannan dokoki.

Idin Bukkoki

13 “Za ku yi Idin Bukkoki kwana bakwai bayan da kun gama tattara amfaninku daga masussukanku, da wurin matsewar ruwan inabinku. 14 Sai ku yi murna a cikin idin, ku da 'ya'yanku mata da maza, da barorinku mata da maza, da Balawe, da baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske, waɗanda suke zaune tare da ku. 15 Za ku kiyaye idin ga Ubangiji Allahnku har kwana bakwai a inda Ubangiji zai zaɓa, gama Ubangiji Allahnku zai yalwata dukan amfanin gonakinku, da dukan ayyukan hannunku don ku cika da murna. 16 “Sau uku a shekara dukan mazajenku za su zo, su hallara a gaban Ubangiji Allahnku a inda zai zaɓa, wato a lokacin idin abinci marar yisti, da lokacin idin makonni, da kuma a lokacin Idin Bukkoki. Kada su hallara a gaban Ubangiji hannu wofi. 17 Kowane mutum zai kawo irin abin da ya iya, gwargwadon albarkar da Ubangiji Allahnku ya sa masa.”

Yin Shari'ar Gaskiya

18 “Sai ku naɗa alƙalai da shugabanni domin garuruwanku waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku bisa ga kabilanku. Sai su yi wa jama'a shari'a da adalci. 19 Kada ku ɓata shari'a, kada ku yi sonzuciya, kada kuma ku karɓi hanci, gama cin hanci yakan makantar da idanun mai hikima, ya karkatar da maganar adali. 20 Adalci ne kaɗai za ku sa gaba domin ku rayu, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. 21 “Kada ku dasa kowane irin itace na tsafi kusa da bagaden Ubangiji Allahnku, wanda za ku gina. 22 Kada kuma ku kafa al'amudi, abin da Ubangiji Allahnku yake ƙi.”

Maimaitawar Shari’a 17

1 “Kada ku miƙa wa Ubangiji Allahnku hadaya da sa ko da tunkiya da take da lahani ko naƙasa, gama wannan abar ƙyama ce ga Ubangiji Allahnku. 2 “Idan aka sami wata, ko wani, daga cikin wani gari da Ubangiji Allahnku yake ba ku, yana aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnku, yana karya alkawarinsa, 3 har ya je, ya bauta wa gumaka, ya yi musu sujada, ko rana, ko wata, ko ɗaya daga cikin rundunar sama, ya yi abin da na hana, 4 idan aka faɗa muku, ko kuwa kun ji labarinsa sai ku yi cikakken bincike. Idan gaskiya ce, aka kuma tabbata an yi wannan mugun abu cikin Isra'ilawa, 5 to, ku kawo macen, ko mutumin, da ya aikata wannan mugun abu a bayan ƙofar garinku, nan za ku jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. 6 Bisa ga shaidar mutum biyu ko uku za a kashe shi, amma ba za a kashe mutum a kan shaidar mutum ɗaya ba. 7 Sai shaidun su fara jifansa sa'an nan sauran jama'a su jajjefe shi. Ta haka za a kawar da mugunta daga cikinsu. 8 “Idan aka kawo muku shari'a mai wuyar yankewa a ɗakin shari'arku, ko ta kisankai ce, ko ta jayayya ce, ko ta cin mutunci ce, ko kowace irin shari'a mai wuyar yankewa, sai ku tashi, ku tafi wurin da Ubangiji Allahnku zai zaɓa. 9 Za ku kai maganar wurin Lawiyawan da suke firistoci, ko kuma a wurin alƙalin da yake aiki a lokacin. Za ku tambaye su, za su faɗa muku yadda za a yanke shari'a. 10 Sai ku yanke shari'ar yadda suka faɗa muku daga wurin da Ubangiji ya zaɓa. Ku lura fa, ku yi yadda suka faɗa muku. 11 Dole ne ku yi yadda suka koya muku, da yadda suka yanke shari'ar. Kada ku kauce dama ko hagu daga maganar da suka faɗa muku. 12 Duk wanda ya yi izgili, ya ƙi yin biyayya da firist wanda yake a can, yana yi wa Ubangiji Allahnku hidima, ko kuma ya ƙi yi wa alƙalin biyayya, to, lalle sai a kashe wannan mutum. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikin Isra'ilawa. 13 Sa'an nan duk jama'a za su ji, su kuwa ji tsoro. Ba za su ƙara yin izgilanci ba kuma.”

Ka'idodin Zaman Sarki

14 “Sa'ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku don ku mallake ta, ku zauna a ciki, sa'an nan ku yi tunanin naɗa wa kanku sarki, kamar al'umman da suke kewaye da ku, 15 to, kwā iya naɗa wa kanku sarki wanda Ubangiji Allahnku ya zaɓa. Sai ku naɗa wa kanku sarki daga cikin jama'arku. Kada ku naɗa wa kanku baƙo wanda ba ɗan'uwanku ba. 16 Amma kada sarkin ya tattara wa kansa dawakai, kada kuma ya sa mutane su tafi Masar don su ƙaro masa dawakai, tun da yake Ubangiji ya riga ya yi muku kashedi da cewar, ‘Kada ku sāke komawa can.’ 17 Kada kuma ya auri mata da yawa don kada zuciyarsa ta karkace. Kada kuma ya tattara wa kansa kuɗi da yawa. 18 Sa'ad da ya hau gadon sarautar, sai ya sa a rubuta masa dokoki daga cikin littafin dokoki wanda yake wurin Lawiyawan da suke firistoci. 19 Kada ya rabu da littafin, amma ya riƙa karanta shi dukan kwanakinsa domin ya koyi tsoron Ubangiji Allahnsa ta wurin kiyaye dukan dokoki da umarnai, 20 don kada zuciyarsa ta kumbura, har ya ga ya fi 'yan'uwansa, don kuma kada ya karkace daga bin umarni zuwa dama ko hagu, don shi da 'ya'yansa su daɗe, suna mulki a Isra'ila.”

Maimaitawar Shari’a 18

Gādon Firistoci da Lawiyawa

1 “Lawiyawa da firistoci, wato dukan kabilar Lawi, ba su da rabo ko gādo tare da mutanen Isra'ila. Hadayun Ubangiji da dukan abin da ake kawo masa, su ne za su zama abincinsu. 2 Ba za su sami gādo tare da 'yan'uwansu ba, Ubangiji ne gādonsu kamar yadda ya alkawarta musu. 3 “To, ga rabon da jama'a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa, ko sā ne ko tunkiya ce, sai su ba firistoci kafaɗar, da kumatun, da tumbin. 4 Sai kuma ku ba su nunan fari na hatsinku, da ruwan inabinku, da manku, da kuma gashin tumakinku wanda kuka fara sausaya. 5 Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su, su da 'ya'yansu, daga dukan kabilanku don su yi aiki da sunan Ubangiji har abada. 6 “Balawe yana da dama ya tashi daga kowane gari na Isra'ila inda yake zaune ya je wurin da Ubangiji ya zaɓa. 7 Idan ya zo, sai ya yi aiki saboda sunan Ubangiji Allahnku kamar sauran 'yan'uwansa Lawiyawa waɗanda suke aiki a gaban Ubangiji a can. 8 Zai sami rabon abincinsa daidai da saura, har da abin da yake na kakanninsa wanda ya sayar.”

Faɗakarwa a kan Ayyukan Arna

9 “Sa'ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, to, kada ku shiga kwaikwayon ayyuka na banƙyama na waɗannan al'ummai. 10 Kada a tarar da wani daga cikinku wanda zai sa 'yarsu ko ɗansu ya wuce ta tsakiyar wuta, ko mai duba, ko mai maita, ko mai bayyana gaibi, ko mai sihiri, 11 ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha'ani da matattu. 12 Ubangiji yana ƙyamar mai yin waɗannan abubuwa. Saboda waɗannan ayyuka masu banƙyama shi ya sa Ubangiji Allahnku yake korar waɗannan al'ummai a gabanku. 13 Sai ku zama marasa aibu a gaban Ubangiji Allahnku.

Allah ya yi Alkawari zai Ta da wani Annabi kamar Musa

14 “Gama waɗannan al'ummai da za ku kora suna kasa kunne ga masu maita da masu duba, amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba. 15 “Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamata daga cikin jama'arku, sai ku saurare shi. 16 “Wannan shi ne abin da kuka roƙa a wurin Ubangiji Allahnku a Horeb, a ranar taron, gama kun ce, ‘Kada ka bar mu mu ƙara jin muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wannan babbar wuta, don kada mu mutu,’ 17 Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Abin da suka faɗa daidai ne. 18 Zan tayar musu da wani annabi kamarka daga cikin 'yan'uwansu. Zan sa magana a bakinsa, zai faɗa musu duk abin da na umarce shi. 19 Duk wanda bai saurari maganata wadda zai faɗa da sunana ba, ni da kaina zan nemi hakkinta a gare shi. 20 Amma duk wani annabin da ya yi izgili yana magana da sunana, ni kuwa ban umarce shi ba, ko kuwa yana magana da sunan gumaka, wannan annabi zai mutu.’ 21 “Ya yiwu ku ce a zuciyarku, ‘Ƙaƙa za mu san maganar da Ubangiji bai faɗa ba?’ 22 Sa'ad da annabi ya yi magana da sunan Ubangiji, idan abin da ya faɗa bai faru ba, bai zama gaskiya ba, to, wannan magana ba Ubangiji ne ya faɗa ba. Wannan annabi ya yi izgili ne kawai, kada ku ji tsoronsa.”

Maimaitawar Shari’a 19

Biranen Mafaka, Iyakoki na Dā

1 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya hallaka al'ummai waɗanda zai ba ku ƙasarsu, sa'ad da kuka kore su, kuka zauna cikin garuruwansu da gidajensu, 2 sai ku keɓe garuruwa uku a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku, ku mallaka. 3 Sai ku shirya hanyoyi, ku kuma raba yankin ƙasa wanda Ubangiji Allahnku zai ba ku ku mallaka kashi uku, domin wanda ya yi kisankai ya gudu zuwa can. 4 Wannan shi ne tanadi domin wanda ya yi kisankai, wato wanda zai gudu zuwa can don ya tsira. Idan ya kashe abokinsa ba da niyya ba, ba kuma ƙiyayya a tsakaninsu a dā, 5 misali, idan mutum ya tafi jeji, shi da abokinsa don su saro itace. Da ya ɗaga gatari don ya sari itace, sai ruwan gatarin ya kwaɓe daga ƙotar, ya sari abokinsa har ya mutu. Irin wannan mai kisankai zai gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen don ya tsira, 6 don kada mai bin hakkin jini ya bi shi da zafin fushinsa, ya cim masa, saboda nisan hanyar, har ya kashe shi, ko da yake bai cancanci mutuwa ba, tun da yake ba ƙiyayya tsakaninsa da abokinsa a dā. 7 Domin haka na umarce ku, ku keɓe wa kanku garuruwa uku. 8 “Sa'ad da Ubangiji Allahnku ya fāɗaɗa ƙasarku kamar yadda ya alkawarta wa kakanninku, har ya ba ku dukan ƙasar da ya alkawarta zai ba kakanninku, 9 in dai kun lura, kun kiyaye umarnin da nake umartarku da shi yau, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa kullum, sa'an nan sai ku ƙara garuruwa uku a kan waɗannan uku ɗin kuma, 10 don kada a zubar da jinin marar laifi a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku gādo, domin kada alhakin jini ya kama ku. 11 “Amma idan wani mutum yana ƙin wani ya kuwa tafi ya yi fakonsa, ya tasar masa, ya yi masa rauni har ya mutu, sa'an nan ya gudu zuwa ɗaya daga cikin garuruwan nan, 12 sai dattawan garinsu su aiko, a kamo shi daga can, sa'an nan su bashe shi ga mai bin hakkin jini don a kashe shi. 13 Kada ku ji tausayinsa. Ta haka za ku hana zub da jinin marar laifi cikin Isra'ila, don ku sami zaman lafiya. 14 “A cikin gādon da za ku samu a ƙasar da Ubangiji Allah yake ba ku ku mallaka, kada ku ci iyakar maƙwabcinku, wanda kakan kakanni suka riga suka kafa.”

Doka a kan Ba da Shaida

15 “Shaidar mutum ɗaya ba za ta isa a tabbatar, cewa mutum ya yi laifi ba, sai a ji shaidar mutum biyu ko uku, kafin a tabbatar da laifin mutum. 16 Idan ɗan sharri ya ba da shaidar zur a kan wani, 17 sai su biyu ɗin su zo a gaban Ubangiji, su tsaya a gaban firistoci da alƙalai waɗanda suke aiki a lokacin. 18 Sai alƙalan su yi bincike sosai. Idan ɗan sharrin ya ba da shaidar zur a kan ɗaya mutumin, 19 to, sai ku yi masa kamar yadda ya so a yi wa wancan mutumin. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. 20 Sauranku za su ji, su ji tsoro, ba za a ƙara aikata irin wannan mugunta ba. 21 Kada ku ji tausayi, zai zama rai maimakon rai, ido maimakon ido, haƙori maimakon haƙori, hannu maimakon hannu, ƙafa maimakon ƙafa.”

Maimaitawar Shari’a 20

Dokoki a kan Yaƙi

1 “Sa'ad da kuka tafi yaƙi da magabtanku, idan kun ga dawakai, da karusai, da sojoji da yawa fiye da naku, kada ku ji tsoronsu. Ubangiji Allahnku wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar yana tare da ku. 2 Sa'ad da kuke gab da kama yaƙi, sai firist ya zo gaba, ya yi magana da jama'a, 3 ya ce musu, ‘Ku ji, ya ku Isra'ilawa, yau kuna gab da kama yaƙi da magabtanku, kada ku karai, ko ku ji tsoro, ko ku yi rawar jiki, ko ku firgita saboda su. 4 Ubangiji Allahnku yana tafe tare da ku, zai yaƙi magabtanku dominku, ya ba ku nasara.’ 5 “Sa'an nan shugabanni za su yi magana da jama'a, su ce, ‘Ko akwai wani mutum a nan wanda ya gina gidan da bai buɗe shi ba tukuna? Sai ya koma gidansa, kada ya mutu a yaƙi, wani dabam ya yi bikin buɗewar. 6 Ko akwai wani mutum wanda ya dasa gonar inabi da bai ci amfaninta ba? Sai ya koma gidansa, kada ya mutu a yaƙi, wani wani dabam ya ci amfaninta. 7 Ko akwai wani mutum wanda yake tashin yarinya, amma bai aure ta ba tukuna? Sai ya koma gidansa, kada ya mutu a yaƙi, wani ya aure ta.’ 8 “Shugabannin yaƙi za su ci gaba da yi wa jama'a magana, su ce, ‘Ko akwai wani mutum a nan wanda yake jin tsoro, wanda zuciyarsa ta karai? Sai ya koma gidansa don kada ya sa zuciyar sauran 'yan'uwansa kuma su karai.’ 9 Sa'ad da shugabannin yaƙi suka daina yi wa jama'a jawabi, sai a zaɓi jarumawan sojoji don su shugabanci mutane. 10 “Sa'ad da kuka kusaci gari don ku yi yaƙi, sai ku fara neman garin da salama. 11 In ya yarda da salamar, har ya buɗe muku ƙofofinsa, sai dukan mutanen da suke cikinsa su yi muku aikin gandu, su bauta muku. 12 Amma idan ya ƙi yin salama da ku, amma ya yi yaƙi da ku, sai ku kewaye shi da yaƙi. 13 Idan Ubangiji Allahnku ya bashe shi a hannunku, sai ku karkashe dukan mazaje da takobi. 14 Amma mata, da yara, da dabbobi, da dukan abin da yake cikin garin, da dukan ganimarsa, sai ku kwashe su ganima, ku mori ganimar magabtanku, wadda Ubangiji Allahnku ya ba ku. 15 Haka za ku yi da dukan garuruwan da suke nesa da ku, wato garuruwan da ba na al'umman da suke kusa da ku ba. 16 “Amma kada ku bar kome da rai a garuruwan mutanen nan da Ubangiji Allahnku yake ba ku su gādo. 17 Za ku hallaka su ƙaƙaf, wato su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa kamar yadda Ubangiji Allahnku ya umarce ku, 18 don kada su koya muku yin abubuwa masu banƙyama waɗanda suka yi wa gumakansu, har ku yi wa Ubangiji Allahnku zunubi. 19 “Sa'ad da kuka kewaye gari da yaƙi, kuka daɗe kuna yaƙi da shi don ku ci shi, kada ku sassare itatuwansa da gatari har ku lalata su, gama za ku ci amfaninsu. Kada ku sassare su, gama itatuwan da suke cikin saura ba mutane ba ne, da za ku kewaye su da yaƙi. 20 Sai dai itatuwan da kuka sani ba su ba da 'ya'ya, su ne za ku sassare, ku yi kagara da su saboda garin da kuke yaƙi da shi har ku ci garin.”

Maimaitawar Shari’a 21

Yadda za a yi da Laifin Kisankai da ba a San wanda ya yi Ba

1 “Idan aka iske gawar mutum wanda wani ya kashe a fili a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku, ku mallaka, ba a kuwa san wanda ya kashe shi ba, 2 sai dattawanku da alƙalanku su fito su auna nisan wurin daga gawar zuwa garuruwan da suke kewaye da gawar. 3 Dattawan garin da ya fi kusa da gawar za su ɗauki karsana wadda ba a taɓa aiki da ita ba, ba a kuma taɓa sa mata karkiya ba. 4 Sai dattawan garin nan su kai karsanar kwari inda ruwa yake gudu, inda ba a taɓa noma ko shuka ba. A can cikin kwarin za a karya wuyan karsanar. 5 Sa'an nan sai firistoci, 'ya'yan Lawiyawa, su fito gaba, gama su ne Ubangiji Allahnku ya zaɓa don su yi masa aiki, su sa albarka da sunansa, su ne kuma masu daidaita kowace gardama da cin mutunci. 6 Sai dukan dattawan garin da ya fi kusa da gawar su wanke hannuwansu a bisa karsanar da aka karya wuyanta a kwarin. 7 Sa'an nan su ce, ‘Hannuwanmu ba su zub da wannan jini ba, idanunmu kuma ba su ga wanda ya zubar da shi ba. 8 Ya Ubangiji, ka kuɓutar da jama'arka, Isra'ila, wadda ka fansa, kada ka bar alhakin jinin marar laifin nan ya kama jama'arka, Isra'ila. Ka gafarta musu alhakin wannan jini.’ 9 Ta haka za ku kawar da alhakin jinin marar laifi daga cikinku, sa'ad da kuka yi abin da yake daidai a wurin Ubangiji.”

Yadda za a yi da Matan da aka Kama wurin Yaƙi

10 “Sa'ad da kuka tafi yaƙi da magabtanku, Ubangiji Allahnku kuwa ya bashe su a hannunku, kun kuwa kama su bayi, 11 in a cikinsu ka ga wata kyakkyawar mace wadda ka yi sha'awarta, to, ka iya aurenta. 12 Sai ka kawo ta gidanka, ta aske kanta, ta yanke farcenta, 13 ta tuɓe tufafin bauta. Sa'an nan sai ta zauna a gida tana makokin mahaifinta da mahaifiyarta har wata ɗaya cif. Bayan haka ka iya shiga wurinta, ka zama mijinta, ita kuma ta zama matarka. 14 In ka ji ba ka bukatarta, sai ka sake ta ta tafi inda take so, amma kada ka sayar da ita, kada kuma ka wahalshe ta, tun da yake ka riga ka ƙasƙantar da ita.”

Ka'ida a kan Gādon Ɗan Fari

15 “Idan mutum yana da mata biyu, amma ya fi ƙaunar ɗayar, idan kuwa dukansu biyu, wato mowar da borar, suka haifi 'ya'ya, idan bora ce ta haifi ɗan fari, 16 to, a ranar da zai yi wa 'ya'yansa wasiyya a kan gādon da zai bar musu, kada ya sa ɗan mowa ya zama kamar shi ne ɗan fari, a maimakon ɗan borar wanda shi ne ɗan farin, 17 Amma sai ya yarda ya ba ɗan farin, wato ɗan borar, za a ba shi riɓi biyu na dukan abin da yake da shi gama shi ne mafarin ƙarfinsa, yana da hakkin ɗan fari.”

Gagararren Ɗa

18 “Idan mutum yana da gagararren ɗa wanda ba ya jin maganar mahaifinsa da ta mahaifiyarsa, sun kuma hore shi, duk da haka bai ji ba, 19 sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su kama shi, su kawo shi wurin dattawan garin a dandalin ƙofar gari. 20 Sai su faɗa wa dattawan garinsu, su ce, ‘Wannan ɗanmu ne, gagararre, ba ya yi mana biyayya. Shi mai zari ne, mashayi!’ 21 Sa'an nan, sai mutanen garin su jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. Dukan Isra'ilawa za su ji, su ji tsoro.”

Waɗansu Dokoki

22 “Idan mutum ya yi laifin da ya isa mutuwa, aka rataye shi a itace har ya mutu, 23 kada a bar gawarsa ta kwana a kan itacen. Sai ku binne shi a ranar da aka rataye shi, gama wanda aka rataye shi la'ananne ne ga Ubangiji. Ku binne shi don kada ku ƙazantar da ƙasar da Ubangiji Allah yake ba ku, ku gāda.”

Maimaitawar Shari’a 22

1 “Idan kun ga ɓataccen san wani, ko tunkiyarsa, to, kada ku ƙyale shi, amma lalle sai ku komar da shi ga mai shi. 2 Idan mutumin ba kusa da ku yake zaune ba, ko kuma ba ku san shi ba, to, sai ku kawo dabbar a gidanku, ta zauna a wurinku, har lokacin da mutumin ya zo ya shaida ta, sa'an nan ku ba shi. 3 Hakanan kuma za ku yi da jakinsa, da riga, da kowane abin wani da ya ɓace, ku kuwa kuka tsinta. Faufau, kada ku ƙyale su. 4 “Idan kun ga jakin wani ko sansa ya faɗi a hanya, kada ku ƙyale shi, sai ku taimake shi ku tashe shi. 5 “Kada mace ta sa suturar maza, kada kuma namiji ya sa suturar mata. Duk mai yin haka, abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku. 6 “Idan kuna tafiya a hanya, kun ga sheƙar tsuntsu a itace, ko a ƙasa, da 'ya'yanta, ko da ƙwayaye a ciki, uwar kuma tana kwance bisa 'ya'yan ko ƙwayayen, kada ku kama uwar duk da 'ya'yan. 7 Sai ku bar uwar ta tafi, amma kun iya kwashe 'ya'yan. Yin haka zai sa ku sami zaman lafiya da tsawon rai. 8 “Sa'ad da kuka gina sabon gida, sai ku ja masa rawani don kada ku jawo wa gidanku alhakin jini idan wani ya fāɗi daga bisa. 9 “Kada ku shuka iri biyu a gonar inabinku don kada abin da kuka shuka da amfanin gonar inabinku su zama haramiyarku. 10 “Kada ku haɗa sa da jaki su yi huɗa tare. 11 “Kada ku sa rigar da aka saƙa da ulu garwaye da lilin. 12 “Sai ku yi wa rigar da kukan sa tuntu huɗu, tuntu ɗaya a kowace kusurwa.

Dokoki a kan Hana Lalata

13 “Idan mutum ya auri mace, ya shiga wurinta, sa'an nan ya ƙi ta, 14 yana zarginta da cewa ta yi abin kunya, yana ɓata mata suna a fili, yana cewa, ‘Na auri wannan mata, amma sa'ad da na kusace ta, sai na iske ita ba budurwa ba ce,’ 15 sai mahaifinta da mahaifiyarta su kawo shaidar budurcin yarinyar a gaban dattawan garin a dandalin ƙofar garin. 16 Sai mahaifinta ya ce wa dattawan, ‘Na ba wannan mutum 'yata aure, amma ya ƙi ta. 17 Yana zarginta da aikata abin kunya, ya ce, bai iske 'yarmu budurwa ba. Amma ga shaidar budurcin 'yata.’ Sai su shimfiɗa tsalala a gaban dattawan. 18 Sai dattawan garin su kama mutumin su yi masa bulala, 19 su ci shi tara shekel ɗari na azurfa, su ba mahaifin yarinyar, gama a fili mutumin ya ɓata sunan budurwar cikin Isra'ila. Za ta zama matarsa, ba shi da iko ya sake ta muddin ransa. 20 “Idan aka tabbatar zargin gaskiya ne, ba a kuma ga shaidar budurcinta ba, 21 sai a kai yarinyar a ƙofar gidan mahaifinta, sa'an nan mutanen garin su jajjefe ta da duwatsu har ta mutu, don ta yi aikin wauta cikin Isra'ila, gama ta yi karuwanci a gidan mahaifinta. Ta haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. 22 “Idan aka iske wani yana kwance da matar wani, sai a kashe dukansu biyu, wato mutumin da matar. Haka za ku kawar da mugunta daga Isra'ila. 23 “Idan a cikin gari wani ya iske budurwar da ake tashinta, ya kwana da ita, 24 sai a kawo su, su biyu ɗin, a dandalin ƙofar gari, ku jajjefe su da duwatsu har su mutu, don yarinyar tana cikin gari, amma ba ta yi kururuwa a taimake ta ba, don kuma mutumin ya ɓata budurwar maƙwabcinsa. Da haka za ku kawar da mugunta daga cikinku. 25 “Amma idan a saura wani ya fāɗa wa yarinyar da ake tashinta, har ya kwana da ita ƙarfi da yaji, sai a kashe wannan mutum. 26 Amma ita yarinyar ba za a yi mata kome ba, domin ba ta yi laifin da ya isa mutuwa ba, gama wannan shari'a daidai take da ta mutumin da ya faɗa wa maƙwabcinsa ya kashe shi. 27 Gama sa'ad da ya same ta a saura, ita wadda ake tashinta ta yi kururuwa, amma ba wanda zai cece ta. 28 “Idan wani ya iske yarinyar da ba a tashinta, ya kama ta, ya kwana da ita, aka kuwa same su, 29 to, sai wanda ya kwana da ita ya ba mahaifinta shekel hamsin na azurfa, ita kuwa za ta zama matarsa, gama ya ci mutuncinta. Ba zai sake ta ba muddin ransa. 30 “Kada mutum ya auri matar mahaifinsa, kada kuma ya kware fatarinta, gama na mahaifinsa ne.”

Maimaitawar Shari’a 23

Waɗanda za a Ware daga cikin Taron Jama'a

1 “Duk wanda aka dandaƙe ko wanda aka yanke gabansa ba zai shiga taron jama'ar Ubangiji ba. 2 “Shege ba zai shiga taron jama'ar Ubangiji ba. Har tsara ta goma zuriyarsa ba za su shiga taron jama'ar Ubangiji ba. 3 “Kada Ba'ammone ko Bamowabe ya shiga taron jama'ar Ubangiji. Har tsara ta goma ta zuriyarsu ba za su shiga taron jama'ar Ubangiji ba, 4 domin ba su zo sun tarye ku, su kawo muku abinci da ruwa ba sa'ad da kuke a hanyarku, lokacin da kuka fito daga Masar. Ga shi kuma, sun yi ijara da Bal'amu ɗan Beyor daga Fetor ta Mesofatamiya ya zo ya la'anta ku. 5 Amma Ubangiji Allahnku ya ƙi saurarar Bal'amu, sai Ubangiji ya juyar da la'anar ta zama muku albarka saboda Ubangiji Allahnku yana ƙaunarku. 6 Har abada kada ku nemar musu zaman lafiya ko wadata. 7 “Kada ku ji ƙyamar Ba'edome gama shi danginku ne. Kada kuma ku ji ƙyamar Bamasare don kun yi baƙunci a ƙasarsa. 8 'Ya'yansu tsara ta uku, za su iya shiga taron jama'ar Ubangiji.”

Kiyaye Sansanin Yaƙi da Tsabta

9 “Sa'ad da kuka kafa sansani don ku yi yaƙi da magabtanku, sai ku kiyaye kanku daga kowane mugun abu. 10 Idan wani a cikinku ya ƙazantu saboda ya zubar da maniyyi da dare, to, sai ya fita daga sansanin, kada ya koma sansanin. 11 Amma da maraice, sai ya yi wanka da ruwa, ya koma sansani sa'ad da rana ta faɗi. 12 “Za ku keɓe wani wuri a bayan sansani inda za ku riƙa zagayawa. 13 Sai ku ɗauki abin tona ƙasa tare da makamanku. Lokacin da za ku zagaya garin yin najasa, sai ku tsuguna ku tona rami da abin tona ƙasa sa'an nan ku rufe najasar da kuka yi. 14 Gama Ubangiji Allahnku yakan yi yawo cikin sansaninku don ya cece ku, ya ba da magabtanku cikin hannunku. Saboda haka dole ku tsabtace sansaninku don kada Ubangiji ya iske wata ƙazanta a cikinku, ya rabu da ku.”

Waɗansu Dokoki

15 “Kada ku ba da bawan da ya tsere, ya zo gare ku, ga ubangijinsa. 16 Zai zauna a wurinku. Sai ya zauna tare da ku, a wurin da ya zaɓa cikin garuruwanku inda ya fi so. Kada ku dame shi. 17 “Kada Isra'ilawa mata da maza su shiga ƙungiyar karuwanci na addini. 18 Kada ku kawo kuɗin da aka samu ta wurin karuwanci, ko kuɗin da aka samu ta wurin yin luɗu a Haikalin Ubangiji don biyan wa'adin da kuka riga kuka yi, gama wannan abin ƙyama ne ga Ubangiji Allahnku. 19 “Kada ku ba danginku rance da ruwa, ko rancen kuɗi ne, ko na abinci, ko na kowane irin abu da akan ba da shi da ruwa. 20 Kun iya ba baƙo rance da ruwa, amma kada ku ba danginku rance da ruwa don Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka a kan dukan abin da za ku yi a ƙasar da kuke shiga, ku kuma mallake ta. 21 “Idan kun yi wa Ubangiji Allahnku wa'adi, to, kada ku yi jinkirin cikawa, gama Ubangiji Allahnku zai neme shi a gare ku, ba kuwa zai zama zunubi a gare ku ba. 22 Idan kun nisanci yin wa'adi, ba zai zama zunubi gare ku ba. 23 Sai ku cika duk abin da kuka faɗa da bakinku, gama da yardarku ne kuka yi wa Ubangiji Allahnku wa'adi wanda kuka alkawarta. 24 “Sa'ad da kuka shiga gonar inabin maƙwabcinku, kuna iya cin 'ya'yan inabin, har ku ƙoshi yadda kuke so, amma kada ku sa wani a jakarku. 25 Sa'ad da kuka shiga hatsin maƙwabcinku da yake tsaye, kun iya ku yi murmuren tsabar da hannunku, amma kada ku sa wa hatsin maƙwabcinku lauje.”

Maimaitawar Shari’a 24

Dokar Kisan Aure

1 “Idan mutum ya sami wata mata ya aura, amma idan ba ta gamshe shi ba saboda ya iske wani abu marar kyau game da ita, har ya ba ta takardar saki a hannunta, ya sallame ta daga gidansa, 2 ta kuwa fita gidansa, idan ta je ta auri wani mutum dabam, 3 idan shi kuma ya ƙi ta, ya ba ta takardar saki a hannunta, ya sallame ta daga gidansa, ko kuma idan ya mutu ne, 4 to, kada mijinta na fari wanda ya sake ta, ya sāke aurenta, tun da yake ta ƙazantu. Gama wannan abar ƙyama ce a wurin Ubangiji. Kada ku jawo alhaki a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku gāda. 5 “Idan mutum ya yi sabon aure, kada ya tafi yaƙi tare da sojoji, ko kuma a sa shi kowane irin aiki. Sai ya huta a gida har shekara ɗaya saboda gidansa, don ya faranta wa matar da ya auro zuciya.”

Waɗansu Dokoki

6 “Kada mutum ya karɓi jinginar dutsen niƙa ko ɗan dutsen niƙa, gama yin haka karɓar jinginar rai ne. 7 “Idan aka iske mutum yana satar danginsa Ba'isra'ile don ya maishe shi bawansa, ko ya sayar da shi, sai a kashe ɓarawon. Ta haka za ku kawar da mugunta daga tsakiyarku. 8 “Game da ciwon kuturta, sai ku lura ku bi daidai da yadda firistoci na Lawiyawa suka umarce ku, ku yi. Sai ku kiyaye, ku aikata yadda na umarce su. 9 Ku tuna da abin da Ubangiji Allahnku ya yi wa Maryamu a lokacin da kuka fito daga Masar. 10 “Idan kun ba maƙwabcinku rance na kowane iri, kada ku shiga gidansa don ku ɗauki jingina. 11 Sai ku tsaya a waje, mutumin da kuka ba shi rancen zai kawo muku jinginar. 12 Amma kada ku yarda abin da aka jinginar ya kwana a wurinku idan mutumin matalauci ne. 13 Sai ku mayar masa da shi a faɗuwar rana domin ya yi barci yafe da rigarsa ya gode muku. Yin haka zai zama muku adalci a wurin Ubangiji Allahnku. 14 “Kada ku zalunci ɗan ƙodago wanda yake matalauci, ko shi danginku ne, ko kuwa baƙon da yake zaune a garuruwan ƙasarku. 15 Sai ku biya shi hakkinsa a ranar da ya yi aikin, kafin faɗuwar rana, gama shi matalauci ne, zuciyarsa tana kan abin hakkinsa, don kada ya yi wa Ubangiji kuka a kanku, har ya zama laifi a gare ku. 16 “Kada a kashe ubanni maimakon 'ya'ya, kada kuma a kashe 'ya'ya maimakon ubanni. Amma za a kashe mutum saboda laifin da ya aikata. 17 “Kada ku karkatar da shari'ar baƙo ko maraya. Kada kuma ku karɓi mayafin matar da mijinta ya rasu abin jingina. 18 Ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, Ubangiji Allahnku ya fanshe ku daga can, saboda haka ina umartarku ku yi wannan. 19 “Idan kun manta da wani dami a gona lokacin girbin amfanin gona, kada ku koma ku ɗauko. Ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske, domin Ubangiji Allahnku ya sa muku albarka a kan dukan aikin hannuwanku. 20 Sa'ad da kuka kakkaɓe 'ya'yan zaitunku, kada ku sāke bin rassan kuna kakkaɓewa, sai ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske. 21 Sa'ad da kuka girbe gonar inabinku kada kuma ku yi kala, sai ku bar wa baƙo, da maraya, da gwauruwa ta gaske. 22 Sai ku tuna, dā ku bayi ne a Masar, don haka nake umartarku ku yi wannan.”

Maimaitawar Shari’a 25

1 “Idan wata gardama ta tashi tsakanin mutane, suka je gaban shari'a, alƙalai kuwa suka yanke musu maganar, suka kuɓutar da marar laifi, suka kā da mai laifin, 2 idan mai laifin ya cancanci bulala, sai alƙali ya sa shi ya kwanta ƙasa, a bulale shi a gabansa daidai yawan bulalar da ta dace da irin laifin da ya yi. 3 Za a iya yi masa bulala arba'in, amma kada ta fi haka, don kada a ci gaba da bugunsa fiye da haka, har ya zama rainanne a idonku. 4 “Kada ku yi wa takarkari takunkumi sa'ad da yake tattaka hatsinku.”

Gādon Aure

5 “Idan 'yan'uwa suna zaune wuri ɗaya tare, in ɗayansu ya rasu bai haihu ba, to, kada matar marigayin ta auri wani baƙo wanda yake ba a cikin dangin mijin ba. Sai ɗan'uwan mijinta ya zo wurinta, ya aure ta, ya yi mata abin da ya kamaci ɗan'uwan miji ya yi. 6 Ɗan farin da za ta haifa, zai zama magajin marigayin don kada a manta da sunansa cikin Isra'ila. 7 Amma idan mutum ya ƙi ya auri matar ɗan'uwansa, marigayi, sai matar ta tafi wurin dattawa a dandalin ƙofar gari, ta ce, ‘Ɗan'uwan mijina, marigayi, ya ƙi wanzar da sunan ɗan'uwansa cikin Isra'ila, gama ya ƙi yi mini abin da ya kamaci ɗan'uwan marigayi, ya yi.’ 8 Sai dattawan garin su kira mutumin, su yi masa magana. Idan ya nace, yana cewa, ‘Ba na so in aure ta,’ 9 sai matar ɗan'uwansa, marigayi, ta tafi wurinsa a gaban dattawan, ta kwaɓe takalmin ƙafarsa, ta tofa masa yau a fuskarsa, ta ce, ‘Haka za a yi wa wanda ya ƙi kafa gidan ɗan'uwansa.’ 10 Za a kira sunan gidansa cikin Isra'ila, ‘Gidan wanda aka kwaɓe masa takalmi.’ ”

Waɗansu Dokoki

11 “Idan mutane biyu suna faɗa da juna, idan matar mutum ɗaya daga cikinsu ta zo don ta taimaki mijinta, idan ta kama marainan wancan mutum da hannunta, 12 sai ku yanke hannunta, kada ku ji tausayi. 13 “Kada ku riƙe ma'aunin nauyi iri biyu a jakarku, wato babba da ƙarami. 14 Kada kuma ku ajiye mudu iri biyu a gidanku, wato babba da ƙarami. 15 Sai ku kasance da ma'aunin nauyi da mudu masu kyau don ku daɗe a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. 16 Gama duk wanda yake aikata irin waɗannan abubuwa, da dukan marasa gaskiya, abin ƙyama ne su ga Ubangiji Allahnku.”

A Karkashe dukan Amalekawa

17 “Ku tuna da abin da Amalekawa suka yi muku a hanya, lokacin da kuka fito daga Masar. 18 Yadda suka yi muku kwanto a hanya, suka fāɗa muku ta baya, suka karkashe waɗanda suka gaji tiɓis. Ba su ko ji tsoron Allah ba. 19 Domin haka sa'ad da Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa daga dukan magabtanku da suke kewaye da ku a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku mallaka, abar gādo, to, sai ku shafe Amalekawa daga duniya, don kada a ƙara tunawa da su. Kada fa ku manta.”

Maimaitawar Shari’a 26

Abin da za a Yi da Nunan Fari da Zaka

1 “Sa'ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ku gāda, kuka mallake ta, kuka zauna cikinta, 2 to, sai ku keɓe nunan fari na dukan amfanin ƙasa wanda kuka shuka a ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku. Ku sa cikin kwando, ku tafi inda Ubangiji Allahnku zai zaɓa don ya tabbatar da sunansa. 3 Ku je wurin firist wanda yake aiki a lokacin, ku ce, ‘Yau, na sakankance a gaban Ubangiji Allahnka, cewa na shiga ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninmu zai ba mu.’ 4 “Sa'an nan firist ya karɓi kwandon daga gare ku ya sa shi kusa da bagaden Ubangiji Allahnku. 5 Sa'an nan kuma sai ku hurta waɗannan kalmomi a gaban Ubangiji Allahnku, ku ce, ‘Ubana Ba'aramiye ne, mayawaci a dā. Ya gangara zuwa Masar yana da jama'a kima, ya yi baƙunci a wurin. Amma a can ya zama al'umma mai girma, mai iko, mai yawa. 6 Masarawa suka wulakanta mu, suka tsananta mana, suka bautar da mu. 7 Amma muka yi kuka ga Ubangiji Allah na kakanninmu. Ubangiji kuwa ya ji kukanmu, ya ga azabarmu, da wahalarmu, da zaluncin da ake yi mana. 8 Sai Ubangiji ya fisshe mu daga Masar da dantsensa mai ƙarfi, mai iko, tare da bantsoro, da alamu, da mu'ujizai. 9 Ubangiji ya kawo mu nan, ya ba mu ƙasar nan, ƙasar da take mai yalwar abinci. 10 Ga shi, yanzu mun kawo nunan fari na amfanin ƙasar, da kai, ya Ubangiji, ka ba mu.’ “Sai ku ajiye shi a gaban Ubangiji Allahnku, ku yi sujada a gaban Ubangiji Allahnku. 11 Ku yi murna kuma, ku da Lawiyawa, da baƙin da suke zaune tare da ku, saboda dukan alherin da Ubangiji Allah ya yi muku, ku da gidanku. 12 “Sa'ad da kuka gama fitar da zakarku ta amfanin gona a shekara ta uku, wadda take shekara ta fid da zaka, sai ku ba Balawe, da baƙo, da maraya, da matar da mijinta ya rasu, don su ci, su ƙoshi a cikin garuruwanku. 13 Sa'an nan za ku ce a gaban Ubangiji Allahnku, ‘Na fitar da tsattsarkan kashi daga cikin gidana na ba Balawe, da baƙo, da maraya, da matar da mijinta ya rasu bisa ga umarnin da ka yi mini. Ban karya wani umarninka ba, ban kuwa manta da su ba. 14 Ban ci kome daga cikin zakar sa'ad da nake baƙin ciki ba, ban kuma fitar da kome daga cikinta ba sa'ad da nake da ƙazanta, ban kuma miƙa wa matattu kome daga cikinta ba. Na yi biyayya da muryar Ubangiji Allahna, na aikata dukan abin da ka umarce ni. 15 Ka duba ƙasa daga Sama, daga wurin zamanka mai tsarki, ka sa wa jama'arka, Isra'ila, albarka duk da ƙasar da ka ba mu, ƙasar da take mai yalwar abinci, kamar yadda ka rantse wa kakanninmu.’ ”

Tsattsarkar Jama'a ta Ubangiji

16 “Yau Ubangiji Allahnku yana umartarku ku kiyaye waɗannan dokoki da farillai. Sai ku lura ku aikata su da dukan zuciyarku da dukan ranku. 17 Yau kun shaida, cewa Ubangiji shi ne Allahnku, za ku yi tafiya cikin tafarkunsa, za ku kiyaye dokokinsa, da umarnansa, da farillansa, za ku kuma yi masa biyayya. 18 Yau kuma Ubangiji ya shaida, cewa ku ne jama'arsa ta musamman, kamar yadda ya alkawarta muku. Ku kuwa za ku kiyaye dukan umarnansa. 19 Shi kuwa zai ɗaukaka ku ku zama abin yabo, masu suna, masu daraja, fiye da dukan al'umman da ya yi. Za ku zama jama'a tsattsarka ta Ubangiji Allahnku kamar yadda ya faɗa.”

Maimaitawar Shari’a 27

Za a Rubuta Dokoki a Dutsen Ebal

1 Musa da dattawan Isra'ila suka umarci jama'a, suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai waɗanda na umarce ku da su yau. 2 Bayan da kuka haye Urdun, kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, sai ku kakkafa manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa. 3 Sai ku rubuta kalmomin wannan shari'a a kansu daidai lokacin da kuka haye ku shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasar da take mai yalwar abinci, kamar yadda Ubangiji Allahnku ya alkawarta wa kakanninku. 4 Sa'ad da kuka haye Urdun ɗin sai ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal bisa ga umarnin da na yi muku yau. Ku yi musu shafe da farar ƙasa. 5 Can za ku gina wa Ubangiji Allahnku bagade da duwatsun da ba a taɓa sassaƙa su da baƙin ƙarfe ba. 6 Sai ku gina wa Ubangiji Allahnku bagade da duwatsun da ba a sassaƙa ba. A bisa wannan bagade za ku miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji Allahnku. 7 Za ku kuma miƙa hadayu na salama ku ci a wurin, ku yi ta murna a gaban Ubangiji Allahnku. 8 Sai ku rubuta dukan kalmomin waɗannan dokoki su fita sosai bisa duwatsun nan.” 9 Sai Musa da Lawiyawan da suke firistoci, suka ce wa Isra'ilawa, “Ku ji. Yau kun zama jama'ar Ubangiji Allahnku. 10 Sai ku saurari muryar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye umarnansa, da dokokinsa waɗanda muke umartarku da su yau.”

La'ana a kan Dutsen Ebal

11 A wannan rana kuma Musa ya umarci jama'a, ya ce, 12 “Sa'ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama'a albarka, wato kabilar Saminu, da ta Lawi, da ta Yahuza, da ta Issaka, da ta Yusufu, da ta Biliyaminu. 13 Waɗannan za su tsaya a bisa kan Dutsen Ebal don su la'anta, wato kabilar Ra'ubainu, da ta Gad, da ta Ashiru, da ta Zabaluna, da ta Dan, da ta Naftali. 14 Sa'an nan Lawiyawa za su ta da murya, su ce wa dukan Isra'ilawa: 15 “ ‘La'ananne ne mutumin da ya sassaƙa, ko ya ƙera gumaka, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannun mai sana'a, ya kafa ta a ɓoye.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 16 “ ‘La'ananne ne wanda ya raina mahaifinsa ko mahaifiyarsa.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 17 “ ‘La'ananne ne wanda ya ci iyakar maƙwabcinsa.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 18 “ ‘La'ananne ne wanda ya karkatar da makaho daga hanya.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 19 “ ‘La'ananne ne wanda ya yi wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa ta gaske shari'a ta rashin gaskiya.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 20 “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya buɗe fatarin matar mahaifinsa.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 21 “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da dabba.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 22 “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da 'yar'uwarsa, wato 'yar mahaifinsa, ko 'yar mahaifiyarsa.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 23 “ ‘La'ananne ne wanda ya kwana da surukarsa.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 24 “ ‘La'ananne ne wanda ya buge maƙwabcinsa daga ɓoye.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 25 “ ‘La'ananne ne wanda aka yi ijara da shi don ya kashe marar laifi.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ 26 “ ‘La'ananne ne wanda bai yi na'am da kalmomin dokokin nan don ya yi aiki da su ba.’ “Sai dukan jama'a su amsa, ‘Amin, Amin!’ ”

Maimaitawar Shari’a 28

Albarkun Biyayya

1 “Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, kuna aikata dukan umarnansa waɗanda nake umartarku da su yau, to, Ubangiji Allahnku zai fifita ku fiye da dukan sauran al'umma. 2 Idan kun yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, dukan albarkun nan za su sauko muku, su zama naku. 3 “Za ku zama masu albarka, ko kuna cikin gari, ko kuna cikin karkara. 4 “'Ya'yanku za su zama masu albarka, hakanan kuma amfanin gonakinku, da 'ya'yan dabbobinku, da 'ya'yan shanunku, da 'ya'yan tumakinku da awakinku. 5 “Kwandunanku da makwaɓan za su yalwata ƙullunku. 6 “Da albarka za ku shiga, da albarka kuma za ku fita. 7 “Ubangiji zai sa ku fatattaki abokan gābanku a gabanku waɗanda suke tasar muku. Ta hanya guda za su auka muku, amma ta hanyoyi bakwai za su gudu daga gabanku. 8 “Ubangiji zai sa wa abin da yake cikin rumbunanku albarka da dukan aikin hannuwanku. Zai sa muku albarka a ƙasar da yake ba ku. 9 “Ubangiji zai sa ku zama tsattsarkar jama'arsa kamar yadda ya rantse muku, idan za ku kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa. 10 Dukan mutanen duniya za su gane ku na Ubangiji ne, za su ji tsoronku. 11 Ubangiji zai arzuta ku ƙwarai da 'ya'ya, da 'ya'yan dabbobi, da amfanin gona, a ƙasar da Ubangiji ya rantse wa kakanninku zai ba ku. 12 Ubangiji zai buɗe muku taskarsa ta sammai, don ya ba ƙasarku ruwa a kan kari, zai kuma sa albarka a kan dukan aikin hannuwanku. Al'ummai da yawa za su karɓi rance a wurinku, amma ku, ba za ku karɓi rance ba. 13 Ubangiji zai sa ku zama kai, ba wutsiya ba. Kullum ci gaba za ku yi, ba baya ba, idan kuka yi biyayya da umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, in kun lura, kun yi aiki da su, 14 idan kuma ba ku kauce zuwa dama ko hagu daga maganar da na umarce ku da ita yau ba, wato don ku bi waɗansu gumaka, ku bauta musu.”

Sakamakon Rashin Biyayya

15 “Amma idan ba za ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ko kuwa ba ku lura kuka aikata umarnansa da dokokinsa waɗanda nake umartar da su yau ba, to, dukan waɗannan la'ana za su auko muku, su same ku. 16 “La'anannu za ku zama a gari da karkara. 17 “La'anannu ne kwandunanku da makwaɓan ƙullunku. 18 “La'anannu ne 'ya'yanku, da amfanin gonakinku, da 'ya'yan shanunku, da 'ya'yan tumakinku da na awakinku. 19 “Da la'ana za ku shiga, da la'ana kuma za ku fita. 20 “Ubangiji zai aiko muku da la'ana, da ruɗewa, da damuwa cikin dukan abin da za ku yi, har ya hallaka ku, ku lalace da sauri saboda mugayen ayyukanku, domin kuma kuka rabu da ni. 21 Ubangiji zai aiko muku da annoba wadda za ta manne muku, ta cinye ku cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta. 22 Ubangiji zai buge ku da ciwon fuka, da zazzaɓi, da ciwon kumburi, da zafi mai tsanani, da fari, da burtuntuna, da fumfuna. Waɗannan za su yi ta damunku har ku lalace. 23 Samaniya da yake bisa kanku za ta zama tagulla, ƙasar kuma da kuke a bisa kanta ta zama baƙin ƙarfe. 24 Ubangiji zai mai da ruwan sama na ƙasarku gāri da ƙura, zai zubo muku da shi daga sama har ku hallaka. 25 “Ubangiji zai sa abokan gabanku su rinjaye ku cikin yaƙi. Ta hanya guda za ku auka musu, amma ta hanyoyi bakwai za ku gudu daga gabansu. Za ku zama abin ƙi ga dukan mulkokin duniya. 26 Gawawwakinku za su zama abinci ga dukan tsuntsayen sama, da namomin duniya. Ba wanda zai kore su. 27 Ubangiji zai buge ku da marurai irin na Masar, da basur, da ƙazwa, da ƙaiƙayi waɗanda ba za su warke ba. 28 Ubangiji kuma zai buge ku da ciwon hauka, da makanta, da rikicewar hankali. 29 Da tsakar rana za ku riƙa lalubawa kamar makaho, ba za ku yi arziki cikin ayyukanku ba. Za a riƙa zaluntarku, ana yi muku ƙwace kullum, ba wanda zai cece ku. 30 “Za ku yi tashin yarinya, wani ne zai kwana da ita. Za ku gina gida, wani ne zai zauna a ciki. Za ku dasa inabinku, wani ne zai girbe amfanin. 31 Za a yanka sanku a idonku, amma ba za ku ci ba. Za a ƙwace jakinku ƙiri ƙiri a idonku, ba za a mayar muku da shi ba. Za a ba magabtanku tumakinku, ba wanda zai cece ku. 32 A idonku za a ba da 'ya'yanku mata da maza ga wata al'umma dabam, za ku yi ta jin kewarsu, amma a banza, gama ba ku da ikon yin kome. 33 Mutanen da ba ku sani ba, su za su ci amfanin gonakinku da dukan amfanin wahalarku. Za a zalunce ku, a murƙushe ku kullum. 34 Abubuwan da idanunku za su gani za su sa ku zama mahaukata. 35 Ubangiji zai bugi gwiwoyinku da ƙafafunku da marurai tun daga tafin ƙafarku har zuwa ƙoƙwan kanku. 36 “Ubangiji zai bashe ku, ku da sarkin da kuka naɗa wa kanku ga wata al'ummar da ku da kakanninku ba ku sani ba. Can za ku bauta wa gumakan itace da na duwatsu. 37 Za ku zama abin ƙi, da abin karin magana, da abin habaici a cikin dukan mutane inda Ubangiji zai kora ku. 38 “Za ku shuka iri da yawa a gonakinku, amma kaɗan za ku girbe gama fara za su cinye. 39 Za ku dasa gonakin inabi, ku nome su, amma ba za ku sha ruwan inabin, ko ku tsinke 'ya'yan inabin ba, gama tsutsa za ta cinye shi. 40 Za ku sami itatuwan zaitun ko'ina cikin ƙasarku, amma ba za ku sami man da za ku shafa ba, gama 'ya'yan za su kakkaɓe. 41 Za ku haifi 'ya'ya mata da maza, amma ba za su zama naku ba, gama za a kai su bauta. 42 Ƙwari za su cinye dukan itatuwanku da dukan amfanin ƙasarku. 43 “Baƙin da suke tare da ku za su yi ta ƙaruwa, ku kuwa za ku yi ta komawa baya baya. 44 Za ku karɓi rance a wurinsu, su ba za su karɓi rance a wurinku ba. Su za su zama kai, ku kuwa za ku zama wutsiya. 45 “Dukan waɗannan la'anoni za su auko muku, su bi ku, su same ku, har ku hallaka, domin ba ku yi biyayya da Ubangiji Allahnku ba, ba ku kiyaye umarnai da dokoki da ya umarce ku da su ba. 46 Za su zama alama da abin mamaki a kanku da zuriyarku har abada. 47 Ba ku bauta wa Ubangiji Allahnku da murna da farin ciki ba, saboda dukan abin da ya ba ku a yalwace, 48 domin haka za ku bauta wa magabtanku waɗanda Ubangiji zai turo muku. Za ku bauta musu da yunwa, da ƙishirwa, da tsiraici, da talauci. Za su sa karkiyar ƙarfe a wuyanka har su hallaka ku. 49 Ubangiji zai kawo wata al'umma daga nesa, wato daga bangon duniya, mai kai sura kamar gaggafa, wadda za ta yi gāba da ku. Al'ummar da ba ku san harshenta ba, 50 al'umma mai zafin hali, wadda ba ta kula da tsofaffi, ba ta kuma jin tausayin yara. 51 Za ta ci shanunku da amfanin ƙasarku har ku hallaka. Ba za ta bar muku hatsi ko ruwan inabi, ko mai, ko 'ya'yan shanunku, ko na tumaki da na awakinku ba, har ta lalatar da ku. 52 Za su kewaye garuruwanku da yaƙi, har dogayen garukanku, da kagaranku waɗanda kuke dogara gare su, su rurrushe. Za su kewaye garuruwan ƙasarku da yaƙi a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya ba ku. 53 Za ku ci naman 'ya'yanku, mata da maza, waɗanda Ubangiji Allahnku ya ba ku, saboda irin tsananin kewayewar da magabtanku suka yi muku da yaƙi. 54 Nagarin mutum mai taushin zuciya wanda yake tare da ku, zai ƙi ɗan'uwansa, da matarsa, da 'ya'yansa da suka ragu, 55 domin kada ya ba wani daga cikinsu naman 'ya'yansa wanda yake ci, gama ba abin da ya rage masa saboda irin tsananin kewayewar garuruwanku da yaƙi wanda abokan gabanku suka kawo muku. 56 Matar kirki mai taushin zuciya wadda take tare da ku wadda ba za ta sa tafin ƙafarta a ƙasa ba saboda taushin zuciyarta da kyakkyawan halinta, za ta ƙi ƙaunataccen mijinta, da ɗanta, da 'yarta. 57 A ɓoye za ta ci mahaifar da take biyo bayan ta haihu, da 'ya'yan da za ta haifa, saboda ba ta da wani abinci lokacin da magabtanku za su kewaye garuruwanku da yaƙi mai tsanani. 58 “Idan ba ku lura, ku aikata dukan maganar dokokin nan da aka rubuta a wannan littafin ba, domin ku ji tsoron sunana nan mai ɗaukaka, mai kwarjini, wato sunan Ubangiji Allahnku, 59 to, Ubangiji zai aukar muku, ku da zuriyarku, da munanan masifu waɗanda ba su kawuwa, da mugayen cuce-cuce marasa warkewa. 60 Sai ya sāke kawo muku cuce-cuce irin na Masar, waɗanda kuka ji tsoronsu, za su kuwa manne muku. 61 Har yanzu kuma Ubangiji zai kawo muku kowace irin cuta, da kowace irin annoba, waɗanda ba a ambace su a littafin dokokin nan ba, har ku hallaka. 62 Ko da yake kuna da yawa kamar taurarin sama, za ku zama 'yan kaɗan, domin ba ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku ba. 63 Kamar yadda Ubangiji ya ji daɗi ya arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku, hakanan kuma zai ji daɗi ya lalatar da ku, ya hallaka ku. Za a fitar da ku daga ƙasar da za ku shiga, ku mallaka. 64 “Ubangiji zai warwatsa ku cikin dukan al'ummai daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Can za ku bauta wa gumakan itace da na dutse waɗanda ku da kakanninku ba ku san su ba. 65 Ba za ku sami zaman lafiya wurin waɗannan al'ummai ba, ko tafin ƙafarku ma ba zai sami wurin hutawa ba. Ubangiji kuma zai sa fargaba a zuciyarku, ya sa idanunku su lalace, ranku zai yi suwu. 66 Kullum ranku zai kasance da damuwa, za ku zauna da tsoro dare da rana, kuna tsoron abin da zai sami ranku. 67 Da safe za ku ce, ‘Da ma maraice ne.’ Da maraice kuma za ku ce, ‘Da ma safiya ce,’ saboda tsoron da yake a zuciyarku, da abubuwan da idanunku suke gani. 68 Ubangiji zai komar da ku Masar cikin jiragen ruwa, ko da yake na ce ba za ku ƙara tafiya can ba. Can za ku sayar da kanku bayi mata da maza, amma ba wanda zai saye ku.”

Maimaitawar Shari’a 29

Alkawarin Ubangiji da Isra'ilawa a Ƙasar Mowab

1 Waɗannan ne zantuttukan alkawari da Ubangiji ya umarci Musa ya faɗa wa Isra'ilawa a ƙasar Mowab, wato banda alkawarin da ya yi da su a bisa Dutsen Horeb. 2 Sai Musa ya kira dukan Isra'ilawa ya ce musu, “Ai, kun ga dukan abin da Ubangiji ya yi wa Fir'auna da barorinsa a dukan ƙasar Masar. 3 Idanunku sun ga manyan wahalai, da alamu, da mu'ujizai masu girma. 4 Duk da haka har wa yau Ubangiji bai ba ku zuciyar ganewa, ko idanun gani, ko kunnuwan ji ba. 5 Shekara arba'in na bi da ku cikin jeji. Rigunanku da takalmanku ba su tsufa ba. 6 Ba ku ci hatsi ba, ba ku kuma sha ruwan inabi ba, ko barasa, don ku sani shi ne Ubangiji Allahnku. 7 Sa'ad da kuka isa wannan wuri, sai Sihon Sarkin Heshbon, da Og, Sarkin Bashan, suka fito su yi yaƙi da mu, amma muka ci su. 8 Muku ƙwace ƙasarsu, muka ba Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa, su gāda. 9 Saboda haka sai ku kiyaye, ku aikata dukan zantuttukan wannan alkawari don ku arzuta a cikin dukan abin da za ku yi. 10 “Yau, ga ku nan tsaye, dukanku a gaban Ubangiji Allahnku, shugabannin kabilanku, da dattawanku, da shugabannin sojojinku, da dukan mazajen Isra'ila, 11 da 'ya'yanku, da matanku, da baƙin da suke a zangonku, da mai yi muku faskare ko mai ɗebo muku ruwa. 12 Don ku ƙulla alkawari da Ubangiji Allahnku, alkawarin da Ubangiji Allahnku yake yi da ku yau. 13 Don ya mai da ku jama'arsa yau, shi kuma ya zama Allahnku kamar yadda ya yi muku magana, da yadda kuma ya rantse wa kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. 14 Ba da ku kaɗai nake yin wannan alkawari ba, 15 amma da wanda ba ya nan tare da mu yau, da shi wanda yake tare da mu a nan yau, a gaban Ubangiji Allahnmu. 16 “Kun sani dai yadda muka zauna a ƙasar Masar, da yadda muka yi ta ratsawa ta tsakiyar al'ummai muka wuce. 17 Kun ga abubuwan da suke da su masu banƙyama, wato gumakansu na itace, da na dutse, da na azurfa, da na zinariya. 18 Kada zuciyar wani mutum, ko ta wata mata ko na wani iyali, ko wata kabila cikinku yau, ta bar bin Ubangiji Allahnku, ta koma ga bauta wa gumakan al'umman nan. Kada a iske wani tushe a cikinku mai ba da 'ya'ya masu dafi, masu ɗaci. 19 Idan wani mutum ya ji zantuttukan la'anar nan sa'an nan ya sa wa kansa albarka a zuciyarsa, yana cewa, ‘Ba abin da zai same ni ko na bi taurin zuciyata,’ wannan zai haddasa lalacewar ɗanye da busasshe gaba ɗaya. 20 Ubangiji ba zai gafarce shi ba, amma fushin Ubangiji da kishinsa za su auko a kan wannan mutum, dukan la'anar kuma da aka rubuta a littafin nan za ta bi ta kansa, Ubangiji kuma zai shafe sunansa daga duniya. 21 Ubangiji zai ware mutumin nan daga dukan kabilan Isra'ila, don ya hukunta shi bisa ga dukan la'anar da aka rubuta a wannan littafin dokoki. 22 “Tsararraki masu zuwa nan gaba, wato 'ya'yan da za su gaje ku, da baƙon da ya zo daga ƙasa mai nisa, za su ga annobar ƙasar, da cuce-cucen da Ubangiji zai ɗora mata. 23 Dukan ƙasa za ta zama kibritu da gishiri, ba shuka, ba amfani, ciyawa kuma ba ta tsirowa, kamar yadda Ubangiji ya kabantar da Saduma da Gwamrata, da Adam da Zeboyim, da zafin fushinsa. 24 Dukan al'ummai za su ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan ƙasa? Me ya sa ya yi fushi mai tsanani haka?’ 25 Sa'an nan jama'a za su ce, ‘Saboda sun yi watsi da alkawarin Ubangiji Allah na kakanninsu, wato alkawarin da ya yi da su sa'ad da ya fisshe su daga ƙasar Masar. 26 Suka tafi suka bauta wa gumaka, suka yi musu sujada, gumakan da ba su san su ba, ba Ubangiji ne ya ba su ba. 27 Saboda haka Ubangiji ya husata da wannan ƙasa, ya kawo mata kowace irin la'anar da aka rubuta a wannan littafin. 28 Ubangiji ya tumɓuke su da zafin fushinsa, da babbar hasala, daga ƙasarsu, ya watsa su cikin wata ƙasa dabam kamar yadda suke a yau.’ 29 “Sanin gaibu na Ubangiji Allahnmu ne, amma abubuwan da aka bayyana namu ne, mu da 'ya'yanmu har abada, don mu kiyaye dukan maganar dokokin nan.”

Maimaitawar Shari’a 30

Sharuɗan Komar da Mutane, da kuma Sa musu Albarka

1 “Sa'ad da duk waɗannan abubuwa suka same ku, wato albarka da la'ana waɗanda na sa a gabanku, in kun tuna da su a zuciyarku a duk inda kuke cikin al'ummai inda Ubangiji Allahnku ya kora ku, 2 kuka sāke komowa wurin Ubangiji Allahnku, ku da 'ya'yanku kuka yi biyayya da maganarsa da zuciya ɗaya, da dukan ranku, bisa ga yadda na umarce ku yau, 3 sa'an nan Ubangiji Allahnku zai komo da ku daga bauta, ya yi muku jinƙai. Zai tattaro ku daga cikin al'ummai inda ya warwatsa ku. 4 Idan korarrunku suna can ƙurewar duniya, Ubangiji Allahnku zai tattaro ku daga can, ya dawo da ku. 5 Ubangiji Allahnku kuma zai komo da ku cikin ƙasar da kakanninku suka mallaka, za ku mallake ta. Ubangiji zai arzuta ku, ya riɓaɓɓanya ku fiye da kakanninku. 6 Ubangiji Allahnku kuma zai tausasa zuciyarku da ta 'ya'yanku domin ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku, domin ku rayu. 7 Ubangiji Allahnku kuwa zai ɗora wa magabtanku da maƙiyanku waɗanda suka tsananta muku waɗannan la'ana. 8 Sa'an nan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye dukan umarnan nan waɗanda na umarce ku da su yau. 9 Ubangiji Allahnku zai arzuta dukan aikin hannuwanku ƙwarai, ya kuma arzutar da 'ya'yanku da 'ya'yan shanu, da amfanin gona, gama Ubangiji zai ji daɗi ya arzuta ku kuma yadda ya ji daɗin kakanninku, 10 idan za ku yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnku, ku kiyaye umarnansa da dokokinsa waɗanda suke rubuce a littafin dokokin nan, idan kuma kun juyo wurin Ubangiji Allahnku da zuciya ɗaya da dukan ranku. 11 “Gama wannan umarni da na yi muku yau, bai fi ƙarfinku ba, bai kuma yi nisa da ku ba. 12 Ba cikin Sama yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai hau zuwa sama, ya sauko mana da shi don mu ji, mu kiyaye?’ 13 Ba kuma a hayin teku yake ba, balle ku ce, ‘Wa zai haye mana wannan teku don ya kawo mana shi don mu ji, mu kiyaye?’ 14 Amma umarnin yana kurkusa da ku, yana cikin bakinku da zuciyarku don ku kiyaye shi. 15 “Ga shi yau, na sa rai da nagarta a gabanku, da mutuwa da mugunta. 16 Idan kuka kiyaye umarnan Ubangiji Allahnku waɗanda nake umartarku da su yau, idan kuma kun ƙaunaci Ubangiji Allahnku, kuna yin tafiya cikin tafarkunsa, kuna kiyaye umarnansa, da dokokinsa, da farillansa, to, za ku rayu, ku riɓaɓɓanya, Ubangiji Allahnku kuwa zai sa muku albarka cikin ƙasar da za ku shiga, ku mallake ta. 17 Amma idan zuciyarku ta kangare kun ƙi ku saurara, amma zuciyarku ta janye ku kun yi wa gumaka sujada, kuka bauta musu, 18 to, ina faɗa muku yau, lalle za ku hallaka. Ba za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun ku shiga ciki don ku mallake ta ba. 19 Ina kiran sama da duniya su zama shaidu a kanku yau, cewa na sa rai da mutuwa a gabanku, da albarka da la'ana. Ku zaɓi rai fa, don ku rayu, ku da zuriyarku. 20 Ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi biyayya da maganarsa, ku manne masa, gama wannan shi ne ranku da tsawon kwanakinku, don ku zauna a ƙasar da Ubangiji Allahnku ya rantse zai ba kakanninku, wato Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.”

Maimaitawar Shari’a 31

Joshuwa zai Gāji Musa

1 Sai Musa ya ci gaba da yi wa dukan Isra'ilawa magana. 2 Ya ce, “Yau shekarata ɗari da ashirin ne, ba na iya kaiwa da komowa. Ubangiji kuwa ya ce mini, ‘Ba za ka haye wannan Urdun ba.’ 3 Ubangiji Allahnku shi ne zai yi gaba ya haye, ya hallaka al'ummar da take gabanku don ku ci su. Joshuwa ne zai shugabance ku, ya haye kamar yadda Ubangiji ya faɗa. 4 Ubangiji zai yi musu kamar yadda ya yi wa Sihon da Og, sarakunan Amoriyawa, da ƙasarsu, sa'ad da ya hallaka su. 5 Ubangiji zai bashe su a gare ku. Za ku yi musu kamar yadda dā na umarce ku. 6 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, kada ku ji tsoro, ko ku firgita saboda su, gama Ubangiji Allahnku yana tare da ku. Ba zai kunyatar da ku ba, ba kuwa zai yashe ku ba.” 7 Sai Musa ya kira Joshuwa, ya yi masa magana a gaban dukan jama'ar Isra'ila, ya ce, “Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka kai wannan jama'a cikin ƙasar da Ubangiji ya rantse zai ba kakanninsu. Kai ne za ka ba su ita gādo. 8 Ubangiji kansa zai bi da kai, ba zai kunyatar da kai ba, ba kuwa zai yashe ka ba. Kada ka ji tsoro, kada kuma ka karai.”

A Karanta Dokokin kowace Shekara ta Bakwai

9 Sai Musa ya rubuta waɗannan dokoki, ya ba firistoci, 'ya'yan Lawiyawa, waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawari na Ubangiji, da dukan dattawan Isra'ila. 10 Sai Musa ya umarce su, ya ce, “A ƙarshen kowace shekara bakwai, a lokacin da aka ƙayyade na shekarar yafewa, a lokacin Idin Bukkoki, 11 sa'ad da dukan Isra'ilawa za su hallara a gaban Ubangiji Allahnku a inda zai zaɓa, to, sai ku karanta musu waɗannan dokoki su ji da kunnuwansu. 12 Ku tara dukan jama'a wuri ɗaya, mata da maza, da yara, da baƙin da suke zaune tare da ku a garuruwanku domin su ji, su koyi tsoron Ubangiji Allahnku, su kuma lura su aikata dukan dokokin nan, 13 domin 'ya'yansu, waɗanda ba su sani ba, su ji, su koyi tsoron Ubangiji Allahnku dukan kwanakinku cikin ƙasar da za ku haye Urdun, ku mallaka.”

Umarnin Ƙarshe da Ubangiji ya Yi wa Musa

14 Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Lokacin rasuwarka ya yi, sai ka kira Joshuwa, ku shigo alfarwa ta sujada, don in ba shi ragamar mulki.” Sai Musa da Joshuwa suka tafi, suka shiga alfarwa ta sujada. 15 Ubangiji kuwa ya bayyana a cikin alfarwar a al'amudin girgije. Al'amudin girgijen kuwa ya tsaya a ƙofar alfarwar. 16 Ubangiji ya ce wa Musa, “Ga shi, za ka rasu ka tarar da kakanninka. Wannan jama'a kuwa za ta fara kaucewa daga hanya, su bi gumakan ƙasar da za su shiga, su zauna. Za su rabu da ni, su ta da alkawarina wanda na yi da su. 17 A wannan rana zan husata da su ƙwarai, in rabu da su, in ɓoye musu fuskata, za a cinye su. Masifu da wahalai za su same su. Za su kuwa ce a ranar, ‘Masifun nan sun same mu domin Allahnmu ba ya tare da mu.’ 18 Hakika kuwa, zan ɓoye musu fuskata sabili da muguntar da suka aikata, suka kuma bi gumaka. 19 “Don haka, sai ka rubuta wannan waƙa, ka koya wa Isra'ilawa. Ka sa ta a bakinsu don waƙar nan ta zama shaida a gare ni game da Isra'ilawa. 20 Sa'ad da na kawo su a ƙasar da take da yalwar abinci, wadda na rantse zan ba kakanninsu, har suka ci, suka ƙoshi, suka yi ƙiba, za su juya, su bi gumaka, su bauta musu. Za su raina ni, su tā da alkawarina. 21 Sa'ad da yawan masifun nan da wahalar nan suka same su, to, waƙar nan za ta ba da shaida a kansu, gama zuriyarsu ba za ta manta da wannan waƙa ba, gama na san ƙudurin da suke yi kafin in kawo su ƙasar da na rantse zan bayar.” 22 Saboda wannan sai Musa ya rubuta wannan waƙa a ranar, ya koya wa jama'ar Isra'ila. 23 Sai Ubangiji ya umarci Joshuwa ɗan Nun ya ce, “Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka kai jama'ar Isra'ila a ƙasar da na rantse zan ba su, ni kuma da kaina zan tafi tare da kai.” 24 Sa'ad da Musa ya gama rubuta maganar dokokin nan sarai a littafin, 25 sai ya umarci Lawiyawa waɗanda suke ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, ya ce, 26 “Ku ɗauki littafin dokokin nan, ku ajiye shi tare da akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku domin ya zama shaida a kanku, 27 gama na san tayarwarku da taurinkanku. Tun ma ina da rai ke nan tare da ku kuka tayar wa Ubangiji, balle bayan rasuwata. 28 Ku tattaro mini dattawan kabilanku da manyanku don in faɗa musu wannan magana a kunnensu, in kuma kira sama da duniya su zama shaida a kansu. 29 Gama na sani bayan rasuwata za ku aikata mugunta, ku kauce daga hanyar da na umarce ku. Masifa za ta auko muku a kwanaki masu zuwa saboda za ku aikata mugunta a gaban Ubangiji, za ku tsokani fushinsa da aikin hannuwanku.”

Waƙar Musa

30 Sa'an nan Musa ya hurta kalmomin wannan waƙa a kunnen dukan taron jama'ar Isra'ila har ƙarshensu.

Maimaitawar Shari’a 32

1 “Ku saurara, ya ku sammai, gama zan yi magana, Bari duniya ta ji maganar bakina. 2 Bari koyarwata ta zubo kamar ruwan sama, Maganata ta faɗo kamar raɓa, Kamar yayyafi a bisa ɗanyar ciyawa, Kamar ɗiɗɗigar ruwa a bisa ganyaye. 3 Gama zan yi shelar sunan Ubangiji, In yabi girman Allahnmu! 4 “Shi Dutse ne, aikinsa kuma cikakke ne, Gama dukan hanyoyinsa masu adalci ne. Allah mai aminci ne, babu rashin gaskiya a gare shi, Shi mai adalci ne, nagari ne kuma. 5 Sun aikata mugunta a gabansa, Su ba 'ya'yansa ba ne saboda lalacewarsu, Su muguwar tsara ce, karkatacciya, 6 Haka za ku sāka wa Ubangiji, Ya ku wawaye, mutane marasa hikima? Ba shi ne Ubanku, Mahaliccinku ba, Wanda ya yi ku, ya kuma kafa ku? 7 “Ku fa tuna da kwanakin dā, Ku yi tunani a kan shekarun tsararraki, Ku tambayi mahaifanku, su za su faɗa muku, Ku tambayi dattawanku, su kuma za su faɗa muku, 8 Sa'ad da Maɗaukaki ya ba al'ummai gādonsu, Sa'ad da ya raba 'yan adam, Ya yanka wa mutane wurin zama bisa ga yawan Isra'ilawa. 9 Gama rabon Ubangiji shi ne jama'arsa, Yakubu shi ne rabon gādonsa. 10 “Ya same shi daga cikin hamada, A jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya kewaye shi, ya lura da shi, Ya kiyaye shi kamar ƙwayar idonsa. 11 Kamar gaggafar da take kaɗa fikafikanta a kan sheƙarta, Tana rufe da 'yan tsakinta, Ta buɗe fikafikanta, ta kama su, Ta ɗauke su a bisa kafaɗunta. 12 Ubangiji ne kaɗai ya bishe shi, Ba wani baƙon allah tare da shi. 13 “Ya sa shi ya hau kan tuddai, Ya ci amfanin ƙasa, Ya sa shi ya sha zuma daga dutse, Ya ba shi mai daga dutsen ƙanƙara. 14 Ya sami kindirmo daga shanu, Da madara daga garken tumaki da na awaki, Da kitse daga 'yan raguna, da raguna, Da bijimai, da bunsurai daga Bashan, Da alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi jaja wur, mai kyau. 15 “Yeshurun ya yi ƙiba, yana harbin iska, Ka yi ƙiba, ka yi kauri, ka yi sumul. Ya rabu da Allahn da ya yi shi, Ya raina Dutsen Cetonsa. 16 Suka sa shi kishi, saboda gumaka, Suka tsokani fushinsa da abubuwan banƙyama. 17 Suka miƙa hadayu ga aljannun da ba Allah ba, Ga gumakan da ba su sani ba, Sababbin allolin da aka shigo da su daga baya, Waɗanda kakanninku ba su ji tsoronsu ba. 18 Kun ƙi kula da Dutsen da ya haife ku, Kun manta da Allahn da ya ba ku rai. 19 “Ubangiji ya gani, ya raina su, Saboda tsokanar da 'ya'yansa mata da maza suka yi masa. 20 Ya ce, ‘Zan ɓoye musu fuskata, Zan ga yadda ƙarshensu zai zama. Gama su muguwar tsara ce, 'Ya'ya ne marasa aminci. 21 Suka sa ni kishi da abin da ba Allah ba, Suka tsokani fushina da gumakansu, Ni kuma zan sa su su yi kishi da waɗanda suke ba mutane ba. Zan tsokane su da wawanyar al'umma. 22 Gama fushina ya kama wuta, Tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za ta cinye duniya da dukan amfaninta, Za ta kama tussan duwatsu. 23 “ ‘Zan tula musu masifu, Zan ƙare kibauna a kansu, 24 Za su lalace saboda yunwa, Zazzaɓi mai zafi, da muguwar annoba za su cinye su. Zan aika da haƙoran namomi a kansu, Da dafin abubuwa masu jan ciki. 25 Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, A cikin ɗakuna kuma tsoro, Zai hallaka saurayi da budurwa, Da mai shan mama da mai furfura. 26 Na ce, “Zan watsar da su, In sa a manta da su cikin mutane.” 27 Amma saboda gudun tsokanar maƙiyi, Kada abokan gābansu su zaci su ne suka ci nasara. Ai, ni ne na yi wannan.’ 28 “Gama su al'umma ce wadda ba ta yin shawara, Ba su da ganewa. 29 Da suna da hikima, da sun gane wannan, Da za su gane da yadda ƙarshensu zai zama! 30 Ƙaƙa mutum ɗaya zai runtumi dubu, Mutum biyu kuma su kori zambar goma, Sai dai Dutsensu ya sayar da su, Ubangiji kuma ya bashe su? 31 Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, Ko abokan gabanmu ma sun san haka. 32 Kurangar inabinsu daga kurangar inabin Saduma ne Da gonakin Gwamrata. 'Ya'yan inabinsu dafi ne, Nonnansu masu ɗaci ne. 33 Ruwan inabinsu dafin macizai ne. Da mugun dafin kumurci. 34 “Wannan ba a jibge suke a rumbunana ba, A ƙulle kuma a taskokina? 35 Sakayya da ɗaukar fansa nawa ne, A lokacin ƙafarsu za ta zame, Gama ranar masifarsu ta kusa, Hallakarsu za ta zo da sauri. 36 Ubangiji zai ɗauka wa jama'arsa fansa, Zai ji ƙan bayinsa, Sa'ad da ya ga ƙarfinsu ya kāsa, Ba kuma wanda ya ragu, bawa ko ɗa. 37 Sa'an nan zai ce, ‘Ina gumakansu, Dutse wanda suka nemi mafaka gare shi, 38 Waɗanda suka ci kitsen hadayunsu, Suka sha ruwan inabin hadayarsu ta sha? Bari su tashi su taimake ku, Bari su zama mafaka! 39 “ ‘Ku duba fa, ni ne shi, Ba wani Allah, banda ni, Nakan kashe, in rayar, Nakan sa rauni, nakan kuma warkar, Ba wanda zai cece su daga hannuna. 40 Na ɗaga hannuna sama, Na rantse da madawwamin raina, 41 Sa'ad da na wasa takobina mai walƙiya, Na riƙe shi da hannuna don yin hukunci, Zan ɗauki fansa a kan magabtana Zan sāka wa maƙiyana. 42 Zan sa kibauna su bugu da jini, Takobina zai ci nama, Da jinin kisassu da na kamammu, Da ƙoƙon kan shugabannin maƙiya.’ 43 “Ya ku al'ummai, ku yabi jama'arsa, Gama zai rama wa bayinsa saboda jininsu, Zai ɗauki fansa a kan magabtansa, Zai tsarkake ƙasar jama'arsa.”

Gargaɗin Musa na Ƙarshe

44 Sai Musa da Joshuwa ɗan Nun suka zo, suka hurta dukan kalmomin wannan waƙa a kunnen jama'a. 45 Sa'ad da Musa ya gama hurta waɗannan kalmomi ga Isra'ila, 46 ya ce musu, “Ku riƙe dukan waɗannan kalmomi a zuciyarku, waɗanda nake yi muku kashedi da su a yau don ku umarci 'ya'yanku su kiyaye dukan maganar dokokin nan sosai. 47 Wannan ba magana kurum ba ce, amma ranku ne. Ta wurin wannan magana ce za ku yi tsawon rai a ƙasar da za ku haye Urdun zuwa ciki don ku mallake ta.”

An Yarda wa Musa ya Hangi Ƙasar Kan'ana

48 A wannan rana ce Ubangiji ya ce wa Musa, 49 “Ka hau duwatsun Abarim, wato Dutsen Nebo wanda yake a ƙasar Mowab, daura da Yariko, ka duba ƙasar Kan'ana wadda zan ba Isra'ilawa su mallaka. 50 Za ka rasu a kan dutsen da za ka hau, za a kai ka wurin mutanen da suka riga ka gidan gaskiya, kamar yadda ɗan'uwanka, Haruna, ya rasu a Dutsen Hor, aka kai shi wurin mutanensa waɗanda suka riga shi gidan gaskiya. 51 Gama ba ku amince da ni ba a gaban mutanen Isra'ila a wurin ruwan Meriba ta Kadesh a jejin Zin a wannan lokaci, domin ba ku nuna tsarkina a gaban jama'ar Isra'ila ba. 52 Za ka ga ƙasar da nake ba jama'ar Isra'ila, amma ba za ka shiga cikinta ba.”

Maimaitawar Shari’a 33

Musa ya Sa wa Kabilan Isra'ila Albarka

1 Wannan ita ce albarkar da Musa, mutumin Allah, ya sa wa Isra'ilawa kafin ya rasu. 2 Ya ce, “Ubangiji ya taho daga Sina'i, Daga Dutsen Faran kuma ya haskaka, Ya taho tare da dubban tsarkakansa, Da harshen wuta a damansa. 3 Hakika, yana ƙaunar jama'arsa, Dukan tsarkaka suna a ikonka, Suna biye da kai, Suna karɓar umarninka. 4 Musa ya ba mu dokoki, Abin gādo ga taron jama'ar Yakubu. 5 Ubangiji shi ne sarki a Yeshurun, Sa'ad da shugabanni suka taru, Dukan kabilan Isra'ila suka taru. 6 “Allah ya sa Ra'ubainu ya rayu, kada ya mutu, Kada mutanensa su zama kaɗan.” 7 A kan Yahuza ya ce, “Ka ji muryar Yahuza, ya Ubangiji, Ka kawo shi wurin jama'arsa. Ka yi yaƙi da ikonka dominsu, Ka taimake shi a kan maƙiyansa.” 8 A kan Lawi ya ce, “Ka ba Mai Tsarki Tumminka da Urim naka, Shi wanda ka jarraba a Masaha, Wanda ka yi jayayya da shi a ruwan Meriba, 9 Wanda ya ce wa mahaifinsa da mahaifiyarsa, ‘Ban kula da ku ba.’ Ya ce wa 'yan'uwansa su ba nasa ba ne. Ya kuma ƙyale 'ya'yansa, Domin sun kiyaye maganarka, Sun riƙe alkawarinka. 10 Suna koya wa Yakubu farillanka, Suna koya wa Isra'ila dokokinka. Suna ƙona turare a gabanka, Suna ƙona hadaya ta ƙonawa a bagadenka. 11 Ya Ubangiji ka inganta jaruntakarsu, Ka karɓi aikin hannuwansu, Ka murƙushe ƙarfin abokan gābansu, Da waɗanda suke ƙinsu don kada su ƙara tashi.” 12 A kan Biliyaminu, ya ce, “Shi ƙaunatacce na Ubangiji ne, Yana zaune lafiya kusa da shi, Ubangiji yana yi masa garkuwa dukan yini, Yana zaune a kan kafaɗunsa.” 13 A kan Yusufu, ya ce, “Ubangiji ya sa wa ƙasarsa albarka, Da kyawawan kyautai daga sama, da raɓa, Da ruwan da yake a ƙasa, 14 Da kyawawan kyautan da rana yake bayarwa, Da kyawawan kyautan da watanni suke bayarwa, 15 Da abubuwa mafi kyau na duwatsun dā, Da kyawawan kyautai na madawwaman tuddai. 16 Da kyautai mafi kyau na duniya da cikarta, Da alherin wanda yake zaune a jeji. Bari waɗannan kyautai su sauka a kan Yusufu, A kan wanda yake keɓaɓɓe daga cikin 'yan'uwansa. 17 Darajarsa kamar ta ɗan farin bijimi take, Ƙahoninsa kamar na ɓauna suke, Da su yake tunkwiyin mutane, Zai tura su zuwa ƙurewar duniya, Haka fa rundunan Ifraimu za su zama, Haka kuma dubban Manassa za su zama.” 18 A kan Zabaluna ya ce, “Ka yi murna da tafiye-tafiyenka, ya Zabaluna, Kai kuma Issaka, cikin alfarwanka. 19 Za su kira mutane zuwa dutse, Can za su miƙa hadayu masu dacewa, Gama za su ɗebo wadatar tekuna, Da ɓoyayyun dukiyar yashi.” 20 A kan Gad, ya ce, “Mai albarka ne wanda ya fāɗaɗa Gad, Gad yana sanɗa kamar zaki, Yana yayyage hannu da ƙoƙon kai. 21 Zai zaɓar wa kansa wuri mai kyau, Gama wurin ne aka keɓe wa shugaba. Ya zo wurin shugabannin mutane, Tare da Isra'ila, ya aikata adalcin Ubangiji, Ya kiyaye farillansa.” 22 A kan Dan, ya ce, “Dan ɗan zaki ne, Mai tsalle daga Bashan.” 23 A kan Naftali, ya ce, “Ya Naftali, ƙosasshe kake da alheri, Cike kake da albarkar Ubangiji. Sai ka mallaki tafki da wajen kudu.” 24 A kan Ashiru, ya ce, “Ashiru mai albarka ne fiye da sauran 'yan'uwansa, Bari ya zama abin ƙauna ga 'yan'uwansa, Ya kuma tsoma ƙafarsa cikin mai. 25 Kurfanka na baƙin ƙarfe ne da tagulla, Ƙarfinka ba zai rabu da kai ba muddin ranka.” 26 “Babu wani kamar Allahn Yeshurun, Wanda yakan sauko daga Sama don ya cece ka, Wanda ya sauko daga bisa da ɗaukakarsa. 27 Allah Madawwami, shi ne wurin zamanka, Madawwaman damatsansa suna tallafarka, Yana kore maka maƙiyanka, Ya ce, ‘Ka hallaka su!’ 28 Da haka Isra'ila yana zaune lafiya, Zuriyar Yakubu tana zaune ita kaɗai A ƙasa mai hatsi da ruwan inabi, Wurin da raɓa yake zubowa daga sama. 29 Mai farin ciki ne kai, ya Isra'ila! Wane ne kamarku, mutanen da Ubangiji ya ceta? Ubangiji ne garkuwarku, Shi ne kuma takobinku mai daraja. Magabtanku za su yi muku fādanci, Amma ku za ku tattake masujadansu.”

Maimaitawar Shari’a 34

Rasuwar Musa

1 Sai Musa ya tashi daga filayen Mowab zuwa Dutsen Nebo, a ƙwanƙolin Fisga wanda yake daura da Yariko. Sai Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, tun daga Gileyad har zuwa Dan, 2 da dukan Naftali, da ƙasar Ifraimu, da ta Manassa, da dukan ƙasar Yahuza har zuwa Bahar Rum, 3 da Negeb, da filin kwarin Yariko, birnin itatuwan giginya, har zuwa Zowar. 4 Ubangiji ya ce masa, “Wannan ita ce ƙasar da na rantse wa Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, zan ba da ita ga zuriyarsu. Na bar ka ka gan ta da idanunka, amma ba za ka haye, ka shiga ba.” 5 Nan fa, a ƙasar Mowab, Musa bawan Ubangiji, ya rasu kamar yadda Ubangiji ya faɗa. 6 Aka binne shi cikin kwarin ƙasar Mowab, kusa da Betfeyor, amma ba wanda ya san inda aka binne shi har yau. 7 Musa ya yi shekara ɗari da ashirin sa'ad da ya rasu. Idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuma bai ragu ba. 8 Isra'ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab har kwana talatin. Sa'an nan kwanakin kuka da makoki domin Musa suka ƙare. 9 Joshuwa ɗan Nun yana cike da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya masa hannuwansa. Isra'ilawa suka yi masa biyayya, suka aikata bisa ga yadda Ubangiji ya umarci Musa. 10 Tun daga lokacin nan, ba a taɓa yin wani annabi a Isra'ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska. 11 Ubangiji ya aike shi ya aikata alamu da mu'ujizai a ƙasar Masar a gaban Fir'auna da dukan barorinsa, da dukan ƙasarsa. 12 Ya kuma aikata ayyuka masu iko, masu bantsoro a gaban dukan Isra'ilawa.

Joshuwa 1

Shirin da aka Yi don Cin Ƙasar Kan'ana

1 Bayan rasuwar Musa, bawan Ubangiji, Ubangiji ya ce wa Joshuwa ɗan Nun, wanda ya yi wa Musa aiki, 2 “Bawana Musa ya rasu, sai ka tashi ka haye Kogin Urdun, kai da dukan jama'ar nan, zuwa cikin ƙasar da nake ba Isra'ilawa. 3 Duk inda tafin sawunku ya taka na riga na ba ku, kamar yadda na alkawarta wa Musa. 4 Tun daga jejin, da Lebanon, har zuwa babban kogin, wato Kogin Yufiretis, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum wajen yamma, za ta zama ƙasarku. 5 Ba mutumin da zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Kamar yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai, ba zan kunyatar da kai ba, ba kuwa zan yashe ka ba. 6 Ka dāge, ka yi ƙarfin hali, gama kai ne za ka yi jagorar wannan jama'a su mallaki ƙasa wadda na rantse zan ba kakanninsu. 7 Ka dai dāge, ka yi ƙarfin hali ƙwarai, kana kiyaye dukan dokokin da bawana Musa ya umarce ka da su. Kada ka kauce musu dama ko hagu, gama da hakanan za ka arzuta cikin dukan harkokinka. 8 Kada wannan littafin dokoki ya rabu da bakinka, amma zai zama abin da za ka yi ta tunani a kansa dare da rana domin ka kiyaye, ka kuma aikata bisa ga dukan abin da aka rubuta a ciki, gama ta haka za ka yi albarka cikin hanyarka, ta haka kuma za ka yi nasara. 9 Ashe, ban umarce ka ba? Ka dāge ka yi ƙarfin hali, kada ka firgita ko ka tsorata, gama Ubangiji Allahnka yana tare da kai duk inda za ka.” 10 Sai Joshuwa ya umarci shugabannin jama'a, ya ce, 11 “Ku shiga zango, ku umarci jama'a, ku ce, ‘Ku shirya wa kanku guzuri, gama nan gaba da kwana uku za ku haye Kogin Urdun don ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku.’ ” 12 Joshuwa kuma ya ce wa Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa, 13 “Ku tuna da maganar da Musa, bawan Ubangiji, ya umarce ku da ita, ya ce, ‘Ubangiji Allahnku zai hutar da ku, zai kuma ba ku wannan ƙasa.’ 14 Da matanku, da 'yan ƙanananku, da dabbobinku, za su zauna a ƙasar da Musa ya ba ku a wannan hayin Urdun, amma jarumawanku su haye tare da 'yan'uwanku da shirin yaƙi domin su taimake su, 15 har lokacin da Ubangiji ya hutar da 'yan'uwanku kamarku, su kuma su mallaki ƙasa wadda Ubangiji Allahnku yake ba su, a sa'an nan za ku koma zuwa ƙasar da take mulkinku, ku mallake ta, wato ƙasar da Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku a hayin Urdun wajen gabas.” 16 Su kuwa suka amsa wa Joshuwa, suka ce, “Iyakar abin da ka umarce mu za mu yi, duk inda ka aike mu kuma za mu tafi. 17 Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya a kowane abu hakanan za mu yi maka biyayya, Ubangiji Allahnka dai ya kasance tare da kai kamar yadda ya kasance tare da Musa. 18 Duk wanda ya ƙi bin umarninka, bai kuwa yi biyayya da maganarka da dukan irin abin da ka umarce shi ba, za a kashe shi. Kai dai ka dāge, ka yi ƙarfin hali.”

Joshuwa 2

Joshuwa ya Aiki 'Yan Leken Asirin Ƙasa zuwa Yariko

1 Sai Joshuwa ɗan Nun ya aiki mutum biyu 'yan leƙen asirin ƙasa daga Shittim a asirce, ya ce musu, “Tafi, ku leƙo asirin ƙasar, musamman Yariko.” Suka tafi, suka shiga gidan wata mace, karuwa, sunanta Rahab, a nan suka sauka. 2 Sai aka faɗa wa Sarkin Yariko, aka ce, “Ga waɗansu mutane sun shigo nan da dad dare domin su bincike ƙasar.” 3 Sarkin Yariko kuwa ya aika wurin Rahab ya ce, “Fito da mutanen da suka zo wurinki, waɗanda suka shiga gidanki, gama sun zo ne domin su leƙi asirin ƙasar duka.” 4 Amma macen ta riga ta ɓoye mutanen nan biyu, sai ta ce, “Gaskiya ce, mutanen sun zo wurina, amma ban san ko daga ina suka zo ba, 5 da maraice kuma, sa'ad da za a rufe ƙofar garin, sai mutanen suka fita, inda suka tafi kuwa ban sani ba, ku bi su da sauri, gama za ku ci musu.” 6 Gama ta riga ta kai su bisa rufin ɗaki, ta rufe su da ƙasheshen rama waɗanda ta shimfiɗa a bisa rufin. 7 Mutanen kuwa suka tafi don su bi bayansu a hanyar Urdun har zuwa mashigai. Da fitar masu bin sawun, sai aka rufe ƙofar garin. 8 Amma kafin 'yan leƙen asirin ƙasar su kwanta, sai ta tafi wurinsu a bisa rufin ɗakin, 9 ta ce musu, “Na sani Ubangiji ya ba ku ƙasar, tsoronku kuma ya kama mu har zukatan mazaunan ƙasar duka sun narke saboda ku. 10 Gama mun ji yadda Ubangiji ya sa ruwan Bahar Maliya ya ƙafe a gabanku a sa'ad da kuka fito daga Masar, da irin abin da kuka yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa waɗanda suke a hayin Urdun, wato Sihon da Og, waɗanda kuka hallakar da su sarai. 11 Da muka ji, sai zukatanmu suka narke, har ba sauran ƙarfin hali da ya ragu a kowane mutum saboda ku. Gama Ubangiji Allahnku shi ne Allahn da yake a Sama daga bisa, da duniya a ƙasa. 12 Yanzu fa, ku rantse mini da Ubangiji, kamar yadda na yi muku alheri, haka ku kuma za ku yi wa gidan mahaifina, ku ba ni tabbatacciyar alama. 13 Ku ceci mahaifina, da mahaifiyata, da 'yan'uwana mata da maza, da dukan abin da yake nasu, ku ceci rayukanmu daga mutuwa.” 14 Mutanen kuwa suka ce mata, “Ranmu a bakin naki, idan ba ki tone al'amarinmu ba, za mu yi miki alheri da aminci sa'ad da Ubangiji ya ba mu ƙasar.” 15 Sa'an nan ta zurarar da su da igiya ta taga, gama gidanta yana haɗe da garun birnin ne. 16 Sai ta ce musu, “Tafi cikin tsaunuka domin kada masu bin sawun su same ku, ku ɓuya a wurin kwana uku, har masu bin sawun su komo, sa'an nan ku kama hanyarku.” 17 Mutanen suka ce mata, “Za mu kuɓuta daga rantsuwarki wadda kika rantsar da mu. 18 A lokacin da za mu shigo ƙasar, sai ki ɗaura wannan jan kirtani a tagar da kika zurarar da mu, ki kuma kawo mahaifinki, da mahaifiyarki, da 'yan'uwanki, da dukan iyalin gidan mahaifinki a gidanki. 19 Idan waninku ya fita daga ƙofar gidanki zuwa kan titi, to, alhakin jininsa yana bisa kansa, mu kuwa sai mu kuɓuta. Amma idan aka sa wa wani hannu wanda yake cikin gida tare da ke, alhakin jininsa yana kanmu. 20 Amma idan kika tone al'amarin nan namu, to za mu kuɓuta daga rantsuwar da kika rantsar da mu.” 21 Sai ta ce, “Bisa ga maganarku ya zama haka.” Sa'an nan ta sallame su, suka tafi. Ta kuwa ɗaura jan kirtanin a tagar. 22 Sai suka tafi, suka shiga tsaunuka, suka yi zamansu a can kwana uku har masu bin sawun suka koma, gama masu bin sawun suka yi ta nema ko'ina a hanyar, amma ba su sami kowa ba. 23 Mutanen nan biyu suka sauko daga tsaunuka, suka haye zuwa wurin Joshuwa ɗan Nun, suka faɗa masa dukan abin da ya same su. 24 Suka kuma ce masa, “Hakika, Ubangiji ya ba da ƙasar duka a hannunmu, banda wannan kuma mazaunan ƙasar duka sun firgita saboda mu.”

Joshuwa 3

Isra'ilawa sun Haye Urdun

1 Joshuwa kuwa ya tashi da sassafe, da shi da dukan jama'ar Isra'ila, suka kama hanya daga Shittim zuwa Urdun, inda suka sauka kafin su haye. 2 Bayan kwana uku sai shugabannin jama'a suka bibiya zango, 3 suna umartar jama'ar suna cewa, “Sa'ad da kuka ga akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku, sai ku tashi daga inda kuke, ku bi shi, 4 domin ku san hanyar da za ku bi, gama ba ku taɓa bin hanyar ba. Sai dai tsakaninku da shi za ku bar rata misalin nisan kamu dubu biyu, kada ku kusace shi.” 5 Sai Joshuwa ya ce wa jama'a, “Ku tsarkake kanku, gama gobe Ubangiji zai aikata abin al'ajabi a tsakiyarku.” 6 Ya kuma ce wa firistocin, “Ku ɗauki akwatin alkawari ku wuce gaban jama'ar.” Sai suka ɗauki akwatin alkawari suka wuce gaban jama'a. 7 Ubangiji kuwa ya ce wa Joshuwa, “A yau ɗin nan zan fara ɗaukaka ka a gaban dukan Isra'ilawa domin su sani, kamar yadda na kasance tare da Musa, haka kuwa zan kasance tare da kai. 8 Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari cewa, ‘Sa'ad da kuka shiga gefen ruwan Urdun, sai ku tsaya cik a wurin.’ ” 9 Joshuwa kuma ya ce wa Isra'ilawa, “Ku kusato ku ji zantuttukan Ubangiji Allahnku.” 10 Joshuwa kuma ya ƙara da cewa, “Ta haka za ku sani Allah mai rai yana tsakiyarku, ba makawa kuwa zai kori Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Hiwiyawa, da Ferizziyawa, da Girgashiyawa, da Amoriyawa, da Yebusiyawa a gabanku. 11 Ga shi, akwatin alkawari na Ubangijin dukkan duniya yana wucewa a gabanku zuwa cikin Urdun. 12 Yanzu fa, ku ɗauki mutum goma sha biyu daga kabilanku, wato mutum ɗaya daga kowace kabila. 13 A sa'ad da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji, Ubangijin dukkan duniya, suka tsoma tafin sawunsu cikin ruwan Urdun, ruwan Urdun zai yanke, ruwan da yake gangarowa zai tsaya tsibi guda.” 14-15 (Da kaka Urdun yakan yi cikowa makil.) Jama'a fa, suka tashi daga alfarwansu don su haye Urdun. Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suna gaba. Da firistocin suka tsoma ƙafafunsu cikin ruwa daga gefe, 16 sai ruwan da yake gangarowa ya tsaya, ya tattaru wuri ɗaya, ya yi soro daga nesa kusa da Adam, birnin da yake kusa da Zaretan. Ruwan kuma da yake gangarowa zuwa Tekun Araba, wato Tekun Gishiri, aka yanke shi ɗungum. Jama'a kuwa suka haye daura da Yariko. 17 A sa'ad da Isra'ilawa duka suke tafiya a kan sandararriyar ƙasa a cikin Urdun, firistoci kuwa waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka yi ta tsayawa a bisa sandararriyar ƙasa a tsakiyar Urdun har al'ummar ta gama hayewa.

Joshuwa 4

Duwatsu Goma Sha Biyu da aka Ɗauka Tsakiyar Urdun

1 Da al'umma duka suka gama haye Urdun, sai Ubangiji ya ce wa Joshuwa, 2 “Ɗauki mutum goma sha biyu daga cikin jama'a, wato mutum ɗaya na kowace kabila. 3 Ka umarce su su ɗauki duwatsu goma sha biyu daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, su haye da su, su ajiye su a masaukin da za su kwana yau.” 4 Sai Joshuwa ya kirawo mutum goma sha biyu waɗanda ya zaɓa daga cikin Isra'ilawa, mutum guda na kowace kabila. 5 Ya ce musu, “Wuce gaban akwatin Ubangiji Allahnku zuwa tsakiyar Urdun, ko wannenku ya ɗauki dutse a kafaɗarsa, don kowace kabila ta Isra'ila. 6 Wannan zai zama alama a gare ku, don ya yiwu wata rana 'ya'yanku za su tambaye ku, su ce, ‘Ina ma'anar waɗannan duwatsu a gare ku?’ 7 Sa'an nan za ku faɗa musu cewa, ‘Domin an yanke ruwan Urdun a gaban akwatin alkawari na Ubangiji sa'ad da ya haye Urdun.’ Waɗannan duwatsu za su zama abin tunawa ga Isra'ilawa har abada.” 8 Sai Isra'ilawa suka yi yadda Joshuwa ya umarta, suka ɗauki duwatsu goma sha biyu a tsakiyar Urdun bisa ga yawan kabilansu kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Joshuwa, suka haye da su zuwa inda suka sauka, a can suka ajiye su. 9 Joshuwa kuma ya kafa duwatsu goma sha biyu a tsakiyar Urdun, a wurin da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya, duwatsun suna nan har wa yau. 10 Gama firistocin da suke ɗauke da akwatin sun tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Joshuwa ya faɗa wa jama'a, da kuma bisa ga dukan abin da Musa ya umarce shi. Mutanen kuwa suka gaggauta, suka haye. 11 Da jama'a duka suka gama hayewa, sai akwatin Ubangiji da firistocin suka wuce gaban jama'ar. 12 Mutanen Ra'ubainu, da na Gad, da rabin kabilar Manassa kuwa suka haye tare da 'yan'uwansu da shirin yaƙi kamar yadda Musa ya umarce su. 13 Mutum wajen dubu arba'in ne (40,000 ), mayaƙa, suka haye da shirin yaƙi a gaban Ubangiji zuwa filayen Yariko. 14 A ranar nan Ubangiji ya ɗaukaka Joshuwa a idon dukan Isra'ilawa, har suka ga kwarjininsa dukan kwanakin ransa kamar yadda suka ga na Musa. 15 Ubangiji kuma ya ce wa Joshuwa, 16 “Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin shaida, su fito daga cikin Urdun.” 17 Sai Joshuwa ya umarci firistocin su fito daga cikin Urdun. 18 Da firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari na Ubangiji suka fito daga tsakiyar Urdun, suka taka sandararriyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya malalo ya tumbatsa kamar dā. 19 Rana ta goma ga watan ɗaya jama'a suka haye Urdun, suka yi zango a Gilgal a gabashin iyakar Yariko. 20 Joshuwa ya kafa duwatsun nan goma sha biyu da suka ɗauko daga Urdun a Gilgal. 21 Sai ya ce wa Isra'ilawa, “Sa'ad da wata rana 'ya'yanku suka tambayi ubanninsu ma'anar duwatsun nan, 22 sa'an nan za ku sanar da 'ya'yanku cewa Isra'ilawa sun haye Urdun da ƙafa a kan sandararriyar ƙasa! 23 Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya ƙafe, har kuka haye kamar yadda Ubangiji Allahnku ya sa Bahar Maliya ta ƙafe har muka haye, 24 domin dukan mutanen duniya su sani Ubangiji yana da iko, domin kuma ku kasance da tsoron Ubangiji Allahnku har abada.”

Joshuwa 5

Yin Kaciya da Kiyaye Idin Ƙetarewa a Gilgal

1 Sa'ad da dukan sarakunan Amoriyawa waɗanda suke wannan hayi, wato yamma da Urdun, da dukan sarakunan Kan'aniyawa da suke bakin teku, suka ji yadda Ubangiji ya sa ruwan Urdun ya ƙafe don Isra'ilawa, har suka haye, sai zukatansu suka narke, har ba wanda yake da sauran kurwa a cikinsu saboda tsoron Isra'ilawa. 2 A lokacin kuwa Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Ka yi wuƙaƙe na duwatsu, ka yi wa mazajen Isra'ila kaciya.” 3 Sai Joshuwa ya yi wuƙaƙe na duwatsu, ya yi wa mutanen kaciya a Gibeyat-ha'aralot, wato dutsen kaciya. da ya sa Joshuwa ya yi musu kaciya ke nan, domin dukan waɗanda aka haifa a hanya cikin jeji bayan fitowarsu daga Masar, ba a yi musu kaciya ba. Dukan mazajen da suka fito daga Masar waɗanda suka isa yaƙi sun rasu cikin jeji a hanyarsu. Waɗannan kuwa an yi musu kaciya kafin fitowarsu. 6 Gama shekara arba'in Isra'ilawa suna ta tafiya a jeji, har dukan al'umma, har da mayaƙan da suka fito daga Masar, suka hallaka, domin ba su kula da muryar Ubangiji ba. A gare su kuwa Ubangiji ya rantse, ba zai bar su su ga ƙasar da ya rantse wa kakanninsu zai ba su ba, ƙasar da yake mai yalwar abinci. 7 'Ya'yansu ne kuwa waɗanda Ubangiji ya tā da su a maimakonsu, su ne Joshuwa ya yi wa kaciya, gama ba su da kaciya, domin a hanya ba a yi musu ba. 8 Da aka gama yi wa al'ummar duka kaciya, sai suka zauna a zango har suka warke. 9 Sai Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “A wannan rana na kawar muku da zargin Masar.” Saboda haka, har wa yau ake kiran sunan wurin Gilgal, wato a kawar. 10 Sa'ad da Isra'ilawa suke zaune a Gilgal, sai suka yi Idin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu ga watan, da maraice, a filayen Yariko. 11 A kashegarin idin, a wannan rana, sai suka ci daga cikin amfanin ƙasar, waina marar yisti da busasshiyar tsaba. 12 Kashegari bayan da suka ci amfanin ƙasar kuwa, mannar ta yanke, mutanen Isra'ila kuma ba su ƙara samunta ba. A wannan shekara suka fara cin amfanin ƙasar Kan'ana.

Joshuwa da Mutumin da yake Riƙe da Takobi

13 Lokacin da Joshuwa yake daura da Yariko, ya ta da idanunsa ya duba, sai ya ga mutum a tsaye a gabansa da takobinsa a zare a hannunsa. Joshuwa ya tafi wurinsa, ya ce masa, “Kana wajenmu ne, ko kuwa kana wajen abokan gābanmu?” 14 Sai mutumin ya ce, “A'a, gama na zo ne kamar sarkin yaƙin rundunar Ubangiji.” Sai Joshuwa ya sunkuyar da kansa, ya rusuna har ƙasa, ya yi sujada, ya ce masa, “Wace magana ce Ubangiji yake faɗa wa bawansa?” 15 Sarkin yaƙin rundunar Ubangiji kuwa ya ce wa Joshuwa, “Cire takalmanka da suke a ƙafafunka, gama wurin da kake tsaye tsattsarka ne.” Haka kuwa Joshuwa ya yi.

Joshuwa 6

Faɗuwar Yariko

1 Aka rufe Yariko ciki da waje, ba mai fita, ba mai shiga saboda Isra'ilawa. 2 Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Duba, na ba da Yariko, da sarkinta, da jarumawanta a hannunka. 3 Kai da dukan mayaƙa za ku zagaya birnin sau ɗaya kowace rana har kwana shida. 4 Sai firistoci bakwai su riƙe ƙahonin raguna a gaban akwatin alkawari. Amma a rana ta bakwai za ku zaga birnin sau bakwai, firistoci su yi ta busar ƙahoni. 5 Sa'ad da suka tsawaita busar ƙahoni, sai dukan jama'a su yi ihu da babbar murya, garun birnin kuwa zai rushe tun daga tushensa. Sai mutane su haura, ko wanne ya nufi inda ya fuskanta sosai zuwa cikin birnin.” 6 Joshuwa ɗan Nun kuwa ya kirawo firistoci, ya ce musu, “Ɗauki akwatin alkawarin, sa'an nan firistoci bakwai su ɗauki ƙaho bakwai na raguna su wuce a gaban akwatin alkawarin Ubangiji.” 7 Ya kuma ce wa jama'a, “Ku wuce, ku zaga birnin, masu makamai kuma su wuce a gaban akwatin Ubangiji.” 8 Kamar yadda Joshuwa ya umarci jama'a, firistoci bakwai da suke riƙe da ƙaho bakwai na raguna a gaban Ubangiji suka wuce gaba, suna busawa, akwatin alkawari na Ubangiji yana biye da su. 9 Masu makamai kuwa suka wuce gaban firistocin da suke busa ƙahonin, 'yan tsaron baya suna biye da akwati, ana ta busa ƙahoni. 10 Amma Joshuwa ya umarci mutane cewa, “Ba za ku yi ihu ba, ba kuwa za ku bari a ji muryarku, ko kuwa wata magana ta fito daga bakinku ba, sai ranar da na ce muku ku yi ihu, sa'an nan za ku yi ihu.” 11 Ya kuwa sa akwatin Ubangiji ya zaga birnin, aka zaga da shi sau ɗaya sa'an nan suka koma zango, suka kwana. 12 Sai Joshuwa ya tashi da sassafe, firistocin suka ɗauki akwatin Ubangiji. 13 Firistoci bakwai ɗin da suke riƙe da ƙaho bakwai na raguna, suka wuce gaban akwatin Ubangiji suna ta busawa, masu makamai suna tafe a gabansu, 'yan tsaron baya suna biye da akwatin Ubangiji, ana ta busa ƙahoni. 14 A rana ta biyu kuma suka zaga birnin sau ɗaya, sa'an nan suka koma zango. Haka suka yi ta yi har kwana shida. 15 A rana ta bakwai kuwa suka tashi da sassafe, suka yi sammako, suka zaga birnin yadda suka saba yi har sau bakwai. A wannan rana kaɗai ne suka zaga birnin sau bakwai. 16 A zagawa ta bakwai, sa'ad da firistoci suka busa ƙahoni, sai Joshuwa ya ce wa jama'a, “Ku yi ihu, gama Ubangiji ya ba ku birnin. 17 Amma birnin da dukan abin da yake cikinsa haram ne ga Ubangiji, sai a hallaka su. Rahab karuwar nan kaɗai ce, da dukan waɗanda suke tare da ita a gidanta za a bari da rai domin ta ɓoye 'yan leƙen asirin ƙasa da muka aika. 18 Amma sai ku tsare kanku daga abubuwan da aka haramta don a hallaka su. Kada ya zama bayan da kuka haramta su ku sāke ɗaukar wani abu daga cikinsu, har da za ku sa zangon Isra'ilawa ya zama abin hallakarwa, ku jawo masa masifa. 19 Amma dukan azurfa, da zinariya, da kwanonin tagulla, da na baƙin ƙarfe keɓaɓɓu ne ga Ubangiji. Za a shigar da su cikin taskar masujadar Ubangiji.” 20 Jama'a suka yi ihu, aka busa ƙahoni. Nan da nan da jama'ar suka ji muryar ƙaho, suka yi ihu da babbar murya, sai garun ya rushe tun daga tushenta. Jama'a kuwa suka shiga birnin, ko wanne ya nufi inda ya fuskanta sosai, suka ci birnin. 21 Sa'an nan suka hallakar da dukan abin da yake a cikin birnin, da mata da maza, yara da tsofaffi, da shanu da tumaki, da jakai. 22 Sa'an nan Joshuwa ya ce wa mutum biyu ɗin nan da suka leƙo asirin ƙasar, “Tafi gidan karuwar, ku fitar da ita, da dukan waɗanda suke nata kamar yadda kuka rantse mata.” 23 Sai samarin da suka leƙo asirin ƙasar suka shiga, suka fito da Rahab, da mahaifinta, da mahaifiyarta, da 'yan'uwanta, da dukan waɗanda suke nata, suka fito da dukan danginta, suka saukar da su a bayan zangon Isra'ilawa. 24 Suka ƙone birnin da wuta da dukan abin da yake a cikinsa, sai dai azurfa, da zinariya, da kwanonin tagulla, da na baƙin ƙarfe ne, suka ajiye a cikin taskar masujadar Ubangiji. 25 Amma Joshuwa ya bar Rahab da rai, da ita da iyalin mahaifinta, da dukan waɗanda suke nata. Rahab ta yi zamanta wurin Isra'ilawa har wa yau domin ta ɓoye manzannin da Joshuwa ya aika don su leƙo asirin Yariko. 26 A lokacin nan Joshuwa ya yi musu magana da rantsuwa ya ce, “La'ananne ne mutum a gaban Ubangiji Wanda ya tashi don ya sāke gina birnin nan Yariko. A bakin ɗan farinsa zai kafa tushensa, A bakin autansa kuma zai gina ƙofofinsa.” 27 Ubangiji yana tare da Joshuwa, ya kuwa yi suna cikin dukan ƙasar.

Joshuwa 7

Zunubin Akan

1 Amma Isra'ilawa suka ci amana, gama Akan, ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera na kabilar Yahuza ya ɗiba daga cikin abubuwan da aka haramta, Sai Ubangiji ya husata da Isra'ilawa. 2 Joshuwa kuma ya aiki mutane daga Yariko zuwa Ai wadda take kusa da Betawen gabashin Betel, ya ce musu, “Ku tafi ku leƙi asirin ƙasar.” Sai mutanen suka tafi, suka leƙo asirin Ai. 3 Da suka komo wurin Joshuwa, sai suka ce masa, “Kada dukan mutane su tafi, amma a bar mutum wajen dubu biyu ko uku su tafi su bugi Ai, kada a sa dukan mutane su sha wahalar zuwa can, domin su kima ne.” 4 Sai mutum wajen dubu uku daga cikin jama'a suka tafi, amma mutanen Ai suka kore su. 5 Mutanen Ai suka kashe mutum wajen talatin da shida daga cikin Isra'ilawa, suka runtume su tun daga ƙofar garin har zuwa Shebarim, suka yi ta karkashe su har zuwa gangaren. Zukatan mutanen Isra'ila kuwa suka narke, suka zama kamar ruwa. 6 Sai Joshuwa ya yayyage tufafinsa, ya faɗi rubda ciki a gaban akwatin Ubangiji har yamma. Shi da dattawan Isra'ila, suka zuba ƙura a bisa kansu. 7 Joshuwa ya ce, “Kaitonmu, ya Ubangiji Allah, me ya sa ka haye da jama'ar nan zuwa wannan hayin Urdun, don ka bashe mu a hannun Amoriyawa, su hallakar da mu? Da ma mun haƙura, mun yi zamanmu a wancan hayin Urdun. 8 Ya Ubangiji, me zan ce bayan da Isra'ilawa sun ba da baya ga abokan gābansu? 9 Gama Kan'aniyawa da dukan mazaunan ƙasar za su ji labari, su kewaye mu, su shafe sunanmu daga duniya, to, me za ka yi don sunanka mai girma?” 10 Ubangiji kuwa ya ce wa Joshuwa, “Tashi, don me ka fāɗi rubda ciki? 11 Isra'ilawa sun yi zunubi. Sun ta da alkawarina, wanda na umarce su, gama sun ɗiba daga cikin abubuwan da aka haramta, sun sa a kayansu, sun yi ƙarya. 12 Saboda haka Isra'ilawa ba su iya tsayawa a gaban abokan gābansu ba, sun ba da baya ga abokan gābansu, gama sun zama haramtattu don hallakarwa. Daɗai, ba zan kasance tare da ku ba, sai dai kun kawar da haramtattun abubuwa da suke cikinku. 13 Tashi, ka tsarkake jama'a, ka ce, ‘Ku tsarkake kanku domin gobe, gama Ubangiji, Allah na Isra'ila ya ce akwai haramtattun abubuwa a tsakiyarku. Ya Isra'ila, ba ku iya tsayawa a gaban abokan gābanku ba, sai kun kawar da haramtattun abubuwa daga tsakiyarku. 14 Da safe kuwa za a gabatar da ku kabila kabila, zai zama kuwa kabilar da Ubangiji ya ware, za a gabatar da ita iyali iyali, iyalin da Ubangiji ya ware kuma, za a gabatar da su gida gida, gidan kuma da Ubangiji ya ware, za a gabatar da su mutum mutum. 15 Zai zama kuwa wanda aka same shi da haramtattun abubuwa, za a ƙone shi da wuta, shi da dukan abin da yake da shi, domin ya tā da alkawarin Ubangiji, ya kuma yi abin kunya cikin Isra'ila.’ ” 16 Joshuwa kuwa ya tashi da sassafe, ya gabatar da Isra'ilawa kabila kabila, aka ware kabilar Yahuza. 17 Ya gabatar da iyalan Yahuza, aka ware iyalin Zera. Ya gabatar da iyalin Zera gida gida, aka ware gidan Zebdi. 18 Ya gabatar da iyalin gidansa mutum mutum, aka ware Akan, ɗan Karmi, ɗan Zabdi, ɗan Zera na kabilar Yahuza. 19 Sai ya ce wa Akan, “Ɗana, ka ba da girma ga Ubangiji, Allah na Isra'ila, ka yabe shi ka gaya mini abin da ka yi, kada ka ɓoye mini.” 20 Akan kuwa ya amsa wa Joshuwa, ya ce, “A gaskiya kam, na yi wa Ubangiji, Allah na Isra'ila zunubi. Ga abin da na yi. 21 A cikin kayan ganimar na ga wata kyakkyawar alkyabba irin ta Shinar, da shekel dari biyu na azurfa, da sandan zinariya mai nauyin shekel hamsin, sai na yi ƙyashi, na kwashe su, ga su a binne a ƙasa a alfarwata da azurfa a ƙarƙashi.” 22 Joshuwa ya aika da manzanni, suka sheƙa a guje zuwa alfarwar, suka tarar da abubuwan a binne cikin alfarwarsa da azurfa a ƙarƙashi. 23 Sai suka kwaso suka kawo wa Joshuwa da dukan Isra'ilawa, suka ajiye su a gaban Ubangiji. 24 Joshuwa kuwa tare da dukan Isra'ilawa suka ɗauki Akan, ɗan Zera, da azurfar, da alkyabbar, da sandan zinariya, da 'ya'yansa mata da maza, da shanunsa, da jakunansa, da tumakinsa, da alfarwarsa, da dukan abin da yake da shi, suka kawo su a Kwarin Akor. 25 Sai Joshuwa ya ce, “Don me ka wahalshe mu? Kai ma, Ubangiji zai wahalshe ka yau!” Dukan Isra'ilawa suka jajjefe su da duwatsu, suka ƙone su da wuta. 26 Suka tara tsibin duwatsu a kansu. Tsibin duwatsun kuwa yana nan har wa yau. Sa'an nan Ubangiji ya huce daga zafin fushinsa. Domin haka ana kiran wurin Kwarin Akor, wato azaba, har wa yau.

Joshuwa 8

An Ci Ai da Yaƙi

1 Ubangiji kuma ya ce wa Joshuwa, “Kada ka ji tsoro ko ka firgita. Ka ɗauki mayaƙa duka, ka tashi, ka tafi Ai. Ga shi, na riga na ba da Sarkin Ai da mutanensa, da birninsa, da ƙasarsa a hannunka. 2 Za ka yi wa Ai da sarkinta kamar yadda ka yi wa Yariko da sarkinta, sai dai ganima da dabbobinta ne za ku washe domin kanku. Ku yi kwanto a bayan birnin.” 3 Joshuwa kuwa tare da dukan mayaƙa suka yi shirin tashi zuwa Ai. Sai Joshuwa ya zaɓi jarumawa ƙarfafa dubu talatin (30,000 ), ya aike su da dad dare. 4 Ya umarce su, ya ce, “Ku tafi, ku yi kwanto a bayan birnin, kada ku yi nisa da birni da yawa, amma dukanku ku kasance da shiri sosai. 5 Da ni da dukan mutanen da suke tare da ni za mu je kusa da birnin. Sa'ad da za su fito don su yi karo da mu kamar dā, za mu gudu daga gare su. 6 Za su kuwa fito su bi mu. Mu kuwa za mu janye su nesa da birnin, gama za su ce, ‘Suna gudunmu kamar dā.’ Haka fa, za mu gudu daga gare su. 7 Ku kuwa ku tashi daga kwanto, ku ci birnin, gama Ubangiji Allahnku zai ba da shi a hannunku. 8 A sa'ad da kuka ci birnin, ku sa wa birnin wuta yadda Ubangiji ya ce. Ku lura fa, da abin da na umarce ku.” 9 Sai Joshuwa ya sallame su, suka tafi inda za su yi kwanto. Suka yi fako tsakanin Betel da Ai, yamma da Ai, amma shi ya kwana tare da jama'a. 10 Joshuwa kuwa ya tashi da sassafe ya tattara mutanen, ya tafi tare da shugabannin Isra'ilawa, suka wuce gaba, suka bi da mutane zuwa Ai. 11 Dukan mayaƙan da suke tare da shi, suka tafi kusa da birnin, suka kafa sansaninsu arewacin Ai. Tsakaninsu da Ai akwai kwari. 12 Ya kuma zaɓi mutum wajen dubu biyar (5,000 ) ya sa su yi kwanto tsakanin Betel da Ai, yamma da birnin. 13 Mutanensu suka kafa sansaninsu arewa da birnin, sansani na 'yan kwanto kuwa yana yamma da birnin, amma Joshuwa ya kwana a kwarin. 14 A sa'ad da Sarkin Ai ya ga wannan, shi da mutanensa duka, wato mutanen birnin, suka gaggauta, suka tafi da sassafe zuwa gangaren wajen Araba don su gabza yaƙi da Isra'ilawa, amma bai san akwai 'yan kwanto a bayan birnin ba. 15 Sai Joshuwa da mutanensa duka suka nuna kamar an rinjaye su, suka yi ta gudu, suka nufi jeji. 16 Saboda haka aka kira dukan mutanen da suke cikin birnin, su fafare su. Da suka fafari Joshuwa, sai aka janye su nesa da birnin. 17 Ba namijin da ya ragu cikin Ai da bai fita ya fafari Isra'ilawa ba, suka bar birnin a buɗe, suka fafari Isra'ilawa. 18 Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Ka miƙa mashin da yake hannunka wajen Ai, gama zan ba da ita a hannunka.” Sai Joshuwa ya miƙa mashin da yake hannunsa wajen birnin. Nan da nan da ya ɗaga hannunsa 19 'yan kwanto suka tashi da sauri daga maɓoyansu, suka shiga birnin, suka ci shi, suka yi sauri, suka cuna wa birnin wuta. 20 Da mutanen Ai suka waiga, sai ga hayaƙin birnin ya murtuke zuwa sama, suka rasa ikon da za su gudu gaba ko baya, gama mutanen da suka gudu zuwa jeji, sun juyo kan masu fafararsu. 21 Sa'ad da Joshuwa da dukan Isra'ilawa suka ga 'yan kwanto sun ci birnin, da kuma hayaƙi ya murtuke bisa, suka juya kan mutanen Ai, suka ɗibge su. 22 Sauran Isra'ilawa kuwa suka fito daga cikin birnin suka fāɗa musu. Har ya zama suna tsakiyar Isra'ilawa gaba da baya. Isra'ilawa suka karkashe su, har ba wanda ya tsira ko ya tsere. 23 Amma suka kama Sarkin Ai da rai, suka kai shi wurin Joshuwa. 24 Sa'ad da Isra'ilawa suka gama karkashe mazaunan Ai duka a jeji inda suka fafare su, sai Isra'ilawa suka koma Ai, suka karkashe waɗanda suke cikinta. 25 A wannan rana aka ƙarasa mutanen Ai duka, mata da maza. Jimillarsu ta kai mutum dubu goma sha biyu (12,000 ). 26 Joshuwa bai janye hannunsa da riƙon mashin ba, sai da ya hallaka mazaunan Ai sarai. 27 Dabbobi da kayayyaki na birnin kaɗai Isra'ilawa suka kwashe ganima bisa ga faɗar Ubangiji zuwa ga Joshuwa. 28 Haka fa Joshuwa ya ƙone Ai, ya maishe ta tsibin kufai har abada. Tana nan haka har wa yau. 29 Ya rataye Sarkin Ai a bisa itace har maraice. Sa'ad da rana yake faɗuwa Joshuwa ya umarta su ɗauke gawarsa daga itacen, su jefa a ƙofar birnin, su tsiba duwatsu da yawa a kanta. Tsibin duwatsun yana nan har wa yau.

An Karanta Albarka da La'ana a Dutsen Ebal

30 Joshuwa ya gina wa Ubangiji Allah na Isra'ilawa bagade a bisa Dutsen Ebal. 31 Ya gina shi kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarci Isra'ilawa, gama haka aka rubuta cikin Attaura ta Musa, aka ce, “Bagaden da aka yi da duwatsun da ba a sassaƙa ba, waɗanda ba mutumin da ya taɓa sa musu guduma.” A bisansa suka miƙa hadayu ta ƙonawa ga Ubangiji, da hadayu na salama. 32 A nan, a idon Isra'ilawa, Joshuwa ya kafa dokokin Musa a bisa duwatsun. 33 Sai Isra'ilawa duka, baƙi da haifaffun gida, tare da dattawansu da shugabanninsu, da alƙalansu, suka tsaya daura da akwatin alkawari, suna fuskantar firistoci, wato Lawiyawa, waɗanda suka ɗauki akwatin alkawari na Ubangiji. Rabin mutanen suka tsaya a gaban Dutsen Gerizim, rabinsu kuma suka tsaya a gaban Dutsen Ebal kamar yadda Musa, bawan Ubangiji, ya riga ya umarta, cewa su sa wa jama'ar Isra'ila albarka. 34 Bayan haka ya karanta dukan zantuttukan shari'a, da na albarka da na la'ana, bisa ga dukan abin da aka rubuta cikin Attaura. 35 Babu wata kalmar da Musa ya umarta, da Joshuwa bai karanta a gaban dukan taron Isra'ilawa ba, tare da mata da ƙanana, da baƙin da suke zaune tare da su.

Joshuwa 9

Munafuncin Gibeyonawa

1 Sa'ad da dukan sarakunan da suke hayin Urdun, na cikin ƙasar tuddai, da na ƙasar kwari a gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon, wato sarakunan Hittiyawa, da na Amoriyawa, da na Kan'aniyawa, da na Ferizziyawa, da na Hiwiyawa, da na Yebusiyawa, suka ji wannan labari, 2 sai suka tattaru, suka haɗa kansu domin su yaƙi Joshuwa da Isra'ilawa. 3 Amma da mazaunan Gibeyon suka ji abin da Joshuwa ya yi wa Yariko da Ai, 4 sai suka yi musu hila, suka shirya guzuri, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu, sun kuwa sha ɗinki. 5 Suka kuma sa tsofaffin takalma waɗanda suka sha gyara, da tsofaffin tufafi. Dukan guzurinsu ya bushe, ya yi fumfuna. 6 Suka tafi wurin Joshuwa da Isra'ilawa a zango a can Gilgal, suka ce musu, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.” 7 Amma Isra'ilawa suka ce wa Hiwiyawa, “Watakila kuna zaune a tsakiyarmu ne, to, ƙaƙa za mu yi muku alkawari?” 8 Su kuwa suka ce wa Joshuwa, “Mu bayinka ne.” Joshuwa kuwa ya ce musu, “Su wane ne ku? Daga ina kuka zo kuma?” 9 Suka amsa masa suka ce, “Daga ƙasa mai nisa ƙwarai, bayinka suka zo saboda sunan Ubangiji Allahnka, gama mun ji labarinsa da dukan abin da ya yi a Masar, 10 da dukan abin da ya yi wa sarakunan nan biyu na Amoriyawa waɗanda suke a hayin Urdun, wato Sihon, Sarkin Heshbon, da Og, Sarkin Bashan, wanda yake a Ashtarot. 11 Dattawanmu da dukan mazaunan ƙasarmu suka ce mana mu ɗauki guzuri a hannunmu don tafiya, mu tafi taryarku, mu ce muku, ‘Mu bayinku ne, yanzu dai sai ku yi mana alkawari.’ 12 Wannan abinci, da ɗuminsa muka ɗauko shi daga gidajenmu a ranar da muka fito zuwa gare ku, amma ga shi, yanzu ya bushe ya yi fumfuna. 13 Waɗannan salkunan ruwan inabi kuma da muka cika sababbi ne, amma ga shi, sun kyakkece, waɗannan tufafinmu kuma da takalmanmu sun tsufa saboda tsawon hanya!” 14 Sai Isra'ilawa suka ɗiba daga cikin guzurin Hiwiyawa, amma ba su nemi shawara wurin Ubangiji ba. 15 Joshuwa kuwa ya yi amana da su, ya yi musu alkawari zai bar su da rai. Shugabannin jama'a kuma suka rantse musu. 16 Amma a rana ta uku bayan da suka yi alkawari da su, suka ji cewa, su maƙwabtansu ne, suna zaune a cikinsu. 17 Sai Isra'ilawa suka kama hanyarsu a rana ta uku suka isa biranen mutanen, wato Gibeyon, da Kefira, da Biyerot, da Kiriyat-yeyarim. 18 Amma Isra'ilawa ba su kashe su ba, domin shugabannin jama'a sun rantse musu da sunan Ubangiji Allah na Isra'ila. Dukan jama'a kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin. 19 Amma shugabanni suka ce wa dukan jama'a, “Mun riga mun rantse musu da sunan Ubangiji Allah na Isra'ila, don haka yanzu ba shi yiwuwa mu taɓa su. 20 Abin da za mu yi musu ke nan, a bar su da rai saboda rantsuwar da muka rantse musu don kada mu jawo wa kanmu fushin Ubangiji!” 21 Suka ƙara da cewa, “A bar su da rai domin su zama masu sarar mana itace, da masu ɗebo mana ruwa.” 22 Joshuwa kuwa ya kirawo su, ya ce musu, “Me ya sa kuka ruɗe mu da cewa, ‘Muna nesa da ku ƙwarai,’ ga shi kuwa, a tsakiyarmu kuke zaune? 23 Yanzu fa ku la'anannu ne, a cikinku ba za a rasa bayin da za su zama masu saro itace da masu ɗebo ruwa domin masujadar Allahnmu ba.” 24 Sai suka amsa wa Joshuwa, suka ce, “Domin bayinka sun ji labari Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa ya ba ku ƙasar duka, ku hallaka dukan mazaunan ƙasar a gabanku, don haka muka ji tsoronku ƙwarai saboda rayukanmu, shi ya sa muka yi haka. 25 Yanzu dai muna a hannunka, ka yi yadda ka ga ya yi maka kyau.” 26 Haka kuwa ya yi musu, ya cece su daga hannun Isra'ilawa, har ba su kashe su ba. 27 Amma Joshuwa ya sa su su zama masu saro itace da masu ɗebo ruwa domin jama'a da bagaden Ubangiji. Zai zama aikinsu na yau da kullum a wurin da Ubangiji zai zaɓa.

Joshuwa 10

An Ci Amoriyawa da Yaƙi

1 Da Adonizedek, Sarkin Urushalima, ya ji yadda Joshuwa ya ci Ai, har ya hallakar da ita sarai kamar yadda ya yi wa Yariko da sarkinta, da kuma yadda mazaunan Gibeyon suka yi amana da Isra'ilawa, har suna zama cikinsu. 2 Sai ya tsorata ƙwarai, gama Gibeyon babban birni ce kamar ɗaya daga cikin alkaryai, har ma ta fi Ai girma, mazajenta duka kuwa ƙarfafa ne. 3 Adonizedek Sarkin Urushalima, ya aika zuwa ga Hoham Sarkin Hebron, da Firam Sarkin Yarmut, da Yafiya Sarkin Lakish, da Debir Sarkin Eglon, ya ce, 4 “Ku zo, ku taimake ni, mu yaƙi Gibeyon, gama ta yi amana da Joshuwa da Isra'ilawa.” 5 Sarakunan nan biyar na Amoriyawa, wato Sarkin Urushalima, da Sarkin Hebron, da Sarkin Yarmut, da Sarkin Lakish, da Sarkin Eglon, suka tattaru da dukan rundunansu, suka haura, suka kafa wa Gibeyon sansani don su yaƙe ta. 6 Gibeyonawa dai suka aika zuwa wurin Joshuwa a zango cikin Gilgal cewa, “Kada ka yar da bayinka. Ka zo wurinmu da sauri, ka cece mu, ka taimake mu, gama dukan sarakunan Amoriyawa da suke zaune a ƙasar tuddai sun tattaru a kanmu.” 7 Sai Joshuwa ya tashi daga Gilgal da dukan mayaƙa, da dukan jarumawa tare da shi. 8 Ubangiji kuwa ya ce wa Joshuwa, “Kada ka ji tsoronsu gama na riga na ba da su a hannunka, ba mutuminsu da zai iya tsayawa a gabanka.” 9 Sai Joshuwa ya tafi ya auka musu ba labari, gama daga Gilgal ya bi dare zuwa can. 10 Ubangiji kuwa ya sa suka gigice a gaban Isra'ilawa. Isra'ilawa suka kashe su da yawa a Gibeyon, suka runtume su ta hanyar haurawa zuwa Ber-horon. Suka yi ta karkashe su har zuwa Azeka da Makkeda. 11 Sa'ad da suke gudun Isra'ilawa suna a gangarar hawan Bet-horon, sai Ubangiji ya jefe su da manyan duwatsu daga sama, har zuwa Azeka, suka mutu. Waɗanda suka mutu ta ƙanƙarar duwatsu sun fi waɗanda Isra'ilawa suka kashe da takobi. 12 Sa'an nan Joshuwa ya yi magana da Ubangiji a gaban Isra'ilawa a ranar da Ubangiji ya ba da Amoriyawa gare su, ya ce, “Ke rana, ki tsaya a Gibeyon, Kai kuma wata, ka tsaya a kan kwarin Ayalon.” 13 Sai rana ta tsaya cik, wata kuma ya tsaya, Har al'ummar ta ɗauki fansa a kan abokan gābansu. Ai, wannan a rubuce yake a littafin Yashar. Rana dai ta tsaya a tsaka, ta yi jinkirin faɗuwa da misalin yini guda. 14 Ba a taɓa yin yini kamar wannan ba, ko kafin wannan yini, ko bayansa kuma, da Ubangiji ya saurari muryar mutum. Gama Ubangiji ya yi yaƙi domin Isra'ilawa. 15 Sa'an nan Joshuwa ya koma zango a Gilgal tare da dukan Isra'ilawa. 16 Waɗannan sarakuna biyar kuma suka gudu, suka ɓuya a cikin kogo a Makkeda. 17 Aka faɗa wa Joshuwa cewa, “An sami sarakunan nan biyar, sun ɓuya a kogo a Makkeda.” 18 Sai Joshuwa ya ce, “Ku mirgina manyan duwatsu, ku rufe bakin kogon, sa'an nan ku sa mutane su yi tsaronsu. 19 Amma kada ku tsaya a can, sai ku runtumi abokan gābanku, ku bugi na bayansu, kada ku bar su su shiga biranensu, gama Ubangiji Allahnku ya riga ya ba da su a Hannunku.” 20 Joshuwa da jama'ar Isra'ila suka karkashe su da yawa ƙwarai, sauransu kuma da suka ragu suka shiga birane masu garu. 21 Sa'an nan dukan mutane suka koma wurin Joshuwa a sansani a Makkeda lafiya. Ba kuma mutumin da ya tsokani Isra'ilawa. 22 Sa'an nan Joshuwa ya ce, “Ku buɗe bakin kogon, ku kawo mini waɗannan sarakuna biyar da suke a kogon.” 23 Suka yi hakanan, suka kawo masa sarakunan nan biyar daga cikin kogon, wato Sarkin Urushalima, da Sarkin Hebron, da Sarkin Yarmut, da Sarkin Lakish, da Sarkin Eglon. 24 Da suka kawo sarakunan a wurin Joshuwa, sai Joshuwa ya kirawo dukan Isra'ilawa, sa'an nan ya ce wa shugabannin mayaƙa, waɗanda suka tafi tare da shi, “Ku matso kusa, ku taka wuyan sarakunan nan.” Suka kuwa zo kusa, suka taka wuyansu. 25 Sai Joshuwa ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ko kuwa ku razana, amma ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, gama haka Ubangiji zai yi da dukan abokan gābanku waɗanda za ku yi yaƙi da su.” 26 Sa'an nan Joshuwa ya buga su, ya kashe su, ya kuma rataye kowane ɗayansu a bisa itace. Suka yini a rataye har maraice. 27 Amma sa'ad da rana take faɗuwa, Joshuwa ya umarta, aka saukar da gawawwakinsu daga bisa itatuwan, aka jefa su cikin kogon inda suka ɓuya. Sa'an nan suka rufe bakin kogon da manyan duwatsu. Har wa yau suna nan. 28 A wannan rana kuwa Joshuwa ya ci Makkeda da Yaƙi, ya kashe mutanenta da sarkinta da takobi, har ba wanda ya ragu. Ya yi wa Sarkin Makkeda kamar yadda ya yi wa Sarkin Yariko. 29 Joshuwa ya zarce, da shi da dukan Isra'ilawa zuwa Libna, suka yi yaƙi da Libna. 30 Ubangiji ya bashe ta da sarkinta a hannun Isra'ilawa, suka kuwa buge ta da takobi, da kowane mutum da yake cikinta, ba su rage kowa cikinta ba. Suka yi wa sarkinta kamar yadda suka yi wa Sarkin Yariko. 31 Joshuwa kuma ya zarce daga Libna, da shi da Isra'ilawa duka, zuwa Lakish, suka kewaye ta da yaƙi, suka auka mata. 32 Ubangiji ya ba da Lakish a hannun Isra'ilawa suka cinye ta da yaƙi cikin kwana biyu. Suka bugi kowane mutum da yake cikinta da takobi kamar yadda suka yi wa Libna. 33 Horam, Sarkin Gezer kuwa, ya kawo wa Lakish gudunmawa, Joshuwa kuwa ya buge shi tare da mutanensa, har ba wanda ya ragu. 34 Joshuwa kuma ya zarce tare da dukan Isra'ilawa daga Lakish zuwa Eglon, suka kewaye ta da yaƙi, suka auka mata. 35 A ran nan suka cinye ta, suka buge ta da kowane mutum da yake cikinta da takobi. Ya hallakar da su a wannan rana kamar yadda ya yi wa Lakish. 36 Joshuwa kuma ya haura tare da dukan Isra'ilawa daga Eglon zuwa Hebron, suka auka mata. 37 Suka cinye ta, suka buge ta, da sarkinta, da garuruwanta, da kowane mutum da yake cikinta da takobi, har ba wanda ya ragu kamar yadda ya yi wa Eglon. Ya hallakar da ita sarai duk da kowane mutum da yake cikinta. 38 Sai Joshuwa ya juya tare da dukan Isra'ilawa zuwa Debir, ya auka mata. 39 Ya cinye ta da yaƙi, da sarkinta, da garuruwanta. Ya buge ta da kowane mutum da yake cikinta da takobi, har ba wanda ya ragu. Kamar yadda ya yi wa Hebron, da Libna da sarkinta, haka kuma ya yi wa Debir da sarkinta. 40 Hakanan kuwa Joshuwa ya cinye dukan ƙasar tuddai, da Negeb, da filayen kwaruruka, da gangare, da sarakunansu duka, ba wanda ya ragu, amma ya hallaka su duka kamar yadda Ubangiji, Allah na Isra'ila ya umarta. 41 Joshuwa kuma ya cinye su da yaƙi tun daga Kadesh-barneya har zuwa Gaza, da dukan ƙasar Goshen har zuwa Gibeyon. 42 Joshuwa kuwa ya cinye sarakunan nan duka da ƙasashensu gaba ɗaya, gama Ubangiji Allah na Isra'ila ya yi yaƙi domin Isra'ilawa. 43 Sa'an nan Joshuwa ya komo tare da dukan Isra'ilawa zuwa zango a Gilgal.

Joshuwa 11

An Ci Yabin da Magoya Bayansa

1 Sa'ad da Yabin Sarkin Hazor ya ji labari, ya aika wa Yobab, Sarkin Madon, da Sarkin Shimron, da Sarkin Akshaf, 2 da sarakunan da suke arewacin ƙasar tuddai, da cikin Araba a kudancin Kinneret, da cikin filayen kwari, da cikin Dor a yamma. 3 Ya kuma aika zuwa ga Kan'aniyawan da suke gabas da yamma, da Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa da suke ƙasar tuddai, da Hiwiyawa da suke zaune a gindin Dutsen Harmon a ƙasar Mizfa. 4 Sai suka fita tare da dukan mayaƙansu, babbar runduna mai yawa kamar yashi a bakin teku, da dawakai, da karusai da yawa ƙwarai. 5 Da sarakunan nan duka suka haɗa ƙarfinsu, sai suka je suka kafa sansaninsu a wuri ɗaya a bakin ruwayen Merom domin su yi yaƙi da Isra'ilawa. 6 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Joshuwa, “Kada ka ji tsoronsu, gama gobe war haka zan ba da su ga Isra'ilawa, su karkashe su duka. Za ku daddatse agaran dawakansu, ku kuma ƙone karusansu.” 7 Sai Joshuwa, tare da dukan mayaƙansa, suka je suka mame su, suka auka musu a bakin ruwayen Merom. 8 Ubangiji kuwa ya ba da su a hannun Isra'ilawa, suka kuwa ɗibge su, suka runtume su, har zuwa Sidon Babba, da Misrefot-mayim, har zuwa gabashin kwarin Mizfa. Suka karkashe su ƙaƙaf. 9 Joshuwa kuwa ya yi musu kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, ya daddatse agaran dawakansu, ya kuma ƙone karusansu. 10 A wannan lokaci Joshuwa ya koma da baya ya ci Hazor, ya kashe sarkinta da takobi, gama a lokacin Hazor ita ce masarautar mulkokin nan. 11 Suka kashe dukan waɗanda suke cikinta da takobi, suka hallakar da su ƙaƙaf, ba wanda ya ragu. Joshuwa kuwa ya ƙone Hazor. 12 Joshuwa kuma ya ci dukan biranen sarakunan nan, da dukan sarakunansu. Ya kashe su da takobi, ya hallakar da su ƙaƙaf kamar yadda Musa bawan Ubangiji ya umarta. 13 Amma mutanen Isra'ila ba su ƙone ko ɗaya daga cikin biranen da suke bisa tuddai ba, sai Hazor kaɗai Joshuwa ya ƙone. 14 Isra'ilawa kuma suka kwashe ganima ta abubuwa masu tamani na biranen game da shanu, amma suka kashe kowane mutum da takobi, har suka hallakar da su, ba su bar kowa ba. 15 Sun yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa bawansa, haka kuma Musa ya umarci Joshuwa, haka kuwa Joshuwa ya yi. Ba abin da bai aikata ba cikin dukan abin da Ubangiji ya umarci Musa.

Joshuwa ya Cinye Ƙasar Duka

16 Ta haka kuwa Joshuwa ya ci ƙasar nan duka, da ƙasar tuddai, da Negeb duka, da dukan ƙasar Goshen, da filayen kwari, da Araba, da ƙasar tuddai ta Isra'ila da filayen kwarinta, 17 tun daga Dutsen Halak wanda ya miƙa zuwa wajen Seyir, har zuwa Ba'al-gad a kwarin Lebanon, a gindin Dutsen Harmon. Ya kama sarakunan wuraren nan, ya buge su ya kashe su. 18 Joshuwa ya daɗe yana yaƙi da su. 19 Ba wani birnin da ya yi amana da Isra'ilawa, sai dai Hiwiyawa da suke zaune a Gibeyon. Saura duka kuwa, an ci su da yaƙi. 20 Gama Ubangiji ne ya taurara zukatansu har da za su tasar wa Isra'ilawa da yaƙi don a hallaka su, a shafe su ba tausayi, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 21 A wannan lokaci kuwa Joshuwa ya tafi ya hallaka Anakawa, wato gwarzayen nan da suke ƙasar tuddai, da Hebron, da Debir, da Anab, da dukan ƙasar tuddai ta Yahuza, da dukan ƙasar tuddai ta Isra'ilawa. Joshuwa ya hallaka su sarai duk da biranensu. 22 Babu wani gwarzon da ya ragu a ƙasar mutanen Isra'ila, sai a Gaza, da Gat, da Ashdod kaɗai ne waɗansunsu suka ragu. 23 Hakanan kuwa Joshuwa ya ci dukan ƙasar yadda Ubangiji ya faɗa wa Musa. Ya kuwa ba da ƙasar gādo ga Isra'ilawa kabila kabila. Ƙasar kuwa ta shaƙata da yaƙi.

Joshuwa 12

Sarakunan da Musa ya Ci da Yaƙi

1 Waɗannan su ne sarakunan ƙasar, waɗanda Isra'ilawa suka cinye da yaƙi, suka mallaki ƙasarsu a hayin Kogin Urdun daga yamma, tun daga kwarin Arnon har zuwa Dutsen Harmon da dukan Araba a wajen gabas, 2 Sihon, Sarkin Amoriyawa wanda yake zaune a Heshbon, wanda yake mulki tun daga Arower wadda take iyakar kwarin Arnon, daga tsakiyar kwarin har zuwa Kogin Yabbok a iyakar Ammonawa, 3 daga kuma Araba zuwa gabashin Tekun Kinneret da zuwa Tekun Araga, wato Tekun Gishiri, a wajen gabas ta hanyar Ber-yeshimot, da wajen kudu zuwa gangaren gindin Dutsen Fisga, 4 da kuma Og, Sarkin Bashan, ɗaya daga cikin sauran Refayawa, wato gwarzayen nan waɗanda suka zauna a Ashtarot da Edirai. 5 Ya mallaki Dutsen Harmon, da Salka, da dukan Bashan, har zuwa iyakar Geshuriyawa, da Ma'akatiyawa, da rabin Gileyad, zuwa kan iyakar ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon. 6 Sai Musa, bawan Ubangiji, da Isra'ilawa suka ci sarakunan nan da yaƙi, sa'an nan ya ba da ƙasarsu ga Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa.

Sarakunan da Joshuwa ya Ci da Yaƙi

7 Waɗannan su ne sarakunan ƙasar, waɗanda Joshuwa da Isra'ilawa suka ci da yaƙi a yammacin Kogin Urdun tun daga Ba'al-gad a kwarin Lebanon zuwa Dutsen Halak wanda ya miƙa zuwa Seyir. Joshuwa ya ba Isra'ilawa ƙasar gādo bisa ga yadda aka karkasa musu, 8 da ƙasar tuddai, da filayen kwaruruka, da kwarin Araba, da gangaren tuddai, da jejin, da Negeb, wato su Hittiyawa, da Amoriyawa, da Kan'aniyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. 9 Sunayen sarakunan su ne, Sarkin Yariko, da Sarkin Ai, da yake kusa da Betel, 10 da Sarkin Urushalima, da Sarkin Hebron, 11 da Sarkin Yarmut, da Sarkin Lakish, 12 da Sarkin Eglon, da Sarkin Gezer, 13 da Sarkin Debir, da Sarkin Geder, 14 da Sarkin Horma, da Sarkin Arad, 15 da Sarkin Libna, da Sarkin Adullam, 16 da Sarkin Makkeda, da Sarkin Betel, 17 da Sarkin Taffuwa, da Sarkin Hefer, 18 da Sarkin Afek, da Sarkin Lasharon, 19 da Sarkin Madon, da Sarkin Hazor, 20 da Sarkin Shimron-meron, da Sarkin Akshaf, 21 da Sarkin Ta'anak, da Sarkin Magiddo, 22 da Sarkin Kedesh, da Sarkin Yakneyam a Karmel, 23 da Sarkin Dor a bakin teku, da Sarkin Goyim na Gilgal, 24 da Sarkin Tirza. Sarakuna talatin da ɗaya ke nan.

Joshuwa 13

Ƙasar da ta Ragu da za a Mallaka

1 Yanzu Joshuwa ya tsufa ƙwarai, sai Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi, ƙasar da za ku mallaka ta ragu da yawa. 2 Wannan ita ce ƙasar da ta ragu, dukan ƙasar Filistiyawa, da ta Geshuriyawa, 3 daga Shihor da yake gabas da Masar zuwa iyakar Ekron a wajen arewa. Wannan ƙasa ta Kan'aniyawa ce. Akwai sarakuna biyar na Filistiyawa da suke a Gaza, da Ashdod, da Ashkelon, da Gat, da Ekron, da ƙasar Awwiyawa, 4 da dukan ƙasar Kan'aniyawa a wajen kudu, da Meyara ta Sidoniyawa, zuwa Afek, har zuwa iyakar Amoriyawa, 5 da ƙasar Gebaliyawa, da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba'al-gad a gindin Dutsen Harmon zuwa iyakar Hamat, 6 da dukan mazaunan ƙasar tuddai, tun daga Lebanon zuwa Misrefot-mayim har da dukan Sidoniyawa. Ni da kaina zan kore su a gaban jama'ar Isra'ila. Kai kuwa za ka raba wa Isra'ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka. 7 Yanzu fa sai ka raba wa kabilai tara da rabi ɗin nan ƙasar ta zama gādonsu.”

Yankin Ƙasar da aka ba Manassa da Ra'ubainu da Gad

8 Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa, sun karɓi nasu gādo wanda Musa ya ba su a hayin Urdun wajen gabas. Abin da Musa, bawan Ubangiji, ya ba su ke nan, 9 daga Arower wadda take a gefen kwarin Arnon da birnin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu ta Medeba zuwa Dibon, 10 da dukan biranen Sihon, Sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon, har zuwa iyakar Amoriyawa, 11 da Gileyad, da yankin ƙasar Geshuriyawa, da Ma'akatiyawa, da dukan Dutsen Harmon, da dukan Bashan, zuwa Salka, 12 da dukan mulkin Og a Bashan, wanda ya yi sarautar Ashtarot da Edirai (Og Kaɗai ne aka bari daga cikin Refayawa). Waɗannan su ne Musa ya ci da yaƙi, ya kore su. 13 Duk da haka jama'ar Isra'ila ba su kori Geshuriyawa, da Ma'akatiyawa ba, amma suka yi zamansu tare da Isra'ilawa har wa yau. 14 Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa na Ubangiji, Allah na Isra'ila, su ne gādonta, kamar yadda Ubangiji ya faɗa masa. 15 Musa ya riga ya ba Ra'ubainawa nasu gādo bisa ga iyalansu. 16 Nasu yankin ƙasar ya miƙa daga Arower wadda take a gefen kwarin Arnon, da birnin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba, 17 da Heshbon, da dukan biranenta da suke kan tudu, wato Dibon, da Bamot-ba'al, da Ba'al-mayon, 18 da Yahaza, da Kedemot, da Mefayat, 19 da Kiriyatayim, da Sibma, da Zeret-shahar da yake bisa tudun da yake cikin kwarin, 20 da Bet-feyor, da gangaren Fisga, da Betyeshimot. 21 Waɗannan duka su ne birane na kan tudu, da dukan masarautar Sihon, Sarkin Amoriyawa wanda ya sarauci Heshbon. Musa ya ci shi da yaƙi da shugabannin Madayana, wato Ewi, da Rekem, da Zur, da Hur, da Reba, wato sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar. 22 Jama'ar Isra'ila kuma suka kashe Bal'amu matsubbaci, ɗan Beyor, da takobi. 23 Urdun kuwa ya zama iyakar yankin ƙasar jama'ar Ra'ubainu. Wannan shi ne gādon Ra'ubainawa bisa ga iyalansu, da biranensu da ƙauyukansu. 24 Musa kuma ya ba Gadawa gādo bisa ga iyalansu. 25 Yankin ƙasarsu shi ne Yazar, da dukan biranen Gileyad da rabin ƙasar Ammonawa zuwa Arower wadda take gabas da Rabba, 26 daga Heshbon zuwa Ramat-mizfe, da Betonim, daga Mahanayim zuwa karkarar Debir, 27 da a kwarin Ber-aram, da Betnimra, da Sukkot, da Zafon, da kuma ragowar mulkin Sihon, Sarkin Heshbon. Kogin Urdun ne iyakar yankin ƙasarsu har zuwa wutsiyar Tekun Kinneret, a gabashin hayin Urdun. 28 Wannan shi ne yankin ƙasar, haɗe da garuruwa, da ƙauyuka, da aka ba mutanen kabilar Gad bisa ga iyalansu. 29 Musa kuma ya ba rabin jama'ar Manassa rabon gādo bisa ga iyalansu. 30 Yankin ƙasarsu ya bi daga Mahanayim, ya haɗa dukan Bashan, da dukan mulkin Og, Sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan, 31 da rabin Gileyad, da Ashtarot, da Edirai, wato garuruwan sarki Og a Bashan. Mutanen Makir ne, ɗan Manassa, aka ba su wannan bisa ga iyalansu. 32 Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun daura da Yariko. 33 Amma Musa bai ba Lawiyawa gādon yankin ƙasa ba. Ya faɗa musu Ubangiji Allah na Isra'ila, shi ne rabon gādonsu.

Joshuwa 14

An Rarraba Ƙasar kan'ana ta Hanyar Kuri'a

1 Waɗannan su ne karkasuwar gādon da Isra'ilawa suka karɓa a ƙasar Kan'ana, wanda Ele'azara, firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin iyalan kabilan Isra'ila suka ba su. 2 Kabilar nan tara da rabi sun karɓi nasu rabon gādo ta hanyar jefa kuri'a, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa. 3 Gama Musa ya riga ya ba kabilar nan biyu da rabi nasu gādo a wancan hayin Kogin Urdun wajen gabas, amma bai ba Lawiyawa rabon gādo ba. 4 Jama'ar Yusufu kuwa kabila biyu ce, wato Manassa da Ifraimu. Ba a kuma ba Lawiyawa rabon gādo a ƙasar ba, sai dai an ba su biranen da za su zauna, da filayen da za su yi kiwon garkensu. 5 Jama'ar Isra'ila fa suka yi kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa, suka rarraba ƙasar ta hanyar kuri'a.

An Ba Kalibu Hebron

6 Mutanen Yahuza suka je wurin Joshuwa a Gilgal, sa'an nan Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, ya ce masa, “Ka dai san maganar da Ubangiji ya yi wa Musa, mutumin Allah, a Kadesh-barneya a kaina. 7 Ina da shekara arba'in sa'ad da Musa bawan Ubangiji ya aike ni daga Kadesh-barneya don in leƙi asirin ƙasar. Na kuma kawo masa ainihin rahoton yadda yake a zuciyata. 8 Amma 'yan'uwana da muka tafi tare, sun karya zukatan jama'ar, amma ni na bi Ubangiji Allahna da aminci. 9 Musa kuwa ya rantse a wannan rana ya ce, ‘Hakika duk inda ƙafafunka suka taka a ƙasar nan zai zama gādonka, kai da 'ya'yanka har abada, domin ka bi Ubangiji Allahnka sosai!’ 10 Ga shi kuwa, Ubangiji ya kiyaye ni har wa yau, kamar yadda ya faɗa, shekara arba'in da biyar ke nan, tun lokacin da Ubangiji ya faɗa wa Musa wannan magana, a lokacin da Isra'ilawa suke yawo a jeji. Ga shi yau ni mai shekara tamanin da biyar ne. 11 Ga shi kuwa, har wa yau ina da ƙarfi kamar ran da Musa ya aike ni. Kamar yadda ƙarfina yake a dā, haka yake a yanzu domin yaƙi, da kuma kai da kawowa. 12 Saboda haka sai ka ba ni ƙasar tuddai da Ubangiji ya ambata a ranar nan, gama a wannan rana ka ji yadda gwarzaye suke a can da manyan birane masu garu, mai yiwuwa ne Ubangiji zai kasance tare da ni, in kore su kamar yadda Ubangiji ya faɗa.” 13 Joshuwa ya sa wa Kalibu, ɗan Yefunne, albarka. Ya ba shi Hebron ta zama gādonsa. 14 Domin haka Hebron ta zama gādon Kalibu, ɗan Yefunne Bakenizze, har wa yau, domin ya bi Ubangiji Allah na Isra'ila sosai. 15 A dā sunan Hebron Kiriyat-arba ne. Arba kuwa babban mutum ne cikin gwarzayen. Ƙasar kuwa ta shaƙata da yaƙi.

Joshuwa 15

Yankin Ƙasar da aka Ba Yahuza

1 Rabon da aka ba jama'ar Yahuza bisa ga iyalansu ya yi kudu, a iyakar Edom zuwa jejin Zin, can kudu nesa. 2 Iyakarsu wajen kudu ta miƙa tun daga ƙarshen Tekun Gishiri, daga wajen gaɓar da ta fuskanci kudu. 3 Ta milla kudanci hawan Akrabbim, ta zarce zuwa Zin, ta haura kudu da Kadesh-barneya, ta wajen Hesruna har zuwa Addar. Sai ta karkata zuwa Karka. 4 Ta zarce zuwa Azemon, ta bi ta rafin Masar zuwa inda ya gangara a teku. Wannan ita ce iyakar mutanen Yahuza wajen kudu. 5 Iyakarsu wajen gabas ta kama daga Tekun Gishiri zuwa bakin Urdun. Wajen arewa kuwa ta miƙa daga bakin teku a inda Kogin Urdun ya gangara a tekun. 6 Iyakar ta bi zuwa Ber-hogla, ta zarce zuwa arewa da Bet-araba, ta haura zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ra'ubainu. 7 Daga kwarin Akor ta wuce zuwa Debir ta yi wajen arewa, sa'an nan ta juya zuwa Gilgal wadda take daura da hawan Adummim wanda yake kudancin gefen kwarin. Sai ta zarce zuwa ruwan En-shemesh, ta ƙare a En-rogel. 8 Daga nan iyakar ta bi ta kwarin ɗan Hinnom a wajen kudancin kafaɗar Yebus, wato Urushalima. Ta kuwa bi ta dutsen da yake shimfiɗe daura da kwarin Hinnom wajen yamma, a arewacin ƙarshen kwarin Refayawa. 9 Ta kuma milla daga kan dutsen zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa, daga can zuwa biranen Dutsen Efron. Daga can kuma ta karkata zuwa Ba'ala, wato Kiriyat-yeyarim. 10 Ta kuma kewaye kudancin Ba'ala zuwa Dutsen Seyir. Ta zarce zuwa arewacin kafaɗar Dutsen Yeyarim, wato Kesalon. Daga nan ta gangara zuwa Bet-shemesh, ta kuma wuce zuwa Timna. 11 Iyakar kuma ta biya wajen kafaɗar tudun, arewa da Ekron, sa'an nan ta karkata zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba'ala, ta tafi zuwa Yabneyel, sa'an nan ta gangara a teku. 12 Bakin Bahar Rum, ita ce iyaka a wajen yamma. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama'ar Yahuza bisa ga iyalansu.

Kalibu ya Ci Hebron da Debir da Yaƙi

13 Kamar yadda Ubangiji ya umarci Joshuwa, ya ba Kalibu, ɗan Yefunne, rabonsa a tsakiyar jama'ar Yahuza. Rabon da aka ba shi, shi ne Kiriyatarba, wato Hebron. Arba shi ne uban Anak. 14 Daga can sai Kalibu ya kori 'ya'yan Anak, maza, su uku, da Sheshai, da Ahiman, da Talmai, zuriyar Anak. 15 Daga can kuma ya tafi ya fāɗa wa mazaunan Debir, dā sunan Debir Kiriyat-sefer ne. 16 Kalibu ya ce, “Duk wanda ya bugi Kiriyat-sefer, har ya ci ta, zan ba shi 'yata Aksa aure.” 17 Otniyel kuwa, ɗan Kenaz, ɗan'uwan Kalibu, ya ci Kiriyat-sefer. Kalibu kuwa ya ba shi Aksa 'yarsa aure. 18 Da ta zo wurinsa, ya zuga ta ta roƙi mahaifinta saura. Da ta sauka daga kan jakinta, sai Kalibu ya ce mata, “Me kike so?” 19 Ta kuwa ce masa, “Ka yi mini alheri, da yake ka tura ni a ƙasar Negeb, ina roƙonka ka ba ni maɓuɓɓugar ruwa.” Kalibu kuwa ya ba ta maɓuɓɓugar tuddai da na kwari.

Biranen Kabilar Yahuza

20 Wannan shi ne gādon jama'ar Yahuza bisa ga iyalansu. 21 Biranen jama'ar Yahuza da suke can kudu sosai wajen iyakar Edom, su ne Kabzeyel, da Eder, da Yagur, 22 da Kina, da Dimona, da Adada, 23 da Kedesh, da Hazor, da Yitnan, 24 da Zif, da Telem, da Beyalot, 25 da Hazor-hadatta, da Kiriyot-hesruna, wato Hazor, 26 da Amam, da Shema, da Molada, 27 da Hazar-gadda, da Heshmon, da Bet-felet, 28 da Hazar-shuwal, da Biyer-sheba, da Biziyotaya, 29 da Ba'ala, da Abarim, da Ezem, 30 da Eltola, da Kesil, da Horma, 31 da Ziklag, da Madmanna, da Sansanna, 32 da Labayot, da Shilhim, da Ayin, da Rimmon. Birane ashirin da tara ke nan da ƙauyukansu. 33 Na filayen kwarin kuwa, su ne Eshtawol, da Zora, da Ashna, 34 da Zanowa, da En-ganim, da Taffuwa, da Enayim, 35 da Yarmut, da Adullam, da Soko, da Azeka, 36 da Shayarim, da Aditayim, da Gedera, da Gederotayim. Birane goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. 37 Da kuma Zenan, da Hadasha, da Migdal-gad, 38 da Dileyan, da Mizfa, da Yokteyel, 39 da Lakish, da Bozkat, da Eglon, 40 da Kabbon, da Lahmam, da Kitlish, 41 da Gederot, da Bet-dagon, da Na'ama, da Makkeda, birane goma sha shida ke nan da ƙauyukansu. 42 Da kuma Libna, da Eter, da Ashan, 43 da Yifta, da Ashna, da Nezib, 44 da Kaila, da Akzib, da Maresha, birane tara ke nan da ƙauyukansu. 45 Da kuma Ekron da garuruwanta da ƙauyukanta. 46 Daga Ekron zuwa tekun, da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod. 47 Ashdod da garuruwanta da ƙauyukanta, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta zuwa rafin Masar da Bahar Rum da bakinta. 48 Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne Shamir, da Yattir, da Soko, 49 da Danna, da Kiriyat-sanna, wato Debir, 50 da Anab, da Eshtemowa, da Anim, 51 da Goshen, da Holon, da Gilo. Birane goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu. 52 Da kuma Arab, da Duma, da Eshan, 53 da Yanim, da Bet-taffuwa, da Afeka, 54 da Hunta, da Kiriyat-arba, wato Hebron, da Ziyor, birane tara ke nan da ƙauyukansu. 55 Da kuma Mawon, da Karmel, da Zif, da Yutta, 56 da Yezreyel, da Yokdeyam, da Zanowa, 57 da Kayin, da Gebeya, da Timna, birane goma ke nan da ƙauyukansu. 58 Halhul, da Bet-zur, da Gedor, 59 da Ma'arat, da Bet-anot da Eltekon, birane shida ke nan da ƙauyukansu. 60 Da kuma Kiriyat-ba'al, wato Kiriyat-yeyarim, da Rabba, birane biyu ke nan da ƙauyukansu. 61 Biranen da suke a jeji kuwa su ne Bet-araba, da Middin, da Sekaka, 62 da Nibshan, da Birnin Gishiri, da En-gedi, birane shida ke nan da ƙauyukansu. 63 Amma jama'ar Yahuza ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zaune a Urushalima ba, don haka Yebusiyawa suka yi zamansu da jama'ar Yahuza cikin Urushalima har wa yau.

Joshuwa 16

Yankin Ƙasar da aka Ba Ifraimu da Manassa

1 Rabon zuriyar Yusufu ya milla tun daga Urdun zuwa wajen Yariko, gabas da ruwan Yariko zuwa jejin. Ya haura daga Yariko zuwa ƙasar tuddai zuwa Betel. 2 Daga Betel ya miƙa zuwa Luz, sa'an nan ya zarce zuwa Atarot, karkarar Arkiyawa. 3 Sai ya gangara yamma zuwa karkarar Yafletiyawa har zuwa karkarar Bet-horon wadda take cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, sa'an nan ya gangara a teku. 4 A nan ne jama'ar Yusufu, wato Manassa da Ifraimu, suka sami nasu gādo. 5 Karkarar jama'ar Ifraimu, bisa ga iyalansu, ita ce iyakar gādonsu a wajen gabas, wato ita ce Atarot-addar har zuwa Bet-horon wadda take kan tudu. 6 Daga can iyakar ta miƙa zuwa teku ta bar Mikmetat a wajen arewa. A wajen gabas kuwa iyakar ta karkata zuwa Ta'anat-Shilo, daga can sai ta zarce gaba a wajen gabas zuwa Yanowa. 7 Daga Yanowa sai ta gangara zuwa Atarot da Nayaran, ta kuma gegi Yariko, sa'an nan ta gangara a Urdun. 8 Daga Taffuwa, sai iyakar ta yi yamma zuwa rafin Kana, sa'an nan ta gangara a teku. Wannan shi ne gādon Ifraimawa bisa ga iyalansu, 9 tare da garuruwan da ƙauyukan da aka keɓe wa Ifraimawa daga cikin gādon jama'ar Manassa. 10 Amma ba su kori Kan'aniyawa da suke zaune a Gezer ba, don haka Kan'aniyawa suka zauna tare da Ifraimawa har wa yau, amma Kan'aniyawa suka zama bayi masu yin aikin dole.

Joshuwa 17

1 Aka ba kabilar Manassa, ɗan farin Yusufu, nata rabon gādo. Makir ƙan farin Manassa, uban Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan domin shi jarumi ne. 2 Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manassa nasu rabon gādo bisa ga iyalansu, wato Abiyezer, da Helek, da Asriyel, da Shekem, da Hefer, da Shemida. Waɗannan su ne 'ya'yan Manassa, maza, bisa ga iyalansu. 3 Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ƙan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manassa ba shi da 'ya'ya maza, sai dai mata. Sunayensu ke nan, Mala, da Nowa, da Hogla, da Milka, da Tirza. 4 Suka zo wurin Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin, suka ce, “Ubangiji ya umarci Musa ya ba mu gādo tare da 'yan'uwanmu maza.” Sai ya ba su gādo tare da 'yan'uwan mahaifinsu bisa ga umarnin Ubangiji. 5 Saboda haka kuwa Manassa ya sami kashi goma banda ƙasar Gileyad da Bashan da yake hayin gabashin Urdun, 6 domin jikokin Manassa mata sun sami gādo tare da jikokinsa maza. Aka ba sauran mutanen kabilar Manassa ƙasar Gileyad. 7 Yankin ƙasar Manassa ya kai daga Ashiru zuwa Mikmetat wadda take gabas da Shekem. Iyakar kuma ta miƙa kudu zuwa mazaunan Entaffuwa. 8 Ƙasar Taffuwa tana hannun mutanen Manassa, amma mutanen Ifraimu ne suke da garin Taffuwa wanda yake iyakar yankin Manassa. 9 Iyakar kuma ta gangara zuwa rafin Kana. Waɗannan birane da suke kudancin rafin, na Ifraimu ne, ko da yake suna cikin biranen Manassa. Iyakar Manassa kuwa ta bi gefen arewacin rafin ta gangara a Bahar Rum. 10 Ƙasar wajen kudu ta Ifraimu ce, ta wajen arewa kuwa ta Manassa. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Mutanen Ashiru suna wajen arewa, mutanen Issaka kuwa wajen gabas. 11 A yankin ƙasar Issaka da na Ashiru, Manassa yana da waɗannan wurare, Bet-sheyan da ƙauyukanta, da Ibleyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Endor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta'anak da ƙauyukanta, da mazaunan Magiddo da ƙauyukanta, da sulusin Nafat. 12 Amma mutanen Manassa ba su iya su mallaki waɗannan birane ba, don haka Kan'aniyawa suka yi zamansu a wuraren. 13 Amma sa'ad da Isra'ilawa suka yi ƙarfi sai suka tilasta su su yi musu aikin dole, amma ba su iya korarsu ba. 14 Kabilan Yusufu suka ce wa Joshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo guda ɗaya? Ga shi kuwa, muna da jama'a mai yawa, gama Ubangiji ya sa mana albarka.” 15 Joshuwa kuwa ya amsa musu, ya ce, “Idan ku babbar jama'a ce, har ƙasar tuddai ta Ifraimu ta kāsa muku, to, sai ku shiga jeji ku sheme wa kanku wuri a ƙasar Ferizziyawa da ta Refayawa.” 16 Sai mutanen kabilan Yusufu suka ce, “Ƙasar tuddai ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan'aniyawa da suke zaune a filin, da waɗanda suke a Bet-sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke cikin Kwarin Yezreyel suna da karusan ƙarfe.” 17 Joshuwa kuma ya ce wa jama'ar gidan Yusufu, wato kabilar Ifraimu da ta Manassa, “Ku babbar jama'a ce, ga shi kuma, kuna da ƙarfi, ba kashi ɗaya kaɗai za ku samu ba, 18 amma ƙasar tuddai kuma za ta zama taku, ko da yake jeji ne. Sai ku sheme, ku mallaka duka. Gama za ku kori Kan'aniyawa, ko da yake su ƙarfafa ne, suna kuma da karusan ƙarfe.”

Joshuwa 18

Rarraba Ƙasa a Shilo

1 Da jama'ar Isra'ila suka ci ƙasar, sai suka tattaru a Shilo inda suka kafa alfarwa ta sujada. 2 Har yanzu akwai sauran kabila bakwai na Isra'ila waɗanda ba su sami gādonsu ba tukuna. 3 Sai Joshuwa ya ce wa jama'ar Isra'ila, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na kakanninku ya ba ku? 4 Ku ba ni mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su auna ƙasar yadda za a raba ta gādo, sa'an nan su komo wurina. 5 Sai su raba ƙasar kashi bakwai. Kabilar Yahuza za ta ci gaba da zama a yankin ƙasarta a wajen kudu, mutanen gidan Yusufu kuwa su zauna a yankin ƙasarsu a wajen arewa. 6 Ku auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sa'an nan ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuwa zan jefa muku kuri'a a gaban Ubangiji Allahnmu. 7 Lawiyawa ba su da rabo tare da ku gama aikin Ubangiji shi ne rabonsu, da rabin ta Manassa sun riga sun sami nasu rabo wanda Musa, bawan Ubangiji, ya ba su a hayin gabashin Urdun.” 8 Joshuwa ya umarci mutanen da za su tafi su auna ƙasar, ya ce, “Ku shiga cikin ƙasar duka, ku auna sa'an nan ku komo wurina, ni kuwa zan jefa muku kuri'a a gaban Ubangiji a nan Shilo.” 9 Sai mutanen suka tafi, suka ratsa ƙasar tudu da ta gangare, suka auna ƙasar, suka raba ta kashi bakwai, suka lasafta garuruwan da suke ciki, sa'an nan suka koma wurin Joshuwa a Shilo. 10 Joshuwa kuwa ya jefa musu kuri'a a gaban Ubangiji a Shilo. Ta haka ya rarraba ƙasar ga jama'ar Isra'ila, kowa ya sami rabonsa.

Yankin Ƙasar da aka Ba Biliyaminu

11 Kuri'ar kabilar Biliyaminu bisa ga iyalanta ta fito. Yankin ƙasar da ya faɗo mata ke nan, ya zama a tsakanin yankin ƙasar kabilar Yahuza da na jama'ar Yusufu. 12 A wajen arewa iyakar ta tashi daga Urdun, ta bi ta tsaunin da yake arewa da Yariko, ta kuma haura tudu wajen yamma, har zuwa hamadar Bet-awen inda ta ƙare. 13 Daga can iyakar ta yi kudu, ta nufi cibiyar Luz, wato Betel, ta gangara zuwa Atarot-addar a bisa dutsen da yake kudu da Bet-horon ta kwari. 14 Daga nan iyakar ta nausa ta nufi yammacin kudancin dutse da yake kudu, daura da Bet-horon, sa'an nan ta tsaya a Kiriyatba'al, wato Kiriyat-yeyarim, birnin Yahuza. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma. 15 A wajen kudu kuwa iyakar ta fara daga karkarar Kiriyat-yeyarim, daga can ta miƙa zuwa Efron a maɓuɓɓugar ruwan Neftowa. 16 Iyakar kuma ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskar kwarin ɗan Hinnon, wanda yake arewa wajen ƙarshen kwarin Refayawa. Ta kuma gangara zuwa kwarin Hinnom ta yi kudu daura da Yebusiyawa, ta gangara zuwa En-rogel. 17 Sai ta nausa ta yi wajen arewa zuwa En-shemesh, sa'an nan ta tafi Gelilot wanda yake daura da hawan Adummim. Daga nan ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ra'ubainu. 18 Sai ta wuce ta yi arewa daura da gefen Bet-araba, daga nan ta gangara zuwa Araba. 19 Ta kuma zarce zuwa arewa daura da gefen Bet-hogla, ta tsaya a arewacin gaɓar Tekun Gishiri a ƙarshen Urdun wajen kudu. 20 Kogin Urdun shi ne iyakar a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Biliyaminu suka gāda. 21 Biranen iyalan kabilar Biliyaminu ke nan Yariko, da Bet-hogla, da Emekkeziz, 22 da Bet-araba, da Zemarayim, da Betel, 23 da Awwim, da Fara, da Ofra, 24 da Kefar-ammoni, da Ofni, da Geba. Birane goma sha biyu ke nan tare da ƙauyukansu. 25 Akwai kuma Gibeyon, da Rama, da Biyerot, 26 da Mizfa, da Kefira, da Moza, 27 da Rekem, da Irfeyel, da Tarala, 28 da Zela, da Elef, da Yebus, wato Urushalima, da Gebeya, da Kiriyat. Birane goma sha huɗu ke nan tare da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon mutanen Biliyaminu bisa ga iyalansu.

Joshuwa 19

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Saminu

1 Kuri'a ta biyu ta faɗa kan kabilar Saminu bisa ga iyalanta. Nasu rabon gādon yana tsakiyar rabon gādon kabilar Yahuza. 2 Waɗannan su ne wuraren da suka gāda, Biyer-sheba, da Sheba, da Molada, 3 da Hazar-shuwal, da Bilha, da Ezem, 4 da Eltola, da Betul, da Horma, 5 da Ziklag, da Bet-markabot, da Hazar-susa, 6 da Bet-lebawot, da Sharuhen. Garuruwa goma sha uku ke nan da ƙauyukansu. 7 Akwai kuma Ayin, da Rimmon, da Eter, da Ashan. Garuruwa huɗu ke nan da ƙauyukansu, 8 da kuma dukan ƙauyukan da suke kewaye da waɗannan garuruwa tun daga Ba'alat-biyer, wato Ramot ta Negeb. Wannan shi ne rabon gādon iyalan kabilar Saminu. 9 Gādon kabilar Saminu yana cikin yankin ƙasar rabon kabilar Yahuza domin rabon kabilar Yahuza ya yi mata yawa, don haka kabilar Saminu ta sami gādo daga cikin tsakiyar gādon kabilar Yahuza.

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Zabaluna

10 Kuri'a ta uku ta faɗa a kan kabilar Zabaluna bisa ga iyalanta. Yankin ƙasar gādonsu ya kai har Sarid. 11 Iyakar ta hau wajen yamma zuwa Marala, ta kai Dabbeshet da rafin da yake gabas da Yakneyam. 12 Daga Sarid, ta nufi wajen gabas zuwa iyakar Kislotabar, sa'an nan ta bi ta Daberat da Yafiya. 13 Daga can ta miƙa wajen gabas zuwa Gat-hefer da Et-kazin, har zuwa Rimmon inda ta nausa zuwa Neya. 14 Daga wajen arewa iyakar ta juya zuwa Hannaton, sa'an nan ta faɗa a kwarin Iftahel. 15 Waɗannan garuruwa, da Kattat, da Nahalal, da Shimron, da Idala, da Baitalami, suna cikin garuruwa goma sha biyu da ƙauyukansu da suke cikin yankin ƙasar kabilar Zabaluna. 16 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke cikin gādon mutanen Zabaluna bisa ga iyalansu.

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Issaka

17 Kuri'a ta huɗu ta faɗo a kan kabilar Issaka bisa ga iyalanta. 18 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar su ne, Yezreyel, da Kesullot, da Shunem, 19 da Hafarayim, da Shiyon, da Anaharat, 20 da Rabbit, da Kishiyon, da Ebez, 21 da Remet da En-ganim, da En-hadda, da Bet-fazzez. 22 Iyakar kuma ta bi ta Tabor, da Shahazuma, da Bet-shemesh. Sa'an nan ta gangara a Kogin Urdun. Akwai garuruwa goma sha shida da ƙauyukansu. 23 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke a yankin ƙasar da kabilar Issaka ta gāda bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Ashiru

24 Kuri'a ta biyar ta fāɗo a kan kabilar Ashiru bisa ga iyalanta. 25 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar, su ne Helkat, da Hali, da Beten, da Akshaf, 26 da Alammelek, da Amad, da Mishal. A wajen yamma, iyakar ta bi ta Karmel da Shihor-libnat. 27 Daga nan sai ta nausa wajen gabas, ta bi ta Bet-dagon, da Zabaluna, da kwarin Iftahel a wajen arewa zuwa Bet-emek da Nayil. Ta yi gaba a wajen arewa zuwa Kabul, 28 da Hebron, da Rehob, da Hammon, da Kana, har ta bi ta Sidon Babba. 29 Daga can ta nausa zuwa Rama, ta bi ta garun birnin Taya, sai kuma ta nausa zuwa Hosa, sa'an nan ta gangara Bahar Rum, wajen Mahalab, da Akzib, 30 da Umma, da Afek, da Rehob. Garuruwa ashirin da biyu ke nan da ƙauyukansu. 31 Waɗannan su ne garuruwa da ƙauyukansu da suke cikin yankin ƙasar da kabilar Ashiru ta gāda bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Naftali

32 Kuri'a ta shida ta faɗo a kan kabilar Naftali bisa ga iyalanta. 33 Tasu iyaka, ta miƙa daga Helef, daga itacen oak da yake cikin Za'anannim, da Adami-nekeb, da Yabneyel har zuwa Lakkum, sa'an nan ta tsaya a Kogin Urdun. 34 Iyakar kuma ta juya wajen kudu zuwa Aznot-tabor, daga can ta miƙa zuwa Hukkok, sa'an nan ta kai Zabaluna wajen kudu, da Ashiru wajen yamma, da Yahuza wajen gabas wajen Urdun. 35 Garuruwan da suke da garu su ne, Ziddim, da Zer, da Hammat, da Rakkat, da Kinneret, 36 da Adama, da Rama, da Hazor, 37 da Kedesh, da Edirai, da En-hazor, 38 da Iron, da Migdal-el, da Horem, da Bet-anat, da Bet-shemesh. Garuruwa goma sha tara ke nan da ƙauyukansu. 39 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne rabon gādon kabilar Naftali da iyalanta.

Yankin Ƙasar da aka Ba Kabilar Dan

40 Kuri'a ta bakwai ta faɗo a kan kabilar Dan bisa ga iyalanta. 41 Garuruwan da suke cikin yankin ƙasar gādonta ke nan, da Zora, da Eshtawol, da Ir-shemesh, 42 da Shalim, da Ayalon, da Itla, 43 da Elon, da Timna, da Ekron, 44 da Elteki, da Gebbeton, da Ba'alat, 45 da Yahud, da Bene-berak, da Gat-rimmon, 46 da Meyarkon, da Rakkon, tare da karkarar da take gefen Yaffa. 47 Sa'ad da Danawa suka rasa karkararsu, suka tafi, suka yaƙi Leshem. Da suka ci ta, sai suka hallaka mutanenta da takobi, suka mallaki ƙasar, suka zauna a ciki. Suka kuma sa wa Leshem, sunan kakansu, wato Dan. 48 Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon kabilar Dan bisa ga iyalanta.

Yankin Ƙasar da aka Ba Joshuwa

49 Sa'ad da mutanen Isra'ila suka gama rarraba gādon ƙasar, suka ba Joshuwa ɗan Nun nasa rabo a cikin nasu. 50 Bisa ga umarnin Ubangiji, suka ba shi garin da ya roƙa, wato Timnatsera a ƙasar tudu ta Ifraimu. Ya sāke gina garin, ya kuwa zauna a ciki. 51 Waɗannan su ne rabe-raben gādon da Ele'azara firist, da Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin kakannin gidajen kabilan jama'ar Isra'ila, suka rarraba ta hanyar jefa kuri'a a gaban Ubangiji a ƙofar alfarwa ta sujada a Shilo. Ta haka suka gama rarraba ƙasar.

Joshuwa 20

An Keɓe Biranen Mafaka

1 Sai Ubangiji ya ce wa Joshuwa, 2 “Ka faɗa wa jama'ar Isra'ila, su keɓe biranen mafaka waɗanda na faɗa wa Musa ya faɗa muku. 3 Domin idan wani mutum ya yi kisankai ba da niyya ba, ba kuma da saninsa ba, sai ya tsere zuwa can. Biranen za su zama muku mafaka daga mai bin hakkin jini. 4 Wanda ya yi kisankan sai ya tsere zuwa ɗaya daga cikin biranen, ya tsaya a bakin ƙofar birnin, ya bayyana wa dattawan garin abin da ya same shi. In sun ji, sai su shigar da shi a birnin, su ba shi wurin zama, ya zauna tare da su. 5 Idan mai bin hakkin jinin ya bi shi, ba za su ba shi wanda ya yi kisankan ba, domin bai kashe maƙwabcinsa da gangan ba, ba kuma ƙiyayya a tsakaninsu dā ma. 6 Zai yi zamansa a birnin har lokacin da aka gabatar da shi gaban dattawa don shari'a, sai kuma bayan rasuwar babban firist na lokacin, sa'an nan wanda ya yi kisankan zai iya komawa garinsu da gidansa daga inda ya tsere.” 7 Saboda haka suka keɓe Kedesh ta Galili a ƙasar tuddai ta Naftali, da Shekem ta ƙasar tuddai ta Ifraimu, da Kiriyat-arba, wato Hebron, ta ƙasar tuddai ta Yahuza. 8 A hayin Urdun, gabas da Yariko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ra'ubainu, da Ramot cikin Gileyad ta kabilar Gad, da Golan cikin Bashan ta kabilar Manassa. 9 Waɗannan su ne biranen mafaka da aka keɓe domin dukan Isra'ilawa, da baƙin da suke baƙuntaka cikinsu. Don duk wanda ya yi kisankai ba da niyya ba zai iya tserewa zuwa can don kada ya mutu ta hannun mai bin hakkin jini. Zai zauna a can har lokacin da za a gabatar da shi a gaban taron jama'a.

Joshuwa 21

Biranen da aka Ba Lawiyawa

1 Shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa suka zo wurin Ele'azara, firist, da wurin Joshuwa ɗan Nun, da shugabannin gidajen kakannin kabilan jama'ar Isra'ila. 2 Suka yi magana da su a Shilo a ƙasar Kan'ana, suka ce musu, “Ubangiji ya umarta ta bakin Musa a ba mu biranen zama da wuraren kiwo domin dabbobinmu.” 3 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai jama'ar Isra'ila suka ba Lawiyawa waɗannan birane da wuraren kiwo daga cikin gādonsu. 4 Kuri'a ta faɗo a kan iyalan Kohatawa. Sai Lawiyawa na zuriyar Haruna firist suka karɓi birane goma sha uku daga kabilar Yahuza, da kabilar Saminu, da kabilar Biliyaminu. 5 Sauran Kohatawa suka karɓi birane goma daga iyalan kabilar Ifraimu, da kabilar Dan, da rabin kabilar Manassa. 6 Gershonawa kuwa suka karɓi birane goma sha uku ta hanyar jefa kuri'a daga iyalan kabilar Issaka, da kabilar Ashiru, da kabilar Naftali, da rabin kabilar Manassa a Bashan. 7 Sai Merariyawa bisa ga iyalansu suka karɓi birane goma sha biyu daga kabilar Ra'ubainu, da ta Gad, da ta Zabaluna. 8 Waɗannan birane da wuraren kiwo nasu su ne jama'ar Isra'ila suka ba Lawiyawa ta hanyar jefa kuri'a kamar yadda Ubangiji ya umarta ta bakin Musa. 9 Daga cikin kabilar Yahuza da kabilar Saminu aka ba zuriyar Haruna waɗannan birane da aka ambata. 10 Zuriyar Haruna tana cikin iyalan Kohatawa waɗanda suke Lawiyawa. Kuri'arsu ce ta fito da farko. 11 Sai aka ba su Kiriyat-arba, wato Hebron, a ƙasar tuddai ta Yahuza tare da wuraren kiwo nata da suke kewaye. Arba shi ne mahaifin Anak. 12 Amma saurukan birnin da ƙauyukansu an ba Kalibu, ɗan Yefunne, su zama mallakarsa. 13 Biranen da aka ba zuriyar Haruna firist ke nan, Hebron tare da wuraren kiwo nata, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Libna tare da wuraren kiwo nata, 14 da Yattir tare da wuraren kiwo nata, da Eshtemowa tare da wuraren kiwo nata, 15 da Holon tare da wuraren kiwo nata, da Debir tare da wuraren kiwo nata, 16 da Ayin tare da wuraren kiwo nata, da Yutta tare da wuraren kiwo nata, da Bet-shemesh tare da wuraren kiwo nata. Birane tara ke nan daga cikin kabilun nan biyu. 17 Daga cikin kabilar Biliyaminu aka ba su birane huɗu, wato Gibeyon tare da wuraren kiwo nata, da Geba tare da wuraren kiwo nata, 18 da Anatot tare da wuraren kiwo nata, da Almon tare da wuraren kiwo nata. 19 Dukan biranen da aka ba firistoci, wato zuriyar Haruna, guda goma sha uku ne tare da wuraren kiwo nasu. 20-22 Aka ba sauran Kohatiyawa na iyalan Lawiyawa birane huɗu daga kabilar Ifraimu. Aka ba su Shekem tare da wuraren kiwo nata, a ƙasar tuddai ta Ifraimu, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Gezer tare da wuraren kiwo nata, da Yokmeyam tare da wuraren kiwo nata, da Bet-horon tare da wuraren kiwo nata. kuma ba su birane huɗu daga kabilar Dan, wato Elteki tare da wuraren kiwo nata, da Gibbeton tare da wuraren kiwo nata, da Ayalon tare da wuraren kiwo nata, da Gat-rimmon tare da wuraren kiwo nata. 25 Daga cikin rabin kabilar Manassa, aka ba su birane biyu, su ne Ta'anak tare da wuraren kiwo nata, da Bileyam tare da wuraren kiwo nata. 26 Dukan birane da wuraren kiwo nasu da aka ba sauran Kohatawa na iyalan Lawiyawa guda goma ne. 27 Aka ba iyalan Gershonawa na cikin Lawiyawa birane biyu daga cikin rabo na rabin kabilar Manassa. Biranen su ne, Golan tare da wuraren kiwo nata, cikin Bashan, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Ashtarot da wuraren kiwo nata. kuma ba su birane huɗu daga cikin kabilar Issaka, biranen su ne, Kishiyon da wuraren kiwo nata, da Daberat da wuraren kiwo nata, da Yarmut da wuraren kiwo nata, da Enganim da wuraren kiwo nata. cikin rabon kabilar Ashiru aka ba su birane huɗu, su ne Mishal da wuraren kiwo nata, da Abdon da wuraren kiwo nata, da Helkat da wuraren kiwo nata, da Rehob da wuraren kiwo nata. 32 Daga cikin rabon kabilar Naftali aka ba su birane uku, su ne, Kedesh ta Galili da wuraren kiwo nata, ita kuwa birnin mafaka ce saboda wanda ya yi kisankai, da Hammon da wuraren kiwo nata, da Kartan da wuraren kiwo nata. 33 Dukan birane da wuraren kiwo nasu da aka ba iyalan Gershonawa guda goma sha uku ne. 34-35 Aka ba iyalan Merari na cikin Lawiyawa birane huɗu daga cikin rabon kabilar Zabaluna. Biranen ke nan, Yakneyam da wuraren kiwo nata, da Karta da wuraren kiwo nata, da Rimmon da wuraren kiwo nata, da Nahalal da wuraren kiwo nata. kuma ba su birane huɗu daga cikin rabon kabilar Ra'ubainu. Biranen ke nan, Bezer da wuraren kiwo nata, da Yahaza da wuraren kiwo nata, da Kedemot da wuraren kiwo nata, da Mefayat da wuraren kiwo nata. cikin kabilar Gad aka ba su birane huɗu, su ne Ramot ta Gileyad da wuraren kiwo nata, wannan birnin mafaka ne domin wanda ya yi kisankai, da Mahanayim da wuraren kiwo nata, da Heshbon da wuraren kiwo nata, da Yazar da wuraren kiwo nata. 40 Dukan biranen da aka ba iyalan Merari na Lawiyawa guda goma sha biyu ne. 41 Jimillar biranen da wuraren kiwo nasu da aka ba Lawiyawa daga cikin mallakar jama'ar Isra'ila guda arba'in da takwas ne. 42 Kowane birni yana da wuraren kiwo nasa kewaye da shi.

Isra'ilawa sun Mallaki Ƙasar

43 Haka kuwa Ubangiji ya ba Isra'ilawa dukan ƙasar da ya rantse zai ba kakanninsu. Suka ci ƙasar, suka zauna a ciki. 44 Ubangiji kuma ya ba da hutawa ko'ina kamar yadda ya rantse wa kakanninsu. Babu wani daga cikin abokan gābansu da ya iya ta da kai da su, gama Ubangiji ya ba da abokan gābansu duka a hannunsu. 45 Ubangiji kuwa ya cika kowane alkawarin alheri da ya yi wa gidan Isra'ila.

Joshuwa 22

Bagade a Bakin Urdun

1 Sa'an nan Joshuwa ya kira mutanen kabilar Ra'ubainu, da na Gad, da rabin kabilar Manassa. 2 Ya ce musu, “Kun aikata dukan abin da Musa, bawan Ubangiji, ya umarce ku, kun kuma yi biyayya da dukan abin da na umarce ku. 3 Ba ku yar da 'yan'uwanku dukan waɗannan yawan kwanaki, har wa yau ba. Amma kuka kiyaye umarnin Ubangiji Allahnku sosai. 4 Yanzu Ubangiji Allahnku ya ba 'yan'uwanku hutawa kamar yadda ya faɗa, yanzu dai sai ku koma, ku tafi gida a ƙasarku ta gādo wadda Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku a hayin Urdun. 5 Sai dai ku kiyaye umarnai da dokokin da Musa, bawan Ubangiji, ya ba ku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku, ku yi tafiya cikin tafarkunsa, ku kiyaye dokokinsa, ku manne masa, ku bauta masa da zuciya ɗaya da dukan ranku.” 6 To, Joshuwa ya sa musu albarka, sa'an nan ya sallame su, suka koma gida. 7 Musa ya riga ya ba rabin kabilar Manassa gādo a Bashan, sauran rabin kabilar kuwa Joshuwa ya ba su gādo tare da 'yan'uwansu a yammacin hayin Urdun. Sa'ad da Joshuwa ya sallame su zuwa gida, ya sa musu albarka, 8 ya ce musu, “Ku koma gidajenku da wadata mai yawa, da dabbobi masu yawa, da azurfa, da zinariya, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da tufafi masu yawa. Ku raba da 'yan'uwanku ganimar da kuka kwaso daga abokan gabanku.” 9 Sai Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka koma gida. Suka yi bankwana da sauran 'yan'uwansu Isra'ilawa a Shilo ta ƙasar Kan'ana. Suka koma ƙasar Gileyad, ƙasar da suka gāda bisa ga umarnin Ubangiji ta bakin Musa. 10 Sa'ad da suka kai Gelilot, kusa da Urdun, a gefen da yake wajen ƙasar Kan'ana, suka gina babban bagade a wurin. 11 Sauran Isra'ilawa kuwa suka ji labari cewa, “Ga shi, Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa sun gina bagade a Gelilot a kan iyakar ƙasar Kan'ana, a wajen hayinsu na yammacin Urdun.” 12 Da Isra'ilawa suka ji haka sai dukansu suka tattaru a Shilo don su kai musu yaƙi. 13 Mutanen Isra'ila kuwa suka aiki Finehas, ɗan Ele'azara, firist, wurin Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa a ƙasar Gileyad. 14 Shugabanni goma suka tafi tare da shi, shugaba ɗaya daga kowace kabilar Isra'ila. Kowane ɗayansu shugaba ne a danginsa a kabilar Isra'ila. 15 Da suka zo wurin Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa a ƙasar Gileyad, ya ce musu, 16 “In ji dukan taron jama'ar Ubangiji, ‘Wane irin cin amana ne wannan da kuka yi wa Allah na Isra'ila har da kuka bar bin Ubangiji yau?’ Kun tayar wa Ubangiji yau da kuka gina wa kanku bagade. 17 Zunubin da aka yi a Feyor, ashe, bai ishe mu ba, har annoba ta wahalar da taron jama'ar Ubangiji? Ga shi, har yanzu ma ba mu gama tsarkakewa daga wannan zunubi ba. 18 Za ku kuma daina bin Ubangiji ne yau? Idan kuka tayar masa yau, gobe zai yi fushi da dukan jama'ar Isra'ila. 19 Idan ƙasar mallakarku ƙazantacciya ce, sai ku haye zuwa ƙasar Ubangiji inda alfarwa ta sujada take, ku sami abin mallaka a tsakaninmu, amma kada ku tayar wa Ubangiji, ku kuma tayar mana ta wurin gina wa kanku wani bagade dabam da bagaden Allahnmu. 20 Lokacin da Akan, ɗan Zera, ya yi rashin aminci cikin abubuwan da aka haramta, ai, dukan Isra'ilawa aka hukunta. Ba shi kaɗai ya hallaka don zunubinsa ba.” 21 Sai Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka amsa wa shugabannin iyalan Isra'ilawa suka ce, 22 “Allah Maɗaukaki, Allah Ubangiji ya sani, bari Isra'ilawa kuma da kansu su sani. Idan tayarwa ce, ko kuwa mun yi wa Ubangiji rashin aminci ne, to, kada ku bar mu da rai yau. 23 Idan mun bar bin Ubangiji, muka gina wa kanmu bagade don mu miƙa hadayun ƙonawa, ko kuwa hadayun gari, ko kuwa hadayun salama, to, bari Ubangiji kansa ya sāka mana. 24 Saboda gudun gaba ne muka yi haka, domin kada wata rana 'ya'yanku su ce wa 'ya'yanmu, ‘Ba ruwanku da Ubangiji, Allah na Isra'ila. 25 Gama Ubangiji ya sa Kogin Urdun ya zama iyaka tsakaninmu da ku Ra'ubainawa da Gadawa domin haka ba ku da wani rabo a cikin Ubangiji.’ To, da haka 'ya'yanku su hana 'ya'yanmu yi wa Ubangiji sujada. 26 Don haka muka ce, ‘Bari mu gina bagade, ba domin miƙa hadayu na ƙonawa, ko na sadaka ba, 27 amma domin ya zama shaida tsakaninmu da ku, da tsakanin zuriyarmu da taku, don mu ci gaba da bautar Ubangiji da hadayunmu na ƙonawa, da na sadaka, da na salama.’ 'Ya'yanku kuma ba za su ce wa 'ya'yanmu, ‘Ba ku da wani rabo a cikin Ubangiji.’ 28 Mun yi tunani, cewa idan wata rana aka ce mana, ko aka ce wa zuriyarmu haka, sai mu ce, ‘Ku dubi bagaden Ubangiji wanda iyayenmu suka gina, ba domin miƙa hadayu na ƙonawa, ko na sadaka ba, amma domin shaida a tsakaninmu da ku.’ 29 Allah ya sawwaƙa mana mu tayar wa Ubangiji, mu bar bin Ubangiji, har mu gina wani bagade don miƙa hadayu na ƙonawa, da na gari, da na sadaka, banda bagaden Ubangiji Allahnmu, wanda yake a gaban mazauninsa.” 30 Sa'ad da Finehas, firist, da shugabannin jama'a, wato shugabannin iyalan Isra'ila, suka ji maganar da Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa suka faɗa, suka ji daɗi a rai. 31 Sa'an nan Finehas, ɗan Ele'azara, firist, ya ce wa Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin Manassawa, “Yau mun sani Ubangiji yana tare da mu domin ba ku ci amanar Ubangiji ba.” 32 Sa'an nan Finehas, ɗan Ele'azara, firist, da shugabannin suka komo daga wurin Ra'ubainawa da Gadawa a ƙasar Gileyad, zuwa ƙasar Kan'ana wurin mutanen Isra'ila, suka ba su rahoton abin da suka ji. 33 Mutanen Isra'ila suka ji daɗin rahoton da aka ba su, suka yabi Allah, ba su sāke yin maganar zuwa yaƙi don su hallaka ƙasar da Ra'ubainawa da Gadawa suke zaune ba. 34 Ra'ubainawa da Gadawa suka sa wa bagaden suna Shaida, domin in ji su, “Shi shaida ne a tsakaninmu, cewa Ubangiji shi ne Allah.”

Joshuwa 23

Joshuwa ya Yi wa Jama'a Jawabi

1 An daɗe bayan da Ubangiji ya hutar da Isra'ilawa daga abokan gābansu waɗanda suke kewaye da su. Joshuwa kuwa ya tsufa, shekarunsa sun yi yawa. 2 Sai Joshuwa ya kira Isra'ilawa duka, da dattawansu, da shugabanninsu, da alƙalansu, da jarumawansu, ya ce musu, “Yanzu na tsufa, shekaruna sun yi yawa, 3 kun dai ga abin da Ubangiji Allahnku ya yi da waɗannan al'ummai duka saboda ku, gama Ubangiji Allahnku shi ne wanda ya yi yaƙi dominku. 4 Ga shi kuma, na rarraba wa kabilanku ƙasashen al'umman da suka ragu, da na waɗanda na shafe su tsakanin Urdun da Bahar Rum wajen yamma. 5 Ubangiji Allahnku ne zai sa su gudu a gabanku, ya kore su daga ƙasar. Ka ku mallaki ƙasarsu kamar yadda Ubangiji Allahnku ya alkawarta muku. 6 Domin haka sai ku yi ƙarfin hali ƙwarai, ku riƙe, ku aikata dukan abin da aka rubuta a littafin dokokin Musa, kada ku kauce dama ko hagu, 7 domin kada ku yi cuɗanya da sauran al'umman da suke zaune tare da ku, kada ku ambaci sunayen gumakansu, ko ku rantse da su, ko ku bauta musu, ko ku sunkuya musu. 8 Amma ku manne wa Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka yi har wa yau. 9 Gama Ubangiji ya kori manyan al'ummai ƙarfafa daga gabanku, har wa yau ba mutumin da ya isa ya yi hamayya da ku. 10 Mutuminku guda zai runtumi mutum dubu nasu, tun da yake Ubangiji Allahnku ne yake yaƙi dominku, kamar yadda ya alkawarta muku. 11 Ku kula da kanku sosai, ku ƙaunaci Ubangiji Allahnku. 12 Gama idan kun kauce, kun koma da baya, kun haɗa kai da sauran al'umman nan da suke tare da ku, har kuka yi aurayya da juna, 13 to, sai ku tabbata Ubangiji Allahnku ba zai dinga korar al'umman nan daga gabanku ba, za su zama muku azargiya, da tarko, da bulala a kwiyaɓunku, da ƙayayuwa a idanunku. Da haka za ku ƙare sarai daga cikin kyakkyawar ƙasar nan da Ubangiji Allahnku ya ba ku. 14 “A yanzu ina gaba da bin hanyar da kowa a duniya yakan bi, ku duka kuwa, a zukatanku da rayukanku, kun sani dukan abubuwan alheri da Ubangiji Allahnku ya alkawarta muku sun tabbata, ba ɗayan da bai tabbata ba. 15 Amma kamar yadda Ubangiji Allahnku ya cika alkawaran da ya yi muku, hakanan kuma Ubangiji zai aukar muku da masifu, har ya hallaka ku daga ƙasar nan mai albarka da Ubangiji Allahnku ya ba ku. 16 Lokacin da kuka karya alkawarin Ubangiji Allahnku da ya umarce ku, kuka tafi kuka bauta wa gumaka, kuka sunkuya musu, to, Ubangiji zai yi fushi da ku, zai kuwa hallaka ku daga ƙasa mai albarka da aka ba ku.”

Joshuwa 24

Jawabin Joshuwa na Bankwana a Shekem

1 Joshuwa kuma ya tara dukan kabilan Isra'ila a Shekem, ya kuma kira dattawa, da shugabanni, da alƙalai, da jarumawan Isra'ila. Suka hallara a gaban Allah. 2 Joshuwa kuwa ya ce wa mutane duka, “Ga abin da Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘A zamanin dā kakanninku, su Tera, mahaifin Ibrahim, da Nahor, suna zaune a hayin Yufiretis. Suka bauta wa gumaka. 3 Sai na ɗauki kakanku Ibrahim daga wancan hayin Kogi, na kawo shi ƙasar Kan'ana, na sa zuriyarsa ta yawaita. Na ba shi Ishaku. 4 Ishaku kuma na ba shi Yakubu da Isuwa. Na kuma ba Isuwa ƙasar tuddai ta Seyir, ya mallake ta, amma Yakubu da 'ya'yansa suka gangara zuwa Masar. 5 Na aiki Musa da Haruna, na aukar wa Masar da annobai ta wurin abin da na yi a cikinta daga baya kuma na fisshe ku. 6 Na kuwa fitar da kakanninku daga Masar. Da suka zo Bahar Maliya, sai Masarawa suka fafari kakanninku da karusai da mahayan dawakai har zuwa teku. 7 A sa'ad da suka yi mini kuka, na sa duhu a tsakaninsu da Masarawa, na sa teku ta shafe Masarawa. Da idonku kun ga abin da na yi wa Masar, kuka kuma zauna a jeji da daɗewa. 8 Sa'an nan na kawo ku a ƙasar Amoriyawa, waɗanda suka zauna a wancan hayin Urdun, waɗanda kuma suka yi yaƙi da ku, na kuwa ba da su gare ku, na hallaka su, kuka mallaki ƙasarsu. 9 Haka kuma Balak, ɗan Ziffor, Sarkin Mowab, ya tashi ya yi yaƙi da Isra'ila, har ya gayyaci Bal'amu, ɗan Beyor, ya zo ya la'anta ku. 10 Amma ban saurari Bal'amu ba, saboda haka ya sa muku albarka, ta haka na cece ku daga hannunsa. 11 Da kuka haye Urdun, kuka zo Yariko, mutanen Yariko kuwa suka yi yaƙi da ku, haka kuma Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Kan'aniyawa da Hittiyawa, da Girgashiyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, amma na ba da su a gare ku. 12 Na kuma aiki zirnako a gabanku, waɗanda suka kori sarakunan nan biyu na Amoriyawa daga gabanku. Ba takobinku, ko bakanku ya kore su ba. 13 Na ba ku ƙasar da ba ku yi wahala a kanta ba, da biranen da ba ku gina ba, ga shi, kuna zaune a ciki, kuna kuma cin 'ya'yan inabi, da na zaitun waɗanda ba ku ne kuka dasa ba.’ 14 “To fa, ku yi tsoron Ubangiji, ku bauta masa da sahihanci da aminci, ku yi watsi da gumakan da kakanninku suka bauta wa a hayin Kogin Yufiretis, da cikin Masar. 15 Idan ba ku da nufi ku bauta wa Ubangiji, to, yau sai ku zaɓi wanda za ku bauta wa, ko gumakan da kakanninku suka bauta wa a wajajen hayin Kogin Yufiretis, ko kuma gumakan Amoriyawa waɗanda kuke zaune a ƙasarsu, amma ni da gidana, Ubangiji za mu bauta wa.” 16 Jama'a kuwa suka amsa suka ce, “Allah ya kiyashe mu da rabuwa da Ubangiji, har a ce mu bauta wa gumaka. 17 Gama Ubangiji Allahnmu ne ya fisshe mu da kakanninmu daga ƙasar Masar, a gidan bauta. Shi ne wanda ya aikata manyan alamu a idonmu, ya kuma kiyaye mu a dukan hanyar da muka bi, da cikin dukan al'umman da muka ratsa. 18 Ubangiji kuwa ya kore mana dukan Amoriyawa waɗanda suke zaune a ƙasar, domin haka za mu bauta wa Ubangiji, gama shi ne Allahnmu.” 19 Amma Joshuwa ya ce wa mutanen, “Ba za ku iya bauta wa Ubangiji ba, gama shi Allah mai tsarki ne, mai kishi kuma, ba kuwa zai gafarta laifofinku da zunubanku ba. 20 Idan kun rabu da Ubangiji, kun bauta wa gumaka, sai ya juyo ya wulakanta ku, ya hallaka ku, ko da yake ya riga ya nuna muku alheri.” 21 Jama'a kuwa suka ce wa Joshuwa, “A'a, mu dai za mu bauta wa Ubangiji ne.” 22 Joshuwa kuma ya ce wa mutanen, “Ku ne shaidun kanku da kanku, kun zaɓi Ubangiji don ku bauta masa.” Sai suka ce, “I, mu ne shaidu.” 23 Joshuwa ya ce, “To, ku kawar da gumakan da suke cikinku, ku sa zuciyarku ga Ubangiji, Allah na Isra'ila.” 24 Jama'a suka ce wa Joshuwa, “Za mu bauta wa Ubangiji Allahnmu, za mu kuma yi biyayya da muryarsa.” 25 A wannan rana, Joshuwa ya yi alkawari da jama'a a Shekem, ya kafa musu dokoki da ka'idodi. 26 Ya kuwa rubuta waɗannan kalmomi a littafin Shari'ar Ubangiji. Ya kuma ɗauki wani babban dutse, ya kafa a ƙarƙashin itacen oak a wuri mai tsarki na Ubangiji. 27 Sai ya ce wa jama'a, “Wannan dutse shi ne shaida a kanmu, gama ya ji dukan abin da Ubangiji ya faɗa mana, domin haka zai zama shaida a kanku, don kada ku yi wa Allahnku ƙarya.” 28 Joshuwa kuwa ya sallami jama'ar, kowane mutum ya koma wurin gādonsa.

Rasuwar Joshuwa da ta Ele'azara

29 Bayan waɗannan al'amura, sai Joshuwa ɗan Nun, bawan Ubangiji, ya rasu yana da shekara ɗari da goma da haihuwa. 30 Suka binne shi a ƙasar gādonsa a Timnat-sera wadda take cikin karkarar tuddai ta Ifraimu, arewa da dutsen Ga'ash. 31 Isra'ilawa kuwa suka bauta wa Ubangiji a dukan zamanin Joshuwa, da dukan zamanin dattawan da suka wanzu bayansa, waɗanda suka san dukan ayyukan da Ubangiji ya aikata domin Isra'ilawa. 32 Kasusuwan Yusufu, waɗanda jama'ar Isra'ila suka kawo daga Masar, an binne su a Shekem a yankin ƙasar da Yakubu ya saya a bakin azurfa ɗari daga wurin 'ya'yan Hamor mahaifin Shekem. Wurin ya zama gādon zuriyar Yusufu. 33 Ele'azara, ɗan Haruna kuma ya rasu, aka binne shi a Gebeya a garin ɗansa, Finehas, wanda aka ba shi a ƙasar tuddai ta Ifraimu.

Littafin Mahukunta 1

Yahuza da Saminu sun Ci Adoni-bezek

1 Bayan da Joshuwa ya rasu, jama'ar Isra'ila suka tambayi Ubangiji suka ce, “Wane ne daga cikinmu zai fara tafiya don ya yaƙi Kan'aniyawa?” 2 Sai Ubangiji ya ce, “Yahuza ne zai tafi, ga shi, na ba da ƙasar a gare shi.” 3 Yahuza kuwa ya ce wa Saminu ɗan'uwansa, “Ka zo tare da ni a wurin da aka ba ni rabon gādona don mu yaƙi Kan'aniyawa, ni kuma zan tafi tare da kai a wurin da aka ba ka rabon gādonka.” Saminu ya tafi tare da shi. 4 Yahuza ya tafi, Ubangiji kuwa ya ba da Kan'aniyawa da Ferizziyawa a gare su, suka kashe mutum dubu goma daga cikinsu a Bezek. 5 Suka iske Adoni-bezek a can, suka yi yaƙi da shi, suka kuma ci Kan'aniyawa da Ferizziyawa. 6 Sai Adoni-bezek ya gudu, amma suka bi shi, suka kama shi. Suka yanyanke manyan yatsotsinsa na hannu da na ƙafa. 7 Ya kuma ce, “Sarakuna saba'in waɗanda aka yanyanke manyan yatsotsinsu na hannu da na ƙafa, suka kalaci abincinsu a ƙarƙashin teburina. Allah kuwa ya yi mini kamar yadda na yi musu.” Suka kawo shi Urushalima, a nan ya mutu.

Kabilar Yahuza ta Ci Urushalima da Hebron

8 Mutanen Yahuza kuwa suka yaƙi Urushalima, suka ci ta, suka karkashe mutanenta, suka kuma cinna mata wuta. 9 Bayan wannan suka gangara kuma, suka yaƙi Kan'aniyawan da suke zaune a ƙasar tudu, da Negeb, da filayen kwari. 10 Suka kuma tafi su yaƙi Kan'aniyawan da suke zaune a Hebron wadda a dā ake kira Kiriyat-arba. Suka kashe Sheshai, da Ahiman, da Talmai.

Otniyel ya Ci Birnin Debir ya Auri Aksa

11 Daga can suka tafi su yaƙi Debir wadda a dā ake kira Kiriyat-Sefer. 12 Kalibu ya ce, “Duk wanda ya fāɗa wa Kiriyat-Sefer da yaƙi har ya ci ta, zan ba shi 'yata Aksa aure.” 13 Sai Otniyel ɗan Kenaz, ƙanen Kalibu ya ci birnin da yaƙi, Kalibu kuwa ya ba shi 'yarsa Aksa aure. 14 Da ta zo wurinsa, ta iza shi ya roƙi mahaifinta saura. Da ta sauka daga kan jakinta, sai Kalibu ya ce mata, “Me kike so?” 15 Sai ta amsa masa, “Ka yi mini alheri, da yake ka tura ni a ƙasar Negeb, ka ba ni maɓuɓɓugan ruwa.” Kalibu kuwa ya ba ta maɓuɓɓugan tuddai da na kwari.

Yawan Wuraren da Yahuza da Biliyaminu Suka Ci

16 Zuriyar Bakene, surukin Musa kuwa suka fita tare da mutanen Yahuza daga birnin dabino, wato Yariko, suka tafi jejin Yahuda da yake a Negeb kudu da Arad. A can suka zauna tare da Amalekawa. 17 Yahuza kuwa da ɗan'uwansa, Saminu, suka tafi suka bugi Kan'aniyawan da suke zaune a Zefat. Suka la'anta birnin, suka hallaka shi, suka sāke wa birnin suna Horma, wato hallakarwa. 18 Yahuza kuma ya ci Gaza da karkararta, da Ashkelon da karkararta, da Ekron da karkararta. 19 Ubangiji kuwa yana tare da Yahuza, ya mallaki ƙasar tuddai, amma bai iya korar waɗanda suke zaune a fili ba, domin suna da karusan ƙarfe. 20 Aka ba Kalibu Hebron kamar yadda Musa ya faɗa. Shi kuwa ya kori 'ya'yan Anak, maza, su uku, a can. 21 Amma mutanen Biliyaminu ba su kori Yebusiyawan da suke zaune a Urushalima ba domin haka Yebusiyawa suka yi zamansu tare da mutanen Biliyaminu a Urushalima har wa yau.

Kabilar Yusufu ta Ci Betel

22 Jama'ar kabilar Yusufu kuwa suka haura don su yaƙi Betel, Ubangiji kuwa yana tare da su. 23 Suka aika a leƙi asirin Betel wadda a dā ake kira Luz. 24 Sai 'yan leƙen asirin ƙasar suka ga wani mutum yana fitowa daga cikin birnin, suka ce masa, “Muna roƙonka ka nuna mana hanyar shiga birnin, mu kuwa za mu yi maka alheri.” 25 Ya kuwa nuna musu, suka shiga suka kashe dukan mutanen birnin, amma suka bar mutumin da iyalinsa duka. 26 Sai mutumin ya tafi ƙasar Hittiyawa, ya gina birni, ya sa masa suna Luz, haka ake kiran birnin har wa yau.

Yawan Wuraren da Manassa da Ifraimu suka Ci

27 Kabilar Manassa ba su kori waɗanda suke zaune a Bet-sheyan, da Ta'anak, da Dor, da Ibleyam, da Magiddo, da garuruwan da suke kusa da su ba, amma Kan'aniyawa suka yi kanekane cikin ƙasar. 28 Sa'ad da Isra'ilawa suka yi ƙarfi, suka sa Kan'aniyawa su yi aikin gandu, amma ba su kore su ba. 29 Mutanen Ifraimu kuma ba su kori Kan'aniyawan da suke zaune cikin Gezer ba, amma Kan'aniyawa suka yi zamansu a Gezer tare da su.

Yawan Wuraren da sauran Kabilai suka Ci

30 Mutanen Zabaluna ma ba su kori mazaunan Kattat da na Nahalal ba, amma Kan'aniyawa suka zauna tare da su, suna yi musu aikin gandu. 31 Haka kuma mutanen Ashiru ba su kori mazaunan Akko, da na Sidon, da Alab, da Akzib, da Helba, da Afek, da Rehob ba. 32 Amma Ashirawa suka yi zamansu tare da Kan'aniyawan ƙasar, gama ba su kore su ba. 33 Mutanen Naftali ma ba su kori mazaunan Bet-shemesh, da na Bet-anat ba, amma suka zauna tare da Kan'aniyawan ƙasar, duk da haka mazaunan Bet-shemesh da na Bet-anat suka zama masu yi musu aikin gandu. 34 Amoriyawa suka matsa wa Danawa, suka angaza su cikin ƙasar tuddai, ba su yarda musu su zauna a filayen ba. 35 Amoriyawa kuwa suka nace su zauna a Heres, da Ayalon, da Shalim. Amma mutanen kabilar Yusufu suka mallake su har suka zama masu yi musu aikin gandu. 36 Iyakar Amoriyawa ta nausa ta kan hawan Akrabbim daga Sela zuwa gaba.

Littafin Mahukunta 2

Mala'ikan Ubangiji a Bokim

1 Mala'ikan Ubangiji ya haura daga Gilgal zuwa Bokim. Ya ce wa Isra'ilawa, “Ni na kawo ku daga Masar zuwa ƙasar da na rantse zan ba kakanninku. Na kuma ce, ‘Ba zan ta da madawwamin alkawarina da ku ba. 2 Ku kuma ba za ku yi alkawari da mazaunan ƙasar nan ba, amma za ku rurrushe bagadansu.’ Duk da haka ba ku yi biyayya da maganata ba. Me ke nan kuka yi? 3 Don haka na ce, ‘Ba zan kore muku su ba, amma za su zamar muku ƙaya, gumakansu kuwa za su zamar muku tarko.’ ” 4 Da mala'ikan Ubangiji ya faɗa wa Isra'ilawa wannan magana, suka yi kuka mai zafi. 5 Saboda haka suka sa wa wuri suna Bokim, wato waɗanda suke kuka. Suka kuma miƙa sadakoki ga Ubangiji a wurin.

Rasuwar Joshuwa

6 Da Joshuwa ya sallami Isra'ilawa, kowane mutum ya tafi domin ya ɗauki gādonsa, don ya mallaki tasa ƙasa. 7 Isra'ilawa kuwa suka bauta wa Ubangiji dukan kwanakin Joshuwa, bayan rasuwarsa kuma suka bauta wa Ubangiji dukan kwanakin dattawan da suka ga dukan manyan ayyukan da Ubangiji ya yi domin Isra'ilawa. 8 Bawan Ubangiji, Joshuwa ɗan Nun, ya rasu yana da shekara ɗari da goma. 9 Suka binne shi a Timnat-sera a ƙasar tuddai ta Ifraimu, arewa da dutsen Ga'ash, a ƙasar gādonsa. 10 Dukan tsarar Joshuwa sun rasu, waɗanda suke tasowa kuwa suka manta da Ubangiji da abubuwan da ya yi wa Isra'ila.

Isra'ilawa sun bar Yi wa Ubangiji Sujada

11 Jama'ar Isra'ila kuwa suka yi wa Ubangiji zunubi, wato suka bauta wa gunkin nan mai suna Ba'al. 12 Suka bar yi wa Ubangiji Allah na kakanninsu sujada, wanda ya fisshe su daga ƙasar Masar. Suka fara yi wa allolin mutanen da suke zaune kewaye da su sujada. Suka rusuna wa allolin, da haka suka sa Ubangiji ya yi fushi. 13 Suka bar yi wa Ubangiji sujada suka bauta wa gumakan nan, wato Ba'al da Ashtarot. 14 Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa, ya bashe su ga waɗanda za su washe su. Ya sa magabtansu da suke kewaye da su suka sha ƙarfinsu, har ya zama Isra'ilawa ba su iya kāre kansu daga maƙiyansu ba. 15 A duk sa'ad da suka tafi yaƙi sai Ubangiji ya yi gāba da su kamar dai yadda ya faɗa. Saboda haka suka shiga wahala ƙwarai. 16 Sa'an nan Ubangiji ya naɗa musu mahukunta masu ƙarfi da suka cece su daga waɗanda suka washe su. 17 Duk da haka ba su kasa kunne ga mahukuntan ba. Suka yi wa Ubangiji ha'inci, suka yi wa waɗansu alloli sujada. Kakanninsu sun bi umarnin Ubangiji amma wannan tsara nan da nan suka bar yin haka ɗin. 18 Sa'ad da Ubangiji ya naɗa musu mahukunci, yakan taimake shi, ya kuwa cece su daga abokan gāba dukan kwanakin mahukuncin. Gama Ubangiji ya ji ƙansu saboda nishinsu, da zaluncin da ake yi musu. 19 Amma idan mahukuncin ya rasu, sai su sāke kaucewa, su yi zunubi fiye da na kakanninsu. Suna bin gumaka, suna bauta musu, suna kuma yi musu sujada, ba su daina mugayen ayyukansu na rashin aminci da taurin zuciya ba. 20 Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa ya ce, “Saboda al'umman nan ta ta da alkawarina wanda na yi da kakanninsu, ba su yi biyayya da maganata ba, 21 don haka daganan gaba ba zan ƙara kore musu wata al'umma daga cikin al'umman da Joshuwa ya rage kafin rasuwarsa ba. 22 Da haka ne zan jarraba Isra'ilawa, in gani ko za su mai da hankali su yi tafiya cikin hanyata, kamar yadda kakanninsu suka yi, ko kuwa ba za su yi ba.” 23 Don haka Ubangiji ya bar waɗannan al'ummai, bai kore su nan da nan ba, bai kuma ba da su ga Joshuwa ba.

Littafin Mahukunta 3

Al'umman da suka Ragu don a Jarraba Isra'ilawa

1 Ubangiji ya bar waɗansu al'ummai a ƙasar domin ya jarraba Isra'ilawan da ba su san yaƙin Kan'ana ba. 2 Ya yi haka ne domin ya koya wa tsararrakin Isra'ila yaƙi, wato waɗanda ba su taɓa yin yaƙi a dā ba. 3 Al'umman da suka ragu a ƙasar su ne, birane biyar na Filistiyawa, da dukan Kan'aniyawa, da Sidoniyawa, da Hiwiyawa da suke zaune a Dutsen Lebanon, tun daga Dutsen Ba'alharmon har zuwa mashigin Hamat, 4 don a jarraba Isra'ilawa da su, a gani ko za su yi biyayya da umarnan Ubangiji da ya ba kakanninsu ta hannun Musa. 5 Saboda haka jama'ar Isra'ila suka zauna tare da Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa. 6 Suka yi aurayya da su, suka kuma yi sujada ga gumakansu.

Otniyel ya Ceci Isra'ilawa

7 Jama'ar Isra'ila kuwa suka manta da Ubangiji Allahnsu, suka yi masa zunubi, suka yi wa gumakan nan Ba'al da Ashtarot sujada. 8 Domin haka Ubangiji ya husata ƙwarai da Isra'ilawa, sai ya bashe su ga Kushanrishatayim, Sarkin Mesofotamiya. Jama'ar Isra'ila kuwa suka bauta masa shekara takwas. 9 Amma sa'ad da Isra'ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, sai Ubangiji ya ta da Otniyel, ɗan Kenaz, ƙanen Kalibu don ya ceci Isra'ilawa. 10 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko masa domin ya hukunta Isra'ilawa. Ya fita ya yi yaƙi da Kushan-rishatayim, Sarkin Mesofotamiya. Ubangiji kuwa ya ba da sarkin a hannun Otniyel, ya rinjaye shi. 11 Ƙasar ta sami zaman lafiya shekara arba'in sa'an nan Otniyel, ɗan Kenaz ya rasu.

Ehud ya Ceci Isra'ilawa daga Mowabawa

12 Jama'ar Isra'ila kuma suka sāke yin zunubi a gaban Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa Eglon Sarkin Mowab ya yi ƙarfi, domin ya yi gaba da su. 13 Sai ya tattaro Amoriyawa da Amalekawa, ya je ya ci Isra'ilawa, ya mallaki birnin dabino, wato Yariko. 14 Isra'ilawa suka bauta wa Eglon Sarkin Mowab, shekara goma sha takwas. 15 Amma sa'ad da Isra'ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, ya ba su wanda zai cece su, wato Ehud, ɗan Gera daga kabilar Biliyaminu, shi kuwa bahago ne. Isra'ilawa suka aika wa Eglon Sarkin Mowab da kyautai ta hannun Ehud. 16 Sai Ehud ya ƙera wa kansa takobi mai kaifi biyu, tsawonsa kamu guda. Ya yi ɗamara da shi wajen cinyarsa ta dama a ƙarƙashin tufafinsa. 17 Sa'an nan ya ɗauki kyautan, ya kai wa Eglon Sarkin Mowab. Eglon kuwa mai ƙiba ne. 18 Da Ehud ya gama ba shi kyautan, sai ya sallami mutanen da suka ɗauko kyautan. 19 Amma Ehud ya juya ya koma daga wajen sassaƙaƙƙun duwatsu kusa da Gilgal, ya ce wa Eglon, “Ranka ya daɗe, na kawo maka saƙo na asiri.” Sai sarki ya ce wa fādawansa, “Ku ba mu wuri!” Dukansu kuwa suka fita, suka ba da wuri. 20 Ehud kuwa ya je wurinsa, yana zaune shi kaɗai a jinkakken shirayi mai sanyi. Sai Ehud ya ce, “Ina da saƙo daga wurin Allah zuwa gare ka!” Sarki kuwa ya tashi daga inda yake zaune, 21 Ehud ya sa hannun hagunsa, ya zaro takobin da yake wajen cinyarsa ta dama, ya kirɓa masa a ciki. 22 Takobin ya shiga duk da ƙotar, kitse ya rufe ruwan takobin gama bai zare takobin daga cikin sarkin ba. Ƙazanta kuwa ta fita. 23 Ehud kuwa ya fita ta shirayin, ya kukkulle ƙofofin ɗakin. 24 Bayan da ya tafi, fādawan suka zo, suka ga ƙofofin ɗakin suna a kulle, sai suka zaci sarkin ya zaga ne ya yi bawali. 25 Suka yi ta jira har suka gaji. Da suka ga dai bai buɗe ba, suka ɗauki mabuɗi, suka buɗe, sai ga ubangijinsu a ƙasa matacce. 26 Sa'ad da suke ta jira, Ehud ya riga ya tsere, ya wuce sassaƙaƙƙun duwatsu zuwa Seyira. 27 Da ya isa can sai ya busa ƙaho a ƙasar tudu ta Ifraimu. Jama'ar Isra'ila kuwa suka gangara tare da shi daga ƙasar tudu. Yana kan gaba. 28 Sai ya ce musu, “Ku biyo ni, gama Ubangiji ya ba da Mowabawa maƙiyanku a gare ku.” Suka gangara, suna biye da shi. Suka ƙwace wa Mowabawa mashigan Urdun, suka hana kowa wucewa. 29 A lokacin ne suka kashe ƙarfafan mutane na Mowabawa mutum wajen dubu goma (10,000 ), ba wanda ya tsira. 30 A ranar nan Isra'ilawa suka rinjayi Mowabawa. Ƙasar kuwa ta sami zaman lafiya har shekara tamanin.

Shamgar ya Ceci Isra'ilawa daga Filistiyawa

31 Bayan Ehud kuma, sai Shamgar ɗan Anat, wanda ya kashe Filistiyawa ɗari shida da tsinken korar shanun noma, shi ma ya ceci Isra'ilawa.

Littafin Mahukunta 4

Debora da Barak sun Ci Sisera

1 Bayan rasuwar Ehud, Isra'ilawa suka sāke yin zunubi a gaban Ubangiji. 2 Ubangiji kuwa ya yarda Yabin Sarkin Kan'ana, wanda yake mulkin Hazor ya ci su da yaƙi. Sisera, wanda yake zaune a Haroshet ta al'ummai, shi ne shugaban sojojin Yabin. 3 Sa'an nan jama'ar Isra'ila suka yi kuka ga Ubangiji suna neman taimako, gama Yabin yana da karusai ɗari tara na ƙarfe, ya kuma tsananta wa Isra'ilawa, ya mugunta musu shekara ashirin. Isra'ilawa kuwa suka yi kuka ga Ubangiji domin ya taimake su. 4 Debora, matar Lafidot, ita ce annabiya. Tana hukuncin Isra'ilawa. 5 Ta zauna a gindin giginyar Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Ifraimu. Isra'ilawa sukan haura zuwa wurinta don ta yi musu shari'a. 6 Sai ta aika a kirawo Barak, ɗan Abinowam, daga birnin Kedesh a ƙasar Naftali. Ta ce masa, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ba ka wannan umarni, ya ce, ‘Ka tafi ka tara mutanenka a Dutsen Tabor, ka kuma ɗauki mutum dubu goma (10,000 ), daga kabilar Naftali da ta Zabaluna. 7 Ni kuwa zan jawo Sisera, shugaban sojojin Yabin, da karusansa, da ƙungiyoyin sojojinsa ya yi karo da kai a Kogin Kishon, zan kuwa bashe shi a hannunka.’ ” 8 Barak ya ce mata, “Idan za ki tafi tare da ni, zan tafi, amma idan ba za ki tafi tare da ni ba, ni ma ba zan tafi ba.” 9 Sai ta ce masa, “Hakika zan tafi tare da kai, amma darajar wannan tafiya ba za ta zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Debora kuwa ta tashi, ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh. 10 Barak kuwa ya kirawo kabilar Zabaluna da ta Naftali zuwa Kedesh. Mutum dubu goma (10,000 ) suka rufa masa baya, Debora kuwa ta haura tare da shi. 11 Eber, Bakene, kuwa, ya ware daga Keniyawa, zuriyar Hobab, surukin Musa, ya kafa alfarwarsa can nesa wajen oak a Za'anannim wanda yake kusa da Kedesh. 12 Aka faɗa wa Sisera cewa, Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa Dutsen Tabor. 13 Sai Sisera ya tattaro karusansa na ƙarfe duka guda ɗari tara, da dukan mutanen da suke tare da shi, tun daga Haroshet ta al'ummai, har zuwa Kogin Kishon. 14 Debora ta ce wa Barak, “Tashi! Gama wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka, gama Ubangiji yana bi da kai!” Sai Barak ya gangaro daga Dutsen Tabor da mutum dubu goma (10,000 ) biye da shi. 15 Ubangiji kuwa ya sa Barak ya yi kaca-kaca da Sisera, da karusansa duka, da rundunar mayaƙansa duka da takobi. Sisera kuwa ya sauka daga karusarsa, ya gudu da ƙafa. 16 Amma Barak ya runtumi karusan da rundunar har zuwa Haroshet ta al'ummai. Aka kashe dukan rundunar Sisera da takobi, ba wanda ya tsira. 17 Amma Sisera ya gudu da ƙafa zuwa alfarwar Yayel matar Eber, Bakene, gama akwai jituwa tsakanin Yabin Sarkin Hazor da gidan Eber, Bakene. 18 Sai Yayel ta fito, ta taryi Sisera, ta ce masa, “Shigo nan, ubangijina, kada ka ji tsoro.” Ya kuwa bi ta zuwa cikin alfarwa, ta ɓoye shi bayan labule. 19 Ya ce mata, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa kaɗan in sha, gama ina jin ƙishi.” Ta kuwa buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, ta kuma lulluɓe shi. 20 Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar alfarwar, idan wani ya zo ya tambaye ki, ‘Ko akwai wani a nan?’ Sai ki ce, ‘Babu.’ ” 21 Amma Yayel, matar Eber, ta ɗauki turken alfarwa da guduma, ta yi sanɗa zuwa wurinsa, ta kafa masa turken a gindin kunne, ya zarce har ƙasa, a sa'ad da yake sharar barcin gajiya. Ya kuwa mutu. 22 Barak kuwa yana bin sawun Sisera. Da Yayel ta gan shi, sai ta fita, ta tarye shi, ta ce masa, “Ka zo, zan nuna maka inda mutumin da kake nema yake.” Ya shiga alfarwarta, sai ga Sisera nan kwance matacce da turke a gindin kunnensa. 23 A wannan rana Allah ya fatattaki Yabin Sarkin Kan'ana, a gaban Isra'ilawa. 24 Isra'ilawa suka yi ta tsananta wa Yabin Sarkin Kan'ana har suka hallaka shi.

Littafin Mahukunta 5

Waƙar Debora da Barak

1 A wannan rana Debora da Barak, ɗan Abinowam, suka raira wannan waka, 2 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Isra'ilawa suka ƙudura su yi yaƙi. Mutane suka sa kansu da farin ciki. Alhamdu lillahi! 3 Ku kasa kunnenku ya ku sarakuna, Ku lura, ya ku hakimai, Zan raira waƙa in yi kaɗe-kaɗe ga Ubangiji, Allah na Isra'ila. 4 Ya Ubangiji, sa'ad da ka bar duwatsun Seyir, Sa'ad da ka fito daga jihar Edom, Ƙasa ta girgiza, Ruwan sama ya zubo daga sararin sama, I, gizagizai suka kwararo da ruwa. 5 Duwatsu suka girgiza a gaban Ubangijin Sina'i, A gaban Ubangiji, Allah na Isra'ila. 6 A zamanin Shamgar ɗan Anat, a zamanin Yayel, Ayarori suka daina bi ta ƙasar, Matafiya suka bi ta ƙananan hanyoyi. 7 Garuruwan Isra'ila, ba kowa ciki, Ba kowa ciki, sai da na zo. Na zo kamar uwa ga Isra'ila, 8 Sa'ad da Isra'ilawa suka zaɓi baƙin alloli, Sai ga yaƙi a ƙasar. Ba a ga garkuwa ko mashi A wurin mutum dubu arba'in na Isra'ila ba. 9 Zuciyata tana wajen shugabannin yaƙi na Isra'ila, Da mutanen da suka ba da kansu da farin ciki. Yabo ya tabbata ga Ubangiji! 10 Ku ba da labari, Ku da kuke haye da fararen jakuna, Kuna zaune a shimfiɗu, Ku da dole ku tafi da ƙafa duk inda za ku. 11 Ku kasa kunne! Da hayaniya mutane a bakin rijiyoyi Suna ba da labarin nasarar Ubangiji, Wato nasarar jama'ar Isra'ila! Sa'an nan jama'ar Ubangiji Suna tahowa daga biranensu. 12 Ki ja gaba, ke Debora, ki ja gaba! Ki ja gaba! Ki raira waƙa, ki ja gaba! Ka ci gaba, kai Barak, Ɗan Abinowam, ka tasa kamammunka gaba! 13 Sa'an nan amintattu sun zo wurin shugabanninsu, Jama'ar Ubangiji suka zo wurina a shirye domin yaƙi. 14 Daga Ilraimu mutane suka gangaro zuwa kwari, Bayan kabilar Biliyaminu da mutanenta. Daga Makir shugabannin sojoji suka zo, Daga Zabaluna kuma jarumawa suka gangaro. 15 Shugabannin Issaka suna tare da Debora, Hakika, Issaka ya zo, Barak kuma ya zo, Suka bi bayansu zuwa kwari. Amma kabilar Ra'ubainu ta rarrabu, Ba su shawarta su zo ba. 16 Don me suka tsaya daga baya tare da tumaki? Don su saurari makiyaya na kiran garkuna? Hakika kabilar Ra'ubainu ta rarrabu, Ba su shawarta su zo ba. 17 Kabilar Gad suna tsaya a gabashin Urdun, Kabilar Dan kuma ta tsaya a wuraren kiwo. Kabilar Ashiru ta zauna a bakin teku, Sun zauna a gefen teku. 18 Amma mutanen Zabaluna da na Naftali Suka kasai da ransu a bakin dāga. 19 Sarakuna suka zo, suka yi yaƙi a Ta'anak, A rafin Magiddo. Sarakunan Kan'ana suka yi yaƙi, Amma ba su kwashe azurfa ba. 20 Daga sama, taurari suka yi yaƙi, Suna gilmawa a sararin sama Suka yi yaƙi da Sisera. 21 Ambaliyar Kishon ta kwashe su, Wato tsohon Kogin Kishon. Zan yi gaba, in yi gaba da ƙarfi! 22 Sa'an nan dawakai sun yi ta rishi Suna ƙwaƙular ƙasa da kofatansu. 23 Mala'ikan Ubangiji ya ce, “Ka la'anta Meroz, Ka la'anta mazauna cikinta sosai, Gama ba su kawo wa Ubangiji gudunmawa ba, Su zo su yi yaƙi kamar sojoji dominsa.” 24 Wadda ta fi kowa sa'a daga cikin mata, sai Yayel, Matar Eber, Bakene, Wadda ta fi kowa sa'a daga cikin matan da suke a alfarwai. 25 Sisera ya roƙi ruwan sha, Sai ta ba shi madara, Ta kawo masa kindirmo a kyakkyawar ƙwarya. 26 Ta ɗauki turken alfarwa a hannunta, Ta riƙe guduma a guda hannun, Ta bugi Sisera, kansa ya fashe, Ta kwankwatse kansa, ya ragargaje. 27 Ya fāɗi a gwiwoyinta, Ya fāɗi ƙasa, yana kwance shiru a ƙafafunta. A ƙafafunta ya sunkuya ya fāɗi, Ya fāɗi matacce har ƙasa. 28 Mahaifiyar Sisera ta duba ta tagogi, Ta leƙa ta kariyar taga, ta ce, “Me ya sa karusarsa ta yi jinkirin zuwa? Don me dawakansa ba su komo da wuri ba?” 29 'Yan matanta mafi hikima suka amsa mata, Ita kuwa ta yi nanatawa, tana cewa, 30 “Nema suke kurum su sami ganima, su raba, Yarinya ɗaya ko biyu domin kowane soja, Tufafi masu tsada domin Sisera, Rinannun tufafi masu ado domin sarauniya.” 31 Ta haka, ya Ubangiji ka sa maƙiyanka su mutu, Amma abokanka su haskaka kamar fitowar rana! Ƙasar kuwa ta zauna lafiya shekara arba'in.

Littafin Mahukunta 6

Kiran Gidiyon

1 Jama'ar Isra'ila kuma suka sāke yin zunubi a gaban Ubangiji, sai Ubangiji ya ba da su ga Madayanawa su mallake su shekara bakwai. 2 Madayanawa kuwa sun fi Isra'ilawa ƙarfi, saboda haka Isra'ilawa suka yi ta ɓuya a kogon dutse, da waɗansu wuraren ɓuya a tsaunuka. 3 Duk lokacin da Isra'ilawa suka yi shuka, sai Madayanawa, da Amalekawa, da waɗansu kabilai na hamada su zo su fāɗa musu. 4 Sukan zo su kafa musu sansani, su ɓaɓɓata amfanin ƙasar har zuwa kusa da Gaza. Ba su barin wani abinci a ƙasar Isra'ila, domin Isra'ilawa ko dabbobinsu. 5 Gama sukan zo da dabbobinsu da alfarwansu da yawa, kamar fara. Su da raƙumansu ba su ƙidayuwa, sukan zo, su lalatar da ƙasar. 6 Isra'ilawa suka sha ƙasƙanci ƙwarai a hannun Madayanawa. Sai suka yi kuka ga Ubangiji domin ya taimake su. 7 Da Isra'ilawa suka yi kuka ga Ubangiji saboda wahalar da Madayanawa suke ba su, 8 sai Ubangiji ya aika musu da wanda ya faɗa musu saƙon Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya ce, “Ni ne na fito da ku daga bauta a Masar. 9 Na cece ku daga Masarawa, da kuma waɗanda suka yi yaƙi da ku a nan. Na kore su a gabanku, na ba ku ƙasarsu. 10 Na faɗa muku, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku, kada ku bauta wa gumakan Amoriyawa, waɗanda kuke zaune a ƙasarsu.’ Amma ba ku yi biyayya da maganata ba.” 11 Mala'ikan Ubangiji ya zo, ya zauna a gindin itacen oak na Yowash mutumin Abiyezer, a ƙauyen Ofra. Ɗansa Gidiyon kuwa yana susukar alkama daga ɓoye, a wurin da ake matse ruwan inabi, don ya ɓuya daga Madayanawa. 12 Mala'ikan Ubangiji kuwa ya bayyana gare shi, ya ce, “Kai jarumi ne, Ubangiji kuma yana tare da kai.” 13 Sai Gidiyon ya ce masa, “Ya shugabana, idan Ubangiji yana tare da mu, me ya sa abubuwan nan suka same mu? Ina kuma ayyukansa masu ban al'ajabi waɗanda kakanninmu suka faɗa mana cewa, ‘Ai, Ubangiji ne ya fisshe mu daga Masar?’ Amma yanzu Ubangiji ya yi watsi da mu, ya ba da mu ga Madayanawa.” 14 Ubangiji ya ce masa, “Tafi da dukan ƙarfinka, ka ceci Isra'ilawa daga Madayanawa. Ni kaina na aike ka.” 15 Gidiyon ya amsa ya ce, “Ubangiji, yaya zan yi in ceci Isra'ilawa? Ga shi, dangina ne mafi ƙanƙanta a kabilar Manassa, ni ne kuma ƙarami a gidanmu.” 16 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Za ka iya, gama zan taimake ka. Za ka muttsuke Madayanawa kamar mutum guda.” 17 Gidiyon kuwa ya ce masa, “Idan ka amince da ni, ka nuna mini alama don in sani kai kake magana da ni. 18 Ina roƙonka, kada ka tashi daga nan, sai na kawo maka hadaya ta abinci.” Ya amsa cewa, “Zan tsaya har ka kawo.” 19 Gidiyon ya tafi gida, ya yanka ɗan akuya, ya dafa, ya yi waina marar yisti ta gāri mudu guda. Ya sa naman a kwandon, romon kuwa ya zuba a tukunya, ya kawo, ya miƙa masa a gindin itacen oak. 20 Mala'ikan Allah kuma ya ce masa, “Ɗauki naman da wainar marar yisti ka sa a kan dutsen nan, sa'an nan ka zuba romon a kai.” Haka kuwa ya yi. 21 Mala'ikan Ubangiji kuwa ya miƙa kan sandan da yake hannunsa, ya taɓa naman da wainar, sai wuta ta fito daga dutsen ta cinye naman da wainar. Mala'ikan Ubangiji kuwa ya ɓace masa. 22 Da Gidiyon ya gane mala'ikan Ubangiji ne, sai ya ce, “Kaitona, Ubangiji Allah, gama na ga mala'ikan Ubangiji fuska da fuska.” 23 Amma Ubangiji ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, ba za ka mutu ba.” 24 Gidiyon kuwa ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya sa masa suna, Ubangiji Salama Ne. Har wa yau bagaden yana nan a Ofra, ta iyalin Abiyezer. 25 A wannan dare Ubangiji ya ce masa, “Ka ɗauki bijimin mahaifinka, da wani bijimin bana bakwai. Sa'an nan ka rushe bagaden gunkin nan Ba'al na mahaifinka, ka sare gumakan da suke kusa da shi. 26 Sa'an nan ka gina wa Ubangiji Allahnka bagade mai kyau a kan wannan kagara. Ka ɗauki bijimi na biyu ka miƙa shi hadayar ƙonawa da itacen gumakan da za ka sare.” 27 Gidiyon fa ya ɗauki mutum goma daga cikin barorinsa, ya yi yadda Ubangiji ya faɗa masa. Amma domin yana tsoron, mutanen gidansa da na gari, bai yi wannan da rana ba, sai da dare. 28 Da mutanen garin suka tashi da safe, sai ga bagaden Ba'al a farfashe, gumakan kuma da suke kusa da shi, an sare. Bijimi na biyu kuma, an miƙa shi hadaya a kan bagaden da aka gina. 29 Suka ce wa juna, “Wa ya yi wannan abu?” Da suka binbincika, sai suka tarar Gidiyon ne, ɗan Yowash, ya yi shi. 30 Sai suka ce wa Yowash, “Ka kawo ɗanka a kashe, gama ya rushe bagaden gunkin nan Ba'al, ya kuma sare gumakan da suke kusa da shi.” 31 Yowash kuwa ya ce wa dukan waɗanda suka tasar masa, “Za ku yi hamayya domin gunkin nan Ba'al, ko kuwa za ku goyi bayansa? Duk wanda ya yi hamayya dominsa za a kashe shi da safe. Idan shi allah ne, to, bari ya yi hamayya don kansa, gama an farfashe bagadensa.” 32 A ranar nan aka laƙaba wa Gidiyon suna Yerubba'al, wato “Bari gunki Ba'al ya yi hamayya don kansa, domin an farfashe bagadensa.” 33 Dukan Madayanawa kuwa, da Amalekawa, da mutanen gabas suka tattaru. Suka haye, suke kafa sansaninsu a kwarin Yezreyel. 34 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko a kan Gidiyon, sai ya busa ƙaho, mutanen Abiyezer suka bi shi. 35 Ya kuma aiki manzanni a ƙasar Manassa duka. Su kuma aka kirawo su su bi shi. Ya kuma aiki manzanni zuwa ga Ashirawa da Zabalunawa, da Naftaliyawa, su kuma suka zo, suka haɗa kai da shi. 36 Sa'an nan Gidiyon ya ce wa Allah, “Ka ce za ka sa ni in ceci Isra'ilawa. 37 To, zan shimfiɗa uku a masussuka. Idan da safe akwai raɓa a kan ulun kaɗai, ƙasa kuwa a bushe, sa'an nan zan sani za ka ceci Isra'ilawa ta hannuna kamar yadda ka faɗa.” 38 Haka kuwa ya zama Kashegari Gidiyon ya tashi da sassafe, sai ya matse ulun, ruwan raɓa da ya matse daga ulun kuwa, ya cika ƙwarya. 39 Gidiyon kuma ya ce wa Allah, “Ina roƙonka, kada ka yi fushi da ni, bari in ƙara magana sau ɗaya kurum, wato in sāke yin gwaji da ulun. Ina roƙonka ka sa a yi raɓa a ƙasa, amma kada ta taɓa ulun.” 40 Haka kuwa Allah ya yi a daren. Aka yi raɓa a ƙasa, amma ulun yana a bushe.

Littafin Mahukunta 7

Gidiyon ya Ci Madayanawa

1 Sai Yerubba'al, wato Gidiyon, da mutanen da suke tare da shi suka yi sammako, suka kafa sansaninsu kusa da maɓuɓɓugan Harod. Madayanawa kuwa suka kafa sansaninsu a arewa da su, kusa da tudun More a kwarin. 2 Ubangiji kuwa ya ce wa Gidiyon, “Mutanen da suke tare da kai sun yi yawa da zan ba da Madayanawa a hannunsu, kada ya zama Isra'ilawa su yi mini fāriya, su ce, ‘Ƙarfinmu ne ya cece mu.’ 3 Yanzu sai ka ce wa mutanen, ‘Duk mai jin tsoro da mai rawar jiki, ya koma gida!’ ” Da Gidiyon ya gwada su, mutum dubu ashirin da biyu (22,000 ) suka koma, dubu goma (10,000 ) suka tsaya. 4 Ubangiji ya ce wa Gidiyon, “Har yanzu mutanen sun yi yawa. Ka kai su bakin rafi domin in jarraba maka su a can. Wanda na faɗa maka shi zai tafi tare da kai, to, shi ne zai tafi, wanda kuma na faɗa ba zai tafi tare da kai ba, to, ba zai tafi ba.” 5 Gidiyon ya kai mutanen bakin rafi, Ubangiji kuwa ya ce wa Gidiyon, “Duk wanda ya tanɗi ruwa kamar kare, sai ka ware shi waje ɗaya. Wanda kuma ya durƙusa ya sha ruwa, ka ware shi waje ɗaya.” 6 Yawan waɗanda suka tanɗi ruwa su ɗari uku ne. Sauran mutane duka kuwa sun durƙusa ne suka sha ruwan. 7 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Gidiyon, “Da mutum ɗari uku ɗin nan da suka tanɗi ruwa zan cece ku. Zan ba da Madayanawa a gare ku, ka sallami sauran, kowa ya koma gidansa.” 8 Mutane suka ɗauki guzuri da ƙahoni, Gidiyon kuwa ya sallami sauran mutane, amma ya bar mutum ɗari uku ɗin nan. Sansanin Madayanawa kuwa yana ƙasa da su a kwarin. 9 A wannan dare sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi, ka tafi sansanin Madayanawa, gama na ba da su gare ka. 10 Amma idan kana jin tsoro ka tafi kai kaɗai, ka tafi tare da Fura, baranka. 11 Za ka ji abin da suke cewa. Bayan haka za ka sami ƙarfin hali da za ka tafi ka fāda wa sansaninsu.” Gidiyon kuwa ya tafi tare da Fura baransa a gefen sansanin abokan gāba. 12 Madayanawa, da Amalekawa, da mutanen gabas duka suna nan da yawa a shimfiɗe cikin kwarin, kamar fara. Raƙumansu kuma suna da yawa kamar yashi a bakin teku. Ba wanda zai iya ƙidaya su. 13 Sa'ad da Gidiyon ya tafi, sai ya ji wani yana faɗa wa abokinsa mafarkin da ya yi. Ya ce, “Na yi mafarki, na ga wainar sha'ir ta faɗo a tsakiyar sansaninmu. Ta zo ta bugi alfarwa. Alfarwar kuwa ta fāɗi rigingine.” 14 Abokinsa ya amsa, ya ce, “Ai, ba wani abu ba ne. Wannan takobin Gidiyon ne, ɗan Yowash. Ba'isra'ile! Allah ya ba shi nasara kan Madayanawa da dukan rundunanmu!” 15 Da Gidiyon ya ji mafarkin, har da fassarar, sai ya yi sujada, ya koma a sansaninsu na Isra'ilawa. Da ya isa, sai ya ce, “Ku tashi, gama Ubangiji ya ba da rundunar Madayanawa a gare ku.” 16 Sai ya raba mutum ɗari uku ɗin kashi uku, ya ba kowannensu ƙaho, da tulu, da jiniya a cikin tulun. 17 Sa'an nan ya ce musu, “Sa'ad da muka kai sansani, sai ku dube ni, ku yi duk abin da nake yi. Yadda na yi, ku ma ku yi haka. 18 Sa'ad da ni da dukan waɗanda suke tare da ni muka busa ƙahoni, sai ku kuma ku busa ƙahonin a kowane gefen sansani, sa'an nan ku yi ihu, ku ce, ‘Ubangiji da Gidiyon!’ ” 19 Gidiyon da mutum ɗari da suke tare da shi, suka kai gefen sansanin wajen tsakiyar dare, bayan an sauya matsara. Sai suka busa ƙahonin, suka fasa tulunan da suke a hannuwansu. 20 Ƙungiyoyi uku ɗin nan suka busa ƙahonin, suka fasa tuluna. Suka riƙe jiniyoyi a cikin hannuwansu na hagu, da ƙahonin busawa a hannuwansu na dama. Sai suka yi kuwwa, suka ce, “Takobin Ubangiji da na Gidiyon!” 21 Kowannensu ya yi tsaye a inda yake kewaye da sansanin. Dukan rundunar Madayanawa kuwa suka gudu, suna ihu. 22 Da suka busa ƙahonin nan ɗari uku, sai Ubangiji ya sa Madayanawa suka yi ta sassare junansu da takuba. Suka gudu zuwa Zerera har Bet-shitta, har kuma zuwa garin Abel-mehola, kusa da Tabbat. 23 Jama'ar kabilar Naftali, da Ashiru, da Manassa, suka ji kira, suka fito, suka runtumi Madayanawa. 24 Gidiyon kuma ya aika a dukan ƙasar tudu ta Ifraimu, ya ce musu, “Ku gangaro, ku yaƙi Madayanawa, ku tare mashigan Kogin Urdun da rafuffuka, har zuwa Bet-bara.” Aka kuwa kira dukan Ifraimawa, su kuwa suka hana wa Madayanawa mashigan Kogin Urdun da rafuffuka, har zuwa Bet-bara. 25 Suka kama sarakunan Madayanawa biyu, Oreb da Ziyib. Suka kashe Oreb a kan dutsen Oreb, Ziyib kuwa suka kashe shi a wurin matsewar ruwan inabi na Ziyib a lokacin da suke runtumar Madayanawa. Sai suka kawo wa Gidiyon kan Oreb da na Ziyib a inda yake a gabashin Urdun.

Littafin Mahukunta 8

1 Mutanen Ifraimu suka ce wa Gidiyon, “Me ke nan ka yi mana, da ba ka kirawo mu lokacin da ka tafi yaƙi da Madayanawa ba?” Suka yi masa gunaguni ƙwarai. 2 Amma ya ce musu, “Yanzu, me na yi fiye da ku? Ai, kalar inabin Ifraimu ta fi dukan girbin Abiyezer, wato ɗan abin da kuka yi ya fi wanda kabilata ta yi nesa. 3 Ga shi, Allah ya ba da Oreb da Ziyib sarakunan Madayanawa a gare ku. To, me na yi wanda ya fi naku?” Da ya faɗi haka, sai suka huce.

Nasara ta Ƙarshe a kan Madayanawa

4 Da Gidiyon ya zo Urdun sai ya haye tare da mutum ɗari uku ɗin nan da suke tare da shi. Ko da yake sun gaji, duk da haka suka yi ta runtumar magabta. 5 Gidiyon ya ce wa mutanen Sukkot, “Ina roƙonku, ku ba mutanen da suke tare da ni abinci, gama sun gaji, ga shi kuwa, ina runtumar Zeba da Zalmunna, sarakunan Madayanawa.” 6 Shugabannin Sukkot kuwa suka ce, “Ba ka riga ka kama Zeba da Zalmunna ba, ta yaya za mu ba sojojinka abinci?” 7 Gidiyon ya ce, “To, sa'ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayuwan jeji.” 8 Daga can ya tafi Feniyel, ya roƙe su yadda ya roƙi mutanen Sukkot. Mutanen Feniyel kuma suka amsa masa daidai yadda mutanen Sukkot suka amsa masa. 9 Sai Gidiyon ya ce wa mutanen Feniyel, “Sa'ad da na dawo cikin salama, zan rushe wannan hasumiya.” 10 Zeba da Zalmunna kuwa suna Karkor tare da rundunarsu, mutum wajen dubu goma sha biyar (15,000 ), waɗanda suka ragu daga cikin rundunar mutanen gabas, gama an kashe mutum dubu ɗari da dubu ashirin (120,000 ), masu takuba. 11 Gidiyon kuwa ya bi ta hanyar gefen hamada wadda take gabas da Noba da Yogbeha, ya faɗa wa rundunar, ta yadda ba su zato. 12 Zeba da Zalmunna, sarakunan nan biyu na Madayana suka gudu, amma ya bi su, ya kamo su. Ya sa dukan rundunarsu ta gigice. 13 Sa'an nan Gidiyon, ɗan Yowash, ya komo daga yaƙin ta hanyar hawan Heres. 14 Gidiyon ya kama wani saurayi na Sukkot, ya yi masa tambayoyi. Shi kuwa ya rubuta masa sunayen sarakuna da na dattawan Sukkot, mutum saba'in da bakwai. 15 Sa'an nan ya zo wurin mutanen Sukkot ya ce musu, “To, ga Zeba da Zalmunna waɗanda kuka yi mini ba'a saboda su, kuna cewa, ‘Ba ka riga ka kama Zeba da Zalmunna ba, ta yaya za mu ba sojojinka da suka gaji abinci?’ To, ga su!” 16 Ya kama dattawan garin Sukkot ya hukunta su da ƙayayuwa. 17 Ya kuma rushe hasumiyar Feniyel, ya karkashe mutanen birnin. 18 Sa'an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka kashe a Tabor?” Suka amsa, “Kamar yadda kake, haka suke. Suna kama da 'ya'yan sarki.” 19 Gidiyon ya ce musu, “Su 'yan'uwana ne, mahaifiyarmu ɗaya. Da ba ku kashe su ba, da ba zan kashe ku ba.” 20 Ya ce wa Yeter, ɗan farinsa, “Tashi, ka kashe su.” Amma saurayin bai zare takobinsa ba, gama yana jin tsoro domin shi yaro ne. 21 Sai Zeba da Zalmunna suka ce, “Tashi da kanka, ka kashe mu, gama yadda mutum yake haka kuma ƙarfinsa yake.” Gidiyon kuwa ya tashi ya kashe Zeba da Zalmunna. Ya kwance kayan ado daga wuyan raƙumansu.

Sauran Ayyukan Gidiyon

22 Sa'an nan mutanen Isra'ila suka ce wa Gidiyon, “Ka yi mulkinmu, kai da 'ya'yanka, da jikokinka, gama ka cece mu daga hannun Madayanawa.” 23 Gidiyon ya ce musu, “Ba zan yi mulkinku ba, ɗana kuma ba zai yi mulkinku ba, Ubangiji ne zai yi mulkinku.” 24 Ya ci gaba ya ce, “Ina roƙon kowannenku ya ba ni 'yan kunne daga cikin ganimar da ya kwaso.” (Gama Madayanawa suna da 'yan kunne na zinariya, gama su mutanen hamada ne.) 25 Suka ce, “Lalle, za mu ba ka su.” Nan da nan suka shimfiɗa mayafi, kowa ya zuba 'yan kunnen da ya kwaso ganima. 26 Nauyin 'yan kunnen zinariya da ya roƙa ya kai shekel dubu ɗaya da ɗari bakwai (1,700 ), banda kayan ado, da na rataye-rataye, da tufafin shunayya waɗanda sarakunan Madayanawa suke sawa, banda ɗan gaba da yake a wuyan raƙumansu. 27 Gidiyon kuwa ya yi gunki da zinariyar, ya ajiye a birninsa, wato Ofra. Isra'ilawa kuma suka bar bin Allah, suka tafi can domin su yi wa gunkin sujada, ya zama tarko ga Gidiyon da iyalinsa. 28 Da haka Isra'ilawa suka mallaki Madayanawa har ba su zamar musu barazana ba. Ƙasar kuwa ta zauna lafiya shekara arba'in a zamanin Gidiyon.

Mutuwar Gidiyon

29 Gidiyon kuwa ya tafi ya zauna a gidansa na kansa. 30 Yana kuma da 'ya'ya maza saba'in, gama yana da mata da yawa. 31 Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take a Shekem, ta haifi masa ɗa, ya sa masa suna Abimelek. 32 Sa'an nan Gidiyon, ɗan Yowash, ya rasu da kyakkyawan tsufa. Aka binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa, a Ofra, birnin kabilar Abiyezer. 33 Bayan rasuwar Gidiyon, sai Isra'ilawa suka sāke yin rashin aminci ga Allah, suka yi wa Ba'al sujada. Suka yi Ba'al-berit ya zama allahnsu. 34 Suka daina bauta wa Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga magabtan da suke kewaye da su. 35 Ba su kuwa sāka wa iyalin Gidiyon da alheri ba, saboda dukan alherin da ya yi wa Isra'ilawa.

Littafin Mahukunta 9

Sarautar Abimelek

1 Abimelek, ɗan Yerubba'al, wato Gidiyon, ya tafi Shekem wurin dukan dangin mahaifiyarsa, ya ce musu, 2 “Ina roƙonku, ku yi magana da shugabannin Shekem, ku ce, ‘Me ya fi muku kyau, 'ya'yan Yerubba'al, maza saba'in su yi mulkinku, ko kuwa mutum ɗaya ya yi mulkinku?’ Amma ku tuna fa ni jininku ne.” 3 Sai dangin mahaifiyarsa suka yi magana da shugabannin Shekem saboda shi. Zuciyarsu kuwa ta saje da Abimelek, gama suka ce, “Shi ɗan'uwanmu ne.” 4 Suka kuma ba shi azurfa saba'in daga cikin gidan gunkin nan Ba'al-berit. Da wannan azurfa Abimelek ya yi ijarar 'yan iska waɗanda suka bi shi. 5 Ya tafi gidan mahaifinsa a Ofra, ya kashe 'yan'uwansa maza, wato 'ya'yan Yerubba'al, mutum saba'in a kan dutse guda. Amma Yotam ƙaramin ɗan Yerubba'al, shi kaɗai ya ragu domin ya ɓuya. 6 Sai shugabannin Shekem duka da na Betmillo suka taru suka naɗa Abimelek sarki kusa da itacen oak na al'amudin da yake a Shekem. 7 Da Yotam ya ji wannan sai ya tafi, ya tsaya a kan Dutsen Gerizim, da babbar murya, ya ce musu, “Ku kasa kunne gare ni ku mutanen Shekem, domin kuma Allah ya kasa kunne gare ku! 8 Wata rana itatuwa suka taru don su naɗa wa kansu sarki. Suka ce wa itacen zaitun, ‘Kai ka zama sarkinmu.’ 9 Amma itacen zaitun ya ce musu, ‘In bar maina wanda da shi ake girmama alloli da mutane, don in tafi in yi ta fama da itatuwa?’ 10 Sai kuma itatuwa suka ce wa itacen ɓaure, ‘Ka zo, ka zama sarkinmu.’ 11 Amma itacen ɓaure ya ce musu, ‘In bar kyawawan 'ya'yana masu zaƙi, don in tafi in yi ta fama da itatuwa?’ 12 Itatuwa kuma suka ce wa kurangar inabi, ‘Ki zo, ki mallake mu.’ 13 Sai kurangar inabi ta ce, ‘In bar ruwan inabina wanda yake faranta zuciyar alloli da ta mutane, don in tafi, in yi ta fama da itatuwa?’ 14 Sa'an nan dukan itatuwa suka ce wa itacen ƙaya, ‘Ka zo, ka zama sarkinmu.’ 15 Itacen ƙaya kuwa ya ce wa itatuwan, ‘In da gaske kuke, kuna so ku naɗa ni sarkinku, to, sai ku zo, ku fake a inuwata, in ba haka ba kuwa, bari wuta ta fito daga itacen ƙaya ta cinye itacen al'ul na Lebanon.’ ” 16 Yotam ya ci gaba da cewa, “Yanzu kun naɗa Abimelek sarki da zuciya ɗaya ke nan? Kun yi wa Yerubba'al da iyalinsa daidai ke nan? Wannan ne abin da ya cancance shi? 17 Ku tuna fa mahaifina ya yi yaƙi dominku. Ya kasai da ransa domin ya cece ku daga Madayanawa. 18 Amma ga shi, yau kun juya kuna gāba da gidan mahaifina. Kun kashe 'ya'yansa maza, su saba'in, a dutse guda, kuka naɗa Abimelek, ɗan da baiwa ta haifa, ya zama sarki a Shekem, don dai kawai shi ɗan'uwanku ne. 19 Yanzu dai idan abin da kuka yi wa Yerubba'al da iyalinsa daidai ne, to, sai ku yi farin ciki da Abimelek, ku sa shi kuma ya ji daɗinku. 20 Amma idan ba haka yake ba, Allah ya sa wuta ta fito daga wurin Abimelek ta cinye mutanen Shekem da na Bet-millo. Bari Allah ya sa kuma wuta ta fito daga wurin mutanen Shekem da na Bet-millo ta cinye Abimelek.” 21 Sa'an nan Yotam ya tsere. Ya tafi ya zauna a Biyer, gama yana tsoron ɗan'uwansa Abimelek. 22 Abimelek kuwa ya yi shekara uku, yana mulkin Isra'ila. 23 Ubangiji kuma ya sa husuma ta tashi tsakanin Abimelek da mutanen Shekem. Shugabannin Shekem kuwa suka tayar masa. 24 Wannan ya faru domin a ɗauki fansar jinin, 'ya'yan Yerubba'al, maza, su saba'in, a kan Abimelek ɗan'uwansu, wanda ya kashe su, da kuma a kan shugabannin Shekem, waɗanda suka taimake shi ya kashe 'yan'uwansa. 25 Shugabannin Shekem kuwa suka sa mutane su yi kwanto a kan dutwatsu gāba da Abimelek. Suka yi wa duk wanda ya bi ta wannan hanya fashi. Sai aka faɗa wa Abimelek. 26 Ga'al, ɗan Ebed, da 'yan'uwansa suka yi ƙaura zuwa Shekem. Shugabannin Shekem kuwa suka amince da shi. 27 Suka tafi gona, suka ɗebo inabi, suka matse, suka yi biki a gidan gunkinsu. Suka ci, suka sha, suka zazzagi Abimelek. 28 Ga'al, ɗan Ebed, ya ce, “Wane ne Abimelek har mu mutanen Shekem za mu bauta masa? Ashe, ba Yerubba'al ne mahaifinsa ba, Zebul kuma shugaban yaƙinsa? Don me za mu bauta masa? Ku yi aminci ga kakanku Hamor, tushen kabilarku! 29 Da ma a ce nake shugabancin mutanen nan, da sai in hamɓare Abimelek!” Sai ya ce wa Abimelek, “Ka tara yawan rundunarka ka fito.” 30 Zebul, shugaban birnin ya ji maganganun Ga'al, ɗan Ebed, sai ya husata. 31 Ya aiki jakadu wurin Abimelek a Aruma, ya ce, “Ga fa Ga'al, ɗan Ebed, da 'yan'uwansa sun zo Shekem, suna kutta garin ya tayar maka. 32 Yanzu sai ka tashi, ka zo da dare tare da mutanen da suke tare da kai, ku yi kwanto a cikin saura. 33 Sa'an nan gobe da safe, da fitowar rana, ku tashi ku fāɗa wa birnin. Idan Ga'al da mutanen da suke tare da shi, suka fito, su kara da kai, ka fatattake su yadda ka iya!” 34 Abimelek da mutanen da suke tare da shi kuwa suka tashi da dare suke yi wa Shekem kwanto da ƙungiya huɗu. 35 Ga'al, ɗan Ebed, kuwa ya fita zuwa ƙofar garin daidai lokacin da Abimelek da mutanensa suka tashi daga wurin kwantonsu. 36 Sa'ad da Ga'al ya ga mutanen, ya ce wa Zebul, “Duba, ga mutane suna zuwa daga kan duwatsu.” Sai Zebul ya ce masa, “Ai, inuwar duwatsu ce kake gani kamar mutane.” 37 Ga'al kuma ya ƙara yin magana, ya ce, “Duba, mutane suna gangarowa kan hanya, ga kuma wata ƙungiya tana zuwa daga wajen itacen oak na masu duba.” 38 Sa'an nan Zebul ya ce masa, “Ina cika bakin nan naka, kai da ka ce, ‘Wane ne Abimelek da za mu bauta masa?’ Waɗannan su ne mutanen da ka raina. Fita, ka yaƙe su mana.” 39 Ga'al kuwa ya fita ya yi jagorar shugabannin Shekem, suka yi yaƙi da Abimelek. 40 Abimelek kuwa ya runtumi Ga'al, shi kuwa ya gudu. Mutane da yawa suka ji rauni, ya bi su har bakin ƙofar birnin. 41 Sai Abimelek ya zauna a Aruma. Zebul kuwa ya kori Ga'al da 'yan'uwansa, ya hana su zama a Shekem. 42 Kashegari mutanen Shekem suka tafi saura, sai aka faɗa wa Abimelek. 43 Shi ma ya kwashi mutanensa, ya raba su ƙungiya uku, suka yi kwanto a saura. Da ya duba, ya ga mutane suna fitowa daga cikin birnin. Ya fāɗa musu, ya karkashe su. 44 Abimelek kuma da ƙungiyar da take tare da shi, suka hanzarta, suka tsare ƙofar birnin. Sauran ƙungiya biyu suka ruga, suka faɗa wa dukan waɗanda suke cikin saura, suka karkashe su. 45 Abimelek ya yi yaƙi dukan yini har ya ci birnin, ya kashe mutanen da suke cikinsa. Ya rushe birnin, ya barbaɗe shi da gishiri. 46 Da shugabannin hasumiyar Shekem suka ji labari, suka gudu zuwa hasumiyar gidan Ba'al-berit don su tsira. 47 Abimelek kuwa ya ji dukan mutanen hasumiyar Shekem sun taru wuri ɗaya. 48 Sai ya tafi da mutanen da suke tare da shi suka hau Dutsen Zalmon. Ya ɗauki gatari ya sari reshen itace, ya saɓe a kafaɗa. Ya ce wa mutanen da suke tare da shi, su yi hanzari su yi kamar yadda ya yi. 49 Kowane mutum kuwa ya sari reshen itace, ya bi Abimelek. Suka tara rassan a jikin hasumiyar. Suka sa wa hasumiyar wuta, duk da mutanen da suke cikinta. Ta haka dukan mutanen hasumiyar Shekem suka mutu, mata da maza, wajen mutum dubu. 50 Sa'an nan Abimelek ya tafi Tebez, ya kewaye ta da sansani, ya ci birnin. 51 Akwai wata hasumiya mai ƙarfi a cikin birnin, sai dukan mutanen garin, mata da maza, har da shugabannin, suka gudu zuwa cikinta, suka kulle kansu, suka hau kan rufin hasumiyar. 52 Abimelek kuwa ya zo ya yaƙi hasumiyar. Ya je kusa da ƙofar hasumiyar don ya ƙone ta. 53 Amma wata mace ta jefi Abimelek da ɗan dutsen niƙa a kā, ƙoƙon kansa ya ragargaje. 54 Nan da nan sai Abimelek ya kira saurayin da yake ɗaukar masa makamai, ya ce masa, “Ka zaro takobinka, ka kashe ni domin kada mutane su ce, ‘Mace ta kashe shi.’ ” Sai saurayin ya soki Abimelek, ya mutu. 55 Da Isra'ilawa suka ga Abimelek ya mutu, sai dukansu suka tafi gida. 56 Ta haka Allah ya saƙa wa Abimelek muguntar da ya yi wa mahaifinsa, da ya kashe 'yan'uwansa maza, su saba'in. 57 Haka kuwa Allah ya sa muguntar mutanen Shekem ta koma kansu. Bakin Yotam, ɗan Yerubba'al, kuma ya kama su.

Littafin Mahukunta 10

Tola da Yayir sun Shugabanci Isra'ilawa

1 Bayan mutuwar Abimelek, sai Tola, ɗan Fuwa, ɗan Dodo, daga kabilar Issaka ya tashi don ya ceci Isra'ilawa. Ya zauna a Shamir, a ƙasar tuddai ta Ifraimu. 2 Ya shugabanci Isra'ilawa shekara ashirin da uku, sa'an nan ya rasu. Aka binne shi a Shamir. 3 Bayansa kuma sai Yayir mutumin Gileyad, ya tashi ya shugabanci Isra'ilawa shekara ashirin da biyu. 4 Yana da 'ya'ya maza guda talatin, waɗanda suke hawan jakai talatin. Suna kuma da birane talatin a ƙasar Gileyad, waɗanda har yanzu ake kira biranen alfarwai. Ana kiran biranen Hawwot-Yayir, wato na Yayir. 5 Yayir ya rasu aka binne shi a Kamon.

Ammonawa sun Matsa wa Isra'ilawa

6 Isra'ilawa suka sāke yi wa Ubangiji zunubi. Suka yi sujada ga Ba'al da Ashtarot, allolin Suriyawa, da na Sidon, da na Mowab, da na Ammonawa, da na Filistiyawa. Suka bar bin Ubangiji, suka daina yi masa sujada. 7 Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa, ya ba da su ga Filistiyawa, da Ammonawa. 8 Suka murƙushe Isra'ilawa, suka matsa musu. Har shekara goma sha takwas suka yi ta matsa dukan Isra'ilawa da suke a hayin Urdun daga gabas, a cikin Gileyad, inda Amoriyawa suke zaune. 9 Ammonawa kuma suka haye Urdun don su yaƙi mutanen Yahuza, da na Biliyaminu, da na kabilar Ifraimu. Isra'ilawa kuwa suka matsu ƙwarai. 10 Sa'an nan Isra'ilawa suka yi kuka ga Ubangiji, suna cewa, “Mun yi maka zunubi, gama mun bar binka, ya Allahnmu, muka yi wa Ba'al sujada.” 11 Ubangiji ya amsa musu, ya ce, “Ban cece ku daga hannun Masarawa, da Amoriyawa, da Ammonawa, da Filistiyawa, 12 da Sidoniyawa, da Amalekawa, da Mawonawa ba, wato su da suka matsa muku a dā, ku kuma kuka yi kuka gare ni? 13 Amma duk da haka kuka bar bina, kuka yi sujada ga waɗansu alloli, don haka ni kuma ba zan ƙara cetonku ba. 14 Tafi, ku yi wa allolin da kuka zaɓa kuka, don su cece ku a lokacin wahalarku.” 15 Amma Isra'ilawa suka ce wa Ubangiji, “Mun yi zunubi, ka yi mana duk irin abin da ka ga dama, amma in ka yarda ka cece mu yau.” 16 Sa'an nan suka zubar da gumakan da suke wurinsu, suka yi wa Ubangiji sujada. Shi kuwa ya damu saboda azabar da Isra'ilawa suke sha. 17 Sojojin Ammonawa kuwa, suka tattaru, suka kafa sansani a Gileyad. Isra'ilawa kuma suka tattaru, suka kafa nasu sansani a Mizfa. 18 Shugabanni da mutanen Gileyad suka ce wa junansu. “Wa zai fara yaƙi da Ammonawa? Shi zai zama shugaban duk wanda yake Gileyad.”

Littafin Mahukunta 11

Yefta ya Ceci Isra'ilawa daga Hannun Ammonawa

1 Yefta mutumin Gileyad ne, shi kuwa jarumi ne, amma mahaifiyarsa karuwa ce. Gileyad ne mahaifinsa. 2 Matar Gileyad ta haifa masa 'ya'ya maza. Sa'ad da suka yi girma, sai suka kori Yefta, suka ce masa, “Ba za ka ci gādo a gidan mahaifinmu ba, gama kai ɗan wata mace ne.” 3 Sai Yefta ya gudu daga wurin 'yan'uwansa, ya zauna a ƙasar Tob. 'Yan iska kuwa suka taru wurin Yefta, sukan tafi yawo tare da shi. 4 Ana nan sai Ammonawa suka kai wa Isra'ilawa yaƙi. 5 Da haka ta auku, sai shugabannin Gileyad suka tafi su komo da Yefta daga ƙasar Tob. 6 Suka ce wa Yefta, “Ka zo, ka zama shugabanmu don mu yi yaƙi da Ammonawa.” 7 Amma Yefta ya ce wa dattawan Gileyad, “Ba ku kuka ƙi ni, kuka kore ni daga gidan mahaifina ba? Me ya sa kuka zo wurina a lokacina da kuke shan wahala?” 8 Sai dattawan Gileyad suka amsa masa, “Abin da ya sa muka zo wurinka yanzu, shi ne domin ka tafi tare da mu ne mu yi yaƙi da Ammonawa, ka kuma zama shugaban dukan jama'ar Gileyad.” 9 Yefta kuwa ya ce musu, “Idan kuka koma da ni gida domin in yi yaƙi da Ammonawa, idan Ubangiji ya ba da su a hannuna, to, zan zama shugabanku.” 10 Suka amsa suka ce wa Yefta, “Ubangiji shi ne shaida tsakaninmu, lalle za mu yi maka kamar yadda ka ce.” 11 Yefta kuwa ya tafi tare da dattawa Gileyad. Su kuwa suka naɗa shi shugabansu da sarkin yaƙinsu. Yefta kuwa ya faɗi dukan abin da yake zuciyarsa a gaban Ubangiji a Mizfa. 12 Yefta kuwa ya aiki jakadu wurin Sarkin Ammonawa da cewa, “Me ya haɗa ka da ni, da ka zo ƙasata da yaƙi?” 13 Sarkin Ammonawa ya amsa wa jakadun Yefta cewa, “Domin lokacin da Isra'ilawa suna tahowa daga Masar sun ƙwace mini ƙasa tun daga Kogin Arnon zuwa Kogin Yabbok, har zuwa Kogin Urdun. Yanzu sai ka mayar mini da ita cikin lumana.” 14 Yefta kuma ya sāke aike da jakadu wurin Sarkin Ammonawa, 15 tare da amsa, ya ce, “Isra'ilawa ba su ƙwace ƙasar Mowab ko ta Ammonawa ba. 16 Amma sa'ad da suka baro Masar, sun bi ta jeji zuwa Bahar Maliya, suka zo Kadesh. 17 Sa'an nan suka aike da jakadu wurin Sarkin Edom, su roƙe shi ya bar su su wuce ta ƙasarsa. Amma Sarkin Edom bai yarda ba. Suka kuma aika wa Sarkin Mowab, shi ma bai yarda ba, don haka Isra'ilawa suka zauna a Kadesh. 18 “Sa'an nan suka ci gaba da tafiya ta cikin hamada. Suka zaga ƙasar Edom da ta Mowab. Da suka kai gabashin ƙasar Mowab, sai suka yi zango a bakin Kogin Arnon, amma ba su haye kogin ba, gama shi ne iyakar ƙasar Mowab. 19 Sa'an nan Isra'ilawa suka aike da jakadu wurin Sihon Sarkin Heshbon ta Amoriyawa, suka roƙe shi, suka ce, ‘Ka yarda mana mu wuce ta ƙasarka.’ 20 Amma Sihon bai amince wa Isra'ilawa su bi ta ƙasarsa, su wuce ba. Ya kuwa tattara mutanensa, ya kafa sansaninsa a Yahaza, ya yi yaƙi da Isra'ilawa. 21 Ubangiji Allah na Isra'ila kuwa ya ba da Sihon da mutanensa duka ga Isra'ilawa, suka ci su da yaƙi. Suka kuwa mallaki dukan ƙasar Amoriyawa da mazaunan ƙasar. 22 Suka mallaki dukan ƙasar Amoriyawa tun daga Kogin Arnon har zuwa Kogin Yabbok, tun kuma daga jeji zuwa Kogin Urdun. 23 To, ai, ka ga Ubangiji Allah na Isra'ila ne ya kori Amoriyawa saboda jama'ar Isra'ila. To, yanzu so kake ka ƙwace mana? 24 Kai ba za ka mallaki abin da Kemosh, allahnka, ya ba ka mallaka ba? Dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya mallakar mana, za mu mallake shi. 25 Kana zaton ka fi Balak, ɗan Ziffor, Sarkin Mowab? Ka ji ya taɓa hamayya da Isra'ilawa? Ko kuwa ka ji ya taɓa yin yaƙi da su? 26 Shekara ɗari uku Isra'ilawa suka yi zamansu a Heshbon da ƙauyukanta, da Arower da ƙauyukanta, da dukan biranen da suke a gefen Kogin Arnon, me ya sa ba ka ƙwace su tun a wancan lokaci ba? 27 Don haka ni ban yi maka laifi ba, kai ne kake yi mini laifi da kake yaƙi da ni. Ubangiji ne alƙali yau, zai shara'anta tsakanin Isra'ilawa da Ammonawa.” 28 Amma Sarkin Ammonawa bai kula da saƙon da Yefta ya aika masa ba. 29 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko wa Yefta, sai ya tashi ratsa Gileyad da Manassa zuwa Mizfa ta Gileyad, daga can ya haura zuwa wurin Ammonawa. 30 Yefta kuwa ya yi wa'adi ga Ubangiji, ya ce, “Idan dai ka ba da Ammonawa a hannuna, 31 duk abin da ya fara fitowa daga ƙofar gidana don ya tarye ni, sa'ad da na komo daga yaƙin Ammonawa da nasara, zai zama na Ubangiji, zan kuwa miƙa shi hadaya ta ƙonawa.” 32 Yefta ya haye zuwa wurin Ammonawa domin ya yi yaƙi da su. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannunsa. 33 Ya karkashe su da mummunan kisa tun daga Arower zuwa yankin Minnit, har zuwa Abel-keramim. Ya cinye biranensu guda ashirin. Da haka Ammonawa suka sha kāshi a hannun Isra'ilawa.

'Yar Yefta

34 Da Yefta ya koma gidansa a Mizfa, sai ga 'yarsa, tilo ta fito da kiɗa da rawa don ta tarye shi. Ita ce kaɗai 'yarsa, banda ita ba shi da ɗa ko 'ya. 35 Sa'ad da ya gan ta sai ya yayyage tufafinsa, ya ce, “Kaito, 'yata, kin karya mini gwiwa, kin zamar mini babban dalilin wahala. Na riga na yi wa'adi ga Ubangiji, ba kuwa zan iya warware shi ba.” 36 Sai ta ce masa, “Baba, idan ka riga ka yi wa'adi ga Ubangiji, sai ka yi da ni bisa ga wa'adinka, da yake Ubangiji ya ɗau maka fansa a kan Ammonawa, abokan gābanka.” 37 Ta kuma ce masa, “Ina so ka yardar mini in tafi kan duwatsu ni da ƙawayena in yi makokin budurcina har wata biyu.” 38 Sai ya ce mata, “Tafi.” Ya sallame ta, ta tafi har wata biyu ɗin. Ita da ƙawayenta kuwa suka yi makokin budurcinta a kan duwatsu. 39 Bayan wata biyu, sai ta koma wurin mahaifinta, shi kuwa ya yi abin da ya yi wa Ubangiji wa'adi. Ta rasu ba ta taɓa sanin namiji ba. Wannan kuwa ya zama al'ada a cikin Isra'ila, 40 wato matan Isra'ilawa sukan fita kowace shekara su yi makoki kwana huɗu don 'yar Yefta, mutumin Gileyad.

Littafin Mahukunta 12

Yefta da Mutanen Ifraimu

1 Mutanen Ifraimu suka yi gangami suka haye zuwa Zafon da shirin yaƙi. Suka ce wa Yefta, “Me ya sa ka haye zuwa yaƙi da Ammonawa, amma ba ka kira mu mu tafi tare da kai ba? To, yanzu za mu ƙone ka da gidanka.” 2 Amma Yefta ya amsa musu, ya ce, “Ni da mutanena mun yi ta jayayya da Ammonawa, na kira ku don ku cece ni, amma ba ku cece ni daga hannunsu ba. 3 Sa'ad da na ga ba ku cece ni ba, sai na yi kasai da raina, na haye don in yi karo da Ammonawa. Ubangiji kuwa ya ba da su a hannuna. Me ya sa kuka zo yau don ku yi yaƙi da ni?” 4 Sa'an nan Yefta ya tara dukan mutanen Gileyad, suka yi yaƙi da mutanen Ifraimu, suka ci su. Mutanen Ifraimu suka ce musu, “Ku mutanen Gileyad masu neman mafaka ne a cikin Ifraimu da Manassa!” 5 Mutanen Gileyad suka hana mutanen Ifraimu hayewa ta mashigan Kogin Urdun. Idan wani mutumin Ifraimu gujajje ya ce, “Ku bar ni in haye.” Sai mutanen Gileyad su tambaye shi, “Kai mutumin Ifraimu ne?” Idan ya ce, “A'a,” 6 sai su ce masa, to, ka ce, “Shibbolet,” sai mutum ya ce, “Sibbolet,” gama ba ya iya faɗa daidai. Sai su kama shi su kashe a mashigan Urdun. Mutanen Ifraimu da aka kashe a lokacin su dubu arba'in da dubu biyu (42,000 ) ne. 7 Yefta mutumin Gileyad ya shugabanci Isra'ilawa shekara shida, sa'an nan ya rasu. Aka binne shi a garinsu, wato Gileyad.

Ibzan, da Elon, da Abdon sun Shugabanci Isra'ilawa

8 Bayan Yefta, sai Ibzan, mutumin Baitalami ya shugabanci Isra'ilawa. 9 Yana da 'ya'ya maza talatin, da 'ya'ya mata talatin. Ya aurar da 'ya'yansa mata ga wata kabila, ya kuma auro wa 'ya'yansa maza 'yan mata daga wata kabila. Ya shugabanci Isra'ilawa shekara bakwai. 10 Sa'an nan ya rasu, aka binne shi a Baitalami. 11 Bayansa kuma, sai Elon mutumin Zabaluna ya shugabanci Isra'ilawa shekara goma. 12 Sa'an nan ya rasu, aka binne shi a Ayalon a ƙasar Zabaluna. 13 Bayan Elon kuma, sai Abdon, ɗan Hillel, mutumin Firaton, ya shugabanci Isra'ilawa. 14 Yana da 'ya'ya maza arba'in, da jikoki maza talatin, suna hawan jakai saba'in. Abdon ya shugabanci Isra'ilawa shekara takwas. 15 Sa'an nan ya rasu, aka binne shi a Firaton ta ƙasar Ifraimu a tudun Amalekawa.

Littafin Mahukunta 13

Haihuwar Samson

1 Isra'ilawa kuma suka sāke yi wa Ubangiji zunubi, sai Ubangiji ya ba da su a hannun Filistiyawa shekara arba'in. 2 Akwai wani mutumin Zora daga kabilar Dan, sunansa Manowa, matarsa bakarariya ce, ba ta haihuwa. 3 Ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare ta, ya ce mata, “Ga shi, ke bakarariya ce, ba ki haihuwa, amma yanzu za ki yi ciki, za ki kuwa haifi ɗa. 4 Yanzu sai ki lura, kada ki sha ruwan inabi, ko abin sha mai gāfi, kada kuma ki ci haramtaccen abu, 5 gama za ki yi juna biyu, ki haifi ɗa. Ba za ki taɓa aske kansa ba Zai zama keɓaɓɓe ga Allah tun daga cikin ciki. Shi ne zai ceci Isra'ilawa daga hannun Filistiyawa.” 6 Macen kuwa ta tafi ta faɗa wa mijinta cewa, “Mutumin Allah ya zo wurina, fuskarsa tana da bantsoro kamar fuskar mala'ikan Ubangiji. Ni kuwa ban tambaye shi inda yake ba, shi kuma bai faɗa mini sunansa ba. 7 Amma ya ce mini, zan yi juna biyu, in haifi ɗa, don haka kada in sha ruwan inabi, ko abin sa maye, kada kuma in ci haramtaccen abu, gama yaron zai zama keɓaɓɓe ga Allah tun daga cikin ciki har zuwa ranar da zai rasu.” 8 Sa'an nan Manowa ya yi roƙo ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangijina, ina roƙonka ka bar mutumin Allah wanda ka aiko, ya sāke zuwa wurinmu, ya faɗa mana abin da za mu yi wa yaron da za a haifa.” 9 Allah kuwa ya ji roƙon Manowa, ya sāke aiko da mala'ikansa wurin matar, sa'ad da take a saura, mijinta kuwa ba ya tare da ita. 10 Don haka sai ta sheƙa a guje zuwa wurin mijinta, ta faɗa masa, “Ga mutumin da ya zo wurina ran nan, ya sāke zuwa.” 11 Manowa fa ya tashi ya tafi tare da ita. Da ya zo wurin mutumin, sai ya tambaye shi, “Kai ne mutumin da ya yi magana da macen nan?” Sai ya amsa ya ce, “Ni ne.” 12 Manowa kuma ya ce, “Lokacin da maganarka ta cika, wane irin yaro ne zai zama, me kuma za mu yi?” 13 Mala'ikan Ubangiji ya amsa, ya ce wa Manowa, “Sai matarka ta kiyaye dukan abin da na faɗa mata. 14 Kada ta ci kowane irin abu da aka yi da inabi, kada kuma ta sha ruwan inabi ko abin sa maye. Kada ta ci haramtaccen abu, amma ta kiyaye dukan abin da na umarce ta.” 15-16 Manowa dai bai san mala'ikan Ubangiji ne ba, sai ya ce wa mala'ikan, “Ina roƙonka ka jira, mu yanka maka ɗan akuya.” Amma mala'ikan ya ce masa, “Ko na jira ba zan ci abincinku ba, amma idan kana so ka yanka, sai ka shirya hadayar ƙonawa, ka miƙa ta ga Ubangiji.” 17 Manowa ya ce, “Ka faɗa mana sunanka domin lokacin da maganarka ta cika mu girmama ka.” 18 Mala'ikan Ubangiji ya ce masa, “Don me kake tambayar sunana? Sunana asiri ne.” 19 Manowa kuwa ya yanka ɗan akuya, ya kuma kawo hadayar gari, ya miƙa a kan dutse ga Ubangiji, mala'ika kuma ya yi al'ajabi. Manowa da matarsa suka yi kallo. 20 Sa'ad da harshen wutar ya hau zuwa samaniya daga bagaden, sai mala'ikan Ubangiji ya hau zuwa sama ta cikin harshen wutar bagaden. Manowa da matarsa sun gani, suka fāɗi a fuskokinsu a ƙasa. 21 Mala'ikan Ubangiji bai sāke bayyana ga Manowa da matarsa ba. Manowa kuma ya gane mala'ikan Ubangiji ne. 22 Manowa ya ce wa matarsa, “Ba shakka za mu mutu gama mun ga Ubangiji!” 23 Amma matarsa ta ce masa, “Da Ubangiji yana so ya kashe mu, ai, da bai karɓi hadayar ƙonawa da hadayar gārinmu ba, da kuma bai nuna mana, ko ya faɗa mana waɗannan abubuwa ba.” 24 Matar kuwa ta haifi ɗa, aka raɗa masa suna Samson. Yaron ya yi girma, Ubangiji ya sa masa albarka. 25 Ruhun Ubangiji ya fara iza shi, sa'ad da yake a zangon Dan, tsakanin Zora da Eshtawol.

Littafin Mahukunta 14

Samson da Budurwa a Timna

1 Samson kuwa ya gangara zuwa Timna inda ya ga ɗaya daga cikin 'yan matan Filistiyawa. 2 Sa'ad da ya hauro zuwa gida sai ya faɗa wa iyayensa, ya ce, “Na ga ɗaya daga cikin 'yan matan Filistiyawa a Timna, ina so ku auro mini ita.” 3 Amma iyayensa suka ce masa, “Cikin 'yan'uwanka da mutanenka duka, ba yarinyar da za ka aura daga cikin 'yan matansu, har ka tafi ka auro mace daga na Filistiyawa marasa kaciya?” Amma Samson ya ce wa mahaifinsa, “Ita ce wadda nake bukata, ka auro mini ita. Ina sonta.” 4 Iyayensa ba su san al'amarin nan daga wurin Ubangiji ne ba, gama Ubangiji yana so wannan ya zama sanadin yaƙi da Filistiyawa, gama a lokacin nan Filistiyawa ne suke mulkin Isra'ilawa. 5 Samson kuwa ya gangara zuwa Timna, shi da iyayensa. Da ya isa gonakin inabin Timna, sai ga sagarin zaki ya taso masa da ruri. 6 Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko a kansa da iko, sai ya yaga zakin da hannu, kamar yadda akan yayyage ɗan akuya. Amma bai faɗa wa iyayensa abin da ya yi ba. 7 Sa'an nan ya gangara ya yi zance da budurwar, yana kuwa sonta. 8 Bayan 'yan kwanaki sai ya koma don ya auro ta. Ya ratse don ya duba gawar zakin da ya kashe, sai ya tarar da cincirindon ƙudan zuma, da kuma zuma a cikin gawar zakin, ya yi mamaki. 9 Ya ɗebo zuman a hannunsa, yana tafe yana sha, har ya isa wurin iyayensa, ya ba su, suka sha, amma bai faɗa musu daga cikin gawar zaki ya ɗebo zuman ba. 10 Mahaifinsa ya tafi gidan iyayen yarinyar, Samson kuma ya shirya liyafa a can, gama haka samari sukan yi. 11 Sa'ad da Filistiyawa suka gan shi suka sa samari talatin su zauna tare da shi. 12 Samson kuwa ya ce musu, “Bari in yi muku ka-cici-ka-cici, idan kun faɗa mini amsarsa a kwana bakwai na bikin, to, zan ba ku rigunan lilin talatin da waɗansu riguna talatin na ado. 13 Amma idan kun kāsa ba ni amsar, to, ku ne za ku ba ni riguna talatin na ado.” Sai suka ce, “To, faɗi ka-cici-ka-cicin mu ji.” 14 Sai ya ce musu, “Daga mai ci, abinci ya fito, Daga kuma mai ƙarfi, zaƙi ya fito.” Ba su iya ba da amsar ba har kwana uku. 15 A rana ta huɗu suka ce wa matar Samson, “Ki rarrashi mijinki ya gaya mana amsar ka-cici-ka-cicin, idan kuwa kin ƙi, to, za mu ƙone ki da gidan mahaifinki da wuta. Kun gayyace mu don ku tsiyata mu ne?” 16 Sai matar Samson ta yi kuka a gabansa tana cewa, “Kai dai maƙiyina ne, ba masoyina ba, ka yi wa mutanena ka-cici-ka-cici, amma ba ka gaya mini amsarsa ba.” Amma ya ce mata, “Ko iyayena ma ban faɗa musu ba, sai in faɗa miki?” 17 Ta kuwa yi ta yi masa kuka har rana ta bakwai ta ƙarewar bikinsu. Amma a rana ta bakwai, ya faɗa mata amsar saboda yawan fitinarta. Ita kuwa ta faɗa wa mutanenta amsar ka-cici-ka-cicin. 18 A rana ta bakwai, kafin rana ta faɗi, mutanen garin suka ce masa, “Me ya fi zuma zaƙi? Me kuma ya fi zaki ƙarfi?” Ya kuwa ce musu, “Da ba don kun haɗa baki da matata ba, Da ba ku san amsar ka-cici-ka-cicin ɗin nan ba.” 19 Sa'an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kansa da iko, ya gangara zuwa Ashkelon. Ya kashe mutum talatin a can, ya kwashe ganima, ya ba waɗanda suka faɗa masa amsar ka-cici-ka-cicin riguna. Ya koma gida a husace saboda abin da ya faru. 20 Aka ɗauki matar Samson aka ba wanda ya yi masa abokin ango.

Littafin Mahukunta 15

1 Bayan 'yan kwanaki, sai Samson ya tafi ya ziyarci matarsa, ya kai mata ɗan akuya, a lokacin girbin alkama. Ya ce wa mahaifinta, “Zan shiga wurin matata a ɗakin kwana.” Amma mahaifinta bai yardar masa ba. 2 Ta ce wa Samson, “Na yi tsammani ba ka sonta ne sam, don haka sai na ba da ita ga wanda ya yi maka abokin ango. Amma ƙanwarta ta fi ta kyau. Ina roƙonka ka ɗauki ƙanwar maimakon matarka.” 3 Sai Samson ya ce musu, “A wannan lokaci, zan zama marar laifi saboda abin da zan yi wa Filistiyawa.” 4 Ya tafi ya kama yanyawa ɗari uku, ya haɗa wutsiyoyinsu, wato wutsiya da wutsiya, sa'an nan ya ɗaura jiniya tsakanin kowaɗanne wutsiya biyu. 5 Da ya sa wa jiniyar wuta, ya sake su zuwa cikin hatsin Filistiyawa. Suka ƙone dammunan hatsi, da hatsin da yake a tsaye, da gonakin zaitun. 6 Filistiyawa kuwa suka ce, “Wane ne ya yi mana wannan abu?” Sai aka ce, “Samson ne, surukin mutumin Timna, domin ya ɗauki matar Samson ya ba wanda ya yi masa abokin ango.” Filistiyawa kuwa suka je suka ƙone matar, ta mutu, suka kuma ƙone gidan mahaifinta. 7 Samson ya ce musu, “Wato haka kuka yi! To, na rantse, ba zan bari ba sai na rama!” 8 Ya kuwa fāɗa musu, ya kashe su da yawa. Sa'an nan ya tafi ya zauna a kogon dutsen Itam.

Samson ya ci Nasara a kan Filistiyawa

9 Filistiyawa suka haura, suka kafa sansani a Yahudiya, suka bazu a cikin Lihai. 10 Mutanen Yahuza suka ce, “Me ya sa kuka kawo mana yaƙi?” Filistiyawa suka ce, “Mun zo ne domin mu kama Samson, mu yi masa kamar yadda ya yi mana.” 11 Sa'an nan mutum dubu uku na Yahuza suka gangara zuwa kogon dutsen Itam. Suka ce wa Samson, “Ba ka sani ba Filistiyawa ne suke mulkinmu? Me ya sa ka yi mana haka?” Shi kuwa ya amsa musu, ya ce, “Kamar yadda suka yi mini, haka ni kuma na yi musu.” 12 Suka ce masa, “Mun gangara zuwa wurinka don mu ɗaure ka, mu miƙa ka gare su.” Samson ya ce musu, “Ku rantse mini idan ba ku ne da kanku kuke so ku kashe ni ba.” 13 Suka ce masa, “A'a, ba za mu kashe ka ba, mu dai za mu kama ka, mu miƙa ga Filistiyawa.” Sa'an nan suka ɗaure shi da sababbin igiyoyi biyu, suka sauko da shi daga dutsen. 14 Sa'ad da ya zo Lihai, sai Filistiyawa suka sheƙo a guje suna ihu suka nufo shi. Ruhun Ubangiji ya sauko kansa da iko, sai igiyoyin da suke a ɗaure da shi suka tsintsinke kamar zaren da ya kama wuta. 15 Ya kuwa sami sabon muƙamuƙin jaki, ya ɗauka ya kashe mutum dubu da muƙamuƙin. 16 Sa'an nan Samson ya raira waƙa ya ce. “Da muƙamuƙin jaki na kashe mutum dubu, Da muƙamuƙin jaki na tsiba su tsibi-tsibi.” 17 Da ya gama, ya jefar da muƙamuƙin. Sai aka ba wurin suna, Ramat-Lihai, wato tudun muƙamuƙi. 18 Ƙishirwa kuwa ta kama shi ƙwarai, sai ya roƙi Ubangiji ya ce, “Kai ne ka yi wannan babbar nasara ta hannun bawanka, yanzu kuwa ko zan mutu da ƙishirwa, har Filistiyawa marasa kaciya su kama ni?” 19 Allah kuwa ya buɗe wani rami daga ƙasa, sai ruwa ya ɓuɓɓugo daga ciki. Da ya sha, hankalinsa ya komo, ya wartsake. Don haka aka ba wurin suna En-hakkore, wato mai kira. Ramin yana nan a Lihai har wa yau. 20 Samson ya shugabanci Isra'ilawa shekara ashirin a zamanin da Filistiyawa suke mulkinsu.

Littafin Mahukunta 16

Samson a Gaza

1 Daga can Samson ya tafi Gaza, inda ya ga wata karuwa, sai ya shiga wurinta. 2 Aka faɗa wa mutanen Gaza, Samson yana nan. Suka kewaye wurin, suka yi fakonsa a ƙofar garin dukan dare. Suka yi shiru dukan dare, suka ce wa junansu, “Za mu jira sai gari ya waye sa'an nan mu kashe shi.” 3 Amma Samson ya yi kwanciyarsa har tsakar dare. Sa'an nan ya tashi ya kama ƙyauren ƙofar birnin, da madogarai biyu na ƙofar, ya tumɓuke su. Ya saɓe su a kafaɗarsa, ya kai su kan dutsen da yake a gaban Hebron.

Samson da Delila

4 Bayan wannan kuma sai ya kama ƙaunar wata mace mai suna Delila a kwarin Sorek. 5 Shugabannin Filistiyawa, su biyar suka je wurinta suka ce mata, “Ki yi masa kirsa, don ki san dalilin irin ƙarfin nan nasa, da kuma yadda za mu yi maganinsa, mu ɗaure shi don mu rinjaye shi. Kowannenmu zai ba ki shekel dubu da ɗari (1,100 ).” 6 Delila kuwa ta ce wa Samson, “Ina roƙonka ka faɗa mini inda babban ƙarfin nan naka yake, da kuma yadda za a ɗaure ka ka rasa kuzari.” 7 Samson ya ce mata, “Idan an ɗaure ni da sababbin tsarkiyoyi guda bakwai, waɗanda ba su bushe ba, to, sai in rasa ƙarfi, in zama kamar kowa.” 8 Sai shugabannin Filistiyawa suka kawo wa Delila sababbin tsarkiyoyi guda bakwai waɗanda ba su bushe ba. Ta kuwa ɗaure shi da su. 9 Tana kuwa da mutane a laɓe cikin wani ɗaki, sai ta ce masa, “Ga Filistiyawa a kanka, Samson!” Da jin haka, sai ya katse tsarkiyoyi kamar zare idan an sa masa wuta. Asirin ƙarfinsa kuwa bai sanu ba. 10 Delila kuma ta ce wa Samson, “Ga shi, ka yi mini ba'a, ka ruɗe ni. Ina roƙonka, ka faɗa mini yadda za a ɗaure ka.” 11 Ya ce mata, “Idan suka ɗaure ni da sababbin igiyoyi waɗanda ba a yi amfani da su ba, to, zan rasa ƙarfi, in zama kamar kowa.” 12 Sai Delila ta ɗauki sababbin igiyoyi, ta ɗaure shi da su, sa'an nan ta ce masa, “Ga Filistiyawa na zuwa kanka, Samson!” Amma ya katse igiyoyin da ta ɗaure shi da su kamar silin zare. Mutanen kuwa na nan laɓe a wani ɗaki. 13 Delila ta ce wa Samson, “Har yanzu dai, ka maishe ni shashasha, kana ta ruɗina. Ka faɗa mini yadda za a ɗaure ka.” Ya ce mata, “Idan kin saƙa tukkwayen bakwai da suke kaina haɗe da zare, kika buga da akwasha sai in rasa ƙarfi, in zama kamar kowa.” 14 Sa'ad da yake barci, Delila ta saƙa tukkwayen nan bakwai da suke kansa haɗe da zare, ta buga da akwasha, sa'an nan ta ce masa, “Ga Filistiyawa a kanka, Samson!” Da ya farka daga barcin, sai ya tumɓuke akwashar, da zaren. 15 Delila ta ce masa, “Ƙaƙa za ka ce kana ƙaunata, alhali kuwa ba na a zuciyarka? Sau uku ke nan ka maishe ni shashasha, ba ka faɗa mini inda ƙarfin nan naka yake ba.” 16 Sa'ad da ta fitine shi yau da gobe da yawan maganganunta, ta tunzura shi, sai ransa ya ɓaci kamar zai mutu. 17 A ƙarshe ya faɗa mata ainihin gaskiyar, ya ce mata, “Ba a taɓa aske gashin kaina ba, gama ni keɓaɓɓe ga Ubangiji ne tun daga cikin uwata. Idan aka yi mini aski, to, ƙarfina zai rabu da ni, in zama marar ƙarfi kamar kowa.” 18 Sa'ad da Delila ta gane ya faɗa mata ainihin gaskiya, sai ta aika a kirawo shugabannin Filistiyawa tana cewa, “A wannan karo ku zo, domin ya faɗa mini ainihin gaskiyar.” Shugabannin Filistiyawa kuwa suka zo wurinta da kuɗi a hannu. 19 Ta kuwa sa shi ya yi barci a cinyoyinta, sai ta kira wani mutum, ta sa shi ya aske tukkwayen nan bakwai da suke kansa. Sa'an nan ta yi ƙoƙari ta sa ya harzuƙa, amma ƙarfinsa ya rabu da shi. 20 Ta ce masa, “Ga Filistiyawa a kanka, Samson!” Sai ya farka daga barcinsa, ya ce, “Zan fita kamar yadda na saba yi koyaushe, in miƙe jikina.” Ashe, bai sani ba, Ubangiji ya rabu da shi. 21 Filistiyawa fa suka kama shi, suka ƙwaƙule idanunsa, suka gangara da shi zuwa Gaza. Suka ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla. Ya yi ta niƙa a kurkuku. 22 Amma gashin kansa ya fara tohowa.

Samson ya Mutu

23 Shugabannin Filistiyawa kuwa suka taru domin su miƙa babbar hadaya ga allahnsu, Dagon. Suka raira waƙa, suka ce, “Allahnmu ya ba da Samson, maƙiyinmu a hannunmu!” 24 Da mutane suka gan shi, sai suka raira waƙar yabon allahnsu, suna cewa, “Allahnmu ya ba da maƙiyinmu a hannunmu, wanda ya fallasa ƙasarmu, ya kashe mutanenmu da yawa.” 25 Sa'ad da suke ta farin ciki, sai suka ce, “A kawo Samson ya yi mana wasa.” Sai suka kawo Samson daga kurkuku, ya kuwa yi wasa a gabansu. Suka sa ya tsaya a tsakanin ginshiƙai. 26 Samson kuwa ya ce wa yaron da yake jagoransa, “Bari in taɓa ginshiƙan da yake ɗauke da gidan nan, domin in jingina.” 27 Gidan kuwa yana cike da mutane mata da maza. Shugabannin nan biyar na Filistiyawa suna wurin. Akwai mutum dubu uku mata da maza, a kan benen da suka zo kallon wasan Samson. 28 Sa'an nan Samson ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Ya Ubangiji Allah, ka tuna da ni, ina roƙonka, ka ƙarfafa ni sau ɗayan nan kaɗai, don in ɗauki fansa a kan Filistiyawa saboda idona biyu da suka ƙwaƙule mini.” 29 Sai Samson ya kama ginshiƙai biyu da suke a tsakiya, waɗanda suke ɗauke da gidan. Ya riƙe su da hannunsa biyu, ɗaya a kowane hannu, sa'an nan ya jingina jikinsa a kansu, 30 ya yi kuwwa ya ce, “Bari in mutu tare da Filistiyawa!” Ya sunkuya da iyakar ƙarfinsa. Ɗakin kuwa ya faɗa a kan shugabannin da dukan mutanen da suke a cikin ɗakin. Mutanen da Samson ya kashe a rasuwarsa sun fi waɗanda ya kashe sa'ad da yake da rai. 31 'Yan'uwansa da dukan danginsa, suka gangara, suka ɗauki gawarsa, suka binne a kabarin Zora da Eshtawol. Samson ya shugabanci Isra'ilawa shekara ashirin.

Littafin Mahukunta 17

Gumakan Mika

1 Akwai wani mutum a ƙasar tudu ta Ifraimu, da ake kira Mika. 2 Shi ne ya ce wa mahaifiyarsa, “Sa'ad da aka sace miki tsabar azurfan nan dubu da ɗari ɗaya (1,100 ), kin hurta la'ana a kan ɓarayin, na kuwa ji ki. To, ga shi, azurfar na wurina, ni na ɗauka.” Sai mahaifiyarsa ta ce, “Allah ya sa maka albarka, ɗana.” 3 Ya mayar wa mahaifiyarsa da azurfar dubu da ɗari (1,100 ). Mahaifiyarsa ta ce, “Domin kada la'anar ta kama ɗana, ina ba da wannan azurfa ga Ubangiji da zuciya ɗaya. Ana iya sassaƙa gunki a kuma yi na zubi saboda haka zan ba ka ita.” 4 Da ya mayar mata da azurfar, ta ɗibi azurfa ɗari biyu ta ba maƙerin azurfa, shi kuwa ya sassaƙa gunki ya kuma yi na zubi. Aka ajiye su a gidan Mika. 5 Mika kuwa yana da ɗakin gumaka. Ya yi gumaka, da falmaransu, da kan gida. Ya keɓe ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza domin ya zama firist nasa. 6 A wannan lokaci ba sarki a Isra'ila, kowa yana ta yin yadda ya ga dama. 7 Akwai wani saurayi Balawe da yake zama a Baitalami ta Yahudiya. 8 Saurayin kuwa ya yi ƙaura daga Baitalami. Sa'ad da yake tafiya sai ya iso gidan Mika, a ƙasar tudu ta Ifraimu. 9 Mika ya tambaye shi, “Daga ina ka zo?” Ya ce, “Ni Balawe ne na Baitalami ta Yahudiya, ina neman wurin da zan zauna.” 10 Mika ya ce masa, “Ka zauna tare da ni, ka zama mai ba ni shawara, da kuma firist, ni kuwa zan riƙa ba ka azurfa goma, da tufafi, da abin zaman gari kowace shekara.” 11 Balawen kuwa ya yarda ya zauna tare da Mika. Ya kuwa zama kamar ɗa ga Mika. 12 Mika kuma ya naɗa shi ya zama firist ɗinsa. Ya kuwa zauna a gidansa. 13 Sa'an nan Mika ya ce, “Yanzu na sani Ubangiji zai sa mini albarka, da yake na sami Balawe ya zamar mini firist.”

Littafin Mahukunta 18

Mika da Kabilar Dan

1 A kwanakin nan ba sarki a Isra'ila. A wannan lokaci kuwa kabilar Dan suna ta neman yankin ƙasar da za su samu, su zauna. Gama har yanzu ba su sami nasu gādon ƙasa tare da sauran kabilar Isra'ila ba. 2 Sai Danawa suka zaɓi mutum biyar jarumai daga kabilarsu, suka aike su daga Zora da Eshtawol, su tafi leƙen asirin ƙasar, su bincike ta. Suka kuwa tafi zuwa ƙasar tudu ta Ifraimu, suka sauka a gidan Mika. 3 Sa'ad da suke a gidan Mika ɗin, sai suka ji muryar saurayin nan, Balawe, suka tsaya suka tambaye shi, “Wa ya kawo ka nan? Me kuma kake yi a nan?” 4 Ya ce musu, “Mun yi yarjejeniya da Mika, in yi masa aikin firist, shi kuma ya biya ni.” 5 Suka ce masa, “In ka yarda ka roƙar mana Allah ko tafiyarmu na da sa'a.” 6 Firist ɗin ya ce musu, “Kada ku damu, Ubangiji yana tare da ku a tafiyarku.” 7 Saboda haka mutanen nan biyar suka tashi, suka zo Layish, suka ga mutane suna zamansu a huce, kamar Sidoniyawa. Ba su da rigima, natsattsu ne, ba su jayayya da kowa, suna da wadata. Suna nesa da Sidoniyawa, ba su sha'anin kome da kowa. 8 Da mutanen nan biyar suka koma wurin 'yan'uwansu a Zora da Eshtawol, sai 'yan'uwan suka tambaye su labarin tafiyarsu. 9 Suka ce, “Ku tashi, mu tafi mu fāɗa musu, gama mun ga ƙasar tana da ni'ima ƙwarai. Kada ku zauna ku ɓata lokaci, ku shiga ku mallake ta! 10 Idan kuka je za ku tarar da mutane suna zama a sake. Ƙasar kuwa babba ce, tana da dukan abin da ɗan adam yake bukata.” 11 Mutum ɗari shida daga kabilar Dan suka yi shirin yaƙi, suka kama hanya daga Zora da Eshtawol. 12 Suka tafi suka kafa sansani a yammacin Kiriyat-yeyarim, birni ne a Yahudiya. Saboda haka ake kiran wurin Mahanedan, wato sansanin Dan, har wa yau. 13 Daga can suka wuce zuwa ƙasar tudu ta Ifraimu, suka zo gidan Mika. 14 Mutum biyar ɗin nan da suka tafi leƙen asirin ƙasar Layish, suka ce wa abokan tafiyarsu, “Ko kun san akwai gunkin itace cikin gidajen nan? Akwai kuma gunki na zubi, da kan gida, da falmaran dominsu. Me ya kamata mu yi musu?” 15 Sai suka juya zuwa gidan Mika, inda saurayin nan Balawe yake, suka gaishe shi. 16 Danawa ɗari shida ɗin da suka yi shirin yaƙi, suka tsaya a bakin ƙofa. 17 Amma mutum biyar ɗin nan da suka tafi leƙen asirin ƙasar suka shiga kai tsaye, suka ɗauki gunkin da aka yi da itace, da falmaran, da kan gida, da gunki na zubi. Firist ɗin kuwa ya tsaya a bakin ƙofa tare da mutum ɗari shida ɗin nan masu shirin yaƙi. 18 Sa'ad da mutum biyar ɗin nan suka shiga gidan Mika suka ɗauki falmaran, da sassaƙaƙƙen gunki, da kan gida, da gunki na zubi, sai firist ɗin ya ce musu, “Me kuke yi?” 19 Suka ce masa, “Yi mana shiru, kame bakinka. Ka biyo mu, ka zama firist namu da mai ba mu shawara. Bai fi kyau ka zama firist na kabilar Isra'ila ba, da a ce ka zama na gidan mutum guda kawai?” 20 Da firist ɗin ya ji haka, sai ya yi murna, ya ɗauki falmaran da kan gida da sassaƙaƙƙen gunki, ya tafi tare da su. 21 Suka juya, suka tafi da 'ya'yansu da dabbobinsu, da mallakarsu. 22 Sa'ad da suka yi 'yar tazara daga gidan Mika sai aka kira maƙwabtan Mika, suka je suka ci wa Danawa. 23 Suka yi wa Danawa tsawa. Da suka waiga, sai suka ce wa Mika, “Me ya faru? Me ya kawo waɗannan 'yan iska?” 24 Mika kuwa ya ce musu, “Kun kwashe allolina da na yi, da firist ɗina, me ya rage mini kuma? Sa'an nan ku ce mini, ‘Me ya faru?’ ” 25 Danawa kuma suka ce masa, “Kada ka kuskura ka ce kome, idan ba haka ba mutanen nan za su harzuƙa, da kai da iyalinka duka ku rasa rayukanku.” 26 Sa'an nan Danawa suka kama hanyarsu. Da Mika ya ga dai sun fi ƙarfinsa, sai ya juya ya koma gida. 27 Da Danawa suka ɗauke gumakan da Mika ya yi, da firist ɗinsa, sai suka je Layish inda suka sami mutane suna zamansu a huce. Suka hallaka su, suka ƙone birnin. 28 Ba wanda zai ceci mutanen Layish, gama suna nesa da Sidon, ba su kuma sha'ani da kowa. A kwari guda ne da Bet-rehob. Danawa kuwa suka sāke gina birnin, suka zauna a ciki. 29 Suka sa wa birnin suna Dan, ɗan Yakubu. Kafin wannan lokaci kuwa ana kiran birnin Layish ne. 30 Danawa fa suka kafa gunkin domin su yi masa sujada. Jonatan, ɗan Gershom, ɗan Musa, shi da 'ya'yansa maza, suka zama firistocin Danawa, har zuwa ranar da aka kwashe mutanen zuwa bauta. 31 Haka fa suka kafa gunkin Mika har duk lokacin da alfarwar Ubangiji take a Shilo.

Littafin Mahukunta 19

Balawe da Ƙwarƙwararsa

1 A lokacin nan ba sarki a Isra'ila. Sai wani Balawe da yake zama a wani lungu na ƙasar tudu ta Ifraimu ya ɗauko wata mace daga Baitalami ta Yahudiya ta zama ƙwarƙwararsa. 2 Ƙwarƙwarar kuwa ta ji haushinsa, ta koma gidan mahaifinta a Baitalami ta Yahudiya. Ta zauna a can har wata huɗu. 3 Sa'an nan mutumin ya tafi ya yi bikonta. Ya tafi da baransa da jaki biyu. Da ya zo gidan mahaifinta, sai ta shigo da shi gidan, mahaifin ya karɓe shi da farin ciki. 4 Mahaifin macen ya i masa ya dakata, sai ya tsaya har kwana uku. Suka ci suka sha tare. 5 A safiyar rana ta huɗun, suka tashi tun da wuri, domin su yi shirin tafiya, amma mahaifin matar ya ce masa, “Ka dakata ka ƙara cin abinci tukuna sa'an nan ka tafi.” 6 Su biyu kuwa suka zauna suka ci suka sha tare. Har yanzu mahaifin mace ya sāke ce masa, “Ina roƙonka ka ƙara kwana, ka saki jikinka ka more.” 7 Sa'ad da mutumin ya tashi zai tafi sai mahaifin macen ya roƙe shi, ya kuma kwana. 8 A rana ta biyar, sai mutumin ya tashi da wuri don ya tafi amma mahaifin macen ya ce masa, “Ka zauna ka ci abinci tukuna har rana ta yi sanyi.” Dukansu biyu suka zauna suka ci tare. 9 Sa'ad da mutumin, da ƙwarƙwararsa, da baransa sun tashi za su tafi, sai mahaifin macen kuma ya ce masa, “Ga shi, rana ta kusan faɗuwa, yamma kuwa ta yi, ina roƙonka, ka sāke kwana ka ji wa ranka daɗi, sa'an nan ka yi sammako gobe ka kama hanyarka zuwa gida.” 10 Amma mutumin bai yarda ya sāke kwana ba, sai ya tashi shi da ƙwarƙwararsa suka kama hanya. Ya kai daura da Yebus, wato Urushalima ke nan. Yana tare da jakinsa biyu da ya yi musu shimfiɗa, da ƙwarƙwararsa. 11 Baran kuwa ya ce wa maigidansa, “In ka yarda mu ratse mu kwana a birnin Yebusiyawan nan.” 12 Amma maigidansa ya ce masa, “Ba za mu tsaya a birnin da mutane ba Isra'ilawa ba ne. Za mu wuce zuwa Gibeya, 13 mu ƙara ɗan nisa, mu tafi mu kwana a Gibeya ko a Rama.” 14 Sai suka wuce, suka yi tafiyarsu. Rana ta faɗi sa'ad da suka kai Gibeya, ta yankin ƙasar Biliyaminu. 15 Suka ratse don su kwana a Gibeya. Balawen ya tafi ya zauna a dandalin garin, gama ba wanda ya kai su gidansa su kwana. 16 To, ga wani tsoho yana komowa daga gona da yamma. Tsohon kuwa mutumin ƙasar tudu ta Ifraimu ne, yana zama a Gibeya, amma mutanen Gibeya kabilar Biliyaminu ne. 17 Da dattijon ya duba ya ga matafiyin a dandalin birnin, ya ce masa, “Ina za ka? Daga ina kuma ka fito?” 18 Balawen ya ce masa, “Muna tahowa ne daga Baitalami ta Yahudiya zuwa wani lungu da yake ƙasar tudu ta Ifraimu, inda nake. Na je Baitalami ta Yahudiya ne, yanzu kuwa ina komawa gida. Ba wanda ya sauke ni a gidansa. 19 Ina da baro domin jakuna, ina kuma da abinci da ruwa inabi don kaina, da ƙwarƙwarata da barana, ba mu rasa kome ba.” 20 Tsohon nan ya ce, “Ku zo mu je gidana, duk abin da kuke bukata zan ba ku, amma kada ku kwana a dandalin.” 21 Sai ya kai su gidansa, ya ba jakan harawa, aka wanke ƙafafun baƙin, sa'an nan suka ci suka sha. 22 Sa'ad da suke cikin jin daɗin ci da sha, 'yan iskan da suke birnin suka zo suka kewaye gidan, suka yi ta bubbuga ƙofar, suka ce wa tsohon, “Ka fito mana da mutumin da ya zo gidanka don mu yi luɗu!” 23 Tsohon kuwa ya fito wurinsu, ya ce musu, “A'a, 'yan'uwana, kada ku yi mugun abu haka, wannan ya sauka a gidana, kada ku yi wannan rashin kunya. 24 Ga 'yata budurwa da ƙwarƙwararsa, bari in fito muku da su, ku yi abin da kuka ga dama da su, amma kada ku yi wa mutumin nan wannan abin kunya!” 25 Amma 'yan iskan ba su yarda ba, sai Balawen ya fitar da ƙwarƙwararsa gare su. Suka yi mata faɗe, suka wulakanta ta dukan dare har kusan wayewar gari, sa'an nan suka ƙyale ta. 26 Da gari ya waye, ƙwarƙwarar ta zo ta fāɗi a ƙofar gidan tsohon, inda maigidanta ya sauka, tana nan har hantsi ya cira. 27 Sa'ad da Balawen ya tashi da safe, ya buɗe ƙofa, ya fita domin ya kama hanyarsa, sai ga ƙwarƙwararsa kwance a ƙofar gida, da hannuwanta a dokin ƙofar. 28 Ya ce mata, “Tashi mu tafi.” Amma ba amsa. Sai ya aza gawarta a kan jaki, sa'an nan ya kama hanya zuwa gida. 29 Da ya isa gida, ya ɗauki wuƙa ya yanyanka gawar ƙwarƙwararsa gunduwa gunduwa har goma sha biyu, ya aika a ko'ina cikin dukan ƙasar Isra'ila. 30 Dukan wanda ya ga haka sai ya ce, “Ba mu taɓa ganin irin wannan abu ba, ba a kuwa taɓa yin haka ba tun daga ranar da Isra'ilawa suka fito daga ƙasar Masar sai yau. Ku yi tunani, me za mu yi a kan wannan al'amari?”

Littafin Mahukunta 20

Yaƙi da Mutanen Biliyaminu

1 Dukan jama'ar Isra'ila fa suka fito tun daga Dan a arewa har zuwa Biyer-sheba a kudu da kuma Gileyad daga gabas. Suka hallara gaba ɗaya a gaban Ubangiji a Mizfa. 2 Dukan shugabannin kabilar Isra'ila suna cikin wannan taron jama'ar Allah. Sojojin ƙafa yawansu ya kai dubu ɗari huɗu (400,000 ). 3 Mutanen Biliyaminu kuwa sun ji labari sauran Isra'ilawa sun haura zuwa Mizfa. Isra'ilawa suka tambayi Balawen suka ce, “Ka faɗa mana yadda wannan mugun abu ya auku.” 4 Balawe, mai ƙwarƙwarar da ka kashe, ya amsa ya ce, “Ni da ƙwarƙwarata muna biyo Gibeya ta Biliyaminu mu kwana. 5 Sai mutanen Gibeya suka kewaye gidan da nake da dare, suna neman kashe ni, da ba su same ni ba, sai suka yi wa ƙwarƙwarata faɗe har ya kai ta ga mutuwa. 6 Ni kuwa na ɗauki gawarta na yanyanka gunduwa gunduwa na aika cikin ƙasar gādon Isra'ila duka, gama waɗannan mutane sun aikata abin ƙyama da abin kunya ga dukan Isra'ila. 7 Dukanku nan Isra'ilawa ne, me za mu yi a kan wannan al'amari?” 8 Dukan jama'a kuwa suka tashi gaba ɗaya, suna cewa, “Daga cikinmu ba wanda zai koma alfarwarsa ko kuwa gidansa. 9 Wannan shi ne abin da za mu yi wa Gibeya, mu zaɓi waɗansunmu su fāɗa mata da yaƙi. 10 Kashi ɗaya daga goma na Isra'ilawa su ba da abinci ga sojoji. Sauran jama'a kuwa su je su hukunta Gibeya saboda muguntar da ta aikata cikin Isra'ila.” 11 Saboda haka dukan mutanen Isra'ila suka taru niyya ɗaya domin su fāɗa wa garin da yaƙi. 12 Kabilar Isra'ila kuwa suka aiki manzanni ga kabilar Biliyaminu suka ce, “Wace irin mugunta ce wannan da kuka aikata? 13 Yanzu sai ku ba da mutanen nan 'yan iska da suke cikin Gibeya don mu kashe su, mu kawar da mugunta daga cikin Isra'ila.” Amma mutanen Biliyaminu ba su kula da maganar 'yan'uwansu, Isra'ilawa ba. 14 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fita daga Gibeya gaba ɗaya domin su yi yaƙi da jama'ar Isra'ila. 15 A ran nan mutanen Biliyaminu suka tattaru daga garuruwansu, mutum dubu ashirin da dubu shida (26,000 ). Banda waɗannan, sai da mazaunan Gibeya suka tara zaɓaɓɓun mutane ɗari bakwai. 16 Daga cikin waɗannan duka akwai zaɓaɓɓun mutane bakwai, bahagwai. Kowannensu yana iya ya baraci gashi guda da majajjawa ba kuskure. 17 Isra'ilawa kuwa banda kabilar Biliyaminu, suka tara mayaƙa dubu ɗari huɗu (400,000 ) horarru.

Yaƙi da Mutanen Biliyaminu

18 Isra'ilawa suka tashi suka tafi Betel. A can suka yi tambaya ga Allah suka ce, “Wace kabila ce daga cikinmu za ta fara faɗa wa kabilar Biliyaminu?” Ubangiji ya ce, “Kabilar Yahuza ce za ta fara.” 19 Sa'an nan Isra'ilawa suka tashi da safe suka kafa sansani kusa da Gibeya. 20 Suka kuwa fita su yi yaƙi da mutanen Biliyaminu, suka jā dāgar yaƙi suna fuskantar Gibeya. 21 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fito daga birnin suka hallakar da mutum dubu ashirin da biyu (22,000 ), daga cikin mutanen Isra'ila a ranar. 22-23 Mutanen Isra'ila suka tafi inda ake sujada suka yi makoki a gaban Ubangiji har zuwa dare. Suka tambaye shi suka ce, “Mu sāke zuwa domin mu yi yaƙi da 'yan'uwanmu mutanen Biliyaminu?” Ubangiji ya ce musu, “I, ku tafi.” Saboda haka sai sojojin Isra'ilawa suka ƙarfafa, suka sāke jān dāga a inda suka jā ta dā. 24 Sai mutanen Isra'ila suka tafi su kara da mutanen Biliyaminu a rana ta biyu. 25 Mutanen Biliyaminu kuwa suka fito daga birnin suka hallakar da mutum dubu goma sha takwas (18,000 ) daga cikin Isra'ilawa. Dukan waɗannan da aka hallaka horarru ne. 26 Dukan rundunan Isra'ilawa suka haura zuwa Betel, suka yi makoki, suka zauna a gaban Ubangiji suka yi azumi har maraice. Sa'an nan suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa da na salama. sāke yin tambaya ga Ubangiji suka ce, “Mu sāke tafiya mu yi yaƙi da 'yan'uwanmu, mutanen Biliyaminu, ko kuwa mu bari?” Ubangiji kuwa ya ce musu, “Ku je, gama gobe zan ba da su gare ku.” A lokacin nan akwatin alkawari na Ubangiji yana nan. Finehas ɗan Ele'azara, ɗan Haruna, shi ne mai aiki a gabansa. 29 Isra'ilawa kuwa suka sa 'yan kwanto kewaye da Gibeya. 30 Sa'an nan suka tafi su kara da mutanen Biliyaminu a rana ta uku. Suka jā dāgar yaƙi gaba da Gibeya kamar dā. 31 Mutanen Biliyaminu kuma suka fito, suka tasar musu. Aka jawo su nesa da birnin. Suka fara kashe Isra'ilawa kamar yadda suka yi a dā, suka kashe wajen mutum talatin a kan karauka wadda ta nufi Betel da wadda ta nufi Gibeya, da filaye. 32 Sai mutanen Biliyaminu suka ce, “Mun fatattake su kamar dā.” Amma Isra'ilawa suka ce, “Mu gudu don mu jawo su nesa da birnin zuwa karauka.” 33 Isra'ilawa duka suka tashi daga wurin da suke, suka jā dāga a Ba'altamar. Mutanensu da suke kwanto a yammacin Gibeya suka fito. 34 Horarrun sojojin Isra'ila, su dubu goma (10,000 ), suka faɗa wa Gibeya. Yaƙi kuwa ya yi zafi, amma mutanen Biliyaminu ba su san masifa tana gab da su ba. 35 Ubangiji kuwa ya fatattake mutanen Biliyaminu a gaban Isra'ilawa. Isra'ilawa kuwa suka hallaka mutanen Biliyaminu dubu ashirin da biyar da ɗari ɗaya (25,100 ) a wannan rana, waɗannan duka kuwa mayaƙa ne. 36 Mutanen Biliyaminu kuwa suka gane an ci su da yaƙi. Mutanen Isra'ila kuwa suka yi ta ja da baya daga mutanen Biliyaminu domin sun dogara ga mutanensu da suka yi wa Gibeya kwanto. 37 Sai 'yan kwanto suka gaggauta suka faɗa wa Gibeya, suka kutsa suka kashe dukan waɗanda suke a birnin. 38 Alamar da mayaƙan Isra'ila da na 'yan kwantonsu suka daidaita a tsakaninsu, ita ce murtukewar hayaƙi a cikin birnin. 39 Idan mutanen Isra'ila sun hangi hayaƙin, sai su juya su fāɗa wa mutanen Biliyaminu da yaƙi. Kafin alamar hayaƙin sai mutanen Biliyaminu suka fara kashe wa Isra'ilawa wajen mutum talatin. Suka ce, “Ai, suna shan ɗibga a hannunmu kamar yadda suka sha da fari.” 40 Amma sa'ad da alamar hayaƙin ta fara murtukewa a cikin birnin, sai mutanen Biliyaminu suka juya, suka duba, suka ga hayaƙi ya murtuke cikin birnin, ya yi sama. 41 Da mutanen Isra'ila suka juyo kansu, sai mutanen Biliyaminu suka tsorata, gama sun ga masifa ta auko musu. 42 Don haka suka juya suka kama gudu suka nufi hamada, amma ba su tsira ba. Aka datse su tsakanin 'yan kwanto da sauran sojojin Isra'ilawa. 43 Suka yi wa mutanen Biliyaminu tarko, suka runtume su ba tsayawa tun daga Menuha har zuwa daura da Gibeya daga gabas. 44 Aka kashe jarumawan mutanen Biliyaminu mutum dubu goma sha takwas (18,000 ). 45 Sauran suka juya, suka gudu, suka nufi wajen hamada zuwa Dutsen Rimmon. A kan hanyoyi, aka kashe musu mutum dubu biyar. Aka kuma runtumi sauran da suka ragu har zuwa Gidom inda suka kashe mutum dubu biyu. 46 Mutanen Biliyaminu da aka kashe a ran nan dubu ashirin da biyar (25,000 ) ne. Dukansu kuwa jarumawa ne. 47 Amma mutum ɗari shida suka juya, suka gudu suka nufi hamada zuwa Dutsen Rimmon inda suka zauna har wata huɗu. 48 Mutanen Isra'ila kuma suka komo, suka fāɗa wa sauran mutanen Biliyaminu. Suka karkashe su, mutane, da dabbobi, da dukan abin da suka iske. Suka ƙone garuruwan wannan yankin ƙasa.

Littafin Mahukunta 21

Mata domin Mutanen Biliyaminu

1 Mutanen Isra'ila kuwa suka yi wa Ubangiji ƙaƙƙarfan alkawari a Mizfa cewa, “Ba wani daga cikinmu da zai ba da 'yarsa aure ga mutumin Biliyaminu.” 2 Sai mutanen Isra'ila suka zo Betel, suka zauna a nan a gaban Allah har maraice. Suka yi makoki mai zafi. 3 Suka ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, me ya sa wannan abu ya faru a cikin Isra'ila, har da za a rasa kabila guda ta Isra'ila?” 4 Kashegari mutanen suka tashi da safe, suka gina bagade a can. Suka miƙa hadayun ƙonawa da na salama. 5 Suka kuma ce, “Daga cikin kabilar Isra'ila, wace ce ba ta halarci wannan taro na gaban Ubangiji ba?” Gama sun riga sun yi ƙaƙƙarfan alkawari cewa, “Duk wanda bai hauro zuwa wurin Ubangiji a Mizfa ba, za a kashe shi.” 6 Jama'ar Isra'ila kuwa suka yi juyayin 'yan'uwansu, mutanen Biliyaminu, suka ce, “Yau an hallaka kabila guda daga cikin Isra'ila. 7 Ƙaƙa za mu yi don mutanen da suka ragu su sami mata. Ga shi, mum riga mu rantse da Ubangiji ba za mu ba su 'ya'yanmu mata su aura ba?” 8 Sa'an nan suka ce, “Wace kabila ce daga cikin kabilar Isra'ila ba ta hauro zuwa wurin Ubangiji a Mizfa ba?” Sai suka ga, ashe, ba wani daga Yabesh-gileyad da ya halarci taron. 9 Gama sa'ad da aka tattara mutanen, aka ga ba wani daga cikin mazaunan Yabesh-gileyad a wurin. 10 Taron jama'a kuma suka aiki jarumawansu mutum dubu goma sha biyu (12,000 ) zuwa Yabesh-gileyad. Suka umarce su cewa, “Ku je ku karkashe mazaunan Yabesh duka har da mata da yara. 11 Abin da za ku yi ke nan, ku je ku kashe dukan maza, da kowace mace wadda ba budurwa ba ce.” 12 Suka sami budurwai ɗari huɗu daga mutanen Yabesh-gileyad, sai suka kawo su zango a Shilo, wadda take a ƙasar Kan'ana. 13 Sa'an nan taron jama'a suka aika wa mutanen Biliyaminu da suke a Dutsen Rimmon, cewa, yaƙi ya ƙare, sai salama. 14 Mutanen Biliyaminu kuwa suka komo, aka ba su budurwan nan da aka bar su da rai aka kawo su Yabesh-gileyad, amma budurwan ba su ishe su ba. 15 Sai mutanen suka yi juyayin mutanen Biliyaminu domin Ubangiji ya naƙasa kabila daga kabilar Isra'ila. 16 Saboda haka dattawan taron jama'a suka ce, “Ƙaƙa za mu yi da waɗanda suka ragu da ba su sami mata ba, da yake an hallaka matan kabilar Biliyaminu?” 17 Sai suka ce, “Tilas, waɗanda suka ragu daga mutanen Biliyaminu su sami gādo domin kada a shafe kabila daga cikin Isra'ila, 18 amma fa ba za mu iya aurar musu da 'ya'yanmu mata ba.” Sun faɗi haka ne kuwa, domin sun riga sun rantse cewa, “Duk wanda ya aurar da 'yarsa ga mutumin Biliyaminu la'ananne ne.” 19 Suka kuma ce, “Ga shi, idin Ubangiji na shekara shekara a Shilo ya kusa.” (Shilo tana arewacin Betel, kudu da Lebona, gabas da hanyar da take tsakanin Betel da Shekem.) 20 Suka umarci mutanen Biliyaminu suka ce, “Ku tafi ku yi kwanto a gonakin inabi, 21 ku lura, idan 'yan matan Shilo sun fito domin su yi rawa, sai ku fito daga cikin gonakin inabi, kowa ya kama daga cikin 'yan matan da ƙarfi, ya sami mata ke nan, ya tafi da ita a ƙasar Biliyaminu. 22 Sa'ad da iyayensu ko 'yan'uwansu sun kawo ƙara gare mu, za mu ce musu, ‘Ku bar mana su, muna roƙonku, domin ba daga wurin yaƙi muka kamo su domin su zama matanmu ba. Amma tun da ba ku ba mu su ba, ba ku da laifin ta da alkawari.’ ” 23 Haka kuwa mutanen Biliyaminu suka yi. Suka kama budurwai gwargwadon yawansu daga cikin masu rawa. Sa'an nan suka koma zuwa yaƙin ƙasarsu ta gādo. Suka sāke gina garuruwansu, suka zauna. 24 Hakanan kuma sauran mutanen Isra'ila suka tashi daga can. Kowa ya tafi wurin kabilarsa, da iyalinsa, da abin da ya mallaka. 25 A lokacin ba sarki a Isra'ila, sai kowa ya yi ta yin abin da ya ga dama.

Rut 1

Elimelek da Iyalinsa a Mowab

1 A zamanin da mahukunta suke mulkin Isra'ila, aka yi yunwa a ƙasar. Sai wani mutumin Baitalami a Yahudiya ya yi ƙaura zuwa ƙasar Mowab, shi da matarsa, da 'ya'yansa maza biyu. 2 Sunan mutumin, Elimelek, matarsa kuwa Na'omi, 'ya'yansu maza kuma Malon da Kiliyon. Su Efratawa ne daga Baitalami ta Yahudiya. Suka tafi Mowab suka zauna a can. 3 Elimelek, mijin Na'omi, ya rasu, aka bar Na'omi da 'ya'yansu maza biyu. 4 Sai suka auri 'yan matan Mowab, Orfa da Rut. Bayan da suka yi wajen shekara goma a can, 5 sai kuma Malon da Kiliyon suka rasu, Na'omi kuwa ta rasa mijinta da kuma 'ya'yanta maza biyu.

Na'omi da Rut sun Komo Baitalami

6 Daga can Mowab, Na'omi ta ji cewa, Ubangiji ya taimaki mutanensa, ya ba su abinci, sai ta tashi daga ƙasar Mowab tare da surukanta. 7 Suka kama hanya zuwa ƙasar Yahudiya. 8 Amma a hanya, sai Na'omi ta ce wa surukanta, “Bari ko waccenku ta koma gidan iyayenta. Ubangiji ya yi muku alheri kamar yadda kuka yi mini alheri, ni da marigayan. 9 Ya sa kuma ko waccenku ta yi aure, ta sami hutawa a gidan miji.” Sa'an nan ta yi bankwana da su ta sumbace su. Sai suka fashe da kuka, 10 suka ce mata, “A'a, mā tafi tare da ke wurin mutanenki.” 11 Amma Na'omi ta ce musu, “Ku koma, 'ya'yana, don me za ku tafi tare da ni? Ina da sauran 'ya'ya maza a cikina ne da za su zama mazajenku? 12 Sai ku koma, 'ya'yana, gama na tsufa da yawa, ba kuma zan sami miji ba. Ko da a ce ina fata in yi aure, a ce ma zan yi aure a daren nan, in haifi 'ya'ya maza, 13 za ku yi ta jira har su yi girma? Ai, ba zai yiwu ba, 'ya'yana. Ina baƙin ciki ƙwarai saboda abin da ya same ku, da yadda Ubangiji ya yi gāba da ni.” 14 Suka sāke fashewa da kuka. Sai Orfa ta yi wa surukarta, sumba, ta yi bankwana da ita, amma Rut ta manne mata. 15 Na'omi ta ce wa Rut, “Kin ga, 'yar'uwarki ta koma wurin mutanenta da wurin gumakanta, sai ki koma, ki bi 'yar'uwarki.” 16 Amma Rut ta ce, “Kada ki yi ta roƙona in rabu da ke, ko in bar binki, gama inda za ki tafi, ni ma can zan tafi, inda kuma za ki zauna, ni ma can zan zauna. Mutanenki za su zama mutanena, Allahnki kuma zai zama Allahna. 17 Inda za ki rasu, ni ma can zan rasu, a binne ni. Idan na bar wani abu ya raba ni da ke, in dai ba mutuwa ba, to, Ubangiji ya yi mini hukunci mai zafi!” 18 Da Na'omi ta ga Rut ta ƙudura ta tafi tare da ita, sai ta ƙyale ta. 19 Su biyu kuwa suka kama hanya har suka isa Baitalami. Da suka isa Baitalami, sai dukan garin ya ruɗe saboda su. Mata suka ce, “Na'omi ce wannan?” 20 Ita kuwa ta ce musu, “Kada ku kira ni Na'omi, wato mai farin ciki, sai dai Mara, wato mai baƙin ciki, gama Mai Iko Dukka ya wahalshe ni ƙwarai. 21 Na tafi a wadace, ga shi, Ubangiji ya komo da ni hannu wofi. Don me kuke kirana mai farin ciki da yake Ubangiji Mai Iko Dukka ya wahalshe ni, ya kuma aukar mini da masifa?” 22 Haka Na'omi ta koma daga ƙasar Mowab tare da surukarta Rut, mutuniyar Mowab. Suka isa Baitalami a farkon kakar sha'ir.

Rut 2

Rut a Gonar Bo'aza

1 Na'omi tana da wani dangin mijinta, Elimelek, sunansa Bo'aza, shi kuwa attajiri ne. 2 Sai Rut, mutuniyar Mowab, ta ce wa Na'omi, “Bari in tafi, in yi kalan hatsi a gonar wanda ya yarda in yi.” Na'omi ta ce mata, “Ki tafi, 'yata.” 3 Rut ta tafi wata gona, tana bin bayan masu girbi, tana kala. Ta yi sa'a kuwa ta fāɗa a gonar Bo'aza, dangin Elimelek. 4 Sai ga Bo'aza ya zo daga Baitalami, ya ce wa masu girbi, “Salamu alaikun.” Suka amsa, “Alaikun salamu.” 5 Sa'an nan Bo'aza ya tambayi baransa da yake shugaban masu girbin, ya ce, “'Yar wace ce wannan?” 6 Baran ya ce, “Ita 'yar Mowab ce wadda ta zo tare da Na'omi daga ƙasar Mowab. 7 Ita ce ta ce mana, ‘In kun yarda, ku bar ni in bi bayan masu girbin, ina kala.’ Haka ta yi ta kala tun da sassafe har yanzu ba hutu, sai dai 'yar shaƙatawar da ta yi kaɗan.” 8 Sa'an nan sai Bo'aza ya ce wa Rut, “Kin ji, 'yata, kada ki bar wannan gona ki tafi wata gona domin kala, amma ki riƙa bin 'yan matan gidana. 9 Ki kula da gonar da suke girbi, ki bi su. Ga shi, na riga na umarci barorina kada su dame ki. Sa'ad da kika ji ƙishirwa, sai ki tafi ki sha ruwa a tuluna, wanda barorin suka ɗebo.” 10 Sai Rut ta rusuna har ƙasa, ta ce masa, “Me ya sa na sami tagomashi a gare ka, har da za ka kula da ni, ni da nake baƙuwa?” 11 Amma Bo'aza ya ce mata, “An faɗa mini dukan abin da kika yi wa surukarki tun lokacin da mijinki ya rasu, da yadda kika bar iyayenki da ƙasarku, kika zo wurin mutanen da ba ki taɓa saninsu ba a dā. 12 Ubangiji Allah na Isra'ila, wanda kika zo neman mafaka gare shi, ya sāka miki da cikakken lada saboda abin da kika yi.” 13 Rut ta ce, “Shugaba, kā yi mini alheri ƙwarai, gama kā ta'azantar da ni, kā yi wa baiwarka maganar alheri, ko da yake ni ba ɗaya daga cikin barorinka ba ce.” 14 Da lokacin cin abinci ya yi, sai Bo'aza ya kira Rut, ya ce, “Zo nan ki ci abinci, ki riƙa tsoma lomarki a ruwan inabin da aka surka.” Sai ta zo, ta zauna kusa da masu girbin. Shi kuwa ya ba ta tumun hatsi. Ta ci, ta ƙoshi har ta bar saura. 15 Sa'ad da ta tashi, za ta yi kala, sai Bo'aza ya umarci barorinsa, ya ce, “Ku bar ta, ta yi kala a tsakanin tarin dammunan, kada ku hana ta. 16 Ku kuma riƙa zarar mata waɗansu daga dammunan don ta ɗauka, kada ku kwaɓe ta.” 17 Ta yi ta kala a gonar har yamma. Ta sussuka abin da ta kalata, ta sami tsaba wajen garwa biyu. 18 Ta ɗauka, ta koma gari, ta nuna wa surukarta abin da ta kalato. Ta kuma kawo mata sauran abincin da ta ci ta ƙoshi har ta rage. 19 Surukarta kuma ta ce mata, “A ina kika yi kala yau? A gonar wa kika yi aiki? Albarka ta tabbata ga wannan mutum wanda ya kula da ke.” Sai ta faɗa mata sunan mutumin da ta yi kala a gonarsa, ta ce, “Sunan mutumin da na yi kala a gonarsa yau, Bo'aza.” 20 Na'omi ta ce wa Rut, “Ubangiji wanda bai daina nuna alheri ga masu rai da marigayan ba, ya sa masa albarka.” Ta ƙara da cewa, “Ai, mutumin, shi danginmu ne na kusa.” 21 Rut kuma, mutuniyar Mowab, ta ce, “Banda wannan ma, ya ce mini, ‘Ki riƙa bin barorina, har lokacin da suka gama mini girbin.’ ” 22 Sa'an nan Na'omi ta ce wa Rut, “Madalla, 'yata, ki riƙa bin 'yan matan gidansa, kada ki tafi wata gona dabam.” 23 Sai ta riƙa bin 'yan matan gidan Bo'aza. Ta yi ta kala har aka gama girbin sha'ir da na alkama, tana zaune tare da surukarta, wato Na'omi.

Rut 3

Bo'aza da Rut a Masussuka

1 Wata rana, Na'omi ta ce wa Rut, “'Yata, ya kamata in nemar miki miji don ki sami gida inda za ki huta, ki ji daɗi. 2 Bo'aza wanda kika yi aiki da barorinsa danginmu ne. Ga shi, zai tafi sussukar sha'ir a masussuka da maraice. 3 Sai ki yi wanka, ki shafa man ƙanshi, ki yafa tufafinki na ado, ki tafi masussukar, amma kada ki bari ya san zuwanki, sai bayan da ya riga ya ci ya sha. 4 Sa'ad da ya kwanta, sai ki lura da inda ya kwanta, sa'an nan ki tafi, ki buɗe mayafinsa a wajen ƙafafunsa, ki kwanta a ciki. Zai kuwa faɗa miki abin da za ki yi.” 5 Rut ta amsa, “Zan yi dukan abin da kika faɗa.” 6 Rut kuwa ta gangara zuwa masussukar, ta yi yadda surukarta ta faɗa mata. 7 Sa'ad da Bo'aza ya ci ya sha yana cikin jin daɗi, sai ya je ya kwanta kusa da tsibin tsabar sha'ir. Sa'an nan Rut ta tafi a hankali, ta buɗe mayafin da ya rufa da shi wajen ƙafafunsa, ta kwanta a ciki. 8 Da tsakar dare, sai mutumin ya farka a firgice, ya juya, sai ga mace kwance a wajen ƙafafunsa. 9 Ya ce, “Wace ce?” Sai ta amsa, “Ni ce Rut, baranyarka, sai ka rufe ni da mayafinka, gama kai dangi ne na kusa.” 10 Sa'an nan ya ce, “Ubangiji ya sa miki albarka 'yata, yanzu kin nuna alheri mafi girma fiye da na dā da yake ba ki nemi saurayi, matalauci ko attajiri ba. 11 Yanzu dai, 'yata, kada ki damu, zan yi miki dukan abin da kika roƙa, gama dukan mutanen garin sun sani ke macen kirki ce. 12 Gaskiya ce, ni dangi na kusa ne, amma akwai wanda yake dangi na kusa fiye da ni. 13 Ki dakata nan sai gobe, da safe za mu gani, idan shi zai cika wajibin dangi na kusa a gare ki. Idan ya cika, to, da kyau, amma idan bai cika ba, na rantse da Allah mai rai, zan cika wajibin dangi na kusa a gare ki. Ki kwanta sai da safe.” 14 Sai ta kwanta a wajen ƙafafunsa har safiya. Sa'an nan ta tashi tun da jijjifi kafin a iya gane fuskar mutum, gama ba ya so a sani mace ta zo masussukar. 15 Bo'aza ya ce mata, “Kawo mayafinki, ki shimfiɗa shi.” Sai ta shimfiɗa mayafin, ya zuba mata sha'ir ya kusa garwa huɗu ya aza mata a kā. Sa'an nan ta koma gari. 16 Lokacin da ta zo wurin surukarta, sai surukarta ta ce mata, “'Yata, ina labari?” Sai ta faɗa mata dukan abin da mutumin ya faɗa mata. 17 Ta kuma ce, “Ga sha'ir da ya ba ni, gama ya ce, ‘Ba za ki koma wurin surukarki hannu wofi ba.’ ” 18 Sai surukarta ta ce, “Ki jira dai, 'yata, har ki ga yadda al'amarin zai zama, gama mutumin ba zai huta ba, sai ya daidaita al'amarin a yau.”

Rut 4

Bo'aza ya Auri Rut

1 Bo'aza fa ya tafi, ya zauna a dandalin ƙofar gari. Sai ga wani daga cikin waɗanda hakkinsu ne su ɗauki Rut, shi ne kuwa wanda Bo'aza ya ambata, ya iso. Bo'aza kuwa ya ce masa, “Ratso nan, wāne, ka zauna.” Sai ya ratsa, ya zauna. 2 Bo'aza ya kuma kirawo goma daga cikin dattawan gari, ya ce musu, “Ku zauna nan.” Suka kuwa zauna. 3 Sa'an nan ya ce wa dangin nan nasa na kusa, “Ga Na'omi wadda ta komo daga ƙasar Mowab, tana so ta sayar da gonar Elimelek danginmu. 4 Don haka na ga ya kamata in sanar da kai cewa, ka saye ta a gaban waɗanda suke zaune a nan, da a gaban dattawan jama'a. Idan za ka fanshi gonar sai ka fanshe ta, idan kuwa ba za ka fansa ba, ka faɗa mini don in sani, gama daga kai sai ni muke da izinin fansar gonar.” Sai mutumin ya ce, “Zan fanshe ta.” 5 Sa'an nan Bo'aza ya ce, “A ranar da ka sayi gonar daga hannun Na'omi, sai kuma ka ɗauki Rut, mutuniyar Mowab, matar marigayin, domin ka ta da zuriyar da za ta gaji marigayin.” 6 Sai dangin nan mafi kusa ya ce, “Ba zan iya ɗaukar Rut ba, domin kada in ɓata nawa gādo. Na bar maka ka ɗauke ta gama ni ba zan iya ba.” 7 Wannan ita ce al'adar Isra'ilawa a dā a kan sha'anin fansa ko musaya, don tabbatar da al'amarin. Sai mai sayarwar ya tuɓe takalminsa ya ba mai sayen. Wannan ita ce hanyar tabbatarwa a cikin Isra'ila. 8 Saboda haka a sa'ad da dangin nan mafi kusa ya ce wa Bo'aza, “Sai ka saye ta,” sai ya tuɓe takalminsa ya ba Bo'aza. 9 Sa'an nan Bo'aza ya ce wa dattawan da dukan jama'ar da suke wurin, “Yau ku ne shaidu, cewa, na sayi dukan abin da yake na Elimelek, da na Kiliyon, da na Malon daga hannun Na'omi. 10 Game da wannan kuma Rut, mutuniyar Mowab, matar marigayi Malon, ta zama matata domin in wanzar da sunan marigayin cikin gādonsa, don kada sunansa ya mutu daga na 'yan'uwansa, da kuma a garinsu. Ku ne fa shaidu a yau.” 11 Dukan jama'a suka ce, “Mu ne shaidu, Ubangiji ya sa matar da za ta zo gidanka ta zama kamar Rahila da Lai'atu waɗanda suka gina gidan Isra'ila. Allah ya arzuta ka cikin Efrata, ya sa ka yi suna a cikin Baitalami, 12 gidanku kuma ya zama kamar gidan Feresa, wanda Tamar ta haifa wa Yahuza, saboda 'ya'yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace.” 13 Bo'aza kuwa ya auri Rut, ta zama matarsa. Ya kuma shiga wurinta, Ubangiji kuwa ya sa ta yi ciki, ta haifa masa ɗa. 14 Sai mata suka ce wa Na'omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, da bai bar ki bā dangi na kusa ba, Allah ya sa ɗan ya yi suna a cikin Isra'ila. 15 Ya zama mai sanyaya miki rai, mai goyon tsufanki, gama surukarki wadda take ƙaunarki, wadda ta fiye miki 'ya'ya maza bakwai, ita ta haife shi.” 16 Sa'an nan Na'omi ta ɗauki yaron ta rungume shi a ƙirjinta, ta zama mai renonsa. 17 Mata, maƙwabta kuwa suka ce, “An haifa wa Na'omi ɗa!” Suka raɗa masa suna Obida, shi ne mahaifin Yesse, uban Dawuda.

Asalin Zuriyar Dawuda

18-22 Wannan shi ne asalin zuriyar Dawuda. Aka fara daga Feresa zuwa Dawuda. Feresa ne mahaifin Hesruna, Hesruna kuma ya haifi Arama, Arama ya haifi Amminadab, Amminadab kuma ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon, Salmon kuma ya haifi Bo'aza, Bo'aza ya haifi Obida, Obida kuma ya haifi Yesse, sa'an nan Yesse ya haifi Dawuda.

1 Sama’ila 1

Haihuwar Sama'ila

1 Akwai wani mutum daga kabilar Ifraimu sunansa Elkana, yana zaune a Rama, a ƙasar tudu ta Ifraimu. Shi ɗan Yeroham ne, jika ga Eliyab, na iyalin Nahat, daga zuriyar Zuf. 2 Yana da mata biyu, sunayensu Hannatu da Feninna. Feninna tana da 'ya'ya, amma Hannatu ba ta haihuwa. 3 A kowace shekara Elkana yakan haura daga garinsu zuwa Shilo domin ya miƙa wa Ubangiji Mai Runduna hadaya, ya kuma yi masa sujada. 'Ya'yan Eli, maza biyu, Hofni da Finehas, su ne firistoci na Ubangiji a can. 4 Duk lokacin da Elkana ya miƙa hadayarsa, sai ya ba Feninna da 'ya'yanta mata da maza nasu rabo. 5 Amma Hannatu, sai ya ba ta babban rabo guda ɗaya, gama yana ƙaunarta, amma Ubangiji ya kulle mahaifarta. 6 Kishiyarta takan tsokane ta don ta ji haushi, gama Ubangiji ya hana mata haihuwa. 7 Haka aka yi ta yi kowace shekara, duk lokacin da suka tafi domin yin sujada, sai Feninna ta tsokane ta. Don haka Hannatu ta yi ta kuka, ta ƙi cin abinci. 8 Elkana mijinta kuwa, ya ce mata, “Hannatu, me ya sa kike kuka? Me ya sa kike ƙin cin abinci? Me ya sa zuciyarki ta ɓaci? Ni ban fi 'ya'ya maza goma a gare ki ba?”

Hannatu da Eli

9 Wata rana a Shilo bayan da sun gama cin abinci, sai Hannatu ta tashi. Eli, firist, kuwa yana zaune a kujera a bakin ƙofar masujadar Ubangiji. 10 Hannatu tana fama da baƙin ciki ƙwarai, sai ta yi addu'a, tana kuka da ƙarfi ga Ubangiji. 11 Ta yi wa'adi, ta ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, idan lalle ka dube ni, ni baiwarka, ka tuna da ni, ba ka manta da ni baiwarka ba, amma ka ba ni ɗa, ni ma sai in ba da shi ga Ubangiji dukan kwanakinsa, aska kuwa ba za ta taɓa kansa ba.” 12 Eli kuwa ya lura da bakin Hannatu sa'ad da take yin addu'a. 13 Gama ta yi addu'ar a zuci, ba a jin muryarta, sai dai leɓunanta suke motsi. Don haka Eli ya zaci tana maye ne, 14 ya kuwa ce mata, “Sai yaushe za ki daina maye? Ki daina shan ruwan inabi.” 15 Hannatu kuwa ta amsa ta ce, “Ba haka ba, ya shugabana, ni mace ce da ke baƙin ciki ƙwarai. Ni ban sha ruwan inabi, ko wani abu mai sa maye ba, amma ina faɗa wa Ubangiji dukan abin da yake a zuciyata. 16 Kada ka zaci ni 'yar iska ce. Ni dai ina faɗar damuwata da tsokanar da ake yi mini ne.” 17 Sai Eli ya ce mata, “Ki sauka lafiya, Allah na Isra'ila ya amsa miki roƙonki.” 18 Ita kuma ta amsa, ta ce, “Bari baiwarka ta sami tagomashi a gare ka.” Sa'an nan ta tafi, ta ci abinci. Ba ta ƙara ɓata ranta ba.

Haihuwar Sama'ila da Miƙawarsa

19 Elkana da iyalinsa suka tashi tun da sassafe suka yi wa Ubangiji sujada, sa'an nan suka koma gidansu a Rama. Elkana fa ya kwana da matarsa, Hannatu. Ubangiji kuwa ya tuna da ita. 20 Ta yi juna biyu, ta haifa ɗa, ta raɗa masa suna Sama'ila, wato “Na roƙo shi daga wurin Ubangiji.” 21 Elkana da iyalinsa duka suka tafi Shilo domin su miƙa wa Ubangiji hadaya ta shekara shekara, ya kuma cika wa'adinsa. 22 Amma Hannatu ba ta tafi ba, sai ta ce wa mijinta, “Da zarar an yaye yaron, zan kai shi domin ya zauna a gidan Ubangiji muddin ransa.” 23 Elkana ya ce mata, “Ki yi abin da kika ga ya fi kyau, ki jira har ki yaye shi, Ubangiji dai ya cika maganarsa.” Hannatu ta tsaya a gida, ta yi ta renon ɗanta. 24 Sa'ad da ta yaye yaron, sai ta ɗauke shi, ta kuma ɗauki bijimi bana uku, da mudun gari, da salkar ruwan inabi, ta kai shi ɗakin Ubangiji a Shilo, yaron kuwa yana ɗan ƙarami. 25 Sai suka yanka bijimin, suka kuma kai yaron wurin Eli. 26 Sa'an nan Hannatu ta ce, “Gafara dai, ba ka tuna da ni ba? Ai, ni ce matar da ta taɓa tsayawa a gabanka, tana roƙon Ubangiji. 27 Na roƙi Ubangiji wannan yaro, Ubangiji kuwa ya biya mini bukatata da na roƙa a gare shi. 28 Saboda haka nake miƙa shi ga Ubangiji muddin ransa. Ya zama na Ubangiji.” A can ya yi wa Ubangiji sujada.

1 Sama’ila 2

Waƙar Hannatu

1 Hannatu kuwa ta yi addu'a ta ce, “Ubangiji ya cika zuciyata da murna. Ina farin ciki da abin da ya yi. Ina yi wa maƙiyana dariya, Ina matuƙar murna domin Allah ya taimake ni. 2 “Babu wani mai tsarki kamar Ubangiji, Babu wani mai kama da shi, Ba mai kiyaye mu kamar Allahnmu. 3 Kada ku ƙara yin magana ta girmankai, Ku daina maganganunku na fariya, Gama Ubangiji Allah shi ne masani, Yana kuma auna dukkan aikin da mutum ya yi. 4 An kakkarya bakunan ƙarfafan sojoji, Amma rarrauna ya zama mai ƙarfi. 5 Ƙosassun mutane suna ƙodago saboda abinci, Masu fama da yunwa kuwa sun daina jin yunwa. Bakarariya ta haifi 'ya'ya bakwai, Wadda ta haifi 'ya'ya da yawa kuwa ta rasa su duka. 6 Ubangiji ne yake kashewa, ya kuma rayar, Yana kai mutane kabari, Ya kuma tā da su. 7 Yakan sa waɗansu mutane su zama matalauta, Waɗansu kuwa attajirai. Yakan ƙasƙantar da waɗansu, Ya kuma ɗaukaka waɗansu. 8 Yakan tā da matalauci daga cikin ƙura, Yakan ɗaga mai bukata daga zaman baƙin ciki. Ya sa su zama abokan 'ya'yan sarki, Ya ɗora su a wurare masu maƙami. Harsashin ginin duniya na Ubangiji ne, A kansu ya kafa duniya. 9 “Zai kiyaye rayukan amintattun mutanensa, Amma mugayen mutane za su lalace cikin duhu, Ba ƙarfin mutum yake sa ya yi nasara ba. 10 Za a hallakar da maƙiyan Ubangiji, Zai yi musu tsawa daga Sama. Ubangiji zai hukunta dukan duniya, Zai ba sarkinsa iko, Zai sa zaɓaɓɓen sarkinsa ya zama mai nasara.” 11 Sa'an nan Elkana ya koma gidansa a Rama, amma yaron ya zauna a Shilo, yana aikin Ubangiji a hannun Eli, firist.

'Ya'yan Eli Maza

12 'Ya'yan Eli, maza kuwa, ba su da kirki, ba su kula da Ubangiji ba. 13 Ko ka'idodi game da abin da firistoci za su karɓa a hannun jama'a. A maimakon haka, lokacin da mutum ya je domin ya miƙa hadayarsa, sai baran firist ya zo da rino a hannunsa a sa'ad da ake dafa naman. 14 Sai ya caka rinon a cikin tukunyar, to, duk abin da ya cako wannan ya zama na firist. Haka suka yi ta yi wa dukan Isra'ilawa da suka zo miƙa hadaya a Shilo. 15 Tun kuma kafin a ƙona kitse, baran firist ɗin yakan zo ya ce wa wanda yake yin hadayar. “Ka ba ni wanda firist zai gasa, gama ba zai karɓi dafaffen nama daga gare ka ba, sai dai ɗanye.” 16 Idan mutumin ya ce, “To, bari a ƙona kitsen tukuna, sa'an nan ka ɗibi iyakar abin da kake bukata,” sai baran firist ɗin ya ce, “A'a, tilas ne ka ba ni yanzu, idan kuwa ba haka ba, zan ɗiba ƙarfi da yaji!” 17 Zunubin 'ya'yan nan maza na Eli ya yi yawa a gaban Ubangiji, gama sun wulakanta hadayar Ubangiji ƙwarai da gaske.

Sama'ila a Shilo

18 Yaron nan Sama'ila yana ta aiki gaban Ubangiji, yana sāye da falmaran. 19 A kowace shekara mahaifiyarsa takan ɗinka 'yar rigar ado, ta kai masa a sa'ad da ita da mijinta sukan tafi miƙa hadayarsu ta shekara shekara. 20 Eli kuwa yakan sa wa Elkana da matarsa albarka, ya ce, “Ubangiji ya ba ka waɗansu 'ya'ya ta wurin matan nan a maimakon wanda kuka ba Ubangiji.” Bayan wannan sai su koma gida. 21 Ubangiji ya sa wa Hannatu albarka, ta haifi 'ya'ya maza uku da mata biyu. Yaron nan Sama'ila kuwa ya girma a gaban Ubangiji.

Eli da 'Ya'yansa Maza

22 Eli kuwa ya tsufa ƙwarai, yana kuma jin dukan abin da 'ya'yansa maza suke yi wa Isra'ilawa, da yadda suke kwana da matan da suke aiki a ƙofar alfarwa ta sujada. 23 Sai ya ce musu, “Me ya sa kuke irin waɗannan abubuwa? Gama kowa yana faɗa mini irin mugayen abubuwan da kuke aikatawa. 24 Haba 'ya'yana, ku bari! Jama'ar Ubangiji suna ta magana a kan wannan mugun abu. 25 Idan mutum ya yi wa wani laifi, Allah yakan kāre shi, amma idan mutum ya yi wa Ubangiji zunubi, wa zai kāre shi?” Amma ba su ji maganar mahaifinsu ba, gama Ubangiji ya riga ya yi shirin kashe su.

Annabci a kan Gidan Eli

26 Yaron nan Sama'ila ya yi ta girma da samun tagomashi a gaban Ubangiji da kuma mutane. 27 Wani annabi ya zo wurin Eli da saƙo daga wurin Ubangiji ya ce, “Sa'ad da kakanka Haruna da iyalinsa suke bauta wa Fir'auna a Masar, na bayyana kaina gare shi. 28 Na zaɓi iyalinsa daga dukan kabilan Isra'ila domin su zama firistocina, su riƙa aiki a bagade, suna ƙona turare, su riƙa ɗaukar keɓaɓɓen akwatina cikin yi mini aiki. Na kuma yardar musu su sami rabonsu daga hadayun da aka ƙona a kan bagade. 29 Me ya sa kuke haɗama a kan hadayuna da sadakokin da na umarta? Eli, don me kake girmama 'ya'yanka fiye da ni, ka bar su suna ta cinye rabo mafi kyau na hadayun jama'ata Isra'ila? 30 Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na yi alkawari a dā cewa, ‘Kai da iyalinka da danginka za ku yi mini aikin firist har abada.’ Amma yanzu na ce ba zan yarda da wannan ba. Waɗanda suke girmama ni, zan girmama su. Waɗanda suke raina ni zan ƙasƙantar da su ƙwarai. 31 Ga shi, lokaci yana zuwa da zan karkashe samari cikin iyalinka da danginka, har da ba za a sami wanda zai rayu har ya tsufa a gidanka ba. 32 Za ka kasance da damuwa da jin kishi, za ka duba dukan albarkun da zan sa wa Isra'ila, amma a gidanka ba za a taɓa samun wanda zai rayu har ya tsufa ba. 33 Zan dai bar ɗaya daga zuriyarka da rai, zai yi mini aikin firist, amma zai makance ya fid da zuciya ga kome. Dukan sauran zuriyarka kuwa za su yi mutuwa ƙarfi da yaji. 34 Lokacin da 'ya'yanka biyu, Hofni da Finehas, za su mutu rana ɗaya wannan zai nuna maka abin da na faɗa sai ya cika. 35 Zan zaɓar wa kaina amintaccen firist wanda zai aikata abin da nake so ya yi, zan kuwa ba shi zuriya da koyaushe za su yi aiki a gaban zaɓaɓɓen sarkina. 36 Dukan wanda ya ragu daga zuriyarka zai je wurin sarki ya roƙi kuɗi da abinci, zai kuma roƙa a yardar masa ya taimaki firistoci da aiki domin ya sami abin da zai ci.”

1 Sama’ila 3

Ubangiji ya Kira Sama'ila

1 Yaron nan Sama'ila yana yi wa Ubangiji aiki a hannun Eli. A lokacin nan Ubangiji bai cika yin magana da mutane ba, ba safai kuma ake samun wahayi ba. 2 Wata rana da dare Eli wanda ya kusa makancewa har ba ya iya gani sosai, yana kwance a masujada. 3 Fitilar Ubangiji kuwa tana ci. Sama'ila kuma yana kwance a masujada inda akwatin alkawarin Allah yake. 4 Ubangiji kuwa ya kira Sama'ila. Sama'ila ya ce, “Na'am.” 5 Ya sheƙa zuwa wurin Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce masa, “Ban kira ka ba, koma ka kwanta.” Sai Sama'ila ya koma ya kwanta. 6 Ubangiji ya sāke kiran Sama'ila. Sama'ila ya tashi ya tafi wurin Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Amma Eli ya ce, “Ban kira ka ba, ɗana koma ka kwanta.” 7 (Sama'ila dai bai san Ubangiji ba tukuna, gama Ubangiji bai riga ya fara magana da shi ba.) 8 Ubangiji kuma ya kira Sama'ila sau na uku. Sai kuma Sama'ila ya tashi ya nufi Eli, ya ce, “Ga ni, gama ka kira ni.” Sa'an nan Eli ya gane Ubangiji ne yake kiran yaron, 9 saboda haka Eli ya ce wa Sama'ila ya koma ya kwanta, idan an sāke kiransa sai ya ce, “Ya Ubangiji, ka yi magana, gama bawanka yana kasa kunne.” Sama'ila kuwa ya koma ya kwanta. 10 Ubangiji kuma ya zo ya tsaya, ya yi kira kamar dā, ya ce, “Sama'ila! Sama'ila!” Sama'ila ya amsa ya ce, “Ka yi magana, gama bawanka yana kasa kunne.” 11 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Sama'ila, “Zan yi wa Isra'ilawa wani abu, duk wanda ya ji kuwa zai razana. 12 A ranar zan cika abin da na faɗa game da Eli da iyalinsa daga farko har zuwa ƙarshe. 13 Na fāɗa masa zan hukunta gidansa har abada saboda 'ya'yansa sun faɗi mugayen maganganu a kaina. Eli kuwa ya sani, amma bai kwaɓe su ba. 14 Domin haka na faɗa da ƙarfi, cewa laifin gidan Eli ba za a yi kafararsa da sadaka, ko da hadaya ba har abada.” 15 Sama'ila ya kwanta har safiya, sa'an nan ya buɗe ƙofofi. Amma ya ji tsoron faɗa wa Eli wahayin. 16 Amma Eli ya kira shi, ya ce, “Ya ɗana, Sama'ila.” Sama'ila ya ce, “Ga ni.” 17 Eli ya tambaye shi, ya ce, “Me Ubangiji ya faɗa maka? Kada ka ɓoye mini. Allah zai hukunta ka idan ka ɓoye mini abin da ya faɗa maka.” 18 Sama'ila kuwa ya faɗa masa kome da kome, bai ɓoye masa kome ba. Sai Eli ya ce, “Ai, Ubangiji ne, bari ya yi abin da ya yi masa daidai.” 19 Sama'ila fa ya yi girma, Ubangiji yana tare da shi. Dukan maganarsa kuwa Ubangiji yana cika ta. 20 Dukan mutanen Isra'ila fa daga wannan kusurwar ƙasa zuwa wancan, sun tabbata Sama'ila annabin Ubangiji ne. 21 Ubangiji kuma ya yi ta bayyana a Shilo inda ya bayyana kansa ga Sama'ila, ya kuma yi magana da shi. Duk lokacin da Sama'ila ya yi magana dukan mutanen Isra'ila suna kasa kunne.

1 Sama’ila 4

Filistiyawa sun Ƙwace Akwatin Alkawari

1 A wannan lokaci Isra'ilawa suka yi shiri su yi yaƙi da Filistiyawa, Isra'ilawa suka kafa sansaninsu a Ebenezer, Filistiyawa kuma suka kafa nasu a Afek. 2 Filistiyawa suka shirya su fara yaƙi. Bayan yaƙi mai zafi, sai Filistiyawa suka ci Isra'ilawa, suka kashe mutane wajen dubu huɗu (4,000 ) a bakin dāga. 3 Da sojojin da suka ragu suka koma sansani, sai shugabannin Isra'ila suka ce, “Me ya sa Ubangiji ya sa Filistiyawa suka ci mu yau? Bari mu kawo akwatin alkawarin Ubangiji daga Shilo ya kasance tare da mu, ya cece mu daga ikon abokan gābanmu.” 4 Sai suka aika zuwa Shilo aka kawo akwatin alkawarin Ubangiji Mai Runduna, wanda yake zaune a tsakanin kerubobi. 'Ya'yan nan na Eli, maza guda biyu, wato Hofni da Finehas, suna tare da akwatin alkawarin. 5 Da akwatin alkawarin Ubangiji ya iso sansanin, sai dukan mutanen Isra'ila suka yi sowa da ƙarfi, har ƙasa ta amsa. 6 Da Filistiyawa suka ji amon sowar suka ce, “Ina ma'anar irin wannan babbar sowa a sansanin Ibraniyawa?” Da suka gane akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga sansanin, 7 sai Filistiyawa suka tsorata, suka ce, “Allah ya shiga sansanin, kaitonmu, gama ba a taɓa yin irin wannan abu ba. 8 Mun shiga uku, wa zai cece mu daga hannun allolin nan masu iko? Waɗannan suka karkashe Masarawa a hamada! 9 Ya ku Filistiyawa, ku yi ƙarfin hali, ku yi jaruntaka don kada ku zama bayin Ibraniyawa kamar yadda suka zama bayinku, ku yi jaruntaka ku yi yaƙi.” 10 Filistiyawa kuwa suka yi yaƙi gadan-gadan, suka ci mutanen Isra'ila. Mutanen Isra'ila suka gudu, kowa ya nufi gidansa. Aka kashe Isra'ilawa da yawa, wato mutum dubu talatin (30,000 ). 11 Aka kuma ƙwace akwatin alkawarin Ubangiji, 'ya'yan Eli guda biyu, Hofni da Finehas kuma, aka kashe su.

Mutuwar Eli

12 Wani mutumin kabilar Biliyaminu ya gudu daga dāgar yaƙin ya zo Shilo da tufafinsa ketattu ga kuma ƙura a kansa. 13 Sa'ad da ya iso, Eli yana zaune a kujerarsa a bakin hanya, yana jira, gama zuciyarsa ta damu saboda akwatin alkawarin Allah. Da mutumin ya shiga gari ya ba da labari, dukan garin ya ruɗe da kuka. 14 Sa'ad da Eli ya ji kukan, sai ya tambaya ya ce, “Me ake wa kuka?” Mutumin kuwa ya gaggauta zuwa wurin Eli ya faɗa masa. 15 (Eli yana da shekara tasa'in da takwas, ya kuwa makance ɗungum.) 16 Mutumin ya ce wa Eli, “Yau daga wurin yaƙin na tsere, na gudo gida.” Eli ya ce, “Dana, me ya faru?” 17 Sai wanda ya kawo labarin ya ce, “Isra'ilawa sun gudu a gaban Filistiyawa, an kashe mutane da yawa, har ma da 'ya'yanka biyu, Hofni da Finehas, sun rasu, an kuma ƙwace akwatin alkawarin Allah.” 18 Da aka ambaci akwatin alkawari, sai Eli ya tuntsura da baya daga inda yake zaune a bakin ƙofar gari, wuyansa kuwa ya karye, ya mutu, gama shi tsoho ne, mai ƙiba. Ya shekara arba'in yana shugabancin Isra'ila.

Mutuwar Matar Finehas

19 Surukar Eli, matar Finehas, tana da juna biyu, ta kusa haihuwa. Sa'ad da ta ji labari an ƙwace akwatin alkawarin Allah, surukinta kuma da mijinta sun rasu, sai ta kama naƙuda farat ɗaya, ta haihu. 20 Tana bakin mutuwa, matan kuwa da suke taimakonta suka ce mata, “Ki yi ƙarfin hali, gama kin haifi ɗa namiji.” Amma ba ta amsa ba, ba ta kuma kula ba. 21 Sai ta sa wa yaron suna Ikabod, wato ɗaukaka ta rabu da Isra'ila domin an ƙwace akwatin alkawarin Allah, domin kuma surukinta da mijinta sun rasu. 22 Ta ce, “Daukaka ta rabu da Isra'ila, gama an ƙwace akwatin alkawarin Allah.”

1 Sama’ila 5

Akwatin Alkawarin Allah a wurin Filistiyawa

1 Sa'ad da Filistiyawa suka ƙwace akwatin alkawarin Allah a Ebenezer, suka kai shi Ashdod. 2 Suka shigar da shi cikin haikalin gunkinsu, Dagon, suka ajiye shi kusa da gunkin. 3 Kashegari da safe sa'ad da mutanen Ashdod suka tashi, sai suka ga Dagon ya faɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Suka ta da shi, suka ajiye a wurinsa. 4 Kashegari da safe kuma da suka tashi, sai suka ga Dagon ya faɗi rubda ciki a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Kan Dagon da hannuwansa a gutsure, suna nan a dokin ƙofa. Gangar jikin ce ta ragu. 5 (Saboda haka firistocin Dagon da waɗanda suke sujada a haikalin Dagon ba su taka dokin ƙafar Dagon a Ashdod ba har wa yau.)

6 Ubangiji kuwa ya hukunta mutanen Ashdod ƙwarai da gaske, ya kuma razanar da su, ya azabtar da su da marurai, su da na kewaye da su. 7 Da mutanen Ashdod suka ga yadda abin yake, sai suka ce, “Kada a bar akwatin alkawarin Allah na Isra'ila tare da mu, gama ya tsananta mana, mu da Dagon, allahnmu.” 8 Sai suka aika, aka kirawo dukan sarakunan Filistiyawa, su biyar, suka ce musu, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Allah na Isra'ila?” Suka ce, “Sai a kai shi Gat.” Su kuwa suka kai shi can. 9 Amma da suka kai shi can sai Ubangiji ya hukunta birnin, ya gigita su, ya yi musu azaba da marurai, yara da manya. 10 Sai suka kai akwatin alkawarin Allah zuwa Ekron. Amma da aka kai shi Ekron, sai mutanen Ekron suka fashe da kuka, suka ce, “Sun kawo mana akwatin alkawarin Allah na Isra'ila don ya kashe dukanmu.” 11 Suka kuma aika a kirawo sarakunan Filistiyawa, suka ce, “Ku aika da akwatin alkawarin Allah na Isra'ila zuwa inda ya fito don kada ya kashe mu duk da iyalinmu.” Dukan birnin ya gigita ƙwarai, gama Ubangiji yana hukunta su da tsanani. 12 Marurai sun fito wa mutanen da ba su mutu ba, mutane suka yi kuka domin allolinsu su cece su.

1 Sama’ila 6

Filistiyawa sun Komar da Akwatin Alkawari

1 Akwatin alkawarin Ubangiji ya yi wata bakwai a ƙasar Filistiyawa. 2 Filistiyawa suka kirawo firistocinsu da bokayensu, suka ce, “Me za mu yi da akwatin alkawarin Ubangiji? Ku sanar da mu yadda za mu komar da shi inda ya fito.” 3 Sai firistocin da bokayen suka ce, “Idan za ku komar da akwatin alkawarin Allah na Isra'ila, dole ku aika da kyauta tare da shi domin zunubinku. Ba dama a komar da akwatin alkawarin hannu wofi. Ta haka za ku sami lafiya, za ku kuma san dalilin da ya sa ya yi ta hukunta ku.” 4 Suka ce, “Wace irin hadaya za mu bayar?” Firistocin suka ce, “Sai ku yi marurai biyar na zinariya da ɓeraye biyar na zinariya bisa ga yawan sarakunan Filistiyawa, gama annoba iri ɗaya ce ta same ku da sarakunanku. 5 Ku yi siffofin marurai da na ɓeraye waɗanda suka lalatar da ƙasar, ku ba da girma ga Allah na Isra'ila, watakila zai ɗauke hukuncinsa a kanku, da allolinku, da ƙasarku. 6 Don me za ku taurare zukatanku kamar yadda Masarawa da Fir'auna suka taurare zukatansu? Sai da Allah ya wahalshe su tukuna kafin su sallami Isra'ilawa su tafi. 7 Yanzu kuwa ku yi sabon keken shanu, ku sami shanun tatsa biyu waɗanda ba a taɓa sa musu karkiya ba, ku ɗaura wa shanun keken, amma ku tsare 'yan maruƙansu a gida. 8 Sa'an nan ku sa akwatin alkawarin Ubangiji a keken shanun, ku kuma sa siffofin maruran da na ɓerayen a cikin wani akwati ku ajiye a gefen akwatin alkawarin. Ku aika da waɗannan abubuwa tare da shi don yin hadaya ta laifi. Sa'an nan ku sa shi a hanya, a bar shi, ya tafi. 9 Ku zuba ido, ku gani, idan ya kama hanya zuwa Bet-shemesh, to, shi ne ya kawo mana wannan babbar masifa, amma idan ba haka ba, za mu sani ba shi ne ya buge mu ba, tsautsayi ne kawai.” 10 Suka yi yadda aka faɗa musu, suka sami shanun tatsa biyu, suka ɗaura musu karkiyar keken. Suka tsare 'yan maruƙansu a gida. 11 Suka sa akwatin alkawarin Ubangiji a keken, da akwatin siffofin ɓerayen zinariya da siffofin maruran. 12 Shanun kuwa suka kama hanya sosai wadda ta nufi wajen Bet-shemesh, suna tafe, suna ta kuka, ba su kauce zuwa dama ko hagu ba, sarakunan Filistiyawa suna biye da su, har zuwa iyakar Bet-shemesh. 13 Mutanen Bet-shemesh kuwa suna cikin yankan alkamarsu a kwari. Da suka ɗaga kai sai suka ga akwatin alkawari, sai suka yi murna matuƙa. 14 Keken shanun kuwa ya shiga gonar Joshuwa mutumin Bet-shemesh, ya tsaya a wurin, kusa da wani babban dutse. Mutanen suka faskare keken shanun, suka yanka shanun suka ƙone su hadaya ga Ubangiji. 15 Lawiyawa kuwa suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji da akwatin da yake gefensa wanda aka sa siffofin zinariya a ciki. Suka ajiye su a kan babban dutsen. Mutanen Bet-shemesh kuwa suka miƙa wa Ubangiji hadaya ta ƙonawa da waɗansu hadayu kuma a wannan rana. 16 Sarakunan nan biyar na Filistiyawa sun ga an yi wannan, sa'an nan suka koma Ekron a ran nan. 17 Waɗannan su ne siffofin marurai na zinariya waɗanda Filistiyawa suka aika domin yin hadaya don laifi ga Ubangiji, ɗaya domin Ashdod, ɗaya domin Gaza, ɗaya domin Ashkelon, ɗaya domin Gat, ɗaya kuma domin Ekron. 18 Suka kai siffofin ɓerayen nan na zinariya kuwa domin garuruwa biyar masu garu da ƙauyuka marasa garu na sarakunan Filistiyawa. Babban dutse inda suka ajiye akwatin Ubangiji yana nan har wa yau a saurar Joshuwa Bet-shemesh. 19 Sai Ubangiji ya kashe mutum saba'in daga cikin mutanen Bet-shemesh domin sun leƙa cikin akwatin alkawari na Ubangiji. Mutanen kuwa suka yi makoki ƙwarai domin Ubangiji ya kashe mutane da yawa daga cikinsu.

Akwatin Alkawari a Kiriyat-yeyarim

20 Mutanen Bet-shemesh suka ce, “Wa ya isa ya tsaya a gaban Ubangiji, Allahn nan mai tsarki? A wurin wa zai tafi don ya rabu da mu?” 21 Sai suka aiki manzanni wurin mutanen Kiriyat-yeyarim, suka ce, “Filistiyawa sun komo da akwatin alkawari na Ubangiji, sai ku zo, ku ɗauka, ku tafi da shi.”

1 Sama’ila 7

1 Mutanen Kiriyat-yeyarim kuwa suka zo suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji suka kai shi gidan Abinadab a bisa tudu. Suka keɓe ɗansa, Ele'azara, ya lura da akwatin alkawarin Ubangiji.

Sama'ila ya Shugabanci Isra'ila

2 Akwatin alkawarin Ubangiji ya daɗe a Kiriyat-yeyarim, ya kai har shekara ashirin. A wannan lokaci kuwa dukan Isra'ilawa suka yi kuka ga Ubangiji don ya taimake su. 3 Sa'an nan Sama'ila ya ce wa mutanen Isra'ila, “Idan da zuciya ɗaya kuke komowa wurin Ubangiji, to, sai ku rabu da bāƙin alloli, da gumakan nan Ashtarot. Ku sa zuciyarku ga bin Ubangiji, ku bauta masa shi kaɗai, shi kuwa zai cece ku daga hannun Filistiyawa.” 4 Isra'ilawa kuwa suka rabu da gumakan Ba'al da Ashtarot, suka bauta wa Ubangiji shi kaɗai. 5 Sama'ila kuma ya ce, “Ku tattara dukan Isra'ilawa a Mizfa, ni kuwa zan yi addu'a ga Ubangiji dominku.” 6 Isra'ilawa fa suka taru a Mizfa, suka kawo ruwa, suka zuba a gaban Ubangiji. Suka yi azumi a ranan nan, suka ce, “Mun yi wa Ubangiji zunubi.” Sama'ila kuwa ya zauna a Mizfa ya yi mulkin Isra'ilawa. 7 Da Filistiyawa suka ji Isra'ilawa sun taru a Mizfa, sai sarakunan Filistiyawa, su biyar, suka tafi, su yi yaƙi da Isra'ilawa. Sa'ad da Isra'ilawa suka ji labari, sai suka tsorata, 8 suka ce wa Sama'ila, “Ka yi ta roƙo ga Ubangiji Allahnmu don ya cece mu daga hannun Filistiyawa.” 9 Sama'ila ya kama ɗan rago ya miƙa shi ɗungum hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Ya kuma yi roƙo ga Ubangiji ya taimaki Isra'ilawa, Ubangiji kuwa ya amsa addu'arsa. 10 A sa'ad da Sama'ila yake miƙa hadaya ta ƙonawa, Filistiyawa suka matso don su yi yaƙi da Isra'ilawa, sai Ubangiji ya buge wa Filistiyawa tsawa mai ƙarfi daga sama, suka kuwa ruɗe suka juya a guje. 11 Isra'ilawa suka fito daga Mizfa suka runtumi Filistiyawa, suka yi ta karkashe su har zuwa kwarin Bet-kar. 12 Sa'an nan Sama'ila ya ɗauki dutse ya kafa shi a tsakanin Mizfa da Shen, ya sa masa suna, Ebenezer, wato “Har wa yau Ubangiji yana taimakonmu.” 13 Ta haka aka ci Filistiyawa. Daganan ba su ƙara shiga yankin ƙasar Isra'ilawa ba, gama Ubangiji ya yi gāba da Filistiyawa a dukan zamanin Sama'ila. 14 Aka mayar wa Isra'ilawa garuruwan da Filistiyawa suka ƙwace musu, tun daga Ekron har zuwa Gat. Isra'ilawa kuma suka ƙwato dukan yankin ƙasarsu daga hannun Filistiyawa. Akwai kuma zaman lafiya tsakanin Isra'ilawa da Ƙan'aniyawa. 15 Sama'ila kuwa ya yi mulkin Isra'ilawa dukan kwanakin ransa. 16 A kowace shekara yakan fita rangadi zuwa Betel, da Gilgal, da Mizfa, inda yakan yi musu shari'a. 17 Sa'an nan kuma ya koma gidansa a Rama inda kuma yakan yi wa Isra'ilawa shari'a. Ya kuma gina wa Ubangiji bagade a can Rama.

1 Sama’ila 8

Isra'ilawa sun Roƙa a Naɗa musu Sarki

1 Da Sama'ila ya tsufa, sai ya naɗa 'ya'yansa maza su zama alƙalan Isra'ila. 2 Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyun kuma Abiya. Su ne alƙalai a cikin Biyer-sheba. 3 Amma 'ya'yansa ba su bi gurbin mahaifinsu ba, amma suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi, suka yi ta cin hanci, suka danne gaskiya. 4 Dukan shugabannin Isra'ila kuwa suka tattaru, suka tafi wurin Sama'ila a Rama, 5 suka ce masa, “Ga shi, ka tsufa, ga kuma 'ya'yanka ba su bi gurbinka ba, yanzu dai sai ka naɗa mana sarki wanda zai yi mulkinmu kamar sauran ƙasashe.” 6 Amma Sama'ila bai ji daɗin roƙonsu ba, na a naɗa musu sarki, saboda haka ya yi addu'a ga Ubangiji. 7 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Sai ka kasa kunne ga dukan abin da suka faɗa maka, gama ba kai suka ƙi ba, amma ni suka ƙi da zama sarkinsu. 8 Irin abubuwan da suke yi maka, irinsu ne suka yi mini tun daga ranar da na fito da su daga Masar har wa yau, sun ƙi ni, suka yi ta bauta wa gumaka. 9 Yanzu dai sai ka saurari maganarsu kurum, amma ka faɗakar da su sosai da sosai, ka kuma nuna musu irin halin sarkin da zai sarauce su.” 10 Sama'ila kuwa ya faɗa wa mutanen da suke roƙo ya naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa. 11 Ya ce musu, “Ga irin halin sarkin da zai sarauce ku, zai sa 'ya'yanku maza su zama sojojinsa, waɗansunsu za su yi aiki da karusan yaƙinsa, waɗansu su zama mahayan dawakansa, da masu kai hari musamman. 12 Waɗansu kuma zai sa su zama shugabannin mutum dubu dubu da na hamsin hamsin. 'Ya'yanku ne za su riƙa yi masa noma da girbi, su ƙera masa kayayyakin yaƙi da na karusansa. 13 Zai sa 'ya'yanku mata yin aikin turare, da dafe-dafe, da toye-toye. 14 Zai ƙwace gonakinku mafi kyau, da gonakinku na inabi, da gonakinku na zaitun, ya ba fādawansa. 15 Zai kuma karɓi ushirin hatsinku da na inabinku ya ba shugabannin fādarsa da sauran fādawansa. 16 Zai ƙwace bayinku mata da maza, da mafi kyau na shanunku da jakunanku, domin su riƙa yi masa aiki. 17 Zai kuma karɓi ushirin dabbobinku. Za ku zama barorinsa. 18 A lokacin za ku yi kuka saboda sarkin da kuka zaɓar wa kanku, amma Ubangiji ba zai kasa kunne ga kukanku ba.” 19 Amma mutane suka ƙi yin abin da Sama'ila ya faɗa musu, sai suka ce, “Duk da haka dai, muna so sarki ya sarauce mu, 20 don mu ma mu zama kamar sauran ƙasashe, mu sami sarki wanda zai sarauce mu, ya shugabance mu zuwa yaƙe-yaƙe.” 21 Sa'ad da Sama'ila ya ji dukan abin da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji. 22 Ubangiji kuwa ya ce wa Sama'ila, “Ka yarda da abin da suka ce, ka naɗa musu sarki.” Sai Sama'ila ya ce wa mutanen Isra'ila, “Kowa ya koma gida.”

1 Sama’ila 9

Aka Zaɓi Saul ya Zama Sarki

1 Akwai wani mutum daga kabilar Biliyaminu, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror, na iyalin Bekorat, dangin Afinya, shi attajiri ne. 2 Yana da wani ɗa, sunansa Saul, kyakkyawan saurayi ne. A cikin jama'ar Isra'ila ba wanda ya fi shi kyau, ya fi kowa tsayi a cikin Isra'ilawa duka. 3 Ana nan sai jakunan Kish, mahaifin Saul suka ɓace, Kish kuwa ya ce wa Saul, ɗansa, “Tashi, kai da ɗaya daga cikin barorin ku tafi, ku nemo jakunan.” 4 Suka bi ta ƙasar tudu ta Ifraimu, suka ratsa ta ƙasar Shalisha, amma ba su same su ba. Suka kuma bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba. Sai suka bi ta ƙasar Biliyaminu, amma ba su same su ba. 5 Da suka kai ƙasar Zuf, sai Saul ya ce wa baransa da yake tare da shi, “Zo mu koma gida, kada babana ya bar damuwa a kan jakunan ya yi ta damuwa a kanmu.” 6 Amma baran ya ce masa, “Ai, akwai wani mutumin Allah a garin nan, ana kuwa ganin girmansa, domin duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa, watakila ya iya faɗa mana inda jakunanmu suke.” 7 Saul ya ce wa baransa, “Idan muka tafi, me za mu ba shi? Gama guzurin da yake tare da mu ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu ba shi.” 8 Baran kuma ya ce wa Saul, “Ina da 'yar azurfa tsaba da zan ba shi domin ya faɗa mana inda za mu same su.” 9 (A dā a Isra'ila, idan wani yana so ya yi tambaya ga Allah, sai ya ce, “Zo, mu tafi wurin maigani.” Gama wanda ake ce da shi annabi yanzu, a dā akan ce da shi maigani.) 10 Sai Saul ya ce wa baransa, “Maganarka daidai ce, zo, mu tafi.” Suka kuwa tafi garin da mutumin Allah yake. 11 Sa'ad da suka haura zuwa garin, suka gamu da waɗansu 'yan mata za su ɗebo ruwa, suka ce musu, “Maigani yana nan?” 12 'Yan matan suka amsa, suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi nan ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu. 13 Da shigarku garin, za ku same shi kafin ya tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu, gama jama'a ba za su ci ba, sai ya je ya sa albarka a sadakar, sa'an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura yanzu, za ku same shi nan da nan.” 14 Suka kuwa haura zuwa cikin garin. Da shigarsu suka ga Sama'ila ya nufo wajen da suke, za shi wurin da ake yin sujadar. 15 Ana gobe Saul zai tafi wurin Sama'ila, Ubangiji ya bayyana wa Sama'ila. 16 Ya ce masa, “Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga kabilar Biliyaminu, sai ka zuba masa mai, ka keɓe shi sarki bisa jama'ata Isra'ila. Zai ceci jama'ata daga hannun Filistiyawa, gama na ga azabar da jama'ata suke sha, gama na ji kukansu.” 17 Da Sama'ila ya ga Saul, sai Ubangiji ya ce masa, “To, ga mutumin da na faɗa maka! Shi ne wanda zai sarauci jama'ata.” 18 Sa'an nan Saul ya tafi wurin Sama'ila a ƙofar gari, ya tambaye shi, “Ina gidan maigani?” 19 Sama'ila ya amsa ya ce, “Ni ne maiganin, wuce gaba, mu tafi wurin yin sujada a kan tudu, gama yau dukanku za ku ci abinci tare da ni. Gobe da safe zan amsa muku dukan tambayoyinku, sa'an nan in sallame ku. 20 A kan zancen jakunanku da suka ɓace yau kwana uku ke nan da suka wuce, kada ka damu, gama an same su. Banda wannan ma, ga wa Isra'ilawa duka suke sa zuciya? Ba kai ba ne da gidan mahaifinka?” 21 Saul ya ce, “Ni mutumin kabilar Biliyaminu ne, kabilar da ta fi ƙanƙanta a Isra'ila. Iyalina kuma su ne mafi ƙanƙanta a iyalan kabilar Biliyaminu. Me ya sa ka faɗa mini irin wannan magana?” 22 Sa'an nan Sama'ila ya shigar da Saul da baransa a babban ɗakin taruwa, ya sa su zauna gaba inda baƙi suke, wajen mutum talatin aka gayyata. 23 Sama'ila kuwa ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman nan da na ba ka, wanda na ce ka ajiye shi dabam.” 24 Sai mai dahuwa ya kawo cinya da gadon baya ya ajiye a gaban Saul. Sa'an nan Sama'ila ya ce, “Sai ka ci naman da aka ajiye a gabanka, gama dominka aka ajiye shi don ka ci a wannan lokaci tare da waɗanda na gayyata.” A wannan rana kuwa Saul ya ci tare da Sama'ila. 25 Sa'ad da suka gangaro daga wurin yin sujadar zuwa cikin gari, sai aka shirya wa Saul gado a kan bene. 26 Ya kwanta, ya yi barci. Sama'ila ya Keɓe Saul ya Zama Sarki Da asuba, Sama'ila ya kira Saul ya ce, “Tashi, in sallame ka.” Saul kuwa ya tashi, shi da Sama'ila suka fita waje zuwa kan titi. 27 Sa'ad da suka kai bayan gari, sai Sama'ila ya ce wa Saul, “Ka sa baranka ya yi gaba, kai ka tsaya nan tukuna domin in faɗa maka abin da Allah ya ce.”

1 Sama’ila 10

1 Sa'an nan Sama'ila ya ɗauki 'yar kwalabar mai, ya zuba wa Saul a kā, ya yi masa sumba, ya ce, “Ubangjiji ne ya keɓe ka, ya naɗa ka sarki a kan jama'arsa. 2 Yau, sa'ad da ka rabu da ni, za ka gamu da mutum biyu kusa da kabarin Rahila a karkarar Biliyaminu a Zelza. Za su ce maka, jakunan da ka tafi nema an same su, yanzu mahaifinka ya daina damuwa saboda jakunan, sai a kanku, yana cewa, ‘Ina zan gane ɗana?’ 3 Sa'ad da ka wuce nan, ka ci gaba zuwa itacen oak a Tabor, a nan mutum uku da suke haurawa zuwa ɗakin Allah a Betel za su gamu da kai. Ɗaya yana ɗauke da 'yan awaki uku, ɗaya kuma yana ɗauke da malmalar abinci guda uku, ɗayan kuwa yana ɗauke da salkar ruwan inabi. 4 Za su gaishe ka, su ba ka malmala biyu, kai kuwa sai ka karɓa. 5 Sa'ad da ka isa Gibeya, wato tudun Allah, inda sansanin sojojin Filistiyawa yake, a nan kuma sa'ad da kake shiga garin, za ka tarar da ƙungiyar annabawa suna gangarowa daga wurin bagaden a kan tudu suna kaɗa garaya, da kuwaru, da sarewa, da molo, suna rawa suna sowa. 6 Sa'an nan Ruhun Ubangiji zai sauko maka, za ka kuwa yi rawa da sowa tare da su, za ka zama wani mutum dabam. 7 Sa'ad da waɗannan alamu suka cika, sai ka yi abin da hali ya nuna maka, gama Ubangiji yana tare da kai. 8 Za ka riga ni zuwa Gilgal inda zan zo in miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama. Sai ka jira ni kwana bakwai, har in zo in sanar da kai abin da za ka yi.” 9 Da Saul ya juya zai tashi daga wurin Sama'ila, sai Ubangiji ya ba shi sabuwar zuciya. Alamun nan kuma suka cika a ranar. 10 Sa'ad da suka iso Gileyad, sai suka tarar da ƙungiyar annabawa. Ruhun Ubangiji kuwa ya sauko a kansa da iko, sai ya shiga rawa da sowa tare da su. 11 Sa'ad da dukan waɗanda suka san shi, suka gan shi yana yin wannan tare da annabawa, suka ce wa junansu, “Me ya faru da ɗan Kish? Saul kuma yana cikin annabawa ne?” 12 Sai wani mutumin da yake wurin ya ce, “Sauran fa, su ma, iyayensu annabawa ne?” Wannan kuwa ya zama karin magana, “Har Saul kuma yana cikin annabawa?” 13 Da ya gama rawa da sowa sai ya tafi wurin bagaden a kan tudu. 14 Kawun Saul kuwa ya tambaye shi, shi da baransa, “Ina ne kuka tafi?” Saul ya ce, “Mun je neman jakuna, da ba mu same su ba, sai muka tafi wurin Sama'ila.” 15 Kawunsa kuma ya ce, “In ka yarda ka faɗa mini abin da Sama'ila ya faɗa maka.” 16 Saul kuwa ya ce wa kawunsa, “Ya faɗa mana a fili an gane jakunan.” Amma bai faɗa wa kawunsa zancen sarautar da Sama'ila ya faɗa masa ba.

An yi Na'am da Zaman Saul Sarki

17 Sama'ila kuwa ya tara mutanen Isra'ila a gaban Ubangiji a Mizfa. 18 Ya ce musu, “In ji Ubangiji Allah na Isra'ila, ‘Ni na fito da Isra'ilawa daga Masar, na cece ku daga Masarawa da kuma daga hannun mulkokin da suka wahalshe ku. 19 Ni ne Allahnku wanda yake cetonku daga dukan masifu da wahalai, amma ga shi yau, kun ƙi ni kuna roƙona in ba ku sarki. To, da kyau, yanzu fa sai ku kusato gaban Ubangiji kabila kabila da iyali iyali.’ ” 20 Sa'an nan Sama'ila ya ce wa kabilan Isra'ila su guso, kuri'a kuwa ta faɗa a kan kabilar Biliyaminu. 21 Sai kuma ya sa kabilar Biliyaminu ta guso iyali iyali, kuri'a kuwa ta faɗa a kan iyalin Matri. Sa'an nan kuma ya guso da iyalin Matri mutum mutum, kuri'a ta faɗa a kan Saul, ɗan Kish. Amma sa'ad da suka neme shi, ba a same shi ba. 22 Suka yi tambaya a wurin Ubangiji, suka ce, “Ko akwai wani dabam?” Ubangiji ya ce, “Ai, ga shi can, ya ɓuya cikin kayayyaki.” 23 Sai suka sheƙa, suka fito da shi daga wurin da ya ɓuya, ya tsaya cikin mutane, ya fi kowa tsayi da misalin ƙafa guda. 24 Sama'ila ya ce wa dukan jama'a, “Kun gan shi? Shi ne wanda Ubangiji ya zaɓa, babu wani kamarsa a cikin dukan jama'a.” Jama'a duka kuwa suka yi sowa suka ce, “Ran sarki ya daɗe!” 25 Sa'an nan Sama'ila ya faɗa wa jama'a ka'idodin sarautar. Ya rubuta su cikin littafi, ya ajiye a wuri mai tsarki. Sa'an nan ya sallami jama'a duka kowa ya koma gidansa. 26 Saul kuma ya koma gidansa a Gibeya tare da waɗansu jarumawa da Allah ya taɓa zuciyarsu. 27 Amma waɗansu shashashan mutane suka ce, “Ƙaƙa wannan yaro zai iya cetonmu?” Suka raina shi, ba su kawo masa gaisuwa ba. Amma bai ce kome ba.

1 Sama’ila 11

Saul ya Ci Ammonawa

1 Sai Nahash Ba'ammone ya kewaye Yabesh da yaƙi. Dukan mutanen Yabesh kuwa suka ce masa, “Ka ƙulla amana da mu, mu kuwa za mu bauta maka.” 2 Nahash Ba'ammone kuwa ya ce, “Zan ƙulla amana da ku a kan wannan sharaɗi, wato in ƙwaƙule idanunku na dama don ku zama abin raini ga Isra'ilawa.” 3 Dattawan Yabesh kuwa suka ce masa, “Ka ba mu zarafi kwana bakwai domin mu aika da manzanni a dukan ƙasar Isra'ila, idan ba mu sami wanda zai cece mu ba, to, sai mu ba da kanmu gare ku.” 4 Da manzannin suka zo Gibeya inda Saul yake, suka ba mutane labarin abin da ya faru. Sai jama'a duka suka yi kuka. 5 Saul kuwa yana dawowa daga gona ke nan, tare da shanunsa na huɗa. Sai ya ce, “Me ya sami jama'a suke kuka haka?” Suka faɗa masa labarin mutanen Yabesh. 6 Da Saul ya ji, sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kansa da iko, ya husata ƙwarai. 7 Ya kwance shanun, ya yanka gunduwa gunduwa, ya aika da su ko'ina a ƙasar Isra'ila ta hannun manzanni, yana cewa, “Duk wanda bai fito ya bi Saul da Sama'ila ba, to, haka za a yi da shanun nomansa!” Jama'a suka ji tsoron abin da Ubangiji zai yi, suka fita gaba ɗaya kamar mutum guda. 8 Sa'ad da Saul ya tara mutane a Bezek, aka sami mutum dubu ɗari uku (300,000 ) daga Isra'ila, dubu talatin (30,000 ) kuma daga Yahuza. 9 Suka faɗa wa manzannin da suka zo. “Ga abin da za ku faɗa wa mutanen Yabesh, ‘Gobe, kafin rana ta yi zafi, za ku sami ceto.’ ” Sa'ad da manzannin suka je, suka faɗa wa mutanen Yabesh saƙon, suka yi murna. 10 Saboda haka mutanen Yabesh suka ce wa Nahash Ba'ammone, “Gobe za mu zo wurinku, ka yi mana yadda ka ga dama.” 11 Gari yana wayewa, sai Saul ya raba mutanen kashi uku, suka fāɗa wa sansanin Ammonawa da kisa tun da sassafe har rana tsaka, aka warwatsa waɗanda suka tsira ɗaya ɗaya. 12 Jama'ar Isra'ila kuwa suka ce wa Sama'ila, “Su wa suka ce Saul ba zai sarauce mu ba? Ka kawo su, mu kashe su.” 13 Amma Saul ya ce, “Ba wanda za a kashe a yau, gama Ubangiji ya yi wa Isra'ila ceto a yau.” 14 Sai Sama'ila ya ce wa jama'a, “Ku zo, mu tafi Gilgal a yi wankan sarautar a can.” 15 Jama'a duka kuwa suka nufi Gilgal, suka yi wa Saul wankan sarauta a gaban Ubangiji. Suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya ta salama. A can kuwa Saul tare da dukan mutanen Isra'ila suka yi murna ƙwarai.

1 Sama’ila 12

Sama'ila ya yi Jawabin Bankwana

1 Sama'ila ya ce wa jama'ar Isra'ila, “Ga shi, na kasa kunne gare ku, na kuwa yi muku abin da kuka ce mini, na naɗa muku sarki. 2 Yanzu ga sarki a gabanku, 'ya'yana maza kuma suna tare da ku. Ni na tsufa, na yi furfura, amma na yi ta kai da kawowa a cikinku tun ina yaro har zuwa yau. 3 To, ga ni nan, ku shaida a kaina a gaban Ubangiji da gaban wanda Ubangiji ya naɗa sarki. Takarkari ko jakin wa na ƙwace? Wa kuma na zalunta, ko na wulakanta? A wurin wa na karɓi hanci don in danne gaskiya? Sai ku shaida, ni kuwa zan mayar masa.” 4 Jama'a suka amsa, suka ce, “Ba ka zalunci kowa ba, ba ka wulakanta kowa ba, ba ka kuma yi wa kowa ƙwace ba.” 5 Sa'an nan ya ce musu, “Ubangiji shi ne shaida, wanda kuma ya naɗa, shi ma shaida ne a yau, cewa ba ku iske ni da laifin kome ba.” Jama'ar suka ce, “Ubangiji ne shaida.” 6 Sama'ila kuma ya ce wa jama'a, “Ubangiji ne ya sa Musa da Haruna su fito da kakanninku daga ƙasar Masar. 7 Yanzu fa ku tsaya shiru don in yi muku magana a kan ayyuka masu adalci na Ubangiji waɗanda ya aikata dominku da kakanninku. 8 Sa'ad da Yakubu da 'ya'yansa suka tafi Masar, Masarawa suka wulakanta su, sai suka kai kuka ga Ubangiji. Ubangiji kuwa ya aiki Musa da Haruna waɗanda suka fito da kakanninku daga ƙasar Masar, suka kawo su su zauna a wannan wuri. 9 Amma suka bar bin Ubangiji Allahnsu. Ubangiji kuwa ya bashe su a hannun Sisera, shugaban rundunar Yabin, Sarkin Hazor, da a hannun Filistiyawa, da kuma a hannun Sarkin Mowab, suka yāƙe su. 10 Sai suka yi wa Ubangiji kuka, suka ce, ‘Mun yi laifi domin mun bar bin Ubangiji, muka bauta wa gumakan nan Ba'al da Ashtarot, amma yanzu muna roƙonka ka cece mu daga hannun abokan gābanmu, mu kuwa za mu bauta maka.’ 11 Ubangiji kuwa ya aika musu da Yerubba'al, wato Gidiyon, da Barak, da Yefta, da Samson, suka cece ku daga hannun abokan gābanku ta kowace fuska. Sa'an nan kuka yi zamanku lafiya. 12 Amma da kuka ga Nahash Sarkin Ammonawa ya zo don ya yi yaƙi da ku, sai kuka ce mini, ‘Mu dai a yi mana sarki da zai sarauce mu,’ alhali kuwa Ubangiji Allahnku ne Sarkinku. 13 To, ga sarkin da kuka zaɓa nan, kuka roƙa. Ga shi, Ubangiji ya naɗa muku shi. 14 Idan za ku yi tsoron Ubangiji, ku bauta masa, ku yi biyayya da maganarsa, ba za ku karya umarnin Ubangiji ba, idan kuma ku da sarkin da yake sarautarku za ku bi Ubangiji Allahnku, kome zai zamar muku daidai. 15 Amma idan kun ƙi yin biyayya da maganar Ubangiji, kuka kuma karya umarnin Ubangiji, to, Ubangiji zai yi gāba da ku da sarkinku. 16 Yanzu fa ku tsaya shiru ku ga babban al'amarin da Ubangiji zai yi a idanunku. 17 Yanzu dai rani ne, ko ba haka ba? Zan roƙi Ubangiji ya aiko da tsawa da ruwan sama, da haka za ku sani, ku kuma ga babbar muguntar da kuka yi wa Ubangiji da kuka roƙa a yi muku sarki.” 18 Sai Sama'ila ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa aka yi tsawa da ruwan sama a wannan rana. Dukan jama'a kuwa suka ji tsoron Ubangiji da Sama'ila ƙwarai. 19 Suka ce wa Sama'ila, “Ka yi wa bayinka roƙo ga Ubangiji Allahnka don kada mu mutu, gama mun ƙara wa kanmu zunubi da muka roƙa a yi mana sarki.” 20 Sama'ila kuwa ya ce musu, “Kada ku razana, gama kun riga kun aikata wannan mugunta, duk da haka kada ku bar bin Ubangiji, amma ku bauta masa da zuciya ɗaya. 21 Kada kuma ku ratse ku bi abubuwa marasa amfani da ba za su amfane ku, ko su cece ku ba, gama ba su da wani amfani. 22 Gama Ubangiji ya yi ƙaƙƙarfan alkawari, ba zai yashe ku ba, gama ya ɗauri aniya ya maishe ku jama'arsa. 23 Amma ni kaina, Allah ya sawwaƙa in yi wa Ubangiji zunubi ta wurin fasa yin addu'a ga Ubangiji dominku. Zan riƙa koya muku kyawawan abubuwa da suke daidai. 24 Ku dai ku yi tsoron Ubangiji, ku bauta masa da aminci, da zuciya ɗaya. Ku tuna da manyan al'amuran da ya yi muku. 25 Amma idan kuka ci gaba da aikata mugunta, za a shafe ku, ku da sarkinku.”

1 Sama’ila 13

Yaƙi da Filistiyawa

1 Saul yana da shekara talatin sa'ad da ya ci sarauta, ya yi shekara arba'in da biyu yana sarautar Isra'ila. 2 Saul ya zaɓi mutum dubu uku (3,000 ) daga Isra'ila, dubu biyu (2,000 ) su zauna tare da shi a Mikmash da ƙasar tuddai ta Betel, dubu ɗaya (1,000 ) kuma su zauna tare da Jonatan a Gibeya ta Biliyaminu, sauran jama'a kuwa ya sallame su, su koma gida, kowa zuwa alfarwarsa. 3 Jonatan kuwa ya kashe wani shugaban yaƙi na Filistiyawa a Geba, Filistiyawa kuwa suka ji labarin abin da ya faru. Sai Saul ya sa aka busa ƙaho ko'ina a ƙasar, na kiran Ibraniyawa su zo yaƙi. 4 Isra'ilawa duka kuwa suka ji cewa Saul ya kashe shugaban yaƙi na Filistiyawa, da kuma, Isra'ilawa sun zama abin ƙi ga Filistiyawa, sai jama'a suka amsa kiran, suka tafi wurin Saul a Gilgal. 5 Sai Filistiyawa suka taru don su yi yaƙi da Isra'ilawa. Suka fito da karusa dubu talatin (30,000 ), da mahayan dawakai dubu shida (6,000 ), da sojoji da yawa kamar yashi a bakin teku, suka kafa sansani a Mikmash, a wajen gabashin Bet-awen. 6 Sa'ad da Isra'ilawa suka ga sun ƙuntata, gama an matsa su ƙwarai, sai suka ɓuya cikin kogwanni, da cikin ruƙaƙe, da duwatsu, da ramummuka, da kwazazzabai. 7 Waɗansu kuwa suka haye Kogin Urdun zuwa ƙasar Gad da Gileyad. Saul kuwa yana can a Gilgal. Dukan mutanen da suka bi shi suka yi ta rawar jiki. 8 Ya dakata kwana bakwai bisa ga adadin lokacin da Sama'ila ya ɗibar masa, amma Sama'ila bai iso Gilgal ba. Mutane suka yi ta watsewa suna barin Saul. 9 Sai Saul ya ce, “Ku kawo mini hadaya ta ƙonawa da hadayun salama.” Ya kuwa miƙa hadaya ta ƙonawa. 10 Yana gama miƙa hadayar ke nan, sai ga Sama'ila ya iso. Saul kuwa ya fita don ya tarye shi, ya gaishe shi. 11 Sai Sama'ila ya ce, “Me ke nan ka yi?” Saul ya amsa ya ce, “Don na ga mutane suna watsewa, suna barina, kai kuma ba ka zo daidai lokacin ba, ga kuma Filistiyawa sun tattaru a Mikmash. 12 Sai na yi tunani cewa, ‘Yanzu Filistiyawa za su gangaro su fāɗa mini a Gilgal, ni kuwa ban riga na roƙi Ubangiji ba,’ don haka ya zama mini tilas in miƙa hadaya ta ƙonawa!” 13 Sama'ila kuwa ya ce wa Saul, “Ka yi wauta, ba ka kiyaye umarnin da Ubangiji Allahnka ya umarce ka da shi ba. Dā Ubangiji ya tabbatar maka da sarautar Isra'ila har abada. 14 Amma yanzu sarautarka ba za ta tabbata ba, gama Ubangiji ya riga ya sami mutum wanda yake so. Ubangiji ya riga ya naɗa shi ya zama sarkin jama'arsa, domin ba ka kiyaye umarnin Ubangiji ba.” 15 Sama'ila ya tashi daga Gilgal zuwa Gibeya ta Biliyaminu. Da Saul ya ƙidaya mutanen da suke tare da shi, ya tarar wajen mutum ɗari shida ne. 16 Sai Saul da ɗansa, Jonatan, da mutanen da suke tare da su suka zauna a Geba ta Biliyaminu. Filistiyawa kuwa suka kafa sansaninsu a Mikmash. 17 Sai runduna uku na mahara suka fito daga sansanin Filistiyawa. Runduna ɗaya ta nufi Ofra, zuwa ƙasar Shuwal. 18 Runduna guda kuma ta nufi Bet-horon, guda kuwa ta nufi iyakar da take fuskantar kwarin Zeboyim wajen jeji. 19 A wannan lokaci ba maƙeri a ƙasar Isra'ila duka, domin Filistiyawa sun hana Ibraniyawa su ƙera wa kansu takuba ko māsu. 20 Saboda haka kowane Ba'isra'ile yakan gangara zuwa Filistiyawa don ya koɗa bakin garmarsa, da fartanyasa, da gatarinsa, da laujensa, 21 duk lokacin da za su koɗar bakin garma da fartanya sai su biya sulusin shekel ne, ladan koɗar gatari da shirya abin korar shanun noma sulusin shekel ne. 22 A ranar da yaƙi ya tashi, ba a sami wanda yake da takobi ko māshi ba a cikin mutanen da suke tare da Saul da Jonatan. Amma Saul da ɗansa, Jonatan, suna da su. 23 Sai ƙungiyar sojojin Filistiyawa ta fita zuwa mashigin Mikmash.

1 Sama’ila 14

Karfin Zuciyar Jonatan

1 Wata rana Jonatan, ɗan Saul, ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo, mu haye mu je sansanin Filistiyawa a wancan hayi.” Amma bai faɗa wa mahaifinsa ba. 2 Saul kuwa yana zaune a karkarar Gibeya a gindin itacen rumman a Migron. Mutum wajen ɗari shida suna tare da shi. 3 Ahiya ɗan Ahitub kuma, ɗan'uwan Ikabod, wato jikan Eli, firist na Ubangiji, yana Shilo, yana sāye da falmaran. Mutane kuma ba su sani ba, ashe Jonatan ya tafi wani wuri. 4 A tsakanin mashigin dutse inda Jonatan yake so ya bi zuwa sansanin Filistiyawa, akwai dutse mai tsayi a kowane gefe. Sunan ɗaya Bozer, ɗayan kuma Sene. 5 Ɗaya dutsen yana wajen arewa a gaban Mikmash, ɗayan kuma yana daga kudu a gaban Geba. 6 Jonatan ya ce wa saurayin da yake ɗaukar masa makamai, “Zo, mu haye zuwa sansanin marasa kaciyan nan, arnan nan, watakila Ubangiji zai yi aiki ta wurinmu, gama ba abin da zai hana Ubangiji ya yiwo ceto ta wurin masu yawa, ko kuwa ta wurin 'yan kaɗan.” 7 Sai mai ɗaukar masa makamai ya ce, “Ka yi abin da yake a zuciyarka, ga shi, ina tare da kai, gama ina goyon bayanka, kamar yadda zuciyarka take haka kuma tawa.” 8 Sa'an nan Jonatan ya ce, “Za mu haye zuwa wurin mutanen, mu nuna kanmu gare su. 9 Idan sun ce mana, ‘Ku dakata har mu zo wurinku,’ to, sai mu tsaya cik, ba za mu tafi wurinsu ba. 10 Amma idan sun ce, ‘Ku haura zuwa wurinmu,’ to, sai mu haura, gama wannan alama ce, wato Ubangiji ya bashe su a hannunmu.” 11 Sai su biyu suka tafi suka nuna kansu ga sansanin Filistiyawa. Da Filistiyawa suka gan su, sai suka ce, “Ku duba, Ibraniyawa suna fitowa daga cikin ramummuka inda suka ɓuya.” 12 Sai suka kira Jonatan da mai ɗaukar makamansa, suka ce, “Ku hauro zuwa wurinmu, mu faɗa muku wani abu.” Jonatan kuwa ya ce wa mai ɗaukar makamansa, “Ka biyo ni, gama Ubangiji ya bashe su a hannun Isra'ilawa.” 13 Sa'an nan Jonatan ya hau dutsen da rarrafe, mai ɗaukar makamansa kuwa yana biye da shi. Jonatan ya fāɗa wa Filistiyawa, ya yi ta kā da su, mai ɗaukar makamansa kuma ya bi bayansa yana ta karkashe su. 14 A wannan karo na farko Jonatan da mai ɗaukar makamansa suka kashe mutum wajen ashirin a wani fili mai fāɗi kamar rabin kadada. 15 Dukan Filistiyawa da suke a filin suka ji tsoro, da mahara da sauran sojoji suka yi rawar jiki, ƙasa ta girgiza, aka yi babbar gigicewa. 16 Da matsara na Saul a Gibeya ta Biliyaminu suka duba, sai ga taron Filistiyawa ya watse, kowa ya nufi wajensa, suna tafiya barkatai. 17 Saul ya ce wa mutanen da suke tare da shi, “Ƙidaya mutane yanzu don ku ga wanda ya fita daga cikinmu.” Da aka ƙirga mutanen sai aka tarar Jonatan da mai ɗaukar makamansa ba su nan. 18 Sai Saul ya ce wa Ahiya, “Kawo akwatin alkawarin Allah a nan.” Gama a wannan lokaci akwatin Allah yana hannun Isra'ilawa. 19 Sa'ad da Saul yake magana da firist ɗin, sai hargowa a sansanin Filistiyawa ta yi ta ƙaruwa, Saul kuwa ya ce wa firist, “Janye hannunka.” 20 Sa'an nan Saul da mutanen da suke tare da shi suka taru, suka tafi su yi yaƙi. Sai suka tarar Filistiyawa sun ruɗe suna ta yaƙi da junansu. Aka yi babbar yamutsewa. 21 Ibraniyawan da suke tare da Filistiyawa a dā, waɗanda suka bi su zuwa sansani, suka koma wajen Isra'ilawan da suke tare da Saul da Jonatan. 22 Waɗanda kuma suka bi ta ƙasar tudu ta Ifraimu, da suka ji labari Filistiyawa suna gudu, suka fito suka fafare su. 23 Haka Ubangiji ya ceci Isra'ilawa a ranan nan. Yaƙin kuwa ya kai har gaba da Bet-awen.

Abin da ya Faru bayan Yaƙin

24 A ran nan kuwa Isra'ilawa sun sha wahala, gama Saul ya yi rantsuwa mai ƙarfi ya ce, “La'ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin faɗuwar rana tun ban ɗauko fansa a kan abokan gābana ba.” Don haka ba mutumin da ya ɗanɗana abinci. dukan mutane suka shiga kurmi, sai ga zuma ko'ina, amma ba wanda ya lakata da yatsa ya sa a baka, domin mutane suna tsoron la'anar Saul. 27 Amma Jonatan bai ji barazanar da mahaifinsa ya yi wa jama'a ba, sai ya lakaci saƙar zuma da kan sandansa ya sa a hannu ya kai baka, sa'an nan idanunsa suka buɗe. 28 Sai wani daga cikin jama'a ya ce, “Ai, mahaifinka ya yi wa mutane barazana da rantsuwa cewa, ‘La'ananne ne mutumin da ya ci abinci kafin faɗuwar rana.’ ” Mutane kuwa suka tafke. 29 Jonatan kuwa ya ce, “Lalle mahaifina ya wahalar da jama'a! Dubi yadda na wartsake sa'ad da na ɗanɗana 'yar zuman nan. 30 Da yaya zai zama yau da a ce mutane sun ci abinci sosai daga ganimar abokan gābansu, wadda suka samo! Ai, da kisan da aka yi wa Filistiyawa ya fi haka.” 31 Filistiyawa sun sha ɗibga a wannan rana, tun daga Mikmash har zuwa Ayalon. Isra'ilawa suka tafke da yunwa. 32 Sai suka yi warwason ganima, suka kwashe tumaki, da shanu, da maruƙa, suka yanyanka su, suka ci naman ɗanye. 33 Sai aka faɗa wa Saul, “Ga shi, mutane suna yi wa Ubangiji laifi, suna cin nama ɗanye.” Saul kuwa ya ce, “Kun ci amana. Ku mirgino babban dutse a nan wurina.” 34 Sa'an nan ya ce, “Ku tafi ku faɗa wa jama'a duka, su kawo takarkarai da tumaki a nan, su yanyanka su, su ci a nan, don kada su yi wa Ubangiji zunubi da cin nama ɗanye.” Sai dukansu suka kawo takarkaransu a wannan dare, suka yanyanka a wurin. 35 Saul kuwa ya gina wa Ubangiji bagade. Shi ne bagade na farko da ya gina wa Ubangiji. 36 Sa'an nan Saul ya ce, “Mu tafi, mu fallasa Filistiyawa da dare har wayewar gari, kada ko mutum ɗaya daga cikinsu ya tsira.” Sai suka ce masa, “Ka yi abin da ka ga ya yi maka kyau.” Amma firist ɗin ya ce, “Bari mu yi tambaya ga Allah.” 37 Saul kuwa ya yi tambaya ga Ubangiji, ya ce, “In runtumi Filistiyawa? Za ka bashe su ga Isra'ilawa?” Amma Ubangiji bai amsa masa a wannan rana ba. 38 Sai Saul ya ce wa shugabanni, “Ku zo nan dukanku don mu bincike, mu san zunubin da aka yi a yau. 39 Hakika, duk wanda ya yi laifin za a kashe shi, ko da Jonatan ne, ɗana.” Amma ba wanda ya ce kome. 40 Ya kuma ce, “Dukanku ku tsaya waje ɗaya, ni kuma da Jonatan, ɗana, mu tsaya waje ɗaya.” Sai jama'ar suka ce wa Saul, “Ka yi abin da ya yi maka kyau.” 41 Sa'an nan Saul ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, me ya sa ba ka amsa mini ba a wannan rana? Idan wannan laifina ne, ko kuwa na ɗana, Jonatan, ya Ubangiji Allah na Isra'ila, ka nuna mana.” Sai amsa ta nuna Jonatan da Saul ne, jama'a kuwa suka kuɓuta. 42 Sa'an nan Saul ya ce, “A jefa kuri'a tsakanina da ɗana Jonatan.” Kuri'a kuwa ta fāɗa a kan Jonatan. 43 Sa'an nan Saul ya ce wa Jonatan, “Ka faɗa mini abin da ka yi!” Jonatan ya ce masa, “Na ɗanɗana 'yar zuma ne da na lakata da kan sandan da yake hannuna, ga ni, a shirye nake in mutu.” 44 Sai Saul ya ce, “Allah ya yi mini abin da ya fi haka, idan ba a kashe ka ba, Jonatan.” 45 Amma jama'a suka ce wa Saul, “Jonatan da ya yiwo babbar nasara domin Isra'ila, a ce za a kashe shi? Kai, a'a! Mun yi alkawari ga Ubangiji mai rai, Jonatan ba zai yi hasarar ko gashi guda daga kansa ba. Abin da ya yi a yau, da taimakon Allah ne ya yi.” Da haka mutane suka ceci Jonatan, har ba a kashe shi ba. 46 Sa'an nan Saul ya komo daga runtumar Filistiyawa, suka koma yankin ƙasarsu.

Mulkin Saul da Iyalinsa

47 Sa'ad da Saul ya ci sarautar Isra'ila, ya yi yaƙi da dukan abokan gābansa da suke kewaye da shi. Ya yi yaƙi da Mowabawa da Ammonawa, da Edomawa, da sarakunan Zoba, da Filistiyawa. Duk inda ya yi yaƙi ya sami nasara. 48 Ya yi aikin jaruntaka, ya bugi Amalekawa, ya ceci Isra'ilawa daga hannun dukan waɗanda suka taso musu. 49 'Ya'yan Saul, maza ke nan, Jonatan, da Yishwi, da Malkishuwa. Yana kuma da 'ya'ya mata biyu, Merab, 'yar fari, da Mikal. 50 Sunan matarsa kuwa Ahinowam 'yar Ahimawaz. Sunan shugaban rundunansa kuwa Abner ne, ɗan Ner, kawunsa. 51 Kish mahaifin Saul, da Ner mahaifin Abner, 'ya'yan Abiyel ne. 52 Saul ya yi ta yaƙi mai zafi da Filistiyawa dukan zamanin da yake sarauta. Idan Saul ya ga ƙaƙƙarfan mutum, ko jarumi, sai ya sa shi cikin sojansa.

1 Sama’ila 15

Yaƙi da Amalekawa

1 Sama'ila ya ce wa Saul, “Ubangiji ya aike ni in zuba maka man keɓewa don ka zama sarkin mutanensa, Isra'ila. Yanzu sai ka yi biyayya da maganar Ubangiji. 2 Zai hukunta Amalekawa saboda sun yi gāba da Isra'ilawa lokacin da suke tahowa daga Masar. 3 Ka tafi yanzu, ka fāɗa wa Amalekawa da yaƙi. Ka hallakar da dukan abin da suke da shi. Kada ka rage kome, ka karkashe su dukka, da mata da maza, da yara da jarirai, da takarkarai, da tumaki, da raƙuma, da jakai.” 4 Saul kuwa ya kira mutanen da ya ƙidaya a Telem, sojoji dubu ɗari biyu (200,000 ) daga Isra'ila, da dubu goma (10,000 ) daga Yahuza. 5 Sa'an nan Saul ya zo birnin Amalekawa ya yi kwanto a cikin kwari. 6 Ya ce wa Keniyawa, “Ku tafi, ku rabu da Amalekawa, don kada in hallaka ku tare da su, gama kun yi wa dukan Isra'ilawa karamci lokacin da suka fito daga Masar.” Keniyawa kuwa suka fita daga cikin Amalekawa. 7 Saul ya ci Amalekawa, tun daga Hawila har zuwa Shur, da yake gabashin Masar, 8 ya kama Agag Sarkin Amalekawa da rai, ya hallaka mutane ƙaƙaf da takobi. 9 Amma Saul da jama'arsa suka bar Agag da rai, ba su kuma kashe tumaki da takarkarai mafi kyau ba, da 'yan maruƙa, da raguna, da dukan abin da yake mai kyau, bai yarda su hallaka su duka ba, amma sun hallaka dukan abin da yake rainanne ko marar amfani.

An Ƙi Saul da Zaman Sarauta

10-11 Sai Ubangiji ya yi magana da Sama'ila ya ce, “Na yi baƙin ciki da na sa Saul ya zama sarki, gama ya rabu da ni, ya yi rashin biyayya ga umarnaina,” Sama'ila kuwa ya yi fushi, ya yi ta roƙo ga Ubangiji dukan dare. 12 Sa'an nan ya tashi tun da sassafe domin ya sadu da Saul. Aka faɗa wa Sama'ila, Saul ya tafi Karmel, ya kafa wa kansa al'amudi, sa'an nan ya juya ya wuce zuwa Gilgal. 13 Sai Sama'ila ya tafi wurin Saul, Saul kuwa ya gaishe shi, ya ce, “Ubangiji ya sa maka albarka, Sama'ila, na yi biyayya ga umarninsa.” 14 Sama'ila ya ce masa, “To, ina baicin wannan kukan shanu da na tumaki da nake ji?” 15 Saul kuwa ya ce, “Ai, mutanena ne suka kawo su daga Amalekawa. Gama sun bar mafi kyau na tumaki, da na shanu domin su miƙa su sadaka ga Ubangiji Allahnka. Mun hallaka sauran ƙaƙaf.” 16 Sa'an nan Sama'ila ya ce wa Saul, “Dakata, in faɗa maka abin da Ubangiji ya faɗa mini a daren jiya.” Sai Saul ya ce, “Faɗa mini.” 17 Sama'ila ya ce, “Ko da yake kana ganin kanka kai ba wani abu ne ba, ashe, ba kai ne yanzu shugaban kabilan Isra'ila ba? Ubangiji ya sa ka zama Sarkin Isra'ila, 18 ya kuma umarce ka ka tafi ka hallakar da waɗannan mugayen mutane, wato Amalekawa. Ya faɗa maka ka yi yaƙi, har ka hallaka su ƙaƙaf, kada ka rage ko guda ɗaya. 19 Me ya sa ba ka yi biyayya da shi ba? Don me ka fāɗa wason ganima, ka yi abin da Ubangiji ba ya so?” 20 Sai Saul ya amsa wa Sama'ila, ya ce, “Na yi wa Ubangiji biyayya, gama na tafi kamar yadda ya faɗa mini, na kamo sarki Agag, na kuma hallaka Amalekawa ƙaƙaf. 21 Amma mutanena ba su kashe tumaki da shanu mafi kyau ba, amma suka kawo su domin sadaka ga Ubangiji Allahnka a Gilgal.” 22 Sai Sama'ila ya ce, “Me Ubangiji ya fi so? Biyayya, ko kuwa sadakoki da hadayu? Ya fi kyau a yi masa biyayya, da a miƙa masa hadayar tumaki mafi kyau. 23 Gama tayarwa kamar zunubin bokanci take. Taurinkai kuma kamar bautar gumaka yake. Kamar yadda ka ƙi umarnin Ubangiji, hakanan shi ma ya ƙi ka da zama sarki.” 24 Sa'an nan Saul ya ce wa Sama'ila, “Na yi zunubi, na yi rashin biyayya ga umarnin Ubangiji da kuma koyarwarsa. Na ji tsoron mutanena, na kuwa biye wa abin da suke so. 25 Yanzu fa, ina roƙonka ka gafarta mini zunubina, ka koma tare da ni domin in yi wa Ubangiji sujada.” 26 Sama'ila ya ce wa Saul, “Ba zan tafi tare da kai ba, gama ka ƙi umarnin Ubangiji, Ubangiji kuwa ya ƙi ka da zama Sarkin Isra'ila.” 27 Sa'an nan Sama'ila ya juya zai tafi, amma Saul ya kama alkyabbar Sama'ila, sai ta yage. 28 Sai Sama'ila ya ce masa, “Yau Ubangiji ya yage sarautar Isra'ila daga gare ka. Ya ba da ita ga maƙwabcinka wanda ya fi ka. 29 Gama Maɗaukaki na Isra'ila ba zai yi ƙarya, ko ya sāke nufinsa ba. Shi ba mutum ba ne, da zai sāke nufinsa.” 30 Sai Saul ya ce, “Na yi zunubi, amma duk da haka ka darajanta ni a gaban shugabannin mutanena, da gaban Isra'ilawa, ka zo, mu tafi tare domin in yi wa Ubangiji Allah sujada.” 31 Sama'ila kuwa ya tafi tare da Saul, Saul kuwa ya yi wa Ubangiji sujada. 32 Sa'an nan Sama'ila ya ce, “Ku kawo mini Agag Sarkin Amalekawa.” Sai Agag ya taho wurinsa, yana rawar jiki don tsoro, yana cewa a ransa, “Hakika, azabar mutuwa ta fi ɗaci.” 33 Sama'ila ya ce masa, “Kamar yadda takobinka ya mai da mata marasa 'ya'ya, haka za a mai da mahaifiyarka ta zama marar ɗa.” Sai Sama'ila ya sassare Agag gunduwa gunduwa a gaban bagade a Gilgal. 34 Sa'an nan Sama'ila ya tafi Rama, Saul kuwa ya tafi gidansa a Gibeya. 35 Daga ran nan Sama'ila bai ƙara saduwa da sarki Saul ba, har rasuwar Sama'ila, amma ya ji juyayin Saul. Ubangiji kuwa bai ji daɗi da ya sa Saul ya zama Sarkin Isra'ila ba.

1 Sama’ila 16

An Keɓe Dawuda ya Zama Sarki

1 Ubangiji ya ce wa Sama'ila, “Har yaushe za ka yi ta ɓacin rai saboda Saul? Ga shi kuwa, na ƙi shi da zama Sarkin Isra'ila. Ka sami man zaitun ka ɗauka. Zan aike ka zuwa wurin Yesse mutumin Baitalami, gama na zaɓi ɗaya daga cikin 'ya'yansa maza ya zama sarki.” 2 Sama'ila kuwa ya ce, “Ƙaƙa zan yi wannan? Gama idan Saul ya ji zai kashe ni.” Sai Ubangiji ya ce, “Ka tafi da ɗan maraƙi, ka ce, ka zo ne ka miƙa wa Ubangiji hadaya. 3 Ka gayyaci Yesse zuwa wurin hadayar, zan nuna maka abin da za ka yi. Za ka zuba wa wanda na nuna maka mai.” 4 Sama'ila ya yi yadda Ubangiji ya faɗa masa, ya tafi Baitalami, inda dattawan garin suka tarye shi da rawar jiki, suka ce masa, “Maigani, wannan ziyara lafiya kuwa?” 5 Ya ce, “I, lafiya lau. Na zo ne in miƙa wa Ubangiji hadaya, sai ku tsarkake kanku, ku zo mu tafi wurin yin hadaya tare.” Ya kuma sa Yesse da 'ya'yansa maza su tsarkake kansu, su je wurin hadayar. 6 Da suka isa wurin hadayar, Sama'ila ya ga Eliyab, ɗan Yesse, sai ya zaci shi ne wanda Ubangiji ya zaɓa. 7 Amma Ubangiji ya ce masa, “Kada ka kula da kyan tsarinsa, ko tsayinsa, domin ba shi nake so ba, gama yadda Ubangiji yake gani, ba haka mutum yake gani ba. Mutum yakan dubi kyan tsari ne kawai, amma Ubangiji yakan dubi zuciya.” 8 Sa'an nan Yesse ya kira Abinadab ya wuce a gaban Sama'ila. Amma Sama'ila ya ce, “Ubangiji kuma bai zaɓi wannan ba.” 9 Sa'an nan Yesse ya sa Shimeya ya zo. Sama'ila kuma ya ce, “Ubangiji bai zaɓi wannan ba.” 10 Ta haka Yesse ya sa 'ya'yansa maza, su bakwai, suka zo a gaban Sama'ila. Sama'ila kuwa ya ce wa Yesse, “Ubangiji bai zaɓi waɗannan ba.” 11 Sai ya tambayi Yesse, “Ko kana da sauran waɗansu 'ya'ya maza?” Yesse ya ce, “Da sauran autan, ga shi kuma, yana wurin kiwon tumaki.” Sama'ila ya ce masa, “Sai ka aika a taho da shi, gama ba zan koma ba, sai ya zo.” 12 Yesse kuwa ya aika aka taho da shi. Ga shi kuwa kyakkyawa ne, idanunsa suna sheƙi. Sai Ubangiji ya ce wa Sama'ila, “Tashi ka zuba masa man keɓewa, shi ne sarkin.” 13 Sama'ila ya ɗauki man zaitun, ya zuba masa a gaban 'yan'uwansa. Ruhun Ubangiji ya sauko da iko a kan Dawuda tun daga wannan rana zuwa gaba. Sama'ila kuwa ya tashi, ya koma Rama.

Dawuda ya Kaɗa wa Saul Garaya

14 Yanzu kuwa Ruhun Ubangiji ya rabu da Saul, sai Ubangiji ya sa mugun ruhu ya azabtar da shi. 15 Barorin Saul kuwa suka ce masa, “To, ga shi yanzu, Ubangiji ya sa mugun ruhu yana azabtar da kai. 16 Saboda haka muna so ka ba mu izini mu tafi, mu nemo mutum gwanin kiɗan garaya, domin sa'ad da mugun ruhun nan da Allah ya sa maka, ya hau kanka, sai ya kaɗa maka garayar don ya sauka.” 17 Saul kuwa ya ce wa barorinsa. “To, sai ku samo mini mutum gwanin kiɗa, ku kawo mini shi.” 18 Sai wani daga cikin samarin ya amsa, ya ce, “Na san wani ɗan Yesse mutumin Baitalami. Shi gwanin kiɗan garaya ne, jarumi ne kuma, mayaƙi, mai lafazi, kyakkyawa, Ubangiji kuwa yana tare da shi.” 19 Sai Saul ya aiki manzanni zuwa wurin Yesse, ya ce, “Ka aiko mini da ɗanka, Dawuda, mai kiwon tumakinka.” 20 Yesse kuwa ya yi wa jaki labtu da abinci, da salkar ruwan inabi, da ɗan akuya, ya aiko Dawuda ɗansa, ya kai wa Saul. 21 Sa'an nan Dawuda ya zo wurin Saul, ya kama aiki. Saul kuwa ya ƙaunaci Dawuda ƙwarai, har Dawuda ya zama mai ɗaukar masa makamai. 22 Sa'an nan Saul ya aika wa Yesse cewa, “Ina so Dawuda. Ka bar shi ya zauna nan ya yi mini aiki.” 23 Tun daga ran nan zuwa gaba, a duk lokacin da mugun ruhun nan da Allah ya sa masa ya hau kansa, sai Dawuda ya ɗauki garaya, ya kaɗa masa. Sa'an nan mugun ruhu ya sauka, sai Saul ya wartsake.

1 Sama’ila 17

Goliyat yana Cakunar Isra'ilawa

1 Sai Filistiyawa suka tattaru a Soko ta Yahuza, suka kafa sansani a tsakanin Soko da Azeka, a Efes-dammim. 2 Saul kuma da mutanen Isra'ila suka tattaru, suka kafa sansani a kwarin Ila, suka jā dāga don su yi yaƙi da Filistiyawa. 3 Filistiyawa suka jeru a tudu guda, Isra'ilawa kuwa a ɗaya tudun. Kwari yana tsakaninsu. 4 Akwai wani jarumi, sunansa Goliyat, ya fito daga sansanin Filistiyawa. Tsayinsa kamu shida da rabi. 5 Yana sa kwalkwali na tagulla a kansa, yana kuma saye da sulke na tagulla wanda nauyinsa ya fi shekel dubu biyar (5,000 ). 6 Ya sa safa ta tagulla a ƙafafunsa, yana kuma da māshi na tagulla saɓe a kafaɗarsa. 7 Gorar māshinsa ta yi kama da dirkar masaƙa. Nauyin ruwan māshinsa na baƙin ƙarfe shekel ɗari shida ne. Mai ɗaukar masa garkuwa yana tafe a gabansa. 8 Goliyat ya ta da murya da ƙarfi, ya yi kira ga rundunar Isra'ila, ya ce, “Don me kuka fito ku jā dāgar yaƙi? Ai, ni Bafiliste ne, ku kuwa barorin Saul! Ku zaɓi mutum guda daga cikinku ya gangaro nan wurina. 9 Idan ya iya yaƙi da ni, ya kashe ni, to sai mu zama bayinku, amma idan na fi ƙarfinsa, na kashe shi, sai ku zama bayinmu, ku bauta mana.” 10 Ya ƙara da cewa, “Na raina rundunan Isra'ila yau. Ku ba ni mutumin da zan yi yaƙi da shi.” 11 Sa'ad da Saul da dukan Isra'ilawa suka ji maganganun da Bafilisten nan yake faɗa, sai suka karaya, suka tsorata ƙwarai.

Dawuda a Sansanin Saul

12 Dawuda kuwa ɗan Yesse ne, wanda yake mutumin Efrata, ta Baitalami cikin Yahuza, yana da 'ya'ya maza guda takwas, ya kuwa riga ya tsufa a zamanin Saul. 13 Manyan 'ya'yansa maza uku sun tafi yaƙi tare da Saul. Sunan babban ɗan, Eliyab, na biye da shi kuma, Abinadab, na ukun kuwa Shimeya. 14 Dawuda shi ne auta. Sa'ad da manyan 'yan'uwansa uku suka tafi tare da Saul wurin yaƙi, 15 Dawuda yakan koma Baitalami lokaci lokaci domin kiwon tumakin mahaifinsa. 16 Goliyat yana ta tsokanar Isra'ilawa safe da maraice, har kwana arba'in. 17 Wata rana ke nan, sai Yesse ya ce wa Dawuda, ɗansa, “Ka ɗauki wannan tumammen hatsi, da malmalar abinci goma, ka kai wa 'yan'uwanka da sauri a sansanin. 18 Ga waɗannan dunƙulen cuku goma, ka kai wa shugaba na mutum dubu. Ka dubo lafiyar 'yan'uwanka, ka kawo mini labari. 19 Da Saul, da 'yan'uwanka, da dukan mazajen Isra'ila suna kwarin Ila, suna yaƙi da Filistiyawa.” 20 Kashegari sai Dawuda ya tashi tun da sassafe, ya bar tumaki a hannun wani makiyayi, ya ɗauki guzurin, ya tafi kamar yadda mahaifinsa, Yesse, ya umarce shi. Ya isa sansani daidai lokacin da runduna suke fita tana kirari na jān dāgar yaƙi. 21 Isra'ilawa da Filistiyawa suka jā dāga, runduna gāba da runduna. 22 Sai Dawuda ya bar abin da ya kawo a wurin mai jiran kaya, ya sheƙa zuwa bakin dāga domin ya gai da 'yan'uwansa. 23 Sa'ad da yake magana da su, sai ga Goliyat, jarumin Filistiyawa na Gat, ya fito daga rundunar Filistiyawa, ya yi maganganu irin na dā. Dawuda kuwa ya ji. 24 Sa'ad da dukan mazajen Isra'ila suka ga mutumin, suka guje masa saboda tsoro. 25 Suka ce, “Kun ga mutumin nan da ya fito? Lalle ya fito ne don ya nuna mana raini. Duk wanda ya kashe shi, sarki zai arzutar da shi, ya ba shi 'yarsa aure, ya kuma 'yantar da gidan mahaifinsa cikin Isra'ila.” 26 Sai Dawuda ya tambayi mutanen da suke kusa da shi, ya ce, “Me za a yi wa wanda ya kashe Bafilisten nan, har ya kawar da zargi daga Isra'ila? Gama wane ne wannan Bafiliste, marar kaciya, da zai raina rundunar Allah mai rai?” 27 Mutane suka maimaita masa abin da sarki ya faɗa. 28 Lokacin da Dawuda yake magana da mutanen, sai Eliyab babban wansa ya ji, ya husata, ya ce wa Dawuda, “Me ya kawo ka nan? Wa ka bar wa 'yan tumakin nan a jeji? Na san rigimarka da taurinkanka, ka zo ne don ka yi kallon yaƙi.” 29 Dawuda kuwa ya ce, “To, me kuma na yi, ba tambaya kawai na yi ba?” 30 Sai ya rabu da shi ya tafi wurin wani, ya sāke yin tambaya irin ta dā, mutane kuma suka ba shi amsa irin ta dā. 31 Sa'ad da waɗansu suka ji maganar da Dawuda ya yi, sai suka faɗa wa Saul. Shi kuwa ya aika a kira Dawuda. 32 Dawuda kuwa ya ce wa Saul, “Kada zuciyar kowa ta karai saboda wannan mutum, baranka zai tafi ya yi yaƙi da shi.” 33 Saul ya ce wa Dawuda, “Ba za ka iya yaƙi da wannan Bafiliste ba, gama kai ɗan saurayi ne, shi kuwa ya saba da yaƙi tun yana saurayi.” 34 Amma Dawuda ya ce wa Saul, “Ai, baranka makiyayin tumakin mahaifinsa ne, sa'ad da zaki ko beyar ya zo ya kama ɗan rago daga garken, 35 nakan bi shi, in fāɗa masa, in ƙwato ɗan ragon daga bakinsa. Idan ya tasar mini da faɗa, sai in kama reronsa, in buge shi, in kashe shi. 36 Baranka ya taɓa kashe zaki da beyar, wannan arne zai zama kamar ɗaya daga cikinsu, tun da yake ya raina rundunar Allah mai rai. 37 Ubangiji wanda ya cece ni daga dāgin zaki da na beyar, zai cece ni daga hannun wannan Bafiliste.” Sa'an nan Saul ya ce wa Dawuda, “Tafi, Ubangiji ya taimake ka.” 38 Ya sa wa Dawuda kayan yaƙinsa, ya sa masa kwalkwalin tagulla a kansa, ya kuma sa masa sulke. 39 Da Dawuda ya sa kayan yaƙin, ya rataya takobi, ya fara tafiya, sai ya ji ba zai iya ba, domin bai saba da su ba. Sai ya ce wa Saul, “Ba zan iya tafiya da waɗannan ba, gama ban saba da su ba.” Ya kuwa tuɓe su. 40 Sa'an nan ya ɗauki sandansa, ya zaɓi duwatsu guda biyar masu sulɓi daga cikin rafi, ya zuba a angararsa. Ya kuma riƙe majajjawarsa, ya tafi, ya fuskanci Bafilisten.

Dawuda ya Kashe Goliyat

41 Bafilisten kuma ya nufo Dawuda, mai ɗaukar masa garkuwa yana gabansa. 42 Sa'ad da ya ga Dawuda, sai ya raine shi, gama Dawuda saurayi ne kawai, kyakkyawa. 43 Ya ce wa Dawuda, “Ni kare ne da za ka nufo da sanduna?” Ya zagi Dawuda da sunan allolinsu na Filistiyawa. 44 Ya kuma ce wa Dawuda, “Ya ka nan, ni kuwa in ba da namanka ga tsuntsayen sama da namomin jeji.” 45 Dawuda kuwa ya ce masa, “Kai, kana nufo ni da takobi, da māshi, da k�re, amma ni ina zuwa wurinka da sunan Ubangiji Mai Runduna, Allah na sojojin Isra'ila, wanda ka raina. 46 A yau Ubangiji zai bashe ka a hannuna, zan buge ka har ƙasa, in datse kanka, in ba da gawawwakin rundunar Filistiyawa ga tsuntsayen sama da namomin jeji, da haka duniya za ta sani lalle akwai Allah cikin Isra'ila. 47 Taron jama'ar nan kuma za su sani Ubangiji yakan yi ceto ba da takobi da māshi ba, gama yaƙi na Ubangiji ne, zai bashe ku a hannunmu.” 48 Goliyat kuwa ya fara gusowa ya gamu da Dawuda, sai Dawuda ya sheƙa zuwa bakin dāgar yaƙin don ya gamu da shi. 49 Sa'an nan Dawuda ya ɗauko dutse daga cikin angararsa, ya wurga, dutsen kuwa ya sami Goliyat a goshi, har ya lume. Goliyat kuwa ya faɗi rubda ciki. 50 Da majajjawa da dutse kawai Dawuda ya ci nasara da Bafilisten. Ya buge shi, ya kashe shi ba tare da takobi a hannunsa ba. 51 Sa'an nan ya sheƙa zuwa wurin Bafilisten, ya zare takobin Bafilisten daga kubensa, ya datse masa kai da shi. Da Filistiyawa suka ga jaruminsu ya mutu, sai suka gudu. 52 Mutanen Isra'ila da na Yahuza suka tashi suka runtumi Filistiyawa, suna ihu, har zuwa Gat da ƙofofin Ekron. Filistiyawan da aka yi wa rauni suka yi ta faɗuwa a hanya tun daga Shayarim, har zuwa Gat da Ekron. 53 Da Isra'ilawa suka komo daga runtumar Filistiyawa, suka wāshe sansanin Filistiyawa. 54 Dawuda kuwa ya ɗauki kan Bafilisten ya kawo Urushalima, amma ya ajiye kayan yaƙin Bafilisten a alfarwarsa.

An Kai Dawuda wurin Saul

55 Sa'ad da Saul ya ga Dawuda ya tafi ya yi yaƙi da Goliyat, ya ce wa Abner, sarkin yaƙinsa, “Abner, ɗan wane ne wannan saurayi?” Abner ya amsa, ya ce, “Ranka ya daɗe, ya sarki, ban sani ba.” 56 Sai ya ce, “Ka tambaya mini, wane ne uban saurayin nan.” 57 Da Dawuda ya komo daga kisan Goliyat, sai Abner ya kai shi wurin Saul, Dawuda yana ɗauke da kan Bafilisten. 58 Saul ya tambayi Dawuda, ya ce, “Saurayi, kai ɗan wane ne?” Dawuda ya amsa, ya ce, “Ni ɗan baranka ne, Yesse, mutumin Baitalami.”

1 Sama’ila 18

Alkawarin Jonatan da Dawuda

1 Da Dawuda ya gama magana da Saul, sai zuciyar Jonatan ta saje da ran Dawuda. Jonatan kuwa ya ƙaunaci Dawuda kamar kansa. 2 Daga ran nan Saul ya riƙe Dawuda, bai bari Dawuda ya koma gidan mahaifinsa ba. 3 Jonatan kuma ya yi dawwamammen alkawari da Dawuda, domin shi, wato Jonatan, yana ƙaunar Dawuda kamar kansa. 4 Sai ya tuɓe rigarsa ya ba Dawuda, ya kuma ba shi jabbarsa, da takobinsa, da bakansa, da abin ɗamararsa. 5 Duk inda Saul ya aiki Dawuda, sai ya tafi, ya kuma ci nasara. Saboda haka Saul ya maishe shi shugaban sojoji. Dukan jama'a da barorin Saul kuma suka ji daɗi.

Saul yana Kishin Dawuda

6 Sa'ad da sojoji suke komowa gida, bayan da Dawuda ya komo daga kisan Goliyat, sai mata daga kowane gari na Isra'ila suka fito domin su taryi sarki Saul. Suna raira waƙar farin ciki, suna rawa, suna kaɗa kuwaru da molaye. 7 Suka raira waƙa, suna cewa, “Saul ya kashe dubbai, amma Dawuda ya kashe dubun dubbai.” 8 Wannan waƙa ta ba Saul haushi, ya ce, “Sun ba Dawuda dubun dubbai, amma dubbai kawai suka ba ni, me kuma ya rage masa, ai, sai sarauta.” 9 Tun daga wannan rana Saul ya fara kishin Dawuda. 10 Kashegari Allah ya sa mugun ruhu ya sauka a kan Saul, sai ya yi ta maganganu a gidansa kamar mahaukaci, sai Dawuda ya yi ta kaɗa masa garaya kamar yadda ya saba yi. Saul kuwa yana riƙe da māshi. 11 Yana cewa a ransa, “Zan nashe shi in kafe shi da bango.” Sau biyu yana cakar Dawuda da māshi, amma Dawuda ya goce. 12 Saul ya ji tsoron Dawuda, gama Ubangiji yana tare da Dawuda, amma ya rabu da Saul. 13 Saboda haka Saul bai yarda Dawuda ya zauna tare da shi ba, amma ya maishe shi shugaban dubu. Shi kuwa ya riƙa bi da su cikin kai da kawowa. 14 Dawuda kuwa ya yi ta yin nasara cikin ayyukansa duka, domin Ubangiji yana tare da shi. 15 Da Saul ya ga Dawuda yana yin nasara, sai ya ƙara jin tsoronsa. 16 Dukan mutanen Isra'ila da na Yahuza suka ƙaunaci Dawuda, domin yana kai da kawowa a cikinsu.

Dawuda ya Auri 'Yar Saul

17 Sai Saul ya ce wa Dawuda, “Ga Merab babbar 'yata, zan ba ka ita ka aura, idan ka yi mini aikin jaruntaka, wato ka yi yaƙin Ubangiji.” (Gama Saul yana tsammani ta wannan hanya Filistiyawa za su kashe Dawuda, ba lalle sai shi da kansa ya kashe shi ba.) 18 Dawuda, ya ce wa Saul, “Wane ni ko iyalin mahaifina a cikin Isra'ila, har da zan zama surukin sarki?” 19 Amma sa'ad da lokaci ya yi da za a ba Dawuda Merab, 'yar Saul, ya aura, sai aka aurar da ita ga Adriyel, mutumin Abel-mehola. 20 Mikal, 'yar Saul kuwa, ta ƙaunaci Dawuda, sai aka faɗa wa Saul, shi kuwa ya yarda da haka. 21 Ya yi tunani a ransa ya ce, “Zan ba shi ita don ta zamar masa sanadin da zai mutu ta hannun Filistiyawa.” Don haka sai Saul ya ce wa Dawuda a karo na biyu, “Yanzu dai za ka zama surukina.” 22 Sai Saul ya umarci fādawansa, ya ce, “Ku yi magana da Dawuda a ɓoye, ku ce masa, ‘Ga shi, sarki yana jin daɗinka, dukan fādawansa kuma suna ƙaunarka, yanzu sai ka zama surukin sarki.’ ” 23 Fādawan Saul kuwa suka faɗa wa Dawuda wannan magana. Sai Dawuda ya ce, “Zama surukin sarki ƙaramin abu ne a ganinku? Ga shi, ni talaka ne wanda ba sananne ba.” 24 Fādawan suka faɗa wa Saul abin da Dawuda ya faɗa. 25 Saul kuma ya ce, “Haka za ku faɗa wa Dawuda, ‘Sarki ba ya so ka ba da sadaki don auren, sai dai ka ba da loɓar Filistiyawa guda ɗari, domin ka ɗauki fansa a kan maƙiyan sarki.’ ” (Saul dai yana so Filistiyawa su kashe Dawuda kawai.) fādawan suka faɗa wa Dawuda abin da Saul ya ce, sai Dawuda ya ji daɗi ƙwarai ya zama surukin sarki. Kafin lokacin da aka yanka masa ya yi, sai Dawuda ya tashi, ya tafi tare da mutanensa, suka kashe Filistiyawa ɗari biyu. Ya kawo loɓarsu duka, aka ba sarki, domin ya zama surukin sarki. Saul kuwa ya aurar da Mikal, 'yarsa, ga Dawuda. 28-29 Da Saul ya gane lalle Ubangiji yana tare da Dawuda, Mikal 'yarsa kuma tana ƙaunar Dawuda, sai ya ƙara jin tsoronsa, ya maishe shi maƙiyinsa na din din din. 30 Sarakunan Filistiyawa sukan zo da yaƙi. Idan sun zo, sai Dawuda ya yi nasara da su fiye da sauran shugabannin yaƙi na Saul. Wannan ya sa ya yi suna.

1 Sama’ila 19

Saul ya Tsananta wa Dawuda

1 Sai Saul ya yi magana da Jonatan, ɗansa, da dukan fādawansa, cewa yana shiri ya kashe Dawuda. Amma Jonatan ɗan Saul yana jin daɗin Dawuda ƙwarai. 2 Jonatan ya faɗa wa Dawuda ya ce, “Saul, mahaifina, yana so ya kashe ka, domin haka sai ka lura da kanka da safe, ka ɓuya a wani lungu. 3 Ni kuwa zan tafi in tsaya kusa da mahaifina a saura inda ka ɓuya, zan yi masa magana a kanka, abin da ya faru, zan sanar da kai.” 4 Jonatan kuwa ya yabi Dawuda a gaban Saul, ya ce masa, “Kada sarki ya yi wa baransa, Dawuda, laifi, gama shi bai yi maka laifi ba, ayyukansa kuma a gare ka masu kyau ne. 5 Ya yi kasai da ransa har ya kashe Bafilisten, Ubangiji kuwa ya ba Isra'ilawa babbar nasara. Kai ma ka gani, ka kuwa yi murna. Me ya sa za ka ɗauki alhakin Dawuda, wanda bai yi maka laifin kome ba?” 6 Saul kuwa ya saurari maganar Jonatan, ya rantse masa ya ce, “Hakika, ba za a kashe shi ba.” 7 Jonatan kuwa ya kira Dawuda ya faɗa masa dukan abin da Saul ya faɗa. Ya kuma kai Dawuda gaban Saul, ya zauna tare da shi kamar dā. 8 Aka kuma yi yaƙi da Filistiyawa, Dawuda kuwa ya tafi ya yi yaƙi da su, ya kashe su da yawa, sai suka gudu a gabansa. 9 Ubangiji kuma ya sa mugun ruhu ya sauko kan Saul sa'ad da yake zaune a gidansa, da māshi a hannunsa. Dawuda kuma yana ta kaɗa masa garaya. 10 Saul kuwa ya yi shiri ya nashi Dawuda, ya kafe shi ga bango. Da ya nashe shi, sai ya goce, māshin ya sami bangon. Dawuda kuwa ya gudu, ya tsere. 11 A daren nan Saul ya aiki manzanni su je gidan Dawuda don su yi fakonsa, su kashe shi da safe. Amma Mikal, matar Dawuda, ta faɗa masa cewa, “Idan ba ka gudu da daren nan ba, gobe za a kashe ka.” 12 Sai ta zurarar da Dawuda ta taga, ya gudu, ya tsere. 13 Mikal kuwa ta ɗauki kan gida ta kwantar da shi a gado, ta kuma sa masa matashin kai na gashin awaki, sa'an nan ta lulluɓe shi da mayafi. 14 Sa'ad da manzannin Saul suka zo don su kama Dawuda, sai ta ce musu, “Ba shi da lafiya.” 15 Saul kuma ya sāke aiken manzannin su tafi su ga Dawuda, ya ce musu, “Ku kawo shi nan wurina a kan gadonsa don in kashe shi.” 16 Da manzannin suka tafi, sai suka tarar da kan gida a gadon, da matashin kai na gashin awaki wajen kansa. 17 Saul kuwa ya ce wa Mikal, “Don me kika ruɗe ni har kika bar maƙiyina ya tsere?” Ta ce wa Saul, “Ya ce mini, idan ban bar shi ya tafi ba, zai kashe ni.” 18 Dawuda ya gudu, ya tsere zuwa wurin Sama'ila a Rama, ya faɗa masa dukan abin da Saul ya yi masa. Shi da Sama'ila suka tafi suka zauna a Nayot. 19 Aka faɗa wa Saul cewa, “Dawuda yana a Nayot ta Rama.” 20 Sai ya aika da manzanni su tafi su kama Dawuda. Da suka kai, suka iske ƙungiyar annabawa suna annabci, Sama'ila kuwa yana tsaye a gabansu. Ruhun Allah ya sauko a kan manzannin Saul, su kuma suka yi annabci. 21 Aka faɗa wa Saul, sai ya sāke aiken waɗansu, su kuma suka shiga yin annabci. Ya kuma sāke aiken manzanni aji na uku, su kuma suka shiga yin annabci. 22 Saul kuma ya tafu Rama da kansa. Da ya kai babbar rijiyar da take a Seku, sai ya tambayi inda Sama'ila da Dawuda suke. Wani ya ce masa, “Suna Nayot ta Rama.” 23 Sai ya tashi daga can zuwa Nayot ta Rama. Ruhun Allah kuwa ya sauko a kansa, sai shi kuma ya shiga yin annabci har ya kai Nayot ta Rama, 24 ya kuma tuɓe tufafinsa, ya yi ta annabci a gaban Sama'ila. Ya kwanta huntu dukan yini da dukan dare. Don haka aka riƙa yin karin magana da cewa, “Har Saul ma yana cikin annabawa?”

1 Sama’ila 20

Abutar Dawuda da Jonatan

1 Sa'an nan Dawuda ya gudu daga Nayot ta Rama, ya zo wurin Jonatan, ya ce masa, “Me na yi? Mene ne laifin da na yi wa mahaifinka da yake so ya kashe ne?” 2 Jonatan ya ce masa, “Allah ya sawwaƙa, ba za a kashe ka ba, gama babana yakan faɗa mini kome, ƙarami ko babba, kafin ya aikata. To, me zai sa babana ya ɓoye mini wannan? Wannan ba haka yake ba.” 3 Amma Dawuda ya rantse masa, ya ce, “Mahaifinka ya hakikance na sami tagomashi a wurinka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada ya baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji da kai kuma, mataki ɗaya yake tsakanina da mutuwa!” 4 Sai Jonatan ya ce wa Dawuda, “Duk abin da ka ce, zan yi maka.” 5 Dawuda kuwa ya ce masa, “Ga shi, gobe ce amaryar wata, dole ne in zauna tare da sarki a teburinsa. Ka bar ni in tafi in ɓuya a saura har kwana uku. 6 Idan mahaifinka bai gan ni ba, sai ka ce masa, ni na roƙe ka ka bar ni in gaggauta zuwa Baitalami, garinmu, domin akwai ba da sadaka ta shekara saboda dukan gidanmu. 7 Idan ka ji ya ce, ‘Da kyau,’ to, baranka zai tsira ke nan, amma idan ya husata, to, sai ka sani yana niyyar kashe ni ke nan, 8 kai kuwa ka nuna mini alheri, gama ka yi mini alkawari mai ƙarfi. Amma idan ina da laifi, sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bar mahaifinka ya kashe ni?” 9 Jonatan ya masa ya ce, “Allah ya sawwaƙe! Da na sani babana yana da nufi ya yi maka mugunta, ai, da na faɗa maka.” 10 Sa'an nan Dawuda ya ce wa Jonatan, “Wane ne zai faɗa mini idan mahaifinka ya amsa maka da fushi?” 11 Jonatan kuwa ya ce masa, “Zo mu tafi saura.” Sai su biyu suka tafi saura. 12 Sa'an nan Jonatan ya ce wa Dawuda, “Ubangiji Allah na Isra'ila zai zama shaida. Gobe war haka, ko jibi zan tattauna maganar da mahaifina, idan da nufin alheri zuwa gare ka, zan aika, in faɗa maka. 13 Amma idan har mahaifina yana da niyyar yi maka mugunta, amma ban sanar da kai ba, to, bari Ubangiji ya hukunta ni. Ubangiji ya kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina. 14 Ba lokacin da nake da rai ne kaɗai za ka nuna mini alherin Ubangiji domin kada in mutu ba. 15 Ko bayan raina kada ka daina nuna wa gidana alheri har abada, lokacin da Ubangiji ya datse maƙiyanka daga fuskar duniya.” 16 Jonatan ya yi alkawari da gidan Dawuda. Ubangiji kuwa zai ɗauki fansa a kan maƙiyan Dawuda. 17 Sai Jonatan ya sa Dawuda ya yi masa alkawari zai ƙaunace shi, gama shi kansa yana ƙaunar Dawuda ƙwarai kamar yadda yake ƙaunar kansa. 18 Sa'an nan Jonatan ya ce wa Dawuda, “Gobe ce amaryar wata, ba kowa a wurin zamanka ke nan da yake ba za ka zo ba. 19 A rana ta uku za a gane ba ka nan sosai, to, sai ka tafi, ka ɓuya a wurin da ka ɓuya a waccan rana. Ka zauna kusa da tarin duwatsu. 20 Zan harba kibau guda uku kusa da tarin duwatsun, kamar ina harbin wani abu ne. 21 Zan aiki yaro ya tafi ya nemo kiban. Idan na ce masa, ‘Duba, ga kiban kusa da kai, ka kawo su,’ To, sai ka fito, ka zo, wato lalle kome lafiya ke nan, ba abin da zai cuce ka. 22 Amma idan na ce wa yaron, ‘Duba, kiban suna a gabanka,’ To, ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka, ka tafi. 23 A kan alkawarin da muka yi, ni da kai kuwa, Ubangiji shi ne shaida a tsakaninmu har abada.” 24 Dawuda ya ɓuya a saura. A ranar amaryar wata kuwa sarki ya zauna domin cin abinci. 25 Ya zauna inda ya saba zama kusa da bango. Jonatan ya zauna daura da shi, Abner kuwa ya zauna kusa da Saul, amma ba kowa a wurin zaman Dawuda. 26 Saul kuwa bai ce kome a wannan rana ba, gama ya zaci wani abu ya sami Dawuda, kila ba shi da tsarki, lalle kam Dawuda ba shi da tsarki. 27 Amma kashegari, wato rana ta biyu ta amaryar watan, ba kowa kuma wurin zaman Dawuda, sai Saul ya ce wa Jonatan, ɗansa, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo wurin cin abinci ba, jiya da yau?” 28 Jonatan ya ce masa, “Dawuda ya roƙe ni da naciya in bar shi ya tafi Baitalami. 29 Ya ce mini, ‘In ka yarda ka bar ni in tafi, gama a gidanmu ana ba da sadaka a gari, ɗan'uwana kuwa ya umarce ni in je. Idan na sami tagomashi a wurinka ka bar ni in tafi in ga 'yan'uwana.’ Abin da ya sa bai zo ba ke nan.” 30 Sai Saul ya husata da Jonatan, ya ce masa, “Kai yaron banza ne, mai ƙin ji, ai, na sani kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulakantar da kanka da mahaifinka. 31 Muddin ɗan Yesse na da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za ta kahu ba. Yanzu sai ka je ka taho mini da shi. Dole kashe shi za a yi.” 32 Jonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa za a kashe shi? Me ya yi?” 33 Sai Saul ya jefe shi da māshi don ya kashe shi. Sai Jonatan ya gane lalle mahaifinsa ya yi niyya ya kashe Dawuda. 34 Sai Jonatan ya tashi da fushi daga wurin cin abinci, bai ci abinci a rana ta biyu ga watan ba, saboda baƙin ciki a kan Dawuda, domin kuma mahaifinsa ya kunyata shi. 35 Da safe Jonatan ya tafi saura tare da wani yaro daidai lokacin da ya shirya da Dawuda. 36 Sai ya ce wa yaron, “Yi gudu, ka nemo kiban da zan harba.” Sa'ad da yaron ya ruga, sai ya harba kibiya gaba da shi. 37 Da yaron ya kai inda Jonatan ya harba kibiyar, sai ya ce masa, “Ba kibiyar tana a gaban ka ba?” 38 Ya ce wa yaron ya yi maza, kada ya tsaya. Sai yaron ya kwashe kiban ya kawo masa. 39 Amma yaron bai san abin da ake nufi ba. Jonatan da Dawuda kaɗai suka san abin da ake ciki. 40 Sa'an nan Jonatan ya ba yaron makamansa, ya ce masa, “Kai su gari.” 41 Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsun, ya rusuna har sau uku. Sa'an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, amma Dawuda ya fi yi. 42 Jonatan ya ce wa Dawuda, “Sai ka tafi lafiya, tun da yake mun riga mun rantse wa juna da sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji zai zama shaida tsakanina da kai, da tsakanin zuriyarmu har abada.’ ” Dawuda ya yi tafiyarsa, Jonatan kuwa ya koma gari.

1 Sama’ila 21

Dawuda ya Gudu daga wurin Saul

1 Sa'an nan Dawuda ya tafi wurin Ahimelek, firist, a Nob. Ahimelek kuwa ya fita da rawar jiki domin ya tarye Dawuda, ya ce masa, “Me ya sa kake kai kaɗai, ba wani tare da kai ba?” 2 Dawuda ya ce masa, “Na zo aikin sarki ne, ya kuwa ce kada in sanar wa kowa abin da ya aiko ni in yi. Jama'ata kuwa na riga na shirya inda zan sadu da su. 3 Yanzu me kake da shi? Sai ka ba ni abinci malmala biyar ko wani abu da kake da shi a nan.” 4 Firist ɗan ya ce wa Dawuda, “Ba ni da abinci don kowa da kowa, sai dai gurasa ta ajiyewa. Zan iya in ba ka muddin dai samarin sun keɓe kansu daga mata.” 5 Dawuda ya ce masa, “Lalle ne a keɓe muke daga mata. Mutanena suka keɓe kansu a koyaushe suka tashi 'yar tafiya, balle fa yanzu da muka fito yin wani abu musamman.” 6 Firist ɗin kuwa ya ba Dawuda tsattsarkan abinci na ajiya, gama ba wani abinci a wurin, sai gurasar ajiyewa kaɗai wadda akan kawar, a sāke sa wata mai ɗumi a ranar da aka kawar da ita. 7 A ranar kuwa akwai wani mutum daga cikin barorin Saul, wanda aka tsare a gaban Ubangiji, sunansa Doyeg, mutumin Edom ne. Shi ne shugaban masu kiwon garkunan Saul. 8 Dawuda kuwa ya ce wa Ahimelek, “Kana da māshi ko takobi a nan kusa? Gama ban zo da takobina ko wani makami ba, domin ka sani sha'anin sarki na gaggawa ne.” 9 Firist ya ce, “Ga takobin Goliyat, Bafiliste wanda ka kashe a kwarin Ila, a naɗe da zane a bayan falmaran. Idan kana so ka ɗauka, sai ka ɗauka, gama banda shi, ba wani takobi a nan.” Dawuda kuwa ya ce, “Ai, ba wanda ya fi wannan, sai ka ba ni shi.” 10 Sai Dawuda ya tashi, yana gudu ke nan daga wurin Saul. Ya tafi wurin Akish, Sarkin Gat. 11 Fādawan Akish kuwa suka ce masa, “Ashe, wannan ba shi ne Dawuda, sarkin ƙasar ba? Ba a kansa suka raira waƙa cikin raye-rayensu suna cewa, ‘Saul ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?’ ” 12 Da Dawuda ya ji waɗannan maganganu, sai ya tsorata ƙwarai da Akish Sarkin Gat. 13 Ya mai da kansa kamar mahaukaci a gabansa. Ya yi zane-zane a ƙyamaren ƙofofin garin. Ya bar yau na bin gemunsa. 14 Akish kuwa ya ce wa fādawansa, “Ashe, mutumin mahaukaci ne? Don me kuka kawo shi wurina? 15 Na rasa mahaukata ne da za ku kawo mini wannan mutum ya yi ta hauka a gabana? Wannan mutum ne zai shiga gidana?”

1 Sama’ila 22

An Kashe Firistoci

1 Dawuda ya bar Gat, ya tsere zuwa kogon Adullam. Da 'yan'uwansa da mutanen gidan ubansa, suka ji labari, suka tafi can wurinsa. 2 Kowane mutum kuma da yake matse, da wanda ake bi bashi, da wanda ransa ba ya kwance, suka tattaru a wurin Dawuda. Shi kuwa ya zama shugabansu. Sun kai wajen mutum ɗari huɗu. 3 Daga can Dawuda ya wuce zuwa Mizfa ta Mowab. Ya ce wa Sarkin Mowab, “Ina roƙonka, ka yarda mahaifina da mahaifiyata su zo su zauna a wurinka kafin in san abin da Ubangiji zai yi da ni.” 4 Sai ya bar iyayensa a wurin Sarkin Mowab, suka zauna a wurinsa duk lokacin da Dawuda yake ta ɓuya a kogwannin duwatsu. 5 Sa'an nan Gad, annabi, ya ce wa Dawuda, “Kada ka zauna a nan, maza ka tafi ƙasar Yahuza.” Sai ya tashi, ya tafi kurmin Haret.

Saul ya Kashe Firistoci na Nob

6 Sai Saul ya ji labari an gane inda Dawuda da mutanensa suke. Saul kuwa yana zaune a Gibeya a gindin itacen tsamiya a kan tudu, yana riƙe da māshinsa. Dukan fādawansa suna tsaye kewaye da shi. ya ce wa fādawan da yake tsaye kewaye da shi, “Ku ji, ya ku mutanen Biliyaminu, ɗan Yesse zai ba ko wannenku gonaki, da gonakin inabi ne? Zai maishe ku shugabanni na dubu dubu, da na ɗari ɗari, har da dukanku kuka yi mini maƙarƙashiya? Ba wanda ya sanar da ni sa'ad da ɗana ya haɗa kai da ɗan Yesse? Ba wanda ya damu saboda da ni, balle a faɗa mini yadda ɗana ya kuta barana ya tayar mini, yana fakona, kamar yadda yake a yau?” 9 Sa'an nan Doyeg, mutumin Edom, da yake tsaye tare da fādawan Saul, ya ce, “Na ga ɗan Yesse yana zuwa Nob wurin Ahimelek, ɗan Ahitub. 10 Shi kuwa ya roƙi Ubangiji domin Dawuda, ya kuma ba shi guzuri, har ya ba shi takobin Goliyat, Bafilisten.” 11 Sarki kuwa ya aika a kira Ahimelek, firist, ɗan Ahitub, da dukan mutanen gidan mahaifinsa, da firistocin da suke a Nob. Dukansu kuwa suka zo wurin sarki. 12 Saul kuwa ya ce, “Ka ji, ya ɗan Ahitub.” Shi kuwa ya amsa ya ce, “Ranka ya daɗe, ina ji.” 13 Saul ya ce masa, “Me ya sa ka yi mini maƙarƙashiya, kai da ɗan Yesse, da yake ka ba shi abinci, da takobi, ka kuma roƙar masa Allah, ga shi yanzu, ya tayar mini, yana fakona, kamar yadda yake yi a yau?” 14 Ahimelek kuwa ya ce wa sarki, “Daga cikin barorinka duka wa yake da aminci kamar Dawuda? Wane ne surukin sarki? Wane ne shugaban jarumawanka, wanda ake girmamawa a gidanka? 15 Yau ne na fara roƙar masa Allah? A'a, kada dai sarki ya zargi baransa ko gidan mahaifina duka, gama baranka bai san kome a kan wannan ba.” 16 Sai sarki ya ce, “Hakika, mutuwa za ku yi, Ahimelek, kai da dukan gidan mahaifinka.” 17 Ya ce wa matsara da yake tsaye kewaye da shi, “Ku fāɗa wa firistocin Ubangiji, ku kashe su gama suna goyon bayan Dawuda, ga shi, sun sani ya gudu, amma ba su faɗa mini ba.” Amma barorin sarki ba su yarda su fāɗa wa firistocin Ubangiji ba. 18 Sa'an nan sarki ya ce wa Doyeg, “Kai ka fāɗa wa firistocin.” Sai Doyeg, mutumin Edom, ya fāɗa wa firistocin, ya kashe mutum tamanin da biyar waɗanda suke saye da falmaran na lilin a wannan rana. 19 Ya kuma hallaka Nob birnin firistoci, ya kashe dukan mata, da maza, da yara, da jarirai, da shanu, da jakai, da tumaki. 20 Amma Abiyata ɗaya daga cikin 'ya'yan Ahimelek, ɗan Ahitub, ya tsere, ya gudu zuwa wurin Dawuda. 21 Sai ya faɗa wa Dawuda Saul ya kashe firistocin Ubangiji. 22 Dawuda kuwa ya ce wa Abiyata, “A ran nan Doyeg, mutumin Edom, yana wurin, na sani lalle zai faɗa wa Saul. Ni na zama sanadin mutuwar dukan mutanen gidan mahaifinka. 23 Sai ka zauna tare da ni, kada ka ji tsoro, gama wanda yake neman raina yana neman naka. Ka yi zamanka lafiya tare da ni.”

1 Sama’ila 23

Dawuda ya Kuɓutar da Garin Kaila

1 Aka faɗa wa Dawuda, cewa Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Kaila, suna washe musu hatsi a masussukai. 2 Sai Dawuda ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Ko in tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce wa Dawuda, “Tafi, ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci mutanen Kaila.” 3 Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, nan ma a Yahuza muna jin tsoro, balle mu tafi Kaila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa.” 4 Dawuda kuma ya sāke roƙon Ubangiji. Sai Ubangiji ya amsa masa, ya ce, “Tashi, ka gangara zuwa Kaila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.” 5 Sa'an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Kaila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kashe su da yawa, suka kwashe shanunsu. Da haka Dawuda ya kuɓutar da mazaunan Kaila. 6 Lokacin da Abiyata ɗan Ahimelek, ya gudu zuwa wurin Dawuda a Kaila, ya zo da falmaran a hannunsa. 7 Aka faɗa wa Saul Dawuda ya zo Kaila. Sai ya ce, “Madalla, Allah ya bashe shi a hannuna, gama ya kulle kansa, da yake ya shiga garin da yake da ƙofofin da akan kulle da sandunan ƙarfe.” 8 Saul ya kirawo dukan mutanensa, su fita yaƙi, su tafi Kaila don su kewaye Dawuda tare da mutanensa. 9 Dawuda kuwa ya sani Saul yana shirya hanyar kashe shi, sai ya ce wa Abiyata, firist, “Kawo falmaran a nan.” 10 Sa'an nan ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, hakika bawanka ya ji Saul yana niyyar zuwa Kaila don ya hallakar da garin saboda ni. 11 Ko mutanen Kaila za su bashe ni a hannunsa? Ko Saul zai zo kamar yadda na ji? Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, ina roƙonka ka faɗa wa bawanka.” Ubangiji kuwa ya ce, “Saul zai zo.” 12 Dawuda kuma ya ce, “Mutanen Kaila za su bashe ni da mutanena a hannun Saul?” Ubangiji ya ce masa, “Za su bashe ku.” 13 Sa'an nan Dawuda da mutanen da suke tare da shi, mutum wajen ɗari shida, suka tashi daga Kaila, suka tafi inda hali ya kai su. Da Saul ya ji Dawuda ya tsere daga Kaila, sai ya fasa tafiya can.

Dawuda a Jejin Ƙasar Tudu

14 Dawuda ya zauna a ɓoye cikin jeji a ƙasar tudu ta jejin Zif. Saul kuwa ya yi ta nemansa kowace rana, amma Ubangiji bai ba da Dawuda a hannunsa ba. kuwa ya ji tsoro, gama Saul ya fito don ya farauci ransa. Sa'ad da yake cikin jejin Zif, a Horesh, sai Jonatan ɗan Saul, ya zo wurinsa, ya tabbatar masa da kiyayyewar Allah. 17 Ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, gama Saul, mahaifina ba zai same ka ba. Za ka zama Sarkin Isra'ila, ni kuma zan zama wazirinka. Saul mahaifina ya san da haka.” 18 Su biyu fa suka yi wa juna alkawari a gaban Ubangiji. Dawuda ya zauna a Horesh, Jonatan kuwa ya koma gida. 19 Sai Zifawa suka haura zuwa wurin Saul a Gibeya, suka ce masa, “Dawuda ya ɓuya a ƙasarmu cikin Horesh a kan tudun Hakila da yake kudu da jejin Yahuza. 20 Sai ka gangara, ka zo, ya sarki, ta yadda kake so. Mu za mu bashe shi a hannun sarki.” 21 Saul ya ce, “Ubangiji ya sa muku albarka, gama kuna jin juyayina. 22 Ku tafi, ku ƙara tabbatar da inda ya ɓuya, da wanda ya gan shi a wurin, gama an faɗa mini, cewa shi mai wayo ne. 23 Ku lura sosai da dukan wuraren da yake ɓuya, sa'an nan ku komo mini da tabbataccen labari. Sa'an nan zan tafi tare da ku. Idan yana ƙasar, zan neme shi ko'ina a ƙasar Yahuza.” 24 Sai suka yi gaba, suka tafi Zif. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon, cikin Araba, kudu da Yeshimon. 25 Saul da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya sauka daga dutsen ya zauna a can jejin Mawon. Da Saul ya ji, sai ya bi Dawuda zuwa jejin Mawon. 26 Saul yana gefe ɗaya na dutsen, Dawuda kuma da mutanensa suna wancan gefe. Dawuda ya yi sauri ya tsere daga Saul domin Saul da mutanensa suna ƙoƙari su kewaye su, su kama su. 27 Suna bin su Dawuda kusa kusa, sai manzo ya zo ya ce wa Saul, “Sai ka komo da sauri domin Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.” 28 Saul kuwa ya koma daga bin Dawuda, ya tafi, ya yi yaƙi da Filistiyawa, don haka aka riƙa kiran wurin, Sela-hammalekot, wato dutsen tserewa. 29 Dawuda kuwa ya tashi daga can, ya tafi jejin En-gedi inda ya ɓuya.

1 Sama’ila 24

Dawuda ya Bar Saul da Rai a En-gedi

1 Da Saul ya komo daga yaƙi da Filistiyawa, sai aka faɗa masa Dawuda yana jejin En-gedi. 2 Sai Saul ya zaɓi mutum dubu uku (3,000 ) daga cikin dukan mutanen Isra'ila, ya tafi ya nemi Dawuda da mutanensa a gaban duwatsun awakin jeji. 3 Saul ya isa garken tumaki a gefen hanya, inda akwai kogo. Sai ya shiga cikin kogon don ya huta. Dawuda da mutanensa kuwa suna zaune a ƙurewar kogon. 4 Mutanen Dawuda suka ce masa, “Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da maƙiyinka a hannunka, ka yi yadda ka ga dama da shi.” Dawuda kuwa ya tashi a hankali, ya yanke shafin rigar Saul. 5 Daga baya zuciyar Dawuda ta kāshe shi domin ya yanke shafin rigar Saul. 6 Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji ya sawwaƙa in yi wa ubangijina irin abu haka, har in miƙa hannuna in kashe keɓaɓɓe na Ubangiji.” 7 Da wannan magana Dawuda ya rinjayi mutanensa, bai yarda musu su fāɗa wa Saul ba. Sai Saul ya fita daga kogon ya kama hanya, ya yi tafiyarsa. 8 Daga baya kuma Dawuda ya fita daga kogon, ya yi kira, ya ce, “Ya ubangijina, sarki.” Da Saul ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna. 9 Ya ce wa Saul, “Me ya sa kake kasa kunne ga maganganun mutanen da suke cewa, ‘Dawuda yana nema ya cuce ka?’ 10 To, yau da idanunka ka ga yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a kogon, har waɗansu suka ce mini in kashe ka, amma na ji tausayinka. Na ce, ‘Ba zan miƙa hannuna in kashe ubangijina ba, gama shi keɓaɓɓe na Ubangiji ne.’ 11 Baba, duba, ga shafin rigarka a hannuna. Tun da yake na yanki shafin rigarka ban kuwa kashe ka ba, sai ka sani ba ni da niyyar yi maka mugunta. Ban yi maka laifi ba, ko da yake kana farautar raina. 12 Ubangiji dai zai shara'anta tsakanina da kai, ya sāke mini, amma hannuna ba zai taɓa ka ba. 13 Mutanen dā suna da karin magana cewa, ‘Daga cikin masu mugunta mugunta yake fitowa.’ Hannuna dai ba zai taɓa ka ba. 14 Shin, sawun wa Sarkin Isra'ila yake bi? Wane ne kuma kake runtuma? Kana bin sawun mataccen kare, da sawun tunkuyau? 15 Ubangiji ne zai zama alƙali, ya hukunta tsakanina da kai. Zai tsaya mini, ya cece ni daga hannunka.” 16 Da Dawuda ya gama faɗa wa Saul wannan magana, sai Saul ya ce, “Ɗana, Dawuda, muryarka ke nan?” Ya yi kuka da ƙarfi. 17 Sa'an nan ya ce wa Dawuda, “Ka fi ni adalci, gama ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta. 18 Yau ka nuna a sarari yadda ka yi mini alheri. Ubangiji ya bashe ni a hannunka, amma ba ka kashe ni ba. 19 Idan mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi ya tafi lafiya? Ubangiji ya sāka maka saboda alherin da ka yi mini yau. 20 Yanzu kuwa na sani za ka zama sarki, sarautar Isra'ila za ta kahu a hannunka. 21 Sai ka rantse mini da Ubangiji, cewa ba za ka hallaka zuriyata a bayana ba, ba kuwa za ka shafe sunana daga cikin gidan ubana ba.” 22 Dawuda kuwa ya yi wa Saul alkawari. Sa'an nan Saul ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka koma wurin ɓuya.

1 Sama’ila 25

Rasuwar Sama'ila

1 Sama'ila kuwa ya rasu. Dukan Isra'ilawa suka taru suka yi makoki dominsa. Suka binne shi a gidansa a Rama.

Dawuda da Abigail

Sai Dawuda ya tashi ya tafi jejin Faran. 2 Akwai wani mutumin Mawon wanda yake da harka a Karmel. Mutumin mai dukiya ne ƙwarai, yana da tumaki dubu uku (3,000 ) da awaki dubu (1,000 ). Yana yi wa tumakinsa sausaya a Karmel. 3 Sunan mutumin kuwa Nabal, sunan matarsa kuma Abigail, ita haziƙa ce, kyakkyawa, amma mijinta miskili ne, marar mutunci. Shi daga zuriyar Kalibu ne. 4 Daga cikin jeji, Dawuda ya ji, cewa Nabal yana yi wa tumakinsa sausaya, 5 sai ya aiki samari goma, ya ce musu, “Ku tafi Karmel wurin Nabal, ku ce ina gaishe shi. 6 Gaisuwar da za ku yi masa ke nan, ku ce, ‘Salama gare ka, salama ga gidanka, salama kuma ga dukan abin da kake da shi. 7 Na ji kana da masu sausaya. Lokacin da makiyayanka suke tare da mu, ba mu cuce su ba, ba abin da ya ɓace musu dukan lokacin da suke a Karmel. 8 Tambayi samarinka, za su faɗa maka. Saboda haka ka yarda samarina su sami tagomashi a wurinka, gama yau ranar biki ce. Muna roƙonka ka ba barorinka, da ɗanka, Dawuda abin da za ka iya ba mu.’ ” 9 Sa'ad da samarin Dawuda suka zo, suka faɗa wa Nabal dukan abin da Dawuda ya ce musu, sai suka dakata. 10 Nabal ya amsa wa barorin Dawuda, ya ce, “Wane ne Dawuda? Wane ne ɗan Yesse? A kwanakin nan akwai barori da yawa waɗanda suka tayar wa iyayengijinsu. 11 Zan ɗauki abincina, da ruwana, da namana wanda na yanka wa masu yi mini sausaya in ba mutanen da ban san inda suka fito ba?” 12 Barorin Dawuda suka koma suka faɗa wa Dawuda abin da Nabal ya ce. 13 Sai Dawuda ya ce wa mutanensa, “Kowa ya rataya takobinsa.” Ko wannensu kuwa ya rataya takobi. Dawuda kuma ya rataya nasa takobi. Mutum wajen arbaminya suka tafi tare da shi. Mutum metan kuwa suka zauna a wurin kayayyakinsu. 14 Sai ɗaya daga cikin samarin Nabal ya faɗa wa Abigail, wato matar Nabal cewa, “Dawuda ya aiko manzanninsa daga jeji su gai da maigida, amma maigida ya zazzage su. 15 Ga shi, mutanen kuwa sun yi mana kirki, ba mu sha wata wahala ba, ba abin da ya ɓace mana dukan lokacin da muke tare da su a jeji. 16 Sun zama mana ganuwa dare da rana dukan lokacin da muke tare da su a wurin kiwon tumaki. 17 Yanzu sai ki yi tunani, ki san abin da ya kamata ki yi, gama ana niyyar yi wa maigida da dukan gidansa ɓarna. Ga shi, maigida yana da mugun hali, ba zai ji kowa ba!” 18 Sai Abigail ta yi sauri, ta ɗauki malmalar abinci guda metan, da salkar ruwan inabi biyu, da tumaki biyar da aka gyara, da soyayyen hatsi mudu uku, da nonnan 'ya'yan inabi guda ɗari, da kauɗar ɓaure guda metan, ta labta wa jakai. 19 Ta ce wa samarin, “Ku yi gaba, ga ni nan tafe bayanku.” Amma ba ta faɗa wa Nabal, mijinta ba. 20 Tana tafiya a kan jaki, ta kai gindin wani dutse ke nan, sai ga Dawuda da mutanensa tafe. Ta tafi, ta sadu da su. 21 Dawuda ya ce a ransa, “Ashe, a banza ne na yi ta lura da dukan abin da yake na mutumin nan a jeji, har ba abin da yake nasa da ya ɓace. Ga shi, ya rama mini alheri da mugunta. 22 Allah ya buge ni in mutu, idan na bar masa wani mutum da rai kafin gobe da safe.” 23 Da Abigail ta ga Dawuda, sai ta yi sauri ta sauka daga kan jakin, ta durƙusa gabansa har ƙasa. 24 Ta faɗi a ƙafafunsa, ta ce, “Ya shugabana, bari laifin ya zama nawa. Ina roƙonka ka bar baiwarka ta yi magana, ka kuma yarda ka ji maganar baiwarka. 25 Kada maigidana ya kula da Nabal, gama wawa ne, kamar yadda sunansa yake, wato wawa. Ni dai ban ga samarin da ubangijina ya aika ba. 26 Yanzu, ya maigida, na rantse da ran Ubangiji da kuma ranka, ka ga Ubangiji ya hana ka zubar da jini, da ɗaukar wa kanka fansa, sai ka bar maƙiyanka da waɗanda suke nema su cuce ka su zama kamar Nabal. 27 Idan ka yarda ka karɓi kyautan nan da baiwarka ta kawo maka domin a ba samarin da yake tare da kai. 28 Ina roƙonka ka gafarta mini laifina. Ubangiji zai sa ka zama sarki, kai da zuriyarka, kana yin yaƙi na Ubangiji. Ba kuwa za ka aikata wani mugun abu ba a dukan kwanakinka. 29 Idan wani ya tashi tsaye don ya bi sawunka, ya kuma nemi ranka, Ubangiji zai kiyaye ranka, amma rayukan maƙiyanka za a wurga su kamar dutsen majajjawa. 30 Sa'ad da Ubangiji ya cika maka dukan alherin da ya yi maka alkawari, ya kuma naɗa ka Sarkin Isra'ila, 31 ba kuwa za ka sami dalilin baƙin ciki ba, ko damuwar lamiri domin ba ka da alhakin jini, ba ka kuma ɗaukar wa kanka fansa. Sa'ad da Ubangiji ya nuna maka alheri, sai ka tuna da ni, baiwarka.” 32 Sa'an nan Dawuda ya ce wa Abigail, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na Isra'ila, wanda ya aike ki ki tarye ni. 33 Basirarki mai albarka ce, ke kuma mai albarka ce, gama kin hana ni zubar da jini da ɗaukar wa kaina fansa yau. 34 Hakika, Ubangiji Allah na Isra'ila ya hana in yi miki ɓarna. Da ba domin kin yi hanzari, kin zo, kin tarye ni ba, da ba wani mutumin Nabal da zai ragu kafin gobe da safe.” 35 Sai Dawuda ya karɓi abin da ta kawo masa. Ya ce mata, “Ki koma gida kada ki damu. Zan yi abin da kike bukata.” 36 Abigail ta koma wurin Nabal, ta iske shi yana biki irin na sarakuna a gidansa. Ya yi ta nishaɗi, ya bugu sosai, don haka ba ta ce masa kome ba sai da safe. 37 Da safe, sa'ad da ruwan inabi ya sake shi, sai Abigail ta faɗa masa abin da ya faru. Zuciyarsa kuwa ta tsinke gaba ɗaya. 38 Bayan kwana goma sai Ubangiji ya bugi Nabal, ya mutu. 39 Sa'ad da Dawuda ya ji Nabal ya mutu, sai ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya sāka mini a kan irin rainin da Nabal ya yi mini. Ya kuma hana ni aikata mugunta. Ya ɗora wa Nabal muguntarsa a kansa.” Sa'an nan Dawuda ya aika, ya nemi Abigail ta zama matarsa. 40 Da barorin Dawuda suka zo wurin Abigail a Karmel, suka ce mata, “Dawuda ne ya aiko mu wurinki domin mu kai ki wurinsa, ki zama matarsa.” 41 Sai ta rusuna har ƙasa, ta ce, “Ni baranyarsa ce, ina a shirye in wanke ƙafafun barorinsa.” 42 Sai ta yi hanzari ta hau jaki, ta ɗauki kuyanginta, su biyar, ta tafi tare da manzannin Dawuda, ta zama matarsa. 43 Dawuda kuma ya auro Ahinowam Bayezreyeliya, dukansu biyu kuwa suka zama matansa. 44 Amma Saul ya aurar da Mikal, 'yarsa, matar Dawuda, ga Falti ɗan Layish wanda yake a Gallim.

1 Sama’ila 26

Dawuda ya Bar Saul da Rai a Zif

1 Zifawa suka zo wurin Saul a Gibeya suka ce, “Ba ga Dawuda yana ɓuya a kan tudun Hakila wanda yake gaban Yeshimon ba?” 2 Saul kuwa ya tashi ya tafi jejin Zif tare da zaɓaɓɓu dubu uku (3,000 ) na Isra'ila don ya nemi Dawuda. 3 Ya kafa sansaninsa a kan tudun Hakila wanda yake gefen hanya, a gaban Yeshimon. Amma Dawuda ya yi zamansa a jeji. Da ya ga Saul ya bi shi cikin jejin, 4 sai ya aiki magewaya, suka tabbata lalle Saul ya zo. 5 Dawuda kuwa ya tashi ya tafi wurin da Saul ya kafa sansani. Ya kuwa ga inda Saul yake kwance, da kuma Abner ɗan Ner, sarkin yaƙin Saul. Saul ya kwanta a sansanin, sojojin suna kewaye da shi. 6 Dawuda ya ce wa Ahimelek Bahitte, da Abishai, ɗan Zeruya, ɗan'uwan Yowab, “Wa zai tafi tare da ni zuwa sansanin Saul?” Abishai ya ce, “Zan tafi tare da kai.” 7 Sai Dawuda da Abishai, suka tafi sansanin Saul da dare. Suka tarar da Saul yana barci cikin sansani da māshinsa a kafe a ƙasa, wajen kansa. Abner kuwa da sauran sojoji suna kwance kewaye da shi. 8 Sa'an nan Abishai ya ce wa Dawuda, “Yau Ubangiji ya ba da maƙiyinka a hannunka, ka bar ni in nashe shi da māshi sau ɗaya kaɗai, in sha zararsa, in haɗa shi da ƙasa!” 9 Amma Dawuda ya ce wa Abishai, “Kada ka hallaka shi, gama wa zai taɓa wanda Ubangiji ya keɓe, ya rasa yin laifi? 10 Hakika Ubangiji zai buge shi, ko ajalinsa ya auka, ko kuwa ya hallaka a wurin yaƙi. 11 Ubangiji ya sawwaƙa in miƙa hannuna in taɓa wanda Ubangiji ya keɓe. Sai dai ka ɗauki māshin da butar ruwa da suke wajen kansa, mu tafi.” 12 Da haka Dawuda ya ɗauki māshi da butar ruwa da suke wajen kan Saul, suka tafi. Ba wanda ya gansu, ba wanda ya sani, ba kuwa wanda ya farka, gama dukansu suna barci, domin Ubangiji ne ya sa barci mai nauyi ya share su. 13 Sa'an nan Dawuda ya haye zuwa wancan gefe, ya tsaya can nesa bisa dutsen, da ɗan nisa tsakaninsu. 14 Sai Dawuda ya kira sojojin sansanin, da kuma Abner ɗan Ner, ya ce, “Ba za ka amsa mini ba, Abner?” Sai Abner ya ce, “Wa yake kiran sarki?” 15 Dawuda ya ce wa Abner, “Kai ba namiji ba ne? Wa yake kama da kai cikin Isra'ila? Me ya sa ba ka lura da mai girma, sarki ba? Wani mutum ya zo don ya hallaka mai girma sarki. 16 Abin da ka yi ba shi da kyau. Ka isa a kashe ka, da yake ba ka lura da mai girma ba, wanda Ubangiji ya keɓe. Ka duba, ina māshin sarki da butar ruwa da suke wajen kansa suke?” 17 Saul ya gane da muryar Dawuda, ya ce, “Muryarka ke nan ɗana, Dawuda?” Dawuda ya amsa, “I, muryata ce, ya mai girma sarki.” 18 Sai ya ƙara da cewa, “Me ya sa mai girma yake bin sawun baransa? Me na yi? Mene ne laifina? 19 Bari sarki ya kasa kunne ga maganar baransa. Idan Ubangiji ne ya kuta ka ka yi gāba da ni, to, bari ya karɓi hadaya, amma idan mutane ne, to, bari su zama la'anannu, gama sun kore ni don kada in sami rabo cikin gādon Ubangiji, suna cewa, ‘Tafi ka bauta wa alloli.’ 20 Kada ka kashe ni a baƙuwar ƙasa nesa da Ubangiji. Don me Sarkin Isra'ila yake so ya kashe ni, ni da nake kamar tunkuyau? Don me zai farauce ni kamar tsuntsun jeji?” 21 Sa'an nan Saul ya ce, “Na yi laifi, ka komo, ɗana Dawuda, ba zan yi maka kome ba, gama raina ya zama da daraja a gare ka kyau. Na yi aikin wauta, na yi laifi da yawa.” 22 Sai Dawuda ya ce, “Ga māshinka! Ka aiko wani saurayi ya zo ya karɓa. 23 Ubangiji dai zai sāka wa kowa bisa ga adalcinsa da amincinsa. Ubangiji ya bashe ka a hannuna yau, amma na ƙi in kashe wanda Ubangiji ya keɓe. 24 Kamar yadda ranka ya zama da daraja a gare ni yau, bari raina kuma ya zama da daraja a gaban Ubangiji, ya cece ni daga dukan wahala.” 25 Sai Saul ya ce wa Dawuda, “Ubangiji ya sa maka albarka, ɗana Dawuda, za ka yi manyan abubuwa, ka kuwa yi nasara!” Dawuda dai ya yi tafiyarsa, Saul kuma ya koma gidansa.

1 Sama’ila 27

Zaman Dawuda tare da Filistiyawa

1 Dawuda ya yi tunani a ransa, ya ce, “Wata rana Saul zai kashi ni, don haka ba abin da ya fi mini, sai in tsere zuwa ƙasar Filistiyawa. Sa'an nan Saul zai fid da zuciya ga nemana a ƙasar Isra'ila. Zan kuwa tsira daga hannunsa.” 2 Dawuda ya tashi tare da mutum ɗari shida da suke tare da shi zuwa wurin Akish, ɗan Mawok, Sarkin Gat. 3 Dawuda da mutanensa da iyalansu suka zauna tare da Akish a Gat. Dawuda yana tare da matansa biyu, Ahinowam Bayezreyeliya, da Abigail Bakarmeliya, wadda Nabal mijinta ya mutu. 4 Da Saul ya ga Dawuda ya tsere zuwa Gat, bai ƙara fita nemansa ba. 5 Dawuda ya ce wa Akish, “Idan na sami tagomashi a wurinka, ka ba ni wurin zama daga cikin garuruwanka na karkara domin in zauna a can. Gama me zai sa baranka ya zauna tare da kai cikin birni sarauta?” 6 Sai Akish ya ba shi Ziklag a wannan rana, saboda haka Ziklag ta zama ta sarakunan Yahuza har wa yau. 7 Dawuda ya yi shekara guda da wata huɗu a ƙasar Filistiyawa. 8 Dawuda yakan fita da mutanensa su kai wa Geshurawa, da Girziyawa, da Amalekawa hari. Waɗannan su ne mazaunan ƙasar a dā, tun daga Shur har zuwa ƙasar Masar. 9 Dawuda yakan fāɗa wa ƙasar, ya hallaka ta, ba zai bar mace ko namiji da rai ba. Ya kuma kwashe tumaki, da shanu, da jakai, da raƙuma, da tufafi, ya komo zuwa wurin Akish. 10 Idan Akish ya tambayi Dawuda, “A ina ka kai hari yau?” Sai ya ce, “Na kai hari a Negeb ta Yahuza, ko Negeb ta Yerameyel, ko Negeb ta Ƙan'aniyawa.” 11 Dawuda bai bar mace ko namiji da rai ba, wato da zai kawo labari, a Gat, domin yana gudun kada su faɗi abin da yake yi, su ce, “Ga abin da Dawuda ya yi.” Abin da Dawuda ya yi ta yi ke nan a lokacin da yake zaune a ƙasar Filistiyawa. 12 Akish kuwa ya amince da Dawuda, yana cewa, “Ya mai da kansa abin ƙi ga mutanensa Isra'ilawa, zai zama barana muddin ransa.”

1 Sama’ila 28

1 A kwanakin nan Filistiyawa suka tattara sojojinsu don su yi yaƙi da Isra'ilawa. Akish kuwa ya ce wa Dawuda, “Sai ka sani fa, kai da mutanenka za ku tafi tare da ni da sojojina.” 2 Sai Dawuda ya ce, “Za ka ga abin da baranka zai yi.” Akish ya ce wa Dawuda, “Da kyau, zan sa ka cikin zaunannun jarumawan da suke kāre ni.”

Saul ya Tafi wurin Mai Duba

3 Sama'ila ya riga ya rasu, dukan Isra'ilawa kuwa suka yi makoki dominsa, suka binne shi a garinsu, wato Rama. Saul kuma ya riga ya kori masu duba da masu maita daga ƙasar. 4 Filistiyawa suka kafa sansaninsu a Shunem. Saul ya tattara Isra'ilawa, su ma suka kafa sansaninsu a Gibowa. 5 Da Saul ya ga rundunar yaƙin Filistiyawa, sai ya tsorata, ya yi rawar jiki ƙwarai. 6 Saul kuwa ya yi tambaya ga Ubangiji, Ubangiji bai amsa masa ba, ko ta mafarkai, ko ta Urim, ko ta annabawa. 7 Sai ya ce wa barorinsa, “Ku nemo mini wata mace mai duba domin in tafi wurinta in yi tambaya.” Barorinsa suka ce masa, “Ai, akwai wata mai duba a Endor.” 8 Sai Saul ya ɓad da kama, ya sa waɗansu tufafi. Shi da waɗansu mutum biyu suka tafi wurin matar da dare. Ya ce mata, “Ina roƙonki ki duba mini ta hanyar sihiri. Ki hawar mini da duk wanda zan faɗa miki.” 9 Matar ta ce masa, “Hakika ka san abin da sarki Saul ya yi, yadda ya karkashe masu duba da masu maita a ƙasar. Me ya sa kake ƙoƙarin kafa mini tarko, don ka sa a kashe ni?” 10 Saul ya rantse mata da Ubangiji, ya ce, “Hakika, ba za a hukunta ki saboda wannan ba.” 11 Sai matar ta ce, “Wa kake so in hawar maka?” Ya ce, “Ki hawar mini da Sama'ila.” 12 Da matar ta ga Sama'ila, sai ta fasa ƙara, ta ce wa Saul, “Don me ka ruɗe ni, ashe, kai ne sarki Saul?” 13 Sarki kuwa ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, me kike gani?” Ta ce masa, “Na ga wani allah yana fitowa daga ƙasa.” 14 Ya ce mata, “Yaya kamanninsa yake?” Ta ce, “Wani tsoho ne yake hawowa, yana naɗe da alkyabba.” Saul ya gane Sama'ila ne, sai ya sunkuyar da kai, ya durƙusa har ƙasa da bangirma. 15 Sai Sama'ila ya ce wa Saul, “Don me ka dame ni, ka hawar da ni?” Saul ya ce, “Ina cikin babbar wahala, gama Filistiyawa suna yaƙi da ni, Allah kuma ya rabu da ni, ya ƙi amsa mini ko ta wurin annabawa ko ta mafarkai, saboda haka na kira ka, ka faɗa mini abin da zan yi.” 16 Sai Sama'ila ya ce masa, “Don me za ka tambaye ni, tun da yake Ubangiji ya rabu da kai, ya zama magabcinka? 17 Ai, abin da Ubangiji ya faɗa mini a kanka, shi ne ya cika, gama Ubangiji ya fizge mulki daga hannunka, ya ba maƙwabcinka Dawuda. 18 Domin ba ka bi maganar Ubangiji ba, ba ka zartar da hukuncinsa mai zafi a kan Amalekawa ba, saboda haka Ubangiji ya yi maka haka yau. 19 Banda haka kuma Ubangiji zai ba da Isra'ilawa tare da kai a hannun Filistiyawa. Gobe, da kai da 'ya'yanka maza za ku kasance tare da ni. Ubangiji zai ba da rundunar yaƙin Isra'ila a hannun Filistiyawa.” 20 Da jin maganar Sama'ila sai Saul ya faɗi ƙasa warwar. Tsoro ya kama shi ƙwarai. Ba shi kuma da ƙarfi domin bai ci kome dukan yini da dukan dare ba. 21 Sai matar ta zo wurin Saul, da ta ga ya tsorata, sai ta ce masa, “Baiwarka ta yi kasai da ranta, ta kuwa kasa kunne gare ka. 22 To, kai ma ka kasa kunne ga baiwarka. Bari in ba ka abinci, ka ci don ka sami ƙarfin tafiya.” 23 Sai ya ƙi, ya ce, “Ba zan ci abinci ba.” Sai da barorinsa da matar suka roƙe shi, sa'an nan ya ji maganarsu, ya tashi daga ƙasa, ya zauna a bakin gado. 24 Matar kuwa ta yi hanzari ta yanka turkakken maraƙinta, ta ɗauki gari ta kwaɓa, ta toya abinci marar yisti da shi. 25 Sa'an nan ta kawo wa Saul da barorinsa, suka ci, sa'an nan suka tashi suka tafi da daren nan.

1 Sama’ila 29

Filistiyawa ba su Amince da Dawuda Ba

1 Filistiyawa suka tattara rundunar yaƙinsu a Afek. Isra'ilawa kuma suka kafa sansaninsu kusa da maɓuɓɓugar da take a Yezreyel. 2 Sa'ad da sarakunan Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari da na mutum dubu dubu, Dawuda kuma da mutanensa suna biye a baya tare da Akish. 3 Shugabannin sojojin Filistiyawa suka ce, “Me waɗannan Ibraniyawa suke yi a nan?” Akish kuwa ya ce wa shugabannin sojojin Filistiyawa, “Ai, wannan Dawuda ne baran Saul, Sarkin Isra'ila, wanda yake tare da ni tun da daɗewa. Tun lokacin da ya zo wurina ban taɓa samunsa da wani laifi ba.” 4 Amma shugabannin sojojin Filistiyawa suka husata da shi, suka ce masa, “Ka sa mutumin nan ya koma wurin da ka zaunar da shi. Ba zai tafi tare da mu zuwa wurin yaƙin ba, don kada ya juya mana gindin baka. Ai, da kawunan mutanenmu ne zai yi sulhu da ubangijinsa. 5 Ko ba Dawuda ɗin nan ne ba, da suka raira masa waƙa cikin raye-rayensu, suna cewa, ‘Saul ya kashe dubbai, Dawuda kuwa ya kashe dubun dubbai?’ ” 6 Akish kuwa ya kira Dawuda, ya ce masa, “Na rantse da ran Ubangiji, kai amintacce ne a ganina, daidai ne kuma ka tafi yaƙi tare da ni, gama ban same ka da wani laifi ba tun daga ranar zuwanka wurina har yau, duk da haka sarakunan ba su amince da kai ba. 7 To, sai ka koma ka isa lafiya, don kada ka tā da hankalin sarakunan Filistiyawa.” 8 Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Wane laifi ka samu a wurin baranka tun daga ranar da na shiga hidimarka har zuwa yau, da ba zan tafi in yi yaƙi da abokan gāban ubangijina sarki ba?” 9 Akish ya amsa wa Dawuda, ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala'ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’ 10 Ka tashi da sassafe kai da barorin ubangijinka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.” 11 Dawuda kuwa ya tashi da sassafe ya kama hanya tare da mutanensa zuwa ƙasar Filistiyawa, amma Filistiyawa suka haura zuwa Yezreyel.

1 Sama’ila 30

Dawuda ya Ci Amalekawa

1 Sa'ad da Dawuda da mutanensa suka koma Ziklag a rana ta uku, sai suka tarar Amalekawa sun riga sun kawo wa Negeb da Ziklag hari. Suka cinye Ziklag, suka ƙone ta. 2 Suka kwashe mata da dukan waɗanda suke ciki manya da ƙanana, suka tafi da su. Ba su kashe kowa ba, amma suka kwashe su, suka tafi. 3 Da Dawuda da mutanensa suka ga an ƙone garin, an kuma kwashe matansu, da 'ya'yansu mata da maza ganima, 4 sai suka yi ta kuka da ƙarfi, har ƙarfinsu ya ƙare. 5 An kwashe matan Dawuda biyu ganima, wato Ahinowam Bayezreyeliya da Abigail Bakarmeliya, matar Nabal wanda ya mutu. 6 Dawuda kuwa ya damu ƙwarai gama mutane suna niyyar su jajjefe shi da duwatsu, domin ransu ya ɓace saboda 'ya'yansu mata da maza. Amma Ubangiji Allahnsa ya ƙarfafa shi. 7 Sai ya ce wa Abiyata firist, ɗan Ahimelek, ya kawo masa falmaran. Abiyata kuwa ya kawo masa. 8 Sai Dawuda ya yi tambaya ga Ubangiji ya ce, “In bi sawun 'yan harin nan? Zan ci musu?” Ya ce masa, “Bi su, gama za ka ci musu, ka ƙwato abin da suka kwashe.” Dawuda da mutanensa ɗari shida suka tashi, suka kama hanya, suka kai rafin Besor inda suka bar mutum metan waɗanda suka kāsa. Amma Dawuda da mutum ɗari huɗu suka ci gaba da bin mutanen. 11 Mutanen Dawuda suka sami wani Bamasare a karkara, suka kawo shi wurin Dawuda. Suka ba shi abinci da ruwa, ya ci ya sha. 12 Suka kuma ba shi kauɗar ɓaure da nonnan inabi biyu. Da ya ci sai ya wartsake, gama ya yi yini uku da dare uku ba ci ba sha. 13 Dawuda kuwa ya tambaye shi, “Wane ne ubangidanka? Daga ina ka fito?” Ya amsa, ya ce, “Ni saurayi ne, Bamasare, baran wani Ba'amaleke. Kwana uku ke nan da ubangidana ya tafi ya bar ni a baya saboda ba ni da lafiya. 14 Mun kai hari a Negeb ta Keretiyawa ta Yahuza, da Negeb ta Kalibu, muka kuma ƙone Ziklag.” 15 Dawuda ya ce masa, “Za ka yarda ka kai ni wurin maharan nan?” Sai ya ce wa Dawuda, “Idan ka rantse mini da Allah, ba za ka kashe ni ba, ba kuwa za ka mai da ni wurin ubangidana ba, sai in kai ka inda maharan nan suke.” 16 Ya kai Dawuda a wurinsu, sai ga su nan a baje ko'ina a ƙasar, suna ci, suna sha, suna rawa, saboda ganima mai yawa da suka kwashe daga ƙasar Filistiyawa da ƙasar Yahuza. 17 Sai Dawuda ya yi ta karkashe su tun faɗuwar rana har zuwa kashegari da yamma. Ba wanda ya tsira daga cikinsu sai samari ɗari huɗu waɗanda suka tsere a kan raƙuma. 18 Dawuda ya ƙwato dukan abin da Amalekawa suka kwashe, har da matansa biyu. 19 Ba abin da ya ɓace, ƙanƙane ko babba, ko cikin 'ya'ya mata da maza, ko kuwa wani abu daga cikin ganimar, duk Dawuda ya komar da su. 20 Ya kuma ƙwato garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu. Mutanensa suka koro shanun, suka yi gaba, suka ce, “Wannan shi ne ganimar Dawuda.” 21 Da Dawuda ya zo wurin mutum ɗari biyu ɗin nan waɗanda suka tafke, suka kāsa binsa, waɗanda aka bar su a rafin Besor, sai suka tafi su taryi Dawuda da mutanensa da suka tafi tare da shi. Sa'ad da Dawuda ya zo kusa da su ya gaishe su. 22 Sai dukan mugaye da marasa kirki daga cikin mutanen da suka tafi tare da Dawuda suka ce, “Tun da yake ba su tafi tare da mu ba, ba za mu ba su kome daga cikin ganimar da muka ƙwato ba, sai dai kowane mutum ya ɗauki matarsa da 'ya'yansa ya tafi.” 23 Amma Dawuda ya ce, “'Yan'uwana, ba za ku yi haka da abin da Ubangiji ya ba mu ba. Ubangiji ya kiyaye mu, ya kuma ba da maharan da suka washe mu a hannunmu. 24 Wa zai goyi bayanku a kan wannan al'amari? Wanda ya tafi wurin yaƙi da wanda ya zauna wurin kaya rabonsu zai zama daidai da juna.” 25 Tun daga wannan rana zuwa gaba, wannan ya zama doka da ka'ida ga Isra'ila. 26 Sa'ad da Dawuda ya komo Ziklag, sai ya aika wa abokansa, dattawan Yahuza, da rabo daga cikin ganimar, ya ce, “Ga kyauta dominku, daga cikin ganimar maƙiyan Ubangiji.” 27 Kyautar domin waɗanda suke a Betel, da Ramot ta Negeb, da Yattir, 28 da Arower, da Sifmot, da Eshtemowa, 29 da Rakal, da garuruwa na Yerameyeliyawa, da garuruwa na Ƙan'aniyawa, 30 da Horma, da Ashan, da Atak, 31 da Hebron, da dukan wuraren da Dawuda da mutanensa suka taɓa tafiya.

1 Sama’ila 31

Rasuwar Saul da 'Ya'yansa Maza

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa. Isra'ilawa kuma suka yi gudun Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa. 2 Filistiyawa suka ci Saul da 'ya'yansa maza. Suka kashe Jonatan, da Abinadab, da Malkishuwa, 'ya'yan Saul. 3 Yaƙin ya matsa wa Saul. Maharba suka harbe shi, suka yi masa mummunan rauni. 4 Sai ya ce wa mai ɗaukar masa makamai, “Ka zare takobinka ka sha zarata da shi domin kada marasa kaciyan nan su zo su sha zarata, su yi mini ba'a.” Amma mai ɗaukar masa makamai bai yarda ba, domin ya ji tsoro da yawa. Sai Saul ya zare takobinsa, ya faɗa a kansa. 5 Da mai ɗaukar masa makamai ya ga Saul ya rasu, shi ma ya fāɗa a kan nasa takobi ya mutu tare da Saul. 6 Haka Saul, da 'ya'yansa maza guda uku, da mai ɗaukar masa makamai, da dukan mutanen da suke tare da shi suka mutu a rana ɗaya. 7 Sa'ad da Isra'ilawa da suke a wancan hayi na kwarin da waɗanda suke a wancan hayin Urdun suka ga mayaƙan Isra'ila sun gudu, Saul kuma da 'ya'yansa sun mutu, sai suka bar garuruwansu, suka gudu. Filistiyawa kuwa suka zo suka zauna a cikinsu. 8 Da Filistiyawa suka zo kashegari don su washe kayan kisassun, sai suka tarar da gawar Saul da gawawwakin 'ya'yansa uku a kan Dutsen Gilbowa. 9 Suka yanke kansa, suka tuɓe makamansa. Suka aika manzannin a ƙasar Filistiyawa da take kusa don su kai wannan albishir zuwa ga haikalin gumakansu, da mutanensu. 10 Suka ajiye makaman Saul cikin haikalin gumakan nan Ashtarot. Suka ɗaure gawarsa a kan garun Bet-sheyan. 11 Da mazaunan Yabesh-gileyad suka ji abin da Filistiyawa suka yi wa Saul, 12 sai dukan jarumawa suka tashi, suka yi tafiya dukan dare. Suka ɗauko gawar Saul da gawawwakin 'ya'yansa daga kan garun Bet-sheyan. Da suka zo Yabesh sai suka ƙone su a can. 13 Suka binne ƙasusuwansu a gindin itacen tsamiya a Yabesh, sa'an nan suka yi azumi kwana bakwai.

2 Sama’ila 1

Dawuda ya ji Labarin Rasuwar Saul da Jonatan

1 Bayan rasuwar Saul, sa'ad da Dawuda ya komo daga karkashe Amalekawa, ya yi kwana biyu a Ziklag. 2 Kashegari sai ga wani mutum ya zo daga sansanin Saul, da tufafinsa a yayyage, da ƙura kuma a kansa. Da ya zo wurin Dawuda sai ya fāɗi ƙasa, ya yi gaisuwa. 3 Sai Dawuda ya tambaye shi, ya ce, “Daga ina ka zo?” Ya ce, “Na tsere ne daga sansanin Isra'ilawa.” 4 Dawuda ya ce masa, “Faɗa mini abin da ya faru.” Sai ya ce, “Mutane sun gudu daga bakin dāga, an kuma kashe galibin mutanenmu. Saul da ɗansa Jonatan kuma sun mutu.” 5 Dawuda ya ce wa mutumin, “Ta yaya ka sani Saul da ɗansa, Jonatan, sun mutu?” 6 Mutumin kuwa ya amsa ya ce, “Ya zama fa ina kan dutsen Gilbowa, sai ga Saul ya jingina a māshinsa. Karusai da mahayan dawakan abokan gāba sun rutsa shi. 7 Da ya waiga, ya gan ni, sai ya kira ni, ni kuwa na amsa, na ce, ‘Ga ni.’ 8 Ya ce mini, ‘Wane ne kai?’ Na ce masa, ‘Ni Ba'amaleke ne.’ 9 Sai ya ce mini, ‘Zo ka kashe ni gama ina cikin azaba, amma raina bai fita ba.’ 10 Sai na tafi na kashe shi domin na tabbata ba zai yi rai ba bayan ya fāɗi. Na kuma cire kambin da yake kansa da ƙarau da yake a dantsensa. Ga su, na kawo wa ubangijina.” 11 Sai Dawuda ya yayyage tufafinsa. Dukan mutanen da suke tare da shi kuma suka yayyage nasu. 12 Suka yi makoki, da kuka, da azumi har maraice saboda Saul, da Jonatan ɗansa, da mutanen Ubangiji, da gidan Isra'ila domin an Karkashe su a yaƙi. 13 Dawuda ya ce wa mutumin nan da ya kawo labarin, “Daga ina ka zo?” Sai ya ce masa, “Ai, ni ɗan wani baƙo ne, Ba'amaleke.” 14 Dawuda ya ce, “Me ya sa ba ka ji tsoro ka miƙa hannunka, ka hallaka wanda Ubangiji ya keɓe ba?” 15 Sai Dawuda ya kira ɗaya daga cikin samarin, ya ce masa, “Ka kashe shi.” Ya dai buge shi, ya mutu. 16 Dawuda kuwa ya ce, “Alhakin jininka yana bisa kanka tun da yake da bakinka ka ce, ‘Ni ne na kashe wanda Ubangiji ya keɓe.’ ”

Dawuda ya yi Makoki domin Saul da Jonatan

17 Sai Dawuda ya raira waƙar makoki domin Saul da Jonatan, ɗansa. 18 Ya umarta a koya wa mutanen Yahuza wannan waƙa. (An rubuta ta a littafin Yashar.) 19 “An kashe darajarki, ya Isra'ila, a kan tuddanki! Jarumawan sojojinmu sun fāɗi! 20 Kada a ba da labarin a Gat, Ko a titin Ashkelon. Kada ku sa matan Filistiyawa su yi murna, Kada ku sa 'yan matan arna su yi farin ciki. 21 “Kada ruwan sama ko raɓa su zubo kan tuddan Gilbowa. Da ma gonakinta su zama marasa ba da amfani. Gama a can ne aka zube garkuwoyin jarumawa a wulakance, Tsatsa ta rufe garkuwar Saul. 22 Bakan Jonatan mai kisa ne, Takobin Saul ba shi da jinƙai, Yana kashe masu iko, yana kuma kashe abokan gāba. 23 “Saul da Jonatan ƙaunatattu ne, suna da bansha'awa, A raye suna tare, haka kuma a mace suna tare. Sun fi gaggafa sauri, Sun fi zaki ƙarfi. 24 “Ku 'yan matan Isra'ila, ku yi makoki domin Saul! Ya suturta ku da mulufi mai ƙayatarwa, Ya yi muku adon lu'ulu'u da zinariya. 25 “Jarumawa sun fāɗi, An kashe su a bakin dāga. Jonatan na kwance matacce a tuddai. 26 “Na damu ƙwarai saboda kai, ɗan'uwana Jonatan, Ƙaunatacce kake a gare ni! Ƙaunarka a gare ni abar al'ajabi ce, Ta fi ƙaunar mace. 27 “Jarumawa sun fāɗi, Makamansu ba su da sauran amfani.”

2 Sama’ila 2

An Naɗa Dawuda Sarkin Yahuza

1 Bayan wannan sai Dawuda ya roƙi Ubangiji, ya ce, “Ko in haura in mallaki ɗaya daga cikin garuruwan Yahuza?” Ubangiji ya ce masa, “Ka haura.” Dawuda kuma ya ce, “Zuwa wane gari zan haura?” Sai Ubangiji ya ce masa, “Zuwa Hebron.” 2 Dawuda kuwa ya haura zuwa can tare da matansa biyu, wato Ahinowam Bayezreyeliya, da Abigail matar marigayi Nabal Bakarmele. 3 Ya kuma tafi tare da mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa. Suka zauna a garuruwan Hebron. 4 Mutanen Yahuza kuwa suka zo, suka naɗa Dawuda da man naɗawa domin ya zama Sarkin Yahuza. Da Dawuda ya ji labari mutanen Yabesh-gileyad, sun binne Saul, 5 sai ya aiki manzanni da saƙo wurin mutanen Yabesh-gileyad ya ce, “Ubangiji ya sa muku albarka da yake kun yi wa Saul, ubangijinku, wannan alheri, har kuka binne shi. 6 Ubangiji ya nuna muku ƙaunarsa da amincinsa. Ni kuwa zan yi muku alheri saboda abin da kuka yi. 7 Yanzu sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Saul shugabanku ya rasu, mutanen Yahuza kuwa sun naɗa ni sarkinsu.”

Dawuda ya Yaƙi Gidan Saul

8 Abner kuwa ɗan Ner, sarkin yaƙin Saul, ya tsere da Ish-boshet, ɗan Saul, zuwa Mahanayim. 9 Ya naɗa shi Sarkin Gileyad, da Ashiru, da Yezreyel, da Ifraimu, da ƙasar Biliyaminu, da dukan Isra'ila. 10 Ish-boshet, ɗan Saul, yana da shekara arba'in sa'ad da ya ci sarautar Isra'ila, ya yi shekara biyu yana sarauta. Amma mutanen Yahuza suka bi Dawuda. 11 Dawuda ya yi shekara bakwai da rabi yana sarautar Yahuza a Hebron. 12 Abner, ɗan Ner, tare da fādawan Ish-boshet, ɗan Saul, suka tashi daga Mahanayim zuwa Gibeyon. 13 Sai kuma Yowab, ɗan Zeruya, tare da fādawan Dawuda suka fita suka tafi tarye su a tafkin Gibeyon. Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe na tafkin. 14 Sai Abner ya ce wa Yowab, “Bari samarin su tashi su yi kokawa a gabanmu.” Yowab kuwa ya ce, “To, sai su tashi.” 15 Sai suka tashi, suka haye. Mutum goma sha biyu a madadin mutanen Biliyaminu da Ish-boshet, ɗan Saul, mutum goma sha biyu kuma a madadin mutanen Dawuda. 16 Kowa ya kama abokin kokawarsa a kā, suka soki juna a kwiɓi da takuba. Suka faɗi tare. Aka sa wa wurin suna Helkat-hazzurim, wato filin takuba, wurin yana nan a Gibeyon. 17 Yaƙin kuwa ya yi zafi a ranar. Mutanen Dawuda suka ci Abner da mutanen Isra'ila. 18 'Ya'yan Zeruya, maza, su uku suna nan, wato Yowab, da Abishai, da Asahel. Asahel maguji ne kamar barewa. 19 Sai ya tasar wa bin Abner haiƙan, bai kauce ba. 20 Da Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne Asahel?” Ya amsa, “Ni ne.” 21 Abner ya ce masa, “Ka daina haye mini, ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka kama shi, ka karɓe masa makaminsa.” Amma Asahel bai daina binsa ba. 22 Abner kuma ya sāke ce masa, “Ka daina bina, kada ka sa in kashe ka fa! Idan na kashe ka kuwa, yaya zan yi ido biyu da dan'uwanka, Yowab?” 23 Amma Asahel bai daina binsa ba, Abner dai ya nashe shi da gindin māshi a ciki, sai mashin ya fita ta bayansa. Ya fāɗi ya mutu nan take. Duk wanda ya zo inda Asahel ya fāɗi ya mutu, sai ya tsaya cik. 24 Amma Yowab da Abishai suka bi Abner, har faɗuwar rana, suka isa tudun Amma, wanda yake gaban Gaiya, a hanya zuwa jejin Gibeyon. 25 Mutanen Biliyaminu kuma suka haɗa kansu, suka goyi bayan Abner, suka zama ƙungiya guda, suka tsaya kan tudu. 26 Abner kuwa ya kira Yowab, ya ce, “Har abada ne takobi zai hallakar? Ba ka sani ba ƙarshen zai yi ɗaci? Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina runtumar 'yan'uwansu?” 27 Yowab ya ce, “Na rantse da Ubangiji, hakika da ba domin ka yi magana ba, da mutanena ba za su daina runtumarka ba har gobe da safe.” 28 Sa'an nan Yowab ya busa ƙaho, dukan mutanensa kuwa suka tsaya, ba su ƙara runtumar mutanen Isra'ila ba, ba wanda kuma ya yaƙi wani. 29 Abner da mutanensa suka bi dare farai, suka ratsa Araba, suka haye Urdun. Suka yi ta tafiya dukan safiyan nan, suka shige Bitron, har suka kai Mahanayim. 30 Da Yowab ya komo daga runtumar Abner, ya tattara mutanensa duka, sai ya ga an rasa mutum goma sha tara daga cikin mutanen Dawuda, banda Asahel. 31 Amma barorin Dawuda suka kashe mutanen Biliyaminu mutum ɗari uku da sittin daga cikin waɗanda suke tare da Abner. 32 Suka ɗauki Asahel, suka tafi suka binne shi a kabarin mahaifinsa a Baitalami. Yowab kuwa da mutanensa suka bi dare farai, gari ya waye musu a Hebron.

2 Sama’ila 3

1 Gidan Saul da gidan Dawuda suka daɗe suna yaƙi da juna. Ƙarfin gidan Dawuda ya yi ta ƙaruwa, amma na gidan Saul ya yi ta raguwa.

'Ya'ya Maza da aka Haifa wa Dawuda a Hebron

2 'Ya'ya maza da aka haifa wa Dawuda a Hebron ke nan, Ahinowam Bayezreyeliya ta haifa masa ɗan farinsa, Amnon. 3 Abigail, matar marigayi, Nabal Bakarmele, ta haifa masa ɗansa na biyu, Kileyab. Ma'aka 'yar Talmai, Sarkin Geshur, ta haifa masa ɗansa na uku, Absalom. 4 Haggit ta haifa masa ɗansa na huɗu, Adoniya. Abital ta haifa masa ɗansa na biyar, Shefatiya. 5 Matarsa Egla ta haifa masa ɗansa na shida, Itireyam. Dukan waɗannan a Hebron ne aka haife su.

Abner ya Bi Dawuda

6 Abner ya ƙasaita sosai a gidan Saul a lokacin da ake yaƙi tsakanin jarumawan Saul da na Dawuda. 7 Saul yana da ƙwarƙwara mai suna Rizfa, 'yar Aiya. Sai Ish-boshet ya ce wa Abner, “Me ya sa ka kwana da ƙwarƙwarar tsohona?” 8 Abner ya husata saboda wannan magana, ya ce, “Kana zato ni maci amanar ƙasa ne? Kana tsammani ina wa ƙasar Yahuza aiki ne? Tun da farko ina ta nuna alheri ga gidan Saul, tsohonka, da 'yan'uwansa, da abokansa, ban kuwa ba da ka a hannun Dawuda ba. Amma ga shi, yau ka zarge ni da laifin kwartanci game da wannan mata. 9 Allah ya la'anta ni, idan ban yi wa Dawuda abin da Ubangiji ya rantse masa ba, 10 wato in mayar wa Dawuda da sarautar gidan Saul. In kafa kursiyin Dawuda a kan Isra'ila da kan Yahuza tun daga Dan har zuwa Biyer-sheba.” 11 Ish-boshet kuwa bai ce wa Abner uffan ba, don yana jin tsoronsa. 12 Sai Abner ya aiki manzanni zuwa wurin Dawuda a Hebron, ya ce, “Ƙasar ta wane ne? Ka yi mini alkawari, ni kuwa zan goyi bayanka, in sa dukkan Isra'ilawa su bi ka.” 13 Dawuda ya ce, “Da kyau, zan yi maka alkawari a kan wannan sharaɗi, ba za ka ga fuskata ba sai ka kawo mini matata, Mikal, 'yar Saul, sa'ad da za ka zo wurina.” 14 Sa'an nan Dawuda ya aiki manzanni zuwa wurin Ish-boshet, ɗan Saul, ya ce, “Ka ba ni matata, Mikal, wadda na biya sadakinta da loɓa ɗari ta Filistiyawa.” 15 Sai Ish-boshet ya aika aka ƙwato Mikal daga wurin mijinta, Falti, ɗan Layish. 16 Mijinta ya bi ta yana ta kuka har zuwa Bahurim. Sai Abner ya ce masa ya koma, ya kuwa koma. 17 Abner ya shawarci dattawan Isra'ila, ya ce, “Dā ma can kuna so Dawuda ya sarauce ku. 18 To, yanzu sai ku yarda ya sarauce ku, gama Ubangiji ya yi wa Dawuda alkawari ya ce, ‘Ta hannun bawana, Dawuda, zan ceci jama'ar Isra'ila daga hannun Filistiyawa, da na dukan abokan gābansu.’ ” 19 Abner kuma ya yi magana da mutanen Biliyaminu, sa'an nan ya tafi ya faɗa wa Dawuda a Hebron abin da dukan Isra'ilawa da dukan kabilar Biliyaminu suka ga ya yi kyau, su yi. 20 Abner tare da mutum ashirin suka zo wurin Dawuda a Hebron, Dawuda kuwa ya yi musu liyafa. 21 Sai Abner ya ce wa Dawuda, “Zan tashi in tafi in tattara wa ubangijina sarki dukan Isra'ilawa, domin su yi alkawari da kai, kai kuma ka sarauce su yadda kake so.” Dawuda kuwa ya sallami Abner, ya tafi lafiya.

An Kashe Abner

22 Sai ga barorin Dawuda da Yowab sun komo daga hari. Sun kawo ganima mai yawa. Abner kuwa ya riga ya tafi, gama Dawuda ya riga ya sallame shi, ya tafi lafiya. 23 Da Yowab da sojojin da suke tare da shi suka iso, sai aka faɗa masa cewa, “Abner ɗan Ner ya zo wurin sarki, sarki kuwa ya bar shi ya tafi lafiya.” 24 Sai Yowab ya tafi wurin sarki ya ce, “Me ke nan ka yi? Abner ya zo wurinka, me ya sa ka bar shi ya tafi lafiya? 25 Ka sani Abner ɗan Ner ya zo ya ruɗe ka ne, ya san fitarka da shigarka, ya kuma san dukan abin da kake yi.” 26 Da Yowab ya fita daga wurin Dawuda, sai ya aiki manzanni su bi bayan Abner. Suka komo da shi a rijiyar Sira, amma Dawuda bai sani ba. 27 Sa'ad da Abner ya komo Hebron, sai Yowab ya raɓa da shi wajen ƙofar garin kamar zai gana da shi, sai ya soke shi a ruwan ciki, ya fāɗi ya mutu, saboda alhakin jinin ɗan'uwansa, Asahel. 28 Daga baya sa'ad da Dawuda ya ji, sai ya ce, “Ni da mulkina baratattu ne a gaban Ubangiji daga alhakin jinin Abner ɗan Ner har abada. 29 Allah ya sa alhakin jinin ya faɗa kan Yowab da dukan gidan ubansa. Ya sa kada a rasa mai ɗiga, ko kuturu, ko wanda yake dogara sanda, ko wanda aka kashe da takobi, ko wanda ba shi da abinci, a gidan Yowab.” 30 Ta haka Yowab da ɗan'uwansa Abishai suka kashe Abner saboda ya kashe ƙanensu, Asahel, a wurin yaƙi a Gibeyon. 31 Dawuda kuwa ya ce wa Yowab da dukan mutanen da suke tare da shi, “Ku kyakketa tufafinku, ku sa tsummoki, ku yi makoki domin Abner.” Sarki Dawuda kuwa ya bi bayan makara. 32 Suka binne Abner a Hebron. Sarki ya ta da murya ya yi kuka a kabarin Abner. Dukan mutane kuma suka yi kuka. 33 Sarki ya yi wannan makoki domin Abner, ya ce, “Don me Abner zai mutu kamar wawa? 34 Hannuwansa ba a ɗaure suke ba, Ƙafafunsa kuma ba a dabaibaye suke ba. Ya mutu kamar wanda mugayen mutane suka kashe.” Dukan mutane suka yi kuka kuma saboda shi. 35 Mutane kuwa suka zo su ba Dawuda magana, ko ya ci abinci tun rana ba ta faɗi ba. Amma Dawuda ya rantse ya ce, “Allah ya buge ni in mutu nan, idan na ɗanɗana abinci ko wani abu kafin rana ta faɗi.” 36 Da mutanen suka lura, sai suka yarda da abin da sarki ya yi, suka kuma ji daɗin kowane abu da sarki ya yi. 37 A wannan rana dukan mutanen Dawuda da dukan mutanen Isra'ila suka gane, ashe, ba nufin Dawuda ba ne a kashe Abner ɗan Ner. 38 Sarki ya ce wa fādawansa, “Ba ku sani ba, basarake ne, babban mutum ne kuma ya faɗi a cikin Isra'ila yau? 39 Yau na raunana, ko da yake ni sarki ne naɗaɗɗe. Waɗannan mutane, 'ya'yan Zeruya, sun fi ƙarfina, Ubangiji ya sāka wa mai aikata mugunta da muguntar da ya aikata.”

2 Sama’ila 4

An Kashe Ish-boshet

1 Da Ish-boshet, ɗan Saul, ya ji labari Abner ya mutu a Hebron, sai gabansa ya faɗi. Dukan mutanen Isra'ila kuma suka tsorata. 2 Shi ɗan nan na Saul yana da shugabanni biyu na 'yan hari, su ne Ba'ana da Rekab, 'ya'yan Rimmon na ƙasar Biliyaminu daga Biyerot, (gama an lasafta Biyerot cikin yankin ƙasar Biliyaminu. 3 Mutanen Biyerot sun gudu zuwa Gittayim inda suke zaman baƙunci har wa yau.) 4 Jonatan, ɗan Saul kuwa, yana da ɗa, sunansa Mefiboshet, amma gurgu ne. Yana da shekara biyar sa'ad da aka kawo labarin mutuwar Saul da Jonatan daga Yezreyel. Sai mai renonsa ta ɗauke shi, ta sheƙa a guje. A sa'ad da take gudu sai ya faɗo, sanadin gurguntakar ke nan. 5 Rekab da Ba'ana 'ya'yan Rimmon suka tafi gidan Ish-boshet da tsakar rana, a lokacin da yake shaƙatawa. 6 Rekab da Ba'ana kuwa, suka laɓaɓa, suka shiga kamar suna neman alkama. 7 Da suka shiga gidan, sai suka iske shi yana kwance a ɗakin kwanansa. Suka buge shi, suka kashe shi, suka datse kansa. Suka ɗauki kansa suka bi ta hanyar Araba, suka yi tafiya dare farai. 8 Suka kai wa Dawuda kan Ish-boshet a Hebron. Suka ce wa sarki Dawuda, “Ga kan Ish-boshet ɗan maƙiyinka, Saul, wanda ya nemi ranka. Ubangiji ya rama wa sarki a kan Saul da zuriyarsa yau.” 9 Amma Dawuda ya ce wa Rekab da Ba'ana, 'ya'yan Rimmon, mutumin Biyerot, “Na rantse da Ubangiji wanda ya fanshe ni daga kowace masifa, 10 sa'ad da wani ya kawo mini labari cewa, ‘Saul ya mutu,’ mutumin ya yi tsammani albishir ne ya kawo mini, sai na kama shi na kashe shi a Ziklag. Ladan da na ba shi ke nan saboda labarinsa. 11 Balle fa ku da kuke mugayen mutane, da kuka kashe adali a gadonsa, a cikin gidansa, ba sai in nemi hakkin jininsa a hannunku ba, in kawar da ku daga duniya?” 12 Sai Dawuda ya umarci samarinsa su kashe su. Suka datsa hannunsu da ƙafafunsu, suka rataye su a gefen tafkin Hebron. Amma suka ɗauki kan Ish-boshet suka binne a cikin kabarin Abner a Hebron.

2 Sama’ila 5

Dawuda ya Zama Sarkin Isra'ilawa da Yahudawa

1 Dukan kabilan Isra'ila kuwa suka zo wurin Dawuda a Hebron, suka ce, “Ga shi, mu 'yan'uwanka ne. 2 A dā sa'ad da Saul yake sarautarmu, kai kake bi da Isra'ilawa zuwa yaƙi, kai kake komo da su. Ubangiji kuma ya ce maka, ‘Kai za ka lura da jama'ata Isra'ila, za ka zama sarkinsu.’ ” 3 Sai dukan dattawan Isra'ila suka tafi wurin sarki Dawuda a Hebron, shi kuwa ya yi alkawari da su a gaban Ubangiji. Su kuwa suka naɗa shi Sarkin Isra'ila duka. 4 Dawuda ya ci sarauta yana da shekara talatin. Ya yi shekara arba'in yana sarauta. 5 Ya yi shekara jama'ar Yahuza shekara bakwai da wata shida a Hebron. Ya kuma yi sarautar jama'ar Isra'ila duk da Yahuza shekara talatin da uku a Urushalima.

Dawuda ya Ci Sihiyona

6 Sarki Dawuda da mutanensa suka tafi Urushalima su yaƙi Yebusiyawa mazaunan ƙasar. Su kuwa suka ce wa Dawuda, “Ba za ka iya zuwa nan ba, makafi kawai da guragu za su kore ka.” A zatonsu Dawuda ba zai iya zuwa can ba. 7 Duk da haka Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, wato birnin Dawuda. 8 A ran nan Dawuda ya ce, “Duk wanda zai kashe Yebusiyawa, to, sai kuma ya haura zuwa wuriyar ruwa ya fāɗa wa guragu da makafi waɗanda ran Dawuda yake ƙi.” Don haka a kan ce, “Makafi da guragu ba za su shiga Haikali ba.” 9 Dawuda ya zauna a kagara. Ya ba ta suna Birnin Dawuda. Ya kuma yi gine-gine kewaye da wurin. Ya fara daga Millo zuwa ciki. 10 Dawuda kuwa ya ƙasaita, gama Ubangiji Allah Mai Runduna yana tare da shi.

Hiram Sarkin Taya ya Yarda da Dawuda

11 Hiram Sarkin Taya ya aiki jakadu zuwa wurin Dawuda. Ya kuma aika masa da katakan itacen al'ul, da kafintoci, da masu yin gini da duwatsu, suka kuwa gina wa Dawuda gida. 12 Dawuda kuwa ya gane lalle Ubangiji ya tabbatar da shi sarki bisa jama'ar Isra'ila, ya kuma ɗaukaka mulkinsa saboda mutanensa, Isra'ila.

'Ya'yan da aka Haifa wa Dawuda a Urushalima

13 Bayan zuwan Dawuda Urushalima daga Hebron, sai ya ɗauki waɗansu ƙwaraƙwarai, ya kuma auri waɗansu mata. Aka kuma haifa masa waɗansu 'ya'ya mata da maza. 14 Sunayen 'ya'yan da aka haifa masa a Urushalima ke nan, Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu, 15 da Ibhar, da Elishuwa, da Nefeg, da Yafiya, 16 da Elishama, da Eliyada, da Elifelet.

Dawuda ya Ci Nasara a kan Filistiyawa

17 Sa'ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila, sai dukansu suka haura zuwa neman ran Dawuda. Da Dawuda ya ji Filistiyawa suna nemansa, sai ya gangara zuwa kagara. 18 Filistiyawa kuwa suka zo suka bazu a kwarin Refayawa. 19 Dawuda kuwa ya yi roƙo ga Ubangiji, ya ce, “Ko in tafi in yi yaƙi da Filistiyawa? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka haura, gama hakika, zan ba da Filistiyawa a hannunka.” 20 Sai Dawuda ya zo Ba'al-ferazim, ya ci Filistiyawa a wurin. Sa'an nan ya ce, “Ubangiji ya huda abokan gabana a idona kamar rigyawa.” Saboda haka aka sa wa wurin suna, “Ubangiji Mai Hudawa.” 21 Filistiyawa suka gudu, suka bar gumakansu a nan, Dawuda da mutanensa suka kwashe su. 22 Filistiyawa suka sāke haurawa, suka bazu a kwarin Refayawa. 23 Dawuda ya kuma roƙi Ubangiji. Ubangiji kuwa ya ce masa, “Kada ka haura zuwa wurinsu gaba da gaba, amma ka bi ta bayansu, ka ɓullo musu daura da itatuwan doka. 24 Sa'ad da ka ji motsin rausayawar rassan itatuwan doka, sai ka yi maza, ka faɗa musu, gama Ubangiji zai wuce gaba domin ya bugi rundunar Filistiyawa.” 25 Sai Dawuda ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya yi ta bugun Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer.

2 Sama’ila 6

Dawuda ya Kawo Akwatin Alkawari a Urushalima

1 Dawuda kuma ya tattara zaɓaɓɓun mutane dubu talatin (30,000 ) na Isra'ila. 2 Sai ya tafi tare da su duka zuwa Kiriyat-yeyarim domin ya kawo akwatin Alkawarin Allah, wanda ake kira da sunan Ubangiji Mai Runduna wanda yake zaune a tsakanin kerubobin. ɗauko akwatin alkawarin Allah daga gidan Abinadab, wanda yake bisa tudu. Suka sa akwatin alkawari a sabuwar karusa. Uzza da Ahiyo, 'ya'yan Abinadab, maza, suka bi da karusar da akwatin alkawarin Allah yake ciki. Ahiyo ne yake tafiya a gaban akwatin alkawarin. 5 Sai Dawuda da Isra'ilawa duka suka yi rawa sosai don farin ciki a gaban Ubangiji. Aka yi ta raira waƙoƙi, ana kaɗa molaye, da garayu, da goge, da kacakaura, da kuge. 6 Da suka zo masussukar Kidon, sai Uzza ya miƙa hannunsa ya riƙa akwatin alkawarin Allah, gama takarkaran sun yi kwarangyasa. 7 Ubangiji ya husata da Uzza, ya buge shi, ya mutu nan take kusa da akwatin alkawarin Allah, saboda ya taɓa akwatin alkawari. 8 Sai Dawuda ya ji haushi domin Ubangiji ya fashe haushinsa a kan Uzza. Aka sa wa wurin suna Feresauzza har wa yau. 9 Dawuda kuwa ya ji tsoron Ubangiji a ran nan, ya ce, “Ƙaƙa zan ajiye akwatin alkawarin Ubangiji a wurina?” 10 Domin haka Dawuda bai yarda ya kai akwatin alkawarin Ubangiji cikin Birnin Dawuda ba, sai ya kai shi gidan Obed-edom Bagitte. 11 Akwatin alkawarin Ubangiji yana a gidan Obed-edom Bagitte har wata uku. Ubangiji kuwa ya sa wa Obed-edom da dukan iyalinsa albarka.

An Iso da Akwatin Alkawari a cikin Urushalima

12 Aka faɗa wa Dawuda sarki, cewa, Ubangiji ya sa wa gidan Obed-edom albarka, da dukan abin da yake da shi saboda akwatin alkawarin Allah. Sai Dawuda ya tafi da murna ya kawo akwatin alkawarin Allah daga gidan Obed-edom zuwa Birnin Dawuda. 13 Sa'ad da masu ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji suka yi tafiya taki shida, sai Dawuda ya yi hadaya da sa, da keɓaɓɓiyar tunkiya. 14 Dawuda ya sa falmaran ta lilin. Ya kuwa yi rawa da dukan ƙarfinsa a gaban Ubangiji. 15 Shi da mutanen Isra'ila duka suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji da sowa da busar ƙaho. 16 Sa'ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga Birnin Dawuda, sai Mikal, 'yar Saul, ta leƙa ta taga, ta ga sarki Dawuda yana tsalle, yana rawa a gaban Ubangiji, sai ta raina shi a zuci. 17 Suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, suka ajiye shi a wurinsa a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa dominsa. Dawuda ya miƙa hadayun ƙonawa da na salama a gaban Ubangiji. 18 Sa'ad da ya gama miƙa hadayun ƙonawa da na salama, sai ya sa wa mutanen albarka da sunan Ubangiji Mai Runduna. 19 Ya kuma rarraba wa dukan taron jama'ar Isra'ila, mata da maza, ƙosai, da nama, da zabibi, sa'an nan dukan mutane suka watse, kowa ya tafi gidansa. 20 Da Dawuda ya komo gida domin ya sa wa iyalinsa albarka, Mikal, 'yar Saul, ta fito domin ta tarye shi, ta ce masa, “Ƙaƙa Sarkin Isra'ila ya ɗauki kansa yau? Ya kware darajarsa a gaban barorinsa mata kamar yadda shakiyyai suke yi.” 21 Sai Dawuda ya ce wa Mikal, “Ai, na yi wannan a gaban Ubangiji wanda ya zaɓe ni a madadin mahaifinki da iyalinsa, ya naɗa ni in zama Sarkin Isra'ila, wato jama'ar Ubangiji. Lalle zan yi rawar farin ciki a gaban Ubangiji. 22 Zan mai da kaina abin raini fiye da haka, zan kuma zama abin raini gare ki, amma barori mata da kika ambata, za su girmama ni.” 23 Mikal, 'yar Saul fa, ba ta haihu ba har ta rasu.

2 Sama’ila 7

Alkawarin Allah da Dawuda

1 Sa'ad da sarki yake zaune a gidansa, Ubangiji kuma ya hutasshe shi daga fitinar abokan gābansa da suke kewaye da shi, 2 sai sarki ya ce wa annabi Natan, “Duba, ga shi, ina zaune a gidan katakon al'ul, amma akwatin alkawarin Ubangiji yana a alfarwa.” 3 Natan kuwa ya ce wa sarki, “Sai ka yi abin da yake a zuciyarka, gama Ubangiji yana tare da kai.” 4 Amma a daren nan Ubangiji ya yi magana da Natan. 5 Ya ce, “Tafi, ka faɗa wa bawana Dawuda, ka ce, in ji Ubangiji, ‘Ɗakin zama za ka gina mini? 6 Har wa yau ban taɓa zama a ɗaki ba, tun lokacin da na fito da Isra'ilawa daga Masar, amma a alfarwa nake kai da kawowa daga wannan wuri zuwa wancan. 7 A cikin kai da kawowata tare da dukan jama'ar Isra'ila ban taɓa ce wa wani daga cikin shugabannin Isra'ila waɗanda na sa su lura da jama'ata Isra'ila, ya gina mini ɗaki na katakon al'ul ba.’ 8 Abin da za ka faɗa wa bawana Dawuda ke nan, in ji Ubangiji Mai Runduna, ‘Na ɗauko ka daga makiyaya inda kake kiwon tumaki domin ka zama sarkin jama'ata Isra'ila. 9 Ban kuwa rabu da kai ba duk inda ka tafi, na kuma kawar da abokan gābanka duka. Zan sa ka shahara kamar shahararrun mutane na duniya. nuna wa jama'ata Isra'ila wuri na kansu inda zan kafa su su zauna. Ba wanda zai sāke damunsu. Mugayen mutane kuma ba za su ƙara wahalshe su kamar dā ba, tun lokacin da na naɗa wa jama'ata Isra'ila mahukunta. Zan hutar da kai daga fitinar abokan gābanka duka. Banda wannan kuma ina shaida maka, cewa, zan sa gidanka ya kahu. 12 Sa'ad da kwanakinka suka ƙare, za ka rasu tare da kakanninka. A bayanka, zan ta da ɗanka, na cikinka. Zan sa mulkinsa ya kahu. 13 Shi ne zai gina mini ɗaki. Ni kuwa zan tabbatar da kursiyin sarautarsa har abada. 14 Zan zama uba gare shi, zai kuma zama ɗa a gare ni. Sa'ad da ya yi laifi zan hukunta shi da sanda kamar yadda mutane suke yi. Zan yi masa bulala kamar yadda 'yan adam suke yi. 15 Amma ba zan daina nuna masa madawwamiyar ƙaunata ba, kamar yadda na yi wa Saul wanda na kawar daga fuskata. 16 Gidanka kuwa da mulkinka za su dawwama a gabana har abada. Gadon sarautarka kuma zai kahu har abada.’ ” 17 Haka kuwa Natan ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.

Addu'ar Dawuda ta Godiya

18 Sarki Dawuda ya tafi ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allah, ko ni ko iyalina ba mu cancanci dukan abin da ka yi mana ba. 19 Ga shi, ka ƙara fiye da haka, ya Ubangiji Allah, gama ka yi magana, cewa, gidan bawanka zai kai kwanaki masu tsawo. Wannan ka'ida ce ta 'yan adam! 20 Me kuma zan ƙara ce maka, gama ka san bawanka, ya Ubangiji Allah. 21 Bisa ga alkawarinka da yardar zuciyarka ne ka aikata waɗannan manyan al'amura domin ka sa in san su. 22 Bisa ga dukan abin da muka ji, kai mai girma ne, ya Ubangiji Allah. Ba kamarka, in banda kai kuma babu wani Allah. 23 Ba wata al'umma kuma a duniya wadda take kama da jama'arka Isra'ila, wadda kai Allah ka fansa ta zama jama'arka. Ka mai da kanka sananne. Ka yi wa jama'arka manyan abubuwa masu banmamaki. Ka kori al'ummai da gumakansu a gaban jama'arka, waɗanda ka fansa daga Masar. 24 Ka zaɓar wa kanka jama'ar Isra'ila su zama mutanenka har abada. Kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu. 25 “Ya Ubangiji Allah, yanzu ka tabbatar da maganar da ka yi da bawanka da gidansa har abada. Ka aikata bisa ga faɗarka. 26 Za a kuwa ɗaukaka sunanka da cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna shi ne Allah na Isra'ila har abada.’ Gidan bawanka Dawuda kuma zai kahu a gabanka. 27 Gama kai, ya Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, kai ne ka sanar wa ni bawanka, cewa, za ka sa gidana ya kahu, saboda haka ni bawanka na sami ƙarfin halin yin wannan addu'a a gare ka. 28 “Yanzu kuwa, ya Ubangiji Allah, kai ne Allah, kana cika alkawarinka koyaushe. Ka kuwa yi wa bawanka alkawari mai girma. 29 Ka yarda da farin ciki ka sa wa gidan bawanka albarka domin gidansa ya dawwama a gabanka har abada, gama kai ne ka faɗa, ya Ubangiji Allah. Ka sa albarkarka ta tabbata a gidan bawanka har abada.”

2 Sama’ila 8

Yaƙe-Yaƙen Dawuda

1 Bayan haka kuma sai Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya kawo ƙarshen mulkinsu a ƙasar. 2 Sa'an nan ya ci Mowabawa da yaƙi. Ya sa su su kwanta a ƙasa sa'an nan ya riƙa auna su da igiya, kowane awo biyu ya sa a kashe su, awo na uku kuwa sai ya sa a bar su da rai. Mowabawa suka zama talakawansa, suka riƙa kawo haraji. 3 Dawuda kuma ya ci Hadadezer ɗan Rehob, Sarkin Zoba, da yaƙi lokacin da shi Hadadezer yake kan tafiya zuwa Kogin Yufiretis don ya tabbatar da ikonsa a wurin. 4 Dawuda ya ƙwace masa mahayan dawakai dubu ɗaya da ɗari bakwai (1,700 ), da sojojin ƙafa dubu ashirin (20,000 ). Dawuda ya yanyanke agarar dawakan, sai dai doki ɗari ne ya bari. 5 Suriyawan Dimashƙu kuwa, suka zo don su taimaki Hadadezer, Sarkin Zoba, Dawuda kuwa ya kashe Suriyawa dubu ashirin da dubu biyu (22,000 ). 6 Sa'an nan ya ajiye ƙungiyoyin sojojinsa a Suriya ta Dimashƙu. Suriyawa suka zama talakawan Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. Duk inda Dawuda ya tafi, Ubangiji yakan taimake shi. 7 Dawuda ya kwashe garkuwoyi na zinariya waɗanda shugabannin sojojin Hadadezer suka riƙe, ya kawo su Urushalima. 8 Ya kuma kwashe tagulla da yawa daga Beta da Berotayi biranen Hadadezer. 9 Sa'ad da Toyi Sarkin Hamat ya ji labari Dawuda ya ci dukan rundunar Hadadezer da yaƙi, 10 sai ya aiki Adoniram ɗansa wurin sarki Dawuda don ya gaishe shi, ya kuma yaba masa saboda ya ci Hadadezer da yaƙi, gama Hadadezer yakan yi yaƙi da Toyi kullum. Adoniram kuwa ya kawo wa Dawuda kyautar kayan azurfa, da na zinariya, da na tagulla. 11 Dawuda ya keɓe wa Ubangiji kayayyakin nan tare da azurfa da zinariya da ya karɓe daga dukan al'umman da ya mallaka, 12 wato azurfa da zinariya na Edomawa, da na Mowabawa, da na Ammonawa, da na Filistiyawa, da na Amalekawa, da ganimar Hadadezer ɗan Rehob, Sarkin Zoba. 13 Dawuda kuwa ya yi suna. Ya kashe Edomawa dubu goma sha takwas (18,000 ) a kwarin Gishiri sa'ad da yake komowa. 14 Sai ya sa ƙungiyoyin sojoji a ƙasar Edom duka. Edomawa suka zama talakawan Dawuda. Ubangiji ya ba Dawuda nasara duk inda ya tafi.

Sarakunan Yaƙi na Dawuda

15 Dawuda ya mallaki Isra'ila duka. Ya yi wa dukan jama'arsa shari'ar gaskiya da adalci. 16 Yowab ɗan Zeruya, shi ne shugaban sojojin. Yehoshafat ɗan Ahilud, shi ne marubuci. 17 Zadok ɗan Ahitub, da Ahimelek ɗan Abiyata, su ne firistoci. Seraiya shi ne magatakarda. 18 Benaiya ɗan Yehoyada, shi ne shugaban Keretiyawa da Feletiyawa, wato matsara. 'Yan'yan Dawuda, maza, suka zama mataimakansa.

2 Sama’ila 9

Dawuda ya Nuna wa Mefiboshet Alheri

1 Dawuda ya yi tambaya, ko akwai wani da ya ragu daga gidan Saul, wanda zai nuna wa alheri saboda Jonatan. 2 Akwai wani bara na gidan Saul, sunansa Ziba. Sai aka kirawo shi wurin sarki Dawuda. Sarki ya tambaye shi, “Kai ne Ziba?” Sai ya amsa, “Ranka ya daɗe, ni ne.” 3 Sa'an nan sarki ya tambaye shi ko akwai wani wanda ya ragu daga gidan Saul, wanda zai nuna masa alherin Allah. Ziba ya ce wa sarki, “Akwai ɗan Jonatan, gurgu ne kuwa.” 4 Sai sarki ya tambaye shi, “Ina yake?” Ziba ya ce, “Yana gidan Makir, ɗan Ammiyel a Lodebar.” 5 Sarki kuwa ya aika aka zo da shi daga gidan Makir, ɗan Ammiyel, daga Lodebar. 6 Da aka zo da Mefiboshet, ɗan Jonatan, wato jikan Saul, sai ya rusuna har ƙasa, ya yi gaisuwa. Dawuda ya ce, “Mefiboshet!” Ya amsa, “Ranka ya daɗe, ga baranka.” 7 Dawuda ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, gama zan yi maka alheri ne saboda mahaifinka, Jonatan. Zan mayar maka da dukan gonakin kakanka, Saul. Kullum kuma za ka riƙa cin abinci a teburina.” 8 Mefiboshet kuwa ya rusuna, ya ce, “Ni wane ne har da za ka kula da ni, ni da ban fi mataccen kare daraja ba?” 9 Sa'an nan sarki ya kira Ziba, baran Saul, ya ce masa, “Dukan abin da yake na Saul, da dukan abin da yake na iyalinsa, na ba ɗan maigidanka. 10 Kai, da 'ya'yanka maza, da barorinka za ku riƙa yi wa iyalin Saul noma, ku kawo musu amfanin domin su sami abinci, amma Mefiboshet kansa, zai riƙa cin abinci a teburina kullum.” (Ziba kuwa yana da 'ya'ya maza goma sha biyar, da barori ashirin.) 11 Ziba ya amsa wa sarki, ya ce, “Baranka zai yi dukan abin da sarki ya umarta.” Mefiboshet kuwa ya riƙa cin abinci a teburin sarki kamar ɗaya daga cikin 'ya'yan sarkin. 12 Mefiboshet yana da ɗa sunansa Mika. Dukan waɗanda suke zaune a gidan Ziba kuma suka zama barorin Mefiboshet. 13 Mefiboshet kuwa ya zauna a Urushalima ya riƙa cin abinci a teburin sarki kullum. Dukan ƙafafunsa kuwa sun naƙasa.

2 Sama’ila 10

Dawuda ya ci Ammonawa da Suriyawa

1 Sa'ad da Sarkin Ammonawa, wato Nahash, ya rasu, sai Hanun ɗansa ya gāje shi. 2 Dawuda ya ce, “Zan yi wa Hanun alheri kamar yadda tsohonsa ya yi mini.” Dawuda kuwa ya aiki manzanni su yi masa ta'aziyya. Amma da suka isa can, 3 sai hakiman Ammonawa suka ce wa Hanun shugabansu, “Kana tsammani Dawuda yana girmama tsohonka ne, da ya aiko manzanninsa su yi maka ta'aziyya? Ai, manzannin nan da ya aiko 'yan leƙen asirin ƙasa ne. Sun zo ne su bincika don su san yadda za a ci birnin.” 4 Sai Hanun ya sa aka aske wa manzannin nan na Dawuda rabin gyammansu suka kuma yanyanke rigunansu daidai ɗuwawu, sa'an nan suka sallame su. 5 Da aka faɗa wa Dawuda sai ya aika a tarye su, gama mutanen sun sha kunya ƙwarai. Sarki Dawuda ya ce musu su zauna a Yariko har gyammansu su toho, sa'an nan su komo. 6 Da Ammonawa suka ga sun sa Dawuda ya yi gāba da su, suka yi sufurin Suriyawan Bet-rehob da na Zoba, mutum dubu ashirin (20,000 ), suka kuma yi sufurin Sarkin Ma'aka da mutanensa dubu ɗaya, da mutanen Ish-tobi dubu goma sha biyu (12,000 ). 7 Da Dawuda ya ji labari, sai ya aiki Yowab da dukan rundunar jarumawan. 8 Ammonawa suka fita suka ja dāgar yaƙi a ƙofar garin, amma Suriyawan Zoba da na Rehob, da mutanen Ish-tobi da na Ma'aka suka ja tasu dāgar a karkara. 9 Da Yowab ya ga an ja masa dāgar yaƙi gaba da baya, sai ya zaɓi waɗansu Isra'ilawa, ya sa su gabza da Suriyawa. 10 Sauran mutane kuwa ya sa su a hannun Abishai, ƙanensa. Ya sa su gabza da Ammonawa. 11 Ya ce musu, “Idan Suriyawa sun fi ƙarfina, ku kawo mini gudunmawa, amma idan Ammonawa sun fi ƙarfinku, sai in kai muku gudunmawa. 12 Mu yi ƙarfin hali, mu yi jaruntaka saboda jama'armu da biranen Allahnmu. Ubangiji ya yi abin da ya gamshe shi.” 13 Sa'an nan Yowab da mutanensa suka matsa, su gabza da Suriyawa. Suriyawa kuwa suka gudu. 14 Da Ammonawa suka ga Suriyawa sun gudu, su ma suka gudu daga gaban Abishai suka shiga birnin. Sa'an nan Yowab ya komo Urushalima daga wurin yaƙi da Ammonawa. 15 Sa'ad da Suriyawa suka ga Isra'ilawa sun ci su, suka tattara kansu. 16 Hadadezer ya aika aka kawo Suriyawan da suke a hayin Kogin Yufiretis. Suka taru a Helam. Shobak shugaban rundunar Hadadezer shi ne ya shugabance su. 17 Sa'ad da Dawuda ya ji labari, ya tara Isra'ilawa duka, ya haye Urdun zuwa Helam. Suriyawa kuwa suka ja dāgar yaƙi, suka yi yaƙi da Dawuda. 18 Amma Suriyawa suka gudu daga gaban Isra'ilawa. Dawuda kuwa ya kashe Suriyawa, mahayan karusai ɗari bakwai, da mahayan dawakai dubu arba'in (40,000 ). Aka yi wa Shobak shugaban rundunarsu rauni wanda ya zama ajalinsa, a can ya rasu. 19 Sa'ad da dukan hakiman Hadadezer suka ga Isra'ilawa sun ci su, sai suka yi sulhu da Isra'ilawa. Suka zama talakawansu. Wannan ya sa Suriyawa suka ji tsoron ƙara kai wa Ammonawa gudunmawa.

2 Sama’ila 11

Dawuda da Bat-Sheba

1 Da bazara lokacin da sarakuna sukan fita zuwa yaƙi, Dawuda ya aiki Yowab, da shugabannin sojojinsa, da sojojin Isra'ila duka. Suka tafi suka ragargaza Ammonawa, suka kuma kewaya Rabba da yaƙi. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima. 2 Wata rana da yamma Dawuda ya tashi daga shaƙatawa, yana yawo a kan rufin soron fādarsa, can ya hangi wata kyakkyawar mata tana wanka. 3 Sai ya aika a bincika kowacece wannan mata, ashe, 'yar Ammiyel ce, matar Uriya Bahitte. 4 Dawuda kuwa ya aiki waɗansu manzanni suka kawo masa ita, ya kwana da ita. (A lokacin kuwa ta gama wankan haila ke nan.) Sa'an nan ta koma gidanta. 5 Matar kuwa ta yi juna biyu, sai ta aika a faɗa wa Dawuda, cewa, tana da ciki. 6 Dawuda kuwa ya aika wurin Yowab ya ce, “Ka aiko mini da Uriya Bahitte.” Yowab kuwa ya aika da Uriya wurin Dawuda. 7 Da Uriya ya iso, sai Dawuda ya tambaye shi labarin Yowab, da lafiyar jama'ar, da labarin yaƙin. 8 Ya kuma ce masa, “Ka tafi gidanka, ka wanke ƙafafunka.” Da Uriya ya fita daga gidan sarki, sarki ya ba da kyauta a kai masa. 9 Amma Uriya bai tafi gidansa ba, sai ya kwana a ƙofar gidan sarki tare da sauran barorin sarki. 10 Da aka faɗa wa Dawuda, cewa, Uriya bai tafi gidansa ba, Dawuda ya kira Uriya ya ce masa, “Ka dawo daga tafiya, me ya sa ba ka tafi gidanka ba?” 11 Uriya ya ce wa Dawuda, “Akwatin alkawari, da mutanen Isra'ila, da na Yahuza, suna zaune a bukkoki. Shuganana Yowab, da barorinsa suna zaune a sansani a karkara, ƙaƙa ni zan tafi gidana in ci in sha, in kwanta da matata? Na rantse da ranka, ba zan yi haka ba.” 12 Dawuda kuma ya ce wa Uriya, “Ka kwana nan kuma yau, gobe in sallame ka.” Sai Uriya ya kwana a Urushalima a ran nan. 13 Kashegari kuma Dawuda ya kira shi liyafa. Ya zo, ya ci ya sha tare da shi, har Dawuda ya sa shi ya bugu. Amma da dare, sai ya tafi ya kwanta a shimfiɗarsa tare da sauran barorin sarki, amma bai tafi gidansa ba. 14 Da safe Dawuda ya rubuta wasiƙa, ya ba Uriya ya kai wa Yowab. 15 A wasiƙar ya ce wa Yowab, “Tura Uriya a gaba a inda yaƙin ya fi zafi, sa'an nan ku ja da baya, ku bar shi don a buge shi a kashe shi.” 16 Sa'ad da Yowab yake kama garin da yaƙi, sai ya sa Uriya a inda ya sani akwai jarumawan gaske. 17 Mutanen garin suka fito suka yi yaƙi da Yowab. Suka kashe waɗansu daga cikin sojojin Dawuda. Uriya Bahitte, shi ma aka kashe shi. 18 Sai Yowab ya aika aka faɗa wa Dawuda labarin yaƙin. ce wa manzo, “Bayan da ka gama faɗa wa sarki labarin yaƙin duka, idan sarki ya husata, har ya ce maka, ‘Me ya sa kuka tafi yaƙi kurkusa da garin? Ba ku sani ba za su tsaya a gefen garu daga ciki su yi harbi? 21 Wa ya kashe Abimelek ɗan Yerubba'al? Ba mace ce a Tebez ta jefe shi da ɗan dutsen niƙa ta kan garu daga ciki ta kashe shi ba? Me ya sa kuka tafi kusa da garu?’ Sai ka faɗa masa cewa, ‘Baranka, Uriya Bahitte, shi ma an kashe shi.’ ” 22 Manzon kuwa ya tafi ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Yowab ya ce. 23 Ya ce, “Abokan gābanmu sun sami sa'a a kanmu. Sun fito su gabza da mu a karkara, amma muka kore su zuwa cikin ƙofar garin. 24 Sai maharba suka tsaya a kan garu daga ciki suka yi ta harbin barorinka. Waɗansu daga cikin barorin sarki sun mutu. Baranka Uriya Bahitte shi ma ya matu.” 25 Dawuda ya ce wa manzon, “Je ka ka faɗa wa Yowab kada wannan abu ya dame shi, ai, takobi ba ya tarar wanda zai kashe. Ku ƙara matsa wa garin lamba, ku faɗa masa har ku ragargaza shi. Ka ƙarfafa Yowab.” 26 Sa'ad da matar Uriya ta ji labarin mutuwar mijinta, ta yi makoki dominsa. 27 Da kwanakin makokin suka ƙare, sai Dawuda ya aika aka kawo ta gidansa, ta zama matarsa, ta haifa masa ɗa. Amma Ubangiji bai ji daɗin mugun abin nan da Dawuda ya yi ba.

2 Sama’ila 12

Natan ya Tsauta wa Dawuda

1 Sai Ubangiji ya aiki Natan wurin Dawuda. Ya je wurinsa ya ce masa, “Akwai waɗansu mutum biyu a cikin wani gari. Ɗayan basarake ne, attajiri, ɗayan kuwa talaka ne, matalauci. 2 Basaraken yana da garkunan tumaki, da na awaki, da na shanu. 3 Amma talakan ba shi da kome sai 'yar tunkiyar da ya sayo. Ya yi renonta, ta yi girma a wurinsa, tare da 'ya'yansa. Takan ci daga cikin ɗan abincinsa, ta kuma sha daga cikin abin shansa, ta kwanta a ƙirjinsa. Ta zama kamar 'ya a gare shi. 4 Wata rana basaraken ya yi baƙo, amma bai yarda ya kamo daga cikin garkensa ya yanka wa baƙon ba, sai ya kamo 'yar tunkiyar talakan nan, matalauci, ya yanka wa baƙon da ya zo wurinsa.” 5 Dawuda ya husata ƙwarai a kan mutumin, ya ce wa Natan, “Hakika mutumin da ya yi haka ya cancanci mutuwa. 6 Sai kuma ya biya diyyar 'yar tunkiya riɓi huɗu, domin ya aikata mugun abu na rashin tausayi.” 7 Sai Natan ya ce wa Dawuda, “Kai ne mutumin. In ji Ubangiji Allah na Isra'ila, ‘Na naɗa ka Sarkin Isra'ila, na cece ka daga hannun Saul. 8 Na kuma ba ka gidan ubangidanka da matansa. Banda wannan kuma na ba ka gidan Isra'ila da na Yahuza. Da a ce wannan ya yi maka kaɗan, da na ƙara maka kuma kamar haka. 9 Me ya sa ka raina maganar Ubangiji, har da ka aikata mugun abu haka a gabansa? Ka kashe Uriya Bahitte ta hannun Ammonawa, ka ɗauki matarsa ta zama matarka. 10 Domin haka takobi ba zai rabu da gidanka ba, domin ka raina ni, ka ɗauki matar Uriya Bahitte ta zama matarka. 11 Na rantse zan sa wani daga cikin iyalinka ya far maka da tashin hankali. A idonka zan ba da matanka ga wani mutum. Zai kwana da su da rana katā. 12 Kai, a ɓoye ka yi naka zunubi, amma zan sa a yi maka a gaban dukan mutanen Isra'ila da rana katā.’ ” 13 Sai Dawuda ya ce wa Natan, “Na yi wa Ubangiji zunubi.” Natan ya ce masa, “Ubangiji ya gafarta maka, ba za ka mutu ba. 14 Amma domin ka ba da ƙofa ga magabtan Ubangiji su zarge shi, wato saboda abin da ka aikata, ɗan da za a haifa maka zai mutu.” 15 Sa'an nan Natan ya tafi gida. Ɗan Dawuda ya Mutu, aka Haifi Sulemanu Ubangiji kuwa ya sa ciwo ya kama yaron da matar Uriya ta haifa wa Dawuda. 16 Dawuda kuwa ya roƙi Allah saboda yaron. Ya yi azumi. Ya shiga ya kwanta a ƙasa dukan dare. 17 Sai fādawansa suka zo suka kewaye shi, don su tashe shi daga ƙasa, amma bai yarda ba, bai kuma ci abinci tare da su ba. 18 An kwana bakwai sai yaron ya mutu. Fādawansa suka ji tsoron faɗa masa rasuwar yaron. Suka ce wa junansu, “Ga shi, tun lokacin da yaron yake da rai mun yi masa magana, amma bai kasa kunne gare mu ba, yaya za mu iya faɗa masa rasuwar yaron? Zai yi wa kansa ɓarna.” 19 Da Dawuda ya ga fādawansa suna raɗa da juna, sai ya gane lalle yaron ya rasu. Ya tambaye su, ya ce, “Yaron ya rasu ne?” Suka amsa cewa, “I, ya rasu.” 20 Sai Dawuda ya tashi daga ƙasa, ya yi wanka, ya shafa mai, ya sake tufafinsa, ya tafi ɗakin sujada, ya yi sujada, sa'an nan ya koma gidansa ya ce a kawo abinci. Suka kawo masa abinci ya ci. 21 Fādawansa suka ce masa, “Me ka yi ke nan? Ka yi azumi, ka yi kuka saboda yaron tun yana da rai, amma da yaron ya rasu ka tashi, ka ci abinci.” 22 Ya ce musu, “Tun yaron yana da rai, na yi azumi da kuka, ina cewa wa ya sani, ko Ubangiji zai yi mini jinƙai, ya bar yaron da rai? 23 Amma yanzu ya rasu, me zai sa kuma in yi azumi? Zan iya koma da shi ne? Ni zan tafi wurinsa, amma shi ba zai komo wurina ba.” 24 Sa'an nan Dawuda ya yi wa Batsheba, matarsa, ta'aziyya. Ya shiga wurinta, ya kwana da ita. Ta haifa masa ɗa. Ya raɗa masa suna Sulemanu. Ubangiji kuwa ya ƙaunace shi, 25 ya kuma umarci annabi Natan ya raɗa wa yaron suna Yedideya, wato ƙaunataccen Ubangiji.

Dawuda ya ci Rabba da Yaƙi

26 Yowab kuwa ya yi yaƙi da Rabba ta Ammonawa, yana kuwa gab da cin birnin. 27 Sai ya aiki manzanni wurin Dawuda ya ce, “Na yaƙi Rabba, na kama hanyar samun ruwansu. 28 Yanzu ka tara sauran sojoji ka fāɗa wa birnin, ka ci shi da kanka. Gama ba na so in yi suna da cin birnin.” 29 Saboda haka sai Dawuda ya tara sauran sojoji duka, ya tafi Rabba, ya yi yaƙi da ita, ya kuwa ci birnin. 30 Sarkinsu, wato Milkom, yana da kambi na zinariya a kansa, nauyinsa ya kai talanti ɗaya na zinariya yana kuma da duwatsu masu daraja cikinsa. Dawuda kuwa ya ɗauke kambin daga kan sarkin ya sa a nasa. Sa'an nan ya kwaso ganima mai ɗumbun yawa daga cikin birnin. 31 Ya kuma kamo mutanen da suke cikin birnin, ya sa su su yi aiki da zartuka, da faretani, da gatura. Ya kuma sa su yi tubula. Haka Dawuda ya yi da dukan biranen Ammonawa. Sa'an nan Dawuda da dukan sojojinsa suka koma Urushalima.

2 Sama’ila 13

Amnon da Tamar

1 Absalom, ɗan Dawuda, yana da kyakkyawar ƙanwa, sunanta Tamar. Ana nan Amnon ɗaya daga cikin 'ya'yan Dawuda, ya ƙaunace ta. 2 Amnon ya matsu har ya fara ciwo saboda Tamar ƙanwarsa. Ita kuwa budurwa ce, ba shi yiwuwa Amnon ya yi wani abu da ita. 3 Amma Amnon yana abuta da Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dawuda. Yonadab kuwa yana da hila. 4 Sai ya ce masa, “Ya ɗan sarki, me ya sa kake damuwa kowace rana? Ba za ka faɗa mini ba?” Sai Amnon ya ce masa, “Na jarabtu ne da Tamar ƙanwar ɗan'uwana Absalom.” 5 Yonadab kuwa ya ce masa, “Kwanta a gadonka ka yi kamar kana ciwo, lokacin da mahaifinka ya zo domin ya duba ka, sai ka ce masa, ‘A bar ƙanwata Tamar ta zo ta ba ni abinci, ta riƙa shirya abincin a idona, don in gani in kuma riƙa ci daga hannunta.’ ” 6 Amnon kuwa ya kwanta, ya yi kamar yana ciwo. Sa'ad da sarki ya zo duba shi, sai Amnon ya ce wa sarki, “Ina roƙo a sa ƙanwata, Tamar, ta zo ta toya mini waina a inda nake, ta riƙa ba ni da hannunta ina ci.” 7 Sai Dawuda ya aika gida, wurin Tamar, ya ce, “Tafi gidan Amnon wanki, ki shirya masa abinci.” 8 Tamar kuwa ta tafi gidan wanta Amnon, inda yake kwance. Sai ta ɗauki ƙullu, ta cuɗa, ta toya waina a idonsa. 9 Ta juye wainar daga kaskon yana gani, amma ya ƙi ci. Ya ce wa waɗanda suke cikin ɗakin su fita. Su kuwa suka fita. 10 Sa'an nan Amnon ya ce wa Tamar, “Kawo abincin a cikin ɗakin kwanana, ki riƙe mini in ci.” Sai ta ɗauki wainar da ta yi, ta kai wa Amnon, wanta, a ɗakin kwana. 11 Amma da ta kawo kusa da shi don ya ci, ya kama ta, ya ce, “Zo in kwana da ke ƙanwata.” 12 Ta ce masa, “Haba, wana, kada ka ƙasƙantar da ni, gama ba a yin haka a cikin Isra'ila, kada ka yi halin dabba. 13 Ni kuwa ina zan sa kaina saboda kunya? Kai kuwa za ka zama ɗaya daga cikin riƙaƙƙun sakarkarin mutane na cikin Isra'ila. Ina roƙonka ka yi magana da sarki, gama ba zai hana ka ka aure ni ba.” 14 Amma Amnon bai ji maganarta ba. Da yake ya fi ta ƙarfi, sai ya yi mata faɗe. 15 Bayan haka sai Amnon ya ƙi ta da mummunar ƙiyayya, har ƙiyayyar ta fi yawan ƙaunar da ya yi mata. Ya ce mata, “Tashi, ki fita.” 16 Sai ta ce masa, “A'a wana, muguntar koran nan da kake yi mini, ta fi ta wadda ka riga ka yi mini.” Amma bai kasa kunne gare ta ba. 17 Sai ya kira baran da yake yi masa hidima, ya ce, “Fitar da matan nan daga gabana, ka rufe ƙofa.” 18 Tamar kuwa tana saye da doguwar riga mai hannuwa, gama haka gimbiyoyi budurwai suke ado. Baran Amnon kuwa ya fitar da ita, ya kulle ƙofar. 19 Tamar ta baɗe kanta da toka, ta keta doguwar rigarta mai hannuwa wadda ta sa, ta rufe fuska da hannu, ta tafi tana ta kuka da ƙarfi. 20 Absalom wanta ya tambaye ta, ya ce, “Ko Amnon wanki ya ɓata ki? To, yi shiru, ƙanwata, shi wanki ne, kada ki damu da yawa.” Tamar kuwa ta zauna a kaɗaice a gidan Absalom wanta. 21 Da Dawuda sarki ya ji wannan, sai ya husata ƙwarai. 22 Amma Absalom bai tanka wa Amnon da wata magana ta alheri ko ta mugunta ba, gama yana ƙin Amnon saboda ya yi wa Tamar ƙanwarsa faɗe.

Absalom ya Rama ya Gudu

23 Bayan shekara biyu cif, sai Absalom ya sa a yi masa sausayar tumaki a Ba'al-hazor, wadda take kusa da Ifraimu. Ya kuma gayyaci dukan 'yan'uwansa, wato 'yan sarki. 24 Ya kuma tafi wurin sarki, ya ce masa, “Ranka ya daɗe, ga shi, ina sausayar tumakina, ina roƙonka, ka zo, kai da fādawanka tare da ni.” 25 Amma sarki ya ce wa Absalom, “A'a ɗana, ba ma tafi duka ba, don kada mu nawaita maka.” Absalom ya dāge cewa, sai sarki ya je, amma duk da haka sarki bai tafi ba, sai dai ya sa masa albarka. 26 Sa'an nan Absalom ya ce, “Idan ba za ka tafi ba, ina roƙonka ka bar Amnon ɗan'uwana ya tafi tare da mu.” Sarki ya ce, “Don me zai tafi tare da kai?” 27 Amma Absalom ya dāge har sarki ya yarda. Amnon da dukan 'ya'yan sarki suka tafi tare da shi. 28 Absalom ya umarci barorinsa, ya ce, “Ku lura sa'ad da Amnon ya bugu da ruwan inabi, in na ce, ‘Bugi Amnon,’ sai ku kashe shi. Kada ku ji tsoro, gama ni na umarce ku, sai dai ku yi ƙarfin hali, ku yi jaruntaka.” 29 Haka kuwa barorin Absalom suka kashe Amnon yadda Absalom ya umarta. Sauran 'ya'yan sarki kuwa suka tashi, kowa ya hau alfadarinsa, ya gudu. 30 Sa'ad da suke kan hanya labari ya kai kunnen Dawuda. Aka ce, “Absalom ya kashe dukan 'ya'yan sarki, ba wanda ya tsira daga cikinsu.” 31 Sai sarki ya tashi ya keta rigunansa, ya kwanta a ƙasa. Dukan barorinsa kuma da suke tsaye a wurin suka kyakketa rigunansu. 32 Amma Yonadab, ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dawuda, ya ce, “Ranka ya daɗe, ba fa dukan 'ya'yan sarki aka kashe ba. Amnon ne kaɗai aka kashe ta umarnin Absalom, gama ya ƙudura wannan tun daga ranar da Amnon ya yi wa Tamar ƙanwarsa faɗe. 33 Don haka, kada shugabana sarki ya damu, cewa, an kashe dukan 'ya'yan sarki, gama Amnon ne kaɗai aka kashe.” 34 Absalom kuwa ya gudu. Sa'an nan sojan da yake tsaro a wannan lokaci ya ga ɗumbun mutane suna tahowa daga hanyar Horonayim, wajen gefen dutse. 35 Sai Yonadab ya ce wa sarki, “Waɗannan 'ya'yan sarki ne suke zuwa, kamar yadda na faɗa.” 36 Yana gama magana ke nan, sai ga 'ya'yan sarki sun iso. Suka yi ta kuka da ƙarfi. Sarki kuma da dukan fādawansa suka yi kuka mai tsanani. 37 Amma Absalom ya gudu ya tafi wurin Talmai, ɗan Ammihud, Sarkin Geshur. Dawuda kuwa ya yi makokin Amnon ɗansa kwana da kwanaki. 38 Absalom ya shekara uku a Geshur. 39 Sai zuciyar sarki ta koma kan Absalom, gama ya haƙura a kan Amnon da yake ya riga ya rasu.

2 Sama’ila 14

Yowab ya Shirya yadda Absalom zai Koma

1 Da Yowab ɗan Zeruya, ya gane zuciyar sarki ta koma kan Absalom, 2 sai ya aika zuwa Tekowa a kira masa wata mace mai hikima. Da ta zo, ya ce mata, “Ki yi kamar kina makoki, ki sa rigunan makoki, kada ki shafa mai. Ki yi kamar wadda ta yi kwanaki da yawa tana makokin rasuwar wani. 3 Sa'an nan ki tafi wurin sarki, ki ce masa haka.” Sai ya faɗa mata abin da za ta faɗa. 4 Sa'ad da macen nan da ta zo daga Tekowa ta isa gaban sarki, sai ta rusuna har ƙasa don bangirma. Sa'an nan ta ce, “Ya sarki, ka yi taimako.” 5 Sai sarki ya tambaye ta, “Me ya dame ki?” Ta ce, “Ni mace ce wadda mijinta ya rasu. 6 Baranyarka tana da 'ya'ya biyu maza, sai suka yi faɗa a gona, inda ba wanda zai raba su, ɗayan kuwa ya bugi ɗayan ya kashe shi. 7 Yanzu kuwa dukan dangi sun tasar mini, suna cewa, in ba da ɗayan wanda ya kashe ɗan'uwansa domin su kashe shi saboda ran ɗan'uwansa da ya kashe. Wato za su hallaka magāji ke nan, ta haka za a yi biyu babu ke nan, su bar mijina ba suna ko zuriya a duniya.” 8 Sarki kuwa ya ce mata, “Ki tafi gidanki, zan daidaita maganarki.” 9 Sai ta ce wa sarki, “Ya ubangijina, sarki, bari laifin ya zauna a kaina da gidan mahaifina, sarki kuwa da gadon sarautarsa ya barata.” 10 Sarki ya ce mata, “In wani ya ƙara ce miki wani abu, ki kawo shi wurina, ba zai ƙara yi miki fitina ba.” 11 Sai ta ce, “Ina roƙonka, ya sarki, ka rantse da Ubangiji Allahnka, kada a bar masu bin hakkin jini su yi ramako, don kada su kashe ɗana.” Ya ce mata, “Na rantse miki da zatin Ubangiji, ko gashin kansa guda ɗaya ba zai faɗi ƙasa ba.” 12 Ta kuma ce, “Ina roƙonka, ya ubangijina sarki, ka bar ni in yi magana.” Sai ya ce, “Yi maganarki.” 13 Sa'an nan ta ce, “To, me ya sa ka yi wa jama'ar Allah irin wannan abu? Gama bisa ga maganar bakinka, ya sarki, ka hukunta kanka tun da yake sarki bai yarda ɗansa ya komo gida ba. 14 Dukanmu mutuwa za mu yi, kamar ruwan da ya zube a ƙasa, wanda ba ya kwasuwa, haka za mu zama. Allah ba yakan ɗauke rai kurum ba, amma yakan shirya hanya domin wanda ya shuɗe ba zai ɓata daga gabansa ba. 15 Saboda mutane sun tsorata ni shi ya sa na zo in faɗa wa ubanjijina, sarki. Na kuwa yi tunani na ce, ‘Zan tafi in faɗa wa sarki, watakila sarki zai amsa roƙona. 16 Gama sarki zai ji, ya cece ni daga hannun mutumin nan da zai hallaka ni tare da ɗana daga cikin jama'ar Allah.’ 17 Na kuma yi tunani a kan maganar ubangijina, sarki, za ta kwantar da zuciyata, gama ubangijina, sarki, kamar mala'ikan Allah yake, yana rarrabe tsakanin nagarta da mugunta. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da kai!” 18 Sai sarki ya ce mata, “Kada ki rufe mini duk abin da zan tambaye ki.” Ta ce, “To, ka yi tambayarka.” 19 Sa'an nan ya ce mata, “Ko akwai hannun Yowab cikin dukan sha'anin nan naki?” Ita kuwa ta amsa, “Na rantse da kai, ya ubangijina, sarki, ba dama a yi maka ƙumbiya-ƙumbiya. Haka ne, Yowab baranka ne ya sa ni. Shi ya sa dukan waɗannan magana a bakin baranyarka. 20 Yowab baranka ya yi wannan don ya daidaita al'amarin. Amma ubangijina yana da hikima irin ta mala'ikan Allah domin ya san dukan al'amuran da suke a duniya.” 21 Sa'an nan sarki ya ce wa Yowab, “To, na yarda, sai ka tafi ka komo da saurayin nan, Absalom.” 22 Sai Yowab ya rusuna har ƙasa da bangirma, ya yi wa sarki kyakkyawan fata. Ya kuma ce, “Yau na sani na sami tagomashi a wurinka, ya ubangijina, sarki, da yake ka amsa roƙona.” 23 Sa'an nan Yowab ya tashi, ya tafi Geshur, ya komo da Absalom Urushalima. 24 Sarki ya ce a sa shi ya koma gidansa, kada ya zo gabansa. Absalom kuwa ya yi zamansa can gidansa, bai je gaban sarki ba.

Absalom ya Sulhunta da Dawuda

25 A cikin Isra'ila duka ba wanda ake yaba kyansa kamar Absalom. Tun daga tafin sawunsa har zuwa bisa kansa ba shi da makusa. 26 Sa'ad da ya yi aski yakan auna nauyin gashin kansa, nauyin yakan kai wajen shekel ɗari biyu. Gama a ƙarshen kowace shekara yake aski, sa'ad da gashin ya yi masa nauyi. 27 Aka haifa wa Absalom 'ya'ya uku maza da 'ya mace guda, sunanta Tamar, ita kuwa kyakkyawa ce. 28 Absalom ya yi shekara biyu cif a Urushalima, amma bai sami izinin ganin sarki ba. 29 Sai Absalom ya aika a kira masa Yowab don ya aike shi wurin sarki, amma Yowab ya ƙi zuwa. Ya kuma sāke aikawa, Yowab kuwa ya ƙi zuwa. 30 Sai ya ce wa barorinsa, “Ga Yowab yana da gonar sha'ir kusa da tawa, ku tafi, ku sa mata wuta.” Barorin Absalom kuwa suka tafi suka sa wa gonar wuta. 31 Yowab kuwa ya tashi ya tafi wurin Absalom har gidansa, ya ce masa, “Don me barorinka suka sa wa gonata wuta?” 32 Absalom ya ce wa Yowab, “Har sau biyu na aika maka domin ka zo in aike ka wurin sarki, ka tambaya mini, ‘Ko me ya sa na komo daga Geshur?’ Da ma ina can har yanzu, ai, da ya fi mini. Yanzu har ni in tafi wurin sarki, idan ina da laifi, ta, ya kashe ni.” 33 Sai Yowab ya tafi wurin sarki, ya faɗa masa. Sarki ya sa a kira Absalom. Absalom kuwa ya zo gaban sarki, ya rusuna har ƙasa. Sarki kuwa ya marabce shi, ya yi masa sumba.

2 Sama’ila 15

Absalom ya Tayar wa Dawuda

1 Bayan wannan Absalom ya samo wa kansa karusa, da dawakai, da zagage mutum hamsin. 2 Absalom yakan tashi da wuri, ya tsaya a kan hanyar da yake shiga ƙofar garin. Idan wani mai kai ƙara ya zo wurin sarki don shari'a, Absalom yakan kira shi, ya ce, “Daga ina kake?” Idan mutumin ya faɗa masa garin da ya fito daga cikin Isra'ila, 3 sai Absalom ya ce masa, “Ƙararka tana da kyau, tana kuma da gaskiya, amma sarki ba zai yi maka shari'a ba.” 4 Yakan kuma ƙara da cewa, “Kai, in da a ce ni ne alƙali a ƙasar, zan yi wa duk wanda ya zo wurina da ƙara, shari'ar gaskiya.” 5 Sa'ad da mutum ya je kusa da shi ya rusuna don ya gaishe shi, Absalom kuwa yakan rungume mutumin ya sumbace shi. 6 Haka Absalom ya riƙa ya wa dukan Isra'ilawan da suka zo wurin sarki don shari'a. Da haka ya saci zukatan mutanen Isra'ila. 7 Bayan shekara huɗu sai Absalom ya ce wa sarki, “Ina roƙonka, ka yardar mini in je Hebron in cika wa'adina wanda na yi wa Ubangiji. 8 Gama na yi wa'adi sa'ad da nake zaune a Geshur ta Suriya. Na yi wa'adi cewa, ‘Idan dai Ubangiji ya komar da ni Urushalima zan bauta masa.’ ” 9 Sarki ya ce masa, “To, ka sauka lafiya.” Sai ya tashi ya tafi Hebron. 10 Amma Absalom ya aiki manzanni a asirce cikin dukan kabilan Isra'ila a faɗa musu haka, “Da zarar kun ji an busa ƙaho, sai ku ce, ‘Absalom shi ne sarki, yana Hebron.’ ” 11 Mutum metan waɗanda ya gayyata daga Urushalima suka tafi tare da shi da zuciya ɗaya ba tare da sanin kome ba. 12 Lokacin da Absalom yake miƙa hadaya, sai ya aika zuwa Gilo a kira masa Ahitofel Bagilone mai ba Dawuda shawara. Maƙarƙashiyar kuwa ta yi ƙarfi. Mutane masu haɗa kai da Absalom suka riƙa ƙaruwa kullum.

Dawuda ya Gudu daga Urushalima

13 Ana nan sai wani manzo ya zo wurin Dawuda, ya ce masa, “Zukatan mutanen Isra'ila suna wajen Absalom.” 14 Sa'an nan Dawuda ya ce wa fādawansa da yake tare da shi a Urushalima, “Mu tashi mu gudu, in ba haka ba ko ɗayanmu ba zai tsere daga hannun Absalom ba. Sai mu hanzarta mu gudu don kada ya tarar da mu, ya yi mana ɓarna, ya kuma kashe kowa da kowa a birnin.” 15 Fādawan suka ce, “Mu a shirye muke mu yi dukan abin da ubangijinmu sarki ya faɗa.” 16 Sarki ya fita, iyalinsa suka bi shi, amma ya bar ƙwaraƙwarai goma su lura da gidan. 17 Sarki ya fita yana tafiya da ƙafa, dukan mutane kuwa suna biye da shi. Da suka zo Bet-Merhak, wato gida na ƙarshe sai suka tsaya. 18 Dukan fādawansa, da matsaransa, wato dukan Keretiyawa, da dukan Feletiyawa, da dukan Gittiyawa, sojoji ɗari shida waɗanda suka bi Dawuda tun daga Gat suka wuce a gabansa. 19 Sarki kuwa ya ce wa Ittayi, shugabansu, “Don me kai kuma za ka tafi tare da mu? Koma ka zauna wurin sabon sarki, gama kai baƙo ne, ɗan gudun hijira kuma daga ƙasarku. 20 Jiya jiya ka zo, ba daidai ba ne in sa ka ka yi ta ragaita tare da mu, ga shi, ban san inda zan tafi ba. Koma tare da 'yan'uwanka. Ubangiji ya nuna maka alherinsa, da amincinsa.” 21 Amma Ittayi ya amsa wa sarki, ya ce, “Na rantse da zatin Ubangiji da darajar ubangijina, sarki, duk inda za ka tafi ko a mutu ko a yi rai zan tafi.” 22 Sai Dawuda ya ce masa, “To, wuce gaba.” Ittayi Bagitte kuwa ya wuce gaba tare da dukan mutanensa da 'yan yaransu. 23 Dukan ƙasar ta yi ta kururuwa sa'ad da mutane suka tashi. Sarki ya haye rafin Kidron, mutane kuma suka haye, suka nufi jeji. 24 Sai ga Abiyata ya zo, sai kuma ga Zadok ya zo tare da dukan Lawiyawa, ɗauke da akwatin alkawarin Allah. Suka ajiye akwatin har dukan mutane suka gama fita daga birnin. 25 Sa'an nan sarki ya ce wa Zadok, “Ka koma da akwatin alkawarin Allah cikin birnin. Idan na sami tagomashi a wurin Ubangiji zai komo da ni, zan sāke ganin akwatin da mazaunin zatinsa. 26 Amma idan Ubangiji bai ji daɗina ba, to, ga ni, sai ya yi yadda ya ga dama da ni.” 27 Sa'an nan sarki ya ci gaba da yi wa Zadok magana, ya ce, “Ka gani, ka koma birni lafiya, kai da Abiyata tare da 'ya'yanku biyu, wato Ahimawaz ɗanka, da Jonatan, ɗan Abiyata. 28 Ni kuwa zan dakata a nan bakin jeji har na sami labari daga gare ka.” 29 Zadok da Abiyata kuwa suka ɗauki akwatin alkawari suka koma Urushalima, suka zauna a can. 30 Dawuda yana tafe ba takalmi a ƙafarsa, ya rufe kansa, yana ta kuka, sa'ad da yake hawan Dutsen Zaitun, dukan mutane kuma da suke tare da shi suka rufe kawunansu, suna hawa, suna kuka. 31 Aka faɗa wa Dawuda cewa, “Ahitofel yana cikin 'yan maƙarƙashiya tare da Absalom.” Sai Dawuda ya yi addu'a, ya ce, “Ya Ubangiji, ina roƙonka, ka wofintar da shawarar Ahitofel.” 32 Da Dawuda ya hau kan dutse inda ake yi wa Allah sujada, sai ga amininsa Hushai Ba'arkite, da ketacciyar riga, da ƙura a kansa, ya zo ya taryi Dawuda. 33 Dawuda kuwa ya ce masa, “Idan ka tafi tare da ni za ka zama mini nawaya. 34 Amma in za ka koma cikin birnin, ka ce wa Absalom, ‘Ya sarki, zan zama baranka kamar yadda na zama baran mahaifinka a dā. Haka zan zama baranka.’ Ta haka za ka watsar da shawarar Ahitofel. 35 Ga shi, Zadok da Abiyata, firistoci, suna tare da kai. Duk abin da ka ji daga gidan sabon sarki, sai ka faɗa wa Zadok da Abiyata, firistoci. 36 Ga 'ya'yansu biyu suna tare da su a can, wato Ahimawaz, ɗan Zadok, da Jonatan, ɗan Abiyata. Duk abin da ka ji, ka aiko su, su zo su faɗa mini.” 37 Hushai, abokin Dawuda kuwa, ya isa Urushalima daidai lokacin da Absalom yake shiga.

2 Sama’ila 16

Dawuda da Ziba

1 Sa'ad da Dawuda ya wuce ƙwanƙolin dutsen kaɗan, sai ga Ziba baran Mefiboshet ya sadu da shi. Ya zo da jaki biyu ya yi musu labtu da gurasa dunƙule ɗari biyu, da zabibi ɗari, da sababbin 'ya'yan itace guda ɗari, da salkar ruwan inabi. 2 Sarki kuwa ya ce wa Ziba, “Me ya sa ka kawo abubuwan nan?” Ziba ya amsa, ya ce, “An kawo wa iyalin sarki jakuna su hau, da abinci, da 'ya'yan itace, domin samari su ci, ruwan inabi kuma domin waɗanda suke rafkewa a jejin su sha.” 3 Sarki kuma ya tambaye shi, “Ina ɗan ubangijinka?” Sai Ziba ya ce, “Yana zaune a Urushalima, yana cewa, ‘Yanzu dai mutanen gidan Isra'ila za su mayar mini da sarautar tsohona.’ ” 4 Da jin haka sai sarki ya ce wa Ziba, “Dukan abin da yake na Mefiboshet ya zama naka.” Ziba kuma ya rusuna ya yi godiya ya ce, “Bari in zama majidaɗin ubangijina, sarki.”

Dawuda da Shimai

5 Sa'ad da Dawuda ya kai Bahurim, sai ga wani mutum sunansa Shimai, ɗan Gera, daga iyalin gidan Saul, ya fito yana ta zagi. 6 Ya jajjefi Dawuda da fādawansa da duwatsu, da sauran jama'a, da dukan jarumawan da suke kewaye da shi. 7 Shimai ya yi ta zagi, yana cewa, “Tafi, tafi, kai mai kisankai, sakarai. 8 Ubangiji ya sāka maka saboda alhakin jinin gidan Saul, wanda ka hau gadon sarautarsa. Yanzu Ubangiji ya ba da sarautar ga Absalom, ɗanka. Duba, masifa ta auko maka, gama kai mai kisankai ne.” 9 Sai Abishai, ɗan Zeruya, ya ce wa sarki, “Ranka ya daɗe, don me za ka bar wannan kare yana ta zaginka? Bari in tafi in fille masa kai.” 10 Amma sarki ya ce masa, “Ba ruwanku, ku 'ya'yan Zeruya. Idan yana zagi saboda Ubangiji ya sa shi, to, wa ya isa ya ce, ‘Don me kake yin haka?’ ” 11 Dawuda kuma ya ce wa Abishai da dukan fādawansa, “Ga shi ma, ɗana na cikina yana neman raina, balle wannan mutumin Biliyaminu! Ku bar shi ya yi ta zagi, gama Ubangiji ne ya umarce shi. 12 Watakila Ubangiji zai dubi azabata, ya sāka mini da alheri saboda wannan zagin da aka yi mini yau.” 13 Dawuda da mutanensa suka ci gaba da tafiyarsu. Shimai kuwa yana biye da su ta gefen dutse, yana tafe, yana ta zagi, yana jifarsa da duwatsu, yana masa ature. 14 Sarki da dukan jama'ar da suke tare da shi suka isa Urdun a rafke. Sai suka shaƙata.

Absalom a Urushalima

15 Absalom kuwa ya zo Urushalima tare da dukan mutanen Isra'ila da suke tare da shi. Ahitofel kuma yana tare da shi. 16 Sa'ad da Hushai Ba'arkite, aminin Dawuda ya zo wurin Absalom, ya ce masa, “Ran sarki ya daɗe!” 17 Sai Absalom ya ce wa Hushai, “Ƙaunar da kake yi wa abokinka ke nan? Me ya sa ba ka tafi tare da abokinka ba?” 18 Hushai ya amsa, ya ce, “Ba haka ba, ni dai zan zama na wanda Ubangiji, da wannan jama'a, dukan mutanen Isra'ila suka zaɓa. Zan zauna tare da mutumin da aka zaɓa. 19 Banda haka ma, wane ne ya kamata in bauta wa, in ba ɗan ubangidana ba? Kamar yadda na bauta wa tsohonka, haka kuma zan bauta maka.” 20 Sa'an nan Absalom ya juya wajen Ahitofel, ya ce, “To, ka kawo shawararka a kan abin da ya kamata mu yi?” 21 Ahitofel kuwa ya ce wa Absalom, “Ka shiga ka kwana, da ƙwarakwaran tsohonka waɗanda ya bar su su lura da gidan. Dukan Isra'ilawa za su sani ba shiri kuma tsakaninka da tsohonka. Dukan masu goyon bayanka kuma za su ƙara ƙarfafa.” 22 Sai suka kafa wa Absalom alfarwa a bisa kan soro, ya shiga ya kwana da ƙwaraƙwaran tsohonsa, a idon mutanen Isra'ila duka. 23 Shawarar da Ahitofel yake bayarwa a lokacin nan ta zama kamar faɗar Allah ce. Absalom duk da Dawuda, shawarar Ahitofel suke bi.

2 Sama’ila 17

Hushai ya Wofintar da Shawarar Ahitofel

1 Ahitofel ya kuma ce wa Absalom, “Bari in zaɓi mutum dubu goma sha biyu (12,000 ), mu tafi mu bi Dawuda da daren nan. 2 Zan fāɗa masa sa'ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya, in firgitar da shi. Dukan mutanen da suke tare da shi za su gudu. Shi kaɗai zan kashe. 3 Zan kawo maka dukan jama'a kamar yadda akan kawo amarya a gidan angonta. Ran mutum guda kaɗai kake nema, sauran mutane duka kuwa su yi zamansu lafiya.” 4 Wannan shawara ta gamshi Absalom da dattawan Isra'ila. 5 Sa'an nan Absalom ya ce, “A kirawo Hushai Ba'arkite don mu ji abin da shi kuma zai faɗa.” 6 Da Hushai ya zo, sai Absalom ya ce masa, “Ga shawarar da Ahitofel ya bayar, mu bi ta? Ko kuwa? Kai, me ka ce?” 7 Sai Hushai ya ce wa Absalom, “A wannan lokaci dai shawarar da Ahitofel ya bayar ba ta da kyau.” 8 Hushai ya ci gaba da cewa, “Ka san tsohonka da jama'arsa jarumawa ne, yanzu a husace suke kamar damisar da aka kwashe wa 'ya'ya a jeji. Tsohonka kuma ya ƙware da sha'anin yaƙi, ba tare da mutanensa zai kwana ba. 9 Yanzu haka yana cikin rami ko dai a wani wuri a ɓoye. Idan an kashe waɗansu daga cikin mutanenka a karo na farko, duk wanda ya ji zai ce, ‘An kashe mutane da yawa daga cikin mutanen Absalom.’ 10 Wannan zai sa jarumi wanda yake da zuciya kamar ta zaki ya karaya don tsoro, gama dukan mutanen Isra'ila sun sani tsohonka jarumi ne, su kuma waɗanda suke tare da shi jarumawa ne. 11 Shawarata ita ce a tattara maka dukan Isra'ilawa tun daga Dan har zuwa Biyer-sheba, yawansu kamar yashi a bakin teku. Kai kuma da kanka ka tafi wurin yaƙin. 12 Da haka za mu tafi mu neme shi duk inda yake, mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo bisa ƙasa. Da shi da mutanensa, ba wanda za a bari da rai. 13 Idan ya gudu zuwa cikin gari, sai dukan jama'armu su zarge garin da igiya, su jā har duk ya watse, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.” 14 Sai Absalom da dukan mutanen Isra'ila suka ce, “Shawarar Hushai Ba'arkite ta fi ta Ahitofel kyau.” Haka Ubangiji ya nufa ya wofintar da kyakkyawar shawarar Ahitofel don ya jawo wa Absalom masifa.

An yi wa Dawuda Sanarwa ya Tsere

15 Sa'an nan Hushai ya ce wa Zadok da Abiyata, firistoci, “Ga irin shawarar da Ahitofel ya ba Absalom da dattawan Isra'ila, ga kuma irin wadda ni na bayar. 16 Yanzu sai ka aika da sauri a faɗa wa Dawuda, kada ya kwana a bakin jeji a daren yau, amma ya haye don kada a hallaka shi tare da mutanensa.” 17 Jonatan da Ahimawaz suna jira a En-rogel. Wata baranya takan tafi ta faɗa musu saƙo, su kuma sai su tafi su faɗa wa sarki Dawuda, don kada a gan su suna shiga birnin. 18 Amma wani saurayi ya gan su, sai ya faɗa wa Absalom. Sai su biyu ɗin suka gudu nan da nan. Suka shiga gidan wani mutum a Bahurim, akwai rijiya a filin gidan. Sai suka shiga rijiyar. 19 Matar gidan kuwa ta yi shimfiɗa a bakin rijiyar, ta baza tsaba a kai, ba kuwa wanda ya san abin da ta yi. 20 Sa'ad da fādawan Absalom suka zo gidan, suka tambayi matar, “Ina Ahimawaz da Jonatan suke?” Sai ta ce musu, “Ai, tuni sun haye kogi.” Sa'ad da suka neme su ba su same su ba, sai suka koma Urushalima. 21 Bayan da fādawan sun tafi, sai mutanen suka fito daga rijiyar. Suka tafi suka ce wa sarki Dawuda, “Ka tashi ka haye kogin nan da nan, gama ka ji irin muguwar shawarar da Ahitofel ya bayar a kanka.” 22 Sai Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka haye Urdun. Kafin wayewar gari ko wannensu ya haye Urdun. 23 Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya yi wa jakinsa shimfiɗa ya hau, ya koma garinsu. Da ya kintsa gidansa, sai ya rataye kansa, ya mutu, aka binne shi a kabarin mahaifinsa.

Dawuda a Mahanayim

24 Dawuda kuwa ya zo Mahanayim. Absalom kuma da dukan mutanen Isra'ila suka haye Urdun. 25 Absalom ya naɗa Amasa ya zama shugaban sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan Yeter ne, Ba'isma'ile, wanda ya auri Abigail 'yar Nahash, 'yar'uwar Zeruya mahaifiyar Yowab. 26 Absalom da mutanen Isra'ila suka kafa sansaninsu a ƙasar Gileyad. 27 Sa'ad da Dawuda ya kai Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lodebar, da Barzillai Bagileyade daga Rogelim, 28 suka kawo wa Dawuda da jama'arsa waɗannan kaya da abinci, wato gadaje, da tasoshi, da tukwane, da alkama, da sha'ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa, 29 da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu. Gama sun sani Dawuda da mutanensa suna jin yunwa, da gajiya, da kishi, a cikin jeji.

2 Sama’ila 18

An Ci Absalom

1 Dawuda kuwa ya shirya sojojin da suke tare da shi, sa'an nan ya naɗa musu shugabanni na dubu dubu da na ɗari ɗari. 2 Ya aiki runduna zuwa yaƙi. Ya sa Yowab ya shugabanci sulusi ɗaya na rundunar, sulusi na biyu kuma ya sa a hannun Abishai, ɗan Zeruya, ɗan'uwan Yowab. Sulusi na uku kuwa ya sa a hannun Ittayi Bagitte. Sa'an nan sarki ya ce wa sojojin, “Ni ma da kaina zan tafi tare da ku.” 3 Amma sojojin suka ce, “Ba za ka tafi tare da mu ba, gama idan muka gudu, ba za su kula da mu ba. Ko rabinmu sun mutu, ba za su kula ba, gama kai kana bakin mutum dubu goma (10,000 ) na mutanenmu. Zai fi kyau kuma ka zauna cikin gari ka riƙa aika mana da taimako.” 4 Sai sarki ya ce musu, “Duk abin da kuka ga ya fi muku kyau, shi zan yi.” Sarki kuwa ya tsaya a bakin ƙofar garin sa'ad da sojojin suke fita, kashi kashi, ɗari ɗari, da dubu dubu. 5 Ya kuma umarci Yowab, da Abishai, da Ittayi ya ce, “Ku lurar mini da saurayin nan, Absalom.” Dukan sojojin suka ji umarnin da sarki ya yi wa shugabanninsu a kan Absalom. 6 Sojojin suka tafi zuwa karkara don su yi yaƙi da mutanen Isra'ila. Suka yi yaƙin a kurmin Ifraimu. 7 Mutanen Isra'ila suka sha kashi a hannun jarumawan Dawuda. A wannan rana aka kashe mutane da yawa, har mutum dubu ashirin (20,000 ). 8 Yaƙin ya bazu ko'ina a ƙasar. A ranar abin da kurmin ya ci ya fi abin da aka kashe da takobi. 9 Absalom yana cikin gudu sai ya fāɗa a hannun jarumawan Dawuda. Sa'ad da yake cikin gudu a kan alfadarinsa, sai alfadarin ya kurɗa tsakanin rassan babban itacen oak. Kansa ya sarƙafe kam cikin rassan itacen oak ɗin, alfadarin kuwa ya wuce, ya bar shi yana rataye yana lilo. 10 Da wani mutum ya gani, sai ya tafi ya faɗa wa Yowab, ya ce, “Na ga Absalom yana reto a itacen oak.” 11 Yowab ya ce wa mutumin da ya faɗa masa, “Kai! Ka gan shi! Me ya sa ba ka buge shi har ƙasa ba? Ai, da na ba ka azurfa goma da abin ɗamara.” 12 Sai mutumin ya ce wa Yowab, “Ko da za a ba ni azurfa dubu a hannuna, ba zan miƙa hannuna in taɓa ɗan sarki ba, gama a kunnuwanmu sarki ya umarce ka, kai da Abishai, da Ittayi cewa, ‘Ku lura mini da saurayin nan, Absalom.’ 13 In da na ci amana har na kashe shi, ba yadda abin zai ɓoyu ga sarki, sa'an nan kai da kanka ka zame, ka bar ni.” 14 Yowab ya ce, “Ba zan ɓata lokaci haka da kai ba.” Sai ya ɗibi mashi uku ya soki Absalom a ƙahon zuciya, tun yana da sauran rai, a maƙale cikin itacen oak. 15 Sa'an nan samari goma masu ɗaukar wa Yowab makamai, suka kewaye Absalom, suka yi ta d�kansa har ya mutu. 16 Sa'an nan Yowab ya busa ƙaho, sojoji suka komo daga runtumar Isra'ilawa. Yowab ya tsai da su. 17 Suka ɗauki gawar Absalom, suka jefa ta cikin wani rami mai zurfi a kurmin, suka tula tsibin duwatsu a kanta. Dukan Isra'ilawa kowa ya tsere zuwa gidansa. 18 Tun Absalom yana da rai ya gina wa kansa al'amudi a kwarin sarki, gama ya ce, “Ba ni da ɗa wanda zai sa a riƙa tunawa da ni.” Ya kira al'amudin da sunansa. Ana kuwa kiransa al'amudin Absalom har wa yau.

An faɗa wa Dawuda Mutuwar Absalom

19 Ahimawaz ɗan Zadok ya ce wa Yowab, “Ka yarda mini in sheƙa a guje in kai wa sarki labari yadda Ubangiji ya cece shi daga hannun magabtansa.” 20 Yowab ya ce masa, “Ba za ka kai labari yau ba, sai wata rana ka kai, amma yau ba za ka kai labari ba, domin ɗan sarki ya mutu.” 21 Sa'an nan Yowab ya ce wa wani mutumin Habasha, “Tafi ka faɗa wa sarki abin da ka gani.” Sai Bahabashen ya rusuna wa Yowab, sa'an nan ya sheƙa a guje. 22 Ahimawaz ɗan Zadok kuma ya ce wa Yowab, “Ko mene ne zai faru dai, ka bar ni in bi bayan Bahabashen a guje.” Yowab ya ce masa, “Don me za ka tafi, ɗana, tun da yake ba za ka sami lada saboda labarin da za ka kai ba?” 23 Ahimawaz ya ce, “Duk dai abin da zai faru, zan tafi.” Sai Yowab ya yardar masa ya tafi. Sa'an nan Ahimawaz ya sheƙa, ya bi ta hanyar fili, ya wuce Bahabashen. 24 Dawuda kuwa yana zaune a tsakanin ƙofofi biyu na garin. Mai tsaro ya hau kan soron da yake kan bangon garu. Da ya ɗaga kai ya duba, sai ya ga mutum yana gudu shi kaɗai. 25 Ya ta da murya, ya faɗa wa sarki. Sai sarki ya ce, “Idan shi kaɗai ne, yana kawo labari ne.” Mutumin ya yi ta ƙara zuwa kusa. 26 Mai tsaron kuma ya ga wani mutum yana zuwa shi ma a guje, sai ya ta da murya wajen mai ƙofar garin, ya ce, “Ga wani mutum kuma yana zuwa a guje!” Sai sarki ya ce, “Shi ma labari yake kawowa.” 27 Mai tsaron ya ce, “Na ga gudun na farin kamar gudun Ahimawaz ɗan Zadok.” Sai sarki ya ce, “Shi mutumin kirki ne, yana kawo kyakkyawan labari ne.” 28 Da Ahimawaz ya zo kusa da sarki, ya ce, “Salama!” Sa'an nan ya rusuna a gaban sarki ya sunkuyar da fuska ƙasa, ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka, wanda ya ba da mutanen da suka tayar wa ubangijina, sarki.” 29 Sai sarki ya ce, “Na ce dai, saurayin nan, Absalom, yana nan lafiya?” Ahimawaz ya amsa, ya ce, “A sa'ad da Yowab ya aiko ni na ga babban hargitsi, amma ban san ko mene ne ba.” 30 Sarki kuwa ya ce, “Koma waje ɗaya, ka tsaya.” Sai ya koma waje ɗaya ya tsaya cik. 31 Sai ga Bahabashe ya iso, ya ce, “Abishirinka, ya ubangijina, sarki, gama a wannan rana ta yau Ubangiji ya cece ka daga hannun waɗanda suka tayar maka.” 32 Sarki ya tambaye shi, “Na ce dai, saurayin nan Absalom, yana lafiya?” Bahabashen ya amsa, “Allah ya sa abokan gāban ubangijina, sarki, da duk waɗanda suka tayar maka da mugunta, su zama kamar saurayin nan.” 33 Sai zuciyar sarki ta tsinke, ya hau cikin ɗakin da yake kan garun ƙofar garin yana ta kuka, yana cewa, “Ya ɗana Absalom, ɗana! Wayyo, ɗana Absalom! Da ma ni ne na mutu, ba kai ba. Ya Absalom, ɗana, ɗana!”

2 Sama’ila 19

Yowab ya Tsauta wa Dawuda

1 Aka faɗa wa Yowab, cewa, sarki yana kuka, yana makoki domin Absalom. 2 Saboda haka sai nasarar da aka ya a ranar ta zama makoki ga jama'a duka, gama jama'a suka ji an ce sarki yana baƙin ciki domin ɗansa. 3 Sojojin suka shiga birni sururu kamar waɗanda sukan shiga birni a ɓoye da kunya saboda sun gudu daga wurin yaƙi. 4 Sarki ya rufe fuskarsa, ya yi kuka da ƙarfi, yana cewa, “Ya ɗana Absalom, ya Absalom, ɗana, ɗana!” 5 Yowab kuwa ya tafi wurin sarki a gidansa ya ce, “Yau ka kunyatar da mutanenka duka waɗanda suka ceci ranka, da rayukan 'ya'yanka mata da maza, da rayukan matanka, da rayukan ƙwaraƙwaranka. 6 Gama kana ƙaunar maƙiyanka, amma kana ƙin waɗanda suke ƙaunarka. Gama yau ka bayyana a fili, shugabannin sojojinka da fādawanka ba a bakin kome suke a gare ka ba. Gama yau na gane da a ce Absalom yana da rai, mu kuwa muka mutu duka, da daɗi za ka ji. 7 Don haka sai ka tashi yanzu, ka fita ka yi wa mutanenka magana mai daɗi. Gama na rantse da Ubangiji idan ba ka fita ba, ba wanda zai zauna tare da kai da daren nan. Wannan kuwa zai fi muni fiye da kowane irin mugun abin da ya taɓa samunka tun daga ƙuruciyarka har zuwa yanzu.” 8 Sa'an nan sarki ya tashi, ya zauna a dandalin ƙofar garu. Aka faɗa wa mutanensa duka, cewa, ga sarki yana zaune a dandalin ƙofar garu. Mutanensa duka kuwa suka zo suka kewaya sarki.

Dawuda ya Tashi za shi Urushalima

Bayan wannan sai dukan Isra'ilawa suka gudu, kowa ya tafi gidansa. 9 Dukan mutanen ƙasar Isra'ila suna ta jayayya, suna cewa, “Sarki Dawuda ne ya cece mu daga hannun abokan gabanmu, ya cece mu daga hannun Filistiyawa, to, ga shi, ya gudu daga ƙasar don ya tsere wa Absalom. 10 Ga shi kuma, Absalom ɗin da muka naɗa ya zama sarkinmu, an kashe shi a yaƙi. Yanzu fa, me ya sa muka yi shiru ba mu komo da sarki ba?” 11 Da labarin abin da Isra'ilawa suke cewa, ya zo gun sarki Dawuda, sai ya aika zuwa wurin firistoci, wato Zadok da Abiyata, a faɗa musu su tambayi dattawan Yahuza abin da ya sa suka zama na ƙarshe a kan komar da sarki a gidansa. 12 Ya ce, “Ai, ku 'yan'uwana ne, da ƙasusuwana, da namana. To, me ya sa za ku zama na ƙarshe a kan komar da sarki? 13 Ku ce wa Amasa, ‘Ashe, kai ba ƙashina da namana ba ne? Allah ya hukunta ni idan ba kai ne shugaban rundunar sojojina a maimakon Yowab ba.’ ” 14 Da haka Dawuda ya rinjayi zukatan mutanen Yahuza, suka zama ɗaya, kamar mutum guda. Sai suka aika wurin sarki, cewa, ya komo tare da dukan fādawansa. 15 Sa'ad da sarki ya iso Urdun. Mutanen Yahuza suka tafi Gilgal suka taryi sarki, domin su hawo da shi Urdun. 16 Shimai ɗan Gera kuma, mutumin Biliyaminu daga Bahurim, ya gaggauta, ya gangara tare da mutanen Yahuza don ya taryi sarki Dawuda. 17 Ya zo tare da mutum dubu (1,000 ) daga kabilar Biliyaminu. Ziba kuma, baran gidan Saul, ya zo a gaggauce a gaban sarki a Urdun tare da 'ya'yansa maza, su goma sha biyar, da barorinsa guda ashirin. 18 Suka haye zuwa wancan hayi don su hawo da iyalin sarki, su kuma yi masa abin da zai ji daɗi. Sa'ad da sarki yake shirin hayewa, sai Shimai ɗan Gera ya zo ya fāɗi a gābansa. 19 Ya ce wa sarki, “Ina roƙon ubangijina, sarki, in ka yarda kada ka riƙe baranka da laifi, kada ka tuna da laifin da baranka ya yi a ranar da ubangijina sarki yake gudu daga Urushalima. Kada sarki ya riƙe wannan a zuci. 20 Gama na sani, ranka ya daɗe, na yi laifi, shi ya sa na zama na farko daga gidan Yusufu yau da na fito domin in taryi ubangijina sarki.” 21 Abishai ɗan Zeruya kuwa ya ce, “Ya kamata a kashe Shimai gama ya zagi wanda Ubangiji ya zaɓa ya zama sarki.” 22 Amma Dawuda ya ce wa Abishai da ɗan'uwansa Yowab, “Ina ruwana da ku, ku 'ya'yan Zeruya? Kuna so ku jawo mini wahala? Ni ne Sarkin Isra'ila yanzu, don haka ba Ba'isra'ilen da za a kashe a yau.” 23 Sa'an nan ya ce wa Shimai, “Ina tabbatar maka, cewa, ba za a kashe ka ba.” 24 Sa'an nan Mefiboshet jikan Saul ya gangara ya taryi sarki. Tun daga ranar da sarki ya gudu har zuwa ranar da ya komo da nasara Mefiboshet bai wanke ƙafafunsa ba, bai kuma yi gyaran fuska ba, bai ma wanke tufafinsa ba. 25 Sa'ad da ya iso daga Urushalima don ya taryi sarki, sai sarki ya ce masa, “Me ya sa ba ka tafi tare da ni ba, Mefiboshet?” 26 Mefiboshet ya amsa ya ce, “Ya ubangijina, sarki, barana ya ruɗe ni, gama na ce masa ya yi wa jaki shimfiɗa don in hau in tafi wurin sarki, gama ka sani ni gurgu ne, ranka ya daɗe. 27 Barana ya ɓata sunana a gaban ubangijina, sarki. Amma ranka ya daɗe, ya sarki, kai kamar mala'ikan Allah kake, sai ka yi abin da ya yi maka daidai. 28 Gama dukan mutanen gidan kakana sun cancanci mutuwa a gabanka, ranka ya daɗe, amma ga shi, ka sa na zama ɗaya daga cikin waɗanda suke ci a teburinka. Ba ni da dalilin da zai sa in yi wa sarki wani kuka kuma.” 29 Sai sarki ya ce masa, “Me ya kawo wannan magana a kan harkokinka? Ai, na riga na zartar, cewa, kai da Ziba za ku raba mallakar Saul.” 30 Mefiboshet ya ce wa sarki, “A ma bar masa duka ya mallaka, ni dai tun da ubangijina, sarki, ya komo gida lafiya, to, alhamdu lillahi.” 31 Barzillai Bagileyade kuma ya gangara daga Rogelim zuwa wurin sarki domin ya yi wa sarki rakiya zuwa hayin Urdun. 32 Barzillai kuwa tsoho ne, yana da shekara tamanin. Ya taimaki sarki da abinci sa'ad da sarki yake a Mahanayim, gama shi attajiri ne. 33 Sarki ya ce wa Barzillai, “Ka zo mu tafi tare zuwa Urushalima, ni kuwa zan riƙa biya maka bukata.” 34 Amma Barzillai ya amsa, ya ce, “Shekaruna nawa suka ragu har da zan tafi Urushalima tare da sarki? 35 A yau ina da shekara tamanin cif. Ba zan iya in rarrabe abu mai daɗi da marar daɗi ba. Ba kuma zan iya ɗanɗana daɗin abin da nake ci ko abin da nake sha ba. Ba zan iya jin daɗin muryar mawaƙa ba. Zan zamar maka kaya kurum, ranka ya daɗe. 36 Ban cancanci wannan irin babban lada ba. Zan dai yi maka 'yar rakiya zuwa hayin Urdun. 37 Ina roƙonka ka bar ni in koma domin in rasu a garinmu, kusa da kabarin mahaifina. Amma ga Kimham barana, bari ya tafi tare da kai, ranka ya daɗe. Ka yi masa yadda kake so.” 38 Sarki ya ce, “To, Kimham zai tafi tare da ni, zan kuwa yi masa abin da zai yi maka daɗi. Duk abin da kake so a gare ni, zan yi maka.” 39 Sa'an nan dukan jama'a suka haye Urdun, sarki kuma ya haye. Ya yi bankwana da Barzillai, ya sumbace shi, ya kuma sa masa albarka. Sai Barzillai ya koma gidansa. 40 Sarki kuwa ya yi tafiya zuwa Gilgal. Kimham kuma ya tafi tare da shi. Mutanen Yahuza duka, da rabin mutanen Isra'ila suna tafe tare da sarki. 41 Sai dukan mutanen Isra'ila suka zo wurin sarki, suka ce masa, “Me ya sa mutanen Yahuza 'yan'uwanmu, suka sace ka, suka kawo sarki da iyalinsa a wannan hayin Urdun, tare da dukan mutanensa?” 42 Dukan mutanen Yahuza suka amsa wa mutanen Isra'ila suka ce, “Domin sarki ɗan'uwanmu ne na kusa. Me ya sa kuke fushi a kan wannan al'amari? Me muka ci a jikin sarki, ko kun ji ya ba mu wani abu ne?” 43 Isra'ilawa kuma suka amsa wa mutanen Yahuza, suka ce, “Muna da rabo goma a wurin sarki Dawuda fiye da ku, don me kuka raina mu? Ba mu ne muka fara maganar komowar sarki ba?” Amma maganar mutanen Yahuza ta fi ta mutanen Isra'ila zafi.

2 Sama’ila 20

Tawayen Sheba

1 Da can akwai wani mutumin banza, ana ce da shi Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Biliyaminu. Shi kuwa ya busa ƙaho, ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu kuwa da gado wurin ɗan Yesse. Ya Isra'ilawa, kowa ya gudu zuwa alfarwarsa.” 2 Sai dukan Isra'ilawa suka janye jiki daga wurin Dawuda, suka bi Sheba, ɗan Bikri, amma mutanen Yahuza suka manne wa sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima. 3 Da Dawuda ya koma gidansa a Urushalima, kwarakwaran nan nasa guda goma waɗanda ya bar su tsaron gida ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya yi ta lura da su, amma bai shiga wurinsu ba. Haka suka zauna a keɓe, suna zaune kamar gwauraye. 4 Sa'an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mini mutanen Yahuza kafin kwana uku, kai kuma ka zo tare da su.” 5 Sai Amasa ya tafi ya kira mutanen Yahuza, amma ya makara, bai zo a lokacin da aka ƙayyade masa ba. 6 Dawuda kuma ya ce wa Abishai, “Sheba ɗan Bikri fa, zai ba mu wuya fiye da Absalom, sai ka ɗauki mutanena, ka bi sawunsa, don kada ya ci garuruwa masu garu har ya tsere mana.” 7 Sa'an nan mutanen Yowab, wato Keretiyawa da Feletiyawa, da dukan jarumawa, suka bi bayan Abishai. Suka fita daga Urushalima don su bi sawun Sheba, ɗan Bikri. 8 Sa'ad da suke a babban dutsen Gibeyon, Amasa ya zo ya tarye su. A lokacin nan Yowab yana saye da rigar yaƙi, ya sha ɗamara, yana kuma rataye da takobi a ɗamararsa. Da ya gabato, sai takobin ya faɗi. 9 Yowab ya ce wa Amasa, “Abokina kana lafiya?” Yowab kuma ya kama gemun Amasa da hannun dama don ya sumbace shi. 10 Amma Amasa bai lura Yowab yana da takobi a hannunsa ba. Yowab kuwa ya kirɓa masa takobin a ciki sau ɗaya, sai hanjin Amasa ya zuba ƙasa, ya mutu. Sa'an nan Yowab da Abishai ɗan'uwansa suka bi sawun Sheba, ɗan Bikri. 11 Sai ɗaya daga cikin samarin Yowab ya tsaya kusa da gawar Amasa ya ce, “Duk wanda yake son Yowab da duk wanda yake goyon bayan Dawuda, ya bi Yowab.” 12 Gawar Amasa kuwa ta birkiɗe da jini tana a tsakiyar hanya. Da mutumin ya ga yadda dukan mutane suka tsaya, sai ya kawar da ita daga tsakiyar hanya zuwa cikin saura, ya rufe ta da tufa, gama dukan wanda ya ga gawar, sai ya ja, ya tsaya. 13 Sa'ad da aka kawar da ita daga kan hanya, dukan mutane kuwa suka bi Yowab domin su bi sawun Sheba ɗan Bikri. 14 Sai Sheba ya bibiya kabilan Isra'ila, har ya kai Abel-bet-ma'aka. Dukan dangin Beri kuwa suka taru suka bi shi zuwa cikin garin. 15 Dukan mutanen da suke tare da Yowab kuma suka zo suka kewaye shi cikin Abel-bet-ma'aka. Suka tula ƙasa a jikin garun garin, daidai da tsayinta, waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe garun. 16 Sai wata mace mai hikima ta yi kira daga cikin garin, ta ce, “Ji mana! A faɗa wa Yowab, ya zo nan, ina so in yi magana da shi.” 17 Da ya zo kusa da ita, sai macen ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “I, ni ne.” Ta ce masa, “Ka kasa kunne gare ni.” Ya ce, “Ina sauraronki.” 18 Ta ce, “A dā sukan ce, ‘A nemi shawara a Abel,’ gama a can ake raba gardama. 19 Garinmu lafiyayye ne, amintacce ne kuma a cikin Isra'ila. Me ya sa kake so ka hallaka garin? Kana so ka rushe abin da yake na Allah?” 20 Yowab ya ce, “Allah ya sawwaƙe! Ba zan lalatar ko in hallakar da birninku ba. 21 Ba haka ba ne, ni dai ina neman mutumin ƙasar tudu ta Ifraimu, wanda ake ce da shi Sheba, ɗan Bikri. Shi ne ya tayar wa sarki Dawuda. Shi kaɗai za ku ba ni, ni kuwa zan janye daga garin.” Macen kuwa ta ce wa Yowab, “To, za a jefar maka kansa ta kan garu.” 22 Macen ta tafi wurin dukan mutanen garin da wayo. Su kuwa suka yanke kan Sheba, ɗan Bikri, suka jefa wa Yowab. Sa'an nan Yowab ya busa ƙaho, suka janye daga garin. Kowa ya tafi gidansa. Yowab kuma ya koma Urushalima wurin sarki.

Fādawan Dawuda

23 Yowab shi ne shugaban dukan sojojin Isra'ila, Benaiya, ɗan Yehoyada shi ne shugaban Keretiyawa da Feletiyawa, wato masu tsaro. 24 Adoniram shi ne shugaban aikin gandu, Yehoshafat, ɗan Ahilud, shi ne marubuci. 25 Shewa shi ne magatakarda. Zadok da Abiyata su ne firistoci. 26 Aira mutumin Yayir shi ne mashawarcin Dawuda.

2 Sama’ila 21

Ramuwa don Gibeyonawa

1 A zamanin Dawuda aka yi yunwa shekara uku bi da bi. Dawuda kuwa ya roƙi Ubangiji. Sai Ubangiji ya ce masa, “Akwai alhakin jini a kan Saul da gidansa, domin ya kashe Gibeyonawa.” 2 (Gibeyonawa dai ba mutanen Isra'ila ba ne, su Amoriyawan da suka ragu ne, waɗanda Isra'ilawa suka rantse musu, cewa, ba za su kashe su ba. Amma Saul, saboda kishin da yake yi domin mutanen Isra'ila da Yahuza, ya nema ya kashe su duk.) 3 Dawuda kuwa ya kira Gibeyonawa ya ce musu, “Me zan yi muku, da me zan yi kafara, domin ku sa wa mutanen Ubangiji albarka?” 4 Gibeyonawa suka amsa suka ce, “Ba zancen azurfa ko zinariya yake tsakaninmu da Saul ko da gidansa ba. Ba kuma wani mutum muke so mu kashe daga cikin Isra'ila ba.” Dawuda kuma ya tambaye su ya ce, “To, me kuke so in yi muku?” 5 Suka ce wa sarki, “Mutumin da ya karkashe mu, ya yi niyyar hallakar da mu, don kada mu kasance tare da Isra'ilawa ko'ina a cikin karkararsu. 6 Sai ka ba mu 'ya'yansa maza bakwai domin mu rataye su a gaban Ubangiji a Gibeya a kan dutsen Ubangiji.” Sarki kuwa ya ce, “To, zan bayar.” 7 Amma sarki ya ware Mefiboshet, ɗan Jonatan, wato jikan Saul, saboda rantsuwar da take tsakaninsa da Jonatan, ɗan Saul. 8 Sai sarki ya sa aka kamo masa Armoni da Mefiboshet, 'ya'yan Saul waɗanda Rizfa, 'yar Aiya, ta haifa masa, da 'ya'ya maza biyar na Adriyel, ɗan Barzillai, mutumin Abelmehola, waɗanda matarsa Merab 'yar Saul ta haifa masa. 9 Sarki kuwa ya bai wa Gibeyonawa su. Sai suka rataye su a kan dutse a gaban Ubangiji. Su bakwai ɗin nan suka hallaka gaba ɗaya. An kashe su a farkon kakar sha'ir. 10 Rizfa kuwa, 'yar Aiya, ta ɗauki algarara ta yi wa kanta shimfiɗa a kan dutsen. Ta zauna a wurin tun daga farkon kaka har zubar ruwan damuna da ya bugi gawawwakin. Ba ta bar tsuntsaye su sauka a kansu da rana ba, ko namomin jeji da dare. 11 Sa'ad da aka sanar wa Dawuda abin da Rizfa, 'yar Aiya, ƙwarƙwarar Saul ta yi, 12 Dawuda ya tafi ya kwaso ƙasusuwan Saul da na ɗansa Jonatan daga wurin mutanen Yabesh a Gileyad. (Gama suka sace su daga dandalin Bet-sheyan, a inda Filistiyawa suka rataye su, a ranar da suka kashe Saul a Gilbowa.) 13 Daga can ne ya kwaso ƙasusuwan Saul da na Jonatan, suka kuma tattara ƙasusuwan waɗanda aka rataye. 14 Aka binne ƙasusuwan Saul da na ɗansa Jonatan a kabarin Kish, tsohon Saul, a Zela a ƙasar Biliyaminu. Aka aikata dukan abin da sarki ya umarta. Bayan haka Allah ya ji addu'arsu a kan ƙasar.

Abishai ya Ceci Dawuda daga Ƙaton Mutum

15 Ana nan sai Filistiyawa suka kai wa Isra'ilawa yaƙi. Dawuda kuwa ya gangara tare da jama'arsa, suka yi yaƙi da Filistiyawa. Dawuda kuwa ya gaji. 16 Sai Ishbi-benob, ɗaya daga cikin Refayawa, gwarzayen nan, wanda nauyin mashinsa ya yi shekel ɗari uku na tagulla, yana kuma rataye da sabon takobi, ya zaci zai iya kashe Dawuda. 17 Abishai ɗan Zeruya kuwa, ya kawo wa Dawuda gudunmawa. Ya faɗa wa Bafilisten, ya kashe shi. Jama'ar Dawuda kuwa suka sa ya yi musu alkawari ba zai ƙara binsu zuwa wurin yaƙi ba. Suka ce, “Kai ne begen Isra'ila, ba mu so mu rasa ka.”

Jarumawan Dawuda sun Kashe Ƙattin Mutane

18 Bayan wannan kuma suka sāke yin yaƙi da Filistiyawa a Gab. Sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin gwarzayen. 19 Suka sake yin yaƙi da Filistiyawa a Gab, sai Elhanan, ɗan Yayir, mutumin Baitalami, ya kashe ɗan'uwan Goliyat na Gat, wanda girman gorar māshinsa ta yi kama da dirkar masaƙa. 20 An kuma yi wani yaƙi a Gat, inda aka sami wani ƙaton mutum wanda shi cindo ne, hannuwa da ƙafafu, wato yana da yatsotsi ashirin da huɗu ke nan. Shi kuma daga cikin zuriyar gwarzayen mutanen ne. 21 Sa'ad da ya nuna wa Isra'ilawa raini, Jonatan ɗan Shimeya, ɗan'uwan Dawuda, ya kashe shi. 22 Waɗannan gwarzaye huɗu sun fito daga zuriyar gwarzayen Gat ne. Dawuda da mutanensa suka kashe su.

2 Sama’ila 22

Waƙar Nasarar Dawuda

1 Wannan waƙa Dawuda ya raira wa Ubangiji sa'ad da Ubangiji ya cece shi daga hannun Saul da dukan sauran abokan gābansa, ya ce, 2 “Ubangiji ne mai cetona, Shi ne ƙaƙƙarfar kagarata. 3 Allahna, shi ne kāriyata, Ina zaune lafiya tare da shi. Yana kāre ni kamar garkuwa, Yana tsare ni, ya kiyaye ni. Shi ne mai cetona. 4 Na yi kira ga Ubangiji, Ya cece ni daga abokan gābana. Yabo ya tabbata ga Ubangiji! 5 Gama raƙuman ruwa na mutuwa sun kewaye ni, Raƙuman ruwa na hallaka suna gangarawa ta kaina. 6 Mutuwa ta ɗaure ni da igiyoyinta da ƙarfi, Kabari kuma ya ɗana mini tarko. 7 A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji, Na yi kira ga Allah domin taimako. Daga cikin Haikalinsa ya ji muryata, Ya kasa kunne ga kukana na neman taimako. 8 “Sa'an nan duniya ta yi tangaɗi, ta girgiza, Harsashin sararin sama ya yi makyarkyata, ya raurawa, saboda fushin Allah. 9 Hayaƙi ya fito daga kafafen hancinsa, Harshen wuta mai cinyewa da garwashi mai ƙuna daga bakinsa. 10 Ya jā sararin sama baya ya sauko, Da girgije mai duhu a ƙarƙashin ƙafafunsa. 11 Ya hau kerub, ya tashi sama, Ya yi tafiya ta fikafikan iska. 12 Ya rufe kansa da duhu, Gizagizai masu kauri cike da ruwa suna kewaye da shi, 13 Garwashi mai ci daga tsawar walƙiya a gabansa. 14 “Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama Aka kuma ji muryar Maɗaukaki. 15 Ya harharba kibau, ya warwatsa magabtansa, Da walƙiyoyin tsawa ya sa su gudu. 16 An bayyana ƙarƙashin teku a fili, An tone tussan duniya, Lokacin da Ubangiji ya yi wa abokan gāba tsautawa, Ya yi musu ruri cikin fushi. 17 Daga Sama Ubangiji ya miƙo ya ɗauke ni, Ya tsamo ni daga zurfafan ruwaye. 18 Ya kuɓutar da ni daga waɗanda suke ƙina, Daga abokan gābana, waɗanda suka fi ƙarfina! 19 Sa'ad da nake cikin wahala sun auka mini, Amma Ubangiji ya kiyaye ni. 20 Ya taimake ni ya fisshe ni daga hatsari, Ya cece ni domin yana jin daɗina. 21 “Ubangiji ya sāka mini bisa ga adalcina, Ya sa mini albarka domin ba ni da laifin kome. 22 Gama na kiyaye dokar Ubangiji, Ban yi wa Allahna tayarwa ba. 23 Na kiyaye dukan dokokinsa, Ban yi rashin biyayya ga umarnansa ba. 24 Ya sani ni marar laifi ne, Na kiyaye kaina daga aikata mugunta. 25 Domin haka ya sāka mini bisa ga adalcina, Gama ya sani ba ni da laifi. 26 “Kai, ya Ubangiji, amintacce ne ga waɗanda suke da aminci, Nagari ne kuma ga waɗanda suke cikakku. 27 Mai Tsarki ne kai ga waɗanda suke tsarkaka, Amma kana gāba da waɗanda suke mugaye. 28 Kakan ceci masu tawali'u, Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai. 29 “Ya Ubangiji, kai ne haskena, Kana haskaka duhuna. 30 Ka ba ni ƙarfi don in auka wa abokan gābana, Da iko domin in murƙushe tsaronsu. 31 “Allahn nan cikakke ne ƙwarai, Maganarsa tabbatacciya ce! Kamar garkuwa yake Ga dukan masu neman kiyayewarsa. 32 Ubangiji shi kaɗai ne Allah, Allah ne kaɗai madogararmu. 33 Allahn nan shi ne mafaka, mai ƙarfi ne a gare ni, Ya sa hanyata ta zama lafiyayyiya. 34 Ya mai da ƙafafuna kamar na barewa, Ya kiyaye ni a kan duwatsu. 35 Ya horar da ni domin yaƙi, Domin in iya tausa baka mafi ƙarfi. 36 “Ya Ubangiji, ka kiyaye ni, ka cece ni, Taimakonka ya sa na zama babba. 37 Ka hana a kama ni, Ban kuwa taɓa faɗuwa ba. 38 Na runtumi abokan gābana, na kuwa hallaka su, Ban tsaya ba sai da na kore su. 39 Na fyaɗa su ƙasa, ba su iya tashi ba, Suna kwance warwar a ƙafafuna. 40 Ka ba ni ƙarfi domin yin yaƙi, Nasara kuma a kan abokan gābana. 41 Ka sa abokan gābana su gudu daga gabana, Na hallaka waɗanda suke ƙina. 42 Suka nemi taimako, amma ba wanda zai cece su, Suka yi kira ga Ubangiji, amma bai amsa musu ba. 43 Na murƙushe su, sun yi laushi kamar ƙura, Na tattake su kamar caɓi a kan tituna, na kuwa watsar da su. 44 “Ka cece ni daga jama'ata mai tawaye, Ka sa in yi mulkin al'ummai, Mutanen da ban san su ba sun zama bayina. 45 Baƙi sun zo suna rusuna mini, Sa'ad da suka ji ni suka yi mini biyayya. 46 Zuciyarsu ta karai, Suka fito daga kagararsu suna rawar jiki. 47 “Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai tsaronsa! Allah ne ƙaƙƙarfan Mai Cetona! Ku yi shelar girmansa! 48 Ya ba ni nasara a kan abokan gabana, Ya sa mutane a ƙarƙashin mulkina, 49 Ya kuɓutar da ni daga hannun maƙiya. Kai, ya Ubangiji, ka ba ni nasara a kan maƙiyana, Ka tsare ni daga mutane masu zafin hali. 50 Domin wannan zan yi yabonka cikin al'ummai, Zan raira yabbai gare ka. 51 Allah ya ba sarkinsa manya manyan nasarori, Ya nuna madawwamiyar ƙauna ga shi wanda ya zaɓa, Wato ga Dawuda da zuriyarsa har abada.”

2 Sama’ila 23

Maganar Dawuda ta Ƙarshe

1 Wannan ita ce maganar Dawuda ta ƙarshe. Dawuda ɗan Yesse, shi ne mutumin da Allah ya ɗaukaka, wanda Allah na Yakubu ya zaɓa ya zama sarki, wanda kuma ya shirya waƙoƙin Isra'ila. Dawuda ya ce, 2 “Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina, Saƙonsa yana kan leɓunana. 3 Allah na Isra'ila ya yi magana, Matsaron Isra'ila ya ce mini, ‘Sarkin da yake mulkin mutane da adalci, Wanda yake mulki da tsoron Allah, 4 Yana kama da hasken rana a kan girgijen alfijir, Rana da take sa ciyawa ta yi ƙyalƙyali bayan an gama ruwan sama.’ 5 “Haka Allah zai sa wa zuriyata albarka, Gama ya yi mini madawwamin alkawari, Duka kuwa a shirye yake, zai kuwa kiyaye. Abin da nake bukata ke nan, Wannan ne nasarata, Na tabbata kuwa Allah zai kammala shi. 6 Amma marasa Allah suna kama da ƙayayuwan da aka zubar, 7 Amma wanda zai taɓa su, sai da wani ƙarfe ko da māshi, Za a ƙone su ƙurmus.”

Jarumawan Dawuda

8 Ga sunayen jarumawan Dawuda, Yosheb-basshebet, daga Takemon, shi ne ɗaya daga cikin shugabanni uku. Ya girgiza māshinsa, ya kashe mutum ɗari takwas baki ɗaya. 9 Wanda yake biye da shi a cikin su uku ɗin shi ne Ele'azara, ɗan Dodo, ɗan Ahowa. Yana tare da Dawuda sa'ad da suka raina Filistiyawan da suka taru don yaƙi. Mutanen Isra'ila kuwa suka jā baya, 10 shi kuwa ya tsaya, ya yi ta yaƙi da Filistiyawa, har hannunsa ya ƙage, har bai iya ɓanɓaruwa daga takobinsa ba. Ubangiji ya ba da babbar nasara a wannan rana. Bayan an gama sai Isra'ilawa suka koma wurin Ele'azara don su kwashi ganima kawai. 11 Biye da Ele'azara kuma, sai Shamma, ɗan Agi, daga Harod. Filistiyawa suka taru a Lihai, inda akwai wata gonar wake. Isra'ilawa kuwa suka guji wa Filistiyawa. 12 Amma Shamma ya tsaya a tsakiyar gonar, ya kāre ta. Ya kuma kashe Filistiyawa. Ubangiji ya ba da babbar nasara. 13 Sai jarumawa uku daga cikin jarumawa talatin, suka tafi wurin Dawuda a kogon Adullam, gab da lokacin girbi. A lokacin kuwa Filistiyawa sun kafa sansani a kwarin Refayawa. 14 Dawuda yana cikin kagara, ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuwa tana a Baitalami. 15 Dawuda ya ji marmari, ya ce, “Kai, da ma wani zai ba ni ruwan rijiyar ƙofar garin Baitalami in sha!” 16 Shahararrun jarumawan nan uku kuwa suka sheƙa a guje, suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka tafi, suka ɗebo ruwa daga rijiyar ƙofar garin Baitalami, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda bai sha ba, ya zuba shi hadaya a gaban Ubangiji. 17 Sa'an nan ya ce, “Ya Ubangiji, ka tsare ni daga shan jinin mutanen da suka sadaukar da ransu.” Saboda haka bai sha ruwan ba. Abubuwan da jarumawan nan uku suka yi ke nan. 18 Abishai, ɗan'uwan Yowab ɗan Zeruya, shi ne shugaban jarumawan nan talatin. Sa'ad da ya girgiza mashinsa, sai da ya kashe mutum ɗari uku. Da haka ya samar wa kansa s�na tare da mutanen nan uku. 19 Shi ya fi shahara daga cikin su talatin ɗin, don haka ya zama shugabansu, amma bai kai su uku ɗin can ba. 20 Benaiya ɗan Yehoyada, mutumin Kabzeyel, jarumi ne. Ya yi manyan ayyuka. Ya kashe ƙwararrun jarumawa biyu na Mowab. Wata rana kuma da aka yi dusar ƙanƙara, sai ya tafi ya kashe zaki a kogo. 21 Ya kuma kashe wani Bamasare mai cika fuska. Bamasaren yana da māshi a hannunsa, amma Benaiya ya tafi wurinsa da sanda, ya fizge mashin daga hannun Bamasaren, ya kashe shi da māshin. 22 Abubuwan da Benaiya, ɗan Yehoyada ya yi ke nan. Da haka ya samar wa kansa suna tare da jarumawan nan talatin. 23 Ya shahara cikin jarumawan nan talatin, amma bai kai su uku ɗin can ba. Dawuda kuwa ya maishe shi ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa. jarumawan da suka zama talatin sun haɗu da waɗannan, 0 7 Asahel, ɗan'uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo, daga Baitalami, Shamma da Elika, daga Harod, Helez, daga Felet, Aira, ɗan Ikkesha, daga Tekowa, Abiyezer, daga Anatot, Sibbekai, daga Husha, Zalmon, daga Aho, Maharai, da Heled, ɗan Ba'ana, daga Netofa, Ittayi, ɗan Ribai, daga Gibeya ta Biliyaminu, Benaiya, daga Firaton, Hurai, daga kwaruruka kusa da Ga'ash, Abiyel, daga Araba, Azmawet, daga Bahurim, Eliyaba, daga Shalim, Yashen, daga Gimzo, Jonatan, ɗan Shamma, daga Harod, Ahiyam, ɗan Sharar, daga Harod, Elifelet, ɗan Ahasbai, daga Ma'aka, Eliyam, ɗan Ahitofel, daga Gilo, Hezro, daga Karmel, Nayarai, daga Arabiya, Igal, ɗan Natan, daga Zoba, Bani, daga Gad, Zelek, daga Ammon, Naharai, (mai ɗaukar wa Yowab, ɗan Zeruya makamai) daga Biyerot, Aira daga Gareb, daga Yattir, Uriya, Bahitte. Dukansu su talatin da bakwai ne shahararrun sojoji.

2 Sama’ila 24

Dawuda ya Ƙidaya dukan Jama'a

1 Ubangiji kuwa ya husata da Isra'ilawa. Ya kuwa zuga Dawuda a kansu, ya ce, “Tafi ka ƙidaya jama'ar Isra'ila da ta Yahuza.” 2 Sai sarki ya ce wa Yowab da shugabannin sojojin su tafi cikin dukan kabilan Isra'ila, tun daga Dan har zuwa Biyer-sheba, su ƙidaya mutanen don ya san yawansu. 3 Amma Yowab ya ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya sa mutanenka su ƙaru har sau ɗari fiye da yadda suke, har ubangijina sarki ya gani da idonsa, amma me ya sa sarki yake so ya yi wannan abu?” 4 Amma maganar sarki ta rinjayi ta Yowab da ta sauran shugabannin sojojin. Yowab kuwa da sauran shugabannin sojojin suka tashi daga gaban sarki suka tafi su ƙidaya mutanen Isra'ila. 5 Suka haye Urdun suka fara daga Arower, da garin da yake tsakiyar kwarin zuwa Gada, har zuwa Yazar. 6 Sa'an nan suka zo Gileyad da Kadesh cikin ƙasar Hittiyawa, daga nan suka tafi Dan-ja'an. Daga Dan-ja'an kuma suka ratsa zuwa Sidon. 7 Suka tafi kagarar Taya da dukan garuruwan Hiwiyawa, da na Ƙan'aniyawa. Daga can suka tafi ƙasar kudu ta Yahuza a Biyer-sheba. 8 Da suka gama ratsa dukan ƙasar, sai suka komo Urushalima bayan wata tara da kwana ashirin. 9 Yowab kuwa ya ba sarki yawan jimillar mutanen da aka samu. A Isra'ila an sami mutanen da suka isa yin yaƙi, su dubu ɗari takwas (800,000 ). A Yahuza kuwa an sami mutum dubu ɗari biyar (500,000 ). 10 Bayan da Dawuda ya ƙidaya mutane, sai lamirinsa ya kā da shi, ya ce wa Ubangiji, “Na yi laifi ƙwarai a kan abin da na yi. Ina roƙonka, ya Ubangiji, ka gafarta mini, gama na yi wauta.” 11 Da Dawuda ya tashi da safe, sai Ubangiji ya yi magana da annabi Gad, wato annabin da yake tare da Dawuda, ya ce, 12 “Tafi ka faɗa wa Dawuda na ba shi abu uku don ya zaɓi ɗaya wanda za a yi masa daga cikinsu.” 13 Sai Gad ya zo wurin Dawuda ya ce masa, “Kana so a yi yunwa shekara uku a ƙasarka? Ko kuwa kana so ka yi ta gudu a gaban abokan gabanka har wata uku? Ko kuwa ka fi so a yi annoba kwana uku a ƙasarka? Yanzu sai ka yi tunani, ka faɗi irin amsar da zan mayar wa Ubangiji da ya aiko ni.” 14 Dawuda kuwa ya ce, “Na shiga uku, gara in faɗa a ikon Ubangiji, gama shi mai rahama ne, da in faɗa a ikon mutum.” 15 Ubangiji kuwa ya aika da annoba a kan Isra'ila tun da safe har zuwa lokacin da aka ƙayyade. Mutum dubu saba'in (70,000 ) suka mutu daga Dan zuwa Biyer-sheba. 16 Sa'ad da mala'ikan Ubangiji ya miƙa hannunsa wajen Urushalima don ya hallaka ta, sai Ubangiji ya tsai da masifar, ya ce wa mala'ikan da yake hallakar da mutanen, “Ya isa, ka janye hannunka.” Mala'ikan ya tsaya kusa da masussukar Arauna Bayebuse. 17 Da Dawuda ya ga mala'ika wanda yake hallakar da mutanen, sai ya ce wa Ubangiji, “Na yi laifi, na aikata mugunta, amma me waɗannan tumaki suka yi? Ina roƙonka, ka hukunta ni da gidan ubana.” 18 A ran nan Gad ya koma wurin Dawuda ya ce masa, “Ka haura ka gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse.” 19 Dawuda kuwa ya haura bisa ga umarnin Ubangiji ta bakin Gad. 20 Da Arauna ya waiga, ya ga sarki da fādawansa suna zuwa wurinsa, sai ya tafi ya tarye su. Ya tafi ya rusuna a gaban sarki har ƙasa, 21 ya ce, “Ranka ya daɗe, ya sarki, me ya kawo ka?” Sai Dawuda ya ce, “Don in sayi masussukarka ne domin in gina wa Ubangiji bagade, domin a kawar wa mutanen da annobar.” 22 Arauna kuwa ya ce wa Dawuda, “Bari ubangijina, sarki, ya karɓa, ya yi abin da yake so. Ga shanun nan domin hadayar ƙonawa, ga kuma itacen sussuka da karkiya domin itacen hadayar.” 23 Dukan waɗannan Arauna ya ba sarki. Ya kuma ce wa sarki, “Ubangiji Allahnka ya karɓa.” 24 Amma sarki ya ce wa Arauna, “A'a, saye zan yi daga gare ka da tamani. Ba zan miƙa wa Ubangiji Allahna hadayun ƙonawa da abin da ban yi wahalarsa ba.” Dawuda ya sayi masussukar da shanu a bakin shekel hamsin na azurfa. 25 Sa'an nan ya gina wa Ubangiji bagade a wurin. Ya miƙa hadayun ƙonawa da na salama. Sa'an nan Ubangiji ya amsa masa addu'o'i saboda ƙasar. Aka kawar wa Isra'ila da annobar.

1 Sarakuna 1

Abishag ta Yi wa Dawuda Hidima

1 Sarki Dawuda ya tsufa ƙwarai, don haka ko an rufe shi da abin rufa ba ya jin ɗumi. 2 Saboda haka fādawansa suka ce masa, “Ranka ya daɗe bari mu nemo maka budurwa, wadda za ta zauna tare da kai, ta riƙa yin maka hidima, ta kwanta a ƙirjinka don ka riƙa jin ɗumi.” 3 Suka kuwa nemi kyakkyawar yarinya a dukan ƙasar Isra'ila. Sai suka sami Abishag a Shunem, suka kawo ta wurin sarki. 4 Ko da yake yarinyar kyakkyawa ce ƙwarai, ta zama mai lura da sarki, ta kuwa yi masa hidima, amma sarki bai yi jima'i da ita ba.

Adonija ya Ci Sarauta

5 Adonija, dan da Haggit ta haifa wa Dawuda, ya ɗaukaka kansa cewa, “Zan zama sarki.” Ya kuwa shirya wa kansa karusai, da dakarai, da zagage hamsin a gabansa. 6 Tsohonsa bai taɓa tsawata masa ba. Shi kuma mutum ne kyakkyawa, an haife shi bayan Absalom. 7 Ya gama baki da Yowab ɗan Zeruya, da Abiyata, firist. Su kuwa suka yarda su goyi bayansa, su taimake shi. 8 Amma Zadok, firist, da Benaiya ɗan Yehoyada, da annabi Natan, da Shimai, da Reyi, da masu tsaron lafiyar Dawuda, ba su goyi bayan Adonija ba. 9 Adonija kuwa ya yi hadaya da tumaki, da bijimai, da turkakkun dabbobi kusa da Dutsen Zohelet, wato dutsen maciji, wanda yake gab da Enrogel. Ya gayyaci dukan 'yan'uwansa, 'ya'yan sarki, da fādawan da suke a Yahuza. 10 Amma bai gayyaci annabi Natan, ko Benaiya, ko masu tsaron lafiyar sarki, ko Sulemanu ɗan'uwansa ba.

An Zaɓi Sulemanu ya Zama Sarki

11 Natan kuwa ya ce wa Bat-sheba tsohuwar Sulemanu, “Ba ki ji cewa Adonija ɗan Haggit ya zama sarki ba? Sarki Dawuda kuma bai sani ba! 12 Yanzu sai ki zo in ba ki shawara domin ki tsira da ranki da na ɗanki Sulemanu. 13 Ki tafi wurin sarki Dawuda, ki ce masa, ‘Ran sarki ya daɗe, ashe, ba ka rantse mini ba cewa, Sulemanu ɗana zai yi mulki bayanka, shi ne kuma zai hau gadon sarautarka? Me ya sa Adonija ya zama sarki?’ 14 Sa'ad da kike magana da sarki, ni ma zan shigo in tabbatar da maganarki.” 15 Bat-sheba kuwa ta tafi wurin sarki a ɗakinsa. Sarki dai ya tsufa ƙwarai, Abishag, yarinyar nan daga Shunem, tana yi masa hidima. 16 Bat-sheba ta rusuna, ta gai da sarki. Sai sarki ya ce mata, “Me kike so?” 17 Ta ce masa, “Ranka ya daɗe, ka riga ka rantse mini da sunan Ubangiji Allahnka, ka ce, ‘Sulemanu ɗanki zai yi mulki bayana, shi ne zai hau gadon sarautata.’ 18 To, ga shi Adonija ya zama sarki, ko da yake kai ba ka sani ba. 19 Ya miƙa hadaya da bijimai, da turkakkun dabbobi, da tumaki da yawa. Ya kuma gayyaci dukan 'ya'yan sarki, da Abiyata firist, da Yowab shugaban sojoji, amma bai gayyaci Sulemanu ɗanka ba. 20 Ranka ya daɗe, yanzu idanun dukan jama'ar Isra'ila suna kallonka don su ga wanda za ka nuna musu ya gāji gadon sarauta a bayanka. 21 In ba haka ba, zai zama sa'ad da ka rasu za a ɗauka ni da ɗana, sulemanu, masu laifi ne.” 22 Tana cikin magana da sarki, sai annabi Natan ya zo. 23 Aka faɗa wa sarki cewa, ga annabi Natan. Da ya zo gaban sarki, sai ya rusuna ya gaishe shi. 24 Sa'an nan ya ce, “Ranka ya daɗe, ashe, ko ka sanar, cewa Adonija ne zai gaje ka? 25 Gama yau ɗin nan ya tafi ya miƙa hadaya da bijimai, da turkakkun dabbobi, da tumaki da yawa. Ya kuma gayyaci dukan 'ya'yan sarki, da Yowab shugaban sojoji, da Abiyata firist. Ga shi, suna ci suna sha tare da shi, suna cewa, ‘Ran sarki Adonija ya daɗe.’ 26 Amma ni da Zadok, firist, da Benaiya ɗan Yehoyada, da ɗanka Sulemanu, bai gayyace mu ba. 27 Ranka ya daɗe ko ka tabbatar da haka, amma ba ka ko faɗa wa fādawanka, cewa ga wanda zai gāje ka ba?”

An Naɗa Sulemanu Sarki

28 Sai sarki Dawuda ya ce, “A kirawo mini Bat-sheba.” Ta kuwa zo gaban sarki. 29 Sa'an nan ya ce mata, “Na yi miki alkawari da Ubangiji mai rai wanda ya fanshe ni daga dukan wahala, 30 a yau ne kuma zan cika alkawarin da na yi miki da sunan Ubangiji Allah na Isra'ila, cewa Sulemanu, ɗanki, zai yi mulki a bayana, shi ne zai hau gadon sarautata ya gāje ni, haka kuwa zan yi yau.” 31 Bat-sheba kuwa ta rusuna har ƙasa, domin girmamawa, ta ce, “Ran ubangijina sarki ya daɗe har abada!” 32 Sarki Dawuda kuma ya ce, “Ku kirawo mini Zadok, firist, da annabi Natan, da Benaiya ɗan Yehoyada.” Su kuwa suka zo gaban sarki, 33 ya ce musu, “Ku tafi tare da fādawana, ku sa Sulemanu, ɗana, ya hau alfadarina, ku kai shi Gihon, 34 a can Zadok firist, da annabi Natan za su zuba masa mai, ya zama sarkin Isra'ila, sa'an nan ku busa ƙaho, ku ce, ‘Ran sarki Sulemanu ya daɗe.’ 35 Sa'an nan ku zo da shi ya hau gadon sarautata, gama shi ne zai zama sarki a maimakona, na sa shi ya zama mai mulkin Isra'ila da Yahuza.” 36 Sai Benaiya ɗan Yehoyada ya ce wa sarki, “Za a yi haka, Ubangiji Allah na ubangijina, sarki, ya tabbatar da haka. 37 Kamar yadda Ubangiji ya kasance tare da ubangijina, sarki, haka kuma ya kasance tare da Sulemanu, ya fifita gadon sarautarsa fiye da na ubangijina, sarki Dawuda!” 38 Saboda haka sai Zadok, firist, da annabi Natan, da Benaiya ɗan Yehoyada, da masu tsaron lafiyar sarki, suka tafi, suka sa Sulemanu ya hau alfadarin sarki Dawuda. Suka kuma kai shi Gihon. 39 A can ne Zadok, firist, ya ɗauki ƙahon mai wanda ya kawo daga alfarwa ta sujada, ya zuba wa Sulemanu. Sa'an nan suka busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka ce, “Ran sarki Sulemanu ya daɗe.” 40 Mutane duka kuwa suka bi shi, suna bushe-bushe, suna murna da yawa, kamar ƙasa ta tsage saboda sowarsu. 41 Adonija da dukan baƙin da suke tare da shi suka ji amon sowa bayan da suka gama cin abinci. Da Yowab ya ji busar ƙaho, sai ya ce, “Mene ne dalilin wannan hargitsi a birni?” 42 Yana cikin magana ke nan sai ga Jonatan ɗan Abiyata, firist, ya zo. Adonija ya ce musu, “Shigo, gama kai nagarin mutum ne, ka kawo albishir.” 43 Jonatan kuwa ya ce wa Adonija, “A'a, gama ubangijinmu, sarki Dawuda, ya naɗa Sulemanu sarki. 44 Sarki ya aiki Zadok, firist, da annabi Natan, da Benaiya ɗan Yehoyada, da masu tsaron lafiyar sarki. Su kuwa suka sa Sulemanu ya hau alfadarin sarki. 45 Zadok firist, da annabi Natan kuma suka zuba masa mai a Gihon don ya zama sarki. Daga can suka tashi da murna don haka ake hayaniya a birnin. Wannan ita ce hayaniyar da kake ji. 46 Sulemanu ne sarki yanzu. 47 Banda wannan kuma, fādawa sun tafi su kai caffa ga sarki Dawuda, suna cewa, ‘Allahnka ya sa Sulemanu ya yi suna fiye da kai, ya kuma f�fita gadon sarautarsa fiye da naka.’ Sai sarki ya sunkuyar da kansa a gadonsa. 48 Sa'an nan ya ce, ‘Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na Isra'ila wanda ya sa ɗaya daga cikin zuriyata ya hau gadon sarautata yau, idona kuwa ya gani.’ ” 49 Sai baƙin Adonija duka suka tashi suna rawar jiki, kowa ya kama hanyarsa. 50 Adonija kuwa ya ji tsoron Sulemanu, sai ya tashi, ya tafi, ya kama zankayen bagade. 51 Aka faɗa wa Sulemanu cewa ga Adonija yana jin tsoron sarki Sulemanu, gama, ga shi, ya kama zankayen bagade, yana cewa, “Bari sarki Sulemanu ya rantse mini tukuna, cewa ba zai kashe ni ba.” 52 Sulemanu kuwa ya ce, “Idan ya nuna kansa nagarin mutum ne, ko gashin kansa guda ɗaya ba zai faɗi ƙasa ba, amma idan aka iske shi da mugunta, to, lalle kashe shi za a yi.” 53 Sarki Sulemanu kuwa ya aika aka kawo shi daga bagaden. Da ya zo, sai ya rusuna, ya gai da sarki Sulemanu. Sulemanu ya ce masa, “Tafi gidanka.”

1 Sarakuna 2

Gargaɗin da Dawuda ya Yi wa Sulemanu

1 Sa'ad da lokacin rasuwar Dawuda ya gabato, sai ya yi wa ɗansa Sulemanu gargaɗi na ƙarshe, ya ce, 2 “Ina gab da rasuwa yanzu. Saboda haka, ka ƙarfafa, ka yi jaruntaka. 3 Ka yi abin da Ubangiji Allahnka ya umarce ka. Ka yi biyayya da dokokinsa, da umarnansa, kamar yadda aka rubuta a dokokin Musa, domin ka yi nasara da dukan abin da kake yi da inda ka nufa duka, 4 domin Ubangiji ya cika maganar da ya faɗa mini cewa, ‘Idan 'ya'yanka suna lura da hanyarsu, sun yi tafiya a gabana da gaskiya da zuciya ɗaya, da dukan ransu, ba za ka rasa mutum wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba.’ 5 “Ka kuma san abin da Yowab ɗan Zeruya ya yi mini, yadda ya kashe shugabannin sojoji na Isra'ila su biyu, wato Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya zubar da jinin yaƙi a lokacin salama. Ya sa jinin yaƙi a kan ɗamararsa wadda take gindinsa, da kuma kan takalmansa da suke ƙafafunsa. 6 Ka san abin da za ka yi, kada ka bar shi ya mutu ta hanyar lafiya. 7 “Amma ka nuna alheri ga 'ya'yan Barzillai daga Gileyad, ka lura da su da kyau, gama sun nuna mini alheri sa'ad da nake gudu daga ɗan'uwanka, Absalom. 8 “Ga kuma Shimai ɗan Gera, daga garin Bahurim ta Biliyaminu. Shi ne ya yi mini mugun zagi sa'ad da na tafi Mahanayim, amma sa'ad da ya zo taryata a Urdun, sai na rantse masa da Ubangiji, na ce ba zan kashe shi ba. 9 Don haka dole ka hukunta shim, ka dai san abin da za ka yi da shi, lalle ne kuma za ka ga an kashe shi.”

Rasuwar Dawuda

10 Sa'an nan Dawuda ya rasu, aka binne shi a birnin Urushalima. 11 Ya yi shekara arba'in yana sarautar Isra'ila. Ya yi mulki shekara bakwai a Hebron, sa'an nan ya yi shekara talatin da uku yana mulki a Urushalima. 12 Sulemanu kuwa ya hau gadon sarautar ubansa, Dawuda. Mulkinsa kuma ya kahu sosai.

Mutuwar Adonija

13 Sa'an nan Adonija ɗan Haggit ya tafi wurin Bat-sheba, tsohuwar Sulemanu. Ta ce masa, “Ka zo lafiya?” Ya ce, “Lafiya lau.” 14 Sa'an nan ya ce, “Ina da wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “To, sai ka faɗa.” 15 Ya amsa ya ce, “Kin sani dai sarauta tawa ce. Ni ne kuwa mutanen Isra'ila duka suka sa zuciya zan ci sarautar, amma al'amarin ya sāke, sai sarautar ta zama ta ƙanena, gama tasa ce bisa ga nufin Allah. 16 Yanzu dai ina da roƙo guda zuwa gare ki, kada ki hana mini.” 17 Ta ce masa, “To, sai ka faɗa.” Sai ya ce, “In kin yarda ki yi magana da sarki Sulemanu, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce ya ba ni yarinyar nan, Abishag, daga Shunem, ta zama matata.” 18 Bat-sheba kuwa ta ce, “Da kyau, zan yi wa sarki magana dominka.” 19 Sa'an nan Bat-sheba ta tafi wurin sarki Sulemanu don ta yi magana da shi a kan Adonija. Sarki ya tashi domin ya tarye ta. Ya rusuna mata, sa'an nan ya zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo mata kujera, ta kuwa zauna a wajen damansa. 20 Sai ta ce, “Ina da wani ɗan roƙo a gare ka, kada ka hana mini shi.” Sarki ya ce mata, “Ya tsohuwata, sai ki faɗi abin da kike so, gama ba zan hana miki ba.” 21 Ta ce, “Bari a ba Adonija, ɗan'uwanka, Abishag daga Shunem, ta zama matarsa.” 22 Sai sarki Sulemanu ya amsa wa tsohuwarsa, ya ce, “Don me kika roƙar wa Adonija Abishag? Ki roƙar masa sarautar mana, gama shi wana ne, Abiyata, firist kuma, da Yowab ɗan Zeruya suna goyon bayansa.” 23 Sai sarki Sulemanu ya rantse da Ubangiji ya ce, “Allah ya kashe ni nan take idan ban sa Adonija ya biya wannan roƙo da ransa ba. 24 Ubangiji ya kafa ni sosai a gadon sarautar tsohona, Dawuda, ya kuma cika alkawarinsa, ya ba ni mulki da zuriyata. Na rantse za a kashe Adonija yau.” 25 Sai Sarki Sulemanu ya aiki Benaiya ɗan Yehoyada, ya kashe Adonija.

An Kori Abiyata an Kashe Yowab

26 Sarki kuma ya ce wa Abiyata, firist, “Ka koma ƙasarka ta gādo a Anatot, gama ka cancanci mutuwa, amma yanzu ba zan kashe ka ba domin ka ɗauki akwatin alkawari na Ubangiji Allah a gaban Dawuda, tsohona, domin kuma ka sha wahala duka tare da tsohona.” 27 Saboda haka Sulemanu ya kori Abiyata daga aikin firist na Ubangiji, ta haka aka cika maganar da Ubangiji ya faɗa a kan gidan Eli a Shilo. 28 Da Yowab ya ji labari, gama har shi ya goyi bayan Adonija, ko da yake bai goyi bayan Absalom ba, sai ya gudu zuwa alfarwa ta Ubangiji, ya kama zankayen bagade. 29 Sa'ad da aka faɗa wa sarki Sulemanu, Yowab ya gudu zuwa alfarwa ta Ubangiji, ga shi, yana wajen bagade, sai Sulemanu ya aiki Benaiya, ɗan Yehoyada, ya je ya kashe shi. 30 Benaiya kuwa ya tafi alfarwa ta Ubangiji, ya ce masa, “Sarki ya ce ka fito.” Amma Yowab ya ce, “A'a, a nan zan mutu.” Benaiya kuma ya je ya faɗa wa sarki abin da Yowab ya ce. 31 Sarki kuwa ya ce masa, “Ka yi yadda ya ce, ka kashe shi, ka binne shi, ta haka za ka kawar mana da hakkin jinin da Yowab ya zubar ba dalili. 32 Ubangiji zai ɗora masa alhakin mugayen ayyukansa, gama ya kashe mutum biyu ba da sanin tsohona Dawuda ba, waɗanda kuma suka fi shi adalci, wato Abner ɗan Ner, shugaban sojojin Isra'ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban sojojin Yahuza. 33 Don haka alhakin jininsu zai koma a kan zuriyar Yowab har abada, amma da Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da gadon sarautarsa, albarkar Ubangiji za ta zauna a kansu har abada.” 34 Benaiya ɗan Yehoyada kuwa ya shiga alfarwar ya kashe shi. Aka binne shi a gidansa a karkara. 35 Sa'an nan sarki ya naɗa Benaiya ɗan Yehoyada, shugaban sojoji a maimakon Yowab, ya kuma naɗa Zadok, firist, a maimakon Abiyata.

Mutuwar Shimai

36 Sai kuma sarki ya aika a kirawo Shimai. Sa'an nan ya ce masa, “Ka gina wa kanka gida a Urushalima, ka zauna a nan, kada ka fita ko kaɗan zuwa wani wuri. 37 Gama ran da ka fita, ka haye rafin Kidron, ka tabbata fa za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.” 38 Shimai kuwa ya ce wa sarki, “Abin da ka faɗa daidai ne, abin da ka ce in yi, zan yi, ranka ya daɗe.” Sai Shimai ya zauna a Urushalima kwanaki da yawa. 39 Amma bayan shekara uku, sai biyu daga cikin bayin Shimai suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma'aka, Sarkin Gat. Da aka faɗa wa Shimai, cewa bayinsa suna a Gat, 40 sai ya tashi, ya yi wa jakinsa shimfiɗa, ya tafi Gat wurin Akish don neman bayinsa. Ya kuwa komo da bayinsa daga Gat. 41 Da aka faɗa wa Sulemanu, cewa Shimai ya fita Urushalima, ya tafi Gat, ya komo 42 sai ya aika a kirawo Shimai, ya ce masa, “Ashe, ban sa ka ka rantse da Ubangiji ba, na kuma dokace ka da ƙarfi, cewa ka tabbata ran da ka fita zuwa ko'ina za ka mutu? Kai kuma ka ce mini, ‘Abin da ka ce daidai ne, zan yi biyayya.’ 43 To, me ya sa ka karya rantsuwar da ka yi da sunan Ubangiji, da kuma umarnin da na umarce ka?” 44 Sarki kuma ya ce masa, “Ka sani sarai irin duk muguntar da ka yi wa tsohona, Dawuda. Haka kuma Ubangiji zai sāka maka bisa ga muguntarka. 45 Amma Ubangiji zai sa mini albarka, ya kuma tabbatar da gadon sarautar Dawuda har abada.” 46 Sa'an nan sarki ya umarci Benaiya ɗan Yehoyada, ya tafi, ya kashe Shimai. Yanzu sarauta ta tabbata a hannun Sulemanu.

1 Sarakuna 3

Sulemanu ya Auri 'Yar Fir'auna

1 Sulemanu ya gama kai da Fir'auna, Sarkin Masar, ta wurin aure, domin ya auri 'yar Fir'auna, ya kawo ta birnin Dawuda kafin ya gama ginin gidan kansa, da Haikalin Ubangiji, da garun Urushalima. 2 Mutane suka yi ta miƙa hadayu a al'amudai dabam dabam, domin ba a gina haikalin Ubangiji ba tukuna. 3 Sulemanu ya ƙaunaci Ubangiji, ya yi tafiya bisa ga koyarwar tsohonsa, Dawuda, amma ya miƙa sadakoki da hadayu da yawa a al'amudai dabam dabam.

Addu'ar Sulemanu don Samun Hikima

4 Sarki kuwa ya tafi Gibeyon don ya miƙa hadaya, gama a can ne akwai babban al'amudi. Ya miƙa hadayu na ƙonawa guda dubu a kan wannan bagade. 5 Ubangiji kuwa ya bayyana ga Sulemanu cikin mafarki a Gibeyon da dare, ya ce masa, “Ka roƙi abin da kake so in ba ka.” 6 Sulemanu ya amsa ya ce, “Kai ne kake nuna ƙauna mai girma a koyaushe ga bawanka Dawuda, tsohona, domin ya yi tafiya a gabanka da aminci, da adalci, da tawali'u. Kai kuwa ka tabbatar masa da wannan ƙauna mai girma, ka kuma ba shi ɗa wanda zai hau gadon sarautarsa a wannan rana. 7 Yanzu, ya Ubangiji Allahna, ka naɗa ni sarki, a matsayin Dawuda, tsohona, ko da yake ni yaro ne ƙarami, ban ƙware ba. 8 Ga ni kuwa a tsakiyar jama'arka wadda ka zaɓa, jama'a mai yawa wadda ba ta ƙidayuwa saboda yawansu. 9 Domin haka ka ba ni hikima ta yi wa jama'arka shari'a, domin in rarrabe tsakanin nagarta da mugunta, gama wane ni in iya mallakar jama'arka mai yawa haka?” 10 Ubangiji kuwa ya ji daɗin abin da Sulemanu ya roƙa. 11 Ya kuma ce masa. “Da yake ka roƙi wannan, ba ka roƙar wa kanka yawan kwanaki, ko wadata ba, ko kuma ran maƙiyanka, amma ka roƙa a ba ka hikima yadda za ka mallaki jama'a, 12 to, zan yi maka yadda ka roƙa, zan ba ka zuciya ta hikima da ganewa har ba wanda ya kai kamarka, ba kuwa wanda zai kai kamarka. 13 Na kuma ba ka abin da ba ka roƙa ba, wato wadata da girma. Domin haka a zamaninka ba za a sami wani sarki kamarka ba. 14 Idan za ka yi mini biyayya ka kuma kiyaye dokokina, da umarnaina kamar yadda tsohonka Dawuda ya yi, to, zan ba ka tsawon rai.” 15 Da Sulemanu ya farka, ashe, mafarki ne, Sa'an nan ya zo Urushalima, ya tafi ya tsaya a gaban akwatin alkawarin Ubangiji. Ya miƙa hadayu na ƙonawa, da hadayu na salama. Ya kuma yi wa dukan barorinsa biki.

Sulemanu ya Shara'anta Mawuyaciyar Matsala

16 Wata rana waɗansu mata masu zaman kansu, su biyu, suka zo gaban sarki. 17 Sai ɗayar ta ce, “Ran sarki ya daɗe, ni da wannan mata a gida ɗaya muke zaune, sai na haifi ɗa namiji, ita kuwa tana nan a gidan. 18 Bayan kwana uku da haihuwata, ita ma sai ta haihu. Mu kaɗai ne, ba kowa tare da mu a gidan. 19 Ana nan sai ɗan wannan mata ya mutu da dare, domin ta kwanta a kansa. 20 Da tsakar daren sai ta tashi, ta ɗauke ɗana daga wurina, sa'ad da nake barci, ta kai shi gadonta, sa'an nan ta kwantar da mataccen ɗanta a wurina. 21 Sa'ad da na tashi da safe don in ba ɗana mama, sai ga shi, matacce. Da na duba sosai, sai na ga ba nawa ba ne, wanda na haifa.” 22 Amma ɗaya matar ta ce, “A'a, mai ran shi ne nawa, mataccen kuwa shi ne naki!” Sai ta fari ta ce, “A'a, mataccen shi ne naki, mai rai ne nawa!” Haka suka yi ta gardama a gaban sarki. 23 Sa'an nan sarki ya ce, “To, kowaccenku ta ce mai ran shi ne nata, mataccen kuwa shi ne na waccan.” 24 Sai ya umarta a kawo takobi. Da aka kawo takobin, 25 sai ya ce, “A raba ɗan nan mai rai kashi biyu, kowacce ta ɗauki rabi.” 26 Saboda zuciyar mahaifiyar ta ainihi ta cika da juyayin ɗanta, ta ce wa sarki, “Ranka ya daɗe kada a kashe yaron! A ba ta!” Amma ɗayar ta ce, “Kada a ba kowa daga cikinmu, a ci gaba a raba shi.” 27 Sa'an nan Sulemanu ya ce, “Kada ku kashe yaron! Ku miƙa wa ta farin, ita ce mahaifiyarsa ta ainihi.” 28 Sa'ad da dukan mutanen Isra'ila suka ji shari'ar da sarki ya yanke, sai suka girmama shi ƙwarai, gama sun gane Allah ya ba shi hikimar daidaita husuma sosai.

1 Sarakuna 4

Fādawan Sulemanu

1 Sarki Sulemanu shi ne sarkin dukan Isra'ila, kuma su ne manyan fādawansa, Azariya ɗan Zadok shi ne firist. Elihoref da Ahija 'ya'yan Seraiya, maza, su ne magatakarda. Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne mai lura da takardu. Benaiya ɗan Yehoyada shi ne shugaban sojoji. Zadok da Abiyata su ne firistoci. Azariya ɗan Natan shi ne shugaban hakimai. Zabud ɗan Natan shi ne mashawarcin sarki da abokinsa. Ahishar shi ne mai lura da bayin fāda. Adoniram ɗan Abda, shi ne mai lura da aikin gandu. 7 Sulemanu kuma ya naɗa mutum goma sha biyu a lardunan Isra'ila. Su ne za su tanaji abinci daga lardunansu domin sarki da iyalinsa. Kowane hakimi yakan kawo abinci wata guda a shekara. su ne hakimai, da kuma lardunan da suke aiki. Ben-hur yana a ƙasar tudu ta Ifraimu. Ben-deker shi ne mai lura da biranen Makaz, da Shalim, da Bet-shemesh, da Elon-bet-hanan. Ben-hesed shi ne mai lura da Arubot, da Soko, da dukan ƙasar Hefer. Ben-abinadab shi ne mai lura da dukan jihar Dor, ya auri Tafat 'yar Sulemanu. Ba'ana ɗan Ahilud shi ne mai lura da biranen Ta'anak da Magiddo, da dukan jihar Bet-sheyan, kusa da garin Zaretan, kudu da garin Yezreyel, har zuwa birnin Abel mehola da birnin Yokmeyam. Ben-geber shi ne mai fura da birnin Ramot-gileyad, da ƙauyukan Yayir da Manassa, waɗanda suke a Gileyad, da kuma yankin Argob, wanda yake a Bashan, duka dai akwai manyan garuruwa sittin masu garu da ƙyamare na tagulla. Abinadab ɗan Iddo shi ne mai lura da birnin Mahanayim. Ahimawaz shi ne mai lura da Naftali, ya auri Basemat 'yar Sulemanu. Ba'ana ɗan Hushai shi ne mai lura da Ashiru da garin Beyalot. Jehoshafat ɗan Faruwa shi ne mai lura da Issaka. Shimai ɗan Ila shi ne mai lura da ƙasar Biliyaminu. Geber ɗan Uri shi ne mai lura da jihar Gileyad wadda Sihon Sarkin Amoriyawa, da Og Sarkin Bashan, suka mallaka. Bayan waɗannan sha biyu akwai hakimi ɗaya da yake kan ƙasar Yahuza.

Hikimar Sulemanu da Wadatarsa

20 Mutanen Yahuza da na Isra'ila suka yi yawa kamar yashi a bakin teku. Suka ci, suka sha, suka yi murna. 21 Sulemanu ya sarauci dukan mulkoki tun daga Kogin Yufiretis a gabas, har zuwa ƙasar Filistiyawa a yamma, daga kudu kuma har zuwa iyakar Masar. Su kuwa suka yi ta kawo wa Sulemanu harajinsu, ya kuwa mallake su dukan kwanakin ransa. 22 Abincin gidan Sulemanu na rana ɗaya garwa talatin na lallausan gari ne, da garwa sittin na gari, 23 da turkakkun bijimai goma, da shanu ashirin daga makiyaya, da tumaki ɗari banda kishimai, da bareyi, da batsiyoyi, da kaji masu ƙiba. 24 Sulemanu ya mallaki dukan ƙasar da take yamma da Kogin Yufiretis, daga Tifsa har zuwa birnin Gaza. Ya mallaki dukan sarakuna yammacin Yufiretis. Akwai zaman lafiya ko'ina a mulkinsa da ƙasashen maƙwabta. 25 Mutanen Yahuza da na Isra'ila suka zauna lafiya tun daga Dan har Biyersheba. Kowa ya yi zamansa a gida dukan kwanakin Sulemanu. 26 Sulemanu kuma yana da rumfuna dubu arba'in (40,000 ) domin dawakan karusansa, da mahayan dawakai dubu goma sha biyu (12,000 ). 27 Hakiman nan nasa sha biyu, kowa ya kawo wa Sulemanu abinci, duk da waɗanda suke zuwa teburin cin abincin Sulemanu. Kowane hakimi yakan kawo abincin da za a ci na wata guda. Ba su fasa kawowa ba. 28 Suka kuma kawo sha'ir da ingirci domin dawakan da suke jan karusai, da sauran dabbobin da suke aiki. Kowanne bisa ga abin da aka sa masa. 29 Allah ya ba Sulemanu hikima, da fahimi, da sani, har ba su misaltuwa. 30 Hikimar Sulemanu ta fi ta dukan mutanen gabas, ko masu hikima na Masar. 31 Gama ya fi dukan mutane hikima, ya fi Etan Ba'ezrahe, da Heman, da Kalkol, da Darda, 'ya'yan Mahol. Ya shahara a ƙasashen da suke kewaye da shi. 32 Ya yi karin magana dubu uku, ya kuma yi waƙoƙi fiye da dubu. 33 Ya yi magana a kan itatuwa da tsire-tsire tun daga itacen al'ul da yake a Lebanon har zuwa ɗaɗɗoya da take tsirowa a jikin bango. Ya kuma yi magana a kan dabbobi, da tsuntsaye, da abubuwa masu rarrafe, da kifaye. 34 Sarakuna daga ko'ina a duniya, sun ji labarin hikimarsa, suka kuma aika da mutane don su ji shi.

1 Sarakuna 5

Yarjejeniya Tsakanin Sulemanu da Hiram

1 Hiram, Sarkin Taya, ya aiki jakadunsa zuwa wurin Sulemanu, sa'ad da ya ji ya gāji tsohonsa, gama Hiram abokin Dawuda ne ƙwarai dukan kwanakinsa. 2 Sai Sulemanu ya aika wurin Hiram, ya ce, 3 “Ka sani tsohona, Dawuda, bai iya gina Haikalin yin sujada ga Ubangiji Allahnsa ba saboda fama da yaƙe-yaƙe da maƙiyan da suke kewaye da shi, kafin Ubangiji ya mallakar masa da su. 4 Amma yanzu Ubangiji Allahna ya hutasshe ni ta kowace fuska, ba fitina ko masifa. 5 Ubangiji kuma ya yi wa tsohona Dawuda alkawari ya ce, ‘Ɗanka, wanda zai gāje ka, shi zai gina mini Haikali.’ Yanzu kuwa na yi niyyar gina wannan haikali domin sujada ga Ubangiji Allahna. 6 Saboda haka sai ka sa a saro mini itatuwan al'ul na Lebanon. Barorina za su haɗu da barorinka, ni kuwa zan biya ka aikin da barorinka za su yi bisa ga yadda ka ce, gama ka sani ba wani daga cikin mutanena da ya iya saran katako kamar mutanenka.” 7 Da Hiram ya ji maganar Sulemanu, sai ya yi murna ƙwarai, ya ce, “Yabo ga Ubangiji saboda wannan rana, gama ya ba Dawuda ɗa mai hikima da zai shugabanci wannan babbar jama'a.” 8 Sa'an nan Hiram ya aika wurin Sulemanu, ya ce, “Na ji saƙonka da ka aiko mini, a shirye nake in yi maka dukan abin da kake bukata a kan katakan itacen al'ul, da na fir. 9 Barorina za su kawo su daga Lebanon zuwa teku. Zan sa a yi gadon fito da su, su bi teku zuwa inda kake so, a can mutanena za su warware su, sa'an nan naka mutane su kwashe su. Kai kuma ka ba da abinci ga mutanena.” 10 Sai Hiram ya ba Sulemanu dukan katakan itacen al'ul da na fir da yake bukata, 11 Sulemanu kuwa yakan ba Hiram alkama mudu dubu ashirin (20,000 ), da tattaccen man zaitun ma'auni dubu ashirin (20,000 ) kowace shekara domin ya ciyar da mutanensa. 12 Ubangiji kuwa ya ba Sulemanu hikima kamar yadda ya yi masa alkawari. Akwai kuma zaman lafiya tsakanin Hiram da Sulemanu, suka kuma ƙulla yarjejeniya da juna. 13 Sarki Sulemanu kuwa ya sa a yi aikin tilas daga cikin Isra'ila duka. Waɗanda aka samu da za su yi aikin tilas ɗin mutum dubu talatin (30,000 ) ne. 14 Ya riƙa aikawa da su zuwa Lebanon, ya raba su mutum dubu goma goma (10,000 ) su yi wata ɗaya ɗaya, sa'an nan su komo gida su yi wata biyu biyu. Adoniram shi ne shugaban aikin tilas ɗin. 15 Sulemanu kuma yana da mutum dubu saba'in (70,000 ) a ƙasar tuddai masu haƙar duwatsu, da dubu tamanin (80,000 ) masu ɗauko duwatsun. 16 Banda waɗannan kuma, Sulemanu ya sa shugabanni dubu uku da ɗari uku (3,300 ) waɗanda suke lura da aikin, da mutanen da suke yin aikin. 17 Bisa ga umarnin sarki Sulemanu suka sassaƙa manyan duwatsu kyawawa don kafa harsashin ginin Haikali. 18 Sai maginan Sulemanu, da na Hiram, da mutanen Gebal suka shirya duwatsu da katakai da za a gina Haikalin.

1 Sarakuna 6

Sulemanu ya Gina Haikalin Ubangiji

1 A shekara ta arbaminya da tamanin bayan fitowar mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar, a shekara ta huɗu ta sarautar Sulemanu, Sarkin Isra'ila, a watan biyu, wato watan Zib, sai Sulemanu ya fara gina Haikalin Ubangiji. 2 Haikalin da sarki Sulemanu ya gina wa Ubangiji, tsawonsa kamu sittin, fāɗinsa kamu ashirin, tsayinsa kamu talatin ne. 3 Tsawon shirayin da yake a gaban Haikalin kamu ashirin ne, wato daidai da fāɗin Haikalin. Fāɗinsa kuma daga gaban Haikalin kamu goma ne. 4 Ya yi wa Haikalin tagogi, suna da fāɗi daga ciki fiye da waje. 5 Ya kuma gina bene mai ɗakuna a jikin bangon Haikalin daga gefe, da kuma bayan Haikalin, har hawa uku, kowanne kamu bakwai da rabi. 6 Fāɗin ɗakuna na ƙasa kamu biyar ne. Fāɗin ɗakunan hawa na biyu kamu shida ne. Fāɗin ɗakunan hawa na uku kuwa kamu bakwai ne. Bangaye a ƙasa sun fi na saman kauri, don ɗakunan su zauna sosai, ba tare da an kafa ginshiƙai a cikin ɗakunan ba. 7 An gina Haikalin da duwatsun da aka sassaka tun daga can wurin da aka haƙo su, don haka ba a ji amon guduma, ko na gatari, ko na wani kayan aiki irin na ƙarfe ba, sa'ad da ake ginin Haikalin. 8 Ƙofar domin ɗakuna na ƙasa tana wajen dama na Haikalin. Akwai matakai zuwa hawa na tsakiya da zuwa bene na uku. 9 Ta haka ya gina Haikalin, ya rufe shi da katakan itacen al'ul. 10 Benayen da ya gina kewaye da Haikalin, kowane bene tsayinsa kamu biyar. An haɗa su da Haikalin da katakan itacen al'ul. 11 Ubangiji ya ce wa Sulemanu, 12 “Idan ka yi biyayya da dokokina da umarnaina, to, zan cika maka alkawarin da na yi wa tsohonka Dawuda. 13 Zan zauna tare da mutanena, wato Isra'ila, a wannan Haikali da kake ginawa, ba kuwa zan taɓa rabuwa da su ba.” 14 Haka fa Sulemanu ya gama gina Haikali.

Kayan Haikali

15 Ya yi bango na ciki da katakan itacen al'ul tun daga ƙasa har sama, ya kuma rufe daɓen da itacen fir. 16 Ya gina Wuri Mafi Tsarki na can ciki, ya gina shi can ƙuryar Haikalin. Tsayinsa kamu ashirin ne, an manne masa katakan itacen al'ul tun daga ƙasa har sama. 17 Tsawon sauran Wuri Mafi Tsarki kuwa kamu arba'in ne. 18 Katakan itacen al'ul na cikin Haikalin, an yi musu zāne mai fasalin gora da na furanni buɗaɗɗu. An rufe bangon daga ciki duka da itacen al'ul, har ba a ganin duwatsun ginin. 19 Ya shirya Wuri Mafi Tsarki na can cikin Haikalin domin a ajiye akwatin alkawari na Ubangiji. 20 Tsawon Wuri Mafi Tsarki na can ciki kamu ashirin ne, fāɗinsa kamu ashirin, tsayinsa kuma kamu ashirin. Ya dalaye shi da zinariya tsantsa. Ya kuma yi bagadensa da itacen al'ul. 21 Sulemanu ya dalaye cikin Haikalin da zinariya tsantsa. Ya kuma gifta sarƙoƙin zinariya a gaban Wuri Mafi Tsarki na can ciki, sa'an nan ya dalaye su da zinariya. 22 Ya dalaye dukan cikin Haikalin da zinariya, ya kuma dalaye bagaden da yake Wuri Mafi Tsarki na can ciki, da zinariya. 23 Ya yi kerubobi guda biyu da itacen zaitun, ya sa su cikin Wuri Mafi Tsarki na can ciki. Tsayin kowane kerub kamu goma ne. kerubobin irinsu ɗaya girmansu kuma ɗaya. Tsawon kowane fiffike na kerub ɗin kamu biyar, wato tsawon daga ƙarshen wannan fiffike zuwa ƙarshen wancan fiffike kamu goma ne. 26 Tsayin kowane kerub kamu goma ne. 27 Ya sa kerubobin daura da juna a can cikin Haikali domin fikafikan su taɓi juna a tsakiya kowane ɗayan kuma ya taɓi bango. 28 Ya dalaye kerubobin da zinariya. 29 Ya zana siffofin kerubobi, da na itatuwan dabino, da na furanni a dukan bangon Haikalin, wato bango na Wuri Mai Tsarki da Wuri Mafi Tsarki na can ciki. 30 Har daɓen ƙasa, ya dalaye shi da zinariya. 31 Ya yi ƙofa biyu na shiga Wuri Mafi Tsarki na can ciki da itacen zaitun. A saman ƙofar ya yi baka. 32 Sai ya zazzāna siffofin kerubobi, da na itatuwan dabino, da na furanni a kan ƙofofi duka biyu, sa'an nan ya dalaye duk ƙofofin da zinariya. 33 Ya yi wa Haikalin madogaran ƙofa masu ƙusurwa huɗu da itacen zaitun. 34 Ya kuma yi ƙyamare biyu a haɗe, ya yi su da itacen fir, 35 ya zazzāna ya adanta su da siffofin kerubobi, da na itatuwan dabino, da na furanni. Sa'an nan ya dalaye su da zinariya bai ɗaya. 36 Ya gina shirayi na ciki da sassaƙaƙƙun duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katakan itacen al'ul. 37 A shekara ta huɗu ta sarautar Sulemanu aka kafa harsashin ginin Haikalin Ubangiji a watan biyu, wato watan Zib. 38 A shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Sulemanu a watan Bul, wato watan takwas, aka gama ginin Haikalin, daidai yadda aka zayyana fasalinsa. Sulemanu ya yi shekara bakwai yana ginin Haikalin.

1 Sarakuna 7

Fādar Sulemanu

1 Sulemanu ya yi shekara goma sha uku yana gina gidansa kafin ya gama shi duka. 2 Ya kuma gina wani ɗaki da katakai daga kurmin Lebanon, tsawonsa kamu ɗari, faɗinsa kuma kamu hamsin, tsayinsa kuwa kamu talatin, a bisa jeri huɗu na ginshiƙan itacen al'ul. Aka shimfiɗa katakan itacen al'ul a bisa ginshiƙan. 3 Aka rufe shi da katakan al'ul a bisa ɗakuna arba'in da biyar da suke gefe, waɗanda suke bisa ginshiƙai. Ɗakuna goma sha biyar a kowane jeri har jeri uku. 4 Aka kuma yi tagogi masu sandunan ƙarfe, jeri uku, kowace taga tana daura da 'yar'uwarta, har jeri uku. 5 Dukan ƙofofin da madogaransu murabba'i ne, taga kuma tana daura da 'yar'uwarta har jeri uku. 6 Ya yi babban shirayi mai ginshiƙai, tsawonsa kamu hamsin, faɗinsa kamu talatin. Akwai kuma wani shirayi mai ginshiƙai a gabansa. 7 Ya kuma gina shirayi ta sarauta inda zai riƙa yin shari'a, ya rufe dukan daɓenta da itacen al'ul. 8 Ya gina gidan da zai zauna a farfajiya na ciki, wajen shirayi. Ya kuma gina wa matarsa, 'yar Fir'auna, gida irin wannan. 9 Aikin gine-ginen nan, an yi shi da duwatsu masu tamani tun daga tushen har zuwa rufin. Sai da aka auna duwatsun sa'an nan aka yanka su da zarto, ciki da baya daidai da juna. 10 An kafa harsashin ginin da manyan duwatsu masu tsada, waɗansu kamu takwas waɗansu goma. 11 Daga sama kuma akwai duwatsu masu tsada waɗanda aka yanka su bisa ga ma'auni, da kuma itacen al'ul. 12 Babbar farfajiyar fāda, da filin Haikali na ciki da shirayin Haikalin yana da bangaye da jerin katakan al'ul domin kowane jeri uku na yankakkun duwatsu.

Aikin Huram

13 Sarki Sulemanu kuwa ya aika a kawo Huram daga Taya, gwanin aikin tagulla ne. 14 Shi ɗan wata mata ne daga kabilar Naftali wadda mijinta ya rasu. Huram mutumin Taya ne, maƙerin tagulla. Yana da hikima, da fahimi, da fasaha na iya yin kowane irin aiki da tagulla. Ya kuwa amsa kiran sarki Sulemanu, ya zo ya yi masa dukan aikinsa. 15 Ya kuwa yi ginshiƙi biyu na zubi da tagulla. Kowane ginshiƙi tsayinsa kamu goma sha takwas ne, da guru mai kamu goma sha biyu kewaye da shi. 16 Ya kuma yi dajiya biyu ta zubi da tagulla don a sa a kan ginshiƙan. Tsayin kowace dajiya kamu biyar ne. 17 Ya yi wa kowace dajiya da take kan ginshiƙan ragogi da tukakkun sarƙoƙi. Kowace dajiya tana da guda bakwai. 18 Ta haka ya yi ginshiƙai jeri biyu kewaye da raga don rufe dajiya wadda take da siffofin rumman, haka kuma ya yi wa ɗaya dajiyar. 19 Dajiyar da take kan ginshiƙai na cikin shirayin an yi su da fasalin bi-rana kamu huɗu huɗu. 20 Dajiyar tana kan ginshiƙan nan biyu kusa da wani abu mai kama da gammo, wanda yake kusa da ragar. Akwai jeri biyu na siffofin rumman guda ɗari biyu a kewaye da dajiyar. 21 Ya kafa ginshiƙan a shirayin Haikalin. Ya kafa ginshiƙi ɗaya a wajen dama, ya sa masa suna, Yakin, wato Allah ya kafa. Ya kafa ɗaya ginshiƙin a wajen hagu, ya sa masa suna Bo'aza, wato da ƙarfin Allah. 22 A bisa kawunan ginshiƙan akwai dajiya masu fasalin bi-rana. Haka aka gama aikin ginshiƙan. 23 Huram kuma ya yi kewayayyiyar babbar kwatarniya ta zubi da tagulla. Faɗinta kamu goma ne, tsayinta kuwa kamu biyar, da'irarta kuma kamu talatin ne. 24 Akwai goruna kewaye da gefensa. Gora goma a kowane kamu ɗaya. Suka kewaye kwatarniya. Gorunan jeri biyu ne, an yi zubinsu haɗe da kwatarniyar. 25 Aka ɗora ta a kan siffofin bijimai goma sha biyu. Siffofin bijimai uku suna fuskantar gabas, uku kuma suna fuskantar yamma, uku suna fuskantar kudu, uku kuma suna fuskantar arewa. An ɗora kwatarniya a kansu. Gindinsu duka na wajen ciki. 26 Kaurin kwatarniya ya kai taƙin hannu guda. An yi gefenta kamar finjali, kamar kuma furen bi-rana. Takan ci garwa dubu biyu. 27 Ya kuma yi dakali goma da tagulla. Kowane dakali tsawonsa kamu huɗu, faɗinsa kuma kamu huɗu, tsayinsa kuwa kamu uku ne. 28 Yadda aka yi dakalan ke nan, dakalan suna da sassa, sassan kuma suna da mahaɗai. 29 Aka zana hotunan zakoki, da na bijimai, da na kerubobi a kan sassan. A kan mahaɗan kuma akwai gammo, aka zana hotunan furanni a ƙarƙashin zakokin da bijiman. 30 Kowane dakali yana da ƙafa huɗu na tagulla kamar na karusa, da sandunan tagulla don sa kwatarniya. A kusurwoyin akwai abubuwa na zubi don tallabar kwatarniya. An zana furanni a kowane gefensu. 31 Bakinsa daga cikin dajiyar ya yi sama kamu guda. Bakin da'ira ne kamar fasalin gammo, kamu ɗaya da rabi. Akwai zāne-zāne a bakin. Sassan murabba'i ne, ba da'ira ba. 32 Ƙafafu huɗu ɗin, suna ƙarƙashin sassan. Sandunan ƙafafun a haɗe suke da dakalan. Tsayin kowace ƙafa kuwa kamu ɗaya da rabi ne. 33 Ƙafafun suna kama da ƙafafun karusa. Sandunan ƙafafun, da gyaffansu, da kome na ƙafafun duka na zubi ne. 34 Akwai ginshiƙi huɗu daga ƙarƙashin kowane dakali. Ginshiƙan suna haɗe da dakalan. 35 Akwai wani abu kamar gammo mai tsayi rabin kamu a kan dakalin. Ginshiƙan kuma da sassan a haɗe suke da dakalin. 36 Ya zana siffofin kerubobi, da na zakoki, da na itatuwan dabino a jikin ginshiƙan da sassan a duk inda ya ga akwai fili. Ya kuma zana furanni kewaye da su. 37 Haka aka yi dakalai, dukansu iri ɗaya ne, girmansu da fasalinsu kuma iri ɗaya ne. 38 Ya kuma yi daruna na tagulla guda goma. Kowane daro yana cin misalin garwa tamanin. Kowane daro kamu huɗu ne. Kowane dakali yana da daro ɗaya. 39 Ya kafa dakali biyar a gefen dama na Haikalin, ya kuma kafa biyar a gefen hagu na Haikalin. Ya kuma sa kwatarniya na zubi a gefen dama na Haikalin, wajen kusurwar gabas maso kudu.

Jerin Kayan Haikali

40-45 Huram kuma ya yi tukwanen ƙarfe da manyan cokula, da daruna. Haka Huram ya gama dukan aikin da ya yi wa Sulemanu a cikin Haikalin Ubangiji. Ga abin da ya yi. ginshiƙai biyu dajiya da take a kawunan ginshiƙan raga biyu don rufe dajiyar da take a kawunan ginshiƙai siffofin rumman ɗari huɗu domin raga biyu ɗin, da jeri biyu na siffofin rumman domin kowace raga don a rufe dajiyar da take a kawunan ginshiƙan dakalai goma daruna goma a kan dakalan kwatarniya ɗaya siffofin bijimai guda goma sha biyu da kwatarniya take zaune a kai, tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da kwanoni Dukan kayayyakin aiki a cikin Haikalin Ubangiji waɗanda Huram ya yi wa sarki Sulemanu, an yi su ne da gogaggiyar tagulla. 46 Sarki ya sa a yi zubinsu a filin Urdun a ƙasar yumɓun da yake tsakanin Sukkot da Zaretan. 47 Sulemanu bai auna nauyin kayayyakin aikin ba domin sun cika yawa. Ba a kuma san nauyin tagullar ba. 48-50 Sulemanu ya yi dukan kayayyakin aikin da suke na Haikalin Ubangiji. bagaden zinariya teburin zinariya inda ake ajiye gurasar ajiyewa alkuki na zinariya guda biyar a gefen dama, biyar kuma a gefen hagu a gaban Wuri Mafi Tsarki na can ciki furanni fitilu arautaki finjalai na zinariya hantsuka daruna cokula farantan wuta na zinariya tsantsa almanani na zinariya domin ƙofofin ɗaki na can cikin Haikali, wato Wuri Mafi Tsarki, da ƙofofin Haikalin 51 Haka sarki Sulemanu ya gama dukan aikin Haikalin Ubangiji. Sai ya kawo abubuwan da tsohonsa Dawuda ya keɓe, wato azurfa, da zinariya, da kayayyakin aiki, ya ajiye su cikin taskokin Haikalin Ubangiji.

1 Sarakuna 8

Sulemanu ya Kawo Akwatin Alkawari cikin Haikali

1 Sai Sulemanu ya sa dattawan Isra'ila duka, da shugabannin kabilai, da shugabannin dangi dangi na Isra'ila, su hallara a gabansa a Urushalima, domin su kawo akwatin alkawari na Ubangiji daga Sihiyona, birnin Dawuda, zuwa Haikali. 2 Dukan jama'ar Isra'ila suka taru gaban sarki Sulemanu, wurin biki a watan Etanim, wato wata na bakwai. 3 Dukan dattawan Isra'ila suka zo, sai firistoci suka ɗauki akwatin alkawarin, 4 suka kawo tare da alfarwa ta sujada, da dukan tsarkakan tasoshin da suke cikin alfarwar. Firistoci da Lawiyawa suka kawo su. 5 Sarki Sulemanu kuwa tare da dukan taron jama'ar Isra'ila, waɗanda suka taru a gabansa, suna tare a gaban akwatin alkawari, suna ta miƙa sadakoki, da tumaki, da bijimai masu yawa, har ba su ƙidayuwa. 6 Sa'an nan firistoci suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji suka sa a cikin Wuri Mai Tsarki na can ciki a Haikalin, a ƙarƙashin fikafikan kerubobi. 7 Gama fikafikan kerubobin suna buɗe a bisa wurin da akwatin alkawarin yake domin su rufe akwatin alkawarin da sandunansa. 8 Sandunansa suna da tsawo har ana iya ganinsu daga ɗaki na can ciki daga Wuri Mai Tsarki, amma ba a iya ganinsu daga waje. Suna nan haka har wa yau. 9 Ba kome a cikin akwatin alkawarin, sai dai alluna na dutse guda biyu waɗanda Musa ya ajiye a ciki tun a Horeb, inda Ubangiji ya yi alkawari da jama'ar Isra'ila sa'ad da suka fito daga ƙasar Masar. 10 Sa'ad da firistoci suka fito daga Wuri Mai Tsarki, sai girgije ya rufe Haikalin Ubangiji, 11 har firistoci ba su iya tsayawa su gama hidima ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika Haikalin Ubangiji. 12 Sa'an nan Sulemanu ya yi addu'a ya ce, “Ubangiji ya ce zai zauna cikin gizagizai masu duhu. 13 Yanzu na gina maka ɗaki mai daraja, Wurin da za ka zauna har abada.”

Jawabin Sulemanu ga Jama'a

14 Sa'an nan sarki Sulemanu ya juya, ya fuskanci jama'a suna tsaye, ya roƙi Allah ya sa musu albarka. 15 Ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na Isra'ila, wanda ya cika alkawarin da ya yi wa tsohona, Dawuda, da ya ce masa, 16 ‘Tun daga ran da na fito da mutanena Isra'ila, daga Masar, ban zaɓi wani birni daga cikin kabilan Isra'ila inda zan gina Haikali domin sunana ba, amma na zaɓi Dawuda ya shugabanci mutanena Isra'ilawa.’ ” 17 Sulemanu ya ci gaba, ya ce, “Tsohona, Dawuda ya yi niyyar gina wa Ubangiji Allah na Isra'ila ɗaki, 18 amma Ubangiji ya ce wa tsohona, Dawuda, ya ji daɗin niyyar da ya yi ta gina Haikali, 19 amma duk da haka ba zai gina Haikalin ba, sai ɗansa wanda za a haifa masa shi ne zai gina Haikali domin sunan Ubangiji. 20 Yanzu Ubangiji ya cika alkawarin da ya yi, gama na tashi a maimakon tsohona, Dawuda, na hau gadon sarautar Isra'ila, kamar yadda ya alkawarta, ga shi kuwa, na gina Haikali saboda Ubangiji Allah na Isra'ila. 21 A cikin Haikalin kuma na shirya wa akwatin alkawari wuri, inda alkawarin Ubangiji yake, wato alkawarin da ya yi wa kakanninmu sa'ad da ya fito da su daga ƙasar Masar.”

Addu'ar Sulemanu

22 Sa'an nan Sulemanu ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron jama'ar Isra'ila. Ya ɗaga hannuwansa sama, 23 ya yi addu'a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, ba wani Allah kamarka cikin Sama a bisa, da cikin duniya a ƙasa, wanda yake cika alkawari, ya nuna ƙauna ga bayinsa, waɗanda suke tafiya a gabansa da zuciya ɗaya. 24 Kai wanda ka cika abin da ka faɗa wa bawanka, Dawuda, tsohona, i, abin da ka faɗa da bakinka ka cika shi yau. 25 Yanzu fa, ya Ubangiji Allah na Isra'ila, ka cika wa bawanka Dawuda, tsohona, sauran abin da ka alkawarta masa, da ka ce, ‘Ba za ka rasa mutum a gabana wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba, in dai zuriyarka sun mai da hankali, sun yi tafiya a gabana kamar yadda kai ka yi.’ 26 Yanzu fa, ya Allah na Isra'ila, sai ka tabbatar da maganarka wadda ka yi wa bawanka, Dawuda, tsohona. 27 “Amma ko Allah zai zauna a duniya? Ga shi, Saman sammai ba ta isa ta karɓe ka ba, balle wannan Haikali da na gina? 28 Duk da haka, ya Ubangiji Allahna, ka ji addu'ata, ni bawanka, da roƙe-roƙena, ka ji kukana da addu'ata da nake yi a gabanka yau. 29 Domin ka riƙa duban Haikalin nan dare da rana, wurin da ka ce sunanka zai kasance domin ka riƙa jin addu'ar da bawanka zai yi yana fuskantar wurin. 30 Sai ka riƙa jin roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra'ilawa, idan sun yi addu'a, suna fuskantar wurin nan, sa'ad da ka ji kuma, sai ka gafarta musu. 31 “Idan mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi, aka ba shi rantsuwa, idan ya zo, ya rantse a gaban bagadenka a wannan Haikali, 32 ya Ubangiji ka ji daga Sama, ka shara'anta bayinka, ka hukunta mai laifin, ka ɗora masa hakkinsa a kansa, amma ka kuɓutar da mara laifin, ka sāka masa bisa ga adalcinsa. 33 “Lokacin da abokan gāba suka ci mutanenka Isra'ila da yaƙi, saboda sun yi maka zunubi, idan sun komo wurinka, suka yabe ka, suka yi addu'a, suka roƙe ka a wannan Haikali, 34 sai ka ji daga Sama, ka gafarta wa jama'ar Isra'ila zunubinsu, sa'an nan ka sāke komar da su zuwa ƙasar da ka ba kakanninsu. 35 “Idan an hore su da rashin ruwan sama, saboda sun yi maka zunubi, idan sun tuba, suna fuskantar wannan Haikali, suka yi addu'a, suka kuma yabe ka, 36 sai ka ji daga Sama, ka gafarta zunuban sarki, da na jama'arka Isra'ila. Ka koya musu kyakkyawar hanyar da za su bi, ka sa a yi ruwan sama a ƙasarka wadda ka ba jama'arka gādo. 37 “Idan akwai yunwa a ƙasar, ko kuma akwai annoba, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fāri, ko tsutsa, sun cinye amfanin gona, idan kuma abokan gāba sun kawo wa jama'arka yaƙi har ƙofar birninsu, duk dai irin annoba da ciwon da yake cikinsu, 38 sai ka kasa kunne ga addu'arsu. Idan ɗaya daga cikin jama'arka Isra'ila ya matsu a zuciyarsa, ya ɗaga hannuwansa sama yana addu'a wajen wannan Haikali, 39 sai ka ji addu'arsa. Ka kasa kunne gare shi, a wurin zamanka a Sama, ka gafarta masa. Kai kaɗai ka san tunanin dukan mutane. Ka yi da kowa bisa ga abin da ya yi, 40 domin mutanenka su yi tsoronka a dukan kwanakinsu a ƙasar da ka ba kakanninmu. 41 “Sa'ad da kuma baƙo wanda yake wata ƙasa mai nisa ya ji labarin sunanka, 42 da manyan al'amura da ka yi wa jama'arka, ya zo domin ya yi maka sujada, da kuma addu'a gare ka a wannan Haikali, 43 sai ka kasa kunne ga addu'arsa. Ka ji daga Sama, wurin zamanka, ka amsa masa abin da ya roƙe ka, domin dukan mutanen duniya su san sunanka, su kuma yi tsoronka kamar jama'arka, Isra'ilawa, domin kuma su sani wannan Haikali da na gina wurin da za a yi maka sujada ne. 44 “Idan jama'arka sun tafi su yi yaƙi da abokan gābansu, idan sun yi addu'a a gare ka, suna fuskantar birnin nan da ka zaɓa, da Haikalin nan wanda na gina saboda sunanka, 45 sai ka kasa kunne ga addu'arsu. Ka ji daga sama, ka ba su nasara. 46 “Idan jama'arka sun yi maka zunubi, gama ba mutumin da ba ya yin zunubi, har ka yi fushi da su, ka kuwa bashe su a hannun abokan gāba, har suka kwashe su zuwa bauta a wata ƙasa mai nisa, 47 idan sun koma cikin hankalinsu a ƙasar da aka kai su bauta, har suka tuba, suka roƙe ka a ƙasar, suna hurta zunubansu da irin muguntar da suka aikata, ka ji addu'arsu, ya Ubangiji. 48 Idan sun komo gare ka da zuciya ɗaya, da dukan ransu a ƙasar abokan gabansu waɗanda suka kai su bauta, suka yi addu'a gare ka, suna fuskantar ƙasarsu wadda ka ba kakanninsu, da birnin da ka zaɓa, da Haikalin da na gina saboda sunanka, 49 sai ka ji addu'arsu da roƙe-roƙensu daga Sama, wurin zamanka, ka amsa, ka ji ƙansu. 50 Ka gafarta dukan zunubansu, da tayarwar da suka yi maka. Ka sa abokan gabansu su ji tausayinsu. 51 Gama su jama'arka ne, mallakarka, waɗanda ka fito da su daga Masar, daga tsakiyar azaba. 52 “Ya Ubangiji Allah, ka dubi jama'arka Isra'ila da sarkinsu da idon rahama, ka kasa kunne gare su duk lokacin da suka yi roƙo a gare ka. 53 Gama ka keɓe su daga sauran dukan al'ummai domin su zama jama'arka kamar yadda ka faɗa ta bakin bawanka Musa, sa'ad da ka fito da kakanninmu daga Masar.”

Addu'a ta Ƙarshe

54 Da Sulemanu ya gama wannan addu'a da roƙo ga Ubangiji, sai ya tashi daga gaban bagaden Ubangiji, inda yake a durƙushe da hannuwansa a miƙe zuwa sama. 55 Ya tsaya, ya sa wa taron jama'ar Isra'ila albarka da babbar murya, ya ce, 56 “Yabo ya tabbata ga Ubangiji wanda ya hutar da jama'arsa, Isra'ilawa, bisa ga yadda ya alkawarta. Daga cikin abin da ya alkawarta duka na alheri ba ko ɗaya da bai cika ba, kamar yadda ya alkawarta wa bawansa, Musa. 57 Ya Ubangiji Allah, sai ka kasance tare da mu kamar yadda ka kasance tare da kakanninmu, kada ka rabu da mu, ko ka yashe mu. 58 Ka sa zukatanmu su juyo gare ka, mu yi tafiya cikin tafarkunka, mu kiyaye umarnanka, da ka'idodinka da dokokinka, waɗanda ka umarci kakanninmu. 59 Ya Ubangiji Allahnmu, ka sa wannan roƙo da na yi ya kasance a gabanka, dare da rana. Ka biya bukatar bawanka, da bukatar jama'arka, Isra'ila, ta kowace rana, 60 domin dukan al'umman duniya su sani Ubangiji shi kaɗai ne Allah, banda shi, ba wani. 61 Ku kuma jama'arsa, sai ku amince da Ubangiji Allahnmu da zuciya ɗaya, ku kiyaye dokokinsa da umarnansa, kamar yadda kuke yi a yau.”

An Keɓe Haikali

62 Sa'an nan sarki Sulemanu, tare da Isra'ilawa duka, suka miƙa sadaka ga Ubangiji. 63 Sulemanu kuwa ya miƙa wa Ubangiji hadaya ta salama da bijimai dubu ashirin da dubu biyu (22,000 ) da tumaki dubu ɗari da dubu ashirin (120,000 ). Ta haka sarki da dukan mutanen Isra'ila suka keɓe Haikalin Ubangiji. 64 A wannan rana kuma ya keɓe tsakiyar filin da yake gaban Haikalin Ubangiji, gama a nan ne ya miƙa hadaya ta ƙonawa, da ta gari, da kitsen sadake-sadake na salama, gama bagaden tagullar da yake gaban Ubangiji ya yi ƙanƙanta ƙwarai da za a yi dukan waɗannan hadayu a kansa. 65 Sa'an nan kuma Sulemanu ya yi biki na kwana bakwai, shi da dukan jama'ar Isra'ila. Mutane suka zo, tun daga Mashigin Hamat a arewa, har zuwa iyakar ƙasar Masar a kudu, suka hallara a gaban Ubangiji Allahnmu. 66 A rana ta takwas ya sallami jama'ar, su kuwa suka yabi sarki. Sa'an nan suka kama hanyar gidajensu suna murna, suna farin ciki saboda dukan alherin da Ubangiji ya yi wa bawansa, Dawuda, da jama'arsa, Isra'ilawa.

1 Sarakuna 9

Ubangiji ya sāke Bayyana ga Sulemanu

1 Da Sulemanu ya gama ginin Haikalin Ubangiji da na fāda, da dukan abin da ya so ya yi, 2 sai Ubangiji ya sāke bayyana gare shi, kamar yadda ya bayyana gare shi a Gibeyon. 3 Ubangiji ya ce masa, “Na ji addu'arka da roƙe-rokenka da ka yi a gare ni, saboda haka na tsarkake Haikalin nan da ka gina, na kuma sa sunana ya kasance a wurin har abada. Idanuna da zuciyata kuma za su kasance a wurin kullum. 4 Amma kai, idan ka yi tafiya a gabana kamar yadda tsohonka, Dawuda, ya yi da aminci, da sahihanci, kana aikata dukan abin da na umarce ka, kana kuma kiyaye dokokina da ka'idodina, 5 sa'an nan zan kafa gadon sarautarka a bisa Isra'ila har abada, kamar yadda na alkawarta wa tsohonka, Dawuda, sa'ad da na ce masa ba za a rasa mutum daga zuriyarsa wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba. 6 Amma idan kai, ko 'ya'yanka, kun bar bina, ba ku kiyaye umarnaina da dokokina ba, waɗanda na yi muku, amma kuka tafi, kuka bauta wa waɗansu gumaka, kuka yi musu sujada, 7 sai in raba jama'ar Isra'ila da ƙasar da na ba su, Haikalin kuma da na tsarkake domin sunana, zan kawar da shi daga gabana. Jama'ar Isra'ila kuwa za su zama abin karin magana, da abin ba'a a wurin dukan mutane. 8 Wannan Haikali kuwa zai zama tsibin juji, duk wanda zai wuce ta wurin, zai yi mamaki, ya yi tsaki, ya ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi wa ƙasar nan da Haikalin nan haka?’ 9 Waɗansu kuwa za su amsa su ce, ‘Saboda sun bar bin Ubangiji Allahnsu wanda ya fito da kakanninsu daga ƙasar Masar, suka bi waɗansu gumaka, suka yi musu sujada, suka bauta musu, domin haka Ubangiji ya ɗora musu wannan masifa.’ ”

Sauran Ayyukan Sulemanu

10 Sulemanu ya yi shekara ashirin kafin ya gama ginin Haikalin Ubangiji da fādarsa. 11 Hiram, Sarkin Taya, kuwa ya ba Sulemanu katakan itacen al'ul da na fir da zinariya, iyakar yadda yake bukata. Sarki Sulemanu kuwa ya ba Hiram garuruwa ashirin a jihar Galili. 12 Amma sa'ad da Hiram ya zo daga Taya domin ya ga garuruwan da Sulemanu ya ba shi, sai ya ga ba su gamshe shi ba. 13 Don haka ya ce wa Sulemanu, “Dan'uwa, waɗanne irin garuruwa ke nan da ka ba ni?” Saboda haka har yanzu ana kiran ƙasar Kabul, wato marar amfani. 14 Hiram kuma ya aika wa Sulemanu da zinariya mai nauyin talanti ɗari da ashirin. 15 Wannan shi ne lissafin aikin tilas da sarki Sulemanu ya sa domin ginin Haikalin, da na fādarsa, da kuma Millo, a kuma gina garun birnin. Ya kuma sa tilas a sāke gina garuruwan Hazor, da Magiddo, da Gezer. 16 Gama Fir'auna ya haura, ya ci Gezer, ya ƙone ta da wuta, ya kuma kashe masu zama cikinta. Sa'an nan ya yi wa 'yarsa, wato matar Sulemanu, kyauta da Gezer ɗin. 17 Sulemanu kuwa ya sāke gina Gezer. Ya kuma sa aka gina Bet-horon ta kwari ta aikin tilas, 18 da Ba'alat, da Tadmor a cikin jeji, a ƙasar Yahuza, 19 da garuruwan ajiyarsa, da garuruwan karusansa, da garuruwan mahayan dawakansa, da duk abin da Sulemanu ya so ya gina a Urushalima, da Lebanon, da dukan ƙasar da ya mallaka. Amoriyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, da suka ragu a ƙasar, wato waɗanda ba mutanen Isra'ila ba, waɗanda mutanen Isra'ila ba su iya hallakarwa ba, Sulemanu ya sa zuriyarsu su yi aikin tilas na bauta, haka kuwa suke har wa yau. 22 Sulemanu bai mai da mutanen Isra'ila bayi ba, amma su ne sojojinsa da dogaransa, da shugabannin sojoji, da shugabannin karusansa, da mahayan dawakansa. 23 Sulemanu yana da masu lura da aiki su ɗari biyar da hamsin, suna lura da masu aikin tilas a wurare dabam dabam da ake wa Sulemanu gini. 24 Da 'yar Fir'auna matar Sulemanu ta fita birnin Dawuda, zuwa gidan kanta wanda Sulemanu ya gina mata, sa'an nan ya gina birnin Millo. 25 Sau uku a shekara Sulemanu yakan miƙa hadayu na ƙonawa, da na salama, da hadayar turare, a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji. Ta haka aka gama ginin Haikali. 26 Sarki Sulemanu kuma ya yi jiragen ruwa a Eziyon-geber wadda take kusa da Elat, a bakin Bahar Maliya a ƙasar Edom. 27 Sarki Hiram ya aiki barorinsa, gogaggun matuƙan jiragen ruwa, da jiragen ruwa tare da barorin Sulemanu. 28 Sai suka tafi Ofir suka kawo wa sarki Sulemanu zinariya mai nauyin talanti ɗari huɗu da shirin.

1 Sarakuna 10

Sarauniyar Sheba ta Ziyarci Sulemanu

1 Sarauniyar Sheba ta ji labarin sunan da Sulemanu ya yi ta dalilin sunan Ubangiji, ta zo don ta jarraba shi da tambayoyi masu wuya. 2 Ta iso Urushalima da 'yan rakiya da yawa, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, da zinariya da yawa, da duwatsu masu daraja. Sa'ad da ta zo wurin Sulemanu, ta faɗa masa duk abin da yake a ranta. 3 Sulemanu ya amsa tambayoyinta dukka, ba abin da ya gagare shi amsawa. Sheba ta yi mamaki sa'ad da ta ga hikimar Sulemanu, da gidan da ya gina, da irin abincinsa, da irin zaman fādawansa, da yadda ma'aikatan gida suke hidima, da irin tufafinsu, da masu ba da abin sha, da hadayu na ƙonawa waɗanda yakan miƙa cikin Haikalin Ubangiji. 6 Sai ta ce wa Sulemanu, “Labarin da na ji a ƙasata a kan al'amuranka da hikimarka, gaskiya ne. 7 Amma ban gaskata da labarin ba, sai da na zo na gani da idona, ashe, ko rabi ma ba a faɗa mini ba, gama hikimarka da wadatarka sun fi abin da na ji. 8 Jama'arka, da fādawanka waɗanda suke tsaye a gabanka kullum, sun yi sa'a gama suna jin hikimarka. 9 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka wanda ya yarda da kai, ya sa ka a kan gadon sarautar Isra'ila, domin Ubangiji yana ƙaunar Isra'ila har abada, ya naɗa ka sarki domin ka zartar da shari'a da adalci.” 10 Sa'an nan Sarauniyar Sheba ta ba sarki talanti ɗari da ashirin na zinariya, da kayan yaji mai yawan gaske, da duwatsu masu daraja. Ba a taɓa kawo kayan yaji da yawa kamar yadda Sarauniyar Sheba ta kawo wa sarki Sulemanu ba. 11 Bayan wannan kuma jiragen ruwa na Hiram da suka kawo zinariya daga Ofir, sun kuma kawo itacen almug da yawa, da duwatsu masu daraja daga can. 12 Da itacen almug ne sarki ya yi ginshiƙai na Haikalin Ubangiji da gidan sarki, ya kuma yi molaye da garayu domin mawaƙa. Har wa yau ba a taɓa samu, ko ganin irin itacen almug kamar wannan ba. 13 Sarki Sulemanu ya ba Sarauniyar Sheba duk abin da ta nuna tana bukata, banda kyautar karamcin da ya yi mata. Sai ta koma ƙasarta tare da barorinta.

Dukiyar Sulemanu da Shahararsa

14 Yawan zinariya da akan kawo wa Sulemanu kowace shekara yakan kai talanti ɗari shida da sittin da shida na zinariya. 15 Banda wanda ya sa wa 'yan kasuwa, da fatake, da harajin dukan sarakunan Arabiya, da na hakimai. 16 Sarki Sulemanu ya yi manyan garkuwoyi guda ɗari biyu da zinariya. Anyi kowace garkuwa da shekel ɗari shida na zinariya. 17 Ya kuma yi waɗansu garkuwoyi guda ɗari uku da zinariya. An yi kowace garkuwa da shekel dari uku na zinariya. Sarki kuwa ya ajiye su a ɗakin da aka gina da katakai daga Lebanon. 18 Ya kuma yi babban gadon sarauta na hauren giwa, sa'an nan ya dalaye shi da tattacciyar zinariya. 19 Gadon sarautar yana da matakai shida da siffar kan maraƙi a bayan gadon sarautar, a kowane gefen mazaunin kuma, akwai wurin ɗora hannu da siffofin zaki biyu suna tsaye a gefen wuraren ɗora hannun. 20 Akwai siffar zaki goma sha biyu suna tsaye a kowane gefen matakan nan shida. Ba a taɓa yin irinsu a kowace masarauta ba. 21 Dukan finjalai na sarki Sulemanu, da zinariya aka yi su, haka kuma finjalan da suke cikin ɗakin da aka gina da katakai daga Lebanon, ba a yi wani finjali da azurfa ba, domin ba a mai da azurfa kome ba a kwanakin Sulemanu. 22 Gama sarki yana da rundunar jiragen ruwa a tekun Tarshish tare da na Hiram. Sau ɗaya a shekara uku rundunar jiragen ruwa na Tarshish sukan kawo zinariya, da azurfa, da hauren giwa, da birai, da ɗawusu masu daraja. 23 Sarki Sulemanu ya fi dukan sarakunan duniya dukiya da hikima. 24 Dukansu suna so su zo wurin Sulemanu don su ji hikimarsa wadda Allah ya ba shi. 25 Kowannensu yakan kawo masa yawan kyautai na kayayyakin azurfa, da na zinariya, da riguna, da turare, da kayan yaji, da dawakai, da alfadarai kowace shekara.

Kasuwancin Sulemanu a kan Dawakai da Karusai

26 Sulemanu kuwa ya tattara karusai da mahayan dawakai. Yana da karusai dubu da ɗari huɗu (1,400 ), da mahayan dawakai dubu goma sha biyu (12,000 ), waɗanda ya zaunar da su a biranen karusai da kuma waɗansu tare da shi a Urushalima. 27 Sarki ya sa azurfa ta gama gari, kamar dai duwatsu a Urushalima, itacen al'ul kuma ya zama kamar jumaiza na Shefela. 28 Sulemanu kuwa ya sayo dawakai daga Masar da Kuye. 'Yan kasuwar sarki sukan sayo dawakai daga Kuye a kan tamaninsu. 29 Akan sayo karusa a Masar a bakin azurfa ɗari shida, doki kuwa a bakin ɗari da hamsin, 'yan kasuwar sarki sukan sayar da su ga dukan sarakunan Hittiyawa da na Suriyawa.

1 Sarakuna 11

Sulemanu ya Ridda

1 Sarki Sulemanu ya ƙaunaci baƙin mata. Banda 'yar Fir'auna, Sarkin Masar, ya auri matan Mowabawa, da na Ammonawa, da na Edomawa, da na Sidoniyawa, da na Hittiyawa. 2 Suna kuwa cikin al'umman da Ubangiji ya umarci jama'ar Isra'ila, ya ce, “Kada ku yi aurayya da su, gama hakika za su karkatar da zuciyarku zuwa gumakansu.” Sulemanu kuwa ya manne wa waɗannan mata da yake ƙauna. 3 Ya auri mata ɗari bakwai, dukansu kuwa gimbiyoyi ne. Yana kuma da ƙwaraƙwarai ɗari uku. Matan nan nasa kuwa suka janye zuciyarsa daga bin Ubangiji, 4 sa'ad da Sulemanu ya tsufa sai suka janye zuciyarsa zuwa bin waɗansu gumaka, bai bi Ubangiji Allahnsa da zuciya ɗaya kamar yadda tsohonsa, Dawuda, ya yi ba. 5 Gama Sulemanu ya bi Ashtoret ta Sidoniyawa, da Milkom, wato gunkin Ammonawa. 6 Ya yi wa Ubangiji zunubi. Bai bi Ubangiji da zuciya ɗaya kamar yadda tsohonsa, Dawuda, ya yi ba. 7 Sulemanu ya gina wa Kemosh, wato gunkin Mowab, da Molek, gunkin Ammonawa, masujadai a kan dutsen da yake gabas da Urushalima. 8 Ya kuma gina masujadai inda dukan matansa baƙi za su riƙa miƙa turare da hadayu ga gumakansu. 9 Ubangiji kuwa ya yi fushi da Sulemanu, domin zuciyar Sulemanu ta rabu da Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda ya bayyana a gare shi sau biyu, 10 ya kuma umarce shi kada ya bi gumaka. Amma bai kiyaye umarnin da Ubangiji ya yi masa ba. 11 Saboda haka Ubangiji ya ce wa Sulemanu, “Tun da yake ka yi haka, ba ka kuwa kiyaye umarnina da dokokina waɗanda na umarce ka da su ba, to, hakika zan ƙwace mulki daga gare ka, in ba baranka. 12 Amma saboda tsohonka, Dawuda, ba zan ƙwace a zamaninka ba, amma zan ƙwace daga hannun ɗanka. 13 Duk da haka ba zan ƙwace mulkin duka ba, amma zan ba ɗanka kabila guda, saboda bawana Dawuda, saboda kuma Urushalima wadda na zaɓa.”

Abokan Gāban Sulemanu

14 Ubangiji kuwa ya sa Hadad Ba'edome, ya tayar wa Sulemanu. Shi Hadad daga jinin sarautar Edom ne. 15 Gama sa'ad da Dawuda ya ci Edom, Yowab, shugaban sojoji, ya tafi don ya binne kisassu, sun yi wata shida a can, shi da mutanensa, sai ya kashe kowane namijin da yake cikin Edom. 16 Gama Yowab da dukan Isra'ilawa sun tsaya a Edom wata shida, sai da ya gama kashe mazajen Edom duka. 17 Amma Hadad ya tsere zuwa Masar tare da waɗansu Edomawa, barorin tsohonsa. Hadad yana ɗan saurayi a lokacin. 18 Suka kama hanya daga Madayana suka zo Faran. Daga Faran suka kwashi mutane tare da su, suka tafi Masar zuwa wurin Fir'auna, Sarkin Masar, wanda ya ba shi gida, ya kuma riƙa ba shi abinci, ya kuma ba shi ƙasa. 19 Hadad kuwa ya sami farin jini ƙwarai a wurin Fir'auna, har ya aurar masa da ƙanwar matarsa, wato ƙanwar Tafenes, sarauniya. 20 Ita kuwa ta haifa masa ɗa, Genubat, wanda Tafenes ta yi renonsa a gidan Fir'auna. Genubat kuwa ya zauna tare da 'ya'yan Fir'auna, maza. 21 Amma sa'ad da Hadad ya ji labari Dawuda ya rasu, Yowab shugaban sojoji shi ma ya rasu, sai Hadad ya ce wa Fir'auna, “Ka yardar mini, in tashi, in koma ƙasata.” 22 Amma Fir'auna ya ce masa, “Me ka rasa a nan har da kake so ka koma ƙasarka?” Hadad ya ce masa, “Ka dai yardar mini kawai in tafi.” Ya kuwa koma ƙasarsa. 23 Allah kuma ya sa Rezon ɗan Eliyada, ya tayar wa Sulemanu, shi Rezon ya gudu daga wurin maigidansa, Hadadezer Sarkin Zoba. 24 Ya tattara wa kansa mutane ya zama shugaban 'yan hari bayan kashe-kashen da Dawuda ya yi. Sai suka tafi Dimashƙu, suka zauna a can, suka naɗa shi Sarkin Dimashƙu. 25 Ya zama abokin gāban Isra'ila a dukan zamanin Sulemanu. Ya yi ta ɓarna kamar yadda Hadad ya yi. Ya ƙi jinin mutane Isra'ila. Ya yi mulkin suriya.

Alkawarin Allah ga Yerobowam

26 Sai Yerobowam ɗan Nebat, Ba'ifraime na Zaretan, baran Sulemanu, wanda sunan mahaifiyarsa Zeruya, wadda mijinta ya rasu, shi ma ya tayar wa sarki. 27 Ga dalilin da ya sa ya tayar wa sarki. Sulemanu ya gina Millo ya kuma faɗaɗa garun birnin Dawuda tsohonsa. 28 Yerobowam mutum ne mai fasaha. Da Sulemanu ya ga shi saurayi ne mai himma, sai ya shugabantar da shi kan aikin tilas na gidan Yusufu. 29 A sa'ad da Yerobowam ya fita Urushalima, sai annabi Ahija mutumin Shilo ya tarar da shi a hanya. Lokacin kuwa Ahija yana saye da sabuwar riga, ba kowa a filin sai su biyu kaɗai, 30 sai Ahija ya kama sabuwar rigar da ya sa, ya kyakketa ta ƙyalle goma sha biyu, 31 ya ce wa Yerobowam, “Kwashi ƙyalle goma, gama haka Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Ga shi, ina gab da in kece sarauta daga hannun Sulemanu, zan ba ka kabila goma. 32 Amma Sulemanu, zai sami kabila ɗaya saboda bawana Dawuda, da kuma ɗaya saboda Urushalima, wato birnin da na zaɓa daga cikin kabilan Isra'ila duka. 33 Domin Sulemanu ya rabu da ni, ya bauta wa Ashtoret, gunkiyar Sidoniyawa, da Kemosh, gunkin Mowab, da Milkom, gunkin Ammonawa. Bai yi tafiya a cikin tafarkuna ba, bai yi abin da yake daidai a gare ni ba, bai kiyaye dokokina, da ka'idodina kamar yadda Dawuda, tsohonsa, ya yi ba. 34 Duk da haka ba zan karɓe sarauta duka daga hannunsa ba, amma zan bar shi ya yi mulki muddin ransa saboda bawana Dawuda, wanda na zaɓa, wanda ya kiyaye umarnaina da dokokina. 35 Amma zan karɓe mulki daga hannun ɗansa in ba ka, zan ba ka kabila goma. 36 Duk da haka zan ba ɗansa kabila guda, domin bawana Dawuda ya kasance da fitila kullum a gabana a Urushalima, birnin da na zaɓa in sa sunana. 37 Zan sa ka yi mulki a kan duk abin da ranka yake bukata, za ka zama Sarkin Isra'ila. 38 Idan za ka kasa kunne ga duk abin da na umarce ka, ka bi tafarkuna, ka aikata abin da yake daidai a gare ni, ka kiyaye dokokina da umarnaina kamar yadda bawana Dawuda ya yi, zan kasance tare da kai, zan sa gidanka ya kahu kamar yadda na sa gidan Dawuda ya kahu, zan ba ka Isra'ila. 39 Zan wahalar da zuriyar Dawuda, amma ba har abada ba.’ ” 40 Sulemanu kuwa ya nema ya kashe Yerobowam, amma Yerobowam ya tashi, ya tsere zuwa Masar, wurin Shishak Sarkin Masar, ya zauna a can har rasuwar Sulemanu.

Rasuwar Sulemanu

41 Sauran ayyukan Sulemanu, da dukan abin da ya yi, da hikimarsa an rubuta su a littafin tarihin Sulemanu. 42 Sulemanu ya yi shekara arba'in yana sarauta a Urushalima a kan Isra'ila duka. 43 Sulemanu ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda, wato Urushalima. Dansa Rehobowam ya gaji sarautarsa.

1 Sarakuna 12

Mulki ya Rabu Biyu

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan mutanen Isra'ila sun tafi Shekem don su naɗa shi sarki. 2 Sa'ad da Yerobowam, ɗan Nebat, ya ji labari, gama a lokacin yana Masar inda ya gudu saboda sarki Sulemanu, sai ya komo daga Masar. 3 Suka aika a kirawo shi, sai Yerobowam da dukan taron jama'ar Isra'ila suka zo suka ce wa Rehobowam, 4 “Tsohonka ya nawaita mana, yanzu sai ka rage mana wahalar aikin tsohonka da nawayarsa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.” 5 Sai ya ce musu, “Ku tafi, ku sāke zuwa bayan kwana uku.” Sai suka tafi. 6 Sarki Rehobowam kuwa ya nemi shawara daga wurin dattawa, waɗanda suka bauta wa tsohonsa, Sulemanu, lokacin da yake da rai. Ya ce musu, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan?” 7 Suka ce masa, “Idan za ka zama mai lura da jama'an nan yau, ka bauta musu, sai ka yi musu magana da kyau, su kuwa za su zama talakawanka har abada.” 8 Amma ya yi watsi da shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawara daga wurin matasa, tsararsa. 9 Ya ce musu, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa mutanen nan da suka roƙe ni cewa in rage musu nawayar da tsohona ya aza musu?” 10 Matasa da suke tsara ɗaya da shi kuwa suka ce masa, “Haka za ka faɗa wa mutanen nan da suka yi magana da kai, cewa tsohonka ya nawaita musu, amma sai ka sawwaƙa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri. 11 Zan ƙara a kan nawayar da tsohona ya aza muku. Shi ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunamai.’ ” 12 Yerobowam da dukan mutane suka zo wurin Rehobowam a rana ta uku kamar yadda ya faɗa musu su zo wurinsa bayan kwana uku. 13 Da suka zo, sai sarki ya yi musu magana da zafi, ya kuma yi watsi da shawarar da dattawa suka ba shi. 14 Ya yi musu magana bisa ga shawarar matasa ya ce, “Tsohona ya nawaita muku, ni kuwa zan ƙara nawaita muku. Tsohona ya yi muku horo da bulala, amma ni zan yi muku da kunamai.” 15 Haka kuwa sarki ya ƙi jin roƙon da jama'a suka yi masa, gama Ubangiji ne ya sa al'amarin ya zama haka domin ya cika maganarsa, wadda ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta bakin Ahija mutumin Shilo. 16 Da mutanen Isra'ila suka ga sarki ya ƙi jin roƙonsu, sai suka yi ihu, suna cewa, “A yi ƙasa da Dawuda da iyalinsa. Me suka taɓa yi mana? Mazajen Isra'ila, bari duka mu tafi gida! Mu bar Rehobowam ya lura da kansa!” Jama'ar Isra'ila fa suka tayar, 17 suka bar Rehobowam ya sarauci jama'ar da ke zaune a yankin ƙasar Yahuza. 18 Sa'an nan sarki Rehobowam ya aiki Adoniram, shugaban aikin tilas, sai mutanen Isra'ila suka jajjefe shi da duwatsu har lahira. Sarki Rehobowam kuwa ya gaggauta, ya hau karusarsa, ya tsere zuwa Urushalima. 19 Da haka mutanen Isra'ila suka tayar wa gidan Dawuda har wa yau. 20 Da dukan mutane suka ji, cewa Yerobowam ya komo, sai suka aika a kirawo shi ga taron jama'a. Suka naɗa shi Sarkin Isra'ila duka. Ba wanda ya bi gidan Dawuda, sai dai kabilar Yahuza. 21 Da Rehobowam ya komo Urushalima, sai ya tara dukan jama'ar gidan Yahuza, da na kabilar Biliyaminu. Aka sami mayaƙa dubu ɗari da dubu tamanin (180,000 ) waɗanda za su yi yaƙi da gidan Isra'ila, don su komar da su a ƙarƙashin mulkin Rehobowam, ɗan Sulemanu. 22 Amma Ubangiji Allah ya yi magana da annabi Shemaiya, 23 ya faɗa wa Rehobowam ɗan Sulemanu, Sarkin Yahuza, da dukan mutanen gidan Yahuza da na Biliyaminu, da sauran jama'a, 24 Ubangiji ya ce, “Kada ku haura zuwa yaƙi da 'yan'uwanku, mutanen Isra'ila, sai kowa ya koma gidansa, gama wannan al'amari daga wurina ne.” Su kuwa suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka koma gida.

Yerobowam ya bar Bin Tafarkin Allah

25 Sa'an nan sarki Yerobowam ya gina Shekem a ƙasar tudu ta Ifraimu, ya zauna can. Daga can kuma ya tafi ya gina Feniyel. 26 Yerobowam kuwa ya ce a zuciyarsa, “Mulkin fa zai koma gidan Dawuda. 27 Idan mutanen nan sun ci gaba da zuwa Urushalima don miƙa wa Ubangiji hadayu, zuciyarsu za ta koma kan sarki Rehobowam, na Yahuza, za su kashe ni, su koma wurinsa.” 28 Sai sarki Yerobowam ya yi shawara, ya siffata 'yan maruƙa biyu da zinariya. Sa'an nan ya ce wa jama'arsa, “Zuwanku Urushalima ya isa, yanzu ga allolinku, ya Isra'ilawa, waɗanda suka fito da ku daga ƙasar Masar.” 29 Ya kafa siffar maraƙi ɗaya a Betel, ɗayan kuma a Dan. 30 Wannan abu ya zama zunubi, gama mutane sun tafi wurin siffofin maruƙan nan a Betel da Dan. 31 Ya kuma gina masujadai a tuddai, sa'an nan ya sa waɗansu daga cikin mutane waɗanda ba Lawiyawa ba, su zama firistoci.

An Soki Sujada a Betel

32 Yerobowam kuma ya sa a yi idi ran goma sha biyar ga wata na takwas kamar yadda ake yi a Yahuza. Ya miƙa hadayu bisa bagade, haka ya yi a Betel. Ya yi ta miƙa hadayu ga siffofin maruƙan da ya yi. Ya kuma sa firistoci a masujadan da ya gina a Betel. 33 Ya tafi gaban bagaden da ya gina a Betel a rana ta goma sha biyar ga wata na takwas, wato watan da ya zaɓa don kansa. Ya kafa wa jama'ar Isra'ila idi. Sai ya tafi don ya ƙona turare a kan bagaden.

1 Sarakuna 13

Annabi ya Faɗakar da Yerobowam

1 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai ga annabi ya fito daga Yahuza zuwa Betel. Yerobowam kuwa yana tsaye kusa da bagaden don ya ƙona turare. 2 Bisa ga umarnin Ubangiji, sai annabin ya ta da murya, ya ce, “Ya bagade, bagade, Ubangiji ya ce za a haifi ɗa a gidan Dawuda, sunansa Yosiya wanda zai miƙa firistoci na masujadan tuddai hadaya a kanka, wato firistoci waɗanda suke ƙona turare. Za a ƙone ƙasusuwan mutane a bisa kanka.” 3 Ya kuma ba da alama a wannan rana cewa, “Wannan ita ce alamar da Ubangiji ya faɗa, za a rushe bagaden, a zubar da tokar da take bisansa.” 4 Da sarki ya ji maganar annabin, wato wadda ya yi a kan bagaden da yake Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden, ya ce, “Ku kama shi.” Hannun da ya miƙa kuwa ya sage, bai iya komo da shi ba. 5 Aka rushe bagaden, aka kuma zubar da tokar daga bagaden bisa ga alamar da annabin ya faɗa da sunan Ubangiji. 6 Sarki Yerobowam ya ce wa annabin, “In ka yarda ka yi roƙo ga Ubangiji Allahnka domina, ka yi mini addu'a don ya warkar da hannuna.” Annabi ya roƙi Ubangiji, sai hannun sarki ya komo daidai. 7 Sa'an nan sarkin ya ce wa annabin, “Zo mu tafi gida don ka shaƙata, zan ba ka lada.” 8 Annabin kuwa ya ce wa sarki, “Ko da za ka ba ni rabin gidanka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuma zan ci abinci ko in sha ruwa a wurin nan ba. 9 Gama Ubangiji ya umarce ni da cewa kada in ci abinci, ko in sha ruwa, ko in koma ta hanyar da na zo.” 10 Haka kuwa ya koma ta wata hanya dabam bai koma ta hanyar da ya bi zuwa Betel ba.

Tsohon Annabi na Betel

11 Akwai wani tsohon annabi a Betel. 'Ya'yansa maza kuwa suka tafi suka faɗa masa dukan abin da annabin Allah ya yi a Betel a wannan rana. Suka faɗa wa mahaifinsu maganar da annabin Allah ya faɗa wa sarki. 12 Tsohon annabin ya tambaye su, “Wace hanya ya bi?” Su kuwa suka nuna masa hanyar. 13 Ya ce musu su ɗaura wa jakinsa shimfiɗa. Sai suka ɗaura wa jakin shimfiɗa, shi kuwa ya hau, 14 ya bi bayan annabin nan da ya fito daga Yahuza, ya same shi yana zaune a gindin itace oak. Ya tambaye shi, “Ko kai ne annabin da ya zo daga Yahuza?” Mutumin ya amsa, “I, ni ne,” 15 Sa'an nan ya ce masa, “Zo mu tafi gida ka ci abinci.” 16 Amma annabin ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ba kuwa zan shiga gida ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a wannan wuri, 17 gama Ubangiji ya ce mini kada in ci abinci, ko in sha ruwa a can, ko in koma ta hanyar da na zo.” 18 Sa'an nan tsohon annabin ya ce masa, “Ai, ni ma annabi ne kamarka. Ubangiji ya yi mini magana ta bakin wani mala'ika, ya ce mini in komar da kai gidana don ka ci abinci, ka sha ruwa.” Amma ƙarya ce ya yi masa. 19 Saboda haka sai annabin ya koma tare da shi, ya ci abinci, ya sha ruwa a gidan tsohon annabin. 20 Sa'ad da suke zaune wurin ci, sai maganar Ubangiji ta zo ga tsohon annabin da ya komar da annabin Allah, 21 sai ya kira annabin Allah, wanda ya zo daga Yahuza, ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Da yake ba ka yi biyayya da maganar Ubangiji ba, ba ka kuma kiyaye umarnin da Ubangiji Allahnka ya umarce ka da shi ba, 22 amma ka komo, ka ci abinci, ka sha ruwa a wurin da ya ce maka, kada ka ci abinci, ko kuwa ka sha ruwa, saboda haka ba za a binne gawarka a kabarin kakanninka ba.’ ” 23 Bayan da ya ci abinci, ya sha sai tsohon annabin ya ɗaura wa jaki shimfiɗa don annabin da ya komo da shi. 24 Sa'ad da annabin Allah ya tafi, sai zaki ya gamu da shi a hanya, ya kashe shi, ya jefar da gawarsa a kan hanya. Sai jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar. 25 Mutane suka wuce, suka ga gawar a kan hanya, da zaki a tsaye kusa da gawar. Suka tafi suka faɗa a birni, inda tsohon annabin nan yake. 26 Sa'ad da tsohon annabin nan ya ji, sai ya ce, “Wannan annabin Allah ne, wanda bai yi biyayya da maganar Ubangiji ba, saboda haka Ubangiji ya bashe shi ga zaki ya yayyage shi, ya kashe shi, kamar yadda Ubangiji ya faɗa masa.” 27 Sa'an nan ya ce wa 'ya'yansa maza, “Ku ɗaura mini shimfiɗa.” Su kuwa suka ɗaura, 28 ya hau ya tafi, ya iske gawar a hanya. Jakin da zakin suna tsaye kusa da gawar. Zakin bai ci gawar ba, bai kuma fāɗa wa jakin ba. 29 Tsohon annabin kuwa ya ɗauki gawar ya ɗora bisa jakin, ya kawo ta cikin birni, wato Betel, don yin makoki da binnewa. 30 Ya binne gawar a kabarinsa, sa'an nan suka yi makoki suna cewa, “Kaito, dan'uwana!” 31 Bayan da ya binne shi, sai ya ce wa 'ya'yansa, “Sa'ad da na rasu, sai ku binne ni a kabarin da aka binne annabin nan. Ku ajiye gawata kusa da tasa. 32 Gama maganar Ubangiji da ya faɗa game da bagaden da yake cikin Betel, da masujadai na kan tuddai waɗanda suke a garuruwan Samariya, za ta cika.”

Zunubin Yerobowam zai Kai shi Hallaka

33 Bayan wannan al'amari Yerobowam bai bar muguwar hanyarsa ba, amma ya naɗa firistoci daga cikin mutane don masujadai da suke kan tuddai. Duk mutumin da yake so, sai ya keɓe shi don ya zama firist na masujada da take kan tudu. 34 Wannan zunubi ya zama sanadi ga gidan Yerobowam, har ya isa a shafe gidan, a hallaka shi ƙaƙaf.

1 Sarakuna 14

Annabcin Ahija

1 A lokacin nan Abaija ɗan Yerobowam ya kwanta ciwo. 2 Yerobowam kuwa ya ce wa matarsa, “Ki tashi, ki ɓad da kama don kada a sani ke matata ce, sa'an nan ki tafi Shilo wurin Ahija, annabin nan wanda ya ce mini zan sarauci jama'an nan. 3 Ki ɗauki malmalar abinci guda goma, da waina, da kurtun zuma, ki tafi wurinsa. Zai faɗa miki abin da zai faru da yaron.” 4 Matar kuwa ta yi haka. Ta tashi ta tafi Shilo a gidan Ahija. Ahija ba ya gani, saboda tsufa. 5 Ubangiji ya ce wa Ahija, “Ga matar Yerobowam tana zuwa don ta tambaye ka abin da zai faru da ɗanta, gama ɗan yana ciwo. To, da haka za ka amsa mata, gama sa'ad da ta zo, za ta nuna kamar ita wata mace ce dabam.” 6 Da Ahija ya ji motsin takawarta a bakin ƙofa, sai ya ce mata, “Ki shigo, matar Yerobowam, me ya sa kike yi kamar ke wata ce dabam? Gama an umarce ni in faɗa miki labari marar daɗi. 7 Ki koma, ki faɗa wa Yerobowam, Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Na ɗaukaka ka daga cikin mutane, na sa ka zama shugaban mutanena, Isra'ilawa. 8 Na yage mulki daga gidan Dawuda na ba ka, duk da haka ba ka zama kamar bawana Dawuda ba, wanda ya kiyaye umarnaina, ya bi ni da zuciya ɗaya, yana yin abin da yake daidai a gare ni. 9 Amma ka aikata mugunta fiye da dukan waɗanda suka riga ka, ka yi wa kanka gumaka, da siffofi na zubi, ka tsokane ni in yi fushi, ka yi watsi da ni. 10 Saboda haka zan kawo masifa a gidanka. Zan datse maka kowane ɗa namiji, ko bawa, ko 'yantacce, daga cikin Isra'ila. Zan ƙone gidanka kamar yadda akan ƙone juji ƙurmus. 11 Duk wanda yake naka wanda zai mutu a birni, karnuka za su cinye shi. Wanda kuma ya mutu a saura tsuntsaye za su cinye shi, ni Ubangiji, ni ne na faɗa.’ 12 “Ki tashi, ki koma gida. Da shigarki birni, yaron zai mutu. 13 Dukan jama'ar Isra'ila za su yi makoki dominsa, su binne shi, gama shi kaɗai zai sami binnewa daga cikin gidan Yerobowam, domin a gare shi kaɗai aka iske abin da Ubangiji, Allah na Isra'ila, yake murna da shi. 14 Ubangiji kuma zai ta da wani wanda zai sarauci Isra'ila, wanda kuma zai rushe gidan Yerobowam daga yanzu har zuwa nan gaba. 15 Ubangiji zai hukunta Isra'ila kamar yadda akan girgiza iwa a baƙin rafi, zai tumɓuke Isra'ila daga wannan ƙasa mai albarka wadda ya ba kakanninsu, ya kuma watsar da su a hayin Kogin Yufiretis, domin sun yi wa kansu gumaka don sun tsokani Ubangiji ya yi fushi. 16 Ubangiji zai rabu da Isra'ila saboda zunuban Yerobowam waɗanda ya yi, da kuma waɗanda ya sa mutanen Isra'ila su yi.” 17 Sa'an nan matar Yerobowam ta tashi, ta tafi Tirza. Amma tana shiga gidan ke nan, sai yaron ya mutu. 18 Jama'ar Isra'ila duka suka binne shi, suka yi makoki dominsa, kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin bawansa, annabi Ahija.

Mutuwar Yerobowam

19 Sauran ayyukan Yerobowam, da yaƙe-yaƙensa, da yadda ya yi mulki, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 20 Yerobowam ya yi mulki shekara ashirin da biyu sa'an nan ya rasu, aka binne shi. Ɗansa Nadab ya gāji sarautarsa.

Mulkin Rehobowam

21 Rehobowam ɗan Sulemanu ya yi mulki a Yahuza. Yana da shekara arba'in da ɗaya sa'ad da ya ci sarauta. Ya kuwa yi shekara goma sha bakwai yana sarauta a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga cikin kabilan Isra'ila duka, domin ya sa sunansa ya kasance a wurin. Sunan tsohuwarsa Na'ama, ita kuwa Ba'ammoniya ce. 22 Mutanen Yahuza suka yi wa Ubangiji zunubi. Suka tsokane shi ya yi fushi saboda zunuban da suka aikata fiye da abin da kakanninsu suka yi. 23 Gama su ma sun gina wa kansu wuraren tsafi a tuddai, da ginshiƙai, da gumaka a tuddai, da cikin duhuwar itatuwa. 24 Fiye da haka kuma akwai mata da maza da suke aikin karuwanci a wuraren da suke tsafin a wurin al'ummai. Mutanen Yahuza sun yi dukan abubuwan ƙazanta na al'ummai waɗanda Ubangiji ya kora sa'ad da Isra'ilawa suke gab da shigar ƙasar. 25 A cikin shekara ta biyar ta sarautar sarki Rehobowam, sai Shishak Sarkin Masar ya kai wa Urushalima yaƙi. 26 Ya kwashe dukiyar Haikalin Ubangiji, da dukiyar gidan sarki duka. Ya kuma kwashe garkuwoyin zinariya waɗanda Sulemanu ya yi. 27 A maimakonsu kuwa sarki Rehobowam ya yi garkuwoyin tagulla, ya sa a hannun shugabannin masu tsaro waɗanda suke tsaron ƙofar gidan sarki. 28 Duk lokacin da sarki ya shiga Haikalin Ubangiji, sai matsara su ɗauki garkuwoyin, su kuma mayar da su a ɗakin tsaro. 29 Sauran ayyukan Rehobowam, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 30 Kullum akan yi ta yin yaƙi tsakanin Rehobowam da Yerobowam, 31 Rehobowam kuwa ya rasu, aka binne shi a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Na'ama, ita kuwa Ba'ammoniya ce. Ɗansa, Abaija ya gāji sarautar.

1 Sarakuna 15

Sarki Abaija na Yahuza

1 A shekara ta goma sha takwas ta sarautar sarki Yerobowam ɗan Nebat, Abaija ya sarauci mutanen Yahuza. 2 Ya yi mulki shekara uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ma'aka, 'yar Absalom, wato kakarsa. 3 Shi kuma ya aikata dukan irin zunubai da tsohonsa ya yi. Bai yi aminci ga Ubangiji Allahnsa sosai, kamar yadda kakansa, Dawuda, ya yi ba. 4 Amma duk da haka, saboda Dawuda, Ubangiji Allahnsa ya ba shi fitila a Urushalima da ya sa ɗansa ya gāje shi, ya kuma kafa Urushalima, 5 domin Dawuda ya aikata abu mai kyau a gaban Ubangiji. Bai ƙetare umarnin da Ubangiji ya ba shi ba dukan kwanakin ransa, sai dai a kan Uriya Bahitte. 6 Akwai yaƙi tsakanin Abaija da Yerobowam dukan kwanakin ransa. 7 Sauran ayyukan Abaija da dukan abin da ya aikata, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 8 Abaija ya rasu, suka binne shi a Urushalima. Ɗansa Asa ya gāji sarautarsa.

Sarki Asa na Yahuza

9 A cikin shekara ta ashirin ta sarautar Yerobowam Sarkin Isra'ila, Asa ya sarauci jama'ar Yahuza. 10 Ya yi shekara arba'in da ɗaya yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ma'aka, 'yar Absalom, wato kakarsa. 11 Asa kuwa ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda kakansa, Dawuda, ya yi. 12 Ya kori mata da maza da suke karuwanci a wuraren tsafi na arna a ƙasar, ya kuma kawar da gumakan da kakanninsa suka yi. 13 Ya kuma fitar da tsohuwarsa Ma'aka daga zaman sarauniya, domin ta yi ƙazantacciyar siffa ta gunkiyar Ashtoret. Asa ya sassare siffar, ya ƙone ta a rafin Kidron. 14 Amma ba a kawar da wuraren tsafi na tuddai ba, duk da haka Asa ya yi aminci sosai ga Ubangiji dukan kwanakinsa. 15 Ya kawo dukan tsarkakakkun abubuwan da tsohonsa ya keɓe, da kuma azurfa, da zinariya, da kwanoni waɗanda shi kansa ya yi, a cikin Haikalin Ubangiji.

Alkawari Tsakanin Asa da Ben-hadad

16 Aka yi ta yaƙi tsakanin Asa da Ba'asha, Sarkin Isra'ila a dukan kwanakin mulkinsu. 17 Ba'asha, Sarkin Isra'ila, ya kai wa Yahuza yaƙi. Sai ya gina Rama don ya hana kowa ya fita ko kuma ya shiga wurin Asa, Sarkin Yahuza. 18 Sa'an nan Asa ya kwashe dukan azurfa da zinariya da suka ragu a ɗakunan ajiya na Haikalin Ubangiji, da na gidan sarki, ya ba barorinsa su kai wa Ben-hadad ɗan Tabrimmon, ɗan Heziyon, Sarkin Suriya, wanda yake zaune a Dimashƙu, ya ce, 19 “Bari mu ƙulla alkawari da juna kamar yadda tsohona da tsohonka suka yi, ga shi, na aika maka da kyautar azurfa da zinariya. Sai ka tafi, ka warware alkawarinka da Ba'asha, Sarkin Isra'ila, domin ya tashi ya bar ni.” 20 Ben-hadad kuwa ya yarda da maganar sarki Asa. Ya kuwa aiki shugabannin sojojinsa su yi yaƙi da garuruwan Isra'ila. Su kuwa suka tafi, suka ci Iyon, da Dan, da Abel-bet-ma'aka, da dukan Kinneret, da dukan ƙasar Naftali. 21 Da Ba'asha ya ji labari, sai ya daina ginin Rama, ya tafi ya zauna a Tirza. 22 Sa'an nan sarki Asa ya gayyaci dukan jama'ar Yahuza, ba wanda aka ɗauke wa. Suka tafi suka kwashe duwatsu da katakai waɗanda Ba'asha yake ginin Rama da su. Da su sarki Asa ya gina Geba ta Biliyaminu, da Mizfa. 23 Sauran dukan ayyukan Asa, da dukan ƙarfinsa, da dukan abin da ya yi, da garuruwan da ya gina, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. Amma da ya tsufa, sai ya sami ciwo a ƙafafunsa. 24 Asa kuwa ya rasu, aka binne shi a Urushalima, Ɗansa Yehoshafat ya gāji sarautarsa.

Sarki Nadab na Isra'ila

25 Nadab ɗan Yerobowam ya ci sarautar Isra'ila a shekara ta biyu ta sarautar Asa Sarkin Yahuza. Ya yi sarautar Isra'ila shekara biyu. 26 Ya yi wa Ubangiji zunubi kamar yadda tsohonsa ya yi, ya kuma sa Isra'ila su yi zunubi. 27 Ba'asha ɗan Ahija kuwa daga gidan Issaka ya yi wa Nadab maƙarƙashiya, ya kashe shi a Gibbeton ta Filistiyawa, gama Nadab da mutanen Isra'ila sun kewaye Gibbeton da yaƙi. 28 Haka Ba'asha ya kashe Nadab a shekara ta uku ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, ya kuwa ci sarautar a maimakonsa. 29 Nan da nan da ya zama sarki, sai ya kashe dukan mutanen gidan Yerobowam, bai bar wani na gidan Yerobowam da rai ba, ya hallaka su sarai, bisa ga maganar Ubangiji wadda ya faɗa wa bawansa Ahija mutumin Shilo. 30 Wannan abu ya faru saboda zunubin Yerobowam da zunubin da ya sa mutanen Isra'ila su yi, ya tsokani fushin Ubangiji Allah na Isra'ila. 31 Sauran ayyukan Nadab, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 32 Aka yi ta yaƙi tsakanin Asa Sarkin Yahuza, da Ba'asha Sarkin Isra'ila dukan kwanakin sarautarsu.

Sarki Ba'asha na Isra'ila

33 A cikin shekara ta uku ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, Ba'asha ɗan Ahija ya yi sarautar Isra'ila a Tirza. Ya yi shekara ashirin da huɗu yana sarauta. 34 Ya aikata zunubi a gaban Ubangiji. Ya bi hanyar Yerobowam da zunubin da ya sa mutanen Isra'ila su yi.

1 Sarakuna 16

1 Ubangiji ya yi magana da Yehu, ɗan Hanani a kan Ba'asha, ya ce, 2 “Tun da yake na ɗauke ka daga cikin ƙura, na maishe ka shugaban jama'ata Isra'ila, kai kuwa ka bi hanyar Yerobowam, ka sa jama'ata, wato Isra'ila, su yi zunubi, suka sa na yi fushi saboda zunubansu, 3 to, zan shafe ka da gidansa, in mai da gidanka kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat. 4 Duk mutumin da yake naka da zai mutu a cikin birni, karnuka ne za su cinye shi. Wanda kuma ya mutu a saura, tsuntsaye ne za su cinye shi.” 5 Sauran ayyukan Ba'asha, da dukan abin da ya yi, da irin ƙarfinsa, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 6 Ba'asha kuwa ya rasu, aka binne shi a Tirza. Sai Ila, ɗansa ya gāji sarautarsa. 7 Ubangiji kuma ya yi magana da Yehu ɗan Hanani, a kan Ba'asha da gidansa, saboda muguntar da ya aikata a gaban Ubangiji, har ya sa Ubangiji ya yi fushi, gama abin da ya aikata ya yi daidai da na Yerobowam, saboda kuma ya hallaka gidan Yerobowam.

Sarki Ila na Isra'ila

8 A shekara ta ashirin da shida ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, Ila ɗan Ba'asha, ya ci sarautar Isra'ila a Tirza. Ya yi sarauta shekara biyu. 9 Amma Zimri, shugaban rabin karusan Ila, ya yi masa maƙarƙashiya. Sa'ad da Ila yake Tirza, ya sha, ya bugu a gidan Arza wanda yake lura da fāda, 10 sai Zimri ya shiga gidan, ya buge shi ya kashe shi. Wannan ya faru a shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza. 11 Da Zimri ya zama sarki, nan da nan sai ya kashe dukan mutanen gidan Ba'asha, bai bar masa wani namiji, ko dangi, ko aboki ba. 12 Haka Zimri ya hallaka gidan Ba'asha bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa a kansa ta bakin annabi Yehu. 13 Wannan kuwa ya faru saboda zunuban Ba'asha da na ɗansa Ila, da zunuban da suka sa jama'ar Isra'ila su yi, har suka sa Ubangiji Allah na Isra'ila ya yi fushi saboda gumakansu. 14 Sauran ayyukan Ila da dukan abin da ya yi an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

Sarki Zimri na Isra'ila

15 A shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, Zimri ya yi sarauta kwana bakwai a Tirza. A lokacin nan sojoji suka kai wa Gibbeton ta Filistiyawa yaƙi. 16 Da sojojin da suke bakin dāga suka ji an ce Zimri ya shirya makirci, ya kashe sarki, sai dukan Isra'ilawa suka naɗa Omri, shugaban sojojin, can a sansani. A wannan rana ya zama Sarkin Isra'ila. 17 Omri kuwa ya tashi daga Gibbeton tare da dukan Isra'ila, suka kai wa Tirza yaƙi. 18 Da Zimri ya ga an ci birnin, sai ya tafi ya shiga hasumiyar da take a fāda, ya sa wa fādar wuta, wutar kuwa ta ƙone shi ya mutu. 19 Wannan ya faru saboda zunuban da ya aikata, ya yi mugun abu a gaban Ubangiji, ya bi hanyar Yerobowam da zunubinsa da ya aikata, har ya sa Isra'ilawa su yi zunubi. 20 Sauran ayyukan Zimri da makircin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

Sarki Omri na Isra'ila

21 Jama'ar Isra'ila suka rabu biyu. Rabi suka bi Tibni ɗan Ginat don su naɗa shi sarki. Rabin kuwa suka bi Omri. 22 Amma jama'ar da suka bi Omri suka rinjayi waɗanda suka bi Tibni ɗan Ginat. Sai Tibni ya mutu, Omri kuwa ya zama sarki. 23 A shekara ta talatin da ɗaya ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, Omri ya ci sarautar Isra'ila. Ya yi shekara goma sha biyu yana sarauta. Ya yi shekara shida yana mulki a Tirza. 24 Sa'an nan ya sayi tudun Samariya daga Shemer a bakin azurfa dubu shida (6,000 ), a wurin Shemer, ya kuwa yi gini a kan tudun, ya sa masa suna Samariya saboda sunan Shemer mai tudun. 25 Omri kuwa ya aikata mugunta a gaban Ubangiji fiye da dukan waɗanda suka riga shi. 26 Ya bi duk irin hanyoyin Yerobowam ɗan Nebat, da irin zunuban da ya sa jama'ar Isra'ila su yi. Suka sa Ubangiji Allah na Isra'ila ya yi fushi saboda gumakansu. 27 Sauran ayyukan da Omri ya yi, da kama-karyar da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 28 Omri kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Ɗansa Ahab ya gāji sarautarsa.

Sarki Ahab na Isra'ila

29 A shekara ta talatin da takwas ta sarautar Asa, Sarkin Yahuza, Ahab ɗan Omri ya yi sarautar Isra'ila. Ahab ɗan Omri kuwa ya yi sarautar Isra'ila a Samariya shekara ashirin da biyu. 30 Shi kuma ya aikata mugunta a gaban Ubangiji fiye da dukan waɗanda suka riga shi. 31 Da yake abu ne mai sauƙi a gare shi ya bi hanyar zunuban Yerobowam ɗan Nebat, sai ya auro Yezebel 'yar Etba'al, Sarkin Sidon, ya kuma bauta wa gunkin nan Ba'al, ya yi masa sujada. 32 Ya gina wa Ba'al bagade a matsafar Ba'al ɗin, da ya gina a Samariya. 33 Ahab kuma ya yi gunkiyan nan Ashtoret. Ahab dai ya yi abin da ya sa Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya yi fushi fiye da dukan sarakunan Isra'ila waɗanda suka riga shi. 34 A cikin kwanakinsa, Hiyel mutumin Betel ya gina Yariko. Ya yi hasarar ɗan farinsa, Abiram, sa'ad da ya kafa harsashin ginin, ya kuma yi hasarar autansa, Segub, sa'ad da ya sa ƙofofin, kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Joshuwa ɗan Nun.

1 Sarakuna 17

Iliya ya yi Annabci za a yi Fari

1 Wani annabi mai suna Iliya, mutumin Tishbi a Gileyad, ya ce wa sarki Ahab, “Na rantse da Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda nake bauta wa, ba za a yi raɓa ko ruwan sama cikin shekarun nan ba, sai da faɗata.” 2 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Iliya, 3 “Ka tashi daga nan ka nufi wajen gabas, ka ɓuya a rafin Kerit, a gabashin Urdun. 4 Za ka riƙa samun ruwan sha daga rafin, na kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.” 5 Iliya kuwa ya tafi, ya yi yadda Ubangiji ya faɗa, ya tafi ya zauna a rafin Kerit wanda yake gabashin Urdun. 6 Hankaki kuma suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da maraice. Yakan kuma sha ruwa daga rafin. 7 Da aka jima sai rafin ya ƙafe saboda ba a yin ruwan sama a ƙasar.

Iliya da Mace Gwauruwa a Zarefat

8 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Iliya. 9 “Tashi ka tafi Zarefat ta Sidon, ka zauna a can. Ga shi, na umarci wata mace wadda mijinta ya rasu ta ciyar da kai.” 10 Sai ya tashi, ya tafi Zarefat. Sa'ad da ya isa ƙofar garin, sai ga wata wadda mijinta ya rasu tana tattara itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa in sha.” 11 Ta juya ta tafi don ta kawo masa ruwan sha ke nan, sai ya sāke kiranta, ya ce, “Ki kuma kawo mini ɗan abinci.” 12 Ta ce, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da abinci, sai dai ɗan gārin da ya ragu a tukunya, da ɗan man da take cikin kurtu. Ga shi, ina tattara itacen don in je in shirya shi domin ni da ɗana, mu ci. Shi ke nan, ba sauran wani abu kuma, sai mutuwa.” 13 Amma Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, ki tafi, ki yi yadda kika ce, amma ki fara yi mini 'yar waina, ki kawo mini, sa'an nan ki yi wa kanki da ɗanki. 14 Gama Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Garin da yake a tukunyarki ba zai ƙare ba, man da yake a kurtunki kuma ba zai ƙare ba, sai ran da Ubangiji ya sa aka yi ruwan sama a ƙasar.’ ” 15 Ta tafi, ta yi yadda Iliya ya ce, dukansu kuwa suka sami isasshen abinci har kwanaki da yawa. 16 Garin da yake cikin tukunyar bai ƙare ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya. 17 Bayan wannan sai ɗan macen, wato ɗan uwargijiyar gidan, ya yi ciwo. Ciwon kuwa ya tsananta har ransa ya fita. 18 Sai macen ta ce wa Iliya, “Me ya haɗa ni da kai, ya mutumin Allah? Ka zo don ka nuna wa Allah zunubina, ka zama sanadin mutuwar ɗana?” 19 Iliya ya ce mata, “Ki kawo mini ɗanki.” Ya karɓe shi daga wurinta, ya kai shi a bene inda yake kwana. Ya kwantar da shi a gadonsa. 20 Sa'an nan ya yi addu'a da gaske ga Ubangiji, ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wa gwauruwan nan da nake zaune wurinta masifa, ka aukar wa ɗanta da ajali?” 21 Sa'an nan ya kwanta ya miƙe a kan yaron sau uku, ya kuma yi addu'a ga Ubangiji, ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka sa ran yaron nan ya komo cikinsa.” 22 Ubangiji kuwa ya amsa wa Iliya, ran yaron ya komo cikinsa, sai ya farfaɗo. 23 Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga soro, ya kai shi cikin gida, ya ba uwar. Ya ce mata, “Ki gani, ɗanki yana da rai.” 24 Sai macen ta ce wa Iliya, “Yanzu na sani kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuwa yana magana ta wurinka.”

1 Sarakuna 18

Iliya ya Koma gun Ahab

1 Bayan 'yan kwanaki, sai Ubangiji ya yi magana da Iliya a shekara ta uku, ya ce, “Tafi, ka nuna kanka ga Ahab, ni kuwa zan sa a yi ruwan sama.” 2 Sai Iliya ya tafi. A lokacin kuwa yunwa ta tsananta a Samariya. 3 Ahab kuwa ya kira Obadiya, shugaban gidansa. Obadiya kuwa mai tsoron Ubangiji ne sosai. 4 A lokacin da Yezebel ta karkashe annabawan Ubangiji, Obadiya ya kwashe annabawa ɗari ya raba su hamsin hamsin ya ɓoye su a kogo, ya ciyar da su, ya shayar da su. 5 Sai Ahab ya ce wa Obadiya, “Ka tafi ko'ina a ƙasar duk inda maɓuɓɓugan ruwa suke, da inda fadamu suke duka, watakila ma sami ciyawa mu ceci rayukan dawakai da alfadarai, don kada mu rasa waɗansu.” 6 Saboda haka suka rabu biyu don su zagaya. Ahab ya bi waje guda, shi kuma ya bi ɗaya wajen. 7 Sa'ad da Obadiya yake tafiya a hanya suka yi kaciɓis da Iliya, Obadiya kuwa ya rabe da shi, sai ya rusuna ya ce, “Shugabana Iliya, kai ne kuwa?” 8 Iliya ya amsa masa ya ce, “Ni ne. Tafi, ka faɗa wa shugabanka, sarki, cewa ga ni nan.” 9 Obadiya ya ce, “Wane laifi na yi, har da za ka ba da ni a hannun Ahab ya kashe ni? 10 Na rantse da Ubangiji Allahnka mai rai, ba al'umma ko mulki da shugabana sarki bai aika a nemo ka ba. In suka ce ba ka nan, sai ya sa mulkin ko al'ummar su rantse, cewa ai, ba su same ka ba. 11 Yanzu kuwa ka ce, in tafi in faɗa masa, cewa ga ka a nan? 12 Rabuwata da kai ke da wuya, sai Ruhun Ubangiji ya kai ka wurin da ban sani ba, don haka, in na tafi na faɗa wa Ahab, in bai same ka ba, to, ni zai kashe, ko da yake ni baranka, tun ina saurayi nake tsoron Ubangiji. 13 Ashe, ba ka ji ba? Na kasa annabawan Ubangiji biyu, na ɓoye su a kogo hamsin hamsin, sa'ad da Yezebel ta kashe annabawan Ubangiji, na ciyar da su, na kuma shayar da su. 14 Yanzu kuwa ka ce, in tafi in faɗa wa sarki Ahab, cewa ga ka nan, ai, zai kashe ni.” 15 Iliya kuwa ya ce, “Na rantse da ran Ubangiji Mai Runduna, wanda nake tsaye a gabansa, hakika zan nuna kaina gare shi yau.” 16 Saboda haka sai Obadiya ya tafi wurin Ahab ya faɗa masa, Ahab kuwa ya tafi wurin Iliya. 17 Sa'ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Kai ne, wanda kake wahalar da Isra'ila?” 18 Iliya kuwa ya amsa ya ce, “Ban wahalar da Isra'ila ba, kai ne da tsohonka, gama kuna ƙin bin umarnan Ubangiji, kuna yi wa Ba'al sujada. 19 Yanzu fa ka aika a tattara mini Isra'ila duka a dutsen Karmel, da annabawan Ba'al, su ɗari huɗu da hamsin, da annabawan Ashtoret kuma, su ɗari huɗu waɗanda Yezebel yake kula da su.”

Iliya da Annabawan Ba'al

20 Sai Ahab ya aika wa dukan jama'ar Isra'ila, ya tattara annabawa ɗin tare da su a dutsen Karmel. 21 Iliya kuwa ya zo kusa da jama'a ya ce, “Har yaushe za ku daina yawo da hankalinku? Idan Ubangiji shi ne Allah, to, ku bauta masa, in kuwa Ba'al ne Allah, to, ku bauta masa.” Mutane duk suka yi tsit, ba su ce uffan ba. 22 Sa'an nan ya ce wa jama'a, “Ni kaɗai ne annabin Ubangiji da ya ragu, amma annabawan Ba'al ɗari huɗu ne da hamsin. 23 To, a ba mu bijimi biyu, su su zaɓi guda su yanyanka gunduwa gunduwa, su shimfiɗa a kan itacen wuta, amma kada su kunna masa wuta. Ni kuma zan shirya ɗaya bijimin, in shimfiɗa bisa itacen wuta ba kuwa zan kunna masa wuta ba. 24 Za ku yi kira ga sunan Ba'al naku, ni kuma zan kira ga sunan Ubangiji. Allahn da ya amsa da wuta, shi ne Allah.” Jama'a duka suka yi sowar nuna yarda da wannan. 25 Sa'an nan Iliya ya ce wa annabawan Ba'al, “Ku zaɓi bijimi guda, ku shirya shi da farko, gama kuna da yawa, sa'an nan ku yi kira ga sunan Ba'al ɗinku, amma fa kada ku kunna wuta.” 26 Suka kuwa kama bijimin da aka ba su, suka gyara shi suka yi ta kira ga sunan Ba'al tun da safe, har tsakar ranar suna ta cewa, “Ya Ba'al, ka amsa mana!” Amma ba murya, ba kuwa wanda ya amsa. Suka yi ta tsalle a wajen bagaden da suka gina. 27 Da rana ta yi tsaka sai Iliya ya yi musu ba'a, ya ce musu, “Ku kira da babbar murya, gama shi wani allah ne, watakila yana tunani ne, ko kuwa ya zagaya ne, ko kuma ya yi tafiya. Watakila kuma yana barci ne, sai a tashe shi.” 28 Suka yi ta kira da ƙarfi bisa ga al'adarsu, suna kuma tsattsaga jikunansu da wuƙaƙe, jini yana ta zuba. 29 Suka yi ta sambatu har azahar, lokacin ba da hadaya, amma ba muryar kowa, ba amsa, ba wanda ya kula. 30 Sa'an nan Iliya ya ce wa jama'a duka su zo kusa da shi. Jama'a duka kuwa suka zo kusa da shi. Sai ya gyara bagaden Ubangiji wanda aka lalatar. 31 Ya ɗibi duwatsu goma sha biyu bisa ga yawan kabilan 'ya'yan Yakubu, wanda Ubangiji ya ce masa, “Za a kira sunanka Isra'ila.” 32 Ya kuwa gina bagade da duwatsun da sunan Ubangiji. Ya kuma haƙa wuriya kewaye da bagaden, za ta ci kamar misalin garwar ruwa guda. 33 Ya shirya itacen wuta, ya yanyanka bijimin gunduwa gunduwa, ya shimfiɗa shi bisa itacen. Sa'an nan ya ce a cika tuluna huɗu da ruwa, a kwarara a kan hadaya ta ƙonawar da kan itacen. 34 Ya kuma sa a kwarara sau na biyu, suka kwarara sau na biyun. Ya ce kuma a kwarara sau na uku, sai suka kwarara sau na ukun. 35 Ruwa kuwa ya malale bagaden, ya cika wuriyar da aka haƙa. 36 A lokacin miƙa hadaya ta maraice, sai annabi Iliya ya matso kuwa, ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Isra'ila, bari ya zama sananne a wannan rana, cewa kai ne Allah a Isra'ila, ni kuma bawanka ne, na yi waɗannan abubuwa duka bisa ga maganarka. 37 Ka amsa mini, ya Ubangiji, ka amsa mini, domin waɗannan mutane su sani, kai Ubangiji, kai ne Allah, kai ne kuma ka juyo da zuciyarsu.” 38 Ubangiji kuwa ya sa wuta ta faɗo, ta cinye hadaya ta ƙonawa, da itacen, da duwatsun, da ƙurar, ta kuma lashe ruwan da yake cikin wuriyar. 39 Sa'ad da dukan mutane suka ga haka, sai suka rusuna suka sunkuyar da kai suka ce, “Ubangiji shi ne Allah, Ubangiji shi ne Allah.” 40 Iliya kuma ya ce musu, “Ku kama annabawan Ba'al, kada ku bar ko ɗaya ya tsere.” Iliya kuwa ya kai su rafin Kishon, ya karkashe su a can.

Ƙarshen Fari

41 Iliya kuwa ya ce wa Ahab, “Sai ka haura ka ci ka sha, gama akwai motsin sakowar ruwan sama.” 42 Sai Ahab ya haura don ya ci ya sha, Iliya kuwa ya hau can ƙwanƙolin Karmel, ya zauna ƙasa, ya haɗa kai da gwiwa. 43 Sa'an nan ya ce wa baransa, “Ka tafi ka duba wajen teku.” Baran kuwa ya tafi ya duba, ya komo ya ce, “Ban ga kome ba.” Sai ya ce, “Ka yi tafiya kana dubawa, har sau bakwai.” 44 A zuwa na bakwai sai ya ce, “Na ga wani ɗan girgije kamar tafin hannu yana tasowa daga teku.” Iliya kuma ya ce, “Tafi, ka faɗa wa Ahab ya shirya karusarsa ya sauka don kada ruwan sama ya hana shi sauka.” 45 Jim kaɗan sai sararin sama ya yi baƙi ƙirin da gizagizai da iska, aka yi ruwan sama mai yawan gaske. Ahab kuwa ya hau karusarsa ya tafi Yezreyel. 46 Ubangiji kuwa ya saukar wa Iliya da iko, ya sha ɗamara, ya sheka a guje, ya riga Ahab isa Yezreyel.

1 Sarakuna 19

Iliya a Dutsen Sina'i

1 Ahab kuwa ya faɗa wa Yezebel dukan abin da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe annabawan Ba'al duka. 2 Sai Yezebel ta aike a wurin Iliya ta ce, “Idan gobe war haka, ban kashe ka ba kamar yadda ka karkashe annabawan nan, to, alloli su hukunta ni.” 3 Sai Iliya ya ji tsoro, ya tashi, ya tsere zuwa Biyer-sheba ta Yahuza. Ya bar baransa a can. 4 Iliya ya yi tafiyarsa yini guda cikin jeji, ya tafi ya zauna a gindin wani itace ya yi roƙo domin ya mutu, yana cewa, “Yanzu ya isa haka, ya Ubangiji, ka karɓi raina, gama ban fi kakannina ba.” 5 Iliya kuwa ya kwanta, ya yi ta barci a gindin itacen. Farat sai mala'ika ya taba shi, ya ce masa, “Tashi, ka ci abinci.” 6 Da ya duba, sai ga waina da zafinta a bisa duwatsu, da butar ruwa a waje ɗaya. Ya ci, ya sha, ya koma kwantawa. 7 Mala'ikan Ubangiji kuma ya sake zuwa sau na biyu, ya taɓa shi, ya ce, “Tashi, ka ci abinci, in ba haka ba kuwa tafiya za ta gagare ka.” 8 Sai Iliya ya tashi ya ci abinci ya sha ruwa ya sami ƙarfi, sa'an nan ya kama tafiya kwana arba'in dare da rana har zuwa Horeb, wato dutsen Allah. 9 A can ya shiga wani kogo domin ya kwana. Ba labari sai Ubangiji ya yi magana da shi, ya ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?” 10 Ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, Allah Mai Runduna, kai kaɗai nake bauta wa kullayaumin. Amma jama'ar Isra'ila sun karya alkawarinka, sun rurrushe bagadanka, sun karkashe annabawanka, ni ne kaɗai na ragu, ga shi kuma, suna nema su kashe ni.” 11 Ubangiji ya ce masa, “Tafi, ka tsaya a kan dutse, a gabana.” Sai ga Ubangiji yana wucewa, babbar iska mai ƙarfi ta tsage dutsen, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasar. 12 Bayan girgizar kuma, sai wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wutar. Bayan wutar sai ƙaramar murya. 13 Sa'ad da Iliya ya ji muryar, sai ya rufe fuskarsa da alkyabbarsa, ya fita, ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?” 14 Ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, Allah Mai Runduna, kai kaɗai nake bauta wa kullayaumin. Amma jama'ar Isra'ila sun karya alkawarinka, sun rurrushe bagadanka, sun karkashe annabawanka, ni ne kaɗai na ragu, ga shi kuma, suna nema su kashe ni.” 15 Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka juya zuwa jeji kusa da Dimashƙu, idan ka isa can, sai ka zuba wa Hazayel mai, ka keɓe shi, ya sama Sarkin Suriya, 16 da Yehu ɗan Nimshi, ka keɓe shi, ya zama Sarkin Isra'ila. Ka kuma zuba wa Elisha, ɗan Shafat na Abel-mehola, mai, ka keɓe shi, ya zama annabi a maimakonka. 17 Duk wanda zai tsere wa Hazayel, Yehu zai kashe shi. Wanda kuma ya tsere wa Yehu. Elisha zai kashe shi. 18 Duk da haka zan rage mutum dubu bakwai(7,000 ) na Isra'ila waɗanda ba su rusuna wa Ba'al da gwiwoyinsu ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”

An Kira Elisha

19 Iliya fa ya tashi daga wurin nan, ya tarar da Elisha ɗan Shafat, yana tare da shanu, garma goma sha biyu. Yana tare da na sha biyun, sai Iliya ya bi ta kusa da shi, ya jefa masa alkyabbarsa. 20 Sai ya bar shanun noma, ya sheƙa gun Iliya, ya ce, “Bari in sumbaci mahaifina da mahaifiyata, in yi bankwana da su, sa'an nan in zo in bi ka.” Sa'an nan Iliya ya ce masa, “Koma, me na yi maka?” 21 Elisha kuwa ya koma, ya kama shanun noman, ya yanka, ya dafa su da karkiyoyinsu. Ya raba wa mutane, suka ci. Sa'an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya zama mai taimakonsa.

1 Sarakuna 20

Ahab ya Ci Suriyawa

1 Ben-hadad Sarkin Suriya kuwa ya tara dukan sojojinsa. Sarakuna talatin da biyu kuma suna tare da shi, da dawakai, da karusai. Ya haura ya kai wa Samariya yaƙi. Ya kuwa yi yaƙi da ita. 2 Sai ya aika da jakadu zuwa cikin birni wurin sarki Ahab na Isra'ila, ya ce masa, “In ji Ben-hadad, 3 ‘Azurfarka da zinariyarka nawa ne, matanka kuma mafi kyau da 'ya'yanka nawa ne!’ ” 4 Ahab Sarkin Isra'ila kuwa ya amsa, ya ce, “Ya maigirma sarki, kamar yadda ka faɗa, ni naka ne da dukan abin da nake da shi.” 5 Jakadun kuwa suka sāke komawa suka ce wa Ahab, “Ben-hadad ya ce, ‘Na aika maka ka ba ni azurfarka, da zinariyarka, da matanka, da 'ya'yanka. 6 Banda haka kuma zan aiko barorina wurinka gobe war haka su bincike gidanka da gidajen fādawanka, su kwashe dukan abubuwan da kake ganin darajarsu su tafi da su.’ ” 7 Ahab Sarkin Isra'ila kuwa ya kirawo dukan dattawan ƙasar, ya ce, “Ku gani fa, ku duba yadda mutumin nan yake neman rikici, gama ya aiko don in ba shi matana, da 'ya'yana, da azurfata, da zinariyata, ni kuwa ban hana masa ba.” 8 Dukan dattawan da mutane, suka ce masa, “Kada ka kula, balle ka yarda.” 9 Sai ya ce wa jakadun Ben-hadad, “Ku ce wa maigirma, sarki, dukan abin da ya nema a wurina da farko, zan yi, amma wannan na ƙarshe, ban zan iya yi ba.” Jakadun kuwa suka koma da wannan labari. 10 Ben-hadad kuwa ya sāke aikawa wurinsa ya ce, “Bari alloli su kashe ni idan ban kai mutane da yawa da za su hallaka Samariya ba.” 11 Sarki Ahab ya amsa, ya ce, “Ku faɗa masa, sojan ainihi, sai ya gama yaƙi sa'an nan ya yi fāriya, amma ba tun kafin a fara ba.” 12 Da Ben-hadad ya ji wannan saƙo sa'ad da yake sha tare da sarakuna a sansani, sai ya ce wa mutanensa, “Kowa ya tsaya a wurinsa.” Sai kowa ya tsaya a wurinsa don yin yaƙi da birnin. 13 Ba da jimawa ba, sai ga annabi ya zo wurin sarki Ahab na Isra'ila, ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ka ga wannan babban taron sojoji? Zan ba da su a hannunka yau, za ka kuwa sani ni ne Ubangiji.’ ” 14 Ahab ya ce, “Wane ne zai yi jagorar yaƙin?” Annabin ya ce, “Ubangiji ya ce, sojoji matasa, wato na hakiman larduna, za su yi yaƙin.” Sarki ya ce, “Wa zai yi jagorar babbar rundunar?” Annabin ya ce, “Kai ne.” 15 Sai ya tara sojoji matasa na hakiman larduna, mutum ɗari biyu da talatin da biyu. Sa'an nan kuma, ya tara dukan mutanen Isra'ila dubu bakwai (7,000 ). 16 Suka tafi da tsakar rana sa'ad da Ben-hadad yake a buge da sha a sansani, shi da sarakuna talatin da biyu waɗanda suka taimake shi. 17 Samarin ne suka fara fita. Sai Ben-hadad ya aiki mutane, suka faɗa masa cewa, “Mutane suna zuwa daga Samariya.” 18 Sai ya ce, “Ku kama su da rai, ko sun zo da nufin salama ko da na yaƙi.” 19 Waɗannan kuwa suka fita daga birnin, wato sojoji matasa, rundunar Isra'ilawa kuma tana biye da su, 20 kowa ya kashe abokin gābansa. Suriyawa kuwa suka gudu, Isra'ilawa kuma suka runtume su. Amma Ben-hadad, Sarkin Suriya, ya tsere kan doki tare da mahayan dawakai. 21 Sarkin Isra'ila ya fita, ya ƙwace dawakai da karusai, ya kashe Suriyawa da yawa. 22 Sa'an nan annabin ya je wurin Sarkin Isra'ila, ya ce masa, “Tafi, ka ƙarfafa kanka, ka yi tunani sosai a kan abin da za ka yi, gama da juyawar shekara Sarkin Suriya zai kawo maka yaƙi.”

Suriyawa sun Kai Yaƙi na Biyu

23 Fādawan Sarkin Suriya suka ce masa, “Allolinsu na tuddai ne, don haka suka fi mu ƙarfi, bari mu yi yaƙi da su a cikin kwari, ta haka za mu ci su ba shakka. 24 Yanzu abin da za ka yi ke nan, sai ka fitar da sarakuna daga matsayinsu, ka sa shugabannin sojoji maimakonsu. 25 Sa'an nan ka tara sojoji kamar yawan waɗanda ka rasa, ka kuma tara dawakai a maimakon na dā, da karusai a maimakon karusai na dā. Mu kuwa za mu yi yaƙi da su a kwari. Ba shakka za mu ci su.” Sarki Ben-hadad ya ji maganarsu, ya kuwa yi hakanan. 26 Da shekara ta juyo, sai Ben-hadad ya tara Suriyawa, suka haura zuwa Afek don su yi yaƙi da Isra'ilawa. 27 Aka tara mutanen Isra'ila, aka ba su guzuri, suka tafi, su yi yaƙi da Suriyawa. Isra'ilawa suka kafa sansani a gabansu kamar 'yan garkuna biyu na awaki, amma Suriyawa suka cika ƙasar. 28 Annabin Allah kuwa ya je wurin Sarkin Isra'ila ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ‘Tun da yake Suriyawa sun ce, Ubangiji shi Allah na tuddai ne, ba Allah na kwari ba, saboda haka zan ba da dukan wannan taron jama'a a hannunka, za ka sani ni ne Ubangiji.’ ” 29 Suka kafa sansani daura da juna kwana bakwai. A rana ta bakwai ɗin, suka kama yaƙi. Isra'ilawa suka kashe Suriyawa mutum dubu ɗari (100,000 ) a rana ɗaya. 30 Sauran kuwa suka gudu zuwa birnin Afek. Garun birnin kuma ya fāɗa a kan mutum dubu ashirin da bakwai (27,000 ) waɗanda suka ragu. Ben-hadad kuwa ya gudu ya shiga ƙurewar ɗaki, a cikin birnin. 31 Fadawansa suka je suka ce masa, “Mun ji an ce sarakunan Isra'ila masu jinƙai ne, bari mu sa tufafin makoki, mu ɗaura igiyoyi a wuyanmu, sa'an nan mu tafi wurin Sarkin Isra'ila, watakila zai bar ka da rai.” 32 Sai suka sa tufafin makoki, suka ɗaura igiyoyi a wuyansu, suka tafi wurin Sarkin Isra'ila, suka ce, “Baranka, Ben-hadad, yana roƙonka ka bar shi da rai.” Ahab kuwa ya amsa ya ce, “Har yanzu yana da rai? Ai, shi kamar ɗan'uwana ne.” 33 Da ma abin da fādawan suke so su ji ke nan, sai suka yi sauri, suka karɓi maganar a bakinsa, suka ce, “I, ɗan'uwanka, Ben-hadad.” Sarki Ahab ya ce musu, “Ku je ku kawo shi.” Ben-hadad kuwa ya zo wurinsa. Ahab ya sa ya shiga tare da shi cikin karusarsa. 34 Ben-hadad ya ce masa, “Biranen da tsohona ya ƙwace daga wurin tsohonka, zan mayar maka. Kai kuma za ka yi karauku a Dimashƙu kamar yadda tsohonka ya yi a Samariya.” Sai Ahab ya ce, “Zan bar ka, ka tafi a kan wannan sharaɗi.” Ya kuwa yi alkawari da shi, sa'an nan ya bar shi, ya tafi.

Annabi ya Soki Ahab

35 Ubangiji ya umarci wani daga cikin annabawa ya ce wa abokinsa bisa ga umarnin Ubangiji, “Ina roƙonka ka buge ni.” Abokinsa kuwa ya ƙi ya buge shi. 36 Sai annabin ya ce wa wannan aboki, “Da yake ba ka yi biyayya da muryar Ubangiji ba, da tashinka daga wurina, zaki zai kashe ka.” Da ya tashi daga wurinsa, sai zaki ya gamu da shi, ya kashe shi. 37 Annabin kuma ya tarar da wani mutum, ya ce masa, “Ina roƙonka ka buge ni.” Mutumin kuwa ya buge shi da ƙarfi ya rotsa shi. 38 Sai annabin ya ɓad da kama, ya ɗaure fuskarsa da ƙyalle, ya tafi, ya jira sarki a hanya. 39 Sa'ad da sarki yake wucewa, sai ya kira sarki, ya ce, “Ni baranka na tafi yaƙi, sai ga shi, soja ya kawo mini mutum, ya ce mini, ‘Ka riƙe wannan mutum, kada ka bar shi ya kuɓuta ko da ƙaƙa, idan ka bari ya kuɓuta a bakin ranka, ko kuwa ka biya talanti ɗaya na azurfa.’ 40 Da na shiga fama da kai da kawowa sai mutumin ya tsere.” Sai Sarkin Isra'ila ya ce masa, “Haka shari'arka za ta zama, gama kai da kanka ka yanke shari'ar.” 41 Annabin ya yi saurim, ya kware ƙyallen a fuskarsa, sa'an nan sarki ya gane, ashe, ɗaya daga cikin annabawa ne. 42 Sa'an nan annabin ya ce wa sarki, “Ubangiji ya ce, ‘Da yake ka bar mutumin da na ƙaddara ga mutuwa ya kuɓuta daga hannunka, haka ranka zai zama a maimakon nasa, mutanenka kuwa a maimakon mutanensa.’ ” 43 Sarkin Isra'ila kuwa ya tafi gidansa a Samariya da baƙin ciki.

1 Sarakuna 21

Ahab da Gonar Inabin Nabot

1 Nabot Bayezreyele yana da gonar inabi a Yezreyel kusa da fādar Ahab, Sarkin Samariya. 2 Sai Ahab ya yi magana da Nabot ya ce, “Ka ba ni gonar inabinka don in mai da ita lambu, gama gonar tana kusa da gidana, ni kuwa zan ba ka wata gonar inabi a maimakonta, idan kuma kana so, sai in ba ka tamanin kuɗinta.” 3 Amma Nabot ya ce wa Ahab, “Ubangiji ya sawwaƙa in ba ka gādon kakannina.” 4 Ahab ya koma gida da baƙin ciki da rai a ɓace saboda abin da Nabot Bayezreyele ya faɗa masa. Ahab ya kwanta a gadonsa, ya mai da fuskarsa bango ya ƙi cin abinci. 5 Yezebel, matarsa kuwa ta zo wurinsa, ta ce masa, “Me ya sa ka damu, ka ruɗe haka, har ka ƙi cin abinci?” 6 Ya ce mata, “Domin na yi magana da Nabot Bayezreyele, na ce ya sayar mini da gonar inabinsa, idan kuma yana so, sai in ba shi wata gonar inabi a maimakon tasa, amma ya ce ba zai ba ni gonar inabin ba.” 7 Yezebel, matarsa, ta ce masa, “Ba kai ne kake mulkin Isra'ila ba? Tashi, ka ci abinci, ka yi farin ciki, zan ba ka gonar inabin Nabot Bayezreyele.” 8 Sa'an nan ta rubuta wasiƙu da sunan Ahab, ta hatimce su da hatiminsa, sa'an nan ta aika da wasiƙun zuwa ga dattawa da fādawan da suke zaune a birnin tare da Nabot. 9 Ta rubuta a wasiƙun, “A yi shelar azumi, a sa Nabot a gaban jama'a. 10 A kuma sa 'yan iska guda biyu, su yi ta zarginsa, su riƙa cewa, ‘Nabot ya zagi Allah da sarki.’ Sa'an nan ku tafi da shi, ku jajjefe shi da duwatsu har ya mutu.” 11 Mutanen birnin kuwa, dattawa da fādawan da suke zaune a birnin suka yi yadda Yezebel ta sa su yi, kamar yadda aka rubuta a wasiƙun da ta aika musu. 12 Suka kuwa yi shelar azumi, suka sa Nabot a gaban jama'a. 'Yan iska guda biyu suka zauna kusa da shi, suka yi ta zarginsa a gaban jama'a, suna cewa, “Nabot ya zagi Allah da sarki.” 13 Sai suka fitar da shi daga cikin birni, suka jajjefe shi da duwatsu har ya mutu. 14 Sa'an nan suka aika wa Yezebel cewa, “An jajjefi Nabot, ya mutu.” 15 Nan da nan da Yezebel ta ji an jajjefi Nabot har ya mutu, sai ta ce wa Ahab, “Tashi, ka mallaki gonar inabin Nabot, wadda ya ƙi sayar maka, gama Nabot ba shi da rai, ya mutu.” 16 Da Ahab ya ji Nabo ya mutu, sai ya tashi ya gangara zuwa gonar inabin Nabot Bayezreyele don ya mai da ta tasa. 17 Sa'an nan Ubangiji ya ce wa Iliya Batishbe, 18 “Tashi, ka tafi, ka sadu da Ahab, Sarkin Isra'ila, wanda yake a Samariya, ga shi can a gonar inabin Nabot inda ya tafi don ya mallake ta. 19 Ka faɗa masa, ni Ubangiji, na ce, ‘Ka kashe mutum, kana kuma ƙwace abin da ya mallaka?’ Ka faɗa masa ga abin da na faɗa, ‘A wurin da karnuka suka lashe jinin Nabot, a nan ne kuma karnuka za su lashe jininka.’ ” 20 Sa'ad da Ahab ya ga Iliya, sai ya ce masa, “Ka tarshe ni ko, maƙiyina?” Iliya ya amsa ya ce, “I, na tarshe ka, gama ka ba da kanka ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. 21 Saboda haka Ubangiji ya ce maka, ‘Ga shi, zan kawo maka masifa, in shafe ka, in datse maka kowane ɗa namiji, bawa ko ɗa, a Isra'ila. 22 Zan sa gidanka ya zama kamar gidan Yerobowam ɗan Nebat, da gidan Ba'asha ɗan Ahija saboda ka sa ni in yi fushi, ka kuma sa mutanen Isra'ila suka yi zunubi.’ 23 A kan Yezebel kuwa Ubangiji ya ce, ‘Karnuka za su cinye Yezebel a cikin Yezreyel.’ 24 Duk wanda yake na Ahab da zai mutu a birni karnuka ne za su cinye shi, wanda kuma ya mutu a waje tsuntsaye ne za su cinye shi.” 25 Babu wani kamar Ahab da ya ba da kansa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji. Matarsa, Yezebel, ita ce ta zuga shi. 26 Ya yi abar banƙyama ƙwarai, ya bi gumaka kamar yadda Amoriyawa suke yi, waɗanda Ubangiji ya kore su a gaban Isra'ilawa. 27 Da Ahab ya ji wannan magana, sai ya yage tufafinsa, ya sa na makoki, ya yi azumi, ya kwanta a tsummokin makoki, ya tashi yana tafiya a hankali. 28 Ubangiji ya yi magana da Iliya Batishbe ya ce, 29 “Ka ga yadda Ahab ya ƙasƙantar da kansa a gabana? Da yake ya ƙasƙantar da kansa a gabana, ba zan kawo masifar a zamaninsa ba, sai a zamanin ɗansa ne, zan kawo masifar a kan gidansa.”

1 Sarakuna 22

Mikaiya ya Yi wa Ahab Kashedi

1 Aka yi shekara uku ba a yi yaƙi tsakanin Suriya da Isra'ila ba. 2 A shekara ta uku ɗin, sai Yehoshafat, Sarkin Yahuza, ya ziyarci Sarkin Isra'ila. 3 Sarkin Isra'ila kuwa ya ce wa fādawansa, “Ko kun sani Ramot-gileyad tamu ce, ga shi kuwa, mun yi shiru, ba mu ƙwace ta daga hannun Sarkin Suriya ba?” 4 Ya kuma ce wa Yehoshafat, “Za ka tafi tare da ni zuwa wurin yaƙi a Ramot-gileyad?” Yehoshafat ya amsa wa Sarkin Isra'ila, “Ni da kai ɗaya ne, mutanena kuma mutanenka ne, dawakaina kuma naka ne.” 5 Yehoshafat ya ce wa Sarkin Isra'ila, “Ka nemi faɗar Ubangiji tukuna.” 6 Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya tara annabawa ɗari huɗu, ya tambaye su, ya ce, “In tafi in yi yaƙi da Ramot-gileyad, ko kuwa kada in tafi?” Su kuwa suka ce masa, “Ka haura, gama Ubangiji zai ba da ita a hannunka.” 7 Amma Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin da za mu tambaya kuma?” 8 Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Da sauran mutum ɗaya wanda za mu iya mu tambaya faɗar Ubangiji, shi ne Mikaiya ɗan Imla, amma ina ƙinsa, gama bai taɓa yin wani annabcin alheri a kaina ba, sai dai na masifa.” Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.” 9 Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya kirawo wani bafāde, ya ce masa, “Maza, ka taho da Mikaiya ɗan Imla.” 10 Sarkin Isra'ila da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune a kujerun sarautarsu, saye da tufafinsu a dandalin ƙofar Samariya. Annabawa kuwa suna annabci a gabansu. 11 Zadakiya ɗan Kena'ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan ƙahoni za ka tunkuyi Suriyawa har su hallaka.’ ” 12 Dukan annabawan suka yi annabci iri ɗaya, suna cewa, “Ka haura zuwa Ramot, za ka yi nasara, gama Ubangiji zai ba da ita a hannunka.” 13 Bafāden da ya tafi kiran Mikaiya ya ce masa, “Ga shi, maganar sauran annabawan iri ɗaya ce, sun yi maganar alheri ga sarki, sai kai ma ka yi magana irin tasu, ka yi maganar alheri ga sarki.” 14 Amma Mikaiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji, abin da Ubangiji ya faɗa mini, shi ne zan faɗa.” 15 Da ya zo gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Mikaiya, mu tafi Ramot don yaƙi, ko kuwa kada mu tafi?” Ya amsa masa ya ce, “Ka haura, za ka yi nasara, Ubangiji zai ba da ita a hannunka.” 16 Sarki Ahab kuwa ya ce masa, “Sau nawa zan roƙe ka kada ka faɗa mini kome sai dai gaskiya ta Ubangiji?” 17 Mikaiya ya ce, “Na ga mutanen Isra'ila duka a warwatse a kan tuddai kamar tumakin da ba su da makiyayi, Ubangiji kuwa ya ce, ‘Waɗannan ba su da shugaba, bari kowa ya koma gidansa lafiya.’ ” 18 Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka ba, ba zai yi wani annabcin alheri a kaina ba sai dai na masifa?” 19 Makaiya kuwa ya ce, “Ka ji maganar Ubangiji, gama na ga Ubangiji yana zaune a kursiyinsa. Dukan taron mala'ikun Sama suna tsaye a wajen damansa da na hagunsa. 20 Ubangiji kuwa ya ce, ‘Wa zai yaudari Ahab, ya tafi ya fāɗa wa Ramot?’ Sai wannan ya ce abu kaza, wani kuma ya ce abu kaza, 21 har da wani ruhu ya fito ya tsaya a gaban Ubangiji ya ce, ‘Ni zan yaudare shi.’ 22 Ubangiji ya ce masa, ‘Ta wace hanya?’ Sai ruhun ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukan annabawansa.’ Sai Ubangiji ya ce, ‘Ba shakka za ka yaudare shi, za ka yi nasara, sai ka tafi.’ ” 23 Mikaiya ya ce, “Ga abin da ya faru, Ubangiji ya bar annabawanka su faɗa maka ƙarya. Amma Ubangiji kansa ya riga ya zartar maka da masifa.” 24 Sa'an nan Zadakiya ɗan Kena'ana ya matso kusa ya mari Mikaiya a fuska, ya ce, “Ƙaƙa Ruhun Ubangiji ya bar ni, ya zo ya yi magana da kai?” 25 Mikaiya ya ce masa, “A ran nan za ka gani, ka kuma gudu ka shiga har ƙurewar ɗaki don ka ɓuya.” 26 Sarki Ahab ya ce, “Ku kama Mikaiya, ku kai shi wurin Amon, shugaban birnin, da wurin Yowash ɗan sarki. 27 Ku ce musu su jefa wannan mutum a kurkuku, a riƙa ciyar da shi da abinci kaɗan da ruwan sha kaɗan, har na komo lafiya.” 28 Mikaiya kuwa ya ce, “In dai ka komo lafiya, to, Ubangiji bai yi magana da ni ba.” Ya ƙara da cewa, “Kowa ya kasa kunne ga abin da na faɗa.”

Mutuwar Ahab

29 Ahab Sarkin Isra'ila da Sarkin Yahuza suka tafi Ramot-gileyad. 30 Sarkin Isra'ila kuwa ya ce wa Sarkin Yahuza, “Zan ɓad da kama in tafi wurin yaƙi, amma kai ka sa tufafinka na sarauta.” Sai Ahab ya ɓad da kama ya tafi wurin yaƙi. 31 Sarkin Suriya dai ya riga ya umarci shugabannin karusan yaƙinsa, su talatin da biyu, ya ce, “Kada ku yi yaƙi da kowa, kome matsayinsa, sai dai Ahab kaɗai.” 32 Sa'ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat, sai suka ce, “Lalle shi ne Ahab.” Sai suka juya don su yi yaƙi da shi. Yehoshafat kuwa ya yi ihu. 33 Da shugabannin karusan yaƙi suke gane ba Ahab ba ne, sai suka rabu da shi. 34 Wani sojan Suriya kuwa ya yi sa'a, ya shilla kibiya kawai, sai ta sami Ahab, ta kafar sulkensa. Saboda haka ya ce wa mai korar karusarsa, “Ka juya, ka fitar da ni daga fagen fama gama an yi mini rauni.” 35 A ran nan yaƙi ya yi tsanani. Aka tallafi Ahab a cikin karusarsa a gaban Suriyawa. Da maraice ya mutu. Jinin raunin da aka yi masa ya zuba a cikin karusar. 36 A wajen faɗuwar rana aka yi wa sojoji shela aka ce, “Kowa ya koma garinsu da ƙasarsu.” 37 Sarki Ahab ya mutu, aka kawo shi Samariya, aka binne shi. 38 Suka wanke karusarsa a tafkin Samariya. Karnuka suka lashe jininsa, karuwai kuma suka yi wanka a tafkin kamar yadda Ubangiji ya faɗa. 39 Sauran ayyukan Ahab da dukan abin da ya yi, da gidan da ya gina na hauren giwa da garuruwan da ya gina, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 40 Ahab ya rasu kamar kakanninsa. Ɗansa Ahaziya ya gāji sarautarsa.

Sarki Yehoshafat na Yahuza

41 Yehoshafat ɗan Asa ya ci sarautar Yahuza a shekara ta huɗu ta sarautar Ahab, Sarkin Isra'ila. 42 Yehoshafat yana da shekara talatin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara ashirin da biyar yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Azuba 'yar Shilhi. 43 Ya bi halin tsohonsa, Asa, bai karkace ba. Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji. Duk da haka ba a rushe wuraren tsafin na tuddai ba. Mutane suka yi ta miƙa hadayu, suka ƙona turare a tuddan. 44 Yehoshafat kuma ya ba Sarkin Isra'ila amana. 45 Sauran ayyukan Yehoshafat, da ƙarfin da ya nuna, da yadda ya yi yaƙi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 46 Ya kori dukan karuwai mata da maza da suka ragu a ƙasar a zamanin tsohonsa Asa. 47 A lokacin babu sarki a Edom sai wakili. 48 Yehoshafat ya yi jiragen ruwa a Tarshish don su tafi Ofir su kwaso zinariya, amma jiragen ba su tafi ba, gama jiragen sun farfashe a Eziyon-geber. 49 Sa'an nan Ahaziya, ɗan Ahab, ya ce wa Yehoshafat. “Ka bar barorina su tafi tare da naka a cikin jirage.” Amma Yehoshafat bai yarda ba. 50 Yehoshafat kuwa ya rasu, aka binne shi a inda aka binne kakanninsa a birnin kakansa Dawuda. Ɗansa Yehoram ya gaji sarautarsa.

Sarki Ahaziya na Isra'ila

51 Ahaziya, ɗan Ahab, ya ci sarautar Isra'ila a Samariya a shekara ta goma sha bakwai ta sarautar Yehoshafat, Sarkin Yahuza. Ya yi sarautar Isra'ila shekara biyu. 52 Ya yi zunubi a gaban Ubangiji. Ya bi halin tsohonsa da na tsohuwarsa, da na Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ila su yi zunubi. 53 Ya bauta wa gunkin nan Ba'al ya yi masa sujada. Ya kuma sa Ubangiji Allah na Isra'ila ya yi fushi, gama ya bi halin tsohonsa.

2 Sarakuna 1

Rasuwar Ahaziya

1 Bayan rasuwar Ahab, Sarkin Isra'ila, sai Mowabawa suka tayar wa Isra'ilawa. 2 Ahaziya ya faɗo daga tagar benensa a Samariya, ya kuwa ji ciwo ƙwarai. Sai ya aiki manzanni, ya ce musu, “Ku tafi, ku tambayi Ba'alzabul, gunkin Ekron, ko zan warke daga wannan ciwo.” 3 Sai mala'ikan Ubangiji ya yi magana da Iliya Batishbe, ya ce, “Tashi, ka tafi, ka sadu da manzannin Sarkin Samariya, ka ce musu, ‘Ba Allah a Isra'ila da za ku tafi ku tambayi Ba'alzabul, gunkin Ekron?’ 4 Ku faɗa wa sarki, Ubangiji ya ce, ‘Ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ” Iliya ya yi kamar yadda Ubangiji ya umarce shi, sai ya tafi. 5 Manzannin kuwa suka koma wurin sarki. Sarki ya ce, “Me ya sa kuka komo?” 6 Suka ce masa, “Wani mutum ya sadu da mu, ya ce mana, mu koma wurinka mu shaida maka, ‘Ubangiji ya ce, ba Allah a Isra'ila, har aka aike ku ku tambayi Ba'alzabul, gunkin Ekron? Domin haka ba za ka tashi daga kan gadon da kake kwance ba, amma lalle za ka mutu.’ ” 7 Sarki ya tambaye su, “Yaya mutumin yake, shi wanda ya sadu da ku, ya faɗa muku irin wannan magana?” 8 Suka ce masa, “Ai, wani gargasa ne mai ɗamara ta fata.” Sarki ya ce, “Ai, Iliya ne Batishbe.” 9 Sa'an nan sarki ya aiki shugaba tare da mutum hamsin su taho da Iliya. Mutumin kuwa ya haura wurin Iliya a kan dutse, ya ce masa, “Ya mutumin Allah, sarki ya umarta ka sauko.” 10 Iliya ya ce wa shugaban da mutum hamsin ɗin, “Idan ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da mutane naka hamsin.” Wuta kuwa ta sauko daga sama, ta cinye shugaban tare da mutanensa hamsin. 11 Sarki kuma ya sāke aiken wani shugaba tare da mutum hamsin. Suka tafi, shugaban ya ce wa Iliya, “Ya mutumin Allah, sarki ya umarta ka sauko da sauri.” 12 Iliya kuwa ya ce musu, “Idan ni mutumin Allah ne, bari wuta ta sauko daga sama ta cinye ka da mutane naka guda hamsin.” Wuta kuwa daga wurin Allah ta sauko daga sama ta cinye shugaban da mutanensa hamsin. 13 Sarki kuma ya sāke aiken wani shugaba, na uku ke nan, tare da mutanensa hamsin. Sai shugaba na uku ya tafi ya rusuna a gaban Iliya, ya roƙe shi, ya ce, “Ya mutumin Allah, ina roƙonka ka ga darajar raina da na barorinka, su hamsin. 14 Gama wuta ta sauko daga sama ta cinye shugabanni biyu tare da mutanensu hamsin hamsin, amma ka dubi darajar raina.” 15 Sa'an nan mala'ikan Ubangiji ya ce wa Iliya, “Ka sauka, ka tafi tare da shi, kada ka ji tsoronsa.” Iliya kuwa ya tashi, ya tafi tare da shi har gaban sarki. 16 Ya ce wa sarki, “Ubangiji ya ce, ‘Domin ka aiki manzanni su yi tambaya wurin Ba'alzabul, gunkin Ekron, ba Allah a Isra'ila ne wanda za ka yi tambaya a wurinsa? Domin haka ba za ka sauko daga kan gadon da kake kwance ba, amma za ka mutu lalle.’ ” 17 Ahaziya kuwa ya mutu bisa ga maganar Ubangiji, daidai yadda Iliya ya faɗa. Sai ɗan'uwansa Yehoram ya gāji gadon sarautarsa a shekara ta biyu ta Yoram ɗan Yehoshafat Sarkin Yahuza, gama Ahaziya ba shi da ɗa. 18 Sauran ayyukan da Ahaziya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

2 Sarakuna 2

An Ɗauki Iliya zuwa Sama

1 Sa'ad da Ubangiji zai ɗauki Iliya zuwa Sama cikin guguwa, Iliya da Elisha suka kama hanya daga Gilgal. 2 Sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ina roƙonka, ka dakata a nan, gama Ubangiji ya aike ni har zuwa Betel.” Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka tafi Betel. 3 Akwai wata ƙungiyar annabawa da take a Betel suka zo, suka ce wa Elisha, “Ko ka sani, yau Ubangiji zai ɗauke maigidanka?” Elisha ya ce, “I, na sani, amma mu bar zancen tukuna.” 4 Sa'an nan Iliya ya ce masa, “Elisha, ina roƙonka ka dakata a nan gama Ubangiji ya aike ni Yariko.” Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Sai suka tafi Yariko. 5 Ƙungiyar annabawa da take Yariko suka zo wurin Elisha suka ce masa, “Ko ka sani yau Ubangiji zai ɗauke maigidanka?” Ya ce, “Na sani, amma mu bar zancen tukuna.” 6 Sa'an nan Iliya ya ce masa, “Ina roƙonka, ka dakata a nan, gama Ubangiji ya aike ni zuwa Kogin Urdun.” Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji da kuma kai kanka, ba zan rabu da kai ba.” Saboda haka suka tafi tare. 7 Waɗansu annabawa hamsin kuma suka tafi tare da su. Iliya da Elisha suka tsaya kusa da kogi, annabawa hamsin ɗin suka tsaya da ɗan nisa. 8 Sa'an nan Iliya ya tuɓe alkyabbarsa, ya naɗe ta, ya bugi ruwa da ita, sai ruwan ya dāre, ya rabu biyu, dukansu biyu fa suka taka sandararriyar ƙasa suka haye. 9 Sa'ad da suka haye, sai Iliya ya ce wa Elisha, “Ka faɗa mini abin da kake so in yi maka kafin a ɗauke ni daga wurinka.” Elisha ya ce, “Bari in sami rabo daga cikin ikonka domin in gaje ka.” 10 Iliya kuwa ya ce, “Ka roƙi abu mai wuya, duk da haka, idan ka gan ni lokacin da za a ɗauke ni, to, abin da ka roƙa za ka samu, amma idan ba ka gan ni ba, to, ba za ka samu ba ke nan.” 11 Da suka ci gaba da tafiya suna taɗi, sai ga karusar wuta da dawakan wuta suka raba su. Aka ɗauke Iliya zuwa Sama cikin guguwa. 12 Elisha kuwa ya gani, ya yi kuka yana cewa, “Ubana, ubana! Mai ikon tsaron Isra'ila! Ka tafi ke nan!” Bai kuwa ƙara ganin Iliya ba.

Elisha ya Gāji Iliya

Da baƙin ciki Elisha ya kama tufafinsa ya kece. 13 Sa'an nan ya ɗauki alkyabbar Iliya wadda ta faɗo daga wurinsa, ya tafi ya tsaya a gaɓar Kogin Urdun. 14 Sai ya ɗauki alkyabban nan da ta faɗo daga wurin Iliya, ya bugi ruwan, yana cewa, “Ina Ubangiji, Allah na Iliya?” Sa'ad da ya bugi ruwan, sai ruwan ya dāre, ya rabu biyu, Elisha kuwa ya haye. 15 Sa'ad da annabawa hamsin da suke Yariko suka ga ya haye ya nufo su, sai suka ce, “Ai, ruhun Iliya yana kan Elisha.” Sai suka tafi su tarye shi, suka rusuna har ƙasa a gabansa, 16 suka kuma ce masa, “Yanzu fa, ga mu mu hamsin ƙarfafa. Bari mu tafi mu nemo maigidanka, mai yiwuwa ne Ruhun Ubangiji ya ɗauke shi, ya jefa shi kan wani dutse, ko cikin wani kwari.” Elisha ya ce, “Kada ku tafi.” 17 Amma suka matsa masa har suka i masa, sai ya yardar musu su tafi. Su kuwa suka tafi su hamsin. Suka yi ta neman Iliya, har kwana uku, amma ba su same shi ba. Op 18 Sa'an nan suka komo wurinsa a Yariko. Sai ya ce musu, “Ai, dā ma na ce muku kada ku tafi.”

Mu'ujizan Elisha

19 Waɗansu mutanen gari suka ce wa Elisha, “Ga shi, garin yana da kyan gani, amma ruwan ba kyau, yana sa ana yin ɓari.” 20 Elisha kuwa ya ce, “Ku kawo mini gishiri a sabuwar ƙwarya.” Su kuwa suka kawo masa, 21 sai ya tafi maɓuɓɓugar ruwa yana barbaɗa gishirin, ya ce, “Haka Ubangiji ya ce, ‘Na warkar da wannan ruwa, ba zai ƙara sa a mutu ko a yi ɓari ba.’ ” 22 Ruwan kuwa ya gyaru bisa ga maganar Elisha, har wa yau. 23 Daganan Elisha ya haura zuwa Betel. A hanya sai ga waɗansu samari sun fito daga cikin gari, suna yi masa eho, suna cewa, “Ka bar wurin nan, kai mai saiƙo.” 24 Elisha ya waiga, ya gan su, ya la'anta su da sunan Ubangiji. Sai waɗansu namomin jeji guda biyu suka fito daga cikin kurmi suka yayyage arba'in da biyu daga cikin samarin. 25 Daganan Elisha ya tafi har Dutsen Karmel, sa'an nan ya koma Samariya.

2 Sarakuna 3

Yaƙi Tsakanin Isra'ila da Mowab

1 A shekara ta goma sha takwas ta sarautar Yehoshafat Sarkin Yahuza, Yehoram ɗan Ahab ya zama Sarkin Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara goma sha biyu. 2 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji, amma bai kai na tsohonsa da tsohuwarsa ba, gama ya kawar da ginshiƙin gunkin nan Ba'al wanda tsohonsa ya yi. 3 Duk da haka, bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 4 Mesha Sarkin Mowab kuwa makiyayin tumaki ni. Yakan ba Sarkin Isra'ila 'yan tumaki dubu ɗari (100,000 ), da raguna dubu ɗari (100,000 ) duk da ulunsu, gandu a shekara. 5 Amma da Ahab ya rasu, Sarkin Mowab kuwa ya tayar wa Sarkin Isra'ila. 6 Sai sarki Yehoram ya fita daga Samariya a lokacin, ya tattara Isra'ila duka. 7 Ya kuma aika wa Yehoshafat Sarkin Yahuza, ya ce, “Sarkin Mowab ya tayar mini, ko za ka yarda ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowabawa?” Yehoshafat ya ce, “Zan tafi, ni kamarka ne, mutanena kuma kamar mutanenka, dawakaina kuma kamar naka. 8 Wace hanya za mu bi?” Yehoram kuwa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.” 9 Yehoram Sarkin Isra'ila ya tafi tare da Sarkin Yahuza da Sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha. 10 Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya ce, “Kaito! Ubangiji ya kirawo mu sarakunan nan uku don ya bashe mu a hannun Mowabawa.” 11 Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji ne a nan, wanda zai tambayar mana Ubangiji?” Sai ɗaya daga cikin fādawan Sarkin Isra'ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, na'ibin Iliya.” 12 Yehoshafat kuwa ya ce, “Gaskiya ne, maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sai sarakunan nan uku suka ɗunguma zuwa wurin Elisha. 13 Elisha kuwa ya ce wa Sarkin Isra'ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan tsohonka da na tsohuwarka.” Amma Sarkin Isra'ila ya ce masa, “A'a, ai, Ubangiji ya kirawo mu, mu sarakunan nan uku, don ya bashe mu a hannun Mowabawa.” 14 Elisha ya amsa ya ce, “Na rantse da Ubangiji Mai Runduna, wanda nake bautarsa, da ba domin ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuza ba, da ba zan kula da kai har ma in dube ka ba. 15 Amma yanzu ku kawo mini makaɗin garaya.” Da makaɗin garaya ya kaɗa, sai ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha. 16 Sai ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ku haƙa kududdufai a kwarin nan. 17 Ko da yake ba ku ga iska, ko ruwan sama ba, duk da haka kwarin zai cika da ruwa domin ku sha, ku da dabbobinku.’ 18 Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji, zai kuma ba da Mowabawa a hannunku. 19 Za ku ci kowane birni mai garu da kowane birni na musamman. Za ku sassare kowane kyakkyawan itace, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku lalatar da gonaki masu kyau da duwatsu.” 20 Kashegari, da safe a lokacin miƙa hadaya, sai ga ruwa ya malalo daga wajen Edom har ƙasar ta cika da ruwa. 21 Da Mowabawa suka ji labari, sarakuna sun kawo musu yaƙi, sai dukan waɗanda suka isa ɗaukar makamai, daga ƙarami zuwa babba, aka kirawo su, suka ja dāga a kan iyaka. 22 Sa'ad da suka tashi da sassafe, rana tana haskaka ruwa, sai suka ga ruwan a gabansu ja wur kamar jini. 23 Sai suka ce, “Wannan jini ne, hakika sarakunan sun yi yaƙi da juna, sun karkashe juna. Bari mu tafi mu kwashi ganima!” 24 Da suka kai sansanin Isra'ilawa, sai Isra'ilawa suka tashi, suka fāɗa musu, har suka gudu. Isra'ilawa kuwa suka bi su, suna ta karkashe su, 25 suka lalatar da biranensu, a kowace kyakkyawar gona kuma, kowannensu ya jefa dutse a cikinta, har aka cika ta da duwatsu, suka kuma tattoshe kowace maɓuɓɓugar ruwa, suka sassare kyawawan itatuwa. Babban birnin Kir-hareset kaɗai ya ragu, Isra'ilawa suka kewaye shi suka fāɗa shi da yaƙi. 26 Da Sarkin Mowab ya ga yaƙin ya juya masa baya, sai ya zaɓi masu takobi ɗari bakwai ya kutsa kai a wajen ɓayar Sarkin Edom, amma suka kāsa. 27 Sai Sarkin Mowab ya kama babban ɗansa, wanda zai gāji sarautarsa, ya miƙa shi hadayar ƙonawa a kan garu. Isra'ilawa kuwa suka tsorata ko allahn abokan gāba zai cuce su, don haka suka janye, suka koma ƙasarsu.

2 Sarakuna 4

Mai na Macen da Mijinta ya Rasu

1 Matar wani daga cikin ƙungiyar annabawa da ya rasu, ta kai kuka wurin Elisha, ta ce, “Maigidana, baranka, wato mijina, ya rasu, ka kuwa sani shi mai tsoron Ubangiji ne, amma wanda yake binsa bashi ya zo zai kwashe 'ya'yana biyu su zama bayinsa.” 2 Sai Elisha ya ce mata, “Me zan yi miki? Ki faɗa mini abin da kike da shi a gida.” Ta ce, “Ni dai ba ni da kome a cikin gidan, sai dai kurtun mai.” 3 Sa'an nan ya ce mata, “Ki tafi ki yi aron tandaye da yawa daga maƙwabtanki waɗanda ba kome a ciki. 4 Sa'an nan ki shiga ɗaki, ke da 'ya'yanki, ku rufe ƙofa. Ki ɗura mai cikin tandayen nan duka, bi da bi.” 5 Sai ta tashi daga wurinsa, ta tafi ta shiga ɗaki tare da 'ya'yanta, ta rufe ƙofar. 'Ya'yan suna kawo tandaye tana ɗurawa. 6 Da tandayen suka cika ta ce wa ɗanta, “Kawo mini wani tandu.” Ɗan kuwa ya ce mata, “Ai, ba saura.” Sai man ya janye. 7 Sai ta koma ta faɗa wa annabi Elisha, shi kuwa ya ce mata, “Ki je ki sayar da man, ki biya bashin, abin da ya ragu kuwa ki ci, ke da 'ya'yanki.”

Elisha da Attajira a Shunem

8 Wata rana Elisha ya wuce zuwa Shunem inda wata mace take da zama, sai ta gayyace shi cin abinci. Don haka duk lokacin da ya bi ta wannan hanya, sai ya ratsa ta gidanta, ya ci abinci. 9 Sai ta ce wa mijinta, “Na gane wannan mutum adali ne, mutumin Allah, wanda kullum yakan wuce ta hanyan nan. 10 Bari mu gina masa ɗan ɗaki a kan bene, mu sa masa gado, da tebur, da kujera, da fitila, don duk sa'ad da ya zo ya sauka a wurin.” 11 Wata rana da Elisha ya zo, ya shiga ɗakin, ya huta. 12 Sai ya ce wa baransa, Gehazi, “Kirawo matan nan.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a gabansa. 13 Ya ce wa Gehazi, “Ka tambaye ta me take so in yi mata saboda dukan wannan wahala da ta yi dominmu? Tana so in yi mata magana da sarki ko da shugaban sojoji?” Sai ta ce, “Ai, ina da dukan abin da nake bukata a cikin jama'ata.” 14 Elisha ya ce, “To, me za a yi mata?” Sai Gehazi ya amsa ya ce, “Ai, ba ta da ɗa, mijinta kuwa tsoho ne.” 15 Sai ya ce, “Kirawo ta.” Da ya kirawo ta, sai ta zo ta tsaya a ƙofar ɗakin. 16 Elisha kuwa ya ce mata, “Baɗi war haka za ki rungumi ɗa na kanki.” Sai ta ce, “A'a, ya shugabana, mutumin Allah, kada fa ka yi mini ƙarya.” 17 Amma macen ta sami juna biyu, ta kuwa haifi ɗa a daidai lokacin da Elisha ya faɗa mata. 18 Da yaron ya yi girma, sai wata rana ya bi mahaifinsa gona zuwa wurin masu girbi. 19 Sai ya ce wa mahaifinsa, “Wayyo, kaina, kaina.” Uban kuwa ya ce wa baransa, “Ka ɗauke shi, ka kai shi wurin uwar.” 20 Da aka ɗauke shi, aka kai wa uwar, sai ya zauna a cinyar uwar har rana tsaka, sa'an nan ya rasu. 21 Sai ta hau, ta kwantar da shi a gadon annabi Elisha, sa'an nan ta rufe ƙofa, ta fita. 22 Sa'an nan ta aika a faɗa wa mijinta, ta ce, “Ka aiko mini ɗaya daga cikin barori da jaki domin in tafi wurin annabi Elisha, zan komo da sauri.” 23 Sai ya ce, “Me ya sa za ki tafi wurinsa yau? Ai, yau ba amaryar wata ba ce, ba kuwa ranar Asabar ba ce.” Ita kuwa ta ce, “Ba kome, kada ka damu.” 24 Amma ta yi wa jakin shimfiɗa, ta kuma ce wa baranta, “Yi ta kora mini jakin, kada ka sassauta, sai na faɗa maka.” 25 Sai ta kama hanya, ta tafi wurin annabi Elisha a Dutsen Karmel. Sa'ad da annabi Elisha ya gan ta zuwa, sai ya ce wa Gehazi, wato baransa, “Duba, ga Bashunemiya can. 26 Ruga ka tarye ta, ka tambayi lafiyarta, da ta mijinta, da ta ɗanta.” Ta amsa, ta ce, “Lafiya ƙalau.” 27 Sa'ad da ta isa wurin annabi Elisha a kan dutsen, sai ta kama ƙafafunsa. Sai Gehazi ya zo zai ture ta. Amma mutumin Allah ya ce masa, “Ƙyale ta kurum, gama tana da baƙin ciki ƙwarai, Ubangiji kuwa ya ɓoye mini abin.” 28 Matar ta ce masa, “Na roƙe ka ka ba ni ɗa ne? Ashe, ban ce maka kada ka ruɗe ni ba?” 29 Elisha ya ce wa Gehazi, “Yi ɗamara, ka ɗauki sandana ka tafi. Duk wanda ka gamu da shi, kada ka gaishe shi, duk kuma wanda ya gaishe ka kada ka amsa, ka tafi ka ɗora sandana a fuskar yaron.” 30 Sai macen ta ce, “Na rantse da Ubangiji da kai kuma, ba zan bar ka ba.” Sai Elisha ya tashi, ya bi ta. 31 Gehazi kuma ya yi gaba, ya ɗora sandan a fuskar yaron, amma ba motsi ko alamar rai. Saboda haka ya koma, ya taryi Elisha, ya faɗa masa yaron bai farka ba. 32 Da Elisha ya kai ɗakin, ya ga yaron yana kwance matacce a gadonsa. 33 Sai ya shiga ya rufe ƙofa, daga shi sai yaron, ya yi addu'a ga Ubangiji. 34 Sa'an nan ya kwanta a kan yaron, ya sa bakinsa a bakin yaron, ya sa idanunsa a idanun yaron, hannuwansa kuma a kan na yaron, ya miƙe jikinsa akan yaron, sai jikin yaron ya yi ɗumi. 35 Elisha ya tashi, ya yi ta kai da komowa a cikin gidan, sa'an nan ya sāke hawan ɗakin, ya miƙe a kan yaron, sai yaron ya yi atishawa har sau bakwai, yaron kuma ya buɗe idanu. 36 Sai ya kira Gehazi ya ce, “Kirawo Bashunemiyar.” Sai ya kirawo ta. Da ta zo wurinsa, ya ce, “Ki ɗauki ɗanki.” 37 Ta kuwa zo, ta faɗi a gaban Elisha har ƙasa, sa'an nan ta ɗauki ɗanta, ta fita.

Mu'ujizai biyu domin Annabawa

38 Elisha kuwa ya koma Gilgal sa'ad da ake fama da yunwa a ƙasar. Sa'ad da ƙungiyar annabawa ke zaune a gabansa, sai ya ce wa baransa, “Dora babbar tukunya, ka dafa wa annabawan nan fate-fate.” 39 Ɗaya daga cikinsu ya tafi saura don ya samo ganyayen ci. Sai ya ga yaɗon inabin jeji, ya ɗebo 'ya'yan ya rungumo cike da hannu, ya zo ya yanyanka ya zuba a tukunyar abinci, ba tare da sanin ko mene ne ba. 40 Amma da suka ɗanɗana, sai suka ta da murya suka ce, “Ya mutumin Allah, akwai dafi a cikin tukunyar nan!” Ba su iya cin abincin ba. 41 Sai Elisha ya ce, “To, ku kawo gari.” Aka kawo masa, ya kuwa zuba garin a tukunyar, sa'an nan ya ce, “Ku kwaso wa mutanen. Yanzu dai kome lafiya.” 42 Wani mutum ya zo daga Ba'alshalisha ya kawo wa annabi Elisha abinci na 'ya'yan fari, da dunƙule ashirin na sha'ir, da ɗanyun zangarkun hatsi. Sai Elisha ya ce wa baransa, ya ba ƙungiyar annabawa su ci, 43 amma baran ya ce, “Ƙaka zan raba wa mutum ɗari wannan abinci?” Elisha ya sāke cewa, “Ka ba mutane su ci, gama Ubangiji ya ce za su ci har su bar saura.” 44 Sai ya ajiye shi a gabansu. Suka ci, suka kuwa bar saura kamar yadda Ubangiji ya faɗa.

2 Sarakuna 5

Na'aman ya Warke daga Kuturta

1 Na'aman kuwa, shugaban sojojin Sarkin Suriya, shi babba ne mai farin jini ƙwarai a wurin ubangidansa, dominta wurinsa ne Ubangiji ya ba Suriyawa nasara. Shi mutum ne ƙaƙƙarfan jarumi, amma kuma kuturu ne. 2 Daga cikin hare-haren da Suriyawa suke kaiwa, sai suka kama wata yarinya daga ƙasar Isra'ila, aka sa ta zama mai yi wa matar Na'aman aiki. 3 Wata rana sai ta ce wa uwargijyarta, “Da a ce ubangijina yana tare da annabin nan wanda yake Samariya, da ya warkar da shi daga kuturtarsa!” 4 Na'aman kuwa ya tafi, ya faɗa wa ubangidansa, ya ce, “Ka ji abin da yarinyan nan ta ƙasar Isra'ila ta ce?” 5 Sai Sarkin Suriya ya ce, “Ka tafi yanzu, zan aika wa Sarkin Isra'ila da takarda.” Na'aman kuwa ya ɗauki azurfa na talanti goma, zinariya kuma na shekel dubu shida (6,000 ), da rigunan ado guda goma, ya kama hanya. 6 Ya kai wa Sarkin Isra'ila tarkardar, wadda ta ce, “Sa'ad da wannan takarda ta sadu da kai, ka sani fa, ni ne na aiko barana, Na'aman, wurinka domin ka warkar da shi daga kuturtarsa.” 7 Da Sarkin Isra'ila ya karanta takardar, sai ya keta tufafinsa, ya ce, “Ni Allah ne, da zan kashe in rayar, har mutumin nan zai aiko mini da cewa in warkar da mutum daga kuturtarsa? Ku duba fa, ku ga yadda yake nemana da faɗa.” 8 Amma sa'ad da Elisha, annabin Allah, ya ji cewa Sarkin Isra'ila ya keta tufafinsa, sai ya aika wa sarki ya ce, “Me ya sa ka keta tufafinka? Bari ya zo wurina, zai sani akwai annabi a Isra'ila.” 9 Na'aman kuwa da dawakansa da karusansa suka tafi suka tsaya a ƙofar gidan Elisha. 10 Sai Elisha ya aiki manzo ya faɗa wa Na'aman ya tafi, ya yi wanka a Kogin Urdun har sau bakwai, naman jikinsa zai warke, zai tsarkaka. 11 Amma Na'aman ya husata, ya yi tafiyarsa, yana cewa, “Na yi tsammani zai fito ya zo wurina ne, ya tsaya, ya yi kira sunan Ubangiji Allahnsa ya kaɗa hannunsa a wurin kuturtar, ya warkar da ni. 12 Ashe, kogin Abana da na Farfar, wato kogunan Dimashƙu, ba su fi dukan ruwayen Isra'ila ba? Da ban yi wanka a cikinsu na tsarkaka ba?” Ya juya, ya yi tafiyarsa da fushi. 13 Amma barorinsa suka je wurinsa, suka ce masa, “Ranka ya daɗe, da a ce annabin ya umarce ka ka yi wani babban abu ne, ashe, da ba ka yi ba, balle wannan, da ya ce ka tafi ka yi wanka, ka tsarkaka?” 14 Sai ya tafi ya yi wanka har sau bakwai a Kogin Urdun bisa ga maganar annabin Allah, sai naman jikinsa ya warke ya zama kamar na ƙaramin yaro, ya tsarkaka. 15 Ya kuwa komo wurin annabi Elisha shi da jama'arsa duka, ya zo ya tsaya a gabansa, ya ce, “Yanzu na sani a duniya duka ba wani Allah banda na Isra'ila, saboda haka, sai ka karɓi kyauta daga wurina.” 16 Amma Elisha ya ce, “Na rantse da Ubangiji, wanda nake bauta masa, ba zan karɓi kome ba.” Ya yi ta roƙonsa ya karɓa, amma ya ƙi. 17 Na'aman kuwa ya ce, “Da yake ka ƙi ka karɓa, ina roƙonka, ka ba baranka labtun alfadari biyu na ƙasa, gama nan gaba baranka ba zai ƙara miƙa hadaya ta ƙonawa ko baiko ga wani gunki ba, sai dai Ubangiji. 18 Sai dai Ubangiji ya gafarta mini lokacin da na bi sarki zuwa cikin haikalin Rimmon, gunkin Suriya, don ya yi sujada. Na gaskata Ubangiji zai gafarta mini.” 19 Elisha kuwa ya ce masa, “Ka sauka lafiya.” Na'aman ya tafi. Amma tun Na'aman bai yi nisa ba, 20 sai Gehazi, baran annabi Elisha, ya ce, “Duba, maigidana ya bar Na'aman Basuriyen nan ya tafi, bai karɓi kome daga cikin abin da ya kawo masa ba. Na rantse da Ubangiji, zan sheƙa a guje, in bi shi, in karɓi wani abu daga gare shi.” 21 Gehazi kuwa ya bi bayan Na'aman. Da Na'aman ya ga wani yana biye da shi a guje, sai ya sauka daga karusarsa, ya juya ya tarye shi, ya ce, “In ce ko lafiya?” 22 Gehazi ya ce, “Lafiya ƙalau, maigidana ne ya aiko ni in faɗa maka, yanzu yanzu waɗansu samari biyu daga ƙungiyar annabawa suka zo wurinsa daga ƙasar tudu ta Ifraimu, yana roƙonka, ka ba ni talanti ɗaya na azurfa da rigunan ado guda biyu in kai masa.” 23 Na'aman kuwa ya ce, “In ka yarda ka karɓi talanti biyu na azurfa.” Ya ƙirga su ya ɗaure kashi biyu, da kuma rigunan ado masu kyau ya ɗora wa barorinsa biyu, ya umarce su su kai wa Gehazi har gida. 24 Sa'ad da Gehazi ya kai tudu, sai ya karɓi kayan daga hannunsu, ya ajiye a gida, sa'an nan ya sallame su, suka tafi. 25 Sai ya shiga, ya tsaya a gaban Elisha, Elisha kuwa ya tambaye shi, “Ina ka tafi, Gehazi?” Sai ya ce, “Ranka ya daɗe ban tafi ko'ina ba.” 26 Amma Elisha ya ce masa, “Ashe, ba ina tare da kai a ruhu ba, sa'ad da mutumin ya juyo daga karusarsa don ya tarye ka? Wannan shi ne lokacin karɓar kuɗi, da riguna, da gonaki na zaitun, da na inabi, da tumaki, da shanu, da barori mata da maza? 27 Saboda haka kuturtar Na'aman za ta kama ka, kai da zuriyarka har abada.” Haka kuwa ya fita a wurinsa kuturu, fari fat kamar auduga.

2 Sarakuna 6

An Tsamo Ruwan Gatari

1 Ƙungiyar annabawa da ke a hannun Elisha suka kawo masa kuka, suka ce, “Ga shi, wurin da muke zaune ya yi mana kaɗan. 2 Ka ba mu izini mu tafi Kogin Urdun, domin mu saro gumagumai a can, mu ƙara wa kanmu wurin zama.” Sai ya ce, “Ku tafi.” 3 Ɗaya daga cikinsu kuwa ya ce, “In ka yarda, ka tafi tare da mu.” Elisha kuwa ya yarda, ya ce, “To, mu tafi.” 4 Ya kuwa tafi tare da su. Sa'ad da suka isa Urdun, suka sassari itatuwa. 5 Amma sa'ad da ɗaya daga cikinsu yake saran wani gungume, sai ruwan gatarinsa ya kwaɓe ya fāɗa a ruwa. Sai ya yi ihu, ya ce, “Wayyo, maigida, me zan yi? Abin aro ne.” 6 Sa'an nan Elisha ya ce, “Daidai ina ya fāɗa?” Da ya nuna masa wurin, sai ya karyi tsumagiya, ya jefa a wurin, ya sa ruwan gatarin ya taso bisa kan ruwan. 7 Sa'an nan ya ce, “Ɗauko.” Sai mutumin ya miƙa hannu, ya ɗauka.

Elisha da Suriyawa

8 Wata rana, sa'ad da Sarkin Suriya yake yaƙi da Isra'ila, sai ya shawarci fādawansa, suka zaɓi wurin da za su kafa sansani. 9 Amma Elisha ya aika wa Sarkin Isra'ila, ya ce, “Ka yi hankali, kada ka wuce wuri kaza, gama Suriyawa suna gangarawa zuwa can.” 10 Sarkin Isra'ila kuwa ya aika zuwa wurin da Elisha ya faɗa masa. Da haka ya riƙa faɗakar da shi, har ya ceci kansa ba sau ɗaya, ba sau biyu ba. 11 Zuciyar Sarkin Suriya kuwa ta ɓaci ƙwarai a kan wannan al'amari, don haka ya kirawo fādawansa, ya ce musu, “Wane ne wannan da yake cikinmu, yana goyon bayan Sarkin Isra'ila?” 12 Ɗaya daga cikin fādawan ya ce, “A'a, ranka ya daɗe, sarki, ai, annabi Elisha ne wanda yake cikin Isra'ila, yake faɗa wa Sarkin Isra'ila maganar da kake faɗa a ɗakin kwananka.” 13 Sai ya ce, “Ku tafi, ku ga inda yake don in aika a kamo shi.” Aka faɗa masa, cewa a Dotan yake. 14 Sai ya aika da dawakai, da karusai, da sojoji da yawa. Suka tafi da dare suka kewaye garin. 15 Da baran annabi Elisha ya tashi da sassafe, ya fita waje, sai ga sojoji, da dawakai, da karusai sun kewaye gari. Sai baran ya ce, “Wayyo, maigidana! Me za mu yi?” 16 Elisha kuwa ya ce masa, “Kada ka ji tsoro gama waɗanda suke tare da mu, sun fi waɗanda suke tare da su yawa.” 17 Sa'an nan Elisha ya yi addu'a ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanunsa ya gani.” Ubangiji kuwa ya buɗe idanun saurayin, sai ga dutsen cike da dawakai da karusan wuta kewaye da Elisha. 18 Da Suriyawa suka gangaro wurinsa, sai Elisha ya yi addu'a ga Ubangiji, ya ce, “Ina roƙonka, ka bugi mutanen nan da makanta.” Ubangiji kuwa ya buge su da makanta bisa ga addu'ar Elisha. 19 Sa'an nan Elisha ya ce musu, “Wannan ba ita ce hanyar ba, ba kuma gari ke nan ba, ku bi ni, ni kuwa in kai ku wurin mutumin da kuke nema.” Sai ya kai su Samariya. 20 Da shigarsu Samariya, sai Elisha, ya ce, “Ya Ubangiji, ka buɗe idanun mutanen nan su gani.” Ubangiji kuwa ya buɗe idanunsu, suka gani, ashe, suna tsakiyar Samariya ne. 21 Da Sarkin Isra'ila ya gan su, sai ya ce wa Elisha, “Ya mai girma, in karkashe su? In karkashe su?” 22 Amma Elisha ya ce, “Ba za ka karkashe su ba. Ba za ka karkashe waɗanda ba kai ka kama su ta wurin takobinka ko bakanka ba. Ka ba su abinci da ruwa su ci su sha, su koma wurin shugabansu.” 23 Sai ya shirya musu babbar liyafa. Sa'ad da suka ci suka sha, sai ya sallame su, suka koma wurin shugabansu. Suriyawa kuwa ba su ƙara dai wa ƙasar Isra'ila hari ba.

Elisha da Yaƙi a Samariya

24 Bayan wannan kuwa Ben-hadad, Sarkin Suriya, ya tattara sojojinsa duka, ya haura ya kewaye Samariya da yaƙi. 25 Aka yi yunwa mai tsanani a Samariya a lokacin da aka kewaye ta da yaƙin, har aka riƙa sayar da kan jaki a bakin shekel tamanin, an kuma sayar da rubu'in mudu na kashin kurciya a bakin shekel biyar. 26 Sa'ad da Sarkin Isra'ila yake wucewa ta kan garun birni, sai wata mace ta yi masa kuka, ta ce, “Ka yi taimako, ran sarki ya daɗe.” 27 Shi kuwa ya ce, “Idan Ubangiji bai taimake ki ba, ƙaƙa zan yi, ni in taimake ki? Ina da alkama ne ko kuwa ina da ruwan inabi? 28 Me yake damunki?” Sai ta amsa, ta ce, “Wannan mace ta ce mini, in kawo ɗana mu ci yau, gobe kuma mu ci nata. 29 Sai muka dafa ɗana muka cinye. Kashegari kuwa na ce mata ta kawo ɗanta mu ci, amma sai ta ɓoye shi.” 30 Da sarki ya ji maganar macen, sai ya keta tufafinsa, sa'ad da yake wucewa ta kan garun birni. Sai mutane suka gani, ashe, yana saye da rigar makoki a ciki. 31 Ya ce, “Allah ya yi mini hukunci mai tsanani, idan ban fille kan Elisha ɗan Shafat yau ba.” 32 Elisha kuwa yana zaune a gidansa, dattawa kuma suna zaune tare da shi. Sai sarki ya aiki mutum, amma kafin mutumin ya isa, sai Elisha ya ce wa dattawan, “Kun ga yadda mai kisankan nan ya aiko don a fille mini kai? Idan mutumin ya zo, sai ku rufe ƙofar, ku riƙe ta da ƙarfi. Ba da jimawa ba sarki zai bi bayansa.” 33 Yana magana da su ke nan, sai sarki ya iso, ya ce, “Wannan masifa daga wurin Ubangiji ta fito, don me zan ƙara jiran Ubangiji kuma?”

2 Sarakuna 7

1 Amma Elisha ya ce, “Kasa kunne ga abin da Ubangiji ya ce! Gobe war haka za a sayar da mudu na lallausan gari a bakin shekel guda, da mudu biyu na sha'ir a bakin shekel guda a ƙofar garin Samariya.” 2 Amma dogarin da yake tare da sarki ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu ba zai yiwu ba.” Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka, zai faru, amma ba za ka ci ba.”

Sojan Suriyawa sun Tafi

3 Akwai mutum huɗu, kutare, waɗanda suke zaune a bakin ƙofar gari, sai suka ce wa junansu, “Me ya sa muke zaune nan har mu mutu? 4 Idan mun ce, ‘Bari mu shiga birni,’ yunwa tana birnin, za mu mutu a wurin. Idan kuma mun zauna a nan za mu mutu. Saboda haka bari mu tafi sansanin Suriyawa, idan sun bar mu da rai, za mu rayu, idan kuwa sun kashe mu, za mu mutu.” 5 Sai suka tashi da magariba, suka tafi sansanin Suriyawa. Da suka isa gefen sansanin Suriyawa, sai suka tarar ba kowa a wurin, 6 gama Ubangiji ya sa sojojin Suriyawa suka ji amon karusai, da na dawakai, da na babbar rundunar soja. Sai suka ce wa junansu, “Ai, Sarkin Isra'ila, ya yi ijara da sarakunan Hittiyawa, da na Masarawa, su zo su fāɗa mana.” 7 Saboda haka suka gudu da almuru, suka bar alfarwansu, da dawakansu, da jakunansu, suka bar sansanin yadda yake, suka tsira da rayukansu. 8 Sa'ad da kutaren nan suka zo sansanin, sai suka shiga wata alfarwa, suka ci suka sha. Suka kwashe azurfa, da zinariya, da tufafi, suka tafi suka ɓoye. Suka koma suka shiga wata alfarwa kuma, suka kwashe abubuwan da suke cikinta. Suka tafi suka ɓoye su. 9 Sa'an nan suka ce wa junansu, “Ba mu kyauta ba. Yau ranar albishir ce, idan mun yi shiru, mun jira har safe, wani mugun abu zai same mu. Domin haka bari mu tafi mu faɗa a gidan sarki.” 10 Sai suka tafi wurin masu gadin ƙofar birnin, suka ce musu, “Mun tafi sansanin Suriyawa ba mu ga kowa ba, ba mu kuma ji motsin kowa a wurin ba, ba kowa a wurin sai dawakai da jakai, a ɗaure, alfarwai kuma suna nan yadda suke.” 11 Sa'an nan masu tsaron ƙofar birnin suka aika a faɗa a gidan sarki. 12 Sai sarki ya tashi da dare ya ce wa fādawansa, “Bari in faɗa muku irin shirin da Suriyawa suka yi a kanmu. Sun sani muna fama da yunwa, domin haka suka fita daga sansanin suka ɓuya a karkara, suna nufin sa'ad da muka fita daga birnin, sai su kama mu da rai, sa'an nan su shiga birnin.” 13 Ɗaya daga cikin fādawan sarki ya ce, “A sa waɗansu mutane su ɗauki dawakai biyar da suka ragu cikin birnin, idan ba su tsira ba, za su zama kamar sauran Isra'ilawan da suka riga suka mutu. Bari mu aika, mu gani.” 14 Aka ɗibi mahayan dawakai biyu, sarki kuwa ya aike su, su bi bayan sojojin Suriyawa, ya ce musu, “Ku tafi, ku gani.” 15 Sai suka bi bayansu har zuwa Kogin Urdun, suka ga tufafi da makamai barjat ko'ina a hanya, waɗanda Suriyawa suka zubar lokacin da suke gudu. Sai manzannin suka komo suka faɗa wa sarki. 16 Sa'an nan mutane suka fita, suka washe sansanin Suriyawa. Aka kuwa sayar da mudu na lallausan gari da mudu biyu na sha'ir a bakin shekel ɗaya ɗaya kamar dai yadda Ubangiji ya faɗa. 17 Sarki kuwa ya sa dogari wanda ya raka shi wajen Elisha ya tsare ƙofar birnin. Sai mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu, kamar yadda annabi Elisha ya faɗa sa'ad da sarki ya tafi wurinsa. 18 Ya faru daidai yadda annabi Elisha ya ce wa sarki, “Za a sayar da mudu biyu na sha'ir, da mudu na lallausan gari a bakin shekel ɗaya ɗaya gobe war haka a ƙofar birnin Samariya.” 19 Dogarin ya ce wa Elisha, “Ko da Ubangiji da kansa zai buɗe tagogin sama, wannan abu zai yiwu ke nan?” Elisha kuwa ya ce, “Za ka gani da idanunka amma ba za ka ci ba.” 20 Haka kuwa ya zama gama mutane suka tattake shi a ƙofar har ya mutu.

2 Sarakuna 8

An Mayar da Gonakin Mata daga Shunem

1 Elisha kuwa ya ce wa matar da ya ta da ɗanta daga matattu, “Ki tashi, ke da gidanki, ki zauna duk inda kika samu, gama Ubangiji ya sa a yi yunwa a ƙasar har shekara bakwai.” 2 Sai matar ta tashi, ta yi kamar yadda annabi Elisha ya faɗa mata. Ta tafi, ita da iyalinta suka zauna a ƙasar Filistiyawa har shekara bakwai. 3 A ƙarshen shekara bakwai ɗin, matar ta komo daga ƙasar Filistiyawa, ta tafi wurin sarki, ta roƙe shi a mayar mata da gidanta da gonarta. 4 A lokacin kuwa sarki yana tare da Gehazi, wato baran annabi Elisha, ya ce, “Ka faɗa mini dukan mu'ujizan da Elisha ya yi.” 5 A sa'ad da yake faɗa wa sarki yadda Elisha ya ta da matacce, sai ga matar da ya ta da ɗanta daga matattu, ta zo ta roƙi sarki ya mayar mata da gidanta da gonarta. Sai Gehazi ya ce, “Ran sarki ya daɗe, ai, ga matar, ga kuma yaronta wanda Elisha ya tashe shi daga matattu.” 6 Da sarki ya tambayi matar sai ta faɗa masa dukan labarin. Sarki kuwa ya sa wani bafade ya mayar mata da dukan abin da yake nata da dukan amfanin gonakin, tun daga ran da ta bar ƙasar har ranar da ta komo.

Hazayel ya Ci Sarautar Suriya

7 Elisha kuwa ya tafi Dimashƙu. A lokacin kuwa Ben-hadad, Sarkin Suriya, yana ciwo. Aka faɗa masa cewa, annabi Elisha ya zo, yana nan, 8 sai sarki ya ce wa Hazayel, ɗaya daga cikin fādawansa, “Ka ɗauki kyauta, ka tafi wurin annabin Allah ka sa ya roƙar mini Ubangiji ko zan warke daga wannan cuta.” 9 Hazayel kuwa ya tafi wurin Elisha tare da kyauta iri iri na kayan Dimashƙu. Raƙuma arba'in ne suka ɗauko kayan. Da ya tafi ya tsaya a gabansa, ya ce, “Danka, Ben-hadad Sarkin Suriyawa, ya aiko ni wurinka don yana so ya ji ko zai warke daga wannan cuta.” 10 Elisha kuwa ya ce masa, “Tafi ka faɗa masa zai warke, amma Ubangiji ya nuna mini lalle zai mutu.” 11 Sai Elisha ya kafa wa Hazayel ido, yana kallonsa, har Hazayel ya ji kunya. Elisha kuwa ya fashe da kuka. 12 Hazayel ya ce, “Me ya sa shugabana yake kuka?” Elisha ya amsa ya ce, “Domin na san irin muguntar da za ka yi wa jama'ar Isra'ila. Za ka ƙone kagaransu da wuta, ka karkashe samarinsu da takobi, za ka kuma fyaffyaɗe ƙananansu a ƙasa, ka tsattsage matansu masu ciki.” 13 Hazayel kuwa ya ce, “Ni wane ne? Ina na sami wannan iko? Ni ba kome ba ne.” Elisha ya amsa ya ce, “Ubangiji ya nuna mini za ka zama Sarkin Suriya.” 14 Sa'an nan Hazayel ya tashi daga wurin Elisha ya koma wurin Ben-hadad. Ben-hadad ya tambaye shi, “Me Elisha ya faɗa maka?” Sai ya ce, “Ya faɗa mini, cewa lalle za ka warke.” 15 Amma kashegari sai Hazayel ya ɗauki bargo, ya tsoma a ruwa, sa'an nan ya rufe fuskar sarki da shi har ya mutu. Sai ya hau gadon sarautarsa.

Sarki Yehoram na Yahuza

16 A shekara ta biyar ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra'ila, Yoram ɗan Yehoshafat Sarkin Yahuza, ya ci sarauta. 17 Yana da shekara talatin da biyu da haihuwa sa'ad da ya ci sarautar. Ya yi shekara takwas yana sarauta a Urushalima. 18 Ya bi halin sarakunan Isra'ila, kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama ya auri 'yar Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji. 19 Duk da haka Ubangiji bai hallaka Yahuza ba, saboda bawansa Dawuda, tun da yake ya alkawarta zai ba shi haske, shi da 'ya'yansa har abada. 20 A zamanin Yoram, Edomawa suka tayar wa Yahuza, suka naɗa wa kansu sarki. 21 Sa'an nan Yoram ya haye zuwa Zayar tare da dukan karusansa. Sai ya tashi da dare da shugabannin karusansa, ya bugi Edomawan da suka kewaye shi, amma sojojinsa suka gudu zuwa alfarwansu. 22 Haka kuwa Edom ta tayar wa Yahuza har wa yau. Alokacin kuma Libna ta tayar wa Yahuza. 23 Sauran ayyukan Yoram da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 24 Yoram kuwa ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Ahaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Ahaziya na Yahuza

25 A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Yehoram ɗan Ahab Sarkin Isra'ila, Ahaziya ɗan Yoram Sarkin Yahuza, ya ci sarauta. 26 Ya ci sarauta yana da shekara ashirin da biyu da haihuwa, ya kuwa yi mulki shekara guda a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ataliya jikanyar Omri, Sarkin Isra'ila. 27 Ya ɗauki halin gidan Ahab. Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda gidan ahab ya yi, gama shi surukin gidan Ahab ne. 28 Sarki Ahaziya kuwa ya tafi tare da Yehoram ɗan Ahab don su yi yaƙi da Hazayel, Sarkin Suriya, a Ramot cikin Gileyad. Suriyawa suka yi wa Yehoram rauni. 29 Sai sarki Yehoram ya koma zuwa Yezreyel don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa'ad da yake yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Ahaziya, ɗan Yoram, Sarkin Yahuza ya tafi ya ziyarci Yehoram ɗan Ahab cikin Yezreyel saboda yana ciwo.

2 Sarakuna 9

An naɗa Yehu Sarkin Isra'ila

1 Elisha kuwa ya kirawo ɗaya daga cikin annabawa matasa, ya ce masa, “Ka sha ɗamara, ka ɗauki wannan kurtun mai, ka tafi Ramot-gileyad. 2 Sa'ad da ka isa can, sai ka nemi Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ka shiga, ka sa ya tashi daga wurin abokansa, ka kai shi cikin ɗaki. 3 Sa'an nan ka ɗauki kurtun man, ka zuba masa a ka, ka ce, ‘Ubangiji ya ce ya keɓe ka Sarkin Isra'ila.’ Sa'an nan ka buɗe ƙofa, ka gudu, kada ka tsaya.” 4 Sai saurayin nan, annabin, ya tafi Ramot-gileyad. 5 Sa'ad da ya isa, sai ga shugabannin sojoji suna taro. Sai ya ce, “Ina da saƙo dominka, ya shugaba.” Yehu kuwa ya ce, “Wane ne a cikinmu?” Sai ya ce, “Kai ne, ya shugaba.” 6 Sai Yehu ya tashi ya shiga ɗaki, saurayin kuwa ya zuba masa mai a ka, ya ce, “Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya keɓe ka sarkin jama'arsa, wato Isra'ila. 7 Za ka hallaka gidan Ahab, maigidanka, domin in ɗau fansar jinin annabawa bayinsa, da fansar jinin sauran bayin Ubangiji a kan Yezebel. 8 Gama dukan gidan Ahab zai hallaka. Zan datse wa Ahab kowane ɗa namiji, bawa ko 'yantacce, cikin Isra'ila. 9 Zan mai da gidan Ahab kamar gidan Yeroboam ɗan Nebat, da kuma kamar gidan Ba'asha ɗan Ahija. 10 Karnuka za su cinye Yezebel a cikin Yezreyel, ba wanda zai binne ta.” Sa'an nan ya buɗe ƙofar, ya gudu. 11 Da Yehu ya fita zuwa wurin sauran shugabannin, sai suka tambaye shi, “Lafiya kuwa, me ya sa mahaukacin nan ya zo wurinka?” Sai ya ce musu, “Ai, kun san mutumin da irin maganarsa.” 12 Suka ce, “Ba mu sani ba, sai ka faɗa mana.” Shi kuwa ya ce, “Ya faɗa mini, cewa Ubangiji ya ce ya keɓe ni Sarkin Isra'ila.” 13 Sai kowane mutum a cikinsu ya yi maza ya tuɓe rigarsa, ya shimfiɗa a kan matakan, sa'an nan suka busa ƙaho, suna cewa, “Yehu ne sarki.”

Yehu ya Kashe Yehoram Sarkin Isra'ila

14 Ta haka Yehu, ɗan Yehoshafat, wato jikan Nimshi, ya tayar wa Yehoram. A lokacin, Yehoram tare da dukan Isra'ila suna tsaron Ramot-gileyad, don kada Hazayel, Sarkin Suriya, ya fāɗa mata. 15 Amma sarki Yehoram ya komo Yezreyel, don ya yi jiyyar raunukan da Suriyawa suka yi masa sa'ad da ya yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Yehu ya ce, “Idan wannan shi ne nufinku, to, kada kowa ya zurare, ya tafi, ya ba da labari a Yezreyel.” 16 Sa'an nan Yehu ya hau karusarsa ya tafi Yezreyel, gama a can ne Yehoram yake kwance. Ahaziya Sarkin Yahuza ya gangara don ya gai da Yehoram. 17 Mai tsaro kuwa yana tsaye a kan hasumiya a Yezreyel, sai ya hangi rundunar Yehu sa'ad da yake zuwa. Ya ce, “Na ga wata runduna.” Sai Yehoram ya ce, “Ka aiki wani, ya hau doki, ya tafi ya tarye su, ya tambaye su, ko lafiya.” 18 Sai wani mutum ya hau doki ya tafi ya tarye su, ya ce, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?” Sai Yehu ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.” Mai tsaro kuma ya ce, “Manzo ya kai wurinsu, amma bai komo ba.” 19 Ya kuma aiki wani, na biyu, a kan doki, ya je wurinsu ya ce musu, “Sarki ya ce, lafiya kuwa?” Yehu ya amsa, ya ce, “Ina ruwanka da lafiya? Kewaya ka bi bayana.” 20 Mai tsaro ya sāke cewa, “Ya kai wurinsu, amma bai komo ba. Ina ganin sukuwar kamar irin ta Yehu, jikan Nimshi, gama yakan yi sukuwa da hauka.” 21 Yehoram kuwa ya ce, “Ku shirya karusa.” Suka shirya masa karusa. Sa'an nan Yehoram Sarkin Isra'ila, da Ahaziya Sarkin Yahuza suka fita, kowa a cikin karusarsa, suka tafi su taryi Yehu. Suka sadu da shi a daidai gonar Nabot mutumin Yezreyel. 22 Da Yehoram ya ga Yehu, sai ya ce, “Lafiya dai?” Yehu ya ce, “Ina fa lafiya, tun da karuwanci da sihirin uwarka, Yezebel, sun yi yawa haka?” 23 Yehoram kuwa ya juyar da karusarsa baya, ya gudu, yana ce wa Ahaziya, “Maƙarƙashiya ce, ya Ahaziya!” 24 Sai Yehu ya ja bakansa da iyakar ƙarfinsa ya ɗirka wa Yehoram kibiya, ta sha zarar zuciyarsa, sai ya ɓingire cikin karusarsa. 25 Yehu ya ce wa Bidkar, “Ka ɗauke shi ka jefar a gonar Nabot mutumin Yezreyel, gama ka tuna sa'ad da ni da kai muke kan dawakai muna biye da Ahab, tsohonsa, yadda Ubangiji ya faɗi wannan magana a kansa cewa, 26 ‘Hakika, kamar yaddajiya na ga jinin Nabot da na 'ya'yansa, ni Ubangiji, zan sāka maka saboda wannan gona.’ Yanzu sai ka ɗauke shi, ka jefar da shi a wannan gona kamar yadda Ubangiji ya faɗa.”

Yehu ya Kashe Ahaziya

27 Da Ahaziya Sarkin Yahuza, ya ga haka, sai ya gudu ta hanyar Bet-haggan. Yehu kuwa ya bi shi, ya ce, “Shi ma a harbe shi.” Sai suka harbe shi a cikin karusarsa a hawan Gur, wanda yake kusa da Ibleyam. Sai ya gudu zuwa Magiddo, ya mutu a can. 28 Fādawansa suka ɗauke shi a cikin karusar zuwa Urushalima, suka binne shi a kabarinsa tare da kakanninsa a birnin Dawuda. 29 Ahaziya ya ci sarautar Yahuza a shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Yehoram ɗan Ahab.

Mutuwar Yezebel

30 Da Yezebel ta ji Yehu ya zo Yezreyel, sai ta shafa wa idanunta launi, ta gyara gashin kanta, sa'an nan ta leƙa ta taga. 31 Da Yehu ya shiga ƙofar garin, sai ta ce, “Kai Zimri, mai kashe maigidansa, me kake yi a nan?” 32 Sai ya ɗaga idanunsa wajen tagar, ya ce, “Wa yake wajena?” Sai babani biyu ko uku suka dube shi, 33 shi kuwa ya ce, “Ku wurgo ta ƙasa.” Sai suka wurgo ta ƙasa. Jininta ya fantsama a jikin bangon da jikin dawakan da suka tattake ta. 34 Sa'an nan Yehu ya shiga gida, ya ci ya sha, ya ce, “Ku san yadda za ku yi da wannan la'ananniyar mace, ku binne ta, gama ita 'yar sarki ce.” 35 Amma da suka tafi don su binne ta, ba su tarar da kome ba sai ƙwaƙwalwa, da ƙafafu, da tafin hannuwanta. 36 Sai suka komo, suka faɗa masa. Sai ya ce musu, “Wannan, ai, faɗar Ubangiji, wadda ya faɗa ta bakin bawansa Iliya Batishbe, ya ce, ‘Karnuka za su cinye naman Yezebel a cikin Yezreyel. 37 Gawar Yezebel za ta zama wa ƙasa taki a Yezreyel don kada wani ya iya cewa wannan ita ce Yezebel.’ ”

2 Sarakuna 10

An Kashe Zuriyar Ahab

1 Ahab yana da 'ya'ya maza saba'in a Samariya, sai Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika zuwa Samariya wurin shugabanni da dattawan birni, da masu lura da 'ya'yan Ahab. 2 Ya ce, “Yanzu dai, da zarar wasiƙun nan sun iso wurinku, da yake kuke lura da 'ya'yan Ahab, kuna kuma da karusai, da dawakai, da kagara, da makamai, 3 sai ku zaɓi wanda ya fi dacewa duka daga cikin 'ya'yan Ahab, ku naɗa shi sarki, ku yi yaƙi, domin ku tsare gidan Ahab.” 4 Amma suka ji tsoro ƙwarai, suka ce, “Ga shi, sarakuna biyu ba su iya karawa da shi ba, balle mu.” 5 Sai wakilin gidan, da wakilin birnin, da dattawa, da masu lura da 'ya'yan sarki, suka aika wurin Yehu suka ce, “Mu barorinka ne, duk abin da ka umarce mu, za mu yi. Ba za mu naɗa wani sarki ba, sai ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.” 6 Sa'an nan Yehu ya rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “Idan kuna goyon bayana, idan kuma kun shirya za ku yi mini biyayya, to, sai ku fille kawunan 'ya'yan Ahab, sa'an nan ku zo wurina a Yezreyel gobe war haka.” 'Ya'yan sarki, maza, su saba'in ne, suna a hannun manyan mutanen birni ne waɗanda suke lura da su. 7 Da wasiƙar ta iso wurinsu, sai suka kwashi 'ya'yan sarki guda saba'in, suka karkashe su. Suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezreyel. 8 Da aka faɗa masa cewa an kawo kawunan 'ya'yan sarki, sai ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar garin har safiya.” 9 Da safe, sa'ad da ya fita, ya tsaya, sai ya ce wa mutane duka, “Ba ku da laifi, ni ne na tayar wa maigidana har na kashe shi, amma wane ne ya kashe dukan waɗannan? 10 Ku sani fa ba maganar da Ubangiji ya faɗa a kan gidan Ahab da ba za ta cika ba, gama Ubangiji ya aikata abin da ya faɗa ta bakin bawansa Iliya.” 11 Haka kuwa Yehu ya karkashe waɗanda suka ragu na gidan Ahab a Yezreyel, wato dukan manyan mutanensa, da abokansa, da firistocinsa. Bai rage masa ko guda ba.

An Kashe Dangin Ahaziya

12 Yehu kuma ya fita zai tafi Samariya. A hanya, sa'ad da yake a Bet-eked ta makiyaya, 13 sai ya sadu da 'yan'uwan Ahaziya Sarkin Yahuza, sai ya ce, “Ku su wane ne?” Sai suka amsa, “Mu 'yan'uwan Ahaziya ne, mun zo mu gai da 'ya'yan sarki ne da 'ya'yan sarauniya.” 14 Yehu kuwa ya ce, “Ku kama su da rai.” Sai suka kama su da rai, suka karkashe su a ramin Bet-eked, su arba'in da biyu ne, ba a rage ko ɗaya a cikinsu ba.

An Kashe dukan sauran Dangin Ahab

15 Da ya tashi daga can, sai ya sadu da Yehonadab ɗan Rekab yana zuwa ya tarye shi. Yehu ya gaishe shi, ya tambaye shi, “Zuciyarka ta amince da ni kamar yadda tawa ta amince da kai?” Yehonadab ya amsa, “I.” Sai Yehu ya ce, “Idan haka ne, to, miƙo mini hannunka.” Sai ya miƙa masa hannunsa. Yehu kuwa ya ɗauke shi zuwa cikin karusa. 16 Ya ce, “Ka zo tare da ni, ka ga kishin da nake da shi domin Ubangiji.” Sai suka tafi cikin karusarsa. 17 Da suka isa Samariya, sai ya kashe duk wanda ya ragu na gidan Ahab a Samariya. Ya share mutanen gidan Ahab kaf kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin annabi Iliya.

An Kashe Masu Sujada ga Ba'al

18 Yehu kuwa ya tara mutane duka, ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba'al kaɗan, amma Yehu zai bauta masa da yawa. 19 Saboda haka, yanzu sai ku kirawo mini dukan annabawan Ba'al, da dukan masu yi masa sujada, da dukan firistocinsa. Kada a manta da wani, gama ina da babbar hadayar da zan miƙa wa Ba'al. Duk wanda bai zo ba, za a kashe shi.” Amma dabara ce Yehu yake yi don ya hallaka waɗanda suke yi wa Ba'al sujada. 20 Yehu kuma ya sa a yi muhimmin taro saboda Ba'al. Aka kuwa kira taron, 21 sai ya aika cikin Isra'ila duka, dukan masu yi wa Ba'al sujada kuwa suka zo, ba wanda bai zo ba. Suka shiga, suka cika haikalin Ba'al makil daga wannan gefe zuwa wancan. 22 Sa'an nan Yehu ya ce wa wanda yake lura da ɗakin tufafi, “Ku fito da tufafi na dukan waɗanda suke yi wa Ba'al sujada.” Shi kuwa ya fito musu da tufafin. 23 Bayan wannan Yehu ya shiga haikalin Ba'al tare da Yehonadab ɗan Rekab, ya ce wa masu yi wa Ba'al sujada, “Ku bincike, ku tabbata, ba wani bawan Ubangiji tare da ku, sai dai masu yi wa Ba'al sujada kaɗai.” 24 Sa'an nan Yehu da Yehonadab suka shiga don su miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Yehu ya riga ya sa mutum tamanin a waje, ya ce musu, “Mutumin da ya bar wani daga cikin waɗanda na bashe su a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.” 25 Nan da nan da Yehu ya gama miƙa hadaya ta ƙonawa, sai ya ce wa mai tsaro da shugabannin, “Ku shiga, ku karkashe su, kada ku bar wani ya tsere.” Da suka karkashe su, sai suka fitar da su waje, sa'an nan suka shiga can cikin haikalin Ba'al. 26 Suka fitar da gumakan da suke cikin haikalin Ba'al, suka ƙone su. 27 Suka yi kaca kaca da gunkin Ba'al da haikalinsa, suka mai da haikalin ya zama salga har wa yau. 28 Yehu ya kawar da Ba'al daga cikin Isra'ila. 29 Amma bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa Isra'ila su yi zunubi. Siffofin maruƙa biyu suna nan a Betel da Dan. 30 Ubangiji kuwa ya ce wa Yehu, “Da yake ka yi abin da yake daidai a gare ni, ka yi wa gidan ahab bisa ga dukan abin da yake a zuciyata, 'ya'yanka, har tsara ta huɗu, za su ci sarautar Isra'ila.” 31 Amma Yehu bai mai da hankali ya yi tafiya a tafarkin Ubangiji Allah na Isra'ila da zuciya ɗaya ba. Bai rabu da zunuban Yerobowam ba, wanda ya sa Isra'ila su yi zunubi.

Mutuwar Yehu

32 A kwanakin an Ubangiji ya soma rage ƙasar Isra'ila. Hazayel kuwa ya yaƙe su a karkarar Isra'ila, 33 tun daga Urdun har zuwa wajen gabas, da dukan ƙasar Gileyad, da ta Gad, da ta Ra'ubainu, da ta Manassa, tun daga Arower wadda take kusa da kwarin Arnon haɗe da Gileyad da Bashan. 34 Sauran ayyukan Yehu da dukan abin da ya yi, da dukan ƙarfinsa an rubuta su a littafin tarihin sarakuna Isra'ila. 35 Yehu kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Yehowahaz ɗansa ya gaji sarautarsa. 36 Yehu ya yi mulkin Isra'ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

2 Sarakuna 11

Sarauniya Ataliya ta Yahuza

1 Sa'ad da Ataliya, uwar Ahaziya, ta ga ɗanta ya rasu, sai ta tashi ta hallaka dukan 'ya'yan sarauta. 2 Amma Yehosheba 'yar sarki Yoram, 'yar'uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin 'ya'yan sarki waɗanda aka kashe, ta ɓoye shi da mai renonsa, an yi ta renonsa cikin ɗaki. Da haka ta tserar da shi daga Ataliya, har ba a kashe shi ba. 3 Ya zauna tare da ita shekara shida a ɓoye, a cikin Haikalin Ubangiji sa'ad da Ataliya take mulkin ƙasar.

Yehoyada ya Tayar

4 A shekara ta bakwai sai Yehoyada ya aika ya kawo shugabannin Keretiyawa da na masu tsaro a Haikalin Ubangiji. Ya yi alkawari da su, ya sa suka yi rantsuwa a Haikalin Ubangiji, sa'an nan ya nuna musu ɗan sarki. 5 Ya kuma umarce su cewa, “Abin da za ku yi ke nan, sai sulusinku da sukan zo aiki a ranar Asabar, su yi tsaron gidan sarki. 6 Sulusinku kuma zai kasance a ƙofar Sur. Ɗaya sulusin kuma zai kasance a bayan masu tsaro, haka za ku yi tsaron gidan, ku tsare shi. 7 Ƙungiyarku biyu kuma waɗanda sukan tashi aiki ran Asabar, za su yi tsaron Haikalin Ubangiji da kuma sarki. 8 Za ku kewaye sarki, kowane mutum ya riƙe makaminsa. Duk wanda ya yi ƙoƙari ya zo kusa, sai a kashe shi. Sai ku kasance tare da sarki duk lokacin da zai fita da duk lokacin da zai shiga.” 9 Shugabannin fa suka aikata bisa ga dukan abin da Yehoyada firist ya umarta. Kowa ya zo duk da mutanensa waɗanda za su huta aiki ran Asabar tare da waɗanda za su yi aiki ran Asabar, suka zo wurin Yehoyada. 10 Firist kuwa ya ba shugabannin māsu da garkuwoyin Dawuda waɗanda suke cikin Haikalin Ubangiji. 11 Matsara suka tsaya, kowa da makaminsa a hannu, daga wajen kudu na Haikalin zuwa wajen arewa. Suka kewaye bagade da Haikali. 12 Sa'an nan ya fito da ɗan sarki, ya sa kambin sarauta a kansa, ya kurma ba shi dokokin. Suka naɗa shi, suka zuba masa man naɗawa, sa'an nan suka yi tāfi suna cewa, “Ran sarki ya daɗe.” 13 Da Ataliya ta ji muryoyin matsara da na jama'a, sai ta zo wurin mutane a Haikalin Ubangiji. 14 Da ta duba, sai ta ga sarki a tsaye kusa da ginshiƙi bisa ga al'ada, shugabanni da masu busa kuwa suna tsaye kusa da sarki. Dukan mutanen ƙasar suna ta murna suna ta busa ƙaho. Sai Ataliya ta kece tufafinta, ta yi ihu, tana cewa, “Tawaye, tawaye!” 15 Yehoyada, firist kuwa, ya umarci shugabannin sojoji, ya ce, “Ku fitar da ita daga nan, duk kuma wanda yake son kāre ta, ku sa takobi ku kashe shi.” Ya kuma ce, “Kada a kashe ta a Haikalin Ubangiji.” 16 Suka kama ta, suka fitar da ita ta ƙofar dawakai zuwa gidan sarki, can suka kashe ta.

Gyare-gyaren Yehoyada

17 Yehoyada kuwa ya yi alkawari tsakanin Ubangiji, da sarki, da jama'a, yadda za su zama jama'ar Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da jama'a. 18 Sai dukan jama'ar ƙasa suka tafi haikalin Ba'al suka farfashe shi, da bagadensa da siffofinsa. Suka kuma kashe Mattan firist na Ba'al a gaban bagaden. Yehoyada kuwa ya sa matsara su yi tsaron Haikalin Ubangiji, 19 ya kuma sa shugabanni, da Keretiyawa, da matsara, da dukan jama'ar ƙasar, su fito da sarki daga Haikalin Ubangiji, suka rufa masa baya ta ƙofar matsara zuwa gidan sarki. Suka sa shi a gadon sarautar sarakuna. 20 Dukan jama'ar ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya huta bayan da an kashe Ataliya a gidan sarki.

Sarki Yowash na Yahuza

21 Yowash yana da shekara bakwai sa'ad da ya ci sarauta.

2 Sarakuna 12

1 A shekara ta bakwai ta sarautar Yehu, Yowash ya ci sarautar. Ya yi shekara arba'in yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Zibiya ta Biyer-sheba. 2 Yowash kuwa ya yi abin da yake daidai ga Ubangiji dukan kwanakinsa, domin Yehoyaka, firist, ya koya masa. 3 Duk da haka ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba, mutane suka ci gaba da miƙa hadayu da ƙona turare a kan tuddan. 4 Yowash ya ce wa firistoci, “Dukan kuɗin tsarkakan abubuwa da ake kawowa a Haikalin ubangiji, da kuɗin da aka tsara wa kowane mutum, da kuɗin da aka bayar da yardar rai, da ake kawowa a Haikali, 5 sai ku karɓa daga junanku, don a gyara duk inda ake bukatar gyara a Haikalin.” 6 Amma har a shekara ta ashirin da uku ta sarautar sarki Yowash, firistocin ba su yi wani gyara a Haikalin ba. 7 Saboda haka Yowash ya kirawo Yehoyada, firist, da sauran firistoci, ya ce musu, “Me ya sa ba ku gyara Haikalin? Daga yanzu kada ku karɓi kuɗi daga wurin abokanku, sai in za ku ba da shi domin gyaran Haikalin.” 8 Firistocin kuwa suka yarda, ba za su karɓi kuɗi daga wurin jama'a ba, ba su kuwa gyara Haikalin ba. 9 Sa'an nan Yehoyada, firist, ya ɗauki akwati, ya huda rami a murfin, sa'an nan ya ajiye shi kusa da bagade a sashin dama na shiga Haikalin Ubangiji. Firistocin da suke tsaron ƙofar suka saka dukan kuɗin da aka kawo a Haikalin Ubangiji. 10 Sa'ad da suka gani akwai kuɗi da yawa a cikin akwatin, sai magatakardan sarki, da babban firist suka zo, suka ƙirga kuɗin da suke a Haikalin Ubangiji suka ƙunsa shi a babbar jaka. 11 Sa'an nan suka ba da kuɗin da aka ƙirga a hannun waɗanda suke lura da aikin Haikalin Ubangiji, domin su biya masassaƙan katakai, da masu haɗawa da suke aikin Haikalin Ubangiji, 12 da masu gini, da masu sassaƙa duwatsu, a kuma sayi katako da sassaƙaƙƙun duwatsu don gyaran Haikalin Ubangiji, da kowane irin abu da ake bukata domin gyaran Haikalin. 13 Amma ba a mori kuɗin da aka kawo a Haikalin Ubangiji domin yin kwanonin azurfa, da abin katse fitila, da tasoshi, da ƙahoni, da kwanonin zinariya ko na azurfa ba. 14 Gama an ba da kuɗin ga ma'aikatan da suke gyaran Haikalin ubangiji. 15 Ba a nemi lissafin kuɗin a wurin mutanen da aka ba su kuɗin don su biya ma'aikatan ba, gama su amintattu ne. 16 Ba a kawo kuɗi na hadaya don laifi da hadaya don zunubi a cikin Haikalin Ubangiji ba, ya zama na firistoci. 17 Hazayel Sarkin Suriya kuwa ya tafi ya yi yaƙi da Gat har ya cinye ta, ya kuma shirya zai yi yaƙi da Urushalima. 18 Sai Yowash Sarkin Yahuza ya kwashe dukan kyautai na yardar rai waɗanda Yehoshafat, da Yoram, da Ahaziya, kakanninsa, sarakunan Yahuza suka keɓe, ya kuma kwashe kyauta ta yardar rai ta kansa, da dukan zinariya da aka samu a baitulmalin Haikalin Ubangiji da baitulmalin gidan sarki, ya aika wa Hazayel, Sarkin Suriya. Sa'an nan Hazayel ya tashi ya bar Urushalima. 19 Sauran ayyukan Yowash da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 20 Fādawansa suka ƙulla maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidan da yake Millo, a kan hanyar da ta nufi Silla. 21 Yozakar ɗan Shimeyat, da Yehozabad ɗan Shemer su ne fādawansa da suka kashe shi. Aka binne shi a makabartar kakanninsa cikin birnin Dawuda. Amaziya ɗansa ya gāji sarautarsa.

2 Sarakuna 13

Sarki Yehowahaz na Isra'ila

1 A shekara ta ashirin da uku ta sarautar Yowash ɗan Ahaziya Sarkin Yahuza, Yehowahaz ɗan Yehu ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara goma sha bakwai. 2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, gama ya aikata irin zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra'ilawa su yi zunubi. Bai rabu da zunuban Yerobowam ba. 3 Ubangiji kuwa ya husata da jama'ar Isra'ila, sai ya dinga ba da su a hannun Hazayel Sarkin Suriya, da hannun Ben-hadad ɗan Hazayel. 4 Sai Yehowahaz ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya ji shi, gama ya ga wahalar da Isra'ilawa suke ciki, wato yadda Sarkin Suriya yake musguna musu. 5 Saboda haka Ubangiji ya ba jama'ar Isra'ila maceci, suka kuwa kuɓuta daga ƙangin Suriyawa, suka zauna a gidajensu lafiya kamar dā. 6 Duk da haka ba su rabu da zunuban gidan Yerobowam ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. Sun aikata irin zunuban Yerobowam. Gunkiyan nan mai suna Ashtoret tana nan a Samariya. 7 Rundunar Yehowahaz kuwa ba ta fi mahaya hamsin, da karusai goma, da dakarai dubu goma (10,000 ) ba, gama Sarkin Suriya ya hallaka rundunar, ya yi kaca kaca da ita kamar ƙura a masussuka. 8 Sauran ayyukan Yehowahaz da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 9 Yehowahaz kuwa ya rasu, aka binne shi a Samariya. Yehowash ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Yehowash na Isra'ila

10 A shekara ta talatin da bakwai ta sarautar Yowash Sarkin Yahuza, Yehowash ɗan Yehowahaz ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi shekara goma sha shida yana sarauta. 11 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da dukan zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa jama'ar Isra'ila su yi zunubi. Ya bi halin Yerobowam ɗan Nebat. 12 Sauran ayyukan Yehowash da dukan abin da ya yi, da irin ƙarfin da ya yi yaƙi da Amaziya Sarkin Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 13 Yehowash kuwa ya mutu, aka binne shi a Samariya, inda ake binne sarakunan Isra'ila, sai Yerobowam na biyu ya gāji gadon sarautarsa.

Annabi Elisha ya Rasu

14 Da Elisha ya kamu da ciwon ajali, sai Yehowash Sarkin Isra'ila ya tafi wurinsa, ya yi kuka a gabansa, yana cewa, “Ubana, Ubana, karusar Isra'ila da mahayan dawakanta!” 15 Elisha kuwa ya ce masa, “Ka ɗauki baka da kibau.” Shi kuwa ya ɗauka. nan ya ce, “Ka buɗe tagar da take wajen gabas.” Sai ya buɗe. Elisha ya kuma ce masa, “Ka ja bakan.” Ya kuwa ja. Sai Elisha ya ɗora hannuwansa a bisa hannuwan sarki. Sa'an nan Elisha ya ce, “Harba.” Sai ya harba. Elisha kuwa ya ce, “Kibiyar Ubangiji ta nasara, kibiyar nasara a kan Suriya. Gama za ka yi yaƙi da Suriyawa a Afek har ka ci su.” 18 Sa'an nan ya ce, “Ka ɗauki kibau.” Shi kuwa ya ɗauka. Sai ya ce wa Sarkin Isra'ila, “Ka caki ƙasa da su.” Sai ya caka har sau uku, sa'an nan ya tsaya. 19 Elisha kuwa ya husata, ya ce, “Da ma ka caka sau biyar ko shida da za ka yi nasara a kan Suriyawa har ka ci su sarai, amma yanzu za ka yi nasara da su sau uku kawai.” 20 Elisha kuwa ya rasu, aka binne shi. Maharan Mowabawa sukan kawo yaƙi a ƙasar da bazara. 21 Wata rana ana binne gawa, sai aka ga mahara, aka jefar da gawar a cikin kabarin Elisha. Da gawar ta taɓi ƙasusuwan Elisha, sai ya farko ya tashi ya miƙe tsaye.

Yaƙi Tsakanin Isra'ila da Suriya

22 Hazayel Sarkin Suriya kuwa ya musguna wa jama'ar Isra'ila a dukan zamanin Yehowahaz. 23 Amma Ubangiji ya nuna musu alheri, ya ji tausayinsu, bai ba su baya ba saboda alkawarinsa da Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu. Bai yarda ya hallaka su ba, bai kuma yi watsi da su ba har wa yau. 24 Da Hazayel Sarkin Suriya ya rasu, sai Ben-hadad ɗansa ya gāji sarautarsa. 25 Sai Yehowash ɗan Yehowahaz ya ƙwace daga hannun Ben-hadad, ɗan Hazayel, biranen da Ben-hadad ya ci da yaƙi daga hannun yehowahaz, tsohonsa. Sau uku Yehowash ya ci shi da yaƙi, sa'an nan ya karɓe biranen Isra'ila.

2 Sarakuna 14

Sarki Amaziya na Yahuza

1 A shekara ta biyu ta sarautar Yehowash ɗan Yehowahaz Sarkin Isra'ila, Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza ya ci sarauta. 2 Yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Yehowaddin ta Urushalima. 3 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma bai kai kamar kakansa Dawuda ba. Ya yi kamar yadda tsohonsa, Yowash ya yi. 4 Amma ba a kawar da wuraren yin tsafi a tuddai ba. Mutane suka yi ta miƙa hadaya, da ƙona turare a matsafai na kan tuddai. 5 Sa'ad da mulkin ya kahu sosai a hannun Amaziya, sai ya kashe fādawan da suka kashe tsohonsa. 6 Amma bai kashe 'ya'yan masu kisankai ƙin ba, don ya bi abin da aka rubuta a littafin dokokin Musa, inda Ubangiji ya umarta cewa, “Kada a kashe iyaye saboda 'ya'ya, kada kuma a kashe 'ya'ya saboda iyaye, amma kowa zai mutu saboda laifin kansa.” 7 Ya kuma kashe Edomawa dubu goma (10,000 ) a Kwarin Gishiri, sa'an nan ya ƙwace Sela, ya ba ta suna Yokteyel, haka ake kiranta har wa yau. 8 Amaziya kuwa ya aiki manzanni wurin Yehowash, ɗan Yehowahaz, ɗan Yehu, Sarkin Isra'ila, yana nemansa da yaƙi. 9 Yehowash Sarkin Isra'ila ya mayar wa Amaziya Sarkin Yahuza da amsa cewa, “A dutsen Lebanon ƙaya ta aika wurin itacen al'ul ta ce, ‘Ka ba ɗana 'yarka ya aura.’ Sai mugun naman jeji na Lebanon ya wuce, ya tattake ƙayar. 10 Yanzu kai, Amaziya, ka bugi Edomawa don haka zuciyarka ta kumbura. To ka gode da darajar da ka samu, ka tsaya a gida, gama don me kake tonon rikici da zai jawo maka fāduwa, kai da mutanen Yahuza?” 11 Amma Amaziya bai ji ba. Sai Yehowash Sarkin Isra'ila ya tafi, ya shiga yaƙi da Amaziya, Sarkin Yahuzam a Bet-shemesh ta Yahuza. 12 Mutanen Isra'ila suka ci na Yahuza. Sai kowane mutum ya gudu gida. 13 Yehowash Sarkin Isra'ila kuwa ya kama Amaziya, Sarkin Yahuza, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-shemesh. Ya kuma zo Urushalima ya rushe garun Urushalima kamu ɗari huɗu daga Ƙofar Ifraimu zuwa Ƙofar Kusurwa. 14 Ya kwashe dukan zinariya, da azurfa, da dukan kwanonin da suke cikin Haikalin Ubangiji, da na baitulmalin gidan sarki, da mutanen da aka ba da su jingina, sa'an nan ya koma Samariya. 15 Sauran ayyukan Yehowash da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, da yadda ya yi yaƙi da Amaziya, Sarkin Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 16 Yehowash ya mutu, aka binne shi a Samariya a makabartar sarakunan Isra'ila, Ɗansa Yerobowam na biyu ya gāji sarautarsa.

Mutuwar Sarki Amaziya na Yahuza

17 Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza, ya yi shekara goma sha biyar bayan rasuwar Yehowash ɗan Yehowahaz Sarkin Isra'ila. 18 Sauran ayyukan da Amaziya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 19 Aka ƙulla makirci a kansa a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma aka aika zuwa Lakish, aka kashe shi a can. 20 Aka kawo gawar a kan dawakai, aka binne a Urushalima a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. 21 Sai dukan mutanen Yahuza suka ɗauki Azariya mai shekara goma sha shida, suka sarautar da shi don ya gāji tsohonsa Amaziya. 22 Shi ne ya gina Elat, ya mai da ita ta Yahuza bayan rasuwar tsohonsa.

Sarki Yerobowam na biyu na Isra'ila

23 A shekara goma sha biyar ta sarautar Amaziya ɗan Yowash Sarkin Yahuza, Yerobowam ɗan Yehowash Sarkin Isra'ila, ya ci sarauta a Samariya. Ya yi mulki shekara arba'in da ɗaya. 24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da dukan zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 25 Ya kafa iyakar Isra'ila daga ƙofar Hamat har zuwa tekun Araba. Wannan kuwa shi ne abin da Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya faɗa ta bakin bawansa annabi Yunana, ɗan amittai, daga Gathefer. 26 Gama Ubangiji ya ga Isra'ila tana shan azaba mai tsanani, gama ba bawa ko ɗa wanda zai taimaki Isra'ila. 27 Ubangiji kuwa bai ce zai shafe sunan Isra'ila daga duniya ba, saboda haka ya cece su ta hannun yerobowam na biyu. 28 Sauran ayyukan Yerobowam na biyu, da dukan abin da ya yi, da ƙarfinsa, da yaƙi da ya yi, da yadda ya ƙwato wa Isra'ila Dimashƙu da Hamat waɗanda suke na Yahuza, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 29 Yerobowam na biyu kuwa ya mutu, kamar kakanninsa, sarakunan Isra'ila. Zakariya ɗansa ya gaji sarautarsa.

2 Sarakuna 15

Sarki Azariya na Yahuza

1 A shekara ta ashirin da bakwai ta sarautar Yerobowam na biyu Sarkin Isra'ila, Azariya ɗan Amaziya Sarkin Yahuza, ya ci sarauta. 2 Yana da shekara goma sha shida sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki shekara hamsin da biyu a Urushalima. Sunan tsohuwarsa, Yekoliya ta Urushalima. 3 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda Amaziya, tsohonsa, ya yi. 4 Duk da haka ba a kawar da wuraren tsafi na kan tuddai ba. Mutane suka yi ta miƙa hadayu da ƙona turare a wuraren tsafi na kan tuddai. 5 Sai Ubangiji ya buge shi da kuturta, ya kuwa zama kuturu har ran da ya rasu. Ya zauna a wani gida a ware. Sai Yotam ɗansa ya zama wakilin gidan, yana kuma mulkin jama'ar ƙasar. 6 Sauran ayyukan Azariya, da dukan abin da ya yi an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 7 Azariya ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda. Yotam ɗansa ya gāji sarautarsa.

Sarki Zakariya na Isra'ila

8 A shekara ta talatin da takwas ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Zakariya ɗan Yerobowam na biyu, ya ci sarautar Isra'ila a Samariya wata shida. 9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda kakanninsa suka yi. Bai rabu da zunuban yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 10 Shallum ɗan Yabesh ya ƙulla masa maƙarƙashiya, ya buge shi a Ibleyam, ya kashe shi, sa'an nan ya hau gadon sarautarsa. 11 Sauran ayyukan da Zakariya ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 12 Wannan shi ne alkawarin da Ubangiji ya yi wa Yehu, cewa 'ya'yansa maza za su zauna a gadon sarautar Isra'ila har tsara ta huɗu. Haka kuwa ya zama.

Sarki Shallum na Isra'ila

13 Shallum ɗan Yabesh ya ci sarauta a shekara ta talatin da tara ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza. Ya yi mulki wata ɗaya a Samariya. 14 Menahem ɗan Gadi daga Tirza ya zo Samariya ya bugi Shallum ɗan Yabesh a Samariya, ya kashe shi, ya hau gadon sarautarsa. 15 Sauran ayyukan Shallum duk da makircin da ya ƙulla, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 16 A lokacin nan sai Menahem ya hallaka Tifsa da dukan waɗanda suke cikinta, da karkararta tun daga Tirza, domin ba su karɓe shi ba, saboda haka ya hallaka ta, ya tsattsage dukan matan da suke da juna biyu.

Sarki Menahem na Isra'ila

17 A shekara ta talatin da tara ta sarautar Azariya, Sarkin Yahuza, Menahem ɗan Gadi, ya ci sarautar. Ya yi shekara goma a Samariya. 18 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. A dukan kwanakinsa bai rabu da zunubin Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 19 Tiglatfilesar, mai mulkin Assuriya, ya kawo wa ƙasar yaƙi, Menahem kuwa ya ba Tiglat-filesar talanti dubu (1,000 ) na azurfa, don dai ya taimake shi yadda sarautarsa za ta kahu sosai. 20 Menahem ya karɓi kuɗin daga mutanen Isra'ila, wato daga attajirai. Ya tilasta wa kowannensu ya ba da azurfa hamsin. Saboda haka Tiglat-filesar mai mulkin Assuriya ya koma ƙasarsa. 21 Sauran ayyukan Menahem, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 22 Menahem ya mutu, ɗansa Fekahiya ya gaji sarautarsa.

Sarki Fekahiya na Isra'ila

23 A shekara ta hamsin ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Fekahiya ɗan Menahem, ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara biyu. 24 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 25 Sai shugaban sojojinsa, wato Feka, ɗan Remaliya daga Gileyad, tare da mutum hamsin suka ƙulla maƙarƙashiya, suka kashe Fekahiya tare da Argob da Ariye a Samariya a fādarsa. Da suka kashe shi, sai Feka ya zama sarki. 26 Sauran ayyukan Fekahiya, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

Sarki Feka na Isra'ila

27 A shekara ta hamsin da biyu ta sarautar Azariya Sarkin Yahuza, Feka ɗan Remaliya ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara ashirin. 28 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. Bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat ba, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi. 29 A zamanin Feka Sarkin Isra'ila, sai Tiglat-filesar mai mulkin Assuriya, ya zo ya ci Iyon, da Abel-bet-ma'aka, da Yanowa, da Kedesh, da Hazor, da Gileyad, da Galili, da dukan ƙasar Naftali. Sa'an nan ya kwashe mutane zuwa bauta a Assuriya. 30 Hosheya ɗan Ila kuwa ya ƙulla wa Feka ɗan Remaliya maƙarƙashiya, ya buge shi ya kashe shi, sa'an nan ya ci sarauta a shekara ta ashirin ta sarautar Yotam ɗan Azariya. 31 Sauran ayyukan Feka da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Isra'ila.

Sarki Yotam na Yahuza

32 A shekara ta biyu ta sarautar Feka ɗan Remaliya Sarkin Isra'ila, Yotam ɗan Azariya Sarkin Yahuza, ya ci sarauta. 33 Yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarautar. Ya yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yerusha, 'yar Zadok. 34 Yotam ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa, Azariya, ya yi. 35 Duk da haka ba a kawar da wuraren tsafi na kan tuddai ba, amma mutane suka yi ta miƙa hadayu da ƙona turare a matsafai na kan tuddai. Shi ne ya gina ƙofa ta bisa ta Haikalin Ubangiji. 36 Sauran ayyukan Yotam, da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 37 A kwanakin nan Ubangiji ya fara aiken Rezin Sarkin Suriya da Feka ɗan Remaliya su yi yaƙi da Yahuza. 38 Yotam ya rasu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin kakansa Dawuda. Sai Ahaz ɗansa ya gaji sarautarsa.

2 Sarakuna 16

Sarki Ahaz na Yahuza

1 A shekara ta goma sha bakwai ta sarautar Feka ɗan Remaliya, Ahaz ɗan Yotam Sarkin Yahuza, ya ci sarauta. 2 Ahaz yana da shekara ashirin sa'ad da ya ci sarautar, ya kuwa yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima. Bai yi abin da yake da kyau a gaban Ubangiji Allahnsa ba, kamar yadda kakansa Dawuda ya yi. 3 Ya bi halin sarakunan Isra'ila. Har ma ya yi hadaya ta ƙonawa da ɗansa, kamar mugayen ayyukan al'ummai da Ubangiji ya kora a gaban mutanen Isra'ila. 4 Ya kuma miƙa hadaya da turaren ƙonawa a wuraren tsafi na kan tuddai da ƙarƙashin itatuwa masu duhuwa. 5 Rezin Sarkin Suriya kuwa, da Feka ɗan Remaliya Sarkin Isra'ila, suka kawo wa Urushalima yaƙi. Suka kewaye Ahaz da yaƙi, amma ba su ci shi ba. 6 A lokacin nan kuma Sarkin Edom ya sāke ƙwace Elat, ya kori Yahudawa daga cikinta, Edomawa suka zo suka zauna a ciki har wa yau. 7 Ahaz kuwa ya aiki manzanni wurin Tiglat-filesar, mai mulkin Assuriya, ya ce, “Ni baranka ne, ɗanka kuma, ka zo ka cece ni daga hannun Sarkin Suriya da Sarkin Isra'ila, waɗanda suke yaƙi da ni.” 8 Ahaz kuma ya kwashe azurfa da zinariya da suke cikin Haikalin Ubangiji, da wadda take cikin baitulmalin sarki, ya aika wa mai mulkin Assuriya kyauta. 9 Tiglat-filesar ya ji roƙonsa, sai ya zo ya faɗa wa Dimashƙu da yaƙi, ya ci ta. Sa'an nan ya kwashe mutane zuwa Kir. Ya kuma kashe sarki Rezin. 10 Sa'ad da sarki Ahaz ya tafi Dimashƙu don ya sadu da Tiglat-filesar, Sarkin Assuriya, ya ga bagaden da yake a Dimashƙu, sai ya aika wa Uriya firist, da siffar bagaden, da fasalinsa, da cikakken bayaninsa. 11 Uriya firist kuwa, ya gina bagaden bisa ga yadda sarki Ahaz ya aika masa daga Dimashƙu. Uriya firist, ya gina bagaden kafin sarki Ahaz ya komo daga Dimashƙu. 12 Da sarki ya komo daga Dimashƙu, ya hango bagaden, sai ya tafi kusa da shi. 13 Sa'an nan ya miƙa hadayarsa ta ƙonawa, da hadayarsa ta gari, da hadayarsa ta sha, ya yayyafa jinin hadayarsa ta salama a bisa bagaden. 14 Sai ya kawar da bagaden tagulla wanda aka keɓe ga Ubangiji, ya sa shi arewacin sabon bagadensa. 15 Sarki Ahaz ya umarci Uriya firist cewa, “Sai ka miƙa hadaya ta ƙonawa ta safe, da hadaya ta gari ta maraice, da hadaya ta ƙonawa ta sarki, da hadayarsa ta gari, da hadaya ta ƙonawa ta dukan jama'ar ƙasar, da hadayarsu ta gari, da hadayarsu ta sha, ka yayyafa dukan jinin hadaya ta ƙonawa, da dukan jinin hadayu a bisa babban bagaden. Amma bagaden tagulla zai zama nawa don yin ibada.” 16 Uriya firist kuwa, ya yi dukan abin da sarki Ahaz ya umarta. 17 Sarki Ahaz kuwa ya yanke sassan dakalan, ya ɗauke daruna da suke bisansu, ya kuma ɗauke kwatarniya da take bisa bijimai na tagulla, ya ajiye kwatarniya a daɓen dutse. 18 Hanyar da aka killace ta Asabar, wadda suka yi a cikin gidan, da ƙofar waje ta shigar sarki, Ahaz ya kawar da su daga Haikalin Ubangiji saboda Sarkin Assuriya. 19 Sauran ayyukan Ahaz waɗanda ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 20 Ahaz ya mutu, aka binne shi a makabartar kakanninsa a birnin Dawuda. Sai ɗansa, Hezekiya, ya gaji sarautarsa.

2 Sarakuna 17

Faɗuwar Samariya da Bautar Isra'ila

1 A shekara ta goma sha biyu ta sarautar Ahaz Samariya Yahuza, Hosheya ɗan Ila ya ci sarautar Isra'ila a Samariya. Ya yi mulki shekara tara. 2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar sauran sarakunan Isra'ila da suka riga shi ba. 3 Sai Shalmanesar Sarkin Assuriya, ya kawo masa yaƙi, Hosheya kuwa ya zama talakansa, yana kai masa haraji. 4 Amma SArkin Assuriya ya gane Hosheya ya tayar masa, gama ya aiki manzanni wurin So, wato Sarkin Masar, ya kuma ƙi ya kai wa Sarkin Assuriya haraji kamar yadda ya saba yi kowace shekara, Saboda haka sai Sarkin Assuriya ya kama shi ya sa shi a kurkuku. 5 Sa'an nan Sarkin Assuriya ya kai wa dukan ƙasar yaƙi, har ya kai Samariya. Ya kewaye Samariya da yaƙi shekara uku. 6 A shekara ta tara ta sarautar Hosheya, Sarkin Assuriya ya ci Samariya, ya kwashe Isra'ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa. 7 Wannan abu ya sami Isra'ila saboda sun yi wa Ubangiji Allahnsu zunubi, shi wanda ya fito da su daga ƙasar Masar, daga hannun Fir'auna, Sarkin Masar. Suka bauta wa gumaka. 8 Suka bi al'adun al'ummai waɗanda Ubangiji ya kora a gabansu, da al'adun da sarakunan Isra'ila suka kawo. 9 Jama'ar Isra'ila kuma suka yi wa Ubangiji Allahnsu abubuwan da ba daidai ba, daga ɓoye. Sun gina wa kansu matsafai a dukan garuruwansu daga hasumiya zuwa birni mai garu. 10 Suka kuma kafa wa kansu ginshiƙai da siffofin gumakan Ashtarot a kowane tudu da a ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa. 11 Suka ƙona turare a kan wuraren tsafi na kan tuddai kamar yadda al'ummar da Ubangiji ya kora daga gabansu suka yi. Suka aikata mugayen abubuwa, suka su Ubangiji ya yi fushi. 12 Suka bauta wa gumaka waɗanda Ubangiji ya ce musu kada su bauta musu. 13 Amma Ubangiji ya faɗakar da jama'ar Isra'ila da jama'ar Yahuza ta bakin annabawa da kowane maigani, cewa su bar mugayen hanyoyinsu, su kiyaye umarnansa da dukan dokokinsa waɗanda ya umarci kakanninsu da su, waɗanda kuma ya aiko musu ta wurin bayinsa annabawa. 14 Duk da haka suka ƙi kasa kunne, suka taurare zuciyarsu kamar yadda kakanninsu suka yi, waɗanda ba su yi imani da Ubangiji Allahnsu ba. 15 Suka yi watsi da dokokinsa, da alkawarinsa da ya yi wa kakanninsu, da kuma faɗakarwar da ya yi musu. Suka bi gumakan banza, suka zama banza, suka bi halin al'ummai da suke kewaye da su, waɗanda Ubangiji ya umarce su kada su yi kamarsu. 16 Suka bar dukan umarnan Ubangiji Allahnsu, suka yi wa kansu siffofin zubi na 'yan maruƙa biyu, suka yi gunkiyan nan, Ashtoret, suka yi wa taurari sujada, suka bauta wa Ba'al. 17 Suka yi hadaya ta ƙonawa da 'ya'yansu mata da maza. Suka yi duba, suka yi sihiri, suka duƙufa ga aikata mugunta a gaban Ubangiji, suka sa shi ya yi fushi. 18 Saboda wannan Ubangiji ya husata da jama'ar Isra'ila, ya kawar da su daga gabansa, ba wanda aka rage, sai dai kabilar Yahuza. 19 Jama'ar Yahuza kuma ba su kiyaye umarnan Ubangiji Allahnsu ba, sai suka bi al'adun da mutanen Isra'ila suka kawo. 20 Ubangiji kuwa ya ƙi dukan zuriyar Isra'ila, ya wahalshe su, ya kuma bashe su a hannun mugayen abokan gāba, ta haka ya kawar da su daga gabansa. 21 Sa'ad da Ubangiji ya ɓalle Isra'ila daga gidan Dawuda, sai suka naɗa Yerobowam ɗan Nebat ya zama sarki. Yerobowam kuwa ya karkatar da jama'ar Isra'ila daga bin Ubangiji. Ya sa su suka aikata babban zunubi. 22 Jama'ar Isra'ila suka yi ta aikata dukan zunuban da Yerobowam ya yi, ba su daina aikata su ba, 23 har lokacin da Ubangiji ya kawar da su daga gabansa kamar yadda ya faɗa ta bakin bayinsa, annabawa. Saboda haka aka fitar da jama'ar Isra'ila daga ƙasarsu zuwa Assuriya har wa yau.

An Zaunar da Assuriyawa cikin Isra'ilawa

24 Sarkin Assuriya kuwa ya kawo mutane daga Babila, da Kuta, da Awwa, da Hamat, da Sefarwayim, ya zaunar da su a garuruwan Samariya a maimakon jama'ar Isra'ila. Sai suka mallaki Samariya, suka zauna a garuruwanta. 25 A farkon zamansu a can, ba su yi tsoron Ubangiji ba saboda haka Ubangiji ya aika da zakoki a cikinsu, suka karkashe waɗansu daga cikinsu. 26 Sai aka faɗa wa Sarkin Assuriya cewa, “Al'umman da ka kwashe ka zaunar da su a garuruwan Samariya ba su san shari'ar Allahn ƙasar ba, domin haka ya aiki zakoki a cikinsu, suna ta karkashe su.” 27 Sa'an nan Sarkin Assuriya ya umarta a aiki firist ɗaya daga cikin firistocin da aka kwashe daga can, ya tafi, ya zauna can don ya koya musu shari'a Allahn ƙasar. 28 Sai firist ɗaya daga cikin firistocin da suka kwashe daga Samariya, ya zo, ya zauna a Betel. Shi kuwa ya koya musu yadda za su yi tsoron Ubangiji. 29 Amma duk da haka kowace al'umma ta riƙa yin gumakanta, tana ajiye su a wuraren yin tsafin na kan tuddai waɗanda Samariyawa suka gina. Kowace al'umma kuma ta yi haka a garin da ta zauna. 30 Mutanen Babila suka yi Sukkot-benot, mutanen Kuta suka yi Nergal, mutanen Hamat suka yi Ashima. 31 Awwiyawa suka yi Nibhaz da Tartak, mutanen Sefarwayim suka miƙa 'ya'yansu hadaya ta ƙonawa ga Adrammelek da Anammelek, gumakansu. 32 Su ma suka yi tsoron Ubangiji, suka sa mutane iri dabam dabam su zama firistocin wuraren tsafinsu na kan tuddai. Firistocin nan suka miƙa hadayu dominsu a ɗakunan tsafinsu na kan tuddai. 33 Waɗannan mutane su ma suka yi wa Ubangiji sujada, amma kuma suka bauta wa gumakansu ta hanyar da al'umman da aka kwaso su daga cikinsu suke yi. 34 Har wa yau suna yin yadda suka yi a dā. Ba su yi tsoron Ubangiji ba, ba su bi dokoki, ko ka'idodi, ko shari'a, ko umarnan Ubangiji ba, waɗanda ya umarci 'ya'yan Yakubu, wanda ya sa wa suna Isra'ila. 35 Ubangiji ya yi alkawari da 'ya'yan Yakubu, ya kuma umarce su kada su yi wa gumaka sujada ko su durƙusa musu, ko su bauta musu, ko su miƙa musu hadayu. 36 Amma su yi tsoron Ubangiji, wanda ya fisshe su daga ƙasar Masar da iko mai girma da ƙarfi, shi za su yi wa sujada, shi kuma za su miƙa wa hadayu. 37 Sai su yi biyayya da dokokinsa da umarnansa da ya rubuta musu. Kada su ji tsoron waɗansu alloli. 38 Kada su manta da alkawarin da ya yi da su, kada kuma su ji tsoron gumaka. 39 Amma su yi tsoron Ubangiji Allahnsu, shi kuwa zai cece su daga hannun dukan abokan gābansu. 40 Duk da haka ba su kasa kunne ba, amma suka yi kamar yadda suka saba yi tun dā. 41 Waɗannan al'ummai suka yi wa Ubangiji sujada, amma suka kuma yi ta bauta wa gumakansu. Haka kuma 'ya'yansu da jikokinsu suka yi kamar yadda kakanninsu suka yi. Haka suke yi har wa yau.

2 Sarakuna 18

Sarki Hezekiya na Yahuza

1 A shekara ta uku ta sarautar Hosheya ɗan Ila Sarkin Isra'ila, Hezekiya ɗan Ahaz Sarkin Yahuza ya ci sarautar. 2 Yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarautar. Ya yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Abi, 'yar Zakariya. 3 Ya aikata abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji kamar yadda kakansa, Dawuda, ya yi. 4 Ya kawar da wuraren tsafi na kan tuddai, ya rurrushe ginshiƙai, ya sassare siffar Ashtoret. Ya kuma farfashe macijin tagulla wanda Musa ya yi, gama har zuwa lokacin jama'ar Isra'ila suna miƙa masa hadaya ta turaren ƙonawa. Aka ba macijin suna Nehushatan. 5 Hezekiya ya dogara ga Ubangiji Allah na Isra'ila. Ba a sami kamarsa a cikin dukan sarakunan Yahuza ba, waɗanda suka yi sarauta a gabansa, ko waɗanda suka yi bayansa. 6 Ya manne wa Ubangiji, bai bar binsa ba, ya kuma kiyaye umarnan da Ubangiji ya ba Musa. 7 Ubangiji kuwa ya kasance tare da shi, duk inda ya nufa sai ya sami albarka. Ya tayar wa Sarkin Assuriya, ya ƙi bautar masa. 8 Ya kuma bugi Filistiyawa har zuwa Gaza da iyakarta daga hasumiya zuwa birni mai garu.

Faɗuwar Samariya

9 A shekara ta huɗu ta sarautar sarki Hezekiya, a lokacin Hosheya ɗan Ila, Sarkin Isra'ila, yana da shekara bakwai da sarauta, sai Shalmanesar Sarkin Assuriya ya kawo wa Samariya yaƙi, ya kewaye ta. 10 A ƙarshen shekara ta uku, ya ci ta da yaƙi. A lokacin Hezekiya yana da shekara shida da sarauta, Hosheya kuwa yana da shekara tara da tasa sarauta. 11 Sarkin Assuriya kuwa ya kwashi Isra'ilawa zuwa Assuriya, ya ajiye su a Hala, da Habor a bakin kogin Gozan, da cikin garuruwan Mediyawa. 12 Ba su yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu ba, amma suka karya alkawarinsa har da dukan abin da Musa bawan Ubangiji ya umarta. Ba su kasa kunne ba, balle su aikata. Domin wannan Samariya ta faɗi.

Assuriyawa sun yi wa Urushalima Barazana

13 A shekara ta goma sha huɗu ta sarautar sarki Hezekiya, sai Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya kawo wa dukan birane masu garu na Yahuza yaƙi, ya kuwa ci su. 14 Sai Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya aika zuwa wurin Sarkin Assuriya a Lakish cewa, “Na yi laifi, ka ƙyale ni, duk abin da ka ɗora mini zan ɗauka.” Sai Sarkin Assuriya ya ce wa Hezekiya Sarkin Yahuza ya ba shi talanti ɗari uku na azurfa, da talanti talatin na zinariya. 15 Hezekiya kuwa ya ba shi dukan azurfar da take cikin Haikalin Ubangiji, da wanda ke cikin baitulmali na gidan sarki. 16 A lokacin sai Hezekiya ya kankare zinariyar da aka dalaye ƙofofi da madogaran ƙofofin Haikalin Ubangiji da ita, ya ba Sarkin Assuriya. 17 Sai Sarkin Assuriya ya aiki Tartan, da Rabsaris, da Rabshake, tare da sojoji da yawa daga Lakish zuwa ga sarki Hezekiya a Urushalima. Suka haura zuwa Urushalima, suka tsaya kusa da wuriyar ruwan kududdufi wanda yake kan tudu, wanda yake a kan karauka zuwa wurin wanki. 18 Sa'ad da suka kira sarki, sai Eliyakim ɗan Hilkiya, wanda yake wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci, suka fito. 19 Sa'an nan Rabshake ya ce musu, “Ku faɗa wa Hezekiya, cewa mai girma, Sarkin Assuriya ya ce, ‘Ga wa kake dogara? 20 Kana tsammani maganganu kurum su ne dabara da ƙarfin yin yaƙi? To, ga wa ka dogara har da ka tayar mini? 21 Ga shi yanzu, kana dogara ga Masar, wannan karyayyen sandan kyauro, wanda yakan yi wa hannun mutumin da yake tokarawa da shi sartse. Haka Fir'auna Sarkin Masar, yake ga dukan waɗanda suke dogara gare shi.’ 22 “Amma idan ka ce mini, ‘Ina dogara ga Ubangiji Allahnmu,’ to, ba masujadansa na kan tuddai da bagadansa ne Hezekiya ya rurrushe ba? Yana ce wa mutanen Yahuza da Urushalima, ‘Za ku yi sujada a gaban wannan bagade a Urushalima?’ 23 Sai ka zo, ku daidaita da ubangidana, Sarkin Assuriya. Zan ba ka dawakai dubu biyu (2,000 ), idan za ka iya samun mahayansu. 24 Ba ka isa ka kara da ko mafi ƙanƙanta na shugabannin sojojin maigidana ba, amma har kana dogara ga Masar don samun karusai da mahaya? 25 Kana tsammani, ba da yardar Ubangiji ba ne na kawo wa wurin nan yaƙi don a hallaka shi? Gama Ubangiji ya ce mini, ‘Ka kai wa wannan ƙasa yaƙi don ka hallaka ta.’ ” 26 Sai Eliyakim ɗan Hilkiya, da Shebna, da Yowa, suka ce wa Rabshake, “Muna roƙonka, ka yi magana da mu barorinka da harshen Aramiya gama muna jinsa, kada ka yi magana da mu da harshen Yahudanci, har mutanen da suke kan garu su ji.” 27 Amma Rabshake ya ce musu, “Ai, ubangidana bai aike ni in yi wannan magana ga ubangidanku da ku kaɗai ba, amma ga dukan mutanen da suke zaune a kan garu, waɗanda aka ƙaddara su tare da ku don su ci najasarsu su sha fitsarinsu.” 28 Sa'an nan Rabshake ya tsaya, ya yi kira da ƙarfi da harshen Yahudanci, ya ce, “Ku ji maganar mai girma, Sarkin Assuriya! 29 Sarki ya ce, ‘Kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, gama ba zai iya cetonku daga hannuna ba. 30 Kada kuma ku yarda Hezekiya ya sa ku dogara ga Ubangiji da cewa lalle Ubangiji zai cece ku, ba za a kuma ba da wannan birni a hannun Assuriya ba.’ 31 Kada ku kasa kunne ga Hezekiya, gama Sarkin Assuriya ya ce, ‘Ku yi amana da ni, ku fito zuwa wurina. Kowane ɗayanku kuwa zai ci 'ya'yan inabinsa da 'ya'yan ɓaurensa, ya kuma sha ruwa daga cikin randarsa, 32 har lokacin da zan zo in kwashe ku, in kai ku wata ƙasa mai kama da taku, ƙasa mai yalwar hatsi, da ruwan inabi, da abinci, da gonakin inabi, da itatuwan zaitun, da zuma, don ku rayu, kada ku mutu! Kada kuma ku yarda Hezekiya ya yaudare ku da cewa Ubangiji zai cece ku. 33 Ko akwai wani allah daga cikin allolin al'ummai, wanda ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannun Sarkin Assuriya? 34 Ina allolin Hamat, da na Arfad, da na Sefarwayim, da na Hena, da na Iwwa? Sun ceci Samariya daga hannuna ne? 35 Daga cikin dukan allolin ƙasashe, wane ne ya taɓa ceton ƙasarsa daga hannuna har da Ubangiji zai ceci Urushalima daga hannuna?’ ” 36 Sai mutanen suka yi tsit, ba wanda ya ce masa uffan, gama sarki ya umarta cewa kada a tanka masa. 37 Sa'an nan Eliyakim ɗan Hilkiya, wanda yake wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da Yowa ɗan Asaf marubuci, suka zo wurin Hezekiya da tufafinsu ketattu, suka faɗa masa irin maganar da Rabshake ya yi.

2 Sarakuna 19

An Ceci Yahuza daga Sennakerib

1 Da sarki Hezekiya ya ji wannan magana, sai ya kyakketa tufafinsa, ya sa rigar makoki, sa'an nan ya shiga Haikalin Ubangiji. 2 Sai ya aiki Eliyakim wakilin gidan sarki, da Shebna magatakarda, da manyan firistoci, saye da tufafin makoki zuwa wurin annabi Ishaya, ɗan Amoz, 3 su ce masa, “Hezekiya ya ce, yau ranar wahala ce, da ta cin mutunci, da ta shan kunya, ga shi, 'ya'ya suna gab da a haife su, amma ba ƙarfin da za a yi yunƙuri a haife su. 4 Mai yiwuwa ne Ubangiji Allahnka ya ji dukan maganganun da Rabshake ya yi wanda ubangidansa, Sarkin Assuriya, ya aiko don yi wa Allah mai rai ba'a. Bari Ubangiji Allahnka ya hukunta masa saboda maganganunsa, sai ka yi addu'a saboda sauran da suka ragu.” 5 Sa'ad da fādawan sarki Hezekiya suka iso wurin Ishaya, 6 sai ya aike da amsa, ya ce musu, “Ku faɗa wa ubangidanku, Ubangiji ya ce, ‘Kada ka ji tsoron maganganun da ka ji daga bakin barorin Sarkin Assuriya, waɗanda suka saɓe ni. 7 Ga shi, zan sa wani ruhu a cikinsa da zai ji jita-jita, har ya koma ƙasarsa, zan sa a kashe shi da takobi a ƙasarsa.’ ” 8 Rabshake kuwa ya koma, ya tarar Sarkin Assuriya yana yaƙi da Libna, gama ya ji labari sarki ya riga ya bar Lakish. 9 Da sarki ya ji labari Tirhaka, Sarkin Habasha, ya fito don ya yi yaƙi da shi, sai ya sāke aikar manzanni wurin Hezekiya, ya ce, 10 “Ku faɗa wa Hezekiya Sarkin Yahuza, kada ya yarda Allahnsa wanda yake dogara gare shi ya yaudare shi da yi masa alkawari, cewa Sarkin Assuriya ba zai ci Urushalima ba. 11 Ya ji abin da Sarkin Assuriya ya yi wa dukan ƙasashe yadda ya hallaka su sarai. To, shi zai kuɓuta? 12 Allolin al'ummai sun cece su ne? Wato al'umman da kakannina suka hallaka, wato Gozan, da Haran, da Rezef, da mutanen Eden da suke Telassar. 13 Ina Sarkin Hamat, da Sarkin Arfad, da sarkin birnin Sefarwayim, da Sarkin Hena, da Sarkin Iwwa?” 14 Hezekiya ya karɓi wasiƙa daga hannun manzannin ya karanta ta, sa'an nan ya shiga Haikalin Ubangiji, ya buɗe ta, ya ajiye ta a gaban Ubangiji. 15 Sa'an nan ya yi addu'a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, kai da kake zaune a kan gadon sarautarka, kai kaɗai ne Allah a dukan mulkokin duniya, kai ne ka yi sama da ƙasa. 16 Ka kasa kunne, ya Ubangiji, ka yi. Ka buɗe idanunka, ya Ubangiji, ka gani, ka kuma ji irin maganar Sennakerib wadda ya aiko don a yi wa Allah mai rai ba'a. 17 A gaskiya kam, ya Ubangiji, sarakunan Assuriya sun lalatar da al'ummai da ƙasashensu. 18 Sun jefar da gumakansu cikin wuta, gama su ba Allah ba ne, amma ayyukan hannuwan mutane ne, waɗanda aka yi da itace da dutse, saboda haka an iya a hallaka su. 19 Yanzu ya Ubangiji Allahnmu, ina roƙonka ka cece mu daga hannunsa domin dukan mulkokin duniya su sani kai kaɗai ne Allah, ya Ubangiji.” 20 Sa'an nan Ishaya, ɗan Amoz, ya aika wa Hezekiya cewa, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ji addu'arka, ya kuma amsa.” 21 Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima ya yi maka dariya, kai Sennakerib, yana yi maka ba'a. 22 Wa kake tsammani ka yi wa ba'a har da zagi? Ba ka ga girmana ba, ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila? 23 Ka aiki manzanninka su nuna mini girmankai saboda ka ci duwatsu mafi tsayi da karusanka, har ma ka ci duwatsun Lebanon. Ka yi fariyar a kan ka datse itatuwan al'ul mafi tsayi da na fir, har kuma ka shiga har can tsakiyar kurmi. 24 Ka yi fariya a kan gina rijiyoyi, ka sha ruwan baƙuwar ƙasa, ƙafafun sojojinka kuma sun tattake Kogin Nilu, ya ƙafe. 25 “Ba ka taɓa ji ba, cewa na ƙaddara wannan tun dā? Abin da yake faruwa yanzu, na shirya shi tun tuni, yadda za ka mai da birane masu garu su zama kufai. 26 Mazauna cikinsu suka rasa ƙarfi, suka damu, suka ruɗe. Suka zama kamar ciyawar saura, ko kuma ciyawar da ta tsiro a rufin soro, da iskar gabas mai zafi ta busa, har ta bushe. 27 “Na san zamanka, da fitarka, da shigowarka, da fushin da kake yi da ni. 28 Na ji irin fushinka da girmankanka, yanzu kuwa zan sa ƙugiya a hancinka, linzami kuma a bakinka, in komar da kai baya, ta hanyar da ka biyo.” 29 Sa'an nan Ishaya ya ce wa sarki Hezekiya, “Wannan zai zama alama a gare ka. A wannan shekara za ku ci gyauro, a shekara ta biyu za ku ci gyauron gyauron, a shekara ta uku kuwa za ku shuka ku girbe, ku dasa inabi a gonakin inabi, ku ci 'ya'yansu. 30 Ringin mutanen gidan Yahuza za su yi saiwa a ƙasa, sa'an nan su ba da 'ya'ya a sama. 31 Gama daga Urushalima ringi zai fito, daga Dutsen Sihiyona kuma waɗanda suka tsira za su fito. Kishin Ubangiji ne zai yi wannan.” 32 Saboda haka Ubangiji ya ce, “Sarkin Assuriya ba zai zo birnin ba, ko ya harba kibiya, ko ya zo kusa da shi da garkuwa, ko ya tsiba masa tudu. 33 Zai koma ta hanyar da ya zo. Ba zai shiga wannan birni ba. 34 Gama zan tsare wannan birni, in cece shi don kaina, da kuma don bawana Dawuda.” 35 A daren nan, sai mala'ikan Ubangiji ya tafi ya kashe Assuriyawa a sansaninsu, mutum dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar (185,000 ). Sa'ad da mutanen Isra'ila suka tashi da sassafe, sai suka ga gawawwakin nan kwance. 36 Sennakerib Sarkin Assuriya, kuwa ya tashi, ya koma gida, ya zauna a Nineba. 37 Sa'ad da yake yin sujada a haikalin gunkinsa Nisrok, sai 'ya'yansa, Adrammelek da Sharezer, suka kashe shi da takobi, sa'an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Sai ɗansa guda, wato Esar-haddon ya gāji gadon sarautarsa.

2 Sarakuna 20

Ciwon Hezekiya da Warkewarsa

1 A waɗannan kwanaki sai Hezekiya ya yi rashin lafiya har yana gab da mutuwa. Sai annabi Ishaya, ɗan Amoz, ya zo wurinsa, ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka, gama mutuwa za ka yi, ba za ka warke ba.” 2 Hezekiya kuwa ya juya fuskarsa bango, ya yi roƙo ga Ubangiji, yana cewa, 3 “Ka tuna da ni yanzu, ya Ubangiji, ina roƙonka, da yadda na yi tafiya a gabanka da aminci, da zuciya ɗaya, na aikata abin da yake mai kyau a gabanka.” Sai ya yi ta rusa kuka. 4 Kafin Ishaya ya fita daga filin tsakiyar fādar, sai Ubangiji ya yi magana da shi, ya ce, 5 “Ka koma, ka faɗa wa Hezekiya sarkin jama'ata cewa, ‘Ni Ubangiji Allahn kakanka, Dawuda, na ji roƙonka, na kuma ga hawayenka, saboda haka zan warkar da kai, a rana ta uku kuwa za ka haura zuwa Haikalin Ubangiji. 6 Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuwa cece ka, kai da wannan birni daga hannun Sarkin Assuriya, zan tsare wannan birni don kaina da kuma don bawana, Dawuda.’ ” 7 Sai Ishaya ya ce, “Ku yi masa farsa da ɓaure, marurun zai warke.” 8 Hezekiya kuwa ya ce wa Ishaya, “Mece ce alama, cewa Ubangiji zai warkar da ni har in haura zuwa Haikalin Ubangiji a rana ta uku?” 9 Sai Ishaya ya ce, “Wannan ita ce alama daga wurin Ubangiji, Ubangiji zai cika alkawarin da ya yi. Ƙaƙa kake so, inuwa ta yi gaba da taki goma, ko kuwa ta yi baya da taki goma?” 10 Hezekiya ya amsa, ya ce, “Ai, ya fi sauƙi inuwa ta yi gaba da taki goma da ta yi baya da taki goma.” 11 Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya komar da inuwa baya da taki goma, bayan da ta riga ta wuce a matakin sarki Ahaz.

Hezekiya ya Karɓi Manzanni daga Babila

12 A lokacin nan sai Merodak-baladan, ɗan Baladan, Sarkin Babila, ya ji labarin rashin lafiyar Hezekiya, sai ya aiki manzanni da wasiƙa da kyautai su kai wa Hezekiya, 13 Hezekiya kuwa ya marabce su, ya kuma nuna musu dukan taskokin dukiyarsa na azurfa, da na zinariya, da na turare, da na mai mai daraja, da na makaman yaƙinsa, da dukan abin da yake akwai a cikin ɗakunan ajiyarsa. Ba abin da ya rage daga cikin gidansa, ko a mulkinsa wanda bai nuna musu ba. 14 Sai annabi Ishaya ya tafi wurin sarki Hezekiya ya ce masa, “Daga ina ne waɗannan mutane? Me suka ce maka?” Hezekiya ya amsa, ya ce, “Sun zo daga ƙasa mai nisa, wato Babila.” 15 Ishaya ya ce, “Me suka gani a fādarka?” Hezekiya ya ce, “Sun ga duk abin da yake ciki, ba wani abu kuma daga cikin taskokina da ban nuna musu ba.” 16 Sa'an nan Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji abin da Ubangiji ya ce, 17 ‘Lokaci yana zuwa da za a kwashe duk abin da yake cikin gidanka, da abin da kakanninka suka tanada, zuwa Babila. 18 Za a kuma kwashe waɗansu 'ya'yanka da ka haifa zuwa Babila, can za a maishe su babani a fādar Sarkin Babila.’ ” 19 Sarki Hezekiya kuwa ya fahimci za a yi zaman lafiya da salama a zamaninsa, don haka ya amsa ya ce, “Jawabin da ka kawo mini daga wurin Ubangiji yana da kyau.”

Rasuwar Hezekiya

20 Sauran ayyukan Hezekiya da dukan ƙarfinsa, da yadda ya yi tafki da wuriyar ruwa don ya kawo ruwa cikin birnin, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 21 Hezekiya kuwa ya rasu. Sai ɗansa, Manassa, ya gāji gadon sarautarsa.

2 Sarakuna 21

Sarki Manassa na Yahuza

1 Manassa yana da shekara goma sha biyu sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara hamsin da biyar yana sarauta a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Hefziba. 2 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji, gama ya aikata abubuwa masu banƙyama waɗanda al'umman da Ubangiji ya kora a gaban jama'ar Isra'ila suka aikata. 3 Gama ya gina matsafai a kan tuddai waɗanda Hezekiya tsohonsa ya rurrushe. Ya kuma gina wa Ba'al bagadai, ya kuma yi gunkiyan nan, wato Ashtoret, kamar yadda Ahab, Sarkin Isra'ila, ya yi. Ya yi wa taurari sujada, ya bauta musu. 4 Ya gina bagadai a Haikalin Ubangiji inda Ubangiji ya ce, “A Urushalima zan sa sunana.” 5 Ya gina wa taurarin sama bagadai a farfajiya biyu ta Haikalin Ubangiji. 6 Ya miƙa ɗansa hadaya ta ƙonawa ya kuma aikata sihiri, ya yi d�ba. Ya yi ma'amala da masu mabiya da mayu. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, ya sa Ubangiji ya yi fushi. 7 Siffar gunkiyan nan Ashtoret wadda ya yi, ya kafa ta a Haikalin da Ubangiji ya ce wa Dawuda da ɗansa Sulemanu, “A cikin wannan Haikali a Urushalima wadda na zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra'ila zan tabbatar da sunana har abada. 8 Ba zan-sa jama'ar Isra'ila su ƙara fita daga ƙasar da na ba kakanninsu ba, idan dai za su kula su aikata dukan abin da na umarce su, su kuma kiyaye dukan dokokin da bawana Musa ya umarce su.” 9 Amma mutanen Yahuza ba su kasa kunne ba. Manassa kuma ya yaudare su, suka aikata mugunta fiye da abin da al'umman da Ubangiji ya hallaka a gaban jama'ar Isra'ila suka aikata. 10 Ubangiji kuwa ya yi magana ta wurin bayinsa annabawa ya ce, 11 “Tun da yake Manassa, Sarkin Yahuza, ya aikata waɗannan abubuwa masu banƙyama, ya kuma aikata mugayen abubuwa fiye da dukan abin da Amoriyawa, waɗanda suka riga shi, suka aikata, ya kuma sa mutanen Yahuza su yi zunubi saboda gumakansa, 12 saboda haka ni Ubangiji Allah na Isra'ila, zan aukar wa Urushalima da mutanen Yahuza da masifa irin wadda duk wanda ya ji labarinta, sai ya kusa suma. 13 Zan gwada Urushalima da magwajin Samariya da kuma ma'aunin gidan Ahab. Zan kuma suɗe Urushalima kamar yadda mutum yakan suɗe akushi sa'an nan ya kifar da shi. 14 Zan jefar da ragowar gādona, in bashe su a hannun abokan gāba, za su zama ganima da abin waso ga dukan abokan gābansu, 15 saboda sun aikata mugunta a gabana, suka tsokane ni in yi fushi tun ranar da kakanninsu suka fito daga Masar har wa yau.” 16 Banda wannan kuma Manassa ya kashe adalai har ya cika Urushalima daga wannan gefe zuwa wancan da jininsu, banda zunubin da ya sa mutanen Yahuza su yi, har suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji. 17 Sauran ayyukan Manassa, da dukan abin da ya aikata, da zunubin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 18 Manassa ya mutu, aka binne shi a lambun gidansa a gonar Uzza. Ɗansa Amon ya gāji gadon sarautarsa.

Sarki Amon na Yahuza

19 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara biyu a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Meshullemet, 'yar Haruz na Yotba. 20 Ya aikata mugun abu a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa, Manassa ya yi. 21 Ya bi halin tsohonsa duka. Ya bauta wa gumakan da tsohonsa ya bauta wa, ya kuma yi musu sujada. 22 Ya rabu da Ubangiji Allah na kakanninsa, bai bi tafarkin Ubangiji ba. 23 Fādawansa kuwa suka ƙulla masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidansa. 24 Amma mutanen ƙasar suka kashe waɗannan da suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiyar. Sai suka naɗa Yosiya ɗan sarki, ya gāji tsohonsa. 25 Sauran ayyukan da Amon ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 26 Aka binne shi a kabarinsa na gonar Uzza. Ɗansa Yosiya ya gāji sarautarsa.

2 Sarakuna 22

Sarki Yosiya na Yahuza

1 Yosiya yana da shekara takwas sa'ad da ya ci sarauta, ya yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yedida, 'yar Adaya na Bozkat. 2 Ya yi abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji. Ya bi dukan halin kakansa, Dawuda, bai kauce dama ko hagu ba.

Yosiya da Littafin Shari'a

3 A shekara ta goma sha takwas ta sarautarsa, sai ya aiki Shafan ɗan Azaliya, wato jikan Meshullam, magatakarda, zuwa Haikalin Ubangiji, ya ce, 4 “Ka tafi wurin Hilkiya babban firist domin a lasafta yawan kuɗin da aka kawo cikin Haikalin Ubangiji, wanda masu tsaron ƙofa suka tattara daga wurin jama'a. 5 A ba da kuɗin a hannun masu lura da ma'aikata waɗanda suke gyaran Haikalin Ubangiji, su kuma su ba waɗanda suke gyaran Haikalin, 6 wato masu sassaƙa, da magina, domin a sayi katako da dutsen da aka haƙo don gyaran Haikalin. 7 Kada a tambaye su yadda suka kashe kuɗin da aka sa a hannunsu, gama su amintattu ne.” 8 Hilkiya babban firist kuwa ya ce wa Shafan magatakarda, “Na iske littafin dokoki a cikin Haikalin Ubangiji.” Hilkiya kuwa ya ba Shafan littafin, shi kuwa ya karanta shi. 9 Sai Shafan magatakarda ya tafi ya faɗa wa sarki cewa, “Baranka ya kwashe kuɗin da ya tarar a Haikali, na kuwa ba masu lura da ma'aikatan Haikalin Ubangiji.” 10 Ya kuma ce wa sarki, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Ya kuwa karanta wa sarki littafin. 11 Sa'ad da sarki ya ji maganar da take cikin littafin dokoki, sai ya kece tufafinsa. 12 Sa'an nan ya umarci Hilkiya firist, da Ahikam ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mikaiya, da Shafan magatakarda, da Asaya baran sarki cewa, 13 “Ku tafi ku yi tambaya ga Ubangiji saboda ni, da jama'a, da dukan mutanen Yahuza a kan maganar littafin nan da aka samo, gama Ubangiji ya yi fushi da muƙwarai saboda kakanninmu domin ba su bi maganar littafin nan ba, har da za su yi dukan abin da aka rubuta mana.” 14 Sai Hilkiya firist, da Ahikam, da Akbor, da Shafan, da Asaya suka tafi wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikwa, wato jikan Harhas, mai tsaron ɗakin da ake ajiye tufafi. A Urushalima take zaune a sabuwar unguwa. Suka kuwa yi magana da ita. 15 Sai ta ce musu, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, a faɗa wa mutumin da ya aiko ku gare ni, 16 ‘Ga shi, zan aukar da masifa a wurin nan, da a mazaunan wurin, bisa ga dukan maganar littafin nan wanda Sarkin Yahuza ya karanta, 17 domin sun rabu da ni, sun ƙona turare ga gumaka don su tsokane ni in yi fushi da aikin hannuwansu. Saboda haka fushina zai ƙuna a kan wurin nan, ba kuwa zai huce ba.’ 18 Amma akan Sarkin Yahuza, wanda ya aiko ku, ku tambayar masa Ubangiji, ku faɗa masa Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘A kan maganar da ka ji, 19 da yake zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gabana sa'ad da ka ji yadda na yi magana gāba da wannan wuri, da kuma mazaunansa, cewa zai zama kufai da la'ana, kai kuwa ka keta tufafinka, ka yi kuka a gabana, hakika na ji kukanka. 20 Domin haka, ba za ka ga hukuncin da yake zuwa a kan Urushalima ba, za a kai ka cikin kabarinka lafiya.’ ” Mutanen kuwa suka mayar wa sarki Yosiya da wannan magana.

2 Sarakuna 23

Gyare-gyaren da Yosiya ya Yi

1 Sarki Yosiya kuwa ya aika, aka tattaro masa dukan dattawan Yahuza da na Urushalima. 2 Sa'an nan ya haura zuwa Haikalin Ubangiji tare da dukan jama'ar Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, da firistoci, da annabawa, da jama'a duka, ƙanana da manya. Sai ya karanta musu dukan maganar littafin alkawarin da aka iske a Haikalin Ubangiji. 3 Sarki ya tsaya kusa da ginshiƙi ya yi alkawari ga Ubangiji, cewa zai bi Ubangiji da zuciya ɗaya, da dukan ransa. Zai kiyaye umarnansa, da farillansa, da dokokinsa, ya bi maganar alkawarin da aka rubuta a littafin. Dukan jama'a kuma suka yi alkawarin. 4 Sa'an nan sarki Yosiya ya umarci Hilkiya, babban firist, da firistoci masu daraja ta biyu, da masu tsaron ƙofa, su fitar da tasoshin da aka yi wa Ba'al, da Ashtoret, da dukan taurarin sama, daga cikin Haikalin Ubangiji. Sai ya ƙone su a bayan Urushalima a saurar Kidron, sa'an nan ya kwashe tokarsu zuwa Betel. 5 Ya kuma tuɓe firistocin gumaka waɗanda sarakunan Yahuza suka naɗa don su ƙona turare a matsafai na kan tuddai a garuruwan Yahuza, da kewayen Urushalima, da firistoci waɗanda suka ƙona turare ga Ba'al, da rana, da wata, da taurari, da dukan rundunan sama. 6 Sai sarki ya fitar da gunkiyan nan Ashtoret, daga cikin Haikalin Ubangiji a Urushalima, ya kai Kidron, ya ƙone ta a ƙoramar Kidron, ta zama toka, ya kuwa watsar da tokar a makabarta. 7 Ya rurrushe ɗakunan karuwai mata da maza da suke a Haikalin Ubangiji, wato wurin da mata suke saƙa labulan gunkiyar. 8 Ya fitar da dukan firistoci daga cikin garuruwan Yahuza, sa'an nan ya lalatar da matsafai na kan tuddai inda firistoci suka ƙona turare, tun daga Geba har zuwa Biyer-sheba. Ya kuma rurrushe matsafai na kan tuddai waɗanda suke a ƙofofin shiga ƙofar Joshuwa, hakimin birnin, waɗanda suke hagu da ƙofar birnin. 9 Duk da haka firistoci matsafai na kan tuddai ba su haura zuwa bagaden Ubangiji a Urushalima ba, amma suka ci abinci marar yisti tare da 'yan'uwansu. 10 Ya kuma lalatar da Tofet, wurin da yake kwarin 'ya'yan Hinnom, don kada kowa ya ƙara miƙa ɗansa ko 'yarsa hadaya ta ƙonawa ga Molek. 11 Ya kawar da dawakan da sarakunan Yahuza suka keɓe wa rana, a ƙofar Haikalin Ubangiji, kusa da shirayin Natan-melek shugaban shirayin da yake cikin farfajiya. Haka kuma ya ƙone karusai waɗanda aka yi wa rana. 12 Ya rurrushe, ya kuma farfasa bagaden da yake bisa rufin benen Ahaz, waɗanda sarakunan Yahuza suka gina, da kuma bagaden da Manassa ya gina a farfajiya biyu ta Haikalin Ubangiji. Sai ya watsar da tokar da ƙurar a rafin Kidron. 13 Ya kuma lalatar da matsafai na kan tuddan da suke gabashin Urushalima, kudu da Dutsen Hallaka, waɗanda Sulemanu Sarkin Isra'ila, ya gina wa Ashtoret gunkiyar Sidoniyawa, da Kemosh gunkin Mowab, da Milkom gunkin Ammonawa. 14 Ya rurrushe ginshiƙai, ya sassare siffofin gumakan, sa'an nan ya rufe wurarensu da ƙasusuwan mutane. 15 Yosiya ya kuma rushe bagaden da yake a Betel, wanda Yerobowam ɗan Nebat ya gina, wanda ya sa mutanen Isra'ila su yi zunubi, tare da tudun, ya farfashe duwatsun, ya niƙe su, sun zama gari, ya kuma ƙone Ashtoret. 16 Da Yosiya ya waiwaya, sai ya ga kaburbura a kan dutse. Ya aika a kwaso ƙasusuwan da suke cikin kaburburan, sai ya ƙone su a bisa bagaden, ya lalatar da shi kamar yadda Ubangiji ya faɗa ta bakin annabi. 17 Ya kuma ce, “Kabarin wane ne wancan da nake gani?” Sai mutanen Betel suka ce masa, “Ai, kabarin annabin Allah ne wanda ya fito daga Yahuza ya yi annabcin waɗannan abubuwan da ka aikata gāba da bagaden Betel.” 18 Sarki kuwa ya ce, “A bar shi yadda yake, kada wani ya taɓa ƙasusuwansa.” Sai suka bar ƙasusuwan annabin da ya zo daga Samariya. 19 Dukan matsafai na kan tuddai da suke a garuruwan Samariya waɗanda sarakunan Isra'ila suka gina, har suka sa Ubangiji ya yi fushi, Yosiya ya watsar da su. Ya yi da su kamar yadda ya yi a Betel. 20 Ya kuma karkashe dukan firistocin matsafai na kan tuddai a bisa bagadan da suke can. Ya ƙone ƙasusuwansu a bisa bagadan. Sa'an nan ya komo Urushalima.

An Kiyaye Idan Ƙetarewa

21 Sarki Yosiya kuwa ya umarci dukan mutane, ya ce, “Ku kiyaye Idin Ƙetarewa ga Ubangiji Allahnku kamar yadda aka rubuta a littafin alkawari.” 22 Gama ba a ƙara kiyaye Idin Ƙetarewa ba tun daga zamanin hakimai waɗanda suka yi hukuncin Isra'ila, ko a zamanin sarakunan Isra'ila da na Yahuza, 23 sai dai a shekara ta goma sha takwas ta sarautar sarki Yosiya an kiyaye Idin Ƙetarewa ɗin nan ga Ubangiji a Urushalima.

Yosiya ya yi Sāke-sāke

24 Yosiya kuma ya kori dukan masu mabiya, da masu maita, da kawunan gidaje, da gumaka, da dukan abubuwa masu banƙyama da ake gani a ƙasar Yahuza, da a Urushalima, don ya sa maganar dokokin da aka rubuta a littafin da Hilkiya firist ya tarar a Haikalin Ubangiji ta kahu. 25 A gabansa, ko bayansa ba wani sarki kamarsa, wanda ya juyo ga Ubangiji da zuciya ɗaya da dukan ransa, da dukan ƙarfinsa domin ya bi dukan dokokin Musa.

Fushin Ubangiji a kan Yahuza

26 Duk da haka Ubangiji bai huce daga fushinsa mai zafi da yake yi da jama'ar Yahuza ba, saboda yawan tsokanar da Manassa ya yi masa. 27 Ubangiji kuwa ya ce, “Zan kawar da jama'ar Yahuza daga gabana kamar yadda na kawar da jama'ar Isra'ila. Zan yi watsi da birnin nan da na zaɓa, wato Urushalima, da Haikalin da na ce sunana zai kasance a wurin.”

Rasuwar Yosiya

28 Sauran ayyukan Yosiya da dukan abin da ya yi, an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 29 A zamaninsa Fir'auna-neko, Sarkin Masar, ya tafi ya tasar wa Sarkin Assuriya da yaƙi a Kogin Yufiretis. Sarki Yosiya kuwa ya yi ƙoƙari ya hana shi wucewa, sa'ad da Fir'auna-neko ya gan shi, sai ya kashe shi a filin yaƙi a Magiddo. 30 Fādawansa kuwa suka ɗauko gawarsa a karusa daga Magiddo, suka kawo Urushalima, suka binne a kabarinsa. Sai jama'ar ƙasa suka naɗa Yehowahaz ɗan Yosiya sarki a matsayin tsohonsa.

Sarki Yehowahaz na Yahuza

31 Yehowahaz yana da shekara ashirin da uku sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Hamutal 'yar Irmiya na Libna. 32 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda kakanninsa suka yi. 33 Fir'auna-neko ya sa shi a kurkuku a Ribla a ƙasar Hamat, don kada ya yi mulki a Urushalima. Ya kuma sa ƙasar ta riƙa ba da gandu, wato haraji, talanti ɗari na azurfa da talanti guda na zinariya. 34 Sai Fir'auna-neko ya sarautar da Eliyakim ɗan Yosiya a matsayin tsohonsa. Ya sāke masa suna ya sa masa suna Yehoyakim. Ya ɗauki Yehowahaz ya tafi da shi Masar, can ya mutu. 35 Yehoyakim yakan ba Fir'auna azurfa da zinariya, ya kuwa sa wa ƙasar haraji don ya sami kuɗin da Fir'auna ya umarta. Ya tilasta wa kowa ya biya azurfa da zinariya bisa ga yadda ya sa masa don ya ba Fir'auna-neko.

Sarki Yehoyakim na Yahuza

36 Yehoyakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara goma sha ɗaya a Urushalima. Sunan tsohuwarsa kuwa Zebida, 'yar Fediya mutumin Ruma. 37 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda dukan kakanninsa suka yi.

2 Sarakuna 24

1 A zamanin Yehoyakim ne Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kawo wa Yahuza yaƙi, Yehoyakim kuwa ya zama baransa har shekara uku daganan kuma ya tayar masa. 2 Ubangiji kuwa ya sa ƙungiyar maharar Kaldiyawa, da ta Suriyawa, da ta Mowabawa, da ta Ammonawa su yi gāba da Yahuza, su hallaka su bisa ga maganar Ubangiji, wadda ya faɗa wa bayinsa annabawa. 3 Hakika haka ya faru ga Yahuza bisa ga umarnin Ubangiji domin a kawar da su daga gaban Ubangiji saboda dukan zunubin Manassa da ya aikata, 4 saboda kuma marasa laifi waɗanda ya kashe, gama ya cika Urushalima da jinin marasa laifi, Ubangiji kuwa ba zai gafarta wa Manassa ba. 5 Sauran ayyukan Yehoyakim da dukan abin da ya yi an rubuta su a littafin tarihin sarakunan Yahuza. 6 Yehoyakim ya rasu. Ɗansa Yekoniya ya gāji gadon sarautarsa. 7 Sarkin Masar kuma bai sāke fitowa daga Masar ba, gama Sarkin Babila ya ƙwace dukan ƙasar da take ta Sarkin Masar, tun daga rafin Masar har zuwa Kogin Yufiretis.

An Kama Sarki Yekoniya da Manya na Yahuza

8 Yekoniya yana da shekara goma sha takwas sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki wata uku a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Nehushta 'yar Elnatan, mutumin Urushalima. 9 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda tsohonsa ya yi. 10 A zamaninsa ne sojojin Nebukadnezzar Sarkin Babila suka zo Urushalima, suka kewaye ta da yaƙi. 11 Nebukadnezzar ya zo birnin lokacin da sojojinsa suka kewaye birnin da yaƙi. 12 Sai Yekoniya Sarkin Yahuza ya ba da kansa ga Sarkin Babila shi da tsohuwarsa, da fādawansa da hakimansa. Sarkin Babila ya kama shi yana da shekara takwas da sarautar, 13 ya kuma kwashe dukan dukiyar da take cikin Haikalin Ubangiji, da dukiyar da take cikin gidan sarki. Sai ya farfashe tasoshin zinariya da suke cikin Haikalin Ubangiji, waɗanda Sulemanu Sarkin Isra'ila, ya yi. Ya aikata abin da Ubangiji ya riga ya faɗa. 14 Nebukadnezzar ya kwashe dukan mutanen Urushalima, da dukan hakimai da dukan jarumawa, da masu sana'a, da maƙera, har sun kai dubu goma (10,000 ). Ba wanda ya ragu sai dai matalautan ƙasar. 15 Ya tafi da Yekoniya a Babila, shi da tsohuwarsa, da fādawansa, da masu maƙami na ƙasar. 16 Sarkin Babila ya kai kamammu Babila, wato jarumawa dubu bakwai (7,000 ), masu sana'a da maƙera dubu ɗaya (1,000 ), dukansu ƙarfafa ne, sun isa zuwa yaƙi. 17 Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya naɗa Mattaniya ɗan'uwan tsohon Yekoniya sarki a maimakon Yekoniya sa'an nan ya ba shi suna Zadakiya.

Sarki Zadakiya na Yahuza

18 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan tsohuwarsa Hamutal, 'yar Irmiya, mutumin Libna. 19 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar yadda Yehoyakim ya yi. 20 Ubangiji kuwa ya husata ƙwarai da mutanen Urushalima da dukan mutanen Yahuza, sai ya kore su daga gabansa. Zadakiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babila.

2 Sarakuna 25

Faɗuwar Urushalima

1 A shekara ta tara ta sarautar Zadakiya a kan rana ta goma ga watan goma, sai Nebukadnezzar Sarkin Babila, tare da sojojinsa, ya kawo wa Urushalima yaƙi. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina mata kagarai. 2 Aka kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Zadakiya. 3 A kan rana ta tara ga watan huɗu, yunwa ta tsananta a birnin gama ba abinci domin mutanen ƙasar. 4 Sai aka huda garun birnin, sarki da mayaƙa suka tsere da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu kusa da gonar sarki, suka bi ta hanyar Araba, ko da yake Kaldiyawa suna kewaye da birnin. 5 Amma sojojin Kaldiyawa suka runtumi sarki suka kamo shi a filayen Yariko. Sojojinsa duka suka watse, suka bar shi. 6 Da suka kama sarkin, sai suka kawo shi wurin Sarkin Babila a Ribla, inda aka yanke masa hukunci. 7 Aka kashe 'ya'yansa maza a idonsa, sa'an nan aka ƙwaƙule masa idanu, aka kuma ɗaure shi da sarƙa, aka kai shi Babila.

Cin Yahuza

8 A shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar Sarkin Babila, a rana ta bakwai ga watan biyar, sai Nebuzaradan, mashawarcin sarki, shugaban sojojinsa kuma, ya shiga Urushalima. 9 Ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gidajen urushalima. Ya ƙone kowane babban gida. 10 Dukan sojojin Kaldiyawa waɗanda suke tare da shugaban, suka rushe garun da yake kewaye da Urushalima. 11 Sai Nebuzaradan shugaban sojojin, ya kwashe sauran mutanen da suka ragu a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran da suka ragu, ya kwashe ya kai su zaman talala. 12 Amma shugaban sojojin ya bar matalautan ƙasar su zama masu gyaran inabi, da masu noma. 13 Sai Kaldiyawa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalansu, da kwatarniyar ruwa na tagullar da yake cikin Haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagullar zuwa Babila. 14 Suka kuma kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da cokula, da tasoshin tagulla da ake amfani da su don hidimar Haikali. 15 Suka kuma kwashe farantan wuta da daruna. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban sojojin ya kwashe. 16 Tagullar da Sulemanu ya yi abubuwan nan da su, wato ginshiƙai biyu, da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna. 17 Tsayin kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne. A kan kowane ginshiƙi akwai dajiyar tagulla, wadda tsayinta ya kai kamu uku. Akwai raga da rumman na tagulla kewaye da dajiyar.

An Kwashe Mutanen Yahuza zuwa Babila

18 Nebuzaradan kuma ya tafi da Seraiya babban firist, da Zafaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofa. 19 Daga cikin birnin kuma ya tafi da wani shugaban sojoji, da 'yan majalisar sarki mutum biyar, da magatakardan shugaban sojoji wanda ya tattara jama'ar ƙasar, da mutum sittin na ƙasar waɗanda aka samu a birnin. 20 Nebuzaradan shugaban sojoji ya kai su wurin Sarkin Babila a Ribla ta ƙasar Hamat. 21 Sarkin Babila kuwa ya kashe su a can. Haka aka kai mutanen Yahuza zuwa zaman talala.

Gedaliya Gwamnan Yahuza

22 A kan sauran waɗanda suka ragu a ƙasar Yahuza, waɗanda Sarkin Babila, Nebukadnezzar, ya bari, ya naɗa musu Gedaliya ɗan Ahikam, wato jikan Shafan, ya zama hakiminsu. 23 Sa'ad da shugabannin mayaƙa su da mayaƙansu suka ji Sarkin Babila ya naɗa Gedaliya ya zama hakimi, sai suka zo tare da mutanensu wurin Gedaliya a Mizfa, wato su Isma'ilu ɗan Netaniya, da Yohenan ɗan Kareya, da Seraiya ɗan Tanhumet, mutumin Netofa, da Yazaniya mutumin Ma'aka. 24 Sai Gedaliya ya rantse musu, su da mutanensu, cewa kada su ji tsoron barorin Kaldiyawa, su zauna a ƙasar, su bauta wa Sarkin Babila, haka zai fi zamar musu alheri. 25 Amma a watan bakwai, sai Isma'ilu ɗan Netaniya, wato jikan Elishama, daga gidan sararta, ya zo tare da mutum goma ya fāda wa Gedaliya, ya kashe shi tare da Yahudawa da Kaldiyawa da suke tare da shi a Mizfa. 26 Sai dukan mutane, manya da ƙanana, da shugabannin mayaƙa, suka tashi, suka gudu zuwa Masar, gama sun ji tsoron Kaldiyawa.

An fitar da Yekoniya daga Kurkuku

27 A rana ta ashirin da bakwai ga watan goma sha biyu, a shekara ta talatin da bakwai ta ɗaurin Yekoniya Sarkin Yahuda, sai Ewil-merodak da ya zama Sarkin Babila ya yi wa Yekoniya alheri, ya sake shi a shekarar da ya ci sarautar. 28 Ya yi masa magana mai kyau, ya kuma ba shi matsayi fiye da sarakunan da suke tare da shi a Babila. 29 Sai Yekoniya ya tuɓe tufafinsa na kurkuku. Kowace rana kuwa yakan ci abinci a teburin sarki har muddin ransa. 30 Sarki kuma ya yanka masa kuɗin da za a dinga ba shi, kowace rana muddin ransa.

1 Tarihi 1

Zuriyar Adamu

1 Adamu ya haifi Shitu, Shitu ya haifi Enosh, 2 Enosh ya haifi Kenan, Kenan ya haifi Mahalalel, Mahalalel ya haifi Yared, 3 Yared ya haifi Anuhu, Anuhu ya haifi Metusela, Metusela ya haifi Lamek. 4 Lamek ya haifi Nuhu, Nuhu ya haifi Shem, da Ham, da Yafet.

Zuriyar 'Ya'yan Nuhu

5 'Ya'yan Yafet, maza ke nan, Gomer, da Magog, da Madai, da Yawan, da Tubal, da Meshek, da Tiras. 6 'Ya'yan Gomer, maza, su ne Ashkenaz, da Rifat, da Togarma. 7 'Ya'yan Yawan, maza, su ne Elisha, da Tarshish, da Kittim, da Rodanim. 8 'Ya'yan Ham, maza, su ne Kush, da Mizrayim, da Fut, da Kan'ana. 9 'Ya'yan Kush, maza, su ne Seba, da Hawila, da Sabta, da Ra'ama, da Sabteka. 'Ya'yan Ra'ama, maza, su ne Sheba da Dedan. 10 Kush shi ne mahaifin Lamirudu wanda shi ne ya fara ƙasaita a duniya. 11 Mizrayim shi ne mahaifin jama'ar Ludawa, da Anamawa, da Lehabawa, da Naftuhawa, 12 da Fatrusawa, da Kasluhawa tushen Filistiyawa ke nan, da Kaftorawa. 13 Kan'ana shi ne mahaifin Sidon ɗan farinsa, da Het, 14 da Yebusiyawa, da Amoriyawa, da Girgashiyawa, 15 da Hiwiyawa, da Arkiyawa, da Siniyawa, 16 da Arwadiyawa, da Zemariyawa, da Hamatiyawa.

Zuriyar Shem

17 'Ya'yan Shem, maza, su ne Elam, da Asshur, da Arfakshad, da Lud, da Aram, da Uz, da Hul, da Geter, da Meshek. 18 Arfakshad shi ne mahaifin Shela, Shela kuma shi ne mahaifin Eber. 19 'Ya'ya biyu maza ne aka haifa wa Eber. Sunan ɗayan Feleg, saboda a lokacinsa ne aka karkasa duniya, sunan ɗan'uwansa kuwa Yokatan. 20 Yokatan shi ne mahaifin Almoda, da Shelef, da Hazarmawet, da Yera, 21 da Adoniram, da Uzal, da Dikla, 22 da Ebal, da Abimayel, da Sheba, 23 da Ofir, da Hawila, da Yobab. Waɗannan duka su ne 'ya'yan Yokatan, maza. 24 Shem ya haifi Arfakshad, Arfakshad ya haifi Shela, 25 Shela ya haifi Eber, Eber ya haifi Feleg, Feleg ya haifi Reyu, 26 Reyu ya haifi Serug, Serug ya haifi Nahor, Nahor ya haifi Tera, 27 Tera ya haifi Abram, wato Ibrahim ke nan.

Zuriyar Isma'ilu da Ketura

28 'Ya'yan Ibrahim, maza, su ne Ishaku da Isma'ilu. 29 Ga zuriyarsu. Nabayot shi ne ɗan farin Isma'ilu, sa'an nan sai Kedar, da Abdeyel, da Mibsam, 30 da Mishma, da Duma, da Massa, da Hadad, da Tema, 31 da Yetur, da Nafish, da Kedema. Waɗannan su ne 'ya'yan Isma'ilu, maza. 32 'Ya'ya maza na Ketura, wato ƙwarƙwarar Ibrahim, su ne Zimran, da Yokshan, da Medan, da Madayana, da Yisbak, da Shuwa. 'Ya'yan Yokshan, maza, su ne Sheba, da Dedan. 33 'Ya'yan Madayana, maza, su ne Efa, da Efer, da Hanok, da Abida, da Eldaya. Waɗannan duka su ne 'ya'yan Ketura, maza.

Zuriyar Isuwa

34 Ibrahim shi ne mahaifin Ishaku. 'Ya'yan Ishaku, maza, su ne Isuwa da Isra'ila. 35 'Ya'yan Isuwa, maza, su ne Elifaz, da Reyuwel, da Yewush, da Yalam da Kora. 36 'Ya'yan Elifaz, maza, su ne Teman, da Omar, da Zeho, da Gatam, da Kenaz, da Tima, da Amalek. 37 'Ya'yan Reyuwel, maza kuwa, su ne Nahat, da Zera, da Shamma, da Mizza. 38 'Ya'yan Seyir, maza kuma, su ne Lotan, da Shobal, da Zibeyon, da Ana, da Dishon, da Ezer, da kuma Dishan. 39 'Ya'yan Lotan, maza, su ne Hori, da Hemam. Timna ce 'yar'uwar Lotan. 40 'Ya'yan Shobal, maza, su ne Alwan, da Manahat, da Ebal, da Sheho, da Onam. 'Ya'yan Zibeyon, maza su ne Aiya da Ana. 41 Dishon shi ne ɗan Ana. 'Ya'yan Dishon, maza kuwa, su ne Hemdan, da Eshban, da Yitran, da Keran. 42 'Ya'yan Ezer, maza, su ne Bilhan, da Zayawan, da Akan. 'Ya'yan Dishan, maza, su ne Uz da Aran. 43-50 Waɗannan su ne sarakunan da suka yi sarauta a ƙasar Edom kafin wani Sarkin Isra'ila ya ci sarauta. Bela ɗan Beyor, sunan birninsa kuwa Dinhaba Yobab ɗan Zera na Bozara Husham na ƙasar Teman Hadad ɗan Bedad na Awit, wanda ya kori Madayanawa a filin Mowab Samla na Masrek Shawul na Rehobot wadda take bakin Kogin Yufiretis Ba'al-hanan ɗan Akbor Hadad na Fau, sunan matarsa kuma Mehetabel 'yar Matred, wato jikar Mezahab 51 Hadad kuwa ya rasu. Sarakunan Edom su ne Timna, da Alwa, da Yetet, 52 da Oholibama, da Ila, da Finon, 53 da Kenaz, da Teman, da Mibzar, 54 da Magdiyel, da Iram.

1 Tarihi 2

'Ya'yan Isra'ila

1 Waɗannan su ne 'ya'yan Isra'ila, maza, Ra'ubainu, da Saminu, da Lawi, da Yahuza, da Issaka, da Zabaluna, 2 da Dan, da Yusufu, da Biliyaminu, da Naftali, da Gad, da Ashiru.

Zuriya Yahuza

3 'Ya'yan Yahuza, maza, su ne Er, da Onan, da Shela. Waɗannan uku Batshuwa Bakan'aniya, ita ce ta haifa masa su. Amma Er, ɗan farin Yahuza, mugu ne a gaban Ubangiji, don haka Ubangiji ya kashe shi. 4 Surukarsa Tamar, matar ɗansa kuma ta haifa masa Feresa da Zera. Yahuza yana da 'ya'ya maza biyar. 5 'Ya'yan Feresa, maza kuwa, su ne Hesruna da Hamul. 6 'Ya'yan Zera, maza, su ne Zabdi da Etan, da Heman, da Kalkol, da Darda. Su biyar ke nan. 7 Karmi shi ne mahaifin Akan wanda ya jawo wa Isra'ila wahala a kan abin da aka haramta. 8 Etan yana da ɗa guda ɗaya, shi ne Azariya. 9 'Ya'yan Hesruna, maza, waɗanda aka haifa masa, su ne Yerameyel, da Arama, da kuma Kalibu. 10 Arama shi ne mahaifin Amminadab. Amminadab kuma shi ne mahaifin Nashon, shugaban 'ya'yan Yahuza. 11 Nashon shi ne mahaifin Salmon. Salmon kuwa shi ne mahaifin Bo'aza. 12 Bo'aza kuma shi ne mahaifin Obida. Obida shi ne mahaifin Yesse. 13 Yesse shi ne mahaifin Eliyab ɗan farinsa, sa'an nan sai Abinadab da Shimeya, 14 da Netanel, da Raddai, 15 da Ozem, da Dawuda. Su 'ya'ya maza bakwai ke nan. 16 'Yan 'yan'uwansu mata kuwa su ne Zeruya da Abigail. 'Ya'yan Zeruya, maza, su ne Abishai, da Yowab, da Asahel, su uku ke nan. 17 Abigail ta haifi Amasa. Mahaifin Amasa shi ne Yeter daga zuriyar Isma'ilu. 18 Azuba, matar Kalibu ɗan Hesruna ta haifa masa 'ya'ya maza. Matarsa Yeriyot kuma ta haifi 'ya'ya maza, su ne Yesher, da Shobab, da Ardon. 19 Sa'ad da Azuba ta rasu sai Kalibu ya auri Efrata wadda ta haifa masa Hur. 20 Hur shi ne mahaifin Uri, Uri kuwa shi ne mahaifin Bezalel. 21 Bayan haka sai Hesruna ya shiga wurin 'yar Makir mahaifin Gileyad, wadda ya aura sa'ad da yake da shekara sittin da haihuwa. Ta haifa masa Segub. 22 Segub shi ne mahaifin Yayir wanda yake da birane ashirin da uku a ƙasar Gileyad. 23 Amma sai Geshur da Aram suka ƙwace garuruwan Hawwotyayir ɗin daga gare su, har da Kenat da ƙauyukanta, garuruwa sittin. Duk waɗannan su ne zuriyar Makir mahaifin Gileyad. 24 Bayan rasuwar Hesruna, Abaija, matarsa, ta haifa masa Ashur, mahaifin Tekowa. 25 'Ya'yan Yerameyel ɗan farin Hesruna, su ne Arama ɗan fari, sa'an nan Buna, da Oren, da Ozem, da Ahaija. 26 Sai Yerameyel ya auro wata mace, sunanta Atara. Ita ce mahaifiyar Onam. 27 'Ya'yan Arama, ɗan farin Yerameyel, su ne Ma'az, da Yamin, da Eker. 28 'Ya'yan Onam, maza, su ne Shammai da Yada. 'Ya'yan Shammai, maza, su ne Nadab da Abishur. 29 Sunan matar Abishur Abihail, ta haifa masa Aban da Molid. 30 'Ya'yan Nadab, maza, su ne Seled da Affayim, amma Seled ya rasu bai bar 'ya'ya ba. 31 Ɗan Affayim shi ne Ishi. Ɗan Ishi kuwa shi ne Sheshan. Ɗan Sheshan shi ne Alai. 32 'Ya'yan Yada, maza, ɗan'uwan Shammai, su ne Yeter da Jonatan. Amma Yeter ya rasu bai bar 'ya'ya ba. 33 'Ya'yan Jonatan su ne Felet da Zaza. Waɗannan su ne zuriyar Yerameyel. 34 Sheshan ba shi da 'ya'ya maza, sai dai 'ya'ya mata. Amma yana da wani bara Bamasare mai suna Yarha. 35 Sai Sheshan ya aurar wa Yarha baransa da 'yarsa, ita kuwa ta haifar masa Attai. 36 Attai shi ne mahaifin Natan, Natan kuma shi ne mahaifin Zabad. 37 Zabad kuwa shi ne mahaifin Eflal, Eflal shi ne ya haifi Obida. 38 Obida shi ne mahaifin Yehu, Yehu kuma shi ne mahaifin Azariya. 39 Azariya shi ne mahaifin Helez, Helez shi ne mahaifin Eleyasa. 40 Eleyasa shi ne mahaifin Sisamai, Sisamai shi ne mahaifin Shallum. 41 Shallum shi ne mahaifin Yekamiya, Yekamiya shi ne mahaifin Elishama. 42 Ɗan Kalibu, ɗan'uwan Yerameyel, shi ne Mesha ɗan farinsa wanda ya haifi Zif. Zif ya haifi Maresha wanda ya haifi Hebron. 43 'Ya'yan Hebron, maza, su ne Kora, da Taffuwa, da Rekem, da Shema. 44 Shema shi ne mahaifin Raham wanda ya kafa Yorkeyam. Rekem kuwa shi ne mahaifin Shammai. 45 Shammai shi ne mahaifin Mayon, Mayon kuwa shi ne mahaifin Bet-zur. 46 Efra ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Haran, da Moza, da Gazez. Haran shi ne mahaifin Gazez. 47 'Ya'yan Yadai, maza, su ne Regem, da Yotam, da Geshan, da Felet, da Efa, da Sha'af. 48 Ma'aka, ƙwarƙwarar Kalibu, ta haifi Sheber da Tirhana. 49 Ta kuma haifi Sha'af mahaifin Madmanna, da Shewa mahaifin Makbena, da mahaifin Gibeya. 'Yar Kalibu ita ce Aksa. 50 Waɗannan su ne zuriyar Kalibu, maza. 'Ya'yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, su ne Shobal wanda ya kafa Kiriyat-yeyarim, 51 da Salma, shi kuwa ya kafa Baitalami, da Haref ɗansa kuma wanda ya kafa Bet-gader. 52 Shobal yana da waɗansu 'ya'ya maza, su ne Rewaiya da wanda yake kakan rabin Manahatiyawa, 53 da iyalan da suke a Kiriyat-yeyarim, da na Itiriyawa, da na Futiyawa, da na Shumatiyawa, da na Mishraiyawa. Daga waɗannan ne Zoratiyawa da Eshtawoliyawa suka fito. 54 Salma, wanda ya kafa Baitalami, shi ne kakan mutanen Netofa, da na Atarot-bet-yowab, da rabin Manahatiyawa, da Zoratiyawa. 55 Iyalan gwanayen rubutu waɗanda suka zauna a Yabez, su ne Tiratiyawa, da Shimeyatiyawa, da Sukatiyawa. Su ne Keniyawa na Hammat, Hammat kuwa shi ne mahaifin mutanen Rekab.

1 Tarihi 3

'Ya'yan Dawuda

1-3 Waɗannan su ne 'ya'yan Dawuda, maza, waɗanda aka haifa masa a Hebron. Amnon wanda Ahinowam Bayezreyeliya ta haifa masa. Kileyab wanda Abigail Bakarmeliya ta haifa masa. Absalom ɗan Ma'aka 'yar Talmai, Sarkin Geshur. Adonaija ɗan Haggit. Shefatiya wanda Abital ta haifa. Itireyam wanda Egla ta haifa. 4 Dukansu shida an haife su ne a Hebron inda ya yi sarauta shekara bakwai da wata shida. Ya yi sarauta a Urushalima shekara talatin da uku. 5 Waɗanda aka haifa masa a Urushalima, su ne Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu, su huɗu ke nan waɗanda Bat-sheba 'yar Ammiyel ta haifa masa. 6 Yana da waɗansu 'ya'ya kuma, su ne Ibhar, da Elishuwa da Elifelet, 7 da Noga, da Nefeg, da Yafiya, 8 da Elishama, da Eliyada, da kuma Elifelet, su tara ke nan. 9 Waɗannan duka su ne 'ya'yan Dawuda, maza, banda 'ya'yan ƙwaraƙwarai. Tamar ita ce 'yar'uwarsu.

Zuriyar Sulemanu

10 Waɗannan su ne zuriyar Sulemanu, daga Rehobowam, sai Abaija, da Asa, da Yehoshafat, 11 da Yoram, da Ahaziya, da Yowash, 12 da Amaziya, da Azariya, da Yotam, 13 da Ahaz, da Hezekiya da Manassa, 14 da Amon, da Yosiya. 15 'Ya'yan Yosiya, maza, su ne Yohenan ɗan farinsa, na biyu shi ne Eliyakim, na uku shi ne Zadakiya, na huɗu shi ne Yehowahaz, 16 Eliyakim yana da 'ya'ya biyu maza, su ne Yekoniya, da Zadakiya. 17 'Ya'yan Yekoniya wanda aka kama, su ne Sheyaltiyel, 18 da Malkiram, da Fedaiya, da Shenazzar, da Yekamiya, da Hoshama, da Nedabiya. 19 Fedaiya yana da 'ya'ya biyu maza, su ne Zarubabel da Shimai. 'Ya'yan Zarubabel, maza, su ne Meshullam, da Hananiya, da Shelomit 'yar'uwarsu, 20 da Hashuba, da Ohel, da Berikiya, da Hasadiya, da Yushab-hesed, su biyar ke nan. 21 'Ya'yan Hananiya, maza, su ne Felatiya, da Yeshaya, da 'ya'yan Refaya, maza, da 'ya'yan Arnan, maza, da 'ya'yan Obadiya, maza, da 'ya'yan Shekaniya, maza. 22 Ɗan Shekaniya shi ne Shemaiya. 'Ya'yan Shemaiya, maza, su ne Hattush, da Igal, da Bariya da Neyariya, da Shafat, su shida ke nan. 23 'Ya'yan Neyariya, maza, su ne Eliyehoyenai, da Hezekiya, da Azrikam, su uku ne nan. 24 'Ya'yan Eliyehoyenai, maza, su ne Hodawiya, da Eliyashib, da Felaya, da Akkub, da Yohenan, da Dalaya, da Anani, su bakwai ke nan.

1 Tarihi 4

Zuriyar Yahuza

1 'Ya'yan Yahuza, maza, su ne Feresa, da Hesruna, da Karmi, da Hur, da Shobal. 2 Rewaiya ɗan Shobal, shi ne mahaifin Yahat. Yahat shi ya haifi Ahumai, da Lahad. Waɗannan su ne iyalin Zoratiyawa. 3 Waɗannan kuma su ne 'ya'yan Itam, Yezreyel, da Ishma, da Idbasha, da 'ya ɗaya, ita ce Hazzelelfoni. 4 Feniyel shi ne mahaifin Gedor, Ezer kuwa shi ne mahaifin Husha. Waɗannan su ne 'ya'yan Hur, maza, wato ɗan farin Efrata, zuriyarsa ne suka kafa Baitalami. 5 Ashur, wanda ya kafa Tekowa, yana da mata biyu, su ne Hela, da Nayara. 6 Nayara ta haifa masa Ahuzzam, da Hefer, da Temeni, da Hayahashtari. Waɗannan su ne 'ya'yan Nayara, maza. 7 'Ya'yan Hela, maza, su ne Zeret, da Izhara, da Etnan. 8 Hakkoz shi ne mahaifin Anub, da Zobeba, shi ne kuma kakan iyalin da suka fito daga zuriyar Aharhel ɗan Harum. 9 Yabez ya fi sauran 'yan'uwansa kwarjini saboda haka mahaifiyarsa ta sa masa suna Yabez, wato da wahala ta haife shi. 10 Yabez ya roƙi Allah na Isra'ila, ya ce, “Ka sa mini albarka, ka faɗaɗa kan iyakata, hannunka kuma ya kasance tare da ni, ka kuma kiyaye ni daga abin da zai cuce ni.” Allah kuwa ya biya masa bukatarsa. 11 Kalibu ɗan'uwan Shuwa, shi ne mahaifin Mehir wanda ya haifi Eshton. 12 Eshton kuwa shi ne ya haifi Bet-rafa, da Faseya, da Tehinna wanda ya kafa birnin Ir-nahash, zuriyar waɗannan mutane kuwa su suka zauna a Reka. 13 'Ya'yan Kenaz, maza, su ne Otniyel da Seraiya. Yana kuma da waɗansu 'ya'ya maza, su ne Hatata da Meyonotai. 14 Meyonotai kuwa shi ne mahaifin Ofra. Seraiya shi ne ya haifi Yowab, Yowab ya kafa kwarin Ge-harashim, saboda su masu sana'a ne. 15 'Ya'yan Kalibu, maza, ɗan Yefunne, su ne Airu, da Ila, da Na'am. Ila shi ya haifi Kenaz. 16 'Ya'yan Yehallelel, maza, su ne Zif, da Zifa, da Tiriya, da Asarel. 17-18 'Ya'yan Ezra, maza, su ne Yeter, da Mered, da Efer, da Yalon. Bitiya 'yar Fir'auna, wadda Mered ya aura, ta haifi waɗannan, Maryamu, da Shammai, da Ishaba wanda ya haifi Eshtemowa. Mered kuma ya auri wata daga kabilar Yahuza, ta haifi Yered wanda ya kafa garin Gedor. Eber kuma ya kafa garin Soko, Yekutiyel kuwa ya kafa garin Zanowa. 19 'Ya'ya maza na matar Hodiya 'yar'uwar Naham, su ne suka zama kakannin Kaila, Bagarme, da Eshtemowa da yake zaune a Ma'aka. 20 'Ya'yan Shimon, maza, su ne Amnon, da Rinna, da Ben-hanan, da Tilon. 'Ya'yan Ishi, maza kuwa, su ne Zohet da Ben-zohet. 21 'Ya'yan Shela, maza, ɗan Yahuza, su ne Er wanda ya kafa garin Leka, da La'ada wanda ya kafa garin Maresha, da iyalan gidan masu aikin lilin da suke zaune a Bet-ashbeya, 22 da Yokim, da mutanen da suke zaune a Kozeba, da Yowash, da Saraf, waɗanda suka yi sarauta a Mowab, sa'an nan suka zauna a Baitalami. (Waɗannan labaru na tun dā ne.) 23 Su ne maginan tukwane, waɗanda suke zaune a Netayim da Gedera. Sun zauna tare da sarki don su yi masa aiki.

Zuriyar Saminu

24 'Ya'yan Saminu, maza, su ne Yemuwel, da Yamin, da Yakin, da Zohar, da Shawul, 25 da Shallum ɗansa, da Mibsam j�kansa, da Mishma j�kan ɗansa. 26 'Ya'yan Mishma, maza, su ne Hammuwel, da Zakkur, da Shimai. 27 Shimai yana da 'ya'ya maza goma sha shida, da 'ya'ya mata shida, amma 'yan'uwansa ba su da 'ya'ya da yawa kamarsa. Iyalin Saminu ba su kai yawan na Yahuza ba. 28 Suka zauna a waɗannan garuruwa, wato Biyer-sheba, da Molada, da Hazar-shuwal, 29 da Bilha, da Ezem, da Eltola, 30 da Betuwel, da Horma, da Ziklag, 31 da Bet-markabot, da Hazarsusa, da Bet-biri, da Shayarim. Waɗannan su ne biranensu tun kafin Dawuda ya yi sarauta. kuwa zauna a waɗansu wurare guda biyar, wato Itam, da Ayin, da Rimmon, da Token, da Ashan, da ƙauyukan da suke kewaye, har zuwa kudu maso gabas da garin Ba'al. Ga lissafin iyalansu da wuraren da suka zauna. 34-37 Meshobab, da Yamlek, da Yosha ɗan Amaziya, Yowel, da Yehu ɗan Yoshibiya, wato j�kan Seraiya, ɗan Asiyel, Eliyehoyenai, da Ya'akoba, da Yeshohaya, da Asaya, da Adiyel, da Yesimiyel, da Benaiya, Ziza ɗan Shifi, wato j�kan Allon, zuriyar Yedaiya, da Shimri ɗan Shemaiya. 38 Waɗannan da aka jera sunayensu, su ne shugabannin iyalansu da gidajen kakanninsu. Sun ƙaru ƙwarai. 39 Suka yi tafiya har zuwa mashigin Gedor, zuwa gabashin kwarin don nema wa garkunansu makiyaya. 40 A can suka sami makiyaya mai kyau mai dausayi. Ƙasar kuwa tana da faɗi, babu fitina, sai salama, gama mazaunan wurin a dā Hamawa ne. 41 Waɗannan da aka lasafta sunayensu, su ne suka zo a kwanakin Hezekiya Sarkin Yahuza, suka fāɗa wa alfarwai da bukkoki waɗanda suka tarar a can, suka hallaka su sarai, sa'an nan suka maye wurinsu saboda akwai makiyaya domin garkunansu a wurin. 42 Waɗansu daga cikinsu, mutum ɗari biyar daga zuriyar Saminu, suka tafi wajen gabashin Edom. Waɗanda suka shugabance su kuwa, su ne 'ya'yan Ishi, wato Felatiya, da Neyariya, da Refaya, da Uzziyel. 43 A can suka karkashe sauran Amalekawan da suka ragu, sa'an nan suka zauna a can har wa yau.

1 Tarihi 5

Zuriyar Ra'ubainu

1 Ra'ubainu shi ne ɗan farin Isra'ila, amma saboda ya ƙazantar da gadon mahaifinsa aka ba 'ya'yan Yusufu, maza, ɗan Isra'ila, gādonsa na ɗan fari. Don haka ba a lasafta shi a kan matsayin ɗan fari ba. 2 Ko da yake Yahuza ya rinjayi 'yan'uwansa, har daga gare shi aka sami shugaba, duk da haka matsayin ɗan farin na Yusufu ne. 3 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, wato ɗan farin Isra'ila, su ne Hanok, da Fallu, da Hesruna, da Karmi. 4 'Ya'yan Yowel, maza, su ne Shemaiya, da Gog, da Shimai, 5 da Mika, da Rewaiya, da Ba'al, 6 da Biyera wanda Tiglat-filesar Sarkin Assuriya ya kai bauta. Shi ne shugaban Ra'ubainawa. 7 Danginsa bisa ga iyalansu da asalinsu a zamaninsu, su ne sarki Yehiyel, da Zakariya, 8 da Bela ɗan Azaz, wato j�kan Shema, ɗan Yowel, wanda ya zauna a Arower har zuwa Nebo da Ba'al-meyon. 9 Ya kuma zauna wajen gabas, har zuwa goshin jejin da yake wajen Kogin Yufiretis, saboda shanunsu sun ƙaru a ƙasar Gileyad. 10 Zuriyar Ra'ubainu suka yi yaƙi da Hagarawa a kwanakin Saul. Suka ci Hagarawa, saboda haka suka zauna a ƙasar da take gabashin Gileyad.

Zuriyar Gad

11 'Ya'yan Gad, maza, suka zauna a ƙasar Bashan, daura da Ra'ubainawa har zuwa Salka. 12 Yowel ne sarki, Shafam kuwa shi ne na biyun, da Yanai, da Shafat, su ne tushen Bashan. 13 Danginsu bisa ga gidajen kakanninsu, su ne Maikel, da Meshullam, da Sheba, da Yorai, da Jakan, da Ziya, da Eber, su bakwai ke nan. 14 Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Abihail ɗan Huri. Ga yadda kakanninsu suke, wato Abihail, ɗan Huri ɗan Yarowa, ɗan Gileyad, ɗan Maikel, ɗan Yeshishai, ɗan Yado, ɗan Buz. 15 Ahi ɗan Abdiyel, wato j�kan Guni, shi ne shugaban gidan kakanninsu. 16 Suka zauna a Gileyad, da Bashan, da garuruwanta, da dukan iyakar makiyayar Sharon. 17 (An rubuta waɗannan duka bisa ga asalinsu a zamanin Yotam, Sarkin Yahuza, da Yerobowam Sarkin Isra'ila.)

Tarihin Kabilai Biyu da Rabi

18 'Ya'yan Ra'ubainu, maza, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa suna da jarumawa masu riƙon garkuwa da takobi, masu harbi kuma da baka. Gwanayen yaƙi ne, su dubu arba'in da huɗu, da ɗari bakwai da sittin ne (44,760 ). 19 Suka yi yaƙi da Hagarawa, da Yetur, da Nafish, da Nodab. 20 Aka taimake su yin yaƙi da abokan gābansu, sai aka ba da Hagarawa da duk waɗanda suke tare da su a hannunsu, saboda suka yi roƙo ga Allah a cikin yaƙin, Allah kuwa ya amsa musu roƙonsu saboda sun dogara gare shi. 21 Sai suka kwashe dabbobinsu, raƙuma dubu hamsin (50,000 ), da tumaki dubu ɗari biyu da dubu hamsin (250,000 ), da jakuna dubu biyu (2,000 ), da kuma mutane dubu ɗari (100,000 ). 22 Aka karkashe mutane da yawa, domin yaƙin na Allah ne. Sai suka gāje wurin zamansu, har lokacin da aka kai su bauta. 23 Mutanen rabin kabilar Manassa suna da yawa, sun zauna a ƙasar, daga Bashan har zuwa Ba'al-harmon, da Senir, da Dutsen Harmon. 24 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu, Efer, da Ishi, da Eliyel, da Azriyel, da Irmiya, da Hodawiya, da Yadiyel. Su jarumawa ne na gaske, masu suna, su ne shugabannin gidajen kakanninsu. 25 Amma mutanen suka yi rashin gaskiya ga Allah na kakanninsu, suka bi gumakan mutanen ƙasar, waɗanda Allah ya hallaka a gabansu. 26 Don haka Allah na Isra'ila ya zuga Ful, Sarkin Assuriya, wato Tiglat-filesar, ya zo ya kwashe su, ya kai su bauta, wato su Ra'ubainawa, da Gadawa, da rabin kabilar Manassa. Ya kai su Hala, da Habor, da Hara, har zuwa kogin Gozan, can suke har yau.

1 Tarihi 6

Zuriyar Manyan Firistoci

1 'Ya'yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari. 2 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel. 3 'Ya'yan Amram kuwa, su ne Haruna, da Musa, da Maryamu. 'Ya'yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar. 4 Zuriyar Ele'azara daga tsara zuwa tsara, su ne Finehas, da Abishuwa, 5 da Bukki, da Uzzi, 6 da Zarahiya, da Merayot, 7 da Amariya, da Ahitub, 8 da Zadok, da Ahimawaz, 9 da Azariya, da Yohenan, 10 da Azariya wanda ya yi hidimar firist a Haikalin da Sulemanu ya gina a Urushalima. 11 Ga Amariya kuma da Ahitub, 12 da Zakok, da Meshullam, 13 da Hilkiya, da Azariya, 14 da Seraiya, da Yehozadak. 15 Sarki Nebukadnezzar ya kama Yehozadak, ya tafi da shi tare da sauran jama'a zuwa zaman talala, sa'ad da Ubangiji ya ba da su a hannun Nebukadnezzar don su yi zaman talala.

Sauran Zuriyar Lawi

16 'Ya'yan Lawi, maza, su ne Gershon, da Kohat, da Merari. 17 Waɗannan su ne sunayen 'ya'yan Gershon, maza, Libni da Shimai. 18 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel. 19 'Ya'yan Merari, maza kuwa, su ne Mali da Mushi. Waɗannan su ne iyalan Lawiyawa bisa ga gidajen kakanninsu. 20 Zuriyar Gershon bi da bi, su ne Libni, da Yahat, da Zimma, 21 da Yowa, da Iddo, da Zera, da Yewaterai. 22 Zuriyar Kohat bi da bi, su ne Izhara, da Kora, da Assir, 23 da Elkana, da Ebiyasaf, da Assir, 24 da Tahat, da Uriyel, da Azariya, da Shawul. 25 'Ya'yan Elkana, maza, su ne Amasai da Ahimot. 26 Zuriyar Ahimot bi da bi, su ne Elkana, da Zofai, da Nahat, 27 da Eliyab, da Yeroham, da Elkana. 28 'Ya'yan Sama'ila, maza, su ne Yowel ɗan farinsa, na biyun shi ne Abaija. 29 Zuriyar Merari bi da bi, su ne Mali, da Libni, da Shimai, da Uzza, 30 da Shimeya, da Haggiya, da Asaya.

Masu Bushe-bushe a Haikali da Dawuda ya Zaɓa

31 Waɗannan su ne waɗanda Dawuda ya sa su su zama mawaƙa a Haikalin Ubangiji, sa'ad da aka kawo akwatin alkawari a cikin Haikalin. 32 Suka yi ta raira waƙoƙi a gaban wurin zama na alfarwa ta taruwa tun kafin Sulemanu ya gina Haikalin Ubangiji a Urushalima. Suka yi hidima bisa ga matsayinsu ta yadda aka tsara. 33 Waɗannan su ne waɗanda suka yi ta raira waƙoƙin, su da 'ya'yansu maza. Daga iyalin Kohat, Heman shi ne shugaban ƙungiyar farko ta mawaƙa, shi ɗan Yowel ne, ɗan Sama'ila, 34 ɗan Elkana, ɗan Yeroham, ɗan Eliyab, ɗan Mahat, 35 ɗan Zafai, ɗan Elkana, ɗan Mahat, ɗan Amasai, 36 ɗan Elkana, ɗan Shawul, ɗan Azariya, ɗan Uriyel, 37 ɗan Tahat, ɗan Assir, ɗan Ebiyasaf, ɗan Kora, 38 ɗan Izhara, ɗan Kohat, ɗan Lawi, ɗan Isra'ila. 39 Asaf kuma shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta biyu. Shi ɗan Berikiya ne, ɗan Shimeya, 40 ɗan Maikel, ɗan Ba'aseya, ɗan Malkiya, 41 ɗan Yewaterai, ɗan Zera, ɗan Iddo, 42 ɗan Yowa, ɗan Zimma, ɗan Shimai, 43 ɗan Yahat, ɗan Gershon, ɗan Lawi. 44 Etan na zuriyar Merari, shi ne shugaban ƙungiyar mawaƙa ta uku, asalinsa shi ɗan Kishi ne, ɗan Abdi, ɗan Malluki, 45 ɗan Hashabiya, ɗan Amaziya, ɗan Hilkiya, 46 ɗan Amzi, ɗan Bani, ɗan Shemer, 47 ɗan Mali, ɗan Mushi, ɗan Merari, ɗan Lawi. 48 Aka sa 'yan'uwansu, Lawiyawa, su yi dukan hidimomi a cikin Haikalin Ubangiji.

Zuriyar Haruna

49 Amma Haruna da 'ya'yansa maza suka miƙa hadayu a kan bagaden hadaya ta ƙonawa, da kan bagaden ƙona turare, domin dukan aikin Wuri Mafi Tsarki, da kuma yin kafara domin Isra'ila bisa ga dukan abin da Musa, bawan Allah, ya umarta. 50 Waɗannan su ne zuriyar Haruna, maza, bi da bi, Ele'azara, da Finehas, da Abishuwa, 51 da Bukki, da Uzzi, da Zerahiya, 52 da Merayot, da Amariya, da Ahitub, 53 da Zadok da Ahimawaz.

Inda Zuriyar Haruna suka Zauna

54 Ga wuraren da aka ba zuriyar Haruna, na iyalin Kohat. Sun karɓi rabo na farko a ƙasar. 55 Rabonsu ya haɗu da Hebron ta yankin ƙasar Yahuza, da makiyayar da suke kewaye da ita. 56 Amma an ba Kalibu ɗan Yefunne saurukan birnin, tare da ƙauyukansa. 57 Suka ba 'ya'yan Haruna, maza, biranen mafaka, wato Hebron, da Libna tare da makiyayarta, da Yattir, da Eshtemowa tare da makiyayarta, 58 da Holon tare da makiyayarta, da Debir tare da makiyayarta, 59 da Ayin tare da makiyayarta, da Bet-shemesh tare da makiyayarta. 60 Daga kabilar Biliyaminu aka ba su Geba tare da makiyayarta, da Allemet tare da makiyayarta, da Anatot tare da makiyayarta. Dukan biranen iyalansu guda goma sha uku ne.

Inda Sauran Lawiyawa suka Zauna

61 Aka ba sauran 'ya'yan Kohat, maza, garuruwa goma daga na rabin kabilar Manassa, ta hanyar kuri'a. 62 Aka kuma ba Gershonawa bisa ga iyalansu, birane goma sha uku daga na kabilar Issaka, da na kabilar Ashiru, da na kabilar Naftali, da na kabilar Manassa da ke nan a Bashan. 63 Haka kuma aka ba 'ya'yan Merari, maza, bisa ga iyalansu, garuruwa goma sha biyu daga na kabilar Ra'ubainu, da na kabilar Gad, da na kabilar Zabaluna. 64 Haka fa, jama'ar Isra'ila suka ba Lawiyawa garuruwa duk da makiyayansu. 65 Daga na kabilar Yahuza, da na kabilar Saminu, da na kabilar Biliyaminu kuma aka ba da waɗannan garuruwan da aka ambaci sunayensu ta hanyar kuri'a. 66 Waɗansu daga cikin iyalan 'ya'yan Kohat, maza, sun sami garuruwa na yankinsu daga cikin kabilar Ifraimu. 67 Sai suka ba su waɗannan biranen mafaka, wato Shekem a ƙasar tudu ta Ifraimu duk da makiyayarta, da Gezer tare da makiyayarta, 68 da Yokmeyam duk da makiyayarta, da Bet-horon duk da makiyayarta, 69 da Ayalon duk da makiyayarta, da Gatrimmon duk da makiyayarta. 70 Daga cikin rabin kabilar Manassa kuma an ba su Ta'anak duk da makiyayarta, da Bileyam duk da makiyayarta. An ba da waɗannan ga sauran iyalai na 'ya'yan Kohat, maza. 71 Daga na rabin kabilar Manassa na gabas, an ba 'ya'yan Gershon, maza, Golan ta Bashan tare da makiyayarta, da Ashtarot duk da makiyayarta. 72 Daga na kabilar Issaka kuma an ba su Kishiyon duk da makiyayarta, da Daberat duk da makiyayarta, 73 da Ramot duk da makiyayarta, da Enganin duk da makiyayarta. 74 Daga cikin kabilar Ashiru kuma an ba da Mishal duk da makiyayarta, da Abdon duk da makiyayarta, 75 da Helkat duk da makiyayarta, da Rehob duk da makiyayarta. 76 Daga na kabilar Naftali kuma an ba da Kedesh ta Galili duk da makiyayarta, da Hammon duk da makiyayarta, da Kartan duk da makiyayarta. 77 Daga na kabilar Zabaluna, an ba sauran Lawiyawa, wato 'ya'yan Merari, maza, Rimmon duk da makiyayarta, da Tabor duk da makiyayarta. 78 Daga na kabilar Ra'ubainu a hayin Urdun a Yariko, wato gabashin Urdun, an ba da Bezer ta cikin jeji duk da makiyayarta, da Yahaza duk da makiyayarta, 79 da Kedemot duk da makiyayarta, da Mefayat duk da makiyayarta. 80 Daga na kabilar Gad kuma an ba da Ramot ta Gileyad duk da makiyayarta, da Mahanayim duk da makiyayarta, 81 da Heshbon duk da makiyayarta, da Yazar duk da makiyayarta.

1 Tarihi 7

Zuriyar Issaka

1 'Ya'yan Issaka, maza, su huɗu ne, wato Tola, da Fuwa, da Yashub, da Shimron. 2 'Ya'yan Tola, maza, su ne Uzzi, da Refaya, da Yeriyel, da Yamai, da Ibsam, da Sama'ila, su ne shugabannin gidajen kakanninsu. 'Ya'yan Tola kuwa manyan mayaƙa ne a zamaninsu. Yawansu a zamanin Dawuda, su dubu ashirin da biyu ne da ɗari shida (22,600 ). 3 Ɗan Uzzi, shi ne Izrahiya. 'Ya'yan Izrahiya, maza, su ne Maikel, da Obadiya, da Yowel, da Isshiya. Su biyar duka manyan mutane ne. 4 A zamaninsu, bisa ga gidajen kakanninsu suna da sojoji dubu talatin da dubu shida (36,000 ) gama suna da mata da yara da yawa. 5 Mayaƙan da aka lasafta bisa ga asalinsu na dukan iyalan Issaka, su dubu tamanin da dubu bakwai ne (87,000 ), jarumawa ne sosai.

Zuriyar Biliyaminu

6 'Ya'yan Biliyaminu su uku ne, wato Bela, da Beker, da Yediyayel. 7 'Ya'yan Bela, maza, su biyar ne, wato Ezbon, da Uzzi, da Uzziyel, da Yerimot, da Iri. Su ne shugabannin gidajen kakanninsu, jarumawa ne su. An lasafta su bisa ga asalinsu, su dubu ashirin da biyu ne da talatin da huɗu (22,034 ). 8 'Ya'yan Beker, maza, su ne Zemira, da Yowash, da Eliyezer, da Eliyehoyenai, da Omri, da Yerimot, da Abaija da Anatot, da Alamet. Waɗannan duka 'ya'yan Beker ne, maza. 9 An lasafta su bisa ga asalinsu a zamaninsu, su dubu ashirin ne da ɗari biyu (20,200 ), jarumawa ne su sosai. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu. 10 Ɗan Yediyayel shi ne Bilhan. 'Ya'yan Bilhan, maza, su ne Yewush, da Biliyaminu, da Ehud, da Kena'ana, da Zetan, da Tarshish, da Ahishahar. 11 Duk waɗannan 'ya'yan Yediyayel, maza ne, bisa ga shugabannin gidajen kakanninsu. Su dubu goma sha bakwai ne da ɗari biyu (17,200 ), jarumawa ne sosai, shiryayyu don yaƙi. 12 Shuffim da Huffim su ne 'ya'yan Iri, maza. Hushim shi ne ɗan Ahiram.

Zuriyar Naftali

13 Naftali yana da 'ya'ya huɗu, su ne Yazeyel, da Guni, da Yezer, da Shallum. Su ne zuriya daga Bilha.

Zuriyar Manassa

14 'Ya'yan Manassa, maza, su ne Asriyel, wanda ƙwarƙwararsa Ba'aramiya ta haifa masa. Ta kuma haifi Makir mahaifin Gileyad. 15 Makir ya auro wa Huffim da Shuffim mata. Sunan 'yar'uwarsa Ma'aka, sunan ɗan'uwansa kuwa Zelofehad, Zelofehad yana da 'ya'ya mata kaɗai. 16 Sai Ma'aka matar Makir ta haifi ɗa, ta sa masa suna Feres, sunan ɗan'uwansa kuwa Sheres. 'Ya'yan Feres maza, su ne Ulam da Rakem. 17 Ɗan Ulam shi ne Bedan. Waɗannan su ne 'ya'ya maza na Gileyad ɗan Makir, j�kan Manassa. 18 'Yar'uwarsa, Hammoleket ta haifi Ishodi, da Abiyezer, da Mala. 19 'Ya'yan Shemida, maza, su ne Ahiyan, da Shekem, da Liki, da Aniyam.

Zuriyar Ifraimu

20 'Ya'yan Ifraimu, maza, daga tsara zuwa tsara, su ne Shutela, da Bered, da Tahat, da Eleyada, da Tahat, 21 da Zabad, da Shutela, da Ezer, da Eleyad waɗanda mutanen Gat, haifaffun ƙasar, suka kashe sa'ad da suka kai hari don su kwashe dabbobinsu. 22 Sai mahaifinsu, Ifraimu, ya yi ta makoki kwanaki da yawa. 'Yan'uwansu kuwa suka zo don su yi masa ta'aziyya. 23 Sa'an nan ya shiga wurin matarsa, ta kuwa sami juna biyu, ta haifi ɗa, ya raɗa masa suna Beriya saboda masifar da ta auko wa gidansa. 24 'Yarsa kuma ita ce Sheyera, wadda ta gina garin Bet-horon na kwari da na tudu, ta kuma gina Uzzen-sheyera. 25 Waɗansu zuriyarsa bi da bi, su ne Refa, da Reshe, da Tela, da Tahan, 26 da Ladan, da Ammihud, da Elishama, 27 da Nun, da Joshuwa. 28 Mallakarsu da wuraren zamansu, su ne Betel duk da garuruwanta, da Nayaran wajen gabas, da Gezer wajen yamma duk da garuruwanta, da Shekem duk da garuruwanta, har zuwa Ayya duk da garuruwanta. 29 Zuriyar Manassa sun mallaki Bet-sheyan, da Ta'anak, da Magiddo, da Dor duk da garuruwan da suke kewaye da su. A nan ne zuriyar Yusufu, ɗan Isra'ila, suka zauna.

Zuriyar Ashiru

30 'Ya'yan Ashiru, maza, su ne Yimna, da Yishuwa, da Yishwi, da Beriya, da 'yar'uwarsu Sera. 31 'Ya'yan Beriya, maza, su ne Eber, da Malkiyel wanda ya kafa garin Birzayit. 32 Eber shi ne mahaifin Yaflet, da Shemer, da Helem, da 'yar'uwarsu Shuwa. 33 'Ya'yan Yaflet, maza, su ne Fasak, da Bimhal, da Ashewat. 34 'Ya'yan Shemer maza, su ne Ahi, da Roga, da Yehubba, da Aram. 35 'Ya'ya maza na ɗan'uwansa Helem, su ne Zofa, da Imna, da Sheles da Amal. 36 'Ya'yan Zofa, su ne Suwa, da Harnefer, da Shuwal, da Beri, da Imra, 37 da Bezer, da Hod, da Shamma, da Shilsha, da Yeter, da Biyera. 38 'Ya'yan Yeter, su ne Yefunne, da Fisfa, da Ara. 39 'Ya'yan Ulla, maza, su ne Ara, da Haniyel, da Riziya. 40 Waɗannan duka su ne zuriyar Ashiru, su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu. Zaɓaɓɓun jarumawa ne su, manyan sarakuna. Yawansu da aka lasafta bisa ga asalinsu don yaƙi su dubu ashirin da dubu shida ne (26,000 ).

1 Tarihi 8

Zuriyar Biliyaminu

1 Biliyaminu yana da 'ya'ya biyar, su ne Bela, da Ashbel, da Ahiram, 2 da Noha, da Rafa. 3 Bela kuma yana da 'ya'ya maza, su ne Adar, da Gera da Abihud, 4 da Abishuwa, da Na'aman, da Ahowa, 5 da Gera, da Shuffim, da Huram. 6 Waɗannan kuma su ne 'ya'yan Ehud, maza. Su ne kuma shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Geba, waɗanda aka kai su bauta a Manahat. 7 Ga sunayensu, Na'aman, da Ahaija, da Gera wanda yake shugabansu lokacin da aka kai su bauta. Shi ne kuma mahaifin Uzza da Ahihud. 8 Shaharayim kuma yana da 'ya'ya maza a ƙasar Mowab bayan da ya saki matansa biyu, wato Hushim da Ba'ara. 9 Matarsa Hodesh ta haifa masa 'ya'ya maza, su ne Yobab, da Zibiya, da Mesha, da Malkam, 10 da Yuz, da Sakiya, da Mirma. Waɗannan su ne 'ya'yansa maza, shugabannin gidajen kakanninsu. 11 Hushim kuma ta haifa masa waɗansu 'ya'ya maza, su ne Abitub da Elfayal. 12 'Ya'yan Elfayal, su ne Eber, da Misham, da Shemed wanda ya gina Ono da Lod da ƙauyukansu, da 13 Beriya, da Shimai, su ne shugabannin gidajen kakanninsu da suke zaune a Ayalon waɗanda suka kori mazaunan Gat, 14 da Ahiyo, da Shashak, da Yeremot. 15 Zabadiya, da Arad, da Eder, 16 da Maikel, da Ishfa, da Yoha, su ne 'ya'yan Beriya, maza. 17 Zabadiya, da Meshullam, da Hizki, da Eber, 18 da Ishmerai, da Izliya, da Yobab, su ne zuriyar Elfayal. 19 Zuriyar Shimai, su ne Yakim, da Zikri, da Zabdi, 20 da Eliyenai, da Zilletai, da Eliyel, 21 da Adaya, da Beraiya, da Shimrat. 22 Zuriyar Shashak, su ne Isfan, da Eber, da Eliyel, 23 da Abdon, da Zikri, da Hanan, 24 da Hananiya, da Elam, da Antotiya, 25 da Ifediya, da Feniyel. 26 Zuriyar Yeroham, su ne Shemsherai, da Shehariya, da Ataliya, 27 da Yawareshiya, da Eliya, da Zikri. 28 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakanninsu a zamaninsu, waɗanda suka zauna a Urushalima.

Zuriyar Saul

29 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a can. Sunan matarsa Ma'aka. 30 Abdon ne ɗansa na fari, sa'an nan Zur, da Kish, da Ba'al, da Nadab, 31 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya, 32 da Miklot, mahaifin Shimeya. Waɗannan su ne suka zauna daura da 'yan'uwansu a Urushalima. 33 Ner shi ne mahaifin Kish, Kish kuma shi ne mahaifin Saul, Saul shi ne mahaifin Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet. 34 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika. 35 'Ya'yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz. 36 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza. 37 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel. 38 Azel ya haifi 'ya'ya maza su shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Ismayel, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan. 39 'Ya'ya maza na Esheke ɗan'uwansa su ne, Ulam, da Yewush, da Elifelet. 40 'Ya'yan Ulam, maza, jarumawa ne sosai, 'yan baka, suna da 'ya'ya maza, da jikoki maza da yawa. Su ɗari da hamsin ne. Waɗannan duka mutanen Biliyaminu ne.

1 Tarihi 9

Waɗanda suka Komo daga Babila

1 Haka kuwa aka lasafta Isra'ilawa bisa ga asalinsu. An rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila. Sai aka kai mutanen Yahuza zaman talala a Babila saboda rashin amincinsu ga Ubangiji. 2 Waɗanda suka fara zama a biranen mallakarsu, su ne Isra'ilawa da firistoci, da Lawiyawa, da kuma ma'aikatan Haikali. 3 Waɗansu mutanen Yahuza, da na Biliyaminu, da na Ifraimu, da na Manassa suka zauna a Urushalima. 4-6 Iyalin Yahuza guda ɗari shida da tasa'in suka zauna a Urushalima, shugabansu kuwa shi ne Utai ɗan Ammihud, j�kan Omri daga wajen Feresa. Waɗansu kakanninsu kuwa su ne Imri da Bani. Zuriyar Shela ɗan Yahuza suna da shugaba mai suna Asaya. Zuriyar Zera ɗan Yahuza kuwa, shugabansu Yuwel. 7 Ga zuriyar Biliyaminu a Urushalima bi da bi, da Sallai ɗan Meshullam, da Hodawiya, da Hassenuwa, 8 da kuma Ibneya ɗan Yeroham, da Ila ɗan Uzzi, wato j�kan Mikri, da Meshullam ɗan Shefatiya, da Reyuwel, da Ibnija. 9 Tare da danginsu a zamaninsu, sun kai ɗari tara da hamsin da shida ne. Duk waɗannan shugabannin gidajen kakanninsu ne.

Firistocin da suke a Urushalima

10 Daga cikin firistoci masu zama a Urushalima su ne Yedaiya, da Yehoyarib, da Yakin, 11 da Azariya ɗan Hilkiya, shi ne jami'in Haikalin Ubangiji, kakanninsa sun haɗu da Shallum ɗan Zadok, da Merayot, da Ahitub, 12 da Adaya ɗan Yeroham, kakanninsa sun haɗu da Fashur, da Malkiya, da Ma'asai ɗan Adiyel, kakanninsa sun haɗu da Yazera, da Meshullam, da Meshillemot, da Immer. 13 Firistacin da suke shugabannin gidajen kakanninsu, sun kai mutum dubu da ɗari bakwai da sittin (1,760 ). Ƙwararru ne cikin hidimar Haikalin Ubangiji. 14 Lawiyawa masu zama a Urushalima kuma, su ne Shemaiya ɗan Hasshub, wanda kakanninsa suka haɗu da Azrikam da Hashabiya daga 'ya'yan Merari, maza, 15 da kuma Bakbakkar, da Heresh, da Galal, da Mattaniya ɗan Mika wanda kakanninsa su ne Zikri da Asaf, 16 da kuma Obadiya ɗan Shemaiya, kakanninsa su ne Galal da Yedutun, da Berikiya ɗan Asa, wato j�kan Elkana, wanda ya zauna a garin Netofa. 17 Masu tsaron Haikalin, su ne Shallum, da Akkub, da Talmon, da Ahiman, da 'yan'uwansu. Shallum shi ne shugaba. 18 Har zuwa yau, iyalinsu suke tsaron ƙofar sarki a wajen gabas. A dā su ne suke tsaron sauran ƙofofin zangon Lawiyawa. 19 Shallum ɗan Kore, wato j�kan Ebiyasaf, tare da 'yan'uwansa na zuriyar Kora, suke lura da masu tsaron ƙofofin alfarwa kamar dai yadda kakanninsu suka lura da zangon Ubangiji. 20 A dā Finehas ɗan Ele'azara shi ne shugabansu, Ubangiji kuwa yana tare da shi. 21 Zakariya ɗan Shallum yake tsaron ƙofar alfarwa ta sujada. 22 Dukan waɗanda aka zaɓa domin su zama masu tsaron ƙofofi, su ɗari biyu ne da goma sha biyu. An lasafta su bisa ga asalinsu da garuruwansu. Dawuda da Sama'ila annabi, su ne suka sa su a matsayinsu na riƙon amana. 23 Saboda haka su da 'ya'yansu maza suke tsaron ƙofofin Ubangiji, wato alfarwa ta sujada. 24 Matsaran ƙofofi suka tsaya a kusurwoyi huɗu, wato gabas da yamma, kudu da arewa. 25 'Yan'uwansu da suke a ƙauyuka kuwa, ya zama musu wajibi su zo wurinsu kowane kwana bakwai, domin su karɓe su tsaron. 26 Su shugabanni huɗu na matsaran ƙofar Lawiyawa ne waɗanda suke da matsayi na riƙon amana, su ne masu lura da ɗakunan Haikalin Allah da dukiyarsa. 27 Sukan kwana suna tsaro kewaye da Haikalin Allah, gama hakkin yana kansu. Su ne sukan buɗe shi kowace safiya. 28 Waɗansunsu suna lura da kayayyakin aiki na cikin Haikali. Sukan ƙidaya su sa'ad da aka shigo da su, da sa'ad da aka fitar da su. 29 Aka sa waɗansu su zama masu lura da kayayyakin Haikalin, da kayayyakin aiki na cikin Wuri Mai Tsarki, da lallausan gari, da ruwan inabi, da mai, da turare, da kayan yaji. 30 Waɗansu 'ya'yan firistoci, maza, suke harhaɗa kayan yaji. 31 Mattitiya, ɗaya daga cikin Lawiyawa, ɗan farin Shallum na iyalin Kora, shi ne mai lura da toya waina. 32 Waɗansu 'yan'uwansu Kohatawa suke lura da gurasar ajiyewa. Sukan shirya ta kowace Asabar. 33 Waɗannan su ne mawaƙa, da shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa, waɗanda suka zauna a ɗakunan Haikali, ba su yin wani aiki dabam, gama dare da rana suke yin aikinsu. 34 Waɗannan su ne manyan shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa a zamaninsu, wato waɗanda suka zauna a Urushalima.

Kakannin Sarki Saul da Zuriyarsa

35 Yehiyel ne ya kafa Gibeyon ya zauna a ciki, sunan matarsa Ma'aka, 36 ɗan farinsa kuma shi ne Abdon. Sa'an nan ga Zur, da Kish, da Ba'al, da Ner, da Nadab, 37 da Gedor, da Ahiyo, da Zakariya, da Miklot, 38 mahaifin Shimeya. Zuriyarsu ne suka zauna a Urushalima daura da 'yan'uwansu. 39 Ner ya haifi Kish, Kish kuma ya haifi Saul, Saul ya haifi Jonatan, da Malkishuwa, da Yishwi, da Ish-boshet. 40 Jonatan ya haifi Mefiboshet, Mefiboshet ya haifi Mika. 41 'Ya'yan Mika, maza, su ne Fiton, da Melek, da Tareya, da Ahaz. 42 Ahaz ya haifi Yehowadda, Yehowadda ya haifi Allemet, da Azmawet, da Zimri. Zimri ya haifi Moza, 43 Moza ya haifi Bineya, da Refaya, da Eleyasa, da Azel. 44 Azel yana da 'ya'ya maza guda shida, su ne Azrikam, da Bokeru, da Isma'ilu, da Sheyariya, da Obadiya, da Hanan.

1 Tarihi 10

Mutuwar Sarki Saul da ta 'Ya'yansa

1 Filistiyawa suka yi yaƙi da Isra'ilawa, Isra'ilawa suka gudu a gaban Filistiyawa, aka karkashe su a Dutsen Gilbowa. 2 Filistiyawa suka kama Saul da 'ya'yansa maza, suka kashe Jonatan da Yishwi, da Malkishuwa. 3 Yaƙin ya tsananta wa Saul, maharba suka rutsa Saul, suka yi masa rauni. 4 Sai Saul ya ce wa mai ɗaukar makamansa, “Zare takobinka, ka kashe ni, don kada marasa kaciyan nan su zo su yi mini ba'a.” Amma mai ɗaukar makamai nasa bai yarda ba, gama yana jin tsoro ƙwarai. Saboda haka sai Saul ya zare takobinsa ya fāɗi a kansa. 5 Sa'ad da mai ɗaukar makamansa ya ga Saul ya mutu, sai shi ma ya faɗi a kan takobinsa ya mutu. 6 Ta haka Saul ya mutu, shi da 'ya'yansa maza guda uku tare da dukan gidansa. 7 Sa'ad da dukan Isra'ilawa waɗanda suke zaune a kwari suka ga sojojin sun gudu, Saul kuma da 'ya'yansa maza sun mutu, sai suka bar garuruwansu suka gudu. Filistiyawa suka zo suka zauna a wurin. 8 Kashegari, sa'ad da Filistiyawa suka tafi su kwashe waɗanda aka kashe, sai suka tarar da Saul da 'ya'yansa maza matattu a Dutsen Gilbowa. 9 Suka kuwa tuɓe tufafinsa, suka datse kansa suka ɗauka duk da kayan yaƙinsa, suka aiki manzanni ko'ina a ƙasar Filistiyawa don su ba gumakansu da jama'arsu wannan albishir. 10 Sai suka ajiye kayan yaƙin Saul a gidan gumakansu, suka kuma rataye kansa a gidan gunkin nan, wato Dagon. 11 Sa'ad da mutanen Yabesh-gileyad suka ji irin abin da Filistiyawa suka yi wa Saul, 12 sai dukan ƙarfafan mutanensu suka tafi suka ɗauki gawar Saul, da gawawwakin 'ya'yansa, suka kawo a Yabesh suka binne ƙasusuwansu a ƙarƙashin itacen oak cikin Yabesh. Suka yi azumi har kwana bakwai. 13 Hakanan Saul ya mutu saboda laifin da ya yi wa Ubangiji, gama bai kiyaye maganar Ubangiji ba, saboda kuma ya nemi shawara wurin masu mabiya. 14 Amma bai nemi Ubangiji ba. Domin haka Ubangiji ya kashe shi, ya ɗauki sarautar, ya ba Dawuda ɗan Yesse.

1 Tarihi 11

Dawuda ya Zama Sarkin Isra'ila da Yahuza

1 Dukan Isra'ilawa kuwa suka taru wurin Dawuda a Hebron, suka ce masa, “Mu ɗaya ne da kai. 2 Ko dā can lokacin da Saul yake sarauta, kai ne kake yi wa Isra'ilawa jagora zuwa yaƙi da komowa. Ubangiji Allahnka kuwa ya ce maka, ‘Za ka yi kiwon jama'ata, wato Isra'ilawa, ka kuma shugabance su.’ ” 3 Sai dattawan Isra'ilawa suka zo wurin sarki Dawuda a Hebron. Dawuda kuwa ya yi alkawari da su a Hebron a gaban Ubangiji, ake kuwa naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila bisa ga faɗar Ubangiji ta bakin Sama'ila.

Dawuda ya Ci Sihiyona

4 Sarki Dawuda kuwa, tare da dukan Isra'ilawa, suka tafi Urushalima, wato Yebus inda Yebusiyawa suke zaune. 5 Sai mazaunan Yebus, suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka Dawuda ya ci Sihiyona, gari mai kagara, wato birnin Dawuda ke nan. 6 Sai Dawuda ya ce, “Duk wanda ya ci Yebusiyawa da fari shi ne zai zama babban shugaban sojoji.” Yowab ɗan Zeruya ne ya fara tafiya, domin wannan aka maishe shi shugaba. 7 Sa'an nan Dawuda ya zauna a kagara, don haka aka kira birnin, birnin Dawuda. 8 Sai ya rutsa birnin da gini tun daga Millo. Yowab kuma ya gyaggyara sauran birnin. 9 Dawuda ya yi ta ƙasaita gaba gaba saboda Ubangiji Mai Runduna yana tare da shi.

Jarumawan Dawuda

10 Waɗannan su ne shugabanni, wato manyan jarumawan Dawuda waɗanda suka goyi bayansa sosai a mulkinsa, tare da dukan Isra'ilawa waɗanda suka naɗa shi sarki bisa ga maganar Ubangiji a kan Isra'ilawa. 11 Wannan shi ne labarin manyan jarumawan Dawuda. Yashobeyam ɗan Bahakmone shi ne shugaban jarumawa talatin. Ya karkashe mutum ɗari uku da māshinsa baki ɗaya. 12 Na biye da shi shi ne Ele'azara ɗan Dodo, Ba'ahohiye, wanda yake ɗaya daga cikin manyan jarumawan nan uku. 13 Yana tare da Dawuda a Efes-dammin sa'ad da Filistiyawa suka taru wuri ɗaya don su yi yaƙi. Akwai wata gonar sha'ir a wurin, sai jama'a suka gudu daga gaban Filistiyawa. 14 Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha'ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya cece su, ya ba su babbar nasara. 15 Wata rana sai uku daga cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara zuwa dutsen Dawuda, a kogon Adullam, sa'ad da rundunar sojojin Filistiyawa suka kafa sansani a kwarin Refayawa. 16 Dawuda yana cikin kagara, sojojin Filistiyawa kuwa suna a Baitalami. 17 Sai Dawuda ya yi marmarin gida, ya ce, “Dā ma wani ya kawo mini ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami in sha!” 18 Sai uku ɗin suka kutsa kai, suka shiga sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take a ƙofar Baitalami, suka ɗauka, suka kawo wa Dawuda, Dawuda kuwa bai sha ba, amma ya kwarara ruwan a ƙasa domin sadaka ga Ubangiji. 19 Sa'an nan ya ce, “Allah ya sawwaƙe mini da zan yi wannan abu a gabansa, da zan sha jinin waɗannan da suka sadaukar da rayukansu, gama sai da suka yi kasai da ransu, sa'an nan suka ɗebo ruwan.” Saboda haka bai sha ruwan ba. Manyan jarumawan nan uku ne suka aikata waɗannan abubuwa. 20 Abishai ɗan'uwan Yowab kuwa shi ne shugaban jarumawa talatin ɗin. Ya girgiza māshinsa, ya kashe mutum ɗari uku. Ya yi suna a cikin jarumawan nan talatin. 21 Cikin jarumawa talatin ɗin, shi ya shahara har ya zama shugabansu. Amma duk da haka bai kai ga jarumawan nan uku ba. 22 Benaiya ɗan Yehoyada, ɗan wani jarumi ne daga Kabzeyel, ya yi manyan ayyuka, ya kashe jarumawa biyu na Mowabawa. Sai ya gangara ya kashe zaki a cikin rami a ranar da ake yin dusar ƙanƙara. 23 Sai kuma ya kashe wani dogon Bamasare mai tsayi kamu biyar. Bamasaren yana da māshi mai kama da dirkar masaƙa a hannunsa, amma sai ya gangaro wurinsa da kulki a hannu, ya ƙwace māshin daga hannun Bamasaren, ya kashe shi da shi. 24 Waɗannan abubuwa Benaiya ɗan Yehoyada ya yi su, ya kuwa yi suna kamar manyan jarumawan nan uku. 25 Ya yi suna a cikin jarumawa talatin ɗin, amma bai kai ga jarumawan nan uku ba. Sai Dawuda ya sa shi ya zama shugaban matsaransa. 26-47 Waɗannan su ne manyan jarumawan sojoji. Asahel ɗan'uwan Yowab Elhanan ɗan Dodo daga Baitalami Shamma daga Harod Helez daga Felet Aira ɗan Ikkesha daga Tekowa Abiyezer daga Anatot Sibbekai daga Husha Ilai daga Aho Maharai daga Netofa Heled ɗan Ba'ana daga Netofa Ittayi ɗan Ribai daga Gibeya ta Biliyaminu Benaiya na Firaton Hurai daga rafuffuka kusa da Ga'ash Abiyel daga Araba Azmawet daga Bahurim Eliyaba daga Shalim 'Ya'yan Yashen, maza, daga Gizon Jonatan ɗan Shimeya daga Harod Ahiyam ɗan Sharar daga Harod Elifelet ɗan Ahasbai Hefer daga Mekara Ahaija daga Felet Hezro daga Karmel Nayarai ɗan Ezbai Yowel ɗan'uwan Natan Mibhar ɗan Hagri Zelek daga Ammon Naharai daga Biyerot (Mai riƙe wa Yowab ɗan Zeruya makamai) Aira da Gareb daga Yattir Uriya Bahitte Zabad ɗan Alai Adina ɗan Shiza (Shi ne shugaba a kabilar Ra'ubainu, yana da ƙungiyarsa mai soja talatin tare da shi) Hanan ɗan Ma'aka Yoshafat daga Mitna Uzziya daga Ashtera Shama da Yehiyel 'ya'yan Hotam, maza, daga Arower Yediyel da Yoha 'ya'yan Shimri, maza, daga Tiz Eliyel daga Mahawa Yeribai, da Yoshawiya 'ya'yan Elna'am, maza Itma daga Mowab Eliyel, da Obida, da Yawasiyel daga Zoba

1 Tarihi 12

Mataimakan Dawuda a Ziklag

1 Mutane da yawa suka haɗa kai da Dawuda lokacin da yake a Ziklag, sa'ad da yake a takure saboda Saul ɗan Kish. Su ma suna cikin manyan jarumawan da suka taimake shi yaƙi. Dukansu gwanayen sojoji ne, suna iya su harba kibiya, ko su yi jifa da majajjawa da hannun dama ko da na hagu. 2 Su daga kabilar Biliyaminu ne, dangin Saul. 3-7 Waɗannan su ne shugabannin sojoji, Ahiyezer, da Yowash, 'ya'yan Shemaiya, maza, daga Gibeya Yeziyel, da Felet, 'ya'yan Azmawet, maza Beraka, da Yehu daga Anatot Ismaya daga Gibeyon babban jarumi ne a cikin jarumawan nan talatin, yana daga cikin shugabannin jarumawa talatin ɗin Irmiya, da Yahaziyel Yohenan, da Yozabad daga Gedera Eluzai, da Yerimot, da Be'aliya Shemariya, da Shefatiya daga Harif Elkana, da Isshiya, da Azarel Yowezer, da Yashobeyam daga iyalin Kora Yowela, da Zabadiya 'ya'ya maza na Yeroham na Gedor 8 Waɗannan su ne sunayen shahararru, ƙwararrun mayaƙa daga kabilar Gad, waɗanda suka haɗa kai da sojojin Dawuda, sa'ad da yake a kagara a hamada. Su gwanayen yaƙi da garkuwa da māshi ne. Fuskokinsu kamar na zakoki, saurinsu kamar bareyi a kan dutse. yadda aka lasafta su bisa ga matsayinsu, da Ezer, da Obadiya, da Eliyab, da Mishmanna, da Irmiya, da Attai, da Eliyel, da Yohenan, da Elzabad, da Irmiya, da Makbannai. 14 Waɗannan daga kabilar Gad shugabannin sojoji ne, waɗansu na mutum dubu, sauransu kuma ƙananan shugabanni ne waɗanda suke shugabancin sojoji ɗari. 15 Su ne waɗanda suka haye Urdun a watan fari na shekara, sa'ad da Kogin Urdun ɗin ya yi ambaliya. Suka kori waɗanda suke zaune a kwaruruka, na wajen gabas da yamma da kogin. 16 Sa'an nan waɗansu daga cikin mazajen Biliyaminu da na Yahuza, suka zo wurin Dawuda a kagararsa. 17 Sai Dawuda ya fito don ya tarye su, ya ce musu, “Idan da salama kuka zo wurina don ku taimake ni, to, zuciyata za ta zama ɗaya da taku, amma idan kun zo ne don ku bashe ni ga maƙiyana, to, Allah na kakanninmu ya duba ya shara'anta, da yake ba ni da laifi.” 18 Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Amasa wanda daga baya ya zama shugaban talatin ɗin, sai ya ce, “Muna tare da kai, ya Dawuda ɗan Yesse! Allah ya ba ka nasara tare da waɗanda suke tare da kai! Allah yana wajenka!” Sa'an nan Dawuda ya marabce su, ya maishe su shugabanni a sojojinsa. 19 Waɗansu sojoji daga Manassa, suka tafi wurin Dawuda sa'ad da yake fita tare da Filistiyawa don su yi yaƙi da Saul. Amma Dawuda bai tafi tare da su ba, domin sarakunan Filistiyawa sun yi shawara, suka sallame shi, don kada ya juya musu gindin baka, ya nemi sulhu a wurin shugabansu Saul, da kawunansu. 20 Sa'ad da yake komawa Ziklag sai sojojin Manassa suka zo wurinsa, wato su Adana, da Yozabad, da Yediyayel, da Maikel, da Yozabad, da Elihu, da Zilletai. A sojojin kabilar Manassa, waɗannan shugabannin sojoji ne na dubu dubu. 21 Suka kuwa taimaki Dawuda sa'ad da mahara suke tasar masa, gama dukansu jarumawa ne sosai, su kuma shugabannin sojoji ne. 22 Kowace rana mutane suna ta zuwa wurin Dawuda don su taimake shi, har suka zama babbar runduna.

Jerin Sojojin Dawuda a Hebron

23 Horarrun sojoji da yawa suka haɗa kai da sojojin Dawuda a Hebron domin su taimaki Dawuda da yaƙi, su mai da shi sarki maimakon Saul, kamar yadda Ubangiji ya alkawarta. Ga yadda yawansu yake. 24 Mutanen Yahuza waɗanda suke riƙe da garkuwoyi da māsu don yaƙi, mutum dubu shida da ɗari takwas (6,800 ). 25 Na kabilar Saminu jarumawa mayaƙa mutum dubu bakwai da ɗari (7,100 ). 26 Na kabilar Lawi akwai mutum dubu huɗu da ɗari shida (4,600 ). 27 Akwai kuma Yehoyada wanda shi ne shugaban gidan Haruna, yana da mutum dubu uku da ɗari bakwai (3,700 ). 28 Na dangin Zadok wanda yake jarumi, saurayi, akwai shugabannin sojoji ashirin da biyu. 29 Na kabilar Biliyaminu, wato kabilar Saul, akwai mutum dubu uku (3,000 ). (Har yanzu yawancin mutanen Biliyaminu ba su daina bin gidan Saul ba.) 30 Na kabilar Ifraimu akwai mutum dubu ashirin da ɗari takwas (20,800 ), jarumawa ne sosai, waɗanda suka shahara a danginsu. 31 Na rabin kabilar Manassa wajen yamma akwai mutum dubu goma sha takwas (18,000 ) waɗanda aka zaɓa domin su zo su naɗa Dawuda ya zama sarki. 32 Na kabilar Issaka akwai shugabanni ɗari biyu, waɗanda suka gane da halin da ake ciki, da abin da ya kamata Isra'ila ya yi. Su ne suke shugabancin 'yan'uwansu. 33 Na kabilar Zabaluna akwai mutum dubu hamsin (50,000 ) suna da kowane irin kayan yaƙi. Suka zo domin su taimaki Dawuda da zuciya ɗaya. 34 Na kabilar Naftali akwai shugabannin sojoji dubu ɗaya (1,000 ) tare da sojoji dubu talatin da dubu bakwai (37,000 ) masu garkuwoyi da māsu. 35 Na kabilar Dan mutum dubu ashirin da takwas da ɗari shida (28,600 ). 36 Na kabilar Ashiru, sojoji dubu arba'in (40,000 ) suka fito da shirin yaƙi. 37 Kabilan gabashin Urdun, wato kabilar Ra'ubainu, da Gad, da rabin kabilar Manassa, su dubu ɗari da dubu ashirin ne (120,000 ), suna da kowane irin kayan yaƙi. 38 Duk waɗannan mayaƙa sun zo Hebron a shirye, da zuciya ɗaya don su naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila duka. Haka kuma dukan sauran Isra'ilawa suka goyi baya da zuciya ɗaya a naɗa Dawuda ya zama sarki. 39 Suka yi kwana uku tare da Dawuda, suka yi ta ci suna sha, gama 'yan garin sun shirya wata liyafa dominsu. 40 Waɗanda kuma suke kusa da su har zuwa Issaka, da Zabaluna da Naftali, sun kawo abinci a kan jakuna, da raƙuma, da alfadarai, da takarkarai. Suka kawo abinci mai yawa, wato gāri da kauɗar ɓaure da nonnan busassun 'ya'yan inabi, da ruwan inabi, da man zaitun. Suka kuma kawo shanu da tumaki domin yanka a ci. Duk an yi wannan domin a nuna farin ciki ƙwarai a cikin dukan ƙasar Isra'ila.

1 Tarihi 13

Dawuda ya yi Niyyar Kawo Akwatin Alkawari a Urushalima

1 Sa'an nan Dawuda ya yi shawara da shugabannin sojoji na dubu dubu da na ɗari ɗari, da kowane shugaba. 2 Ya kuma yi magana da dukan taron Isra'ilawa, ya ce, “Idan kun ga ya yi kyau, idan kuma nufin Ubangiji Allahnmu ne, to, bari mu aika a ko'ina wurin 'yan'uwanmu waɗanda aka rage a ƙasar Isra'ila, mu kuma aika wa firistoci da Lawiyawa waɗanda suke tare da su a biranensu masu makiyaya domin su zo wurinmu. 3 Sa'an nan mu ɗauko akwatin alkawari na Allahnmu mu kawo shi wurinmu, gama mun ƙyale shi tun zamanin Saul.” 4 Jama'a kuwa suka amince da shawarar, suka yarda kuma a yi haka ɗin.

Dawuda ya Tafi ya Kawo Akwatin Alkawari

5 Haka fa, Dawuda ya tattara dukan Isra'ilawa wuri ɗaya, daga Shihor ta Masar, har zuwa mashigin Hamat domin a kawo akwatin alkawari na Allah daga Kiriyat-yeyarim. 6 Sai Dawuda tare da dukan Isra'ilawa, suka haura zuwa Ba'al, wato Kiriyat-yeyarim ta Yahuza, domin su ɗauko akwatin alkawarin Allah daga can, inda ake kira bisa sunan Ubangiji, wanda kuma yake zaune a wurin kerubobi. 7 Suka ɗauko akwatin alkawarin Allah a sabon keken shanu daga gidan Abinadab. Uzza da Ahiyo suka kora keken shanun. 8 Sai Dawuda da dukan Isra'ilawa suka yi rawa da iyakar ƙarfinsu a gaban Allah, suna raira waƙoƙi suna kaɗa, garayu, da molaye, da ganguna, da kuge, suna busa ƙaho. 9 Sa'ad da suka kai masussukar Kidon, sai Uzza ya miƙa hannunsa don ya riƙe akwatin alkawarin saboda gargada. 10 Sai Ubangiji ya husata da Uzza, ya buge shi, ya mutu nan take a gaban Allah, saboda ya miƙa hannunsa ya kama akwatin alkawari. 11 Sai Dawuda ya ɓata ransa saboda da Ubangiji ya hukunta Uzza da fushi, sai ya sa wa wannan wuri suna Feresa-uzza, wato hukuncin Uzza. 12 Sa'an nan Dawuda ya ji tsoron Allah, ya ce, “Ƙaƙa zan kawo akwatin alkawarin Allah a gidana?” 13 Don haka Dawuda bai kai akwatin alkawarin zuwa cikin birninsa ba, amma ya raɓa da shi zuwa gidan Obed-edom wanda yake daga Gat. 14 Akwatin alkawarin Allah kuwa ya kasance a gidan Obed-edom har wata uku. Ubangiji kuwa ya sa wa iyalin Obed-edom da dukan abin da yake da shi albarka.

1 Tarihi 14

Hiram da Dawuda

1 Sai Hiram Sarkin Taya ya aiki manzanni wurin Dawuda, su kai masa itatuwan al'ul, da magina, da massassaƙa domin a gina masa fāda. 2 Dawuda kuwa ya gane Ubangiji ya tabbatar masa da sarautar Isra'ila, mulkinsa kuwa ya ɗaukaka ƙwarai saboda jama'arsa, Isra'ila.

'Ya'yan da aka Haifa wa Dawuda a Urushalima

3 Dawuda kuwa ya ƙara auren waɗansu mata a Urushalima, suka haifi 'ya'ya mata da maza. 4 Ga sunayen 'ya'yan da aka haifa masa a Urushalima, Shimeya, da Shobab, da Natan, da Sulemanu, 5 da Ibhar, da Elishuwa, da Elifelet, 6 da Noga, da Nefeg, da Yafiya, 7 da Elishama, da Eliyada, da Elifelet.

Dawuda ya Ci Filistiyawa da Yaƙi

8 Sa'ad da Filistiyawa suka ji an naɗa Dawuda ya zama Sarkin Isra'ila duka, sai dukan Filistiyawa suka haura, suna neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya fita domin ya yi yaƙi da su. 9 Filistiyawa suka iso kwarin Refayawa suka fara fatali da shi. 10 Sai Dawuda ya roƙi Allah, ya ce, “In tafi in yi yaƙi da Filistiyawa? Za ka bashe su a hannuna?” Ubangiji kuwa ya amsa masa, ya ce, “Ka haura, gama zan bashe su a hannunka.” 11 Sai suka haura zuwa Ba'al-ferazim, Dawuda kuwa ya ci su da yaƙi a wurin. Sai ya ce, “Allah ya raraki maƙiyana ta hannuna, kamar yadda ruwa yakan rarake ƙasa.” Don haka aka sa wa wurin suna Ba'al-ferazim. 12 Filistiyawa suka gudu suka bar gumakansu a wurin. Dawuda kuwa ya yi umarni, aka ƙone su duka. 13 Filistiyawa kuma suka sāke kawo yaƙi a kwarin. 14 Dawuda ya sāke yin roƙo ga Allah, Allah kuwa ya ce masa, “Kada ka hau zuwa wurinsu, ka kewaye ka ɓullo musu ta baya daura da itatuwan tsamiya. 15 Sa'ad da ka ji motsi kamar na tafiyar sojoji a bisa itatuwan tsamiya, sai ka fita ka yi yaƙi, gama Allah ya wuce ta gabanka don ya bugi sojojin Filistiyawa.” 16 Dawuda fa ya yi daidai yadda Ubangiji ya umarce shi. Suka bugi sojojin Filistiyawa tun daga Geba har zuwa Gezer. 17 Sunan Dawuda kuma ya kai ko'ina cikin dukan ƙasashe. Ubangiji kuwa ya sa dukan al'ummai su ji tsoron Dawuda.

1 Tarihi 15

An Kawo Akwatin Alkawari a Urushalima

1 Dawuda kuwa ya gina wa kansa gidaje a birninsa, ya kuma kafa alfarwa domin akwatin alkawari na Allah. 2 Sai Dawuda ya ce, “Kada wani ya ɗauki akwatin alkawari na Allah sai Lawiyawa kaɗai, gama su ne Ubangiji ya zaɓa domin su riƙa ɗaukar akwatin alkawarin Ubangiji, su kuma yi masa hidima har abada.” 3 Saboda haka Dawuda ya tattara Isra'ilawa duka a Urushalima don a kawo akwatin alkawarin Ubangiji a wurinsa, inda aka riga aka shirya masa. 4 Dawuda kuma ya tattara zuriyar Haruna a wuri ɗaya, tare kuma da Lawiyawa. 5 Waɗanda aka tattaro ke nan, daga iyalin Kohat su ɗari da shirin ne. Uriyel shi ne shugabansu. 6 Daga iyalin Merari su ɗari biyu da ashirin, Asaya ne shugabansu. 7 Daga iyalin Gershon ɗari da talatin, Yowel ne shugabansu. 8 Daga iyalin Elizafan ɗari biyu, Shemaiya ne shugabansu. 9 Daga iyalin Hebron su tamanin, Eliyel ne shugabansu. 10 Daga iyalin Uzziyel ɗari da goma sha biyu, Amminadab ne shugabansu. 11 Sa'an nan Dawuda ya kira Zadok da Abiyata firistoci, da Lawiyawa, wato Uriyel, da Asaya, da Yowel, da Shemaiya, da Eliyel, da Amminadab, 12 ya ce musu, “Ku ne shugabanni na gidajen kakanninku, Lawiyawa. Sai ku tsarkake kanku da 'yan'uwanku domin ku iya kawo akwatin alkawarin Allah na Isra'ila a inda na shirya masa. 13 Gama Ubangiji Allahnmu ya fashe fushinsa a kanmu saboda ba ku ne kuka ɗauke shi a karo na farko ba, saboda kuma ba mu yi masa sujada kamar yadda aka umarta ba.” 14 Sa'an nan firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu domin su kawo akwatin alkawarin Ubangiji Allah na Isra'ila. 15 Lawiyawa fa suka ɗauki akwatin alkawarin Allah a bisa sandunansa a kafaɗunsu, kamar yadda Musa ya umarta bisa ga maganar Ubangiji. 16 Dawuda ya umarci shugabannin Lawiyawa su sa 'yan'uwansu mawaƙa su riƙa raira waƙa da murna, da kayayyakin bushe-bushe, da kaɗe-kaɗe, da molaye, da garayu, da kuge masu amon gaske. 17 Saboda haka Lawiyawa suka zaɓi Heman ɗan Yowel, da Asaf ɗan Berikiya daga cikin 'yan'uwansu. Daga iyalin Merari kuma aka zaɓi Etan ɗan Kishi. 18 Daga cikin 'yan'uwansu, har yanzu aka zaɓi mataimakansu, wato Zakariya, da Ben, da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Unno, da Eliyab, da Benaiya, da Ma'aseya, da Mattitiya, da Elifelehu, da Mikneya, da Obed-edom, da Yehiyel, da masu tsaron ƙofofi. 19 Haka aka zaɓi mawaƙa, wato Heman, da Asaf, da Etan don su buga kuge na tagulla. 20 Su Zakariya, da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Unno, da Eliyab, da Ma'aseya, da Benaiya, su ne masu kaɗa molaye da murya a sama. 21 Su Mattitiya, da Elifelehu, da Mikneya, da Obed-edom, da Yehiyel, da Azaziya suke jā da garayu da murya ƙasa-ƙasa. 22 Kenaniya shugaban Lawiyawa shi ne yake bi da waƙoƙi domin shi gwani ne. 23 Berikiya da Elkana su ne masu tsaron ƙofa ta akwatin alkawari. 24 Sai Shebaniya, da Yehoshafat, da Netanel, da Amasai, da Zakariya, da Benaiya, da Eliyezer, firistoci, suka yi ta busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah. Obed-edom da Yehiya su ne kuma masu tsaron ƙofar akwatin alkawari. 25 Haka Dawuda, da dattawan Isra'ilawa, da shugabannin dubu dubu, suka tafi da murna domin su ɗauko akwatin alkawarin Ubangiji daga gidan Obed-edom. 26 Saboda Allah ya taimaki Lawiyawa waɗanda suka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji, sai suka yi hadaya da bijimai bakwai da raguna bakwai. 27 Dawuda yana saye da kyakkyawar taguwa ta lilin tare da Lawiyawa duka waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawari, da mawaƙa, da Kenaniya shugaban mawaƙan. Dawuda kuma ya sa falmaran ta lilin. 28 Da haka fa Isra'ilawa duka suka kawo akwatin alkawarin Ubangiji, suna ta sowa, suna ta busa ƙaho, suna kaɗa kuge da molaye, da garayu. 29 Sa'ad da akwatin alkawarin Ubangiji ya shigo birnin Dawuda, sai Mikal 'yar Saul ta leƙa ta taga, ta ga sarki Dawuda yana ta rawa, yana murna, sai ta ji ya saƙali mata a zuci.

1 Tarihi 16

1 Suka fa shigo da akwatin alkawarin Allah, suka ajiye shi a cikin alfarwar da Dawuda ya kafa masa, suka miƙa hadayu na ƙonawa da na salama a gaban Allah. 2 Da Dawuda ya gama miƙa hadayar ƙonawa da ta salama, sai ya sa wa jama'a albarka da sunan Ubangiji. 3 Ya kuma rarraba wa Isra'ilawa mata da maza, gurasa, da gunduwar nama, da kauɗar zabibi. 4 Ya kuma sa waɗansu Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka Ubangiji Allah na Isra'ila, su gode masa, su kuma yabe shi. 5 Asaf shi ne shugaba, na biye da shi su ne Zakariya da Aziyel, da Shemiramot, da Yehiyel, da Mattitiya, da Eliyab, da Benaiya, da Obed-edom, da Yehiyel, waɗanda za su kaɗa molaye da garayu. Asaf kuwa shi ne mai kaɗa kuge. 6 Benaiya da Yahaziyel firistoci, su ne za su riƙa busa ƙaho a gaban akwatin alkawarin Allah.

Waƙar Yabo ta Dawuda

7 A wannan lokaci ne Dawuda ya fara sa Asaf da 'yan'uwansa su riƙa raira waƙoƙin yabo ga Ubangiji. 8 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi! 9 Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi, Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi! 10 Ku yi murna saboda mu nasa ne, Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji! 11 Ku je wurin Ubangiji neman taimako, Ku tsaya a gabansa koyaushe. 12 Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki, Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke. 13 Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu. 14 Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu, Umarnansa domin dukan duniya ne. 15 Zai cika alkawarinsa har abada, Alkawaransa kuma don dubban zamanai, 16 Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim, Da alkawarin da ya yi wa Ishaku. 17 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila, Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce, 18 “Zan ba ka ƙasar Kan'ana, Za ta zama mallakarka.” 19 Jama'ar Ubangiji kima ne, Baƙi ne kuwa a ƙasar. 20 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa, Daga wannan mulki zuwa wancan. 21 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba, Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su. 22 Ya ce, “Kada ku taɓa bayina, zaɓaɓɓu, Kada ku cuci annabawana!” 23 Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku dukan duniya, Ku yi shelar albishir na ceton da ya yi mana kowace rana. 24 Ku yi shelar ɗaukakarsa ga al'ummai, Da ayyukansa masu girma ga dukan mutane, 25 Ubangiji da girma yake, wajibi ne mu yabe shi, Dole mu yi tsoronsa fiye da dukan alloli. 26 Gama allolin dukan sauran al'umma gumaka ne, Amma Ubangiji shi ne ya halitta sammai. 27 Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi, Iko da farin ciki sun cika haikalinsa. 28 Ku yi yabon Ubangiji, ku dukan mutanen duniya, Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa! 29 Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja, Kuna kawo sadaka, kuna zuwa Haikalinsa. Ku rusuna a gaban Mai Tsarki da sahihiyar zuciya, 30 Ku yi rawar jiki a gabansa, ku dukan duniya! Hakika duniya ta kahu sosai, ba za ta jijjigu ba. 31 Duniya da sararin sama, ku yi farin ciki! Ku faɗa wa al'ummai, Ubangiji shi ne sarki. 32 Ki yi ruri, ke teku, da dukan abin da yake cikinki, Ka yi farin ciki, kai saura da dukan abin da yake cikinka. 33 Itatuwa a jeji za su yi sowa domin murna Sa'ad da Ubangiji zai zo ya yi mulki a duniya. 34 Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce! 35 Ku ce masa, “Ka cece mu, ya Allah Mai Cetonmu, Ka tattara mu, ka kuɓutar da mu daga al'ummai, Domin mu gode maka, Mu kuma yabi sunanka mai tsarki.” 36 Ku yabi Ubangiji Allah na Isra'ila! Ku yi ta yabonsa har abada abadin! Sa'an nan dukan jama'a suka ce, “Amin, Amin,” suka yabi Ubangiji.

An Zaɓi Lawiyawa domin Akwatin Alkawari

37 Dawuda ya sa Asaf tare da 'yan'uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji domin a yi hidima kullayaumin a gaban akwatin alkawarin kamar yadda aka bukaci a yi kowace rana. 38 Akwai kuma masu tsaron ƙofofi, wato Obed-edom ɗan Yedutun tare da 'yan'uwansa, su sittin da takwas, da Hosa. 39 Sai ya bar Zadok firist da 'yan'uwansa firistoci a wurin zama na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon. 40 Kowace safiya da maraice suna miƙa hadayu na ƙonawa ga Ubangiji a bisa bagaden ƙona hadaya, kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, waɗanda ya ba Isra'ilawa. 41 Tare da su kuma akwai Heman, da Yedutun, da sauran waɗanda aka zaɓa musamman domin su yi godiya ga Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa. 42 Heman da Yedutun suna lura da ƙaho, da kuge, da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin raira waƙoƙin yabo ga Allah. 'Ya'yan Yedutun, maza, su aka ba aikin tsaron ƙofa. 43 Sa'an nan dukan jama'a suka watse, kowa ya koma gidansa, Dawuda kuma ya koma gidansa, ya sa wa iyalinsa albarka.

1 Tarihi 17

Alkawarin da Allah ya yi wa Dawuda

1 Sa'ad da Dawuda yake zaune a fādarsa, sai ya ce, wa annabi Natan, “Ga shi, ni ina zaune a cikin gidan da aka yi da itacen al'ul, amma akwatin alkawarin Ubangiji yana cikin alfarwa.” 2 Natan ya amsa masa ya ce, “Ka yi duk abin da zuciyarka ta ɗauka, gama Allah yana tare da kai.” 3 Amma a wannan dare Ubangiji ya yi magana da Natan, ya ce, 4 “Ka tafi, ka faɗa wa bawana, Dawuda, cewa ni Ubangiji na ce, ‘Ba za ka gina mini ɗakin da zan zauna a ciki ba. 5 Gama tun ranar da na fito da Isra'ilawa ban taɓa zama a cikin ɗaki ba, amma daga alfarwa zuwa alfarwa, daga wannan mazauni kuma zuwa wancan. 6 A dukan wuraren da na tafi tare da Isra'ilawa, ban taɓa faɗa wa wani daga cikin hakiman Isra'ila, waɗanda na ba da umarni su yi kiwon jama'ata, cewa su gina mini ɗaki da itacen al'ul ba.’ 7 “Saboda haka fa sai ka faɗa wa bawana Dawuda cewa, ‘Ni Ubangiji Mai Runduna, na ɗauko ka daga kiwon tumaki domin ka zama sarkin jama'ata Isra'ila. 8 Na kuwa kasance tare da kai a duk inda ka tafi, na kuma hallaka maƙiyanka a gabanka. Zan sa ka shahara kamar waɗanda suka shahara a duniya. 9 Zan zaɓo wa jama'ata, wato Isra'ila, wuri, zan dasa su, su zauna a wuri na kansu, don kada a sāke damunsu, kada kuma masu mugunta su ƙara lalata su kamar dā, 10 tun lokacin da na sa hakimai su shugabanci jama'ata Isra'ila. Zan rinjayi dukan maƙiyanka. Banda wannan kuma na yi alkawari zan ci dukan maƙiyanka, in mallakar da su ga zuriyarka. 11 Sa'ad da lokacinka ya yi da za ka mutu, zan ta da ɗaya daga cikin zuriyarka, ɗaya daga cikin 'ya'yanka maza, zan kafa mulkinsa. 12 Shi ne zai gina mini Haikali, zan kafa gadon sarautarsa har abada. 13 Ni zan zama uba a gare shi, shi kuwa ya zama ɗa a gare ni, ba zan kawar masa da madawwamiyar ƙaunata ba, kamar yadda na kawar da ita daga wanda ya riga ka sarauta. 14 Zan zauna da shi a gidana da mulkina har abada. Gadon sarautarsa kuwa zai kahu har abada.’ ” 15 Natan kuwa ya faɗa wa Dawuda dukan abin da Allah ya bayyana masa.

Addu'ar Dawuda ta Godiya

16 Sarki Dawuda kuwa ya shiga alfarwa, ya zauna a gaban Ubangiji ya ce, “Wane ne ni, ya Ubangiji Allah, mene kuma gidana da za ka yi mini haka? 17 Amma wannan ƙanƙanen abu ne a gare ka, ya Allah. Ka kuma yi alkawari, cewa za ka tsawaita kwanakin zuriyar bawanka, ka ɗauke ni kamar ni wani babban mutum ne, ya Ubangiji Allah. 18 Me kuma ni Dawuda zan ƙara ce maka, a kan girman da ka ba bawanka? Gama ka san bawanka. 19 Ya Ubangiji, saboda bawanka ne, da kuma bisa ga yardar ranka, ka aikata wannan babban al'amari, domin ka bayyana waɗannan manyan abubuwa. 20 Ya Ubangiji, ba wani kamarka, ba kuma wani Allah sai kai, bisa ga duk abin da muka ji da kunnuwanmu. 21 Wace al'umma ce take a duniyar nan kamar jama'arka, Isra'ila, wadda kai, Allah, ka je ka fanshe ta, ta zama jama'arka, domin ka yi suna ta wurin manyan abubuwa masu banmamaki, kamar yadda ka kori al'ummai a gaban jama'arka, wadda ka fansa daga Masar? 22 Gama ka mai da jama'ar Isra'ila ta zama taka har abada. Kai kuma, ya Ubangiji, ka zama Allahnsu. 23 “Yanzu dai, ya Ubangiji, bari maganar da ka yi wa bawanka da gidansa ta tabbata har abada, ka kuma aikata yadda ka faɗa. 24 Bari sunanka ya kahu, ya ɗaukaka har abada, a riƙa cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna, shi ne Allah na Isra'ilawa.’ Gidan bawanka Dawuda kuma ya kahu a gabanka. 25 Gama kai, ya Allahna, ka riga ka bayyana wa bawanka, cewa za ka sa zuriyata su zama sarakuna, don haka ne, ni bawanka na sami ƙarfin halin yin wannan addu'a gare ka. 26 Yanzu dai ya Ubangiji, kai Allah ne, ka riga ka yi alkawarin wannan kyakkyawan abu gare ni, bawanka. 27 Ina roƙonka, ka sa wa gidan bawanka albarka, domin ya dawwama a gabanka, gama ya Ubangiji, abin da ka sa wa albarka, ya albarkatu ke nan har abada.”

1 Tarihi 18

Dawuda ya Faɗaɗa Mulkinsa

1 Bayan haka kuma Dawuda ya ci Filistiyawa da yaƙi, ya mallake su, ya ƙwace Gat da garuruwanta daga hannunsu. 2 Ya kuma ci Mowab da yaƙi, Mowabawa suka zama bayin Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. 3 Dawuda kuma ya ci Hadadezer, Sarkin Zoba, da yaƙi a Hamat, sa'ad da ya tafi ya kafa mulkinsa a Kogin Yufiretis. 4 Sai Dawuda ya ƙwace karusai dubu (1,000 ), da mahayan dawakai dubu bakwai (7,000 ), da sojojin ƙasa dubu ashirin (20,000 ) daga gare shi. Dawuda kuma ya yanyanke agarar dawakan da suke jan karusai, amma ya bar waɗansu dawakai daga cikinsu waɗanda suka isa jan karusai ɗari. 5 Sa'ad da Suriyawa daga Dimashƙu suka zo don su taimaki Hadadezer Sarkin Zoba, sai Dawuda ya karkashe mutum dubu ashirin da dubu biyu (22,000 ) daga cikin Suriyawan. 6 Sa'an nan Dawuda ya sa ƙungiyoyin sojoji a Suriya ta Dimashƙu, Suriyawa kuma suka zama bayin Dawuda, suka riƙa kawo masa haraji. Ubangiji kuwa ya taimaki Dawuda duk inda ya tafi. 7 Dawuda kuma ya ƙwato garkuwoyi na zinariya waɗanda barorin Hadadezer suke ɗauke da su, ya kawo su Urushalima. 8 Dawuda kuma ya kwaso tagulla mai yawan gaske daga Beta da Berotayi, biranen Hadadezer. Da su ne Sulemanu ya yi kwatarniya, da ginshiƙai, da kayayyakin Haikali. 9 Sa'ad da Toyi, Sarkin Hamat, ya ji an ce Dawuda ya riga ya ci nasara a kan sojojin Hadadezer, Sarkin Zoba, 10 sai ya aiki Adoniram ɗansa wurin sarki Dawuda, don ya gaishe shi, ya kuma yabe shi saboda ya yi yaƙi da Hadadezer, har ya ci shi, gama Hadadezer yakan yi yaƙi da Toyi. Adoniram kuwa ya kawo kayayyaki iri iri na zinariya, da na azurfa, da na tagulla. 11 Sarki Dawuda kuwa ya keɓe waɗannan ga Ubangiji, tare da azurfa da zinariya waɗanda ya kwaso daga al'umman da ya ci, wato Edom, da Mowab, da mutanen Ammon, da na Filistiya, da na Amalek. 12 Abishai ɗan Zeruya kuma ya ci nasara a kan Edomawa, mutum dubu goma sha takwas (18,000 ) a Kwarin Gishiri. 13 Sai ya sa ƙungiyoyin sojoji a Edom, dukan Edomawa kuma suka zama bayin Dawuda. Ubangiji kuwa ya taimaki Dawuda duk inda ya tafi.

Manyan Ma'aikatan Dawuda

14 Da haka Dawuda ya yi mulki bisa dukan Isra'ila. Ya yi wa dukan jama'arsa adalci da gaskiya. 15 Yowab ɗan Zeruya shi ne shugaban sojoji, Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubuci. 16 Zadok ɗan Ahitub da Ahimelek ɗan Abiyata su ne firistoci, Seraiya kuwa shi ne magatakarda. 17 Benaiya ɗan Yehoyada shi ne shugaban Keretiyawa da Feletiyawa, wato matsara. 'Ya'yan Dawuda, maza, su ne manyan ma'aikata na kusa da shi.

1 Tarihi 19

Dawuda ya Ci Ammonawa da Suriyawa

1 Bayan haka kuma Nahash Sarkin Ammonawa ya rasu, ɗansa kuma ya gāji sarautarsa. 2 Sa'an nan Dawuda ya ce, “Zan nuna alheri ga Hanun ɗan Nahash, gama tsohonsa ya nuna mini alheri.” Don haka Dawuda ya aiki manzanni su yi wa Hanun ta'aziyyar rasuwar tsohonsa. Fādawan Dawuda suka zo ƙasar Ammon wurin Hanun, domin su yi masa ta'aziyya. 3 Amma hakiman Ammonawa suka ce wa Hanun, “Kana tsammani Dawuda yana girmama tsohonka ne da ya aiko manzanni su yi maka ta'aziyya? Fādawansa sun zo wurinka ne don su leƙi asirin ƙasar, su bincike ta, su ci ta da yaƙi.” 4 Hanun kuwa ya kama fādawan Dawuda, ya aske gyammansu, ya yanyanke rigunansu a tsaka daga wajen kwankwaso, sa'an nan ya sallame su. 5 Waɗansu mutane kuwa suka je suka faɗa wa Dawuda abin da ya sami mutanen. Sai ya aiko a tarye su, gama an ƙasƙanta mutanen nan da gaske. Sai sarki ya ce, “Ku zauna a Yariko, har lokacin da gyammanku suka tohu sa'an nan ku iso.” 6 Sa'ad da Ammonawa suka ga sun mai da kansu abin ƙi ga Dawuda, sai Hanun da Ammonawa suka aika da talanti dubu (1,000 ) na azurfa don su yi ijara da karusai da mahayan dawakai daga Mesofotamiya, da jihohin Ma'aka ta Suriya, da Zoba. 7 Suka yi ijarar karusai dubu talatin da dubu biyu (32,000 ), da Sarkin Ma'aka, tare da jama'arsa. Suka zo suka kafa sansani a gaban Medeba. Ammonawa kuwa suka tattaru daga biranensu don su yi yaƙi. 8 Da Dawuda ya ji labari, sai ya aiki Yowab tare da dukan sojoji, ƙarfafan mutane. 9 Sai Ammonawa suka fito suka jā dāga a ƙofar birninsu. Sarakunan da suka zo suka ware suka zauna a saura. 10 Da Yowab ya ga an kafa masa yaƙi gaba da baya, sai ya zaɓi waɗansu jarumawa na gaske a Isra'ila, ya sa su su kara da Suriyawa. 11 Sa'an nan ya sa sauran sojoji a hannun Abishai ɗan'uwansa. Suka jā dāgar yaƙi da Ammonawa. 12 Yowab ya ce wa Abishai, “Idan Suriyawa sun fi ƙarfina, to, sai ka taimake ni, amma idan Ammonawa sun fi ƙarfinka, to, sai in taimake ka. 13 Mu yi ƙarfin hali, mu yi jaruntaka saboda jama'armu da biranen Allahnmu. Bari Ubangiji ya yi abin da ya ga ya yi masa kyau.” 14 Yowab da jama'ar da suke tare da shi suka matso don su yi yaƙi da Suriyawa, sai Suriyawa suka gudu daga gabansu. 15 Da Ammonawa suka ga Suriyawa sun gudu, su ma suka gudu daga gaban Abishai, ɗan'uwan Yowab, suka shiga birni. Sa'an nan Yowab ya komo Urushalima. 16 Da Suriyawa suka ga Isra'ilawa sun ci su da yaƙi sai suka aiki manzanni suka kira Suriyawa waɗanda suke hayin kogi. Shobak shugaban sojojin Hadadezer ne yake shugabantarsu. 17 Sa'ad da aka faɗa wa Dawuda, sai ya tattara Isra'ilawa duka ya haye Urdun, ya zo wurinsu, ya jā dāga don ya yi yaƙi da su. Aka fara gabza yaƙi, 18 sai Suriyawa suka gudu a gaban Isra'ilawa, Dawuda ya karkashe Suriyawa, mutum dubu bakwai (7,000 ) masu karusai, da sojojin ƙasa dubu arba'in (40,000 ). Ya kuma kashe Shobak shugaban sojojin. 19 Da barorin Hadadezer suka ga Isra'ilawa sun ci su da yaƙi, sai suka ƙulla zumunci da Dawuda, suka bauta masa. Saboda haka Suriyawa ba su ƙara yarda su taimaki Ammonawa ba.

1 Tarihi 20

Dawuda ya Ci Rabba

1 Da bazara, lokacin da sarakuna sukan fita su yi yaƙi, sai Yowab ya tafi da sojoji suka lalatar da ƙasar Ammonawa. Suka tafi, suka kewaye Rabba da yaƙi. Amma Dawuda ya yi zamansa a Urushalima. Yowab ya bugi Rabba ya yi nasara da ita. 2 Sai Dawuda ya ciro kambi daga kan sarkinsu, sai ya iske nauyinsa talanti ɗaya na zinariya ne, akwai kuma duwatsu masu daraja a cikinsa. Dawuda ya sa kambin a kansa. Ya kwaso ganima da yawa a birnin. 3 Ya kuma fito da mutanen da suke ciki, ya yanyanka su da zartuna da makamai masu kaifi, da gatura. Haka Dawuda ya yi wa dukan biranen Ammonawa. Sa'an nan Dawuda da dukan jama'a suka koma Urushalima.

Yaƙi da Gwarzayen Filistiyawa

4 Bayan wannan kuma, sai yaƙi ya tashi a Gat tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa, sai Sibbekai mutumin Husha ya kashe Siffai, ɗaya daga cikin zuriyar ƙattin nan. Aka ci Filistiyawa. 5 Yaƙi kuma ya sāke tashi tsakanin Isra'ilawa da Filistiyawa, sai Elhanan ɗan Yayir, ya kashe Lahmi ɗan'uwan Goliyat daga Gat, wanda yake gorar māshinsa ta yi ya dirkar masaƙa. 6 Yaƙi ya sāke tashi a Gat, inda wani cindo, ƙaton mutum yake. Yana da yatsotsi ashirin da huɗu, wato a kowane hannu yana da yatsa shida, hakanan kuma a kowace ƙafarsa. Shi kuma daga zuriyar ƙattin nan ne. 7 Sa'ad da ya yi wa mutanen Isra'ila ba'a, sai Jonatan ɗan Shimeya, wato ɗan'uwan Dawuda, ya kashe shi. 8 Waɗannan uku ne Dawuda da jama'arsa suka kashe daga zuriyar ƙattin na Gat.

1 Tarihi 21

Dawuda ya Ƙidaya Mutane

1 Shaiɗan ya tashi gaba da Isra'ila, sai ya iza Dawuda ya ƙidaya Isra'ilawa. 2 Dawuda fa ya ce wa Yowab da sauran shugabannin jama'a, “Ku tafi, ku ƙidaya jama'ar Isra'ila tun daga Biyer-sheba har zuwa Dan, ku kawo mini labari don in san yawansu.” 3 Amma Yowab ya ce, “Ubangiji ya riɓaɓɓanya yawan jama'arsa har sau ɗari bisa kan yadda suke a yanzu! Ranka ya daɗe, ya sarki, ashe, dukkansu ba naka ba ne? Me zai sa shugabana ya so a yi haka? Me zai sa ya zama sanadin tuntuɓe ga mutanen Isra'ila?” 4 Duk da haka, sarki ya sa Yowab ya bi umarninsa. Sai Yowab ya tashi, ya bibiya ƙasar Isra'ila duka, sa'an nan ya komo Urushalima. 5 Yowab ya kawo wa Dawuda adadin yawan mutanen. Jimillar dukan Isra'ila zambar dubu ne da dubu ɗari (1,100,000 ) waɗanda za su iya yaƙi. Jimillar mutanen Yahuza kuwa dubu ɗari huɗu da dubu saba'in ne (470,000 ) waɗanda suka isa zuwa yaƙi. 6 Amma bai ƙidaya Lawiyawa da mutanen Biliyaminu ba, domin Yowab bai ji daɗin umarnin sarki ba. 7 Allah bai ji daɗin wannan al'amari ba, don haka sai ya bugi Isra'ila. 8 Sai Dawuda ya ce wa Allah, “Na yi zunubi ƙwarai saboda abin nan da na aikata. Amma ina roƙonka ka gafarta mini laifina, gama na yi aikin wauta ƙwarai da gaske.” 9 Sa'an nan Ubangiji ya yi magana da Gad, annabin Dawuda, ya ce, 10 “Je ka ka faɗa wa Dawuda, ka ce, ‘Ubangiji yana so ka zaɓi ɗaya daga cikin abu uku, wanda zai yi maka.’ ” 11 Gad kuwa ya tafi wurin Dawuda ya ce masa, “Ubangiji ya ce, ka zaɓa, 12 ko shekara uku na yunwa, ko kuwa ka sha ɗibga a hannun maƙiyanka har wata uku, maƙiyanka su yi ta fafararka, ko kwana uku na takobin Ubangiji, wato annoba ke nan da zai aukar wa ƙasar, mala'ikan Ubangiji zai yi ta hallakarwa ko'ina a ƙasar Isra'ila. Yanzu fa, sai ka yi tunani, ka ba ni amsar da zan mayar wa wanda ya aiko ni.” 13 Dawuda kuwa ya ce wa Gad, “Na shiga uku, gara in fāɗa a hannun Ubangiji, gama shi mai yawan jinƙai ne, kada ka bar ni in faɗa a hannun mutum.” 14 Saboda haka Ubangiji ya aiko da annoba a kan Isra'ila. Mutum dubu saba'in (70,000 ) na Isra'ila suka mutu. 15 Allah ya aiko mala'ikansa don ya hallaka Urushalima, amma sa'ad da yake gab da hallaka ta, sai Ubangiji ya gani, ya janye shirin annobar, ya ce wa mala'ikan hallakarwa, “Ya isa, janye hannunka.” Mala'ikan Ubangiji kuwa na tsaye kusa da masussukar Arauna Bayebuse. 16 Dawuda ya ɗaga idonsa, sai ya ga mala'ikan Ubangiji yana tsakanin sama da ƙasa, da takobinsa a zare a hannunsa a kan Urushalima. Sa'an nan Dawuda tare da dattawa suka fāɗi rubda ciki, suna saye da tufafin makoki. 17 Dawuda ya ce wa Allah, “Ai, ni ne na ba da umarni a ƙidaya jama'ar. Hakika, ni na yi zunubi, na kuwa aikata mummunan abu, amma waɗannan talakawa fa, me suka yi? Ya Ubangiji Allahna, ka bar hannunka ya yi gāba da ni da gidan tsohona, amma kada ka yi gāba da jama'arka, har da za ka aukar musu da annoba.” 18 Mala'ikan Ubangiji ya umarci Gad ya faɗa wa Dawuda ya haura, ya gina wa Ubangiji bagade a masussukar Arauna Bayebuse. 19 Dawuda kuwa ya haura kamar yadda Gad ya faɗa masa da sunan Ubangiji. 20 Arauna yana cikin sussukar alkama, sai ya waiwaya ya ga mala'ika. 'Ya'yansa maza su huɗu kuwa, waɗanda suke tare da shi suka ɓuya. 21 Sa'ad da Dawuda ya tafi wurin Arauna, da Arauna ya ga Dawuda, sai ya fito daga masussukar ya tafi ya fāɗi rub da ciki a gaban Dawuda ya gaishe shi. 22 Sai Dawuda ya ce masa, “Ka ba ni wannan masussuka don in gina wa Ubangiji bagade. Ka sayar mini da masussukar a bakin cikakken kuɗinta, domin a kawar wa jama'a da annobar.” 23 Arauna ya ce wa Dawuda, “Ka karɓa, na ba ka, sai ka yi abin da kake so da ita, ranka ya daɗe. Zan kuma ba da bijimai domin hadayu na ƙonawa, in ba da keken sussuka domin itacen wuta, in kuma ba da alkama don hadaya ta gari. Zan ba ka waɗannan duka.” 24 Amma sarki Dawuda ya ce wa Arauna, “A'a, zan biya cikakken kuɗinta. Ba zan karɓi abinka kawai in ba Ubangiji ba, ba kuwa zan miƙa masa hadayu na ƙonawa da abin da ban biya ba.” 25 Sai Dawuda ya biya Arauna shekel ɗari shida na zinariya domin masussukar. 26 Dawuda ya gina wa Ubangiji bagade a wurin, ya miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama. Sai ya yi roƙo ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya amsa masa ta wurin wutar da ta sauko daga sama a bisa bagaden hadayar ta ƙonawa. 27 Sa'an nan Ubangiji ya umarci mala'ikan, shi kuwa ya mai da takobinsa a kube.

Inda za a Yi Haikalin

28 Da Dawuda ya ga Ubangiji ya amsa masa a masussukar Arauna Bayebuse, sai ya miƙa hadaya a wurin. 29 Gama wurin zama na Ubangiji wanda Musa ya yi a jeji, da bagaden hadaya ta ƙonawa suna cikin masujada a Gibeyon. 30 Dawuda bai iya zuwa wurin don ya yi tambaya ga Allah ba, saboda yana jin tsoron takobin mala'ikan Ubangiji.

1 Tarihi 22

1 Sa'an nan sai Dawuda ya ce, “A nan Haikalin Ubangiji Allah zai kasance, da kuma bagaden ƙona hadaya domin Isra'ila.”

Shirye-shiryen da Dawuda ya Yi don Gina Haikali

2 Dawuda kuwa ya umarta a tattaro dukan baƙin da suke a ƙasar Isra'ila. Ya sa waɗansu su farfasa duwatsu, su sassaƙe duwatsun domin ginin Haikalin Allah. 3 Dawuda kuma ya cika manyan ɗakunan ajiya da ƙarafa don yin ƙusoshi na ƙyamaren ƙofofi, da mahaɗai, ya kuma tara tagulla mai yawa wanda ta fi ƙarfin awo, 4 da katakan al'ul da ba a san adadinsu ba, gama Sidoniyawa da mutanen Taya sun kawo wa Dawuda itacen al'ul mai ɗumbun yawa. 5 Dawuda kuwa ya ce, “Ɗana Sulemanu yaro ne, bai gogu da duniya ba. Ga shi, Haikalin da za a gina wa Ubangiji zai zama mai ƙayatarwa ƙwarai, zai zama sananne mai daraja cikin dukan ƙasashe, saboda haka sai in tanada masa.” Domin haka Dawuda ya tara kayayyakin gini masu ɗumbun yawa kafin rasuwarsa. 6 Sai Dawuda ya kira Sulemanu ɗansa, ya yi masa wasiyyar gina Haikalin Ubangiji, Allah na Isra'ila. 7 Dawuda kuwa ya ce wa Sulemanu, “Ɗana, na ƙudura a zuciyata in gina Haikali saboda sunan Ubangiji Allah. 8 Amma Ubangiji ya ce mini, ‘Ka zubar da jini da yawa, ka yi manyan yaƙe-yaƙe, don haka ba za ka gina Haikali saboda sunana ba, gama a gabana ka zubar da jini mai yawa a duniya. 9 Za a haifa maka ɗa, zai zama mutumin salama. Zan kuwa ba shi zaman lafiya da abokan gāba da suke kewaye da shi, gama za a ce da shi Sulemanu, wato salama. Zan kawo wa Isra'ila salama, da natsuwa a zamaninsa. 10 Shi zai gina Haikali saboda sunana. Zai zama ɗana, ni kuwa zan zama uba a gare shi, zan kafa gadon sarautarsa a Isra'ila har abada.’ 11 “To, ɗana, Ubangiji ya kasance tare da kai, domin ka yi nasara ka gina Haikalin Ubangiji Allahnka, kamar yadda ya faɗa a kanka. 12 Ubangiji dai ya ba ka basira da haziƙanci domin sa'ad da ya sa ka ka lura da Isra'ila ka kiyaye dokokinsa. 13 Za ka arzuta idan ka kula ka kiyaye dokoki da ka'idodi da Ubangiji ya umarci Musa saboda Isra'ila. Ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali. Kada ka ji tsoro, kada kuma ka karaya. 14 Da wahala mai yawa na yi tanadi domin Haikalin Ubangiji, zinariya wajen talanti dubu ɗari (100,000 ), da azurfa kuma wajen talanti zambar dubu (1,000,000 ), domin gina Haikalin Ubangiji. Bayan wannan akwai tagulla da ƙarfe masu tarin yawa. Na kuma tanada katakai da duwatsu. Kai kuma sai ka ƙara a kansu. 15 Kana da ma'aikata jingim, su masu fasa duwatsu, da magina, da masassaƙa, da gwanayen masu sana'o'i iri dabam dabam, masu yawan gaske. 16 Za su yi aiki da zinariya, da azurfa, da tagulla, da ƙarfe. Tashi, ka kama aiki, Ubangiji ya kasance tare da kai!” 17 Dawuda kuma ya umarci dukan shugabannin Isra'ila su taimaki ɗansa Sulemanu. 18 Ya ce, “Ubangiji Allahnku yana tare da ku, ya ba ku zaman lafiya a kowane sashi. Gama ya ba da mazaunan ƙasar a hannuna, an murƙushe ƙasar a gaban Ubangiji da jama'arsa. 19 Yanzu fa sai ku sa hankalinku da zuciyarku ga neman Ubangiji Allahnku. Ku tashi, ku gina wa Ubangiji Allah tsattsarkan wuri domin a kawo akwatin alkawari na Ubangiji, da tsarkakakkun tasoshin Allah a cikin Haikalin da aka gina saboda sunan Ubangiji.”

1 Tarihi 23

1 Sa'ad da Dawuda ya tsufa, yana da shekaru da yawa, sai ya naɗa ɗansa Sulemanu ya zama Sarkin Isra'ila.

Ayyukan Lawiyawa

2 Dawuda kuwa ya tattara dukan shugabannin Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa. 3 Aka ƙidaya Lawiyawa maza tun daga mai shekara talatin har sama, jimillarsu dubu talatin da dubu takwas (38,000 ). 4 Sai Dawuda ya ce dubu ashirin da dubu huɗu (24,000 ) daga cikinsu za su yi hidimar Haikalin Ubangiji, dubu shida (6,000 ) kuma su zama manyan ma'aikata da alƙalai, 5 dubu huɗu (4,000 ) su zama matsaran ƙofofi, dubu huɗu (4,000 ) kuma za su zama masu raira yabbai ga Ubangiji da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe waɗanda ya yi. 6 Dawuda kuwa ya kasa su kashi kashi bisa ga 'ya'yan Lawi maza, wato Gershon, da Kohat, da Merari. 7 'Ya'yan Gershon maza, su ne Libni da Shimai. 8 'Ya'yan Libni, maza, su ne Yehiyel, shi ne babba, da Zetam, da Yowel, su uku. 9 'Ya'yan Shimai, maza kuwa, su ne Shelomit, da Heziyel, da Haran, su uku. Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu, Libni. 10 'Ya'yan Shimai, maza, su ne Yahat, da Zaina, da Yewush, da Beriya. 'Ya'yan Shimai, maza, ke nan, su huɗu. 11 Yahat shi ne babba, Zaina shi ne na biyu, amma Yewush, da Beriya ba su da 'ya'ya da yawa, saboda haka ana lasafta su a haɗe gida ɗaya. 12 'Ya'yan Kohat, maza, su ne Amram, da Izhara, da Hebron, da Uzziyel, su huɗu ke nan. 13 'Ya'yan Amram, maza, su ne Haruna, da Musa. Aka keɓe Haruna domin ya tsarkake abubuwa mafi tsarki, domin shi da 'ya'yansa za su ƙone turare a gaban Ubangiji, su yi masa hidima, su riƙa sa albarka da sunansa har abada. 14 Amma 'ya'yan Musa mutumin Allah, an lasafta su tare da kabilar Lawi. 15 'Ya'yan Musa, maza, ke nan, Gershom da Eliyezer. 16 Ɗan Gershom babba shi ne Shebuwel. 17 Ɗan Eliyezer shi ne Rehabiya, shugaba, shi Eliyezer ba shi da waɗansu 'ya'ya, amma Rehabiya yana da 'ya'ya da yawa. 18 Ɗan Izhara shi ne Shelomit, shugaba. 19 'Ya'yan Hebron, maza, su ne Yeriya, shi ne babba, da Amariya na biyu, da Yahaziyel na uku, da kuma Yekameyam na huɗu. 20 'Ya'yan Uzziyel, maza, su ne Mika, da Isshiya. 21 'Ya'yan Merari, su ne Mali da Mushi. 'Ya'yan Mali su ne Ele'azara da Kish. 22 Ele'azara kuwa ya rasu ba shi da 'ya'ya maza, sai 'yan mata kaɗai, sai 'yan'uwansu, 'ya'yan Kish, maza, suka aure su. 23 'Ya'yan Mushi, maza, su uku ne, wato Mali, da Eder, da Yerimot. 24 Waɗannan su ne 'ya'yan Lawi, maza, bisa ga gidajen kakanninsu, wato su ne shugabannin da aka rubuta sunayensu ɗaya ɗaya daga mai shekara ashirin da haihuwa zuwa sama. Su ne za su yi hidima a cikin Haikalin Ubangiji. 25 Gama Dawuda ya ce, “Ubangiji Allah na Isra'ila ya hutar da jama'arsa, yana kuwa zama a Urushalima har abada. 26 Yanzu Lawiyawa ba za su riƙa ɗaukar alfarwar sujada tare da kayayyakin yin aiki a cikinta ba.” 27 Bisa ga maganar Dawuda ta ƙarshe aka ƙidaya 'ya'yan Lawiyawa, maza, daga mai shekara ashirin zuwa sama. 28 Aikinsu shi ne su taimaki 'ya'yan Haruna, maza, gudanar da aiki cikin Haikalin Ubangiji, wato lura da farfajiyoyi da ɗakuna, da tsabtace tsarkakan abubuwa, da yin taimako cikin kowace hidimar Haikalin Ubangiji. 29 Za su kuma taimaka wajen gurasar ajiyewa, da lallausan gari na hadaya ta gari, da waina marar yisti, da abin da akan toya, da abin da akan kwaɓa, da ma'aunan nauyi da na girma. 30 Za su kuma riƙa tsayawa kowace safiya su yi godiya, su kuma yabi Ubangiji. Haka kuma za su riƙa yi da maraice, 31 da kuma lokacin miƙa wa Ubangiji hadayun ƙonawa a ranakun Asabar, da lokacin tsayawar amaryar wata, da lokacin ƙayyadaddun idodi, za su tsaya a gaban Ubangiji bisa ga yawansu da ake bukata. 32 Su ne za su riƙa lura da alfarwa ta sujada, da Wuri Mai Tsarki, za su kuma taimaki 'ya'yan Haruna, maza, 'yan'uwansu, da yin hidimar Haikalin Ubangiji.

1 Tarihi 24

Ayyukan da aka Raba wa Firistoci

1 Ga yadda 'ya'yan Haruna, maza, suka karkasu. 'Ya'yan Haruna, maza, su ne Nadab, da Abihu, da Ele'azara, da Itamar. 2 Amma Nadab da Abihu sun riga mahaifinsu mutuwa, ba su kuma da 'ya'ya. Saboda haka Ele'azara da Itamar suka shiga aikin firistoci. 3 Sai Dawuda da Zadok daga zuriyar Ele'azara, da Ahimelek daga zuriyar Itamar suka karkasa su bisa ga ƙayyadaddun lokatansu na yin aiki. 4 Tun da yake akwai manyan mutane da yawa a zuriyar Ele'azara fiye da zuriyar Itamar, sai suka karkasa su haka, shugabannin gidajen kakannin zuriyar Ele'azara mutum goma sha shida, na zuriyar Itamar kuwa su takwas, bisa ga gidajen kakanninsu. 5 Da haka aka karkasa su ta hanyar kuri'a gama akwai ma'aikatan Wuri Mai Tsarki da kuma ma'aikata na Allah daga zuriyar Ele'azara da zuriyar Itamar. 6 Shemaiya, ɗan Netanel marubuci, Balawe, ya rubuta su a gaban sarki da shugabanni, da Zadok firist, da Ahimelek ɗan Abiyata, da shugabannin gidajen kakannin firistoci, da Lawiyawa. Aka ɗauki gida guda daga gidajen kakannin Ele'azara, aka kuma ɗauki ɗaya daga gidajen kakannin Itamar. 7-18 Ga yadda aka shirya ƙungiyoyin iyali ashirin da huɗu su sami aikinsu, 1 ) Yehoyarib, 2 ) Yedaiya, 3 ) Harim, 4 ) Seyorim, 5 ) Malkiya, 6 ) Mijamin, 7 ) Hakkoz, 8 ) Abaija, 9 ) Yeshuwa, 10 ) Shekaniya, 11 ) Eliyashib, 12 ) Yakim, 13 ) Huffa, 14 ) Yeshebeyab, 15 ) Bilga, 16 ) Immer, 17 ) Hezir, 18 ) Haffizzez, 19 ) Fetahiya, 20 ) Yehezkel, 21 ) Yakin, 22 ) Gamul, 23 ) Delaiya, 24 ) Ma'aziya. 19 Waɗannan suna da aikin da aka ba su na hidimar Haikalin Ubangiji bisa ga ka'idar da kakansu Haruna ya kafa musu, kamar yadda Ubangiji Allah na Isra'ila ya umarce shi. 20 Sauran 'ya'yan Lawi, maza, na wajen Amram, shi ne Shebuwel. Na wajen Shebuwel, shi ne Yedaiya. 21 Na wajen Rehabiya, shi ne Isshiya, 22 Na wajen Izhara, shi ne Shelomit, na wajen Shelomit, shi ne Yahat. 23 Na wajen Hebron, su ne Yeriya na fari, da Amariya, da Yahaziyel, da Yekameyam. 24 Na wajen Uzziyel, shi ne Mika, na wajen Mika, shi ne Shamir. 25 Ɗan'uwan Mika, shi ne Isshiya. Na wajen Isshiya, shi ne Zakariya. 26 Na wajen Merari, Mali da Mushi, da Yayaziya. Na wajen Yayaziya, shi ne Beno. 27 Na wajen Merari, wato na wajen Yayaziya, su ne Beno, da Shoham, da Zakkur, da Ibri. 28 Na wajen Mali, shi ne Ele'azara wanda ba shi da 'ya'ya maza. 29 Na wajen Kish, ɗan Kish, shi ne Yerameyel. 30 'Ya'yan Mushi, maza, su ne Mali, da Eder, da Yerimot. Waɗannan su ne 'ya'yan Lawiyawa, maza, bisa ga gidajen kakanninsu. 31 Su ma suka jefa kuri'a kamar yadda 'yan'uwansu, 'ya'yan Haruna, maza, suka yi a gaban sarki Dawuda, da Zadok, da Ahimelek, da shugabannin gidajen kakanni na firistoci da na Lawiyawa. Shugaban gidan kakanni ya jefa kuri'a daidai da ƙanensa.

1 Tarihi 25

Ƙungiyoyin Mawaƙa

1 Dawuda fa da shugabannin Lawiyawa suka zaɓi waɗansu daga cikin 'ya'yan Asaf, maza, da na Heman, da na Yedutun domin su raira waƙa da garayu, da molaye, da kuge. Ga waɗanda suka yi wannan hidima. 2 Daga cikin 'ya'yan Asaf, maza, Zakkur, da Yusufu, da Netaniya, da Asharela, Asaf mahaifinsu ne yake bi da su, shi ne kuma mawaƙin sarki. 3 Na wajen Yedutun, su ne 'ya'yan Yedutun, maza, wato Gedaliya, da Zeri, da Yeshaya, da Shimai, da Hashabiya, da Mattitiya, su shida ne. Mahaifinsu Yedutun shi ne yake bi da su, shi ne kuma mai raira waƙoƙi da garaya domin godiya da yabon Ubangiji. 4 Na wajen Heman, su ne 'ya'yan Heman, maza, wato Bukkiya, da Mattaniya, da Uzziyel, da Shebuwel, da Yerimot, da Hananiya, da Hanani, da Eliyata, da Giddalti, da Romamti-yezer, da Yoshbekasha, da Malloti, da Hotir, da Mahaziyot. 5 Allah ya ba Heman, wato annabin sarki, 'ya'ya maza su goma sha huɗu, da 'ya'ya mata su uku, kamar yadda ya yi alkawari, domin ya ba Heman iko. 6 Dukansu tsohonsu ne yake bi da su da raira waƙoƙi, da kaɗa kuge, da molaye da garayu, cikin Haikalin Ubangiji, domin yin sujada. Asaf, da Yedutun, da Heman suna ƙarƙashin umarnin sarki. 7 Jimillar horarrun mawaƙa don raira waƙa ga Ubangiji, su da 'yan'uwansu, duka waɗanda suke ƙwararru, su ɗari biyu da tamanin da takwas ne. 8 Sai suka jefa kuri'a domin su ba kowa aikin da zai yi, yaro da babba, malami da almajiri. 9-31 Waɗannan su ne shugabannin ƙungiyoyi ashirin da huɗu, na goma sha biyu biyu, bisa ga yadda aka tsara su ga aikin. 1 ) Yusufu daga iyalin Asaf, 2 ) Gedaliya, 3 ) Zakkur, 4 ) Zeri, 5 ) Netaniya, 6 ) Bukkiya, 7 ) Asharela, 8 ) Yeshaya, 9 ) Mattaniya, 10 ) Shimai, 11 ) Uzziyel, 12 ) Hashabiya, 13 ) Shebuwel, 14 ) Mattitiya, 15 ) Yeremot, 16 ) Hananiya, 17 ) Yoshbekasha, 18 ) Hanani, 19 ) Malloti, 20 ) Eliyata, 21 ) Hotir, 22 ) Giddalti, 23 ) Mahaziyot, 24 ) Romamtiyezer.

1 Tarihi 26

Masu Tsaron Haikali da Shugabanni

1 Ƙungiyoyin masu tsaron ƙofofi ke nan. Na wajen Kora shi ne Shallum ɗan Kore, daga cikin iyalin Ebiyasaf. 2 Shallum kuwa yana da 'ya'ya maza, su ne Zakariya, da Yediyayel, da Zabadiya, da Yatniyel, 3 da Elam, da Yehohanan, da Eliyehoyenai, su bakwai ke nan. 4 Obed-edom kuma Allah ya ba shi 'ya'ya maza, su ne Shemaiya, da Yehozabad, da Yowa, da Sakar, da Netanel, 5 da Ammiyel, da Issaka, da Fauletai, da su Allah ya sa masa albarka. 6 Ɗan farin Obed-edom, wato Shemaiya ya haifi 'ya'ya maza waɗanda suka yi shugabanci a gidan kakansu, gama su jarumawa ne. 7 'Ya'yan Shemaiya, su ne Otni, da Refayel, da Obida, da Elzabad, waɗanda 'yan'uwansu, Elihu, da Semakiya jarumawa ne. 8 Waɗannan duka iyalin Obed-edom ne. Su da 'ya'yansu maza da 'yan'uwansu suna da ƙarfi da gwaninta na yin aiki. Su sittin da biyu ne daga wajen Obed-edom. 9 Shallum yana da 'ya'ya maza da 'yan'uwa, su goma sha takwas jarumawa. 10 Hosa kuma na wajen 'ya'yan Merari, maza, yana da 'ya'ya maza, Shimri shi ne babba, ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, duk da haka mahaifinsa ya maishe shi babba. 11 Hilkiya shi ne na biyu, da Tebaliya na uku, da Zakariya na huɗu. Dukan 'ya'yan Hosa, maza, da 'yan'uwansa, su goma sha uku ne. 12 Aka rarraba masu tsaron Haikali ƙungiya ƙungiya, bisa ga iyali, aka raba musu ayyuka a Haikali kamar dai sauran Lawiyawa. 13 Sai suka jefa kuri'a bisa ga gidajen kakanninsu, ba a damu da yawan jama'a a iyali ba, a kan kowace ƙofar. 14 Kuri'a ta ƙofar gabas ta faɗo a kan Shallum. Sai aka jefa kuri'a don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma'ana, sai kuri'a ta ƙofar arewa ta faɗo a kansa. 15 Kuri'a ta ƙofar kudu ta faɗo a kan Obed-edom. Aka sa 'ya'yansa maza su lura da ɗakunan ajiya. 16 Kuri'a ta ƙofar yamma kusa da Ƙofar Shalleket, a kan hanyar da ta haura, ta faɗo a kan Shuffim da Hosa. Aka raba aikin tsaro bisa ga lokatan da aka tsara bi da bi. 17 A kowace rana Lawiyawa shida suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu biyu suke tsaron ɗakunan ajiya. 18 A ɗan ɗakin da yake wajen yamma, akwai masu tsaro huɗu a hanyar, biyu kuma a ɗan ɗakin. 19 Waɗannan su ne ƙungiyoyin masu tsaron ƙofofi daga zuriyar Kora da ta Merari.

Sauran Ayyukan Haikali

20 Sauran Lawiyawa, 'yan'uwansu kuwa, suke lura da baitulmalin Haikalin Allah, da ɗakin ajiyar kayan da aka keɓe ga Allah. 21 Libni daga cikin iyalin Gershon, shi ne kakan ƙungiyoyin iyali da dama, iyalin Yehiyel ne ɗaya daga cikinsu. 22 Biyu daga cikin wannan iyali, wato Zetam da Yowel, suke lura da baitulmalin Haikali da ɗakin ajiyar kaya. 23 Aka raba aiki kuma ga zuriyar Amram, da ta Izhara, da ta Hebron, da kuma ta Uzziyel. 24 Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami'in baitulmalin. 25 Ta wurin ɗan'uwan Gershom, wato Eliyezer ya sami dangantaka da Shelomit. Eliyezer shi ne mahaifin Rehabiya, wanda ya haifi Yeshaya, uban Yoram, da Zikri, da Shelomit. 26 Shi wannan Shelomit da 'yan'uwansa suke lura da kyautai waɗanda sarki Dawuda, da shugabannin, gidajen kakanni, da shugabannin dubu dubu, da na ɗari ɗari, da shugabannin sojoji suka keɓe ga Allah. 27 Daga cikin ganimar yaƙi suka keɓe wani sashi domin gyaran Haikalin Ubangiji. 28 Dukan kuma abin da Sama'ila annabi, da Saul ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruya, suka keɓe an sa su a hannun Shelomit da 'yan'uwansa.

Ayyukan Sauran Lawiyawa

29 Kenaniya da 'ya'yansa maza na wajen Izhara su ne aka danƙa wa al'amuran sasantawa na Isra'ilawa, wato sun zama shugabanni da alƙalai. 30 Hashabiya da 'yan'uwansu, su dubu da ɗari bakwai (1,700 ), gwanaye ne, daga zuriyar Hebron, su ne suke lura da Isra'ilawan yamma da Urdun a kan aikin Ubangiji da na sarki. 31 Yeriya shi ne shugaban zuriyar Hebron bisa ga asalinsu. A shekara ta arba'in ta sarautar Dawuda, sai aka bincika, aka tarar akwai ƙarfafan mutane, jarumawa a cikinsu, a Yazar ta Gileyad. 32 Sarki Dawuda ya sa shi, shi da 'yan'uwansu su dubu biyu da ɗari bakwai (2,700 ) gwanaye, waɗanda suke shugabancin gidajen kakanni, su lura da kabilar Ra'ubainu, da ta Gad, da rabin kabilar Manassa a kan dukan ayyukan Allah da na sarki.

1 Tarihi 27

Manyan Ma'aikatan Mulki

1 Ga lissafin kawunan iyalin Isra'ilawa, da shugabannin dangi, da jama'a masu gudanar da ayyukan mulki. A kowane wata akan sauya aikin ƙungiyar mutum dubu ashirin da dubu huɗu (24,000 ), a ƙarƙashin shugaban aiki na wannan wata. Kowane wata akan sauya, wata ƙungiya ta kama aiki. 2-15 Waɗannan su ne shugabanni don kowane wata. Wata na 1, Yashobeyam, ɗan Zabdiyel. (Shi daga dangin Feresa na kabilar Yahuza ne.) Wata na 2, Dodai, ɗan Ahowa. (Miklot yake bi masa a shugabancin.) Wata na 3, Benaiya, ɗan Yehoyada firist. Shugaba ne daga cikin sanannun nan “Talatin.” (Ɗansa Ammizzabad ya gāje shi a shugabancin ƙungiya.) Wata na 4, Asahel, ƙanen Yowab. (Ɗansa Zabadiya ya gāje shi.) Wata na 5, Shimeya, daga zuriyar Izhara. Wata na 6, Aira, ɗan Ikkesha, daga Tekowa. Wata na 7, Helez, mutumin Ifraimu, daga Felet. Wata na 8, Sibbekai, daga garin Husha. (Shi daga dangin Zera ne, na kabilar Yahuza.) Wata na 9, Abiyezer, daga Anatot na kabilar Biliyaminu. Wata na 10, Maharai, daga Netofa. (Shi ma daga dangin Zera ya fito.) Wata na 11, Benaiya, daga Firaton na kabilar Ifraimu. Wata na 12, Heled, daga Netofa. (Shi daga zuriyar Otniyel ne.)

Aikin Mulkin Kabilan Isra'ila

16-22 Ga jerin sunayen masu mulkin kabilan Isra'ila. Ra'ubainu: Eliyezer ɗan Zikri, Saminu: Shefatiya ɗan Ma'aka, Lawi: Hashabiya ɗan Kemuwel, Haruna: Zadok, Yahuza: Eliyab ɗaya daga cikin 'yan'uwan sarki Dawuda, Issaka: Omri ɗan Maikel, Zabaluna: Ishmaiya ɗan Obadiya, Naftali: Yerimot ɗan Azriyel, Ifraimu: Hosheya ɗan Azaziya, Manassa ta Yamma: Yowel ɗan Fedaiya, Manassa ta Gabas: Iddo ɗan Zakariya, Biliyaminu: Yawasiyel ɗan Abner, Dan: Azarel ɗan Yeroham. Waɗannan su ne shugabannin kabilai. 23 Sarki Dawuda bai ƙidaya waɗanda shekarunsu suka kasa ashirin ba, gama Ubangiji ya yi alkawari zai sa mutanen Isra'ila su yi yawa kamar taurari a sararin sama. 24 Yowab ɗan Zeruya ne ya fara ƙidayar, amma bai gama ba. Allah ya hukunta wa Isra'ila saboda wannan ƙidaya, saboda haka ba za a taɓa samun cikakken adadi a lissafin da yake a ajiye na fādawan sarki Dawuda ba.

Masu Lura da Dukiyar Sarki

25-30 Ga lissafin masu sarrafa dukiyar sarki. Ɗakin ajiya na sarki: Azmawet ɗan Adiyel, Ƙaramin ɗakin ajiya: Jonatan ɗan Uzziya, Aikin gona: Ezri ɗan Kabilu, Kurangar Inabi: Shimai daga Rama, Ɗakin ajiyar Inabi: Zabdi daga Shefam, Itatuwan zaitun da na ɓaure (a gindin tsaunukan yamma): Ba'al-hanan daga Geder, Ajiyar man zaitun: Yowash, Garken shanu na filin Sharon: Shirtai daga Sharon, Garken shanu na cikin kwari: Shafat ɗan Adlai, Raƙuma: Obil Ba'isma'ile, Jakuna: Yedaiya daga Meronot, Tumaki: Yaziz Bahagire. 31 Dukan waɗannan su ne masu lura da dukiyar sarki Dawuda.

Ƙwararrun Mashawartan Dawuda

32 Jonatan, kawun Dawuda, shi ne mai ba da shawara, yana da ganewa, shi kuma magatakarda ne. Shi da Yehiyel ɗan Hakmoni su ne masu koya wa 'ya'yan sarki, maza. 33 Ahitofel shi abokin shawarar sarki ne. Hushai Ba'arkite kuwa shi ne abokin sarki. 34 Sai Yehoyada ɗan Benaiya, da Abiyata suka gāji matsayin Ahitofel. Yowab shi ne babban shugaban sojojin sarki.

1 Tarihi 28

Dawuda ya Danƙa Ginin Haikali ga Sulemanu

1 Dawuda ya yi umarni a tara dukan shugabannin Isra'ila, da shugabannin kabilai, da shugabannin ƙungiyoyin da suke bauta wa sarki, da shugabannin dubu dubu, da na ɗari ɗari, da masu lura da dukan dukiya da dabbobin sarki, da na 'ya'yansa, da fādawa, da manyan sojoji, da jarumawa, a Urushalima. 2 Sarki Dawuda fa ya miƙe tsaye, ya ce, “Ku saurare ni, ku 'yan'uwana, da jama'ata. Na yi niyya a zuciyata in gina wa akwatin alkawari na Ubangiji wurin hutawa, da wurin zaman zatin Allah. Na riga na yi shiri domin ginin, 3 amma Allah bai yardar mini in yi da kaina ba, domin ni mayaƙi ne, na kuwa zubar da jini. 4 Duk da haka Ubangiji Allah na Isra'ila ya zaɓe ni da zuriyata daga cikin gidan mahaifina, in zama Sarkin Isra'ilawa har abada. Gama shi ya zaɓi Yahuza ya zama shugaba. Daga cikin gidan Yahuza kakana, da kuma daga cikin 'ya'yan mahaifina, maza, ya ji daɗina har ya naɗa ni sarkin dukan Isra'ila. 5 Daga cikin dukan 'ya'yana maza, (gama Ubangiji ya ba ni 'ya'ya maza da yawa), ya zaɓi ɗana Sulemanu ya hau gadon sarautar Isra'ila, abin mulkin Ubangiji. 6 “Ya ce mini, ‘Ɗanka Sulemanu ne zai gina Haikalina da shirayuna, gama na zaɓe shi ya zama ɗa a gare ni, ni kuwa in zama uba a gare shi. 7 Zan tabbatar da mulkinsa har abada idan ya bi umarnaina da ka'idodina da himma kamar yadda ake yi a yau.’ 8 “Saboda haka a gaban dukan Isra'ila, wato taron jama'ar Ubangiji, da kuma gaban Allahnmu, sai ku kiyaye, ku bi dukan umarnan Ubangiji Allahnku don ku mallaki ƙasan nan mai kyau, ku kuma bar wa 'ya'yanku ita gādo har abada. 9 “Kai kuwa ɗana Sulemanu, sai ka san Allah na tsohonka, ka bauta masa da zuciya ɗaya, da kuma yardar rai, gama Ubangiji mai binciken dukan zukata ne, ya kuma san kowane irin nufi da tunani. Idan ka neme shi, za ka same shi, in kuwa ka rabu da shi, shi ma zai yi watsi da kai har abada. 10 Ka lura, gama Ubangiji ya zaɓe ka domin ka gina Haikali, wato Wuri Mai Tsarki. Ka yi ƙarfi, ka kama aiki.” 11 Sa'an nan Dawuda ya ba ɗansa Sulemanu tsarin shirayin Haikalin, da ɗakunansa, da ɗakunan ajiya, da benaye, da Wuri Mafi Tsarki, inda ake gafarta zunubi. 12 Ya kuma ba shi tsarin dukan abin da ya yi nufin yi, na filayen Haikalin Ubangiji da dukan ɗakuna na kewaye, da ɗakunan ajiya na Haikalin Allah, da ɗakunan ajiye kyautan da aka keɓe ga Ubangiji. 13 Ya kuma ba shi tsarin ƙungiyoyin firistoci da na Lawiyawa, da na dukan hidimar da za a yi a Haikalin Ubangiji, da aikin lura da kayayyakin aiki na cikin Haikalin Ubangiji. 14 Ya kuma faɗa wa Sulemanu yawan zinariya da za a yi kwanoni da ita don yin aiki, da yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita don yin aiki, 15 da yawan zinariya da za a yi alkukan fitilu, da kuma fitilun, da yawan zinariya da za a yi kowane alkuki da fitilunsa, da yawan azurfa da za a yi alkuki bisa ga yadda za a yi amfani da kowane alkuki, 16 da yawan zinariya da za a yi teburorin gurasar ajiyewa, da azurfar da za a yi teburorin azurfa, 17 da yawan zinariya tsantsa wadda za a yi cokula masu yatsotsi, da daruna, da finjalai, da kwanoni da ita, da yawan azurfa da za a yi kwanoni da ita, 18 da yawan zinariya tsantsa wadda za a yi bagaden ƙona turare da ita. Ya kuma ba shi tsarin zinariya ta kerubobin da za su miƙe fikafikansu su rufe akwatin alkawari na Ubangiji. 19 Sarki Dawuda ya ce, “Dukan wannan rubutacce ne daga wurin Ubangiji zuwa gare ni domin in fahimci fasalin aikin filla filla.” 20 Sarki Dawuda kuma ya ce wa ɗansa Sulemanu, “Ka yi ƙarfin hali, ka dāge sosai, ka kama aikin, kada ka ji tsoro, kada kuwa ka karai, gama Ubangiji Allah, wato Allahna, yana tare da kai. Ba zai bari ka ji kunya ba, ba kuwa zai rabu da kai ba, har ka gama dukan aikin Haikalin. 21 Ga dai ƙungiyoyin firistoci da na Lawiyawa, suna nan domin yin hidima a Haikalin Allah, ga kuma gwanaye na kowace irin sana'a suna tare da kai don yin kowane irin aiki. Shugabanni da dukan jama'a suna ƙarƙashinka duka.”

1 Tarihi 29

Ba da Kyautai domin Gina Haikali

1 Sarki Dawuda fa ya yi magana da dukan taron, ya ce, “Ga shi, ɗana Sulemanu, wanda Allah ya zaɓa, shi dai saurayi ne tukuna, bai gogu da duniya ba tukuna, aikin kuwa babba ne, gama Haikali ba na mutum ba ne, amma na Ubangiji Allah ne. 2 A halin yanzu dai na riga na yi iyakacin ƙoƙarina, har na tanada waɗannan abubuwa saboda Haikalin Allahna, wato zinariya saboda kayayyakin zinariya, azurfa saboda kayayyakin azurfa, tagulla saboda kayayyakin tagulla, baƙin ƙarfe saboda kayayyakin baƙin ƙarfe, itace kuwa saboda kayayyakin itace, da duwatsu da yawa masu daraja, da masu launi iri iri. 3 Saboda kuma ƙaunar Haikalin Allahna da nake yi, shi ya sa na ba da zinariyata da azurfata domin Haikalin Allahna, banda wanda na riga na tanada saboda Haikali mai tsarki. 4 Na ba da zinariya tsantsa, talanti dubu uku (3,000 ), da azurfa tsantsa, talanti dubu bakwai (7,000 ), domin yin ado a bangon Haikalin, 5 da kuma dukan kayayyakin da masu sana'a za su yi. Yanzu fa ko akwai mai niyyar ba da sadaka ta yardar rai ga Ubangiji?” 6 Sa'an nan shugabannin gidajen kakanni, da shugabannin kabilai, da shugabanni na dubu dubu, da na ɗari ɗari, da masu lura da aikin sarki, suka bayar da yardar rai. 7 Sun ba da zinariya talanti dubu biyar (5,000 ), da darik dubu goma (10,000 ), da azurfa talanti dubu goma (10,000 ), da tagulla talanti goma sha takwas (18,000 ), da ƙarfe talanti dubu ɗari (100,000 ). 8 Dukan waɗanda suke da duwatsu masu daraja suka bayar da su cikin taskar Haikalin Ubangiji, ta hannun Yehiyel Bagershone. 9 Sai jama'a suka yi murna da ganin yadda suka bayar hannu sake, gama sun kawo sadakokinsu a gaban Ubangiji da zuciya ɗaya, shi sarki Dawuda kuma ya yi murna ƙwarai.

Dawuda ya Yabi Allah

10 Dawuda ya yabi Ubangiji a gaban dukan taron, ya ce, “Ya Ubangiji Allah na kakanmu Yakubu, yabo ya tabbata gare ka har abada abadin! 11 Girma, da iko, da daraja, da nasara, da ɗaukaka duk naka ne, ya Ubangiji, gama dukan abin da yake cikin sammai da duniya naka ne. Mulki kuma naka ne, ya Ubangiji. Kai ne Maɗaukaki duka. 12 Dukan wadata da girma daga gare ka suke, kai kake mulki da dukan iko da ƙarfi. Kai ne kake da iko ka ba mutum iko da ƙarfi. 13 Yanzu ya Allahnmu, muna gode maka muna kuma yabon sunanka mai daraja. 14 “Amma wane ni ko kuma jama'ata, da za mu iya kawo sadaka mai yawa haka? Gama dukan kome daga gare ka yake. Daga cikin abin da muka karɓa daga wurinka muka ba ka. 15 Gama mu kamar baƙi ne, masu yawo a gabanka kamar kakanninmu. Kwanakinmu a duniya kamar inuwa ne, ba za mu tsere wa mutuwa ba. 16 Ya Ubangiji Allahnmu, duk wannan da muka kawo domin mu gina maka Haikali saboda sunanka mai tsarki, daga gare ka ne muka samu, duka naka ne. 17 Da yake na sani, ya Allahna, kakan gwada zuciya, kana ƙaunar gaskiya, bisa ga amincewar zuciyata, da yardar rai, na miƙa maka dukan waɗannan abubuwa. Ina murna da ganin jama'arka waɗanda suke nan a tattare, sun kawo maka sadakokinsu da yardar rai. 18 Ya Ubangiji, Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, kakanninmu, ka tabbatar da yardar rai ɗin nan a rayukan jama'arka, ka bi da zukatansu zuwa gare ka. 19 Ka kuma ba ɗana Sulemanu cikakkiyar zuciya, har da zai kiyaye umarnanka, da shaidunka, da dokokinka, domin ya aikata su duka, ya kuma gina Haikali wanda na riga na yi tanadi dominsa.”

Sulemanu ya Gāji Dawuda

20 Sa'an nan Dawuda ya ce wa taro duka, “Sai ku yabi Ubangiji Allahnku yanzu.” Taron jama'a kuwa suka yabi Ubangiji Allah na kakanninsu, suka rusuna har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada, suka kuma girmama sarki. 21 Kashegari sai suka miƙa wa Ubangiji hadayu, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji, bijimai dubu ɗaya (1,000 ), da raguna dubu ɗaya (1,000 ), da 'yan raguna dubu ɗaya (1,000 ), da hadayunsu na sha, da hadayu masu yawa domin Isra'ila duka. 22 Sai suka ci, suka sha, suka yi murna a gaban Ubangiji a wannan rana. Sai suka sāke shelar naɗin Sulemanu ɗan Dawuda sarki, a karo na biyu, suka shafa masa man keɓewa domin ya zama mai mulki na Ubangiji, Zadok kuwa shi ne firist. 23 Sai Sulemanu ya zauna a kan gādon sarauta na Ubangiji maimakon tsohonsa Dawuda. Ya yi nasara a cikin sarautar, Isra'ilawa dukansu suka yi masa biyayya. 24 Dukan ma'aikatan hukuma kuwa, da manyan mutane, da kuma dukan 'ya'yan sarki Dawuda, suka yi alkawari za su yi wa sarki Sulemanu biyayya. 25 Ubangiji kuwa ya ɗaukaka Sulemanu ƙwarai da gaske a gaban dukan Isra'ilawa, ya ɗaukaka sarautarsa fiye da ta waɗanda suka riga shi sarauta a Isra'ila.

Sarautar Dawuda a Taƙaice

26 Dawuda ɗan Yesse ya yi mulki bisa dukan Isra'ila, 27 har shekara arba'in. Ya yi mulki a Hebron shekara bakwai sa'an nan ya yi mulki shekara talatin da uku a Urushalima. 28 Sa'an nan ya rasu da kyakkyawan tsufa, cike da shekaru, da arziki, da daraja. Ɗansa Sulemanu kuma ya gāji sarautarsa. 29 An fa rubuta ayyukan sarki Dawuda daga farko har ƙarshe a tarihin Sama'ila, annabi, da na annabi Natan, da na annabi Gad. 30 An rubuta labarin mulkinsa, da ikonsa, da al'amuran da suka same shi, da Isra'ilawa, da dukan mulkokin ƙasashe na kewaye.

2 Tarihi 1

Addu'ar Sulemanu ta Neman Hikima

1 Sulemanu ɗan Dawuda ya kahu sosai cikin mulkinsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi, Ubangiji kuwa ya sa shi ya zama mashahuri. 2 Sulemanu ya yi magana da dukan manya, wato shugabannin dubu dubu, da na ɗari ɗari, da alƙalai, da dukan shugabanni na Isra'ila, wato shugabannin gidajen kakanni. 3 Sa'an nan Sulemanu da dukan waɗanda suke tare da shi, suka tafi masujadar da take a Gibeyon, gama alfarwar sujada ta Allah, wadda Musa, bawan Ubangiji ya yi a jeji, tana can. 4 Amma dai Dawuda ya riga ya ɗauko akwatin alkawari na Allah daga Kiriyat-yeyarim, ya kawo shi a wurin da ya shirya, gama ya kafa masa alfarwa a Urushalima. 5 Amma bagaden tagulla wanda Bezalel ɗan Uri daga dangin Hur, ya yi, yana a gaban Wuri Mai Tsarki na Ubangiji, sai Sulemanu da taron jama'a suka yi sujada ga Ubangiji a can. 6 Sulemanu kuwa ya haura, ya tafi wurin da bagaden tagulla yake a gaban Ubangiji, a cikin alfarwa ta sujada, ya miƙa hadayun ƙonawa dubu a kansa. 7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Sulemanu, ya ce masa, “Ka roƙe ni abin da kake so in ba ka.” 8 Sai Sulemanu ya ce wa Allah, “Ka nuna wa tsohona Dawuda madawwamiyar ƙaunarka, har ka naɗa ni sarki a matsayinsa. 9 Yanzu fa ya Ubangiji Allah, alkawarin da ka yi wa tsohona ya cika, gama ka naɗa ni sarki a kan jama'a mai yawa kamar turɓaya. 10 Yanzu sai ka ba ni hikima da sani yadda zan iya kai da kawowa a gaban wannan jama'a, gama wa zai iya mulkin wannan jama'a taka mai yawa haka?” 11 Allah kuwa ya amsa wa Sulemanu ya ce, “Tun da kana da irin wannan tunani a zuciyarka, ba ka kuwa roƙi dukiya, ko wadata, ko girma, ko ran maƙiyanka ba, ba ka kuma roƙi tsawon rai ba, amma ka roƙa wa kanka hikima da sani domin ka iya yin mulkin jama'ata wadda na naɗa ka sarki a kanta, 12 to, na ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka dukiya, da wadata, da girma, waɗanda ba wani sarkin da ya taɓa samun irinsu, ba kuma wani sarkin da zai taɓa samun irinsu.” 13 Daga nan sai Sulemanu ya taso daga masujadar da take Gibeyon inda alfarwa ta sujada take, ya zo Urushalima inda ya zauna yana mulkin Isra'ila.

Sulemanu ya Tara Dawakai da Karusai

14 Sai Sulemanu ya tara karusai da mahayan dawakai. Yana da karusai dubu ɗaya da ɗari huɗu (1,400 ), da mahayan dawakai dubu goma sha biyu (12,000 ), sai ya sa su a biranen karusai, waɗansu kuma a Urushalima tare da shi. 15 Sarki ya yawaita azurfa da zinariya har suka zama kamar duwatsu a Urushalima. Haka kuma ya yi da itatuwan al'ul, suka yawaita kamar itatuwan ɓaure a fadama. 16 Wakilan sarki suka ɗauki nauyin shigo da dawakai daga Masar da Kilikiya, 17 suka kuma shigo da karusai daga Masar. Suka riƙa sayar wa sarakunan Hittiyawa da na Suriyawa karusai a kan azurfa ɗari shida shida, kowane doki kuma a kan azurfa ɗari da hamsin.

2 Tarihi 2

Shirye-shiryen Ginin Haikali

1 Sai Sulemanu ya yi niyya a ransa zai gina Haikali saboda sunan Ubangiji, ya kuma gina wa kansa fāda. 2 Don haka, sai ya sa mutane dubu saba'in (70,000 ) don ɗaukar kaya, dubu tamanin (80,000 ) su haƙo duwatsu a tsaunuka, dubu uku da ɗari shida (3,600 ) kuma su ne shugabanni. 3 Sulemanu fa ya aika wurin Hiram Sarkin Taya ya ce, “Yadda ka yi wa tsohona Dawuda, wato ka aiko masa da itatuwan al'ul domin ya gina gida inda zai zauna, ni ma ina so ka yi mini haka. 4 Ga shi dai, na yi niyyar gina Haikali saboda sunan Ubangiji Allahna, in kuma keɓe masa shi, domin a riƙa ƙona masa turare mai daɗin ƙanshi, inda kuma za a riƙa ajiye gurasar ajiyewa dukan lokaci, don kuma a riƙa miƙa hadayun ƙonawa safe da yamma, da ranakun Asabar, da na amarya wata, da kuma a lokatan ƙayyadaddun idodin Ubangiji Allahnmu, yadda dai aka faralta a riƙa yi a cikin Isra'ila. 5 Haikalin nan kuwa da nake niyyar ginawa babba ne, gama Allahnmu ya fi dukan alloli. 6 Amma wa ya isa ya gina masa Haikali, shi wanda sama da saman sammai ba su iya ɗaukarsa ba. Ni wane ne da zan gina masa Haikali, sai dai wurin da za a riƙa ƙona turare a gabansa? 7 Saboda haka sai ka aiko mini da mutum wanda ya gwanance a kan aiki da azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da kuma shunayya, da garura, da shuɗɗan zare, da wanda kuma ya gwanance da aikin sassaƙa, domin ya yi aiki tare da gwanayen mutane da nake da su a Yahuza da Urushalima, waɗanda tsohona Dawuda ya kawo. 8 Ka kuma aiko mini da itacen al'ul, da na fir, da katakon algum daga Lebanon, gama na sani barorinka sun san yadda ake yanyanka katakan Lebanon. Barorina za su yi aiki tare da barorinka, 9 domin su shirya mini katako mai yawa. Gama Haikalin da zan gina mai girma ne ƙwarai, mai banmamaki. 10 Zan ba barorinka masu aikin katako misalin mudu dubu ashirin (20,000 ) ta sussukakkiyar alkama, da mudu dubu ashirin (20,000 ) ta sha'ir, da misalin garwar ruwan inabi dubu ashirin (20,000 ), da ta mai dubu ashirin (20,000 ).” 11 Hiram, Sarkin Taya kuwa, ya ba Sulemanu amsar takardarsa, ya ce, “Saboda Ubangiji yana ƙaunar jama'arsa, ya naɗa ka sarkinsu.” 12 Hiram ya ci gaba da cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda ya yi sama da ƙasa, ya ba sarki Dawuda ɗa mai hikima, mai hankali, mai ganewa, wanda zai gina Haikali dominsa, ya gina fāda kuma domin kansa. 13 Yanzu zan aika maka da Huram mutum mai gwaninta, mai ganewa. 14 Shi ɗan wata mace mutuniyar Dan, mahaifinsa kuwa mutumin Taya ne. Huram ya gwanance a kan aiki da zinariya, da azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da dutse, da itace, da kuma shuɗi, da shunayya, da garura, da lilin mai kyau. Shi kuma zai iya sassaƙa kowane irin abu da aka sa shi ya sassaƙa, tare da gwanayenka, da na tsohonka, ubangidana, wato Dawuda. 15 To, yanzu, sai ka aiko wa barorinka da alkama, da sha'ir, da mai, da ruwan inabi kamar yadda ka alkawarta. 16 Mu kuwa za mu yanko maka dukan katakan da kake bukata a Lebanon, mu kawo maka su a kan gadajen fito ta hanyar teku, zuwa Yafa, domin ka kwashe ka kai Urushalima.”

An Fara Ginin Haikali

17 Sarki Sulemanu ya ƙidaya dukan baƙin da suke a ƙasar Isra'ila, kamar yadda tsohonsa Dawuda ya yi. Yawan baƙin da aka samu sun kai dubu ɗari da dubu hamsin da uku, da ɗari shida (153,600 ). 18 Sai ya zaɓi mutum dubu saba'in (70,000 ) daga cikinsu su zama masu ɗaukar kaya, dubu tamanin (80,000 ) kuma don su riƙa haƙo duwatsu daga tsaunuka, dubu uku da ɗari shida (3,600 ) kuwa don su zama shugabanni.

2 Tarihi 3

Sulemanu ya Gina Ɗakin Sujada domin Ubangiji

1 Sulemanu kuwa ya fara ginin Haikalin Ubangiji a Urushalima a kan Dutsen Moriya, inda Ubangiji ya taɓa bayyana ga tsohonsa Dawuda, inda kuma Dawuda ya riga ya shirya a daidai masussukar Arauna Bayebuse. 2 Ya fara ginin a ran biyu ga watan biyu a shekara ta huɗu ta sarautarsa. 3 Ga awon harsashin da Sulemanu ya kafa domin ginin Haikalin Ubangiji. Tsawonsa bisa ga tsohon magwajin, kamu sittin ne, fāɗin kuwa kamu ashirin. 4 Tsawon shirayi daga gaban Haikalin ya yi daidai da fāɗin Haikalin, wato kamu ashirin, sa'an nan tsayinsa kamu ɗari da ashirin. Aka shafe ciki da zinariya tsantsa. 5 Ya jera itatuwan fir a cikin babban ɗakin, sa'an nan ya shafe su da zinariya tsantsa, ya kuma zana siffofin itatuwan dabino da na sarƙoƙi. 6 Banda wannan kuma ya ƙawata Haikalin da duwatsu masu daraja da zinariya irin ta Farwayim. 7 Ya kuma shafe Haikalin duk da ginshiƙansa, da bakin ƙofofinsa, da bangayensa, da ƙyamarensa da zinariya, ya kuma zana siffofin kerubobi a jikin bangaye. 8 Sai ya gina Wuri Mafi Tsarki. Tsawonsa daidai da fāɗin Haikalin, wato kamu ashirin, fāɗinsa kuma kamu ashirin. Ya shafe shi da zinariya tsantsa, wadda jimillar nauyinta ta yi talanti ɗari shida. 9 Nauyin ƙusoshin ya kai shekel hamsin na zinariya. Ya kuma shafe benaye da zinariya tsantsa. 10 Ya sassaƙa siffofin kerubobi biyu na itace, a Wuri Mafi Tsarki, ya shafe su da Zinariya. 11 Tsawon fikafikan kerubobin duka kamu ashirin ne, fiffike ɗaya, kamu biyar, ya taɓo bangon ɗakin, ɗaya fiffiken kuma wanda shi ma kamu biyar ne, ya taɓo fiffiken kerub ɗaya ɗin. 12 Guda kerub ɗin kuma, fiffikensa guda ya taɓo bangon ɗakin, ɗaya fiffiken shi ma ya taɓo fiffiken kerub na farko. 13 Tsawon fikafikan kerubobin ya kai kamu ashirin. Su kerubobin a tsaye suke, suna fuskantar babban ɗakin. 14 Sai ya yi labule mai launin shuɗi, da shunayya, da garura, da lilin mai kyau, sa'an nan ya zana siffofin kerubobin a jikin labulen.

Kayan Haikali

15 Ya kuma yi ginshiƙai biyu domin ƙofar Haikalin, tsayinsu kamu talatin da biyar ne, ya yi wa ginshiƙan dajiya, tsayin kowace dajiya kamu biyar ne. 16 Ya yi sarƙoƙi, ya rataya wa ginshiƙan, ya kuma yi siffofin rumman guda ɗari, ya maƙala wa sarƙoƙin. 17 Sai ya kafa ginshiƙin a ƙofar Haikali, ɗaya a wajen kudu, ɗaya kuma a wajen arewa. Ya sa wa na wajen kudu suna Yakin, na wajen arewa kuwa Bo'aza.

2 Tarihi 4

1 Ya yi bagade na tagulla, tsawonsa kamu ashirin ne, fāɗinsa kuma kamu ashirin, tsayinsa kuwa kamu goma. 2 Ya yi kwatarniya kewayayyiya ta zubi, kamu goma daga gāɓa zuwa gāɓa, tsayinsa kuwa kamu biyar ne, da'irarsa kuwa kamu talatin. 3 A ƙashiyar kwatarniya akwai siffofin bijimai kamu goma kewaye da ita har jeji biyu. Gaba ɗaya aka yi zubinsu da na kwatarniya. 4 Kwatarniya tana bisa bijimai goma sha biyu, uku suna fuskantar gabas, uku suna fuskantar yamma, uku suna fuskantar kudu, uku kuma suna fuskantar arewa. Kwatarniya tana bisa bijiman, gindin ko wannensu yana daga ciki. 5 Kaurin kwatarniya taƙi guda ne, bakinsa kamar bakin finjali ne, kamar kuma siffar furen bi-rana. Kwatarniya kuwa tana iya ɗaukar fiye da garwa dubu uku na ruwa. 6 Ya kuma yi daro goma na wanki, ya ajiye biyar a wajen kudu, biyar kuma a wajen arewa, don a riƙa ɗauraye abubuwan da ake hadayar ƙonawa da su. Amma kwatarniya don firistoci su riƙa wanka a ciki ne. 7 Sa'an nan ya yi alkuki goma na zinariya kamar yadda aka tsara. Ya sa su cikin Haikali, biyar a sashen dama, biyar kuma a hagu. 8 Ya kuma yi tebur goma, ya ajiye a cikin Haikalin, biyar a dama, biyar kuma a hagu. Ya kuma yi kwanonin zinariya guda ɗari. 9 Sa'an nan ya yi wani shirayi domin firistoci, ya kuma yi wani babban shirayi, ya yi ƙofofi domin shirayun. Ya dalaye ƙyamaren ƙofofin da tagulla. 10 Ya girka kwatarniya a kusurwar kudu maso gabas daura da Haikalin. 11-16 Huram kuma ya yi tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da daruna. Huram kuwa ya gama dukan aikin da ya alkawarta wa sarki Sulemanu a Haikalin Allah: ginshiƙi biyu dajiya biyu a kan ginshiƙi biyu siffar tukakkiyar sarƙa a kan kowane ginshiƙi Siffar rumman guda ɗari huɗu domin raga don rufe dajiyar ginshiƙan dakali goma daro goma kwatarniya bijimi goma sha biyu da suke ɗauke da kwatarniya kwanoni, manyan cokula masu yatsotsi, wato ya yi dukan kayan nan da tagulla domin haikalin Ubangiji 17 Sarki ya yi zubinsu a filin Urdun tsakanin Sukkot da Zaretan a wuri mai yumɓu. 18 Haka Sulemanu ya yi kayayyakin nan da yawa ƙwarai, har ba a iya lissafin yawan nauyin tagullar da aka yi amfani da ita ba. 19-22 Haka kuwa Sulemanu ya yi dukan kayayyakin nan da suke cikin Haikalin Allah, duk da zinariya tsantsa aka yi su: bagade na zinariya tebur don ajiye gurasar ajiyewa alkukai tare da fitilunsu na zinariya tsantsa, domin a kunna su a gaban Wuri Mafi Tsarki na ciki kamar yadda aka tsara furanni fitilu arautaki hantsuka daruna cokula farantan wuta ƙofofi na can ciki ƙofofi na waje

2 Tarihi 5

1 Sulemanu ya kammala dukan aikin Haikalin Ubangiji. Sa'an nan ya kawo kayayyakin da tsohonsa Dawuda ya riga ya keɓe, wato azurfa da zinariya, da dukan kayan girke-girke, da tasoshi, ya ajiye su a taskokin Haikalin Allah.

Sulemanu ya Kawo Akwatin Alkawari a Haikali

2 Sulemanu kuwa ya tattara dattawan Isra'ila, da shugabannin kabilai, da shugabannin gidajen kakannin jama'ar Isra'ila, a Urushalima, domin a yi bikin fito da akwatin alkawari na Ubangiji da yake a alfarwa a birnin Dawuda, wato Sihiyona. 3 Sai dukan mutanen Isra'ila suka hallara a gaban sarki, a wurin bikin, a wata na bakwai ke nan. 4 Sa'an nan dukan dattawan Isra'ila suka zo, Lawiyawa kuwa suka ɗauko akwatin. 5 Suka kuma kawo akwatin, da alfarwa ta taruwa, da dukan tsarkakakkun kayayyakin da suke cikin alfarwar. Lawiyawa da firistoci ne suka kawo su. 6 Sarki Sulemanu da dukan taron mutanen Isra'ila da suka hallara a gaban akwatin suka yi ta miƙa hadayun tumaki da bijimai masu yawan gaske, har ba su ƙidayuwa. 7 Sa'an nan firistoci suka shigar da akwatin alkawari na Ubangiji a wurinsa, wato a Wuri Mafi Tsarki na cikin Haikalin, a ƙarƙashin fikafikan kerubobi. 8 Gama kerubobin sun miƙe fikafikansu bisa a daidai wurin da akwatin yake, wato kerubobin sun yi wa akwatin da sandunansa kamar rumfa ke nan. 9 Sandunan akwatin dogaye ne ƙwarai, har ana ganin kawunansu a gaban Wuri Mafi Tsarki na can ciki. Amma daga waje ba a iya ganinsu. Suna a wannan wuri har yau. 10 Ba kome cikin akwatin sai alluna biyu waɗanda Musa ya sa a ciki sa'ad da suke a Horeb. A Horeb ne Ubangiji ya ƙulla alkawarin da mutanen Isra'ila, sa'ad da suka fito daga Masar.

Ɗaukakar Ubangiji

11 Firistocin suka fito daga Wuri Mai Tsarki na Haikalin Allah, gama dukan firistocin da suka hallara, sun tsarkake kansu ba tare da kula da bambancin matsayi ba. 12 Dukan Lawiyawa mawaƙa, wato su Asaf, da Heman, da Yedutun tare da 'ya'yansu maza da 'yan'uwansu, aka sa su su tsaya a gabashin bagade, suna sāye da lilin mai kyau, suna ta kaɗa kuge, da molaye da garayu, ga kuma firistoci ɗari da ashirin masu busa ƙaho tare da su. 13 Ya zama aikin mabusan ƙaho ne, da mawaƙa duka, su haɗa kai, har a ji su suna yabon Ubangiji, suna godiya, sa'ad da suka ɗaga waƙa daidai da muryar ƙaho da ta kuge, da dukan kayan bushe-bushe suka yi ta raira waƙa cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Gama shi nagari ne, Ƙaunarsa kuwa madawwamiya ce.” Gidan kuwa, wato Haikalin Ubangiji, ya cika da girgije, 14 har ma firistoci ba su iya tsayawa su ci gaba da hidima ba saboda girgijen, gama ɗaukakar Ubangiji ta cika Haikalin Allah.

2 Tarihi 6

Maganar Sulemanu ga Mutane

1 Sulemanu ya ce, “Ubangiji ya riga ya faɗa zai zauna a cikin girgije mai duhu. 2 Yanzu kuwa na gina maka ƙasaitaccen ɗaki, Na gina maka wurin da za ka zauna har abada.” 3 Sa'an nan sarki ya juya, ya dudduba, ya sa wa dukan taron jama'ar Isra'ila albarka, dukansu kuwa suka tsaya. 4 Sai ya ce, “Ubangiji Maɗaukaki ne, Allah na Isra'ila wanda ya yi wa tsohona Dawuda alkawari, ga shi kuwa ya cika shi, gama ya ce, 5 ‘Tun daga ranar da na fito da jama'ata daga ƙasar Masar, ban zaɓi wani birni daga cikin dukan kabilan Isra'ila ba, inda zan gina wurin da sunana zai kasance, ban kuma zaɓi wani mutum da zai shugabanci jama'ata Isra'ila ba. 6 Amma na zaɓi Urushalima domin sunana ya kasance a wurin, na kuma zaɓi Dawuda ya zama shugaban jama'ata Isra'ila.’ 7 “Ya zama kuwa tsohona Dawuda ya yi niyyar gina Haikali domin sunan Ubangiji, Allah na Isra'ila. 8 Amma Ubangiji ya ce wa ubana Dawuda, ya kyauta, tun da yake ya yi niyya a zuciyarsa zai gina ɗaki saboda sunansa. 9 Duk da haka, ba shi zai gina Haikalin ba, ɗansa wanda za a haifa masa, shi ne zai gina Haikalin domin sunansa. 10 “Yanzu fa Ubangiji ya cika alkawarin da ya yi, gama na gāji matsayin ubana Dawuda, na kuwa hau gadon sarautar Isra'ila, yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuwa gina Haikali domin sunan Ubangiji, Allah na Isra'ila. 11 A can na ajiye akwati inda aka sa alkawarin da Ubangiji ya yi wa jama'ar Isra'ila.”

Addu'ar Sulemanu

12 Sulemanu ya miƙe a gaban bagaden Ubangiji a idon dukan taron Isra'ila ya ɗaga hannuwansa. 13 Sulemanu ya riga ya yi dakali na tagulla, tsawonsa kamu biyar, fāɗinsa kamu biyar, tsayinsa kamu uku, ya ajiye shi a tsakiyar filin, ya tsaya a kai. Ya durƙusa a gwiwoyinsa, a idon dukan taron jama'ar Isra'ila, ya ɗaga hannuwansa sama, 14 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra'ila, ba wani Allah kamarka a sama ko a duniya, wanda yake cika alkawari, kana nuna madawwamiyar ƙauna ga bayinka masu tafiya a gabanka da zuciya ɗaya. 15 Kai ka cika alkawarin da ka yi wa bawanka, tsohona Dawuda. Abin da ka faɗa ka kuma aikata. 16 Yanzu fa, ya Ubangiji, Allah na Isra'ila, ka cika alkawarin da ka yi wa bawanka tsohona cewa, ‘Daɗai, ba za a rasa wanda zai hau gadon sarautar Isra'ila ba, in dai 'ya'yanka maza za su lura da al'amuransu, don su yi tafiya bisa ga shari'ata, yadda kai ka yi tafiya a gabana.’ 17 Saboda haka, ya Ubangiji, Allah na Isra'ila, ka tabbatar da maganarka wadda ka yi wa bawanka Dawuda. 18 “Ashe kuwa Allah zai zauna tare da ɗan adam a duniya? Ga shi kuwa, sama da saman sammai ba su iya ɗaukarka ba, balle fa ɗakin da na gina. 19 Duk da haka ka kula da addu'ar bawanka da roƙe-roƙensa. Ya Ubangiji Allahna, ka kasa kunne ga kuka da addu'ar da bawanka yake yi a gabanka. 20 Ka dubi wajen Haikalin nan dare da rana, wurin da ka yi alkawari za ka sa sunanka, ka kasa kunne ga addu'ar da bawanka zai yi wajen wannan wuri, 21 ka ji roƙe-roƙen bawanka da na jama'ar Isra'ila, sa'ad da suke addu'a suna fuskantar wannan wuri, ka ji daga wurin da kake zaune a Sama, sa'ad da ka ji, ka gafarta. 22 “Idan wani ya yi wa maƙwabcinsa laifi, har aka sa shi ya rantse, ya kuwa zo ya rantse a gaban bagaden a wannan Haikali, 23 sai ka ji ka yi wa bayinka shari'a daga Sama, ka hukunta wa mugun, ka ɗora masa alhakinsa, ka baratar da adalin, ka ba shi sakayyar adalcinsa. 24 “Idan abokan gāba sun kori jama'arka, wato Isra'ila, saboda laifin da suka yi maka, sa'an nan suka juyo suka shaida sunanka, suka yi addu'a, suka yi roƙo a gabanka a wannan Haikali, 25 sai ka ji daga Sama ka gafarta zunubin jama'arka Isra'ila, ka komo da su ƙasar da ka ba su, su da kakanninsu. 26 “Sa'ad da aka kulle sammai, ba ruwan sama saboda sun yi maka zunubi, sa'an nan suka fuskanci wurin nan suka yi addu'a, suka shaida sunanka, suka juyo suka daina zunubinsu a sa'ad da ka hukunta su, 27 sai ka ji daga Sama ka gafarta zunubin bayinka, wato jama'arka Isra'ila, lokacin da ka koya musu kyakkyawar hanya da za su bi. Sai ka sa a yi ruwa a ƙasarka, wadda ka ba jama'arka gādo. 28 “Idan ana yunwa a ƙasar, ko annoba, ko burtuntuna, ko fumfuna, ko fārā, ko gamzari, ko da maƙiyansu za su kewaye biranensu da yaƙi, ko kowace irin annoba, da kowace irin cuta da take akwai, 29 kowace irin addu'a, kowane irin roƙo da kowane mutum, ko jama'ar Isra'ila suka yi, ko wannensu yana sane da irin wahalarsa, da baƙin cikinsa, ya kuwa ɗaga hannunsa wajen wannan Haikali, 30 sa'an nan za ka ji daga wurin zamanka a Sama, ka yi gafara, ka kuwa sāka wa kowa bisa ga al'amuransa, wanda ka san zuciyarsa, gama kai kaɗai ne ka san zukatan mutane, 31 don su yi tsoronka su yi tafiya bisa ga dokokinka muddin ransu, a ƙasar da ka ba kakanninmu. 32 “Haka kuma baƙo wanda ba cikin jama'arka Isra'ila yake ba, idan ya taho daga wata ƙasa mai nisa saboda girman sunanka da ƙarfin ikonka, in ya zo ya yi sujada, yana fuskantar Haikalin nan, 33 ka ji daga Sama wurin zamanka, ka kuwa aikata bisa ga dukan irin roƙon da baƙon ya yi gare ka. Domin ta haka sauran al'umman duniya za su san sunanka, su kuma yi tsoronka, yadda jama'arka Isra'ila suke yi, za su kuma sani cewa wannan Haikali da na gina, ana kiransa da sunanka. 34 “Sa'ad da jama'arka za su fita don yin yaƙi da magabtansu, duk dai ko ta ina ne za ka aike su, in sun yi addu'a gare ka, suna fuskantar wannan birni wanda kai ka zaɓa, da Haikalin nan da na gina saboda sunanka, 35 sai ka ji addu'arsu da roƙe-roƙensu daga Sama, ka biya muradinsu. 36 “Sa'ad da suka yi maka zunubi (gama ba wani ɗan adam da ba ya yin zunubi), ka kuwa yi fushi da su, har ka bashe su a hannun magabtansu, magabtansu suka kakkama su suka kai wata ƙasa ta nesa ko ta kusa, 37 duk da haka idan sun yi niyya a ransu a can ƙasar da aka kai su baƙunta, suka tuba, suka roƙe ka a can ƙasar baƙunci tasu, suna cewa, ‘Mun yi zunubi, mun aikata laifi, mun kuma yi mugunta,’ 38 in sun tuba da zuciya ɗaya, a ƙasar da aka kai su, in sun fuskanci ƙasarsu wadda ka ba kakanninsu, da birnin da ka zaɓa, suka yi addu'a, suna kuma fuskantar Haikalin nan da na gina domin sunanka, 39 sai ka ji addu'arsu da roƙe-roƙensu, daga wurin zamanka a Sama, ka sa su yi nasara, ka biya musu muradinsu, ka gafarta wa jama'arka waɗanda suka yi maka zunubi. 40 “Yanzu fa, ya Allahna, ina roƙonka, ka buɗe idanunka, ka kasa kunnuwanka, ka saurari addu'ar da ake yi a wannan wuri. 41 Yanzu fa, ya Ubangiji ka tashi ka tafi wurin hutawarka, kai da akwatin ikonka. Ya Ubangiji Allah ka yi wa firistocinka sutura da cetonka, adalanka kuma su yi farin ciki da nagartarka. 42 Ya Ubangiji Allah kada ka juya baya ga keɓaɓɓenka, ka tuna da madawwamiyar ƙaunarka ga bawanka Dawuda.”

2 Tarihi 7

Ƙeɓewar Haikali

1 Sa'ad da Sulemanu ya gama yin addu'arsa, sai wuta ta sauko daga sama, ta cinye hadayar ƙonawa tare da sauran hadayu, darajar Ubangiji kuma ta cika Haikalin. 2 Firistoci ba su iya shiga Haikalin Ubangiji ba saboda darajar Ubangiji ta cika Haikalin. 3 Sa'ad da dukan Isra'ilawa suka ga wuta ta sauko daga sama, ɗaukakar Ubangiji kuma na cike da Haikalin, sai suka sunkuyar da kansu ƙasa, suka yi sujada, suka yabi Ubangiji, saboda nagarinsa da madawwamiyar ƙaunarsa. 4 Sa'an nan sarki da dukan jama'a suka miƙa hadaya a gaban Ubangiji. 5 Sarki Sulemanu kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da dubu biyu (22,000 ), da tumaki dubu ɗari da dubu ashirin (120,000 ). Ta haka sarki tare da dukan jama'a suka keɓe Haikalin Allah. 6 Sai firistoci suka tsaya a matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a nasu matsayi riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji, gama madawwamiyar ƙaunarsa tabbatacciya ce har abada. A duk lokacin da Dawuda zai yabi Ubangiji tare da su, sai firistoci waɗanda suke daura da su su busa ƙaho, sa'an nan sai dukan Isra'ilawa su miƙe tsaye. 7 Sa'an nan Sulemanu ya tsarkake tsakiyar filin da yake a gaban Haikalin Ubangiji, gama a wurin ne ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayu domin salama, saboda bagaden tagulla wanda Sulemanu ya yi bai iya ɗaukar hadayu domin ƙonawa, da ta gari, da ta kitse ba. 8 A wannan lokaci, Sulemanu ya yi biki a wurin har kwana bakwai, tare da dukan Isra'ilawa, da waɗanda suka zo tun daga ƙofar Hamat, har zuwa rafin Masar, taron kuwa mai girma ne ƙwarai. 9 A rana ta takwas kuwa suka yi wani muhimmin taro, domin su keɓe bagaden. Sun yi kwana bakwai suna yin bikin. 10 A ran ashirin da uku ga watan bakwai, sai sarki ya sallami jama'a su koma gidajensu, suna ta murna da farin ciki a zuciyarsu saboda alherin da Ubangiji ya nuna wa Dawuda, da Sulemanu, da kuma jama'arsa Isra'ila.

Ubangiji ya Sāke Bayyana ga Sulemanu

11 Haka kuwa Sulemanu ya gama Haikalin Ubangiji da fādar sarki. Ya fa yi nasara cikin dukan irin abin da ya yi niyya game da Haikalin Ubangiji da fādarsa. 12 Sa'an nan Ubangiji ya bayyana ga Sulemanu da dare, ya ce masa, “Na ji addu'arka, na kuwa zaɓi wannan wuri domin kaina, domin ya zama Haikalin miƙa hadaya. 13 Har idan na kulle sammai yadda ba za a yi ruwan sama ba, ko kuma in umarci fara su cinye ƙasar, ko kuwa in aiko da annoba cikin jama'ata, 14 in jama'ata waɗanda ake kiransu da sunana za su yi tawali'u, su yi addu'a, su nemi fuskata, su juyo su bar mugayen ayyukansu, sa'an nan sai in ji su daga Sama, in gafarta zunubansu, in kuma warkar da ƙasarsu. 15 Yanzu idanuna za su kasance a buɗe, kunnuwana kuma za su saurari addu'ar da za a yi a wannan wuri. 16 Yanzu fa na riga na zaɓi wannan Haikali, na kuwa keɓe shi domin sunana ya kasance a wurin har abada. Idanuna da zuciyata kuma za su kasance a wurin kullayaumin. 17 Amma kai, idan za ka yi zamanka a gabana kamar yadda tsohonka Dawuda ya yi, ka kuma aikata bisa ga dukan abin da na umarce ka, ka kiyaye dokokina da farillaina, 18 to, zan kafa gadon sarautarka, yadda na alkawarta wa tsohonka Dawuda, cewa ba za a rasa mutumin da zai yi mulkin Isra'ila ba. 19 Amma idan ka juya, ka bar dokokina da umarnaina waɗanda na sa a gabanka, har ka shiga bautar gumaka kana musu sujada, 20 to, sai in tumɓuke ka daga ƙasata wadda na ba ka, wannan Haikali kuma wanda na riga na keɓe domin sunana, zan kawar da shi daga fuskata, zan kuwa maishe shi abin karin magana, abin raini ga dukan sauran al'umma. 21 “Haikali kuwa, wanda aka ɗaukaka, duk mai wucewa zai yi mamaki ya ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi wa wannan ƙasa da wannan Haikali haka?’ 22 “Sa'an nan kuma za su ce, ‘Saboda sun rabu da Ubangiji, Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga ƙasar Masar, amma suka bi waɗansu gumaka, suka yi musu sujada, suka bauta musu, saboda haka ne ya aukar musu da duk wannan bala'i.’ ”

2 Tarihi 8

Waɗansu Ayyukan Sulemanu

1 A ƙarshen shekara ashirin waɗanda Sulemanu ya yi yana gina Haikalin Ubangiji da fādarsa, 2 sa'an nan ya sāke giggina biranen da Hiram ya ba shi, ya zaunar da Isra'ilawa a cikinsu. 3 Sai Sulemanu ya tafi ya ci Hamat-zoba da yaƙi. 4 Sa'an nan ya gina Tadmor a jeji, a Hamat kuwa ya gina biranen ajiya. 5 Ya kuma gina Bet-horon ta kan tudu da Bet-horon ta kwari, birane masu kagara kuwa ya gina musu garu, da ƙofofi, da ƙyamare, 6 da kuma Ba'alat da dukan biranen ajiya waɗanda yake da su, da birane don karusansa, da birane don mahayan dawakansa, ya gina dukan abin da yake bukata a Urushalima, da Lebanon, da a dukan ƙasashen da suke cikin mulkinsa. 7 Dukan jama'ar da suka ragu a ƙasar, wato Hittiyawa, da Amoriyawa, da Ferizziyawa, da Hiwiyawa, da Yebusiyawa, waɗanda Isra'ilawa ba su hallaka ba, 8 daga cikin zuriyarsu waɗanda suka ragu a ƙasar a bayansu, waɗanda Isra'ilawa ba su hallaka ba, su ne Sulemanu ya tilasta su biya gandu, haka kuwa suke har wa yau. 9 Amma Sulemanu bai bautar da kowa daga cikin mutanen Isra'ila ba, su ne mayaƙansa, da shugabannin yaƙi, da shugabannin karusansa, da mahayan dawakansa. 10 Manyan shugabanni na sarki Sulemanu, mutum ɗari biyu ne da hamsin waɗanda suke iko da jama'a. 11 Sulemanu kuwa ya kawo 'yar Fir'auna daga birnin Dawuda zuwa gidan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za ta zauna a gidan Dawuda, Sarkin Isra'ilawa ba, saboda duk wuraren da akwatin Ubangiji ya shiga sun tsarkaka.” 12 Sai Sulemanu ya miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden da ya gina wa Ubangiji a gaban shirayi. 13 Sulemanu ya yi bisa ga abin da aka wajabta a yi kowace rana, bisa ga umarnin Musa a miƙa hadayu domin ranakun Asabar, da na amaryar wata, da kuma lokatan idodi uku na shekara, wato idin abinci marar yisti, da idin makonni, da na bukkoki. 14 Bisa ga ka'idar da tsohonsa Dawuda ya tsara, sai Sulemanu ya karkasa firistoci ƙungiya ƙungiya domin su yi hidima, Lawiyawa kuma bisa ga matsayinsu na yin yabo da hidima a gaban firistoci, kamar yadda aka wajabta kowace rana. Matsaran ƙofa kuma aka karkasa su ƙungiya ƙungiya bisa ga yawan ƙofofin, gama haka Dawuda, mutumin Allah, ya umarta. 15 Firistoci da Lawiyawa kuwa, ba su kauce wa umarnin sarki a kan kowane al'amari ba, ko a kan sha'anin taskoki. 16 Haka Sulemanu ya kammala aikinsa, da aka aza harsashin gina Haikalin Ubangiji, har zuwa ran da aka gama. Haka kuwa aka kammala aikin Haikalin Ubangiji. 17 Sai Sulemanu ya tafi Eziyon-geber da Elat da suke a gaɓar teku a ƙasar Edom. 18 Hiram kuwa ya aika wa Sulemanu jiragen ruwa tare da barori waɗanda suka saba da sha'ani a teku. Sai barorin tare da barorin Sulemanu, suka tafi Ofir, suka ɗauko zinariya talanti ɗari huɗu da hamsin, suka kawo wa sarki Sulemanu.

2 Tarihi 9

Sarauniyar Sheba ta Ziyarci Sulemanu

1 Sa'ad da Sarauniyar Sheba ta ji labarin irin suna da Sulemanu ya yi, sai ta zo Urushalima don ta jarraba shi da tambayoyi masu wuya. Ta zo da 'yan rakiya masu yawa, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, da zinariya mai yawa, da duwatsu masu daraja. Sa'ad da ta zo wurin Sulemanu, ta faɗa masa dukan abin da yake a ranta. 2 Sulemanu kuwa ya amsa dukan tambayoyin da ta yi masa, ba wani abu da yake ɓoye ga Sulemanu wanda ya kāsa bayyana mata. 3 Sa'ad da Sarauniyar Sheba ta ga hikimar Sulemanu, da gidan da ya gina, 4 da irin abincin da yake kan tebur ɗinsa da irin zaman manyan mutanensa, da barorin da suke yi masa hidima, da irin tufafinsu, da masu ba da abin sha, da irin tufafinsu, ta kuma ga hadayun ƙonawa da yake miƙawa a Haikalin Ubangiji, sai ta ji ba ta da sauran kuzari. 5 Sarauniya ta ce wa sarkin, “Ashe, gaskiya ce, labarinka da na ji a ƙasata a kan al'amuranka da hikimarka. 6 Amma dā ban gaskata labarinsu ba, sai da na zo na gani da idona, ashe, ko rabin yawan hikimarka ma ba a faɗa mini ba. Ashe, duk labarin da aka faɗa mini, ka zarce haka ƙwarai. 7 Masu farin ciki ne mutanenka, da barorinka waɗanda suke yi maka hidima kullayaumin, gama kullum suna jin hikimarka. 8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka wanda yake murna da kai, wanda ya hawar da kai gadon sarautarsa, don ka zama sarki a gaban Ubangiji Allahnka. Gama Allah yana ƙaunar Isra'ila, zai kuwa tabbatar da su har abada, shi ya sa ya naɗa ka sarkinsu, don ka aikata gaskiya da adalci.” 9 Sa'an nan kuma ta ba sarki zinariya talanti ɗari da ashirin, da kayan yaji masu yawan gaske, da duwatsu masu daraja. Irin kayan yajin da Sarauniyar Sheba ta ba sarki Sulemanu ba irinsa. 10 Bayan haka kuma barorin Hiram tare da barorin Sulemanu waɗanda suka kawo zinariya daga Ofir, sun kuma kawo itatuwan algum da duwatsu masu daraja. 11 Da itatuwan algum ɗin, sarki ya yi matakan Haikalin Ubangiji da na fādar sarki, ya kuma yi garayu, da molaye saboda mawaƙa. Ba a taɓa ganin irinsu a ƙasar Yahuza ba. 12 Sarki Sulemanu kuwa ya ba Sarauniyar Sheba duk abin da ranta yake bukata, da iyakar abin da take so, banda abin da ta kawo wa sarki. Sa'an nan ta koma ƙasarta, ita da barorinta.

Dukiyar Sulemanu da Shahararsa

13 Yawan zinariya da Sulemanu yake samu a shekara guda, talanti ɗari shida da sittin da shida, 14 banda wadda 'yan kasuwa da fatake sukan kawo masa. Dukan sarakunan Arabiya da masu mulkin ƙasar kuma sun kawo wa Sulemanu zinariya da azurfa. 15 Sai Sulemanu sarki ya ƙera manyan garkuwoyi guda ɗari biyu na zinariya, kowace garkuwa nauyinta shekel ɗari shida ne na zinariya. 16 Ya kuma ƙera garkuwa ɗari uku ƙanana na zinariya, kowace garkuwa nauyinta shekel ɗari uku ne. Sarki fa ya ajiye su a gidan da aka gina da katakai daga Lebanon. 17 Sarki ya yi babban gadon sarauta na hauren giwa, ya dalaye shi da zinariya. 18 Gadon sarautar yana da matakai da 'yar kujerar zinariya ta ɗora ƙafa haɗe da gadon. A kowane gefen gadon an yi wurin ɗora hannu, akwai kuma siffar zaki a tsaye kusa da kowane wurin ɗora hannun. 19 Akwai kuma siffofin zaki goma sha biyu, zaki biyu a kowane mataki, gefe da gefe. Ba ma sarautar da aka taɓa yi irin wannan. 20 Dukan tasoshi da finjalai na sarki Sulemanu, da zinariya tsantsa aka yi su. Hakanan kuma dukan tasoshi da finjalai da suke cikin gidan da aka gina da katakai daga Lebanon, na zinariya ne tsantsa. Ba a mai da azurfa a bakin kome ba a zamanin Sulemanu. 21 Sau ɗaya a shekaru uku, sarki yakan aika da jiragen ruwa zuwa Tarshish tare da barorin Hiram, su kawo zinariya, da azurfa, da hauren giwa, da manyan birai, da ɗawisu. 22 Sarki Sulemanu ya fi dukan sarakunan duniya dukiya da hikima. 23 Sarakunan duniya duka suna nema su sadu da Sulemanu, don su ji irin hikimar da Allah ya ba shi. 24 Kowannensu yakan kawo masa kyautai na kayayyakin azurfa, da na zinariya, da riguna, da turare, da kayan yaji, da dawakai, da alfadarai, masu yawan gaske a kowace shekara. 25 Sulemanu kuwa yana da ɗakunan dawakai da na karusai dubu huɗu (4,000 ), yana da mahayan dawakai dubu goma sha biyu (12,000 ) waɗanda suke zaune a biranen karusai, waɗansu kuma a Urushalima tare da sarki. 26 Ya mallaki dukan sarakuna tun daga Yufiretis, har zuwa ƙasar Filistiyawa har kuma zuwa kan iyakar Masar. 27 Sarki ya sa azurfa ta gama gari, kamar duwatsu a Urushalima, ya kuma sa itatuwan al'ul su yalwata kamar itatuwan ɓaure a Shefela. 28 Dawakan Sulemanu, sayo su aka yi daga Masar, da dukan sauran ƙasashe.

Rasuwar Sulemanu

29 Sauran ayyukan Sulemanu daga farko har ƙarshe an rubuta su a tarihin annabi Natan. An kuma rubuta su a annabcin Ahaija Bashilone, da kuma a wahayin Iddo maigani, game da Yerobowam ɗan Nebat. 30 A Urushalima, Sulemanu ya yi shekara arba'in yana mulkin dukan Isra'ila. 31 Sulemanu ya rasu aka binne shi tare da kakanninsa a birnin tsohonsa Dawuda, Rehobowam ɗansa shi ya gāje shi.

2 Tarihi 10

Kabilan Arewa sun yi Tawaye

1 Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra'ilawa sun tafi don su naɗa shi sarki. 2 Da Yerobowam ɗan Nabat, ya ji wannan labari (gama a Masar yake sa'ad da ya guje wa sarki Sulemanu), Yerobowam kuwa ya komo daga Masar. 3 Aka aika a kira shi, sai Yerobowam da dukan Isra'ilawa, suka je wurin Rehobowam suka ce, 4 “Tsohonka ya tsananta mana, yanzu sai ka sawwaƙa mana irin tsananin da muka sha daga wurin tsohonka, da irin tilastawar da ya yi mana, sa'an nan sai mu bauta maka.” 5 Rehobowam kuwa ya ce musu, “Ku komo bayan kwana uku.” Sai jama'a suka tafi. 6 Rehobowam ya nemi shawara a gun dattawan da suke tare da tsohonsa Sulemanu, sa'ad da yake da rai, ya ce, “Wace shawara za ku ba ni don in amsa wa jama'ar nan?” 7 Su kuwa suka ce masa, “Idan za ka nuna wa jama'ar nan alheri, ka daɗaɗa musu rai, ka kuma yi musu magana mai daɗi, za su zama barorinka har abada.” 8 Amma ya ƙi yarda da shawarar da dattawan suka ba shi, ya nemi shawara daga wurin matasa waɗanda suka girma tare, masu yi masa hidima. 9 Ya ce musu, “Wace irin shawara za ku bayar wadda za mu amsa wa jama'an nan da suka ce mini, ‘Ka sawwaƙa mana wahalar da muka sha daga wurin tsohonka?’ ” 10 Sai matasa waɗanda suka girma tare da shi, suka ce masa, “Ga abin da za ka faɗa wa jama'an nan da suka ce maka, tsohonka ya tsananta musu, yanzu sai ka sawwaƙa musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun ubana kauri! 11 Ubana ya tsananta muku ƙwarai, amma ni zan tsananta muku fiye da shi, ubana ya hore ku da bulala, amma ni zan hore ku da kunamai.’ ” 12 Sai Yerobowam tare da dukan jama'a suka koma wurin Rehobowam a rana ta uku, kamar yadda sarki ya faɗa, “Bayan kwana uku ku komo.” 13 Sarki Rehobowam ya amsa musu da kakkausan harshe, gama bai karɓi shawarar dattawan ba. 14 Sarki Rehobowam ya yi aiki da shawarar da matasa suka ba shi, ya ce, “Ubana ya tsananta muku fiye da shi, ya hore ku da bulala, amma ni, da kunama zan hore ku.” 15 Sarki bai kasa kunne ga jama'ar ba, gama wannan al'amari, Allah ne ya aukar da shi, domin ya cika maganar da ya faɗa wa Yerobowam ɗan Nebat, ta bakin Ahaija Bashilone. 16 Da Isra'ilawa duka suka ga sarki bai saurare su ba, jama'ar kuwa suka amsa wa sarkin, suka ce, “Wane rabo muke da shi a wurin Dawuda? Ba mu da gādo a wurin ɗan Yesse. Kowa ya tafi alfarwarsa, ya ku Isra'ilawa. Ku bar Rehobowam ya lura da gidansa.” Isra'ilawa duka kowa ya tafi alfarwarsa. 17 Amma Rehobowam ya ci gaba da mulki bisa Isra'ilawan da suke a biranen Yahuza. 18 Sai sarki Rehobowam ya aiki Adoniram shugaban aikin dole, jama'ar Isra'ila kuwa suka jejjefe shi da duwatsu har ya mutu. Sai sarki Rehobowam ya gaggauta ya hau karusarsa, ya tsere zuwa Urushalima. 19 Tun daga wannan lokaci kuwa har zuwa yau, Isra'ilawa suka tayar wa gidan Dawuda.

2 Tarihi 11

Annabcin Shemaiya

1 Sa'ad da Rehobowam ya kai Urushalima, sai ya tattara zaɓaɓɓun mayaƙa, mutum dubu ɗari da dubu tamanin (180,000 ) daga cikin jama'ar Yahuza da ta Biliyaminu don su yi yaƙi da Isra'ila, su komo wa Rehobowam da mulki. 2 Sai Ubangiji ya yi magana da Shemaiya, mutumin Allah, ya ce, 3 “Ka faɗa wa Rehobowam ɗan Sulemanu, Sarkin Yahuza, da dukan Isra'ilawa da suke a Yahuza da Biliyaminu, ka ce, 4 ‘Ga abin da Ubangiji ya faɗa, kada ku yi yaƙi da 'yan'uwanku, kowa ya komo alfarwarsa, gama wannan al'amari daga gare ni yake.’ ” Suka kuwa ji maganar Ubangiji, suka koma, ba su tafi yaƙi da Yerobowam ba.

Rehobowam ya Arzuta

5 Rehobowam ya zauna a Urushalima, ya kuwa gina birane masu kagara a Yehuza. 6 Ya gina Baitalami, da Itam, da Tekowa, 7 da Bet-zur, da Soko, da Adullam, 8 da Gat, da Maresha, da Zif, 9 da Adorayim, da Lakish, da Azeka, 10 da Zora, da Ayalon, da Hebron. Waɗannan su ne birane masu kagara a Yahuza da Biliyaminu. 11 Ya kuma ƙara ƙarfin kagaran, ya sa sarakunan yaƙi a cikinsu. Ya tara abinci, da mai, da ruwan inabi a cikinsu. 12 Ya sa garkuwoyi da māsu a cikin dukan biranen nan, ya ƙara musu ƙarfi ƙwarai. Haka ya riƙe Yahuza da Biliyaminu.

Firistoci da Lawiyawa sun Zo Yahuza

13 Firistoci da Lawiyawa da suke a dukan Isra'ila kuwa suka komo gare shi daga dukan wuraren da suke. 14 Sai Lawiyawa suka bar makiyayarsu da dukiyarsu, suka koma Yahuza da Urushalima, saboda Yerobowam da 'ya'yansa maza sun hana su yi hidimarsu ta firistocin Ubangiji. 15 Sai Yerobowam ya naɗa firistoci don masujadansa, saboda siffofin bunsurai, da na maruƙa, waɗanda ya yi. 16 Amma su waɗanda zuciyarsu take ga Ubangiji, Allah na Isra'ila, daga kowace kabilar Isra'ila, sukan bi Lawiyawa zuwa Urushalima domin su miƙa hadaya ga Ubangiji, Allah na kakanninsu. 17 Sai suka ƙarfafa mulkin Yahuza, suka tsare mutuncin Rehobowam ɗan Sulemanu har shekara uku. Suka yi shekara uku suna tafiya a tafarkin Sulemanu.

Iyalin Rehobowam

18 Rehobowam kuwa ya auri Mahalat 'yar Yeremot ɗan Dawuda, wadda Abihail 'yar Eliyab ɗan Yesse ta haifa. 19 Mahalat ta haifa masa 'ya'ya maza, su ne Yewush, da Shemariya, da Zaham. 20 Banda Mahalat kuma, sai ya auri Ma'aka 'yar Absalom, wadda ta haifa masa Abaija, da Attai, da Ziza, da kuma Shelomit. 21 Rehobowam ya fi ƙaunar Ma'aka, 'yar Absalom, fiye da dukan matansa, da ƙwaraƙwaransa. Yana kuwa da matan aure goma sha takwas, da ƙwaraƙwarai sittin. 'Ya'yan da ya haifa maza ashirin da takwas ne, 'ya'ya mata kuwa sittin. 22 Sai Rehobowam ya zaɓi Abaija ɗan Ma'aka, ya zama shugaban 'yan'uwansa, gama nufinsa ya zama sarki. 23 Sai ya yi hikima ya rarraba waɗansu 'ya'yansa maza ko'ina cikin gundumomin ƙasar Yahuza da ta Biliyaminu, a dukan birane masu kagara, ya tanada musu abinci a yalwace. Ya kuma samo musu mata masu yawan gaske.

2 Tarihi 12

Shishak ya Kai wa Yahuza Yaƙi

1 Da mulkin Rehobowam ya kahu, ya kuma yi ƙarfi, sai Rehobowam da dukan Isra'ilawa tare da shi suka bar bin shari'ar Ubangiji. 2 A shekara ta biyar ta mulkin sarki Rehobowam, Isra'ilawa ba su bi Ubangiji da aminci ba, saboda haka Shishak, Sarkin Masar, ya hauro don ya yi yaƙi da Urushalima. 3 Aka faɗo masa da karusai dubu da ɗari biyu (1,200 ), da mahayan dawakai mutum dubu sittin (60,000 ). Mutanen da suka taho tare da sarki Shishak daga Masar, ba a san adadinsu ba, akwai Libiyawa, da Sukkimiyawa, da kuma Habashawa. 4 Ya ci birane masu kagara na Yahuza, har ya dangana da Urushalima. 5 Sai annabi Shemaiya ya zo wurin Rehobowam da sarakunan Yahuza waɗanda suka tattaru a Urushalima saboda Shishak, ya ce musu, “Ubangiji ya ce kun yashe shi, don haka shi ma ya bashe ku a hannun Shishak.” 6 Sai sarakunan Isra'ila tare da sarki Rehobowam, suka ƙasƙantar da kansu, suka ce, “Ubangiji mai adalci ne.” 7 Da Ubangiji ya ga sun ƙasƙantar da kansu, sai ya yi magana da Shemaiya cewa, “Tun da yake sun ƙasƙantar da kansu, to, ba zan hallaka su ba, amma zan cece su, ba zan kwararo fushina ta hannun Shishak a kan Urushalima ba. 8 Duk da haka fa, za su zama bayin Shishak don su san bautata dabam take da wadda ake yi wa mulkokin ƙasashe.” 9 Sai Shishak Sarkin Masar ya zo ya fāɗa wa Urushalima da yaƙi, ya kuwa kwashe dukiyoyin da suke cikin Haikalin Ubangiji, da na fādar sarki, ya yi musu ƙaƙaf. Ya kuma kwashe garkuwoyi na zinariya, waɗanda Sulemanu ya yi. 10 Sai sarki Rehobowam ya ƙera garkuwoyin tagulla a madadin na zinariya, ya sa su a hannun shugabannin matsara, masu tsaron gidan sarki. 11 A duk lokacin da sarki ya shiga Haikalin Ubangiji, sai matsara su kawo su, daga baya kuma su maishe su a ɗakin matsaran. 12 Da sarki Rehobowam ya ƙasƙantar da kansa, sai fushin Ubangiji ya huce, don haka bai sa aka hallaka shi ƙaƙaf ba, har ma halin zama a ƙasar Yahuza ya yi kyau.

Mulkin Rehobowam a Taƙaice

13 Sarki Rehobowam kuwa ya kafa mulkinsa sosai a Urushalima, yana da shekara arba'in da ɗaya da haihuwa ya ci sarauta, ya yi mulki shekara goma sha bakwai a Urushalima, birnin da Ubangiji ya zaɓa daga dukan kabilan Isra'ila domin ya sa sunansa a wurin. Sunan tsohuwar Rehobowam Na'ama, Ba'ammoniya. 14 Amma ya aikata mugunta domin bai nemi Ubangiji a zuciyarsa ba. 15 Ayyukan Rehobowam, daga farko har zuwa ƙarshe an rubuta su a littafin tarihin annabi Shemaiya, da na Iddo maigani. Kullum yaƙi ne tsakanin Rehobowam da Yerobowam. 16 Rehobowam fa ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda. Abaija ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 13

Sarki Abaija na Yahuza

1 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin sarki Yerobowam, sai Abaija ya ci sarautar Yahuza. 2 Ya yi mulki shekara uku a Urushalima, sunan tsohuwarsa Ma'aka, 'yar Uriyel na Gibeya. Sai yaƙi ya ɓarke a tsakanin Abaija da Yerobowam. 3 Abaija ya tafi da rundunar jarumawansa, dubu ɗari huɗu (400,000 ) zaɓaɓɓun mutane. Yerobowam shi kuma ya jā dāgar yaƙi don ya kara da Abaija, yana da mutum dubu ɗari takwas (800,000 ), zaɓaɓɓun mayaƙa ƙarfafa. 4 Sai Abaija ya hau kan Dutsen Zemarayim, wanda yake a ƙasar Ifraimu mai tuddai, ya ce, “Ku kasa kunne gare ni, ya Yerobowam da dukanku Isra'ilawa. 5 Ashe, ba ku sani ba, Ubangiji Allah na Isra'ila, ya ba da sarautar Isra'ila ga Dawuda, da 'ya'yansa maza har abada, ta wurin alkawarin gishiri? 6 Duk da haka Yerobowam ɗan Nebat, baran Sulemanu ɗan Dawuda, ya tashi, ya yi wa ɗan ubangidansa tawaye, 7 waɗansu marasa amfani, 'yan iska, suka taru suka goyi bayansa, suka raina Rehobowam ɗan Sulemanu, saboda a lokacin shi yaro ne, ba shi da ƙarfin zuciya, bai iya tsayayya da su ba. 8 Yanzu kuma, so kuke ku ƙi mulkin Ubangiji wanda yake hannun 'ya'yan Dawuda, maza, saboda yawan mayaƙan da kuke da shi, da gumakan maruƙan zinariya da kuke da su, waɗanda Yerobowam ya yi muku. 9 Ashe, ba ku kori firistocin Ubangiji, 'ya'yan Haruna, maza, da Lawiyawa ba, kuka yi wa kanku firistoci kamar na al'umman sauran ƙasashe? Duk wanda ya zo ya miƙa ɗan bijimi da raguna bakwai don ya tsarkake kansa, ya zama firist na gumaka ke nan, ba na Allah ba. 10 “Amma a gare mu, Ubangiji shi ne Allahnmu, ba mu kuwa rabu da shi ba. Muna da firistoci, 'ya'yan Haruna, maza, masu yi wa Ubangiji hidima, da Lawiyawa masu yi musu hidima. 11 Safe da yamma suna miƙa wa Ubangiji hadayun ƙonawa, da turare mai daɗin ƙanshi, sukan ajiye gurasar ajiyewa a kan tebur ɗin zinariya tsantsa, sukan lura da alkukin zinariya, da kuma fitilunsa kowane maraice, gama muna riƙe da umarnin Ubangiji Allahnmu, amma ku kun rabu da shi. 12 Ga shi kuwa, Allah yana tare da mu, shi ne shugabanmu, firistocinsa kuwa suna da ƙahon da akan busa lokacin yaƙi, don su busa kira na yin yaƙi. Ya ku Isra'ilawa, kada ku yi yaƙi da Ubangiji, Allah na kakanninku, gama ba za ku yi nasara ba.” 13 Ashe, Yerobowam ya riga ya sa 'yan kwanto, su yi musu yankan baya. Ƙungiyar mayaƙan Isra'ila tana fuskantar ta Yahuza, 'yan kwanto kuma suna bayansu. 14 Da Yahuza suka duba, sai ga yaƙi a gabansu da bayansu. Sai suka yi kuka ga Ubangiji, firistoci kuma suka busa ƙaho. 15 Mutanen Yahuza suka yi k�wwar yaƙi. Da suka yi kuwwar yaƙin sai Ubangiji ya sa Yerobowam da dukan jama'ar Isra'ila su gudu a gaban Abaija da Yahuza. 16 Mutanen Isra'ila kuwa suka gudu a gaban Yahuza, Allah ya bashe su a hannunsa. 17 Abaija fa, da jama'arsa suka karkashe su, mugun kisa. Mutum dubu ɗari biyar (500,000 ) zaɓaɓɓu na Isra'ila, aka karkashe. 18 Haka kuwa aka ci nasara a kan mutanen Isra'ila a wannan lokaci. Mutanen Yahuza sun yi rinjaye saboda sun dogara ga Ubangiji, Allah na kakanninsu. 19 Abaija ya runtumi Yerobowam, ya ƙwace masa waɗansu birane, wato Betel tare da ƙauyukanta, da Yeshana tare da ƙauyukanta, da kuma Efron tare da ƙauyukanta. 20 Mulkin Yerobowam bai ƙara farfaɗowa a zamanin Abaija ba. Ubangiji kuma ya bugi Yerobowam, ya mutu. 21 Amma Abaija ya ƙasaita, ya auro mata goma sha huɗu, ya haifi 'ya'ya maza ashirin da biyu, da 'ya'ya mata goma sha shida. 22 Sauran ayyukan Abaija, da al'amuransa, da jawabansa, an rubuta su a littafin tarihin annabi Iddo.

2 Tarihi 14

Sarki Asa na Yahuza

1 Sarki Abaija kuwa ya rasu, suka binne shi tare da kakanninsa a birnin Dawuda. Ɗansa Asa shi ya gāji gadon sarautarsa. Ƙasar ta sami sakewa har shekara goma a zamaninsa. 2 Asa ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji Allahnsa. 3 Ya kawar da baƙin bagadai da masujadai, ya rurrushe ginshiƙai, ya kuma tumɓuke Ashtarot. 4 Ya umarci Yahuza su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu, su kiyaye doka, da umarni. 5 Daga cikin dukan biranen Yahuza, ya kawar da masujadai da bagaden ƙona turare. A zamaninsa an sami zaman lafiya a mulkinsa. 6 Ya giggina birane masu kagara a Yahuza, gama ƙasar tana zaman lafiya. A waɗannan shekaru bai yi yaƙi da kowa ba, saboda Ubangiji ya kawo masa salama. 7 Sai ya ce wa mutanen Yahuza, “Bari mu giggina waɗannan birane, mu kewaye su da garu, da hasumiya, da ƙofofi masu ƙyamare. Ƙasar tamu ce har yanzu, saboda mun nemi Ubangiji Allahnmu. Mun neme shi, ya kuwa ba mu salama a kowace fuska.” Suka yi ta gini, suka kuwa arzuta. 8 Sarki Asa kuwa yana da soja dubu ɗari uku (300,000 ) a Yahuza, ko wanne yana da kutufani da māshi, yana da soja dubu ɗari biyu da dubu tamanin (280,000 ) daga Biliyaminu, 'yan baka ko wanne da garkuwarsa. Dukansu manyan jarumawa ne. 9 Sai Zera mutumin Habasha ya zo da soja zambar dubu (1,000,000 ) da karusa ɗari uku har Maresha, don ya yi yaƙi da su. 10 Don haka sai Asa ya fito ya gamu da shi, suka kuwa jā dāga a kwarin Zefata a Maresha. 11 Asa kuwa ya yi kuka ga Ubangiji Allahnsa, ya ce, “Ya Ubangiji, ba wani mai taimako kamarka, wanda zai yi taimako sa'ad da mai ƙarfi zai kara da marar ƙarfi, ka taimake mu, ya Ubangiji Allahnmu, gama a gare ka muke dogara, da sunanka kuma muka zo don mu yi yaƙi da wannan babbar runduna. Ya Ubangiji, kai ne Allahnmu, kada ka bar mutum ya rinjayi jama'arka.” 12 Ubangiji kuwa ya fatattaki Habashawa a gaban Asa da Yahuza, Habashawa kuwa suka gudu. 13 Sai Asa da jama'ar da suke tare da shi, suka runtume su har zuwa Gerar. Habashawa suka fāɗi duka, ko ɗaya, ba wanda ya ragu da rai, gama an ragargaza su a gaban Ubangiji da gaban sojojin. Mutane suka kwashe ganima mai yawa gaske. 14 Suka hallaka dukan birane da suke kewaye da Gerar, gama tsoron Ubangiji ya kama su. Suka washe dukan biranen, gama biranen suna cike da ganima. 15 Suka kware alfarwan masu kiwon dabbobi, suka kora tumaki, da raƙuma masu yawan gaske. Sa'an nan suka komo Urushalima.

2 Tarihi 15

Gyare-gyaren da Asa ya Yi

1 Ruhun Allah kuwa ya sauko a kan Azariya ɗan Oded, 2 sai ya fita ya taryi Asa, ya ce masa, “Ka ji ni, ya Asa, kai da dukan Yahuza da Biliyaminu, Ubangiji yana tare da ku idan kuna tare da shi. Idan kuwa kun neme shi, za ku same shi, amma idan kun rabu da shi, shi ma zai rabu da ku. 3 Isra'ila kuwa ta daɗe ba ta bin Allah na gaskiya, ba ta da firist mai koya mata, ba ta kuma bin shari'a. 4 Amma lokacin da suke shan wahala suka juyo ga Ubangiji Allah na Isra'ila, suka neme shi, suka same shi. 5 A waɗancan lokatai, ba salama ga mai fita ko ga mai shiga, gama babban hargitsi ya wahalar da dukan mazaunan ƙasashe. 6 An kacancana su, al'umma tana gāba da al'umma, birni kuma gāba da birni, gama Allah ya yi ta wahalshe su da kowace irin wahala. 7 Amma ku sai ku yi ƙarfin hali, kada ku firgita, gama za a ba ku ladan aikinku.” 8 Da Asa ya ji irin kalmomin da annabi Azariya ɗan Oded ya hurta, sai ya yi ƙarfin zuciya, ya kawar da gumakan nan masu banƙyama daga dukan ƙasar Yahuza da ta Biliyaminu, daga kuma biranen da ya ci a ƙasar tuddai na Ifraimu. Sa'an nan ya gyara bagaden Ubangiji wanda yake a ƙofar shirayin Haikalin Ubangiji. 9 Sai ya tattara dukan mutanen Yahuza da na Biliyaminu, da kuma na Ifraimu, da na Manassa, da na Saminu, waɗanda suke zaman baƙunci tare da su. Da yawa daga cikin Isra'ilawa suka yi ƙaura zuwa wurinsa, sa'ad da suka ga Ubangiji Allahnsa yana tare da shi. 10 Suka taru a Urushalima a wata na uku na shekara ta goma sha biyar ta sarautar Asa. 11 A ran nan suka miƙa wa Ubangiji hadayun bijimai ɗari bakwai, da tumaki dubu bakwai (7,000 ) daga cikin ganimar da suka kwaso. 12 Sai suka ƙulla alkawari, cewa za su nemi Ubangiji Allah na kakanninsu da dukan zuciyarsu da ransu. 13 Duk wanda kuma bai nemi Ubangiji, Allah na Isra'ila ba, za a kashe shi, ko yaro ko babba, ko mace ko namiji. 14 Sai suka rantse wa Ubangiji da murya mai ƙarfi, suna sowa, suna busa kakaki da ƙaho. 15 Dukan Yahuza ta yi murna saboda rantsuwar, gama da zuciya ɗaya suka rantse, suka kuwa neme shi da iyakar aniya, sun kuwa same shi. Don haka Allah ya hutasshe su a kowane al'amari. 16 Asa kuma ya tuɓe tsohuwarsa, Ma'aka, daga matsayinta na sarauniya don ta ƙera wata siffa mai banƙyama ta Ashtoret. Sai Asa ya sare siffar nan, ya niƙe ta, ya ƙone a rafin Kidron. 17 Amma ba a kawar da masujadan da suke Isra'ila ba, duk da haka zuciyar Asa sarai take, ba wani aibi duk kwanakinsa. 18 Sai ya shigar da sadakar da shi da tsohonsa suka keɓe don Haikalin Ubangiji, wato azurfa, da zinariya, da kwanoni da tasoshi, da finjalai iri iri. 19 Ba a kuma ƙara yin wani yaƙi ba har shekara ta talatin da biyar ta mulkinsa Asa.

2 Tarihi 16

Asa ya Haɗa Kai da Ben-hadad

1 A shekara ta talatin da shida ta mulkin Asa, sai Ba'asha, Sarkin Isra'ila, ya haura ya fāɗa wa Yahuza da yaƙi, ya gina Rama don ya hana kowa fita, ko shiga wurin Asa, Sarkin Yahuza. 2 Sa'an nan Asa ya ɗebo azurfa da zinariya daga dukiyar da take cikin Haikalin, da na fādar sarki, ya aika wa Ben-hadad da su, wato Sarkin Suriya, wanda yake zaune a Dimashƙu, yana cewa, 3 “Bari mu haɗa kai, da ni da kai kamar yadda ubana da naka suka yi. Ga shi, na aika maka da azurfa da zinariya. Ka tafi ka warware haɗa kan da take tsakaninka da Ba'asha, Sarkin Isra'ila, don ya janye ya rabu da ni.” 4 Ben-hadad kuwa ya kasa kunne ga sarki Asa, ya aika da shugabannin rundunan sojojinsa suka yi yaƙi da biranen Isra'ila. Suka ci Iyon, da Dan, da Abel-bet-ma'aka, da dukan biranen ajiya na Naftali. 5 Da Ba'asha ya ji haka, sai ya daina gina Rama, ya bar aikin da yake yi. 6 Sa'an nan sarki Asa ya kawo dukan mutanen Yahuza, suka kwashe duwatsun da katakan da Ba'asha yake gina Rama da su, ya gina Geba da Mizfa da su.

Annabi Hanani

7 A lokacin nan sai Hanani, maigani, ya zo wurin Asa, Sarkin Yahuza, ya ce masa, “Da yake ka dogara ga Sarkin Suriya, maimakon ka dogara ga Ubangiji Allahnka, shi ya sa rundunar sojojin Sarkin Suriya ta kuɓuta daga hannunka. 8 Ai, Habashawa da Libiyawa rundunar sojoji ne masu yawan gaske, suna kuma da karusai da mahayan dawakai masu yawa ƙwarai. Amma duk da haka, saboda ka dogara ga Ubangiji, sai ya bashe su a hannunka. 9 Idon Ubangiji fa, yana kai da komowa ko'ina a duniya don ya nuna ikonsa ga dukan waɗanda suka dogara gare shi da zuciya ɗaya. Ka yi wauta a cikin wannan al'amari. Tun daga yanzu har zuwa nan gaba za ka yi ta fama da yaƙoƙi.” 10 Sai Asa ya yi fushi da maiganin, ya sa shi a kurkuku saboda maganar da ya yi masa, gama ya husata da shi ƙwarai. A wannan lokaci kuma sai Asa ya ƙuntata wa waɗansu daga cikin jama'a.

Ƙarshen Mulkin Asa

11 Ayyukan Asa, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuza da na Isra'ila. 12 A shekara ta talatin da tara ta mulkin Asa, sai wani ciwo ya kama shi a ƙafa. Ciwon kuwa ya tsananta ƙwarai, duk da haka Asa bai nemi taimakon Ubangiji ba, sai na magori. 13 Asa fa ya rasu bayan shekara biyu da ciwon, a shekara ta arba'in da ɗaya ta mulkinsa. 14 Aka binne shi a kabarin da shi da kansa ya haƙa a birnin Dawuda. Aka sa shi a makara wadda aka cika da kayan ƙanshi da na turare yadda gwanayen aikin turare suka shirya, suka hura babbar wuta don su darajanta shi.

2 Tarihi 17

Mulkin Yehoshafat ya Kahu

1 Yehoshafat ɗansa kuwa ya gāji gadon sarautarsa, ya kahu sosai gāba da Isra'ila. 2 Ya sa sojoji a kowane birni mai kagara a Yahuza, ya kuma sa ƙungiyoyin sojoji masu tsaro a ƙasar Yahuza, da kuma a biranen Ifraimu waɗanda tsohonsa Asa ya ci da yaƙi. 3 Ubangiji kuwa yana tare da Yehoshafat saboda ya bi halin tsohonsa da ya yi da fari, bai kuwa nemi Ba'al ba. 4 Ya nemi Allah na ubansa, ya bi umarnansa. Bai bi halin Isra'ila ba. 5 Saboda haka ne Ubangiji ya ba shi ikon riƙon wannan mulki. Yahuza duka kuwa ta kawo wa Yehoshafat haraji, ya kuwa zama riƙaƙƙen mai dukiya, wanda kuma ake girmamawa. 6 Zuciyarsa ta ƙarfafa cikin al'amuran Ubangiji. Ya kawar da masujadai, da Ashtarot daga ƙasar Yahuza. 7 A shekara ta uku ta sarautarsa, sai ya aika da ma'aikatansa, su Ben-hail, da Obadiya, da Zakariya, da Netanel, da kuma Mikaiya don su yi koyarwa a biranen Yahuza. 8 Tare da su kuma akwai Lawiyawa, da Shemaiya, da Netaniya, da Zabadiya, da Asahel, da Shemiramot, da Jonatan, da Adonaija, da Tobiya, da Tob-adonaija, tare da waɗannan Lawiyawa akwai firistoci, Elishama da Yehoram. 9 Suka koyar a Yahuza, suna tare da Littafin Shari'ar Ubangiji, wato Attaura. Suka shiga ko'ina a biranen Yahuza suka koyar da jama'a.

Gawurtar Yehoshafat

10 Tsoron Ubangiji kuwa ya kama dukan mulkokin ƙasashen da suke kewaye da Yahuza, har ba su iya fāɗa wa Yehoshafat da yaƙi ba. 11 Sai waɗansu daga cikin Filistiyawa suka kawo wa Yehoshafat kyautai da azurfa domin haraji. Larabawa ma suka kawo masa raguna dubu bakwai da ɗari bakwai (7,700 ), da bunsurai dubu bakwai da ɗari bakwai (7,700 ). 12 Yehoshafat ya daɗa ƙasaita, ya giggina kagarai, da biranen ajiya a Yahuza. 13 Yana kuwa da manya manyan wuraren ajiya a biranen Yahuza. Yana kuma da gwarzayen sojoji masu yawa a Urushalima. 14 Ga jimillar sojojin bisa ga gidajen kakanninsu. Na Yahuza mai shugabannin dubu dubu, shugaba Adana yana shugabancin sojoji dubu ɗari uku (300,000 ) gwarzaye. 15 Mai bi masa, sai shugaba Yehohanan yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu da dubu tamanin (280,000 ). 16 Mai biye da Yehohanan kuma shi ne shugaba Amasiya, ɗan Zikri, wanda ya ba da kansa don bauta wa Ubangiji, shi kuma yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu (200,000 ) gwarzaye. 17 Na Biliyaminu kuma sarkin yaƙi shi ne Eliyada, gwarzo ne, yana shugabancin sojoji dubu ɗari biyu (200,000 ), 'yan baka da garkuwa. 18 Na biye da Eliyada kuma shi ne shugaba Yehozabad wanda yake da sojoji dubu ɗari da dubu tamanin (180,000 ) shirayayyu don gabza yaƙi. 19 Waɗannan suke yi wa sarki hidima, banda waɗanda sarki ya sa a birane masu kagara ko'ina a Yahuza.

2 Tarihi 18

Annabi Mikaiya ya Gargaɗi Ahab

1 Yehoshafat ya arzuta, ya kuma sami ɗaukaka sai ya yi ma'amala da Ahab ta wurin aurayya. 2 Bayan 'yan shekaru sai ya kai wa Ahab ziyara a Samariya. Ahab kuwa ya yanka tumaki masu yawan gaske, da bijimai da yawa, domin Yehoshafat da mutanen da suke tare da shi. Ahab ya rinjaye shi don su fāɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi. 3 Sai Ahab, Sarkin Isra'ila, ya ce wa Yehoshafat, Sarkin Yahuza, “Za ka tafi tare da ni zuwa Ramot-gileyad?” Sai ya amsa, ya ce, “Ni ma kamarka ne, jama'ata kuma kamar jama'arka ce, za mu je yaƙin tare da kai.” 4 Yehoshafat kuma ya ce wa Sarkin Isra'ila, “Sai ka nemi faɗar Ubangiji tukuna.” 5 Ahab kuwa ya tattara annabawa, mutum ɗari huɗu, ya ce musu, “Mu je mu faɗa wa Ramot-gileyad da yaƙi, ko in haƙura?” Sai suka ce, “Ka tafi, gama Allah zai ba da ita a hannun sarki.” 6 Amma Yehoshafat ya ce, “Ba wani annabin Ubangiji a nan wanda za mu tambaye shi kuma?” 7 Sai Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Akwai sauran mutum guda wanda za mu iya neman nufin Ubangiji daga gare shi, shi ne Mikaiya, ɗan Imla, amma na ƙi shi saboda ba ya yin annabcin kirki a kaina, sai dai na rashin alheri kullum.” Amma Yehoshafat ya ce, “Kada sarki ya faɗi haka.” 8 Sa'an nan Sarkin Isra'ila ya kira wani jarumi ya ce masa, “Maza ka kawo Mikaiya ɗan Imla.” 9 A sa'an nan Sarkin Isra'ila, da Yehoshafat, Sarkin Yahuza, suna zaune kowa a gadon sarautarsa, kowane ya caɓa ado, suna kuwa zaune a filin da yake ƙofar Samariya. Dukan annabawa kuwa suna ta yin annabci a gabansu. 10 Sai Zadakiya ɗan Kena'ana ya yi ƙahonin ƙarfe, ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Da waɗannan za ka sassoki Suriyawa har su hallaka!’ ” 11 Dukan annabawa kuma suka yi annabci, suna cewa, “Ka haura zuwa Ramot-gileyad ka ci nasara, gama Ubangiji zai ba da ita a hannun sarki.” 12 Jarumin fa da ya je ya kira Mikaiya ɗin, ya ce masa, “Ka kula fa, dukan maganganun da annabawa suke yi, sun yi wa sarki daɗi. Don haka kai ma ka yi maganar da za ta gamshi sarki kamar yadda suka yi.” 13 Amma Mikaiya ya ce, “Na rantse da Ubangiji abin da Allahna ya faɗa mini, shi zan faɗa.” 14 Da Mikaiya ya zo gaban sarki, sai sarki ya ce masa, “Mikaiya, mu haura zuwa Ramot-gileyad mu fāɗa mata da yaƙi, ko in haƙura?” Mikaiya kuwa ya amsa, ya ce, “Ka haura, gama za ka ci nasara, gama za a bashe su a hannunka.” 15 Amma sarki ya ce masa, “Har sau nawa zan rantsar da kai don kada ka faɗa mini kome, sai gaskiya da sunan Ubangiji?” 16 Mikaiya kuwa ya ce, “Ina ganin dukan Isra'ilawa a warwatse bisa tsaunuka, kamar tumakin da ba su da makiyayi. Ubangiji kuma ya ce, ‘Waɗannan ba su da makiyayi, bari dukansu, kowa ya koma gidansa da salama.’ ” 17 Sarkin Isra'ila fa ya ce wa Yehoshafat, “Ban faɗa maka ba, cewa ba zai yi annabcin alheri game da ni ba, sai na rashin alheri?” 18 Sai Mikaiya ya ce, “Ji maganar Ubangiji, na ga Ubangiji yana zaune a bisa kursiyinsa, dukan rundunan sama suna tsaye dama da shi da hagu da shi. 19 Sai Ubangiji ya ce, ‘Wa zai ruɗi Ahab, Sarkin Isra'ila, don ya haura zuwa Ramot-gileyad ya fāɗi?’ Sai wannan ya faɗi abu kaza, wancan kuma ya faɗi abu kaza. 20 Sai wani ruhu ya zo ya tsaya a gaban Ubangiji, ya ce, ‘Ni zan ruɗe shi.’ Sai Ubangiji ya ce masa, ‘Ta ƙaƙa?’ 21 Sai ya ce, ‘Zan tafi in zama ruhun ƙarya a bakin dukan annabawansa.’ Sa'an nan Ubangiji ya ce, ‘To, za ka ruɗe shi har ka yi nasara. Je ka, ka yi hakanan.’ 22 “Saboda haka Ubangiji ya sa ruhun ƙarya a bakunan annabawanka, gama Ubangiji ya faɗa, masifa za ta same ka.” 23 Sai Zadakiya ɗan Kena'ana, ya matso ya mari Mikaiya a kumatu ya ce, “Ta wace hanya ruhun Ubangiji ya fita daga gare ni ya zo ya yi magana da kai.” 24 Mikaiya kuwa ya ce, “Za ka gani a ranar da ka shiga ƙuryar ɗaki na can ciki don ɓuya.” 25 Sai Sarkin Isra'ila ya ce, “Ku kama Mikaiya, ku komar da shi wurin Amon mai mulkin birnin, da yarima Yowash. 26 Ku ce, ‘Sarki ya ce ku sa wannan mutum a kurkuku, ku ciyar da shi da ɗan abinci da ruwa kaɗan har in komo lafiya.’ ” 27 Sai Mikaiya ya ce, “Idan har ka komo lafiya, wato Ubangiji bai yi magana da ni ba ke nan.” Sai ya ce, “Ku ji, ya ku jama'a duka.”

Mutuwar Ahab

28 Sarkin Isra'ila fa, da Yehoshafat Sarkin Yahuza, suka haura zuwa Ramot-gileyad. 29 Sarkin Isra'ila ya ce wa Yehoshafat, “Zan ɓad da kama, in shiga yaƙi, amma kai, sai ka sa rigunanka.” Sarkin Isra'ila kuwa ya ɓad da kama, suka shiga yaƙi. 30 Sarkin Suriya ya umarci shugabannin karusansa, ya ce, “Kada ku yi yaƙi da yaro ko babba, sai dai da Sarkin Isra'ila, shi kaɗai.” 31 Sa'ad da shugabannin karusai suka ga Yehoshafat, suka ce, “Wannan ne Sarkin Isra'ila,” sai suka juya suka yi yaƙi da shi. Amma Yehoshafat ya yi kururuwa, Ubangiji Allah ya kuɓutar da shi, Allah kuwa ya kawar da su daga gare shi. 32 Da shugabannin karusai suka ga, ashe, ba Sarkin Isra'ila ba ne, sai suka daina binsa suka juyo. 33 Amma wani mutum ya harba kibiya haka kawai, ya sami Sarkin Isra'ila a mahaɗin kafaɗa. Sai sarkin ya ce wa wanda yake korar karusarsa, “Juya ka fitar da ni daga wurin yaƙin, gama an yi mini rauni.” 34 Ran nan yaƙin ya tsananta, Sarkin Isra'ila kuma ya jingina a cikin karusarsa, yana fuskantar Suriyawa har maraice, rana na fāɗuwa yana rasuwa.

2 Tarihi 19

Annabi Yehu ya Tsauta wa Yehoshafat

1 Yehoshafat Sarkin Yahuza ya koma gidansa a Urushalima lafiya. 2 Sai Yehu maigani, ɗan Hanani, ya fita domin ya tarye shi, ya ce wa sarki Yehoshafat, “Za ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci maƙiyan Ubangiji? Saboda haka hasalar Ubangiji za ta same ka. 3 Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da gumakan Ashtarot daga ƙasar, ka sa zuciyarka ga neman Allah.”

Yehoshafat ya Zaɓi Alƙalai

4 Yehoshafat ya yi zamansa a Urushalima, ya sāke shiga jama'a, tun daga Biyer-sheba har zuwa ƙasar tuddai ta Ifraimu, ya komar da su zuwa wurin Ubangiji, Allah na kakanninsu. 5 Sai ya naɗa alƙalai a ƙasar, a dukan biranen Yahuza masu kagara, birni birni. 6 Sai ya ce wa alƙalan, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari'ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa'ad da kuke yanke shari'a. 7 Yanzu fa ku yi tsoron Ubangiji. Ku lura da abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu bai yarda da rashin yin adalci ba, ko son zuciya, ko karɓar rashawa.” 8 Yehoshafat kuma ya naɗa waɗansu Lawiyawa, da firistoci, da waɗansu shugabannin iyalan Isra'ilawa, saboda su yi shari'a tsakani da Ubangiji, su daidaita tsakanin masu jayayya. A Urushalima za su zauna. 9 Sai ya umarce su ya ce, “Haka za ku yi saboda tsoron Ubangiji, ku yi aminci, ku yi da zuciya ɗaya kuma. 10 A duk lokacin da 'yan'uwanku daga birane suka kawo muku maganar wata shari'a, wadda ta shafi zub da jini, ko karya shari'a, ko umarni, ko dokoki, ko farillai, sai ku koya musu, don kada su aikata laifi a gaban Ubangiji, don kada hasala ta same ku, ku da 'yan'uwanku. Abin da za ku yi ke nan, don kada ku yi laifi. 11 Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al'amuran da suke na wajen Ubangiji. Zabadiya, ɗan Isma'ilu mai mulkin gidan Yahuza, shi ne shugabanku a kan dukan al'amuran da suke na wajen sarki. Lawiyawa kuwa su zama muhimman ma'aikatanku. Kada ku ji tsoro a cikin aikinku, Ubangiji kuwa ya kasance tare da masu gaskiya.”

2 Tarihi 20

Yaƙi da Mowab, da Ammon, da Edom

1 Bayan wannan sai mutanen Mowab, da mutanen Ammon, tare da waɗansu daga cikin Me'uniyawa, suka zo su yi yaƙi da Yehoshafat. 2 Sai waɗansu mutane suka zo suka faɗa wa Yehoshafat cewa, “Mutane masu yawan gaske suna zuwa su yi yaƙi da kai daga Edom, da kuma teku, har sun iso Hazazon-tamar,” wato En-gedi. 3 Sai Yehoshafat ya ji tsoro ya himmatu ga neman Ubangiji, ya kuma sa a yi shela, a yi azumi a dukan Yahuza. 4 Yahuza suka tattaru don su nemi taimako daga wurin Ubangiji. Daga cikin dukan biranen Yahuza, mutane suka zo don su nemi Ubangiji. 5 Sai Yehoshafat ya tsaya a gaban taron jama'ar Yahuza da na Urushalima, a Haikalin Ubangiji, a gaban sabuwar farfajiya, 6 ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na kakanninmu, kai ne Allah na cikin Sama, kai ne kuma kake mulkin dukan al'umman duniya. A gare ka iko da ƙarfi suke, don haka ba wanda ya isa ya jā da kai. 7 Ya Allahnmu, kai ne ka kori jama'ar ƙasan nan a gaban jama'arka Isra'ila, ka kuma ba da ita har abada ga zuriya masoyinka Ibrahim. 8 Suka kuwa zauna a cikinta, suka gina Wuri Mai Tsarki saboda sunanka cewa, 9 ‘Idan wani mugun abu ya same mu, kamar takobi, ko hukunci, ko annoba, ko yunwa, to, za mu tsaya a gaban wannan gida, a gabanka kuma, gama sunanka yana cikin gidan nan, idan mun yi maka kuka saboda wahalarmu, kai kuwa za ka ji, ka cece mu.’ 10 “Yanzu kuma ga mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, waɗanda ka hana Isra'ilawa su kai musu yaƙi sa'ad da suka fito daga ƙasar Masar, su ne mutanen da Isra'ila suka ƙyale, ba su hallaka su ba. 11 Dubi irin sakayyar da suka zo su yi mana, so suke su kore mu daga mallakarka, wanda ka gādar mana. 12 Ya Allahnmu, ba za ka hukunta su ba? Ba mu da ƙarfin da za mu yi yaƙi da wannan babban taro da suke zuwa su yi yaƙi da mu. Mun rasa abin da za mu yi, amma a gare ka muke zuba ido.” 13 A sa'an nan kuwa mutanen Yahuza suna tsaye a gaban Ubangiji, su da ƙananansu, da matansu, da 'ya'yansu. 14 A tsakiyar taron sai Ruhun Ubangiji ya sauka a kan Yahaziyel ɗan Zakariya, ɗan Benaiya, ɗan Yehiyel, ɗan Mattaniya, Balawe, na 'ya'yan Asaf, maza. 15 Sai Yahaziyel ya ce, “Ku ji, ku dukanku, mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima, da sarki Yehoshafat, ga abin da Ubangiji yake faɗa muku, ‘Kada ku ji tsoro, ko ku razana saboda wannan babban taro, gama wannan yaƙi ba naku ba ne, amma na Allah ne. 16 Ku gangara ku fāɗa musu gobe. Ga shi kuwa, za su haura ta hawan Ziz, za ku tarar da su a ƙarshen kwarin a gabashin jejin Yeruyel. 17 Ba ku za ku yi wannan yaƙi ba, ku dai, ku jā dāga, ku tsaya kurum ku ga nasarar da Ubangiji zai ciwo muku, ya Yahuza da Urushalima. Kada ku ji tsoro ko ku razana, gobe ku fita ku tsaya gāba da su, gama Ubangiji yana tare da ku.’ ” 18 Yehoshafat fa ya sunkuyar da kansa ƙasa, dukan Yahuza da mazaunan Urushalima kuma suka fāɗi ƙasa a gaban Ubangiji, suna masa sujada. 19 Sai Lawiyawa daga Kohatawa da Koratiyawa suka tashi tsaye suka yabi Ubangiji Allah na Isra'ila da babbar murya. 20 Sai suka tashi da sassafe suka tafi jejin Tekowa. Sa'ad da suka fita sai Yehoshafat ya tsaya, ya ce, “Ku saurara gare ni, ku mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima. Ku gaskata da Ubangiji Allahnku, za ku kahu. Ku gaskata annabawansa, za ku ci nasara.” 21 Sa'ad da ya yi shawara da jama'a, sai ya zaɓi waɗanda za su raira waƙa ga Ubangiji, su yabe shi a natse sa'ad da suke tafe a gaban runduna, su ce, “Ku yi godiya ga Ubangiji, Saboda madawwamiyar ƙaunarsa Tabbatacciya ce har abada.” 22 Sa'ad da suka fara raira waƙa, suna yabo, sai Ubangiji ya sa wa mutanen Ammon, da na Mowab, da na Dutsen Seyir, 'yan kwanto, 'yan kwanton kuwa suka fatattake su. 23 Gama mutanen Ammon da na Mowab suka tasar wa mazaunan Dutsen Seyir, suka hallaka su ƙaƙaf. Sa'ad da suka karkashe mazaunan Seyir sai suka fāɗa wa juna, suka yi ta hallaka kansu da kansu. 24 Da mutanen Yahuza suka zo hasumiyar tsaro ta jeji, suka duba sai suka ga gawawwaki kawai a kwance, ba wanda ya tsira. 25 Sa'ad da Yehoshafat da jama'arsa suka je kwasar ganima, sai suka sami shanu masu yawan gaske, da kayayyaki, da tufafi, da abubuwa masu daraja, waɗanda suka yi ta kwasa har suka gaji. Kwana uku suka yi suna ta kwasar ganimar saboda yawanta. 26 Sai suka taru a kwarin Beraka, wato albarka, a rana ta huɗu, a nan suka yabi Ubangiji. Don haka har wa yau ake kiran wurin, “Kwarin Beraka.” 27 Sai kowane mutumin Yahuza da na Urushalima, tare da Yehoshafat shugabansu, suka koma Urushalima suna murna, gama Ubangiji ya sa su yi farin ciki saboda maƙiyansu. 28 Suka shigo Urushalima da molaye da garayu, da ƙaho zuwa Haikalin Ubangiji. 29 Tsoron Ubangiji kuwa ya kama dukan mulkokin ƙasashe sa'ad da suka ji Ubangiji ya yi yaƙi da maƙiyan Isra'ilawa. 30 Mulkin Yehoshafat kuwa ya sami salama, gama Allahnsa ya ba shi hutawa a kowane gefe.

Ƙarshen Mulkin Yehoshafat

31 Yehoshafat ya yi mulkin Yahuza. Yana da shekara talatin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara ashirin da biyar. Sunan tsohuwarsa Azuba, 'yar Shilhi. 32 Ya bi tafarkin tsohonsa, Asa, bai kuwa kauce ba, ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji. 33 Duk da haka ba a kawar da masujadai ba, domin har yanzu mutanen ba su tsayar da zukatansu ga Allahn kakanninsu ba. 34 Sauran ayyukan Yehoshafat, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin tarihin Yehu ɗan Hanani, wanda aka rubuta a littafin sarakunan Isra'ila. 35 Bayan haka sai Yehoshafat, Sarkin Yahuza, ya haɗa kai da Ahaziya Sarkin Isra'ila, wanda ya aikata mugunta. 36 Ya haɗa kai da shi, suka gina jiragen ruwa don su riƙa zuwa Tarshish. A Eziyon-geber suka gina jiragen ruwan. 37 Sai Eliyezer ɗan Dodawahu mutumin Maresha, ya yi annabci gāba da Yehoshafat, ya ce, “Saboda ka haɗa kanka da Ahaziya, Ubangiji zai hallaka abin da ka yi.” Don haka jiragen ruwa suka farfashe, suka kāsa tafiya Tarshish.

2 Tarihi 21

1 Yehoshafat ya rasu, aka binne shi a birnin Dawuda tare da kakanninsa, ɗansa kuma ya gāji gadon sarautarsa.

Sarki Yoram na Yahuza

2 Yoram yana da 'yan'uwa maza, su ne Azariya, da Yehiyel, da Zakariya, da Azariya, da Maikel da kuma Shefatiya. Waɗannan 'ya'ya maza ne na Yehoshafat, Sarkin Yahuza. 3 Tsohonsu ya ba su kyautai da yawa na azurfa da zinariya, da abubuwa masu daraja, da birane masu garu a Yahuza, amma ya ba da mulkin ga Yoram, saboda shi ne ɗan fari. 4 Sa'ad da Yoram ya hau gadon sarautar tsohonsa, ya kahu sosai, sai ya karkashe dukan 'yan'uwansa da takobi, ya kuma karkashe waɗansu daga cikin sarakunan Yahuza. 5 Yoram yana da shekara talatin da biyu sa'ad da ya hau gadon sarauta, ya kuwa yi mulki a Urushalima shekara takwas. 6 Ya yi yadda sarakunan Isra'ila suka yi, kamar yadda gidan Ahab ya yi, gama matarsa 'yar Ahab ce. Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. 7 Duk da haka Ubangiji bai yarda ya hallaka gidan Dawuda ba, saboda alkawarin da ya riga ya yi da Dawuda, gama ya riga ya alkawarta zai ba shi haske, shi da 'ya'yansa maza har abada. 8 A zamaninsa Edomawa suka tayar wa Yahuza, suka naɗa wa kansu sarki. 9 Sai Yoram ya wuce, shi da shugabannin sojojinsa tare da dukan karusansa. Sai ya tashi da dare ya fatattaki Edomawa waɗanda suka kewaye shi, shi da shugabannin karusansa. 10 Har wa yau Edom ya tayar wa Yahuza. A wannan lokaci kuma Libna ta tayar wa mulkinsa, saboda Yoram ya rabu da bin Ubangiji Allah na kakanninsa. 11 A kan wannan kuma, ya yi masujadai a tuddan ƙasar Yahuza, ya sa mutanen Urushalima su zama marasa aminci, ya sa Yahuza ta ratse. 12 Sai annabi Iliya ya rubuta masa wasiƙa ya ce, “Ga abin da Ubangiji Allah na tsohonka Dawuda ya ce, ‘Da yake ba ka bi halin tsohonka Yehoshafat ba, da halin Asa Sarkin Yahuza, 13 amma ka bi irin halin sarakunan Isra'ila, har ka sa Yahuza da mazaunan Urushalima su zama marasa aminci, yadda gidan Ahab ya yi, ka kuma karkashe 'yan'uwanka, waɗanda kuke uba ɗaya, waɗanda suka fi ka kirki, 14 ga shi, ni Ubangiji zan aukar da babbar abboba a kan jama'arka, da 'ya'yanka maza, da matanka, da a kan abin da ka mallaka duka. 15 Kai da kanka kuma za ka kamu da ciwon hanji mai tsanani, saboda tsananin ciwo, hanjinka zai tsintsinke ya yi ta zuba kowace rana.’ ” 16 Sai Ubangiji ya kuta Filistiyawa da Larabawan da suke kusa da Habashawa, su yi gāba da Yoram. 17 Suka zo suka faɗa wa Yahuza da yaƙi. Suka washe dukan dukiyar da aka samu a gidan sarki, suka tafi da ita. Suka kuma kwashe 'ya'yansa, da matansa, ba wanda aka bar masa, sai Ahaziya autansa. 18 Bayan haka kuma, sai Ubangiji ya sa masa ciwon hanji wanda ba shi warkuwa. 19 Ana nan a ƙarshen shekara biyu, sai cutar ta sa hanjinsa ya zubo, ya kuwa rasu saboda tsananin ciwo. Jama'arsa ba su hura masa wuta ta girmamawa kamar yadda aka yi wa kakanninsa ba. 20 Yana da shekara talatin da biyu, ya ci sarauta, ya yi shekara takwas yana mulki a Urushalima, ba wanda ya yi baƙin cikin mutuwarsa. Aka binne shi a birnin Dawuda, amma ba a kaburburan sarakuna ba.

2 Tarihi 22

Sarki Ahaziya na Yahuza

1 Sai mazaunan Urushalima suka naɗa Ahaziya, autansa, ya gāji gadon sarauta, saboda ƙungiyar mutanen da suka zo tare da Larabawa a sansanin sun karkashe dukan 'yan'uwansa maza. Ahaziya ɗan Yoram Sarkin Yahuza, ya fara mulki. 2 Ahaziya yana da shekara arba'in da biyu sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki shekara guda a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Ataliya jikar Omri. 3 Ya kuma bi gurbin gidan Ahab, gama tsohuwarsa ita ce mai ba shi shawarar yadda zai aikata mugunta. 4 Ya kuwa aikata mugunta a gaban Ubangiji kamar gidan Ahab, gama su ne mashawartansa bayan rasuwar tsohonsa, wato shawarar da ta kai shi ga lalacewa. 5 Ya kuwa bi shawararsu. Ya tafi tare da Yehoram ɗan Ahab, Sarkin Isra'ila, don su yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya, a Ramot-gileyad. Suriyawa kuwa suka yi wa Yehoram rauni. 6 Don haka sai ya koma Yezreyel don ya yi jiyyar raunukan da aka yi masa a Rama, sa'ad da suka yi yaƙi da Hazayel Sarkin Suriya. Sai Ahaziya ɗan Yoram, Sarkin Yahuza, ya gangara don ya gai da Yehoram ɗan Ahab a Yezreyel wanda yake rashin lafiya.

Yehu ya kashe Ahaziya

7 Allah ya ƙaddara hallakar Ahaziya ta zo ta wurin ziyarar da ya kai wa Yehoram. Gama sa'ad da ya zo, sai ya fita tare da Yehoram don su yi yaƙi da Yehu ɗan Nimshi, wanda Ubangiji ya keɓe don ya kakkaɓe gidan Ahab. 8 Sa'ad da Yehu yake hukunta wa gidan Ahab, sai ya gamu da sarakunan Yahuza, da 'ya'yan 'yan'uwan Ahaziya, maza, suna yi wa Ahaziya hidima, sai ya karkashe su. 9 Ya kuma sa aka nemi Ahaziya. Aka kamo shi sa'ad da ya ɓuya a Samariya, suka kawo shi wurin Yehu, suka kashe shi, suka binne shi, gama suka ce, “Shi jikan Yehoshafat ne wanda ya nemi Ubangiji da zuciya ɗaya.” Don haka a gidan Ahaziya ba wanda ya isa ya riƙe mulkin.

Sarauniya Ataliya ta Yahuza

10 Da Ataliya tsohuwar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta tashi ta karkashe duk 'yan sarautar gidan Yahuza. 11 Amma sai Yehosheba, 'yar sarki Yoram, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya, ta sace shi daga cikin 'ya'yan sarki waɗanda aka kashe su ta sa shi da mai renonsa a ɗakin kwana. Haka fa, Yehosheba 'yar sarki Yoram, matar Yehoyada firist, ta yi, gama ita 'yar'uwar Ahaziya ce, ta ɓoye Yowash don kada Ataliya ta kashe shi. 12 Yowash yana ɓoye a Haikalin Allah har shekara shida, a lokacin da Ataliya take mulkin ƙasar.

2 Tarihi 23

An Ƙwace wa Ataliya Mulki

1 A shekara ta bakwai sai Yehoyada ya yi ƙarfin hali, ya haɗa kansa da shugabanni na ɗari ɗari, wato Azariya ɗan Yeroham, da Isma'ilu ɗan Yehohanan, da Azariya ɗan Obed, da Ma'aseya ɗan Adaya, da kuma Elishafat ɗan Zikri. 2 Sai suka shiga ko'ina cikin Yahuza, suka tattaro Lawiyawa daga dukan biranen Yahuza, da shugabannin gidajen kakannin Isra'ila, suka kuwa zo Urushalima. 3 Sai dukan taron suka yi wa sarki alkawari, a Haikalin Allah. Yehoyada ya ce musu, “Wannan shi ne ɗan sarki, sai ya ci sarauta kamar yadda Ubangiji ya faɗa a kan 'ya'yan Dawuda, maza. 4 Ga abin da za ku yi. Sulusin firistoci da Lawiyawa waɗanda ba su aiki ran Asabar, su za su yi tsaron ƙofofi. 5 Sulusinsu kuma a fādar sarki, ɗayan sulusin kuwa a gangare, sauran jama'a duka kuwa a filayen Haikalin Ubangiji. 6 Amma kada kowa ya shiga Haikalin Ubangiji, sai dai firistoci da Lawiyawa masu hidima, su ne za su iya shiga, gama su tsarkaka ne. Amma dukan jama'a su kiyaye shari'a, kada su shiga Wuri Mai Tsarki na Ubangiji. 7 Lawiyawa za su kewaye sarkin, ko wanne da makamansa a hannu, duk wanda ya shiga ɗakin, sai a kashe shi. Su kuma kasance tare da sarki in zai shiga ko zai fita.” 8 Sai Lawiyawa da dukan Yahuza suka yi yadda Yehoyada, firist, ya umarta. Kowannensu ya kawo mutanensa waɗanda ba su aiki ran Asabar, da masu kama aiki ran Asabar, gama Yehoyada, firist, bai sallami ƙungiyoyin ba. 9 Sai Yehoyada firist, ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin Haikalin Allah. 10 Sai ya sa mutane duka su yi tsaron sarki, ko wanne da makami a hannu, tun daga gefen kudu har gefen arewa na Haikalin, da kuma kewaye da bagade da Haikali. 11 Sai ya kawo ɗan sarkin, ya sa masa kambi, ya ba shi dokoki goma, aka yi shela aka ce shi ne sarki. Yehoyada da 'ya'yansa maza suka naɗa shi, suka ce, “Ran sarki ya daɗe!” 12 Sa'ad da Ataliya ta ji sowar mutane, suna ta ribibi suna yabon sarki, sai ta shiga Haikalin Ubangiji wurin jama'a. 13 Sa'ad da ta duba, sai ga sarki yana tsaye wajen ginshiƙin bakin ƙofa, ga shugabanni da masu busa ƙaho kewaye da sarkin. Dukan jama'a suna murna, suna busa ƙaho, mawaƙa kuma da kayan kaɗe-kaɗe da na bushe-bushensu, suna shugabancin shagalin. Sai Ataliya ta yayyage tufafinta ta ce, “Tawaye! Tawaye!” 14 Sai Yehoyada, firist, ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku kawo ta a tsakiyar sojoji, duk wanda ya bi ta a kashe shi da takobi.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada ku kashe ta a Haikalin Ubangiji.” 15 Sai suka kama ta. Da suka kai Ƙofar Doki ta fādar sarki, sai suka kashe ta a can.

Gyare-gyaren Yehoyada

16 Sai Yehoyada da dukan jama'a, da sarkin, suka ɗauki alkawari za su zama jama'ar Ubangiji. 17 Sai dukan jama'a suka tafi gidan Ba'al, suka rushe shi, suka kuma ragargaza bagadansa, da siffofinsa. Suka kashe Mattan, firist ɗin Ba'al, a gaban bagadan. 18 Yehoyada kuma ya sa matsaran da za su yi tsaron Haikalin Ubangiji a ƙarƙashin ikon firistoci, Lawiyawa, waɗanda Dawuda ya shirya don su lura da Haikalin Ubangiji, su miƙa hadayu na ƙonawa ga Ubangiji, yadda aka rubuta a Attaura ta Musa, da murna da waƙa kamar yadda Dawuda ya shirya. 19 Ya kuma sa 'yan tsaron ƙofa a ƙofofin Haikalin Ubangiji, don kada wani marar tsarki na kowane iri ya shiga. 20 Sai ya sa shugabanni, da dattawa, da masu mulki, da dukan jama'ar ƙasar, suka rufa wa sarki baya, daga Haikalin Ubangiji suka bi ta Ƙofar Bisa zuwa fādar sarki. Suka zo suka zaunar da sarki a gadon sarauta. 21 Dukan jama'ar ƙasar suka yi murna, zaman lafiya ya komo birnin, bayan da an kashe Ataliya.

2 Tarihi 24

Sarki Yowash na Yahuza

1 Yowash yana da shekara bakwai sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi shekara arba'in yana mulki a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Zibiya, daga Biyer-sheba. 2 Yowash ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji a dukan zamanin Yehoyada firist. 3 Sai Yehoyada ya auro masa mata biyu, ya haifi 'ya'ya mata da maza. 4 Bayan wannan sai Yowash ya yi niyya ya gyara Haikalin Ubangiji. 5 Sai ya tattara firistoci da Lawiyawa, ya ce musu, “Ku shiga biranen Yahuza, ku tattara kuɗi daga dukan Isra'ilawa domin a riƙa gyaran Haikalin Ubangijinku kowace shekara. Ku hanzarta al'amarin fa.” Amma Lawiyawa ba su hanzarta ba. 6 Sai sarki ya kira Yehoyada babban firist, ya ce masa, “Don me ba ka sa Lawiyawa su tafi Yahuza, da Urushalima, su karɓo kuɗin da Musa, bawan Ubangiji, ya aza wa taron jama'ar Isra'ila su kawo domin alfarwar sujada ba?” 7 Gama 'ya'ya maza na Ataliya, muguwar matan nan, sun kutsa kai a cikin Haikalin Ubangiji, suka yi amfani da dukan tsarkakan kayayyakin Haikalin Ubangiji domin gumaka. 8 Don haka sai sarki ya ba da umarni, a yi babban akwati, a ajiye shi a waje a ƙofar Haikalin Ubangiji. 9 Sai aka yi shela a Yahuza da Urushalima, a kawo wa Ubangiji kuɗin da Musa, bawan Allah, ya aza wa Isra'ila sa'ad da suke cikin jeji. 10 Sai dukan sarakuna, da dukan jama'a, suka yi farin ciki, suka kawo kuɗin da aka aza musu, suka zuba a babban akwatin, har ya cika. 11 Duk lokacin da Lawiyawa suka kawo wa 'yan majalisar sarki babban akwatin sa'ad da suka gan shi cike da kuɗi, sai magatakardan sarki, da na'ibin babban firist, su zo su juye kuɗin da yake cikin babban akwatin, sa'an nan su mayar da shi a inda yake. Haka suka yi ta yi kullum, har suka tara kuɗi masu yawan gaske. 12 Sarki kuwa da Yehoyada suka ba da kuɗin ga waɗanda suke lura da aikin Haikalin Ubangiji. Suka sa magina, da masassaƙa su gyara Haikalin Ubangiji, suka kuma sa masu aikin baƙin ƙarfe da na tagulla su gyara Haikalin Ubangiji. 13 Sai ma'aikatan da aka sa su yi aikin, suka yi aiki sosai, suka tafiyar da gyaran, suka gyara Haikalin Ubangiji, ƙarfinsa ya koma kamar yadda yake dā. 14 Da suka gama aikin, sai suka kawo wa sarki da Yehoyada sauran kuɗin. Da waɗannan kuɗin aka yi tasoshi, da kayan girke-girke na Haikalin Ubangiji, da kuma kayan hidima da miƙa hadayu na ƙonawa, da tasoshi domin turare, da kwanoni na zinariya da na azurfa.

An sāke Shirin Yehoyada

Suka yi ta miƙa hadayu na ƙonawa a cikin Haikalin Ubangiji, dukan kwanakin Yehoyada. 15 Yehoyada kuwa ya tsufa ƙwarai, ya yi tsawon rai, ya rasu. Ya rasu yana da shekara ɗari da talatin da haihuwa. 16 Suka binne shi a birnin Dawuda a inda ake binne sarakuna, saboda ya aikata nagarta a Isra'ila, da kuma a gaban Allah da Haikalin Allah. 17 Bayan rasuwar Yehoyada, sai sarakunan Yahuza suka zo suka yi mubaya'a a gaban sarki, sarki kuwa ya karɓa. 18 Sai suka ƙyale Haikalin Ubangiji Allah na kakanninsu, suka bauta wa Ashtarot da gumaka. Hasala kuwa ta auko a kan Yahuza da Urushalima, saboda wannan mugunta da suka yi. 19 Duk da haka Allah ya aika musu da annabawa don su komo da su wurinsa. Ko da yake sun shaida musu kuskurensu, duk da haka ba su kula ba. 20 Sai Ruhun Allah ya sauko wa Zakariya, ɗan Yehoyada, firist, ya tsaya a gaban jama'a ya yi magana da su, ya ce, “Ga abin da Allah ya ce, ‘Don me kuke ƙetare umarnan Ubangiji, har da za ku rasa albarka? Saboda kun rabu da bin Ubangiji, shi ma ya rabu da ku.’ ” 21 Amma suka yi masa maƙarƙashiya, sarki kuma ya ba da umarni, suka jejjefe annabin da duwatsu har ya mutu a farfajiyar Haikalin Ubangiji. 22 Sarki Yowash bai tuna da irin alherin da Yehoyada mahaifin Zakariya ya yi masa ba, amma ya kashe ɗansa. Sa'ad da Zakariya yake bakin mutuwa, sai ya ce, “Bari Ubangiji ya gani ya kuma sāka.” 23 A ƙarshen shekara sai sojojin Suriyawa suka kawo wa Yowash yaƙi suka je Yahuza da Urushalima, suka hallaka dukan shugabannin jama'a, suka kwashi ganima mai yawa, suka aika wa Sarkin Dimashƙu. 24 Ko da yake mutanen Suriya kima ne, duk da haka Ubangiji ya sa suka ci nasara a kan babbar rundunar Yowash, saboda sun rabu da Ubangiji Allah na kakanninsu. Ta haka suka hukunta wa Yowash. 25 Sa'ad da suka tafi, sun bar shi da rauni mai tsanani ƙwarai, sai barorinsa suka yi masa maƙarƙashiya suka kashe shi a gadonsa, saboda ya kashe ɗan Yehoyada firist. Ya mutu, aka binne shi a birnin Dawuda, amma ba su binne shi a kabarin sarakuna ba. 26 Waɗannan su ne waɗanda suka yi masa maƙarƙashiyar, Yozakar ɗan Shimeyat wata Ba'ammoniya, da Yehozabad ɗan Shimrit wata mutuniyar Mowab. 27 Labarin 'ya'yansa maza da annabcin da aka kawo a kansa da labarin sāke ginin Haikalin Allah, an rubuta su a sharhin littafin sarakunan. Sai Amaziya ɗan Yowash ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 25

Sarki Amaziya na Yahuza

1 Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarauta, ya yi shekara ashirin da tara yana mulki a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yehowaddin ta Urushalima. 2 Ya aikata abin da yake mai kyau a gaban Ubangiji, amma bai rasa aikata laifi a zuciyarsa ba. 3 Da ya ga mulkin ya kahu a hannunsa sosai, sai ya karkashe fādawa waɗanda suka kashe tsohonsa, sarki Yowash. 4 Amma bai karkashe 'ya'yansu ba, bisa ga abin da yake a rubuce a Shari'a, wato Attaura ta Musa, inda Ubangiji ya yi umarni cewa, “Ba za a kashe iyaye saboda 'ya'yansu ba, ba za a kuma kashe 'ya'ya saboda iyaye ba, amma mutum zai mutu saboda laifin kansa.” 5 Sa'an nan Amaziya ya tattara mazajen Yahuza, ya kasa su bisa ga gidajen kakanninsu, a ƙarƙashin shugabanni na dubu dubu, da na ɗari ɗari, a dukan Yahuza da Biliyaminu. Sai ya tara 'yan shekara ashirin ko fi, ya sami mutum dubu ɗari uku (300,000 ) ƙarfafa, waɗanda suka isa zuwa yaƙi, wato za su iya riƙon māshi da garkuwa. 6 Ya kuma ɗauko sojan haya, mutum dubu ɗari (100,000 ) jarumawa daga Isra'ila a bakin talanti ɗari na azurfa. 7 Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, kada ka yarda rundunar sojojin Isra'ila su tafi tare da kai, gama Ubangiji ba ya tare da Isra'ila, wato da dukan Ifraimawan nan. 8 Amma idan ka zaci ta wannan hanya ce za ka zama da ƙarfi don yaƙi, Allah zai kā da kai a gaban maƙiyi, gama Allah yana da iko ya yi taimako, ko kuwa ya ƙi.” 9 Amaziya kuwa ya ce wa annabin Allah, “To, me za mu yi yanzu game da azurfar da muka ba sojojin Isra'ila?” Sai annabin Allah ya amsa ya ce, “Ubangiji yana da iko ya ba ka fiye da haka.” 10 Sai Amaziya ya sallami rundunar sojojin da suka zo daga Ifraimu, su koma gida. Sai suka yi fushi da Yahuza ƙwarai suka koma gida cike da hasala mai zafi. 11 Amma Amaziya ya yi ƙarfin hali ya shugabanci jama'arsa, suka tafi Kwarin Gishiri, suka karkashe mutanen Seyir dubu goma (10,000 ). 12 Mutanen Yahuza kuma suka kama waɗansu mutum dubu goma (10,000 ) da rai, suka kai su a ƙwanƙolin dutse, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa daga ƙwanƙolin dutsen, duka suka yi kaca-kaca. 13 Amma sojojin rundunar da Amaziya ya sallama, bai yarda su tafi yaƙi tare da shi ba, suka faɗa wa biranen Yahuza da yaƙi, tun daga Samariya har zuwa Bet-horon, suka kashe mutum dubu uku (3,000 ), a cikinsu suka kwashe ganima mai yawan gaske. 14 Da Amaziya ya komo daga kisan Edomawa, sai ya kwaso gumakan mutanen Seyir, ya ajiye su su zama gumakansa, ya yi musu sujada, ya kuma miƙa musu hadaya. 15 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da Amaziya. Ubangiji ya aiki annabi a wurinsa. Annabin ya ce masa, “Don me ka koma ga gumakan da ba su iya ceton jama'arsu daga hannunka ba?” 16 Yana magana ke nan, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Ka rufe baki! In kuwa ba haka ba in sa a kashe ka.” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”

Yaƙi da Isra'ila

17 Sa'an nan Amaziya Sarkin Yahuza, ya yi shawara ya aika wa Yehowash ɗan Yehowahaz ɗan Yehu, Sarkin Isra'ila, ya ce, “Ka zo mu gabza da juna fuska da fuska.” 18 Yehowash Sarkin Isra'ila fa ya aika wa Amaziya Sarkin Yahuza, da amsa ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika wa itacen al'ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana 'yarka aure,’ sai wani naman jeji na Lebanon da yake wucewa, ya tattake ƙayar. 19 Ka ce, ga shi, ka ci Edom, zuciyarka ta sa ka fāriya. Amma yanzu sai ka yi zamanka, don me ka tsokano wahalar da za ta kā da kai, da kai da Yahuza tare da kai?” 20 Amma Amaziya ya ƙi ji, gama al'amarin daga wurin Allah yake, domin ya bashe su a hannun maƙiyansu, saboda sun koma ga gumakan Edom. 21 Sarkin Isra'ila kuwa ya haura, da shi da Amaziya Sarkin Yahuza, suka gabza da juna fuska da fuska a Bet-shemesh, wadda take a ƙasar Yahuza. 22 Sai Isra'ila ya runtumi Yahuza, kowane mutum ya gudu zuwa gidansa. 23 Yehowash Sarkin Isra'ila, ya kama Amaziya Sarkin Yahuza ɗan Yowash, wato jikan Ahaziya, a Bet-shemesh, ya kawo shi Urushalima. Ya rushe garun Urushalima har tsawon kamu ɗari huɗu, tun daga Ƙofar Ifraimu har zuwa Ƙofar Kusurwa, 24 sai ya kwashe dukan zinariya da azurfa, da dukan tukwane da tasoshi da aka samu a Haikalin Allah, waɗanda iyalin Obededom suke tsaro, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya. 25 Sarki Amaziya ɗan Yowash, Sarkin Yahuza, ya rayu shekara goma sha biyar bayan rasuwar Yehowash ɗan Yehowahaz Sarkin Isra'ila. 26 Sauran ayyukan Amaziya, daga farko har ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuza da na Isra'ila. 27 Daga lokacin da Amaziya ya bar bin Ubangiji, sai suka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, amma ya gudu zuwa Lakish, sai suka sa a bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi. 28 Sai suka kawo shi a bisa dawakai, suka binne shi tare da kakanninsa a birnin Dawuda.

2 Tarihi 26

Sarki Azariya na Yahuza

1 Dukan jama'ar Yahuza fa suka ɗauki Azariya, ɗan shekara goma sha shida, suka naɗa shi sarki, ya gāji gadon sarautar tsohonsa Amaziya. 2 Ya gina Elat, ya komar da ita ga Yahuza, bayan rasuwar sarki. 3 Azariya yana da shekara goma sha shida sa'ad da ya ci sarauta. Ya kuwa yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyu, sunan tsohuwarsa Yekoliya ta Urushalima. 4 Azariya ya yi abin da yake daidai saboda Ubangiji, bisa ga dukan irin abin da tsohonsa Amaziya ya aikata. 5 Ya mai da hankalinsa ga bin Ubangiji a kwanakin Zakariya, wanda ya koya masa tsoron Allah. Dukan lokacin da yake bin Ubangiji, Allah ya wadata shi. 6 Azariya kuwa ya tafi ya yi yaƙi da Filistiyawa, ya rushe garun Gat, da na Yamniya, da na Ashdod. Ya giggina birane a ƙasar Ashdod, da waɗansu wurare na Filistiyawa. 7 Allah ya taimake shi a kan Filistiyawa, da Larabawa, waɗanda suke zaune a Gur-ba'al, da kuma Me'uniyawa. 8 Ammonawa kuma suka kawo masa haraji, sunan Azariya ya kai har kan iyakar Masar, gama ya shahara ƙwarai. 9 Banda haka kuma, Azariya ya gina hasumiyai a Urushalima a Ƙofar Kusurwa, da Ƙofar Kwari, da kan kusurwa, ya kuma yi musu kagara. 10 Ya kuma gina hasumiyai a jeji, ya haƙa tafuka masu yawa, saboda yana da garkunan dabbobi da yawa, da waɗanda suke Shefela da waɗanda suke a filin tudu. Yana kuma da manoma da masu yi wa kurangar inabi aski a tuddai, da wajen ƙasashe masu dausayi, gama shi mai son noma ne ƙwarai. 11 Har yanzu kuma, Azariya yana da rundunar sojoji waɗanda suka iya yaƙi ƙungiya ƙungiya, yadda Yehiyel magatakarda, da Ma'aseya jarumi, suka karkasa su bisa ga umarnin Hananiya, ɗaya daga cikin 'yan majalisar sarki. 12 Jimillar shugabannin gidajen kakanni na ƙarfafan mutane jarumawa, dubu biyu da ɗari shida (2,600 ) ne. 13 Suna da sojoji dubu ɗari uku da dubu bakwai da ɗari biyar (307,500 ) a ƙarƙashin ikonsu waɗanda suke da ƙarfin yin yaƙi sosai, da za su taimaki sarki a kan maƙiyansa. 14 Azariya ya shirya wa sojojinsa garkuwoyi, da māsu, da kwalkwali, da sulke, da bakuna, da duwatsun majajjawa. 15 A Urushalima ya yi na'urori waɗanda gwanayen mutane ne suka ƙago don a sa su a hasumiya, da kan kusurwoyi, don a harba kibau, da manyan duwatsu. Da haka sunansa ya bazu ko'ina, gama ya sami taimako mai banmamaki, har ya zama mai ƙarfin gaske.

An Hukunta Azariya Saboda Girmankai

16 Amma sa'ad da ya yi ƙarfi, sai ya shiga girmankai, wanda ya zamar masa hallaka. Sai ya yi izgili a gaban Ubangiji Allahnsa, ya shiga Haikalin Ubangiji don ya ƙona turare a bisa bagaden ƙona turare. 17 Amma Azariya firist, ya bi shi tare da firistoci tamanin na Ubangiji, mutane ne jarumawa. 18 Sai suka hana sarki Azariya, suka ce masa, “Ba aikinka ba ne, Azariya, ka ƙona turare ga Ubangiji, wannan aikin firistoci ne, 'ya'yan Haruna, waɗanda aka keɓe su don ƙona turare. Fita daga wurin nan mai tsarki, gama ka yi kuskure, ba za ka sami daraja daga wurin Ubangiji Allah ba.” 19 Azariya ya yi fushi, a lokacin kuwa yana riƙe da farantin ƙona turare a hannunsa, sa'ad da ya yi fushi da firistocin, sai kuturta ta faso a goshinsa, a nan gaban firistocin a cikin Haikalin Ubangiji, wajen bagaden ƙona turare. 20 Sai Azariya babban firist tare da sauran firistocin suka dube shi, sai ga kuturta a goshinsa! Sai suka tunkuɗa shi waje nan da nan. Shi kansa ma ya hazarta ya fita saboda Ubangiji ya buge shi. 21 Ta haka sarki Azariya ya kuturce, har zuwa ranar mutuwarsa. Saboda kuturtarsa, ya zauna a keɓe a wani gida, gama an fisshe shi daga Haikalin Ubangiji. Yotam ɗansa shi ya shugabanci iyalin gidan sarki, yana kuma mulkin jama'ar ƙasa. 22 Sauran ayyukan Azariya, daga farko har zuwa ƙarshe, annabi Ishaya ɗan Amoz ya rubuta su. 23 Azariya ya rasu, suka binne shi tare da kakanninsa a hurumin sarakuna, gama suka ce, “Shi kuturu ne.” Sai Yotam ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 27

Sarki Yotam na Yahuza

1 Yotam yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki shekara goma sha shida a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Yerusha 'yar Zadok. 2 Ya aikata abin da yake daidai saboda Ubangiji, kamar dukan abin da tsohonsa Azariya ya yi, sai dai bai kutsa cikin Haikalin Ubangiji ba. Amma jama'a suka ci gaba da aikata rashin kirki. 3 Ya gina ƙofar bisa, ta Haikalin Ubangiji, ya yi gine-gine masu yawa a garun Ofel. 4 Ya kuma gina birane a ƙasar tuddai ta Yahuza, da kagara, da hasumiya a tuddai masu kuramu. 5 Ya yi yaƙi da Sarkin Ammonawa, ya kuwa ci nasara, har Ammonawa suka ba shi talanti ɗari na azurfa a wannan shekara, da alkama mudu dubu goma (10,000 ) da sha'ir mudu dubu goma (10,000 ). Haka Ammonawa suka yi ta biya a shekara ta biyu da ta uku. 6 Yotam ya shahara, saboda ya daidaita al'amuransa a gaban Ubangiji Allahnsa. 7 Sauran ayyukan Yotam, da dukan yaƙe-yaƙensa da al'amuransa, an rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila da na Yahuza. 8 Ya ci sarauta, yana da shekara ashirin da biyar, ya kuma yi shekara goma sha shida yana mulki a Urushalima. 9 Sai Yotam ya rasu, suka binne shi a birnin Dawuda. Ahaz ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 28

Sarki Ahaz na Yahuza

1 Ahaz yana da shekara ashirin sa'ad da ya ci sarauta, ya yi shekara goma sha shida yana mulki a Urushalima. Amma shi bai yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda kakansa Dawuda ya yi ba. 2 Ya aikata irin al'amuran da sarakunan Isra'ila suka yi. Ya kuma yi gumakan Ba'al na zubi. 3 Banda haka ma ya ƙona turare a kwarin ɗan Hinnom, ya ƙone 'ya'yansa maza bisa ga ƙazantattun al'adun al'ummai, waɗanda Ubangiji ya kore su daga gaban mutanen Isra'ila. 4 Ya miƙa hadayu, ya ƙona turare a masujadai da a bisa tuddai, da ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa.

Yaƙin Suriya da Isra'ila

5 Saboda haka Ubangiji Allahnsa ya bashe shi a hannun Sarkin Suriya. Suka ci shi da yaƙi suka kama mutanensa da yawa, suka kai su Dimashƙu. Aka kuma bashe shi a hannun Sarkin Isra'ila, wanda ya ci shi da yaƙi, ya kashe masa mutane masu yawa. 6 Gama Feka, ɗan Remaliya, ya kashe mutum dubu ɗari da dubu ashirin (120,000 ) cikin Yahuza a rana ɗaya, dukansu kuwa jarumawa ne, don sun bar bin Ubangiji Allah na kakanninsu. 7 Sai Zikri wani ƙaƙƙarfan mutumin Ifraimu, ya kashe Ma'aseya ɗan sarki, da Azrikam, sarkin fāda, da Elkana wanda yake daga sarki sai shi. 8 Mutanen Isra'ila kuwa suka kwaso 'yan'uwansu da suka kama, mutum dubu ɗari biyu (200,000 ), mata, da 'ya'ya mata, da 'ya'ya maza. Suka kuma kwaso ganima mai yawan gaske daga gare su. Suka kawo ganimar a Samariya.

Annabcin Oded

9 Amma wani annabin Ubangiji yana nan, sunansa Oded. Shi wannan annabi ya tafi ya taryi rundunar da ta zo Samariya, ya ce musu, “Ga shi, saboda Ubangiji Allah na kakanninku ya yi fushi da Yahuza, ya bashe su a hannunku, ku kuka kashe su da zafin fushi wanda ya kai har sama. 10 Yanzu kuwa kuna niyya ku mai da jama'ar Yahuza da ta Urushalima su zama bayinku mata da maza. Ashe, ku kanku ba ku da waɗansu zunuban da kuka yi wa Ubangiji Allahnku? 11 Yanzu fa, sai ku saurare ni, ku mayar da kamammun da kuka kwaso daga 'yan'uwanku gama Ubangiji yana fushi da ku ƙwarai.” 12 Waɗansu daga cikin shugabannin 'ya'ya maza na Ifraimu, wato su Azariya ɗan Yohenan, da Berikiya ɗan Meshillemot, da Yehizkiya ɗan Shallum, da Amasa ɗan Hadlai suka tashi suka tsayar da masu komowa daga wurin yaƙin. 13 Suka ce musu, “Kada ku shigo nan da waɗanda kuka kamo daga wurin yaƙin, gama so kuke ku jawo mana laifi a gaban Ubangiji, a kan manyan zunuban da muka riga muka yi, gama Ubangiji yana fushi da Isra'ila ƙwarai.” 14 Don haka sai sojoji suka bar waɗanda suka kamo daga wurin yaƙi, da ganima a gaban sarakuna da dukan taron. 15 Sai mutanen da aka kira sunansu suka tashi, suka ɗauki kamammun, da ganimar, suka sa wa dukan waɗanda suke tsirara sutura. Suka sa musu sutura, suka ba su takalma, suka ba su abinci da abin sha, suka shafa musu mai. Suka hawar da dukan raunana a kan jakuna, suka kai su wurin 'yan'uwansu a Yariko, wato birnin itatuwan dabino, sa'an nan suka koma Samariya.

Ahaz ya Roƙi Assuriya Taimako

16 A wannan lokaci kuwa sarki Ahaz ya nemi taimako wurin sarakunan Assuriya. 17 Gama Edomawa suka sāke kai wa Yahuza yaƙi, suka kama mutane suka tafi da su. 18 Filistiyawa kuma sun kai hari a biranen ƙasar Shefela, da Negeb ta Yahuza, har suka ci Bet-shemesh, da Ayalon, da Gederot, da Soko da ƙauyukanta, da Timna da ƙauyukanta, da Gimzo da ƙauyukanta. Sai suka zauna a can. 19 Ubangiji kuwa ya ƙasƙantar da Yahuza, saboda Ahaz Sarkin Yahuza ya yi ganganci a Yahuza, ya zama marar aminci ga Ubangiji. 20 Sai Tiglatfilesar, Sarkin Assuriya, ya zo ya yi yaƙi da shi, ya wahalshe shi, maimakon ya taimake shi. 21 Sai Ahaz ya kwaso kaya daga Haikalin Ubangiji, da fādar sarki, da na sarakuna, ya ba Sarkin Assuriya, amma sam, bai taimake shi ba. 22 Duk da wannan wahala da sarki Ahaz yake sha a wannan lokaci, sai ƙara rashin aminci yake yi ga Ubangiji. 23 Gama ya miƙa hadaya ga gumakan Dimashƙu, ga waɗanda suka ci shi da yaƙi, ya ce, “Saboda gumakan sarakunan Suriya sun taimake su, ni ma zan miƙa musu hadaya don su taimake ni.” Amma suka zama masa dalilin lalacewa, shi da dukan Isra'ila. 24 Sai Ahaz kuma ya tattara tasoshi da tukwane na Haikalin Ubangiji, ya farfashe su. Ya kuma kukkulle ƙofofin Haikalin Ubangiji, ya gina wa kansa bagadai a kowane lungu na Urushalima. 25 A kowane birni na Yahuza, ya yi masujadai inda zai ƙona turare ga gumaka, ya sa Ubangiji, Allah na kakanninsa ya yi fushi. 26 Sauran ayyukansa da dukan al'amuransa, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuza da na Isra'ila. 27 Ahaz ya rasu, suka binne shi cikin birnin Urushalima, amma ba su kai shi hurumin sarakunan Isra'ila ba. Hezekiya ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 29

Sarki Hezekiya na Yahuza

1 Hezekiya ya ci sarauta sa'ad da yake da shekara ashirin da biyar. Ya yi mulki shekara ashirin da tara a Urushalima. Sunan tsohuwarsa Abaija, 'yar Zakariya. 2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji kamar yadda kakansa Dawuda ya yi duka.

Hezekiya ya Tsabtace Haikali

3 A shekara ta fari ta mulkinsa, a wata na farko, sai ya buɗe ƙofofin Haikalin Ubangiji ya gyaggyara su. 4 Sai ya shigo da firistoci da Lawiyawa, ya tara su a filin da yake wajen gabas. 5 Sai ya ce musu, “Ku ji ni, ya ku Lawiyawa. Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake Haikalin Ubangiji Allah na kakanninku, ku kawar da ƙazantar da take a Wuri Mai Tsarki. 6 Gama kakanninmu sun yi rashin aminci, sun aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnmu, sun rabu da shi sun ba da baya ga mazaunin Ubangiji. 7 Sun kuma rurrufe ƙofofin shirayi suka kashe fitilu, sun daina ƙona turare ko miƙa hadayun ƙonawa a Wuri Mai Tsarki ga Allah na Isra'ila. 8 Don haka Ubangiji ya yi fushi da Yahuza da Urushalima, ya sa suka zauna da tsoro, abin banmamaki, abin ba'a kamar yadda kuke gani da idanunku. 9 Saboda wannan an kashe kakanninmu da takobi, 'ya'yanmu mata, da 'ya'yanmu maza da matanmu, an kai su bauta. 10 “Yanzu na yi niyya a zuciyata in yi alkawari da Ubangiji Allah na Isra'ila, domin ya huce daga zafin fushin da yake yi da mu. 11 'Ya'yana, kada ku yi sakaci, gama Ubangiji ne ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa, ku yi masa hidima, ku ƙona masa turare.” 12-14 Sa'an nan sai Lawiyawa suka tashi, na Kohatawa, Mahat ɗan Amasai, da Yowel ɗan Azariya, na Merari, Kish ɗan Abdi, da Azariya ɗan Yehallelel, na Gershonawa, Yowa ɗan Zimma, da Eden ɗan Yowa, na Elizafan, Shimri da Yehiyel, na Asaf, Zakariya da Mattaniya, na Heman, Yehiyel da Shimai, na Yedutun, Shemaiya da Uzziyel. 15 Sai suka tattara 'yan'uwansu maza, suka tsarkake kansu, suka shiga bisa ga umarnin sarki, bisa ga maganar Ubangiji domin su tsabtace Haikalin Ubangiji. 16 Firistoci fa, suka shiga can cikin Haikalin Ubangiji domin su tsabtace shi. Suka kwaso dukan ƙazantar da take a Haikalin Ubangiji, suka zuba ta a farfajiyar Haikalin Ubangiji. Sai Lawiyawa suka kwashe, suka zubar a rafin Kidron. 17 A rana ta fari a watan ɗaya suka fara aikin tsarkakewar. A rana ta takwas ga watan suka kai shirayin Ubangiji da aikin, kwana takwas suka ɗauka domin tsabtace Haikalin Ubangiji, a ranar sha shida ga watan ɗaya suka gama.

An Sāke Keɓe Haikali

18 Sai suka tafi wurin sarki Hezekiya suka ce, “Mun tsabtace Haikalin Ubangiji duka, da bagaden hadayar ƙonawa tare da dukan tasoshi, da tukwane, da teburin gurasar ajiyewa da kuma dukan kayayyakin da suke ciki. 19 Dukan kayayyakin da sarki Ahaz ya lalatar a zamaninsa, sa'ad da ya zama marar aminci, mun shirya su mun tsarkake su, suna nan a gaban bagaden Ubangiji.” 20 Sarki Hezekiya kuwa ya tashi da sassafe ya tattara manyan gari suka haura zuwa Haikalin Ubangiji. 21 Suka kawo bijimai bakwai, da raguna bakwai, da 'yan raguna bakwai, da bunsurai bakwai, domin yin hadaya don zunubi saboda mulkin, da Wuri Mai Tsarki, da kuma Yahuza. Sai ya umarci firistoci, wato 'ya'yan Haruna, maza, su miƙa su a kan bagaden Ubangiji. 22 Sai suka yanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin, suka yayyafa a jikin bagaden. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Hakanan kuma suka yanka 'yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. 23 Sa'an nan suka kawo wa sarki da taron jama'a bunsuran yin hadaya domin zunubi, suka ɗora hannuwansu a kan bunsuran. 24 Sai firistocin suka yanka su suka tsarkake bagaden da jinin bunsuran, don a yi kafara saboda dukan Isra'ila. Gama sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi saboda dukan Isra'ila. 25 Sai ya zaunar da Lawiyawa a Haikalin Ubangiji, masu kuge, da molaye, da garayu, bisa ga umarnin Dawuda, da na Gad, maigani na sarki, da na annabi Natan. Gama umarnin daga wurin Ubangiji ya zo ta wurin annabawansa. 26 Lawiyawa suka tsaya da kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Dawuda, firistoci kuwa suna riƙe da ƙahoni. 27 Sai Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawar a bisa bagaden. Sa'ad da aka fara miƙa hadaya ta ƙonawa, sai aka fara raira waƙa ga Ubangiji, aka busa ƙaho, sai sauran masu kayan kaɗe-kaɗe da na bushe-bushe na Dawuda, Sarkin Isra'ila, suka kama. 28 Dukan taron suka yi sujada, mawaƙa suna ta raira waƙa, masu ƙahoni suka yi ta busa. Aka yi ta yin haka har lokacin da aka gama miƙa hadayar ƙonawa. 29 Bayan da an gama yin hadaya ta ƙonawa, sai sarki, tare da dukan waɗanda suke tare da shi, suka sunkuya suka yi sujada. 30 Sai sarki Hezekiya tare da sarakunansa, suka faɗa wa Lawiyawa su yi ta raira yabo ga Ubangiji da kalmomin Dawuda, da na Asaf maigani. Da murna suka raira yabo, suka sunkuya suka yi sujada. 31 Hezekiya kuwa ya amsa ya ce, “Yanzu dai kun tsarkake kanku ga Ubangiji. Sai ku zo kusa ku kawo hadayu da sadakoki na godiya a Haikalin Ubangiji.” Sai taron suka kawo hadayu da sadakoki na godiya, dukan waɗanda suka yi niyya kuwa suka kawo hadayu na ƙonawa. 32 Jimillar hadayu na ƙonawa waɗanda taron suka kawo, su ne bijimai saba'in, da raguna ɗari, da 'yan raguna ɗari biyu, waɗannan duka kuwa don hadaya ne ta ƙonawa ga Ubangiji. 33 Abubuwan da aka keɓe kuwa bijimai ɗari shida ne, da tumaki dubu uku (3,000 ). 34 Amma su firistoci kima ne, don haka sun kāsa fiɗa dukan dabbobin da za a miƙa su hadaya ta ƙonawa. Sai 'yan'uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu. 35 Banda hadayu masu yawa na ƙonawa da aka yi, akwai kuma kitse na hadaya ta salama, akwai kuma hadaya ta sha don kowace hadaya ta ƙonawa. Da haka fa aka maido hidimar Haikalin Ubangiji. 36 Hezekiya da dukan jama'a suka yi murna saboda abin da Allah ya yi wa jama'a, gama farat ɗaya abin ya faru.

2 Tarihi 30

Yin Idin Ƙetarewa

1 Sai Hezekiya ya aika zuwa ga dukan Isra'ila da Yahuza, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa ga Ifraimu, da Manassa, cewa sai su zo Haikalin Ubangiji a Urushalima, domin su yi Idin Ƙetarewa na Ubangiji Allah na Isra'ila. 2 Gama sarki da sarakunansa da dukan majalisar da take a Urushalima sun tsai da shawara a yi Idin Ƙetarewa a wata na biyu, 3 gama ba su iya yinsa a lokacinsa ba, saboda yawan firistocin da suka tsarkake kansu bai isa ba, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba. 4 A ganin sarki da na jama'a duka, shirin ya yi daidai. 5 Sai suka ba da umarni a yi shela a Isra'ila duka, tun daga Biyer-sheba, har zuwa Dan, cewa sai mutane su zo Idin Ƙetarewa na Ubangiji Allah na Isra'ila a Urushalima, gama jama'a mai yawan gaske ba su zo wurin yin idin kamar yadda aka umarta ba. 6 Sai mazanni suka tafi ko'ina da ina a dukan ƙasar Isra'ila da ta Yahuza da wasiƙu daga wurin sarki da sarakunansa, yadda sarki ya umarta. “Ya ku jama'ar Isra'ila, ku komo wurin Ubangiji Allah na Ibrahim, da Ishaku, da Isra'ila domin ya sāke juyowa zuwa ga sauranku, waɗanda kuka kuɓuta daga hannun sarakunan Assuriya. 7 Kada fa ku zama kamar kakanninku ko 'yan'uwanku, marasa bangaskiya ga Ubangiji Allah na kakanninsu, saboda haka ya maishe su kufai kamar yadda kuka gani. 8 Kada ku yi taurin kai kamar yadda kakanninku suka yi, amma ku miƙa kanku ga Ubangiji, ku zo Wuri Mai Tsarki, wanda ya tsarkake har abada, ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin ya huce daga zafin fushin da yake yi da ku. 9 Gama idan kun juyo zuwa ga Ubangiji, 'yan'uwanku da 'ya'yanku za su sami rahamar waɗanda suka kama su, su komo wannan ƙasa. Gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne, mai jinƙai, ba zai kawar da fuskarsa daga gare ku ba, idan kun komo gare shi.” 10 Manzannin fa suka tafi gari gari a ƙasar Ifraimu, da ta Manassa, har zuwa Zabaluna, amma suka yi musu dariyar raini, suka yi musu ba'a. 11 Sai mutane kaɗan na Ashiru, da na Manassa, da na Zabaluna suka yi tawali'u, suka zo Urushalima. 12 Ikon Allah kuma yana kan Yahuza, ya ba su zuciya ɗaya ta su yi abin da sarki da sarakunansa suka umarta bisa ga maganar Ubangiji. 13 Mutane da yawa kuwa suka zo Urushalima don su yi idin abinci marar yisti a wata na biyu, aka yi babban taro. 14 Sai suka kama aiki, suka kawar da bagadan da suke cikin Urushalima, da dukan bagadan ƙona turare suka kwashe suka zubar a kwarin Kidron. 15 Suka yanka ɗan rago na Idin Ƙetarewa a rana ta sha huɗu ga wata na biyu. Suka sa firistoci da Lawiyawa su sha kunya, saboda haka sai suka tsarkake kansu, suka kawo hadayu na ƙonawa a Haikalin Ubangiji. 16 Sai suka ɗauki matsayinsu wanda aka ayyana bisa ga dokar Musa, mutumin Allah, firistocin suka yafa jinin da suka karɓa daga hannun Lawiyawa. 17 Gama akwai waɗansu da yawa daga cikin taron waɗanda ba su tsarkake kansu ba, saboda haka ya zama tilas Lawiyawa su yanka ɗan rago na Idin Ƙetarewa saboda dukan wanda ba shi da tsarki, domin a tsarkake shi ga Ubangiji. 18 Gama akwai jama'a jingim, da yawa kuwa mutanen Ifraimu ne, da na Manassa, da na Issaka, da na Zabaluna, da ba su tsarkake kansu ba, duk da haka sun ci Idin Ƙetarewa ba yadda aka ƙayyade ba. Sai Hezekiya ya yi addu'a dominsu, yana cewa, “Ya Ubangiji mai alheri, ka gafarta wa ko wanne 19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko bai yi bisa kan dokar tsarkakewa na Wuri Mai Tsarki ba.” 20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya, ya warkar da jama'ar. 21 Jama'ar Isra'ila waɗanda suke a Urushalima kuwa sun yi idin abinci marar yisti da murna mai yawa, har kwana bakwai. Lawiyawa kuma da firistoci suka yabi Ubangiji kowace rana, suna raira waƙa da iyakar ƙarfinsu ga Ubangiji. 22 Hezekiya kuwa ya yi magana ta ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna fasaha a hidimar Ubangiji.

An Ƙara Yin Idin

Mutane fa suka ci abincin idin har kwana bakwai, suna miƙa hadayu na salama, suna ta yin godiya ga Ubangiji Allah na kakanninsu. 23 Sai dukan taron suka yarda su ci gaba da yin idin har waɗansu kwana bakwai ɗin kuma, sai suka ci gaba da yin idin har kwana bakwai da murna. 24 Gama Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya ba taron bijimai dubu (1,000 ) da tumaki dubu bakwai (7,000 ), don yin hadayu, sarakuna kuma sun ba taron bijimai dubu (1,000 ) da tumaki dubu goma (10,000 ). Firistoci da yawa suka tsarkake kansu. 25 Dukan taron Yahuza, da firistoci, da Lawiyawa, da dukan taron jama'a da suka zo daga Isra'ila, da baƙi waɗanda suka zo daga ƙasar Isra'ila, da baƙin da suka zauna a Yahuza, suka yi murna. 26 Saboda haka an yi babban farin ciki a Urushalima, gama tun daga zamanin Sulemanu ɗan Dawuda, Sarkin Isra'ila, ba a yi wani abu kamar haka a Urushalima ba. 27 Sai firistoci da Lawiyawa suka tashi suka sa wa jama'a albarka, aka kuwa ji muryarsu, addu'arsu kuma ta kai wurin zamansa a Sama.

2 Tarihi 31

Shirin Hezekiya domin Firistoci da Lawiyawa

1 Sa'ad da aka gama duka, sai dukan Isra'ilawa da suka hallara, suka bi cikin biranen Yahuza, suka farfashe al'amudan, suka ragargaza Ashtarot, suka farfashe masujadai da bagadai duka da suke a Yahuza da Biliyaminu, da na Ifraimu da Manassa har suka hallakar da su duka. Sa'an nan dukan jama'ar Isra'ila suka koma garuruwansu, ko wanne zuwa mahallinsa. 2 Hezekiya kuma ya raba firistoci da Lawiyawa kashi kashi, ko wanne da hidimarsa, firistoci da Lawiyawa, don hadayu na ƙonawa da na salama, su yi hidima a ƙofofin Ubangiji, don su yi godiya da yabo. 3 Daga dukiyarsa kuma ya ba da taimako na abin yin hadayun ƙonawa, wato hadayun ƙonawa na safe da na maraice, da hadayun ƙonawa na ranakun Asabar, da na amaryar wata, da na ƙayyadaddun idodi, kamar yadda aka rubuta a Attaura ta Ubangiji. 4 Hezekiya ya kuma umarci jama'ar da ke zaune a Urushalima su riƙa ba da rabon firistoci da na Lawiyawa, domin su mai da hankali ga dokar Ubangiji. 5 Nan da nan da aka baza labarin umarnin ko'ina, sai jama'ar Isra'ila suka ba da nunan fari na hatsinsu, da ruwan inabi, da mai, da zuma, da amfanin gona duka, suka kuma kawo zaka mai yawa ta kowane irin abu. 6 Jama'ar Isra'ila da na Yahuza waɗanda suke zaune a garuruwan Yahuza, su ma sun kawo tasu zaka ta shanu, da ta tumaki, da ta abubuwan da aka keɓe aka kuma tsarkake domin Ubangiji Allahnsu, suka tara su tsibi tsibi. 7 A wata na uku ne suka fara tattara tsibi tsibin, suka gama a wata na bakwai. 8 Sa'ad da Hezekiya da sarakuna suka zo suka ga tsibi tsibin, sai suka yabi Ubangiji da jama'arsa Isra'ila. 9 Hezekiya kuma ya yi wa firistoci da Lawiyawa tambaya a kan tsibi tsibin. 10 Sai Azariya, babban firist na gidan Zadok, ya amsa masa, ya ce, “Tun lokacin da suka fara kawo sadakarsu a Haikalin Ubangiji, mun ci mun ƙoshi, abin da ya ragu kuwa yana da yawa, gama Ubangiji ya sa wa jama'arsa albarka, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.” 11 Sai Hezekiya ya umarce su su shirya ɗakuna a Haikalin Ubangiji, suka kuwa shirya. 12 Da aminci suka kawo sadakokinsu, ta zaka da ta keɓaɓɓun abubuwa. Babban shugaban da yake lura da su kuwa, shi ne Konaniya, Balawe, da Shimai ɗan'uwansa, shi ne na biyu, 13 sa'an nan da Yehiyel, da Azaziya, da Nahat, da Asahel, da Yerimot, da Yozabad, da Eliyel, da Ismakiya, da Mahat, da Benaiya su ne shugabanni, mataimakan Konaniya da Shimai waɗanda sarki Hezekiya da Azariya babban shugaban Haikalin Allah suka naɗa. 14 Kore kuwa ɗan Imna Balawe, mai tsaron ƙofar gabas, yake lura da hadayu na yardar rai ga Allah, don ya karkasa bayarwar da aka keɓe domin Ubangiji da hadayu mafi tsarki. 15 Eden, da Miniyamin, da Yeshuwa, da Shemaiya, da Amariya, da Shekaniya suna taimakonsa da zuciya ɗaya a biranen firistoci, don su rarraba wa 'yan'uwansu rabonsu, tsofaffi da yara, duka ɗaya ne, bisa ga ƙungiyoyinsu, 16 da su kuma waɗanda aka rubuta bisa ga asali, 'yan samari masu shekara uku zuwa sama, duk dai waɗanda za su shiga Haikalin Ubangiji don yin hidima, kamar yadda aka tsara, bisa ga matsayinsu yadda aka karkasa su. 17 Aka kuma rubuta firistoci bisa ga gidajen kakanninsu, na wajen Lawiyawa kuwa, tun daga mai shekara ashirin zuwa sama, bisa ga matsayinsu, ta yadda aka karkasa su. 18 Aka rubuta firistoci tare da dukan ƙananan 'ya'yansu, da matansu, da 'ya'yansu mata da maza, dukansu gaba ɗaya, gama da zuciya ɗaya suka tsarkake kansu. 19 Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa 'ya'yan Haruna, firist, maza kuwa, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namiji da aka rubuta na Lawiyawa, nasa rabo. 20 Haka kuwa Hezekiya ya yi a dukan Yahuza, ya aikata abin da yake daidai, da aminci, a gaban Ubangiji Allahnsa. 21 Kowane irin aiki da ya kama na hidimar Haikalin Allah, wanda yake kuma bisa ga doka da umarni, na neman Allahnsa, ya yi su da zuciya ɗaya, ya kuwa arzuta.

2 Tarihi 32

Assuriyawa sun Yi Barazana ga Urushalima

1 Bayan waɗannan abubuwa, da waɗannan ayyukan aminci, sai Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya kawo wa Yahuza yaƙi, ya kafa sansani kewaye da garuruwa masu garu, yana zaton zai ci su da yaƙi su zama nasa. 2 Da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo da nufin ya yi yaƙi da Urushalima, 3 sai ya yi shawara shi da jarumawansa da manyan mutanensa, su datse ruwan da yake fitowa daga maɓuɓɓugar da take bayan birni, suka kuwa taimake shi. 4 Don haka mutane da yawa suka taru suka daddatse dukan maɓuɓɓugai da rafuffuka da suke gudu cikin ƙasar, suna cewa, “Bari mu hana sarakunan Assuriya samun ruwa idan sun iso Urushalima.” 5 Sai ya kama aiki gadangadan, ya sāke gina dukan garukan da suka rushe, ya gina hasumiya a kai, ya kuma gina wani garu bayan wannan, ya ƙara ƙarfin Millo a birnin Dawuda, ya kuma yi makamai na yaƙi da garkuwoyi masu yawan gaske. 6 Sai ya sa manyan sojoji su shugabanci jama'a. Su tattaro su gare shi a dandalin ƙofar birni, ya yi musu magana ta ƙarfafawa ya ce, 7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda Sarkin Assuriya, da dukan taron da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su. 8 Hannun mutum yake tare da shi, amma mu Ubangiji Allahnmu yake tare da mu, domin ya taimake mu, ya yi yaƙi dominmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuza. 9 Bayan wannan sai Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya aika da barorinsa zuwa Urushalima, sa'an nan kuma ya kewaye Lakish da dukan mayaƙansa tare da shi, yana yaƙi da Hezekiya, Sarkin Yahuza, da dukan mutanen Yahuza waɗanda suke a Urushalima, yana cewa, 10 “Ga abin da Sennakerib, Sarkin Assuriya, ya ce, ‘Ga me kake dogara, da har yanzu kuka dāge a cikin Urushalima, ga shi kuwa, yaƙi ya kewaye ta? 11 Ai, Hezekiya, ba ruɗinku yake yi ba, don ya sa ku mutu da yunwa da ƙishi sa'ad da yake ce muku Ubangiji Allahnku zai cece ku daga hannun Sarkin Assuriya? 12 Ashe, ba wannan Hezekiya ba ne ya ɗauke masujadansa da bagadansa, ya kuma umarci Yahuza da Urushalima, su yi sujada a gaban bagade guda, a kansa ne kuma za su ƙona hadayu? 13 Ashe, ba ku san abin da ni da kakannina muka yi wa dukan jama'ar waɗansu ƙasashe ba? Gumakan al'umman waɗannan ƙasashe sun iya ceton ƙasashensu daga hannuna? 14 Daga cikin dukan gumakan waɗannan al'ummai waɗanda kakannina suka hallakar da su sarai, ba wanda ya iya ceton jama'arsa daga hannuna, har da Allahnku zai iya cetonku daga hannuna? 15 Yanzu fa kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, ko ya ɓad da ku haka, kada kuwa ku gaskata shi, gama ba wani gunki na wata al'umma, ko wani mulki wanda ya taɓa ceton jama'arsa daga hannuna, ko kuma daga hannun kakannina. Wane Allah naku har da zai iya cetonku daga hannuna?’ ” 16 Barorinsa kuwa suka ƙara yin maganganun saɓo gāba da Ubangiji Allah da bawansa Hezekiya. 17 Ya kuma rubuta wasiƙu, ya zargi Ubangiji Allah na Isra'ila, ya yi maganar saɓo, yana cewa, “Kamar yadda gumakan al'umman sauran ƙasashe suka kāsa ceton jama'arsu daga hannuna, hakanan kuma Allahn Hezekiya ba zai iya ceton jama'arsa daga hannuna ba.” 18 Da babbar murya, da Yahudanci kuwa, suka yi ta yin magana da jama'ar Urushalima waɗanda suke kan garu, don a tsoratar da su, a kuma firgita su, don su ci birnin. 19 Suka yi ta magana a kan Allah na Urushalima, kamar yadda suka yi magana a kan gumakan al'ummai, wato aikin hannuwan mutane.

Ubangiji ya Ceci Hezekiya

20 Sai sarki Hezekiya, da annabi Ishaya ɗan Amoz, suka yi addu'a saboda wannan al'amari, suka yi kuka zuwa Sama. 21 Ubangiji kuwa ya aiki mala'ika wanda ya karkashe manyan jarumawa, da sarakunan yaƙi, da shugabanni, da kowane riƙaƙƙen soja, da sarkin yaƙi da yake a sansanin Sarkin Assuriya. Sai ya koma ƙasarsa cike da kunya. Sa'ad da ya shiga gidan gunkinsa, sai waɗansu daga cikin 'ya'yan cikinsa suka kashe shi da takobi. 22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mazaunan Urushalima daga hannun Sennakerib Sarkin Assuriya, daga kuma hannun dukan maƙiyansa, ya hutar da su ta kowace fuska. 23 Mutane da yawa suka kawo wa Ubangiji sadakoki a Urushalima, suna kuma kawo wa Hezekiya Sarkin Yahuza abubuwa masu daraja. Saboda haka ya sami ɗaukaka a idon dukan sauran al'ummai, tun daga wannan lokaci har zuwa gaba.

Hezekiya ya yi Ciwo

24 A kwanakin nan kuwa Hezekiya ya yi ciwo gab da mutuwa, sai ya yi addu'a ga Ubangiji, Ubangiji kuwa ya amsa masa ya ba shi alama. 25 Amma Hezekiya bai nuna godiya a kan amfanin da ya samu ba, saboda girmankai. Saboda haka hasala ta auka kansa, da kan Yahuza da Urushalima. 26 Amma Hezekiya ya ƙasƙantar da kansa saboda girmankan da ya yi, shi da mazaunan Urushalima, saboda haka hasalar Ubangiji ba ta faɗa musu a kwanakin Hezekiya ba.

Hezekiya ya Karɓi 'Yan Saƙo daga Babila

27 Hezekiya yana da dukiya ƙwarai, yana kuma da girma. Sai ya gina wa kansa taskoki inda zai ajiya azurfa, da zinariya, da duwatsu masu daraja, da kayan yaji, da garkuwoyi, da dukan tasoshi, da kwanoni masu daraja. 28 Yana kuma da ɗakunan ajiya na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai. Yana da wuraren turke shanu na kowane iri, yana kuma da garkunan tumaki. 29 Ya kuma giggina wa kansa birane, yana da garkunan tumaki da na awaki, da na shanu a yalwace. Gama Allah ya mallakar masa da abubuwa masu yawa. 30 Hezekiyan nan kuwa ya datse ruwan da yake gangarawa daga kogin Gihon, ya karkatar da su su gangara zuwa wajen yammacin birnin Dawuda. Hezekiya ya arzuta da dukan ayyukan da ya yi. 31 A kan 'yan saƙon sarakunan Babila kuwa, waɗanda aka aiko su don su bincika irin abin al'ajabi da ya faru a ƙasar, sai Allah ya ƙyale shi kurum don ya jarraba shi, ya san dukan abin da yake a zuciyarsa.

Mutuwar Hezekiya

32 Sauran ayyukan Hezekiya da kyawawan ayyukansa, ga shi, an rubuta su a wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a littafin sarakunan Yahuza da na Isra'ila. 33 Sai Hezekiya ya rasu, suka binne shi a sashe na bisa na hurumin 'ya'yan Dawuda, maza. Dukan Yahuza da mazaunan Urushalima suka girmama shi sa'ad da ya rasu. Sai Manassa ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 33

Sarki Manassa na Yahuza

1 Manassa yana da shekara goma sha biyu sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara hamsin da biyar yana mulki a Urushalima. 2 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, ya yi irin ayyukan banƙyama da al'ummai waɗanda Ubangiji ya kore su a gaban jama'ar Isra'ila suke yi. 3 Gama ya sāke giggina masujadai waɗanda Hezekiya, tsohonsa, ya rurrushe. Ya kakkafa bagadai don Ba'al, ya kuma yi Ashtarot. Ya yi sujada ga dukan rundunar sama, ya bauta musu. 4 Ya kuma giggina bagadai a cikin Haikalin Ubangiji inda Ubangiji ya ce, “A Urushalima sunana zai kasance har abada.” 5 Ya giggina bagadai ga dukan rundunar sama a farfajiyan nan biyu na cikin Haikalin Ubangiji. 6 Ya miƙa 'ya'yansa maza hadaya ta ƙonawa a kwarin ɗan Hinnom. Ya yi bokanci, ya yi duba, ya yi tsubbu, yana kuma sha'ani da makarai da mayu. Ya aikata mugunta ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanar fushin Ubangiji. 7 Sai ya kafa gunkin da ya yi a cikin Haikalin Allah, wanda Allah ya faɗa wa Dawuda da ɗansa Sulemanu ya ce, “A cikin wannan Haikali da a Urushalima, inda na zaɓa daga cikin dukan kabilan Isra'ila, zan sa sunana har abada. 8 Ba zan ƙara fitar da Isra'ila daga ƙasar da na ba kakanninku ba, in dai sun lura, sun kiyaye, sun aikata dukan abin da na umarce su, da dukan shari'a, da dokoki, da ka'idodi da aka bayar ta hannun Musa.” 9 Ta haka kuwa Manassa ya lalatar da Yahuza da mazaunan Urushalima. Suka aikata muguntar da ta fi ta al'umman da Ubangiji ya hallaka a gaban jama'ar Isra'ila.

Tuban Manassa

10 Ubangiji fa ya yi magana da Manassa da jama'arsa, amma ba wanda ya kula. 11 Saboda haka Ubangiji ya sa sarakunan yaƙi na Sarkin Assuriya su kamo Manassa da ƙugiyoyi, su ɗaure shi da sarƙoƙin tagulla, su kai shi Babila. 12 Amma sa'ad da yake wahala, sai ya roƙi jinƙan Ubangiji Allahnsa, ya ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa. 13 Sa'ad da ya yi addu'a gare shi, Allah ya karɓi roƙonsa da hurwarsa, ya sāke komar da shi Urushalima da mulkinsa. Sa'an nan ne Manassa ya sani Ubangiji shi ne Allah. 14 Bayan haka sai ya gina garu a bayan garin Dawuda a yammacin Gihon, a kwari har zuwa Ƙofar Kifi, ya kewaye da shi zuwa Ofel, ya gina shi da tsayi sosai. Sa'an nan ya sa sarakunan yaƙi a garuruwa masu garu na Yahuza. 15 Ya kwashe gumaka da siffofi daga cikin Haikalin Ubangiji, da dukan bagadan da ya giggina a bisa dutse na Haikalin Ubangiji da a Urushalima. Ya zubar da su a bayan birnin. 16 Ya kuma komar da bagaden Ubangiji, ya miƙa hadayu na salama da na godiya, ya kuma umarci Yahuza ta bauta wa Ubangiji Allah na Isra'ila. 17 Duk da haka dai jama'a suka ci gaba da miƙa hadayunsu a masujadai, amma ga Ubangiji Allahnsu kaɗai.

Ƙarshen Mulkin Manassa

18 Sauran ayyukan Manassa, da addu'o'insa zuwa ga Allahnsa, da abubuwan da masu gani suka faɗa sa'ad da suka yi masa magana da sunan Ubangiji Allah na Isra'ila, suna cikin littafin tarihin sarakunan Isra'ila. 19 Addu'arsa, da yadda Allah ya karɓi roƙonsa, da dukan zunubinsa, da rashin amincinsa, da wuraren da ya gina masujadai, ya kafa Ashtarot da siffofi, kafin ya ƙasƙantar da kansa, suna nan a rubuce a littafin Hozai. 20 Haka fa Manassa ya rasu, suka binne shi a gidansa, sai Amon ɗansa ya gāji gadon sarautarsa.

Sarki Amon na Yahuza

21 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara biyu yana mulki a Urushalima. 22 Shi ma ya aikata mugunta a gaban Ubangiji yadda Manassa, tsohonsa, ya yi. Amon ya miƙa hadaya ga dukan siffofin da tsohonsa, Manassa, ya yi ya bauta musu. 23 Bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji yadda tsohonsa, Manassa, ya yi ba, amma shi Amon ya yi ta yin zunubi a kai a kai. 24 Sai fadawansa suka yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a gidansa. 25 Jama'ar ƙasar kuwa suka karkashe dukan waɗanda suka yi wa sarki Amon maƙarƙashiyar, suka naɗa Yosiya, ɗansa, ya gāji gadon sarautarsa.

2 Tarihi 34

Sarki Yosiya na Yahuza

1 Yosiya yana da shekara takwas sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki shekara talatin da ɗaya a Urushalima. 2 Ya aikata abin da yake daidai a gaban Ubangiji, yana bin al'amuran da kakansa Dawuda ya yi, bai kauce dama ko hagu ba.

Yosiya yana gāba da Arnanci

3 A shekara ta takwas ta mulkinsa, a lokacin yana yaro, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma, sha biyu, sai ya fara tsarkake Yahuza da Urushalima daga masujadai, da Ashtarot, da sassaƙaƙƙun siffofi, da siffofi na zubi. 4 Sai suka farfashe bagadai na Ba'al a gabansa, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu. Ya ragargaza Ashtarot, da sassaƙaƙƙun siffofi, da na zubi, ya maishe su ƙura. Ya barbaɗa su a kan kaburbura waɗanda suka miƙa hadayu a kansu. 5 Ya kuma ƙone ƙasusuwan firistoci a bisa bagadansu, ya tsarkake Yahuza da Urushalima. 6 A biranen Manassa, da na Ifraimu, da na Saminu, har zuwa Naftali, a kangwayensu kewaye da su, 7 ya farfashe bagadai, ya buge Ashtarot da siffofi, ya maishe su gari, ya tumɓuke dukan bagadan ƙona turare a dukan ƙasar Isra'ila, sa'an nan ya koma Urushalima.

An Gano Littafin Shari'a

8 A shekara ta goma sha takwas ta mulkinsa, bayan da ya gama tsarkake ƙasar, da Haikalin, sai ya aiki Shafan ɗan Azaliya, da Ma'aseya mai mulkin birnin, da Yowa ɗan Yowahaz, wanda yake magatakarda domin su gyara Haikalin Ubangiji Allahnsa. 9 Sai suka zo wurin Hilkiya babban firist, suka ba shi kuɗin da aka kawo a Haikalin Allah, wanda Lawiyawa, masu tsaron ƙofa, suka tattara daga mutanen Manassa da na Ifraimu, daga sauran Isra'ila, da kuma na dukan Yahuza da Biliyaminu, tare da na mazaunan Urushalima. 10 Sai suka ba da kuɗin ga ma'aikata masu lura da Haikalin Ubangiji, da ma'aikatan da suke aiki a Haikalin Ubangiji, don gyare-gyare, su maishe shi kamar yadda yake dā, 11 sai suka ba masassaƙa da magina kuɗin, don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katako, don yin tsaiko da tankar gine-ginen da sarakunan Yahuza suka bari, har suka lalace. 12 Mutanen fa suka yi aiki mai aminci tare da waɗanda suke lura da su domin su gabatar da aiki, wato Yahat da Obadiya, Lawiyawa, 'ya'yan Merari, maza, da Zakariya da Meshullam na wajen 'ya'yan Kohatawa, da waɗansu Lawiyawa da suke da gwanintar bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe. 13 Su ne shugabannin masu ɗaukar kaya, suke kuma nuna wa kowane ma'aikaci irin aikin da zai yi, waɗansu daga cikin Lawiyawa, magatakarda ne, da ma'aikatan hukuma, da masu tsaron ƙofofi. 14 Sa'ad da suke fitowa da kuɗin da aka kawo a Haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya gāno littafin Shari'ar Ubangiji wanda aka bayar ta hannun Musa. 15 Sai Hilkiya ya ce wa magatakarda Shafan, “Na gāno Littafin Shari'a a Haikalin Ubangiji.” Sai Hilkiya ya ba Shafan littafin. 16 Shafan kuma ya kai wa sarki littafin, sa'an nan ya faɗa wa sarki cewa, “Dukan abin da aka sa barorinka su yi suna yi. 17 Sai suka juye kuɗin da aka samu don Haikalin Ubangiji, suka miƙa wa masu lura da aikin, da ma'aikatan.” 18 Magatakarda Shafan kuwa ya faɗa wa sarki, ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta wa sarki littafin. 19 Da sarki ya ji irin maganganun da littafin ya faɗa, sai ya yayyage tufafinsa. 20 Sa'an nan sarki ya umarci Hilkiya, da Ahikan ɗan Shafan, da Akbor ɗan Mika, da magatakarda Shafan, da Asaya baran sarki, ya ce, 21 “Ku tafi ku yi tambaya a wurin Ubangiji domina, da kuma domin sauran waɗanda suka ragu a Isra'ila da Yahuza, a kan abin da littafin da aka gāno ya faɗa, gama Ubangiji ya yi fushi da mu da hasala mai tsanani saboda kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji, su aikata bisa ga dukan abin da aka faɗa a wannan littafi ba.” 22 Hilkiya kuwa tare da waɗanda sarki ya aika suka tafi wurin annabiya Hulda, matar Shallum ɗan Tikwa, ɗan Harhas, mai lura da wurin ajiyar tufafi, tana zaune a Urushalima, a unguwa ta biyu. Suka faɗa mata saƙon sarki, 23 sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya ce in faɗa wa mutumin da ya aiko gare shi, 24 ‘Ni Ubangiji, na ce zan kawo masifa a kan wannan wuri da a kan mazaunan wurin, wato dukan la'anar da aka rubuta a littafin da aka karanta a gaban Sarkin Yahuza. 25 Da yake sun bar bina suka ƙona turare ga gumaka domin su sa ni in yi fushi da dukan ayyukan hannuwansu, saboda haka zan yi fushi da wannan wuri, ba kuwa zan huce ba.’ 26 Amma a kan Sarkin Yahuza wanda ya aike ku ku tambayi Ubangiji, ga abin da za ku faɗa masa, ‘Ni Ubangiji, Allah na Isra'ila na ce, a kan maganar da ka ji, 27 da yake zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah, sa'ad da ka ji maganarsa a kan wurin nan da mazaunan wurin, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yayyage tufafinka ka yi kuka a gabana, ni kuma na ji ka. 28 Ga shi, zan kai ka wurin da kakanninka suke, a kabarinka a binne ka da salama, ba za ka ga dukan masifun da zan kawo wa wurin nan da mazaunansa ba.’ ” Sai suka isar da amsa wurin sarki.

Yosiya ya Kawar da Arnanci

29 Sarki ya aika a kirawo dukan dattawan Yahuza da na Urushalima. 30 Sai sarki ya haura zuwa Haikalin Ubangiji tare da dukan mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima, da firistoci, da Lawiyawa, da dukan jama'a, babba da yaro. Sai ya karanta dukan maganar da take a littafin alkawari wanda aka gāno a Haikalin Ubangiji, a kunnen dukansu. 31 Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya yi alkawari a gaban Ubangiji, cewa zai bi Ubangiji, ya kiyaye umarnansa, da farillansa, da dokokinsa da zuciya ɗaya, da dukan ransa. Zai yi aiki da alkawarin da yake rubuce a wannan littafi. 32 Ya kuma sa dukan waɗanda suke a Urushalima da na Biliyaminu, su tsaya a kan wannan magana. Mazaunan Urushalima kuwa suka yi yadda alkawarin Allah ya ce, wato Allah na kakanninsu. 33 Yosiya kuwa ya kawar da dukan abubuwan banƙyama daga dukan ƙasar da jama'ar Isra'ila suke da ita. Ya sa dukan waɗanda suke a Isra'ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. A dukan kwanakin ransa, ba su kauce daga bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.

2 Tarihi 35

Yosiya ya Yi Idin Ƙetarewa

1 Yosiya kuwa ya yi Idin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima. A rana ta goma sha huɗu ga wata na fari suka yanka ragon Idin Ƙetarewa. 2 Ya sa firistoci a matsayinsu, ya ƙarfafa su a hidimar Haikalin Ubangiji. 3 Ya kuma faɗa wa Lawiyawa, tsarkakakku na Ubangiji, waɗanda suke koya wa dukan Isra'ila, ya ce, “Ku sa tsattsarkan akwatin alkawari a Haikalin da Sulemanu ɗan Dawuda, Sarkin Isra'ila, ya gina. Ba za ku sāke ɗaukarsa bisa kafaɗunku ba. Yanzu fa sai ku kama hidimar Ubangiji Allahnku da jama'arsa Isra'ila. 4 Ku karkasa kanku bisa ga gidajen kakanninku ƙungiya ƙungiya, ku bi bayanin Dawuda, Sarkin Isra'ila, da na ɗansa Sulemanu. 5 Ku tsaya a Wuri Mai Tsarki, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin 'yan'uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa. 6 Ku yanka abin Idin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku shirya wa 'yan'uwanku su yi bisa ga maganar Ubangiji ta hannun Musa.” 7 Sarki Yosiya fa ya ba da gudunmawar abin yin hadaya ga waɗanda ba firistoci ba, waɗanda suke wurin, raguna da 'yan awaki daga cikin garken tumaki da na awaki, yawansu ya kai dubu talatin (30,000 ) da kuma bijimai dubu uku (3,000 ). Waɗannan duk daga mallakar sarki ne. 8 Da yardar rai manyan ma'aikatansa, sarakunansa, suka ba da gudunmawa ga jama'ar, da firistoci, da Lawiyawa. Hilkiya, da Zakariya, da Yehiyel, manyan ma'aikatan Haikalin Allah, suka ba firistoci abin yin hadaya don Idin Ƙetarewa, tumaki da awaki dubu biyu da ɗari shida (2,600 ), da bijimai ɗari uku. 9 Konaniya kuma tare da Shemaiya da Netanel, 'yan'uwansa, da Hashabiya, da Yehiyel, da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, su suka ba Lawiyawa abin yin hadayar Idin Ƙetarewa, raguna da 'yan awaki dubu biyar (5,000 ), da bijimai ɗari biyar. 10 Sa'ad da aka shirya yin hidimar, firistoci suka tsaya a wurinsu, Lawiyawa kuwa suka tsaya bisa ga ƙungiyoyinsu, yadda sarki ya umarta. 11 Sai suka yanka ragon Idin Ƙetarewar. Sa'an nan firistoci suka karɓi jinin daga gare su, suka yayyafa, Lawiyawa kuma suka yi ta fiɗa. 12 Sa'an nan suka keɓe hadayu na ƙonawa domin su rarraba bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakanni waɗanda su ba firistoci ba ne, don su miƙa wa Ubangiji kamar yadda aka rubuta a littafin Musa. Hakanan kuma suka yi da bijiman. 13 Suka gasa ragon hadayar Idin Ƙetarewa bisa ga ka'idar, sai suka dafa tsarkakan hadayu a tukwane, da manyan tukwane, da kwanoni, nan da nan suka kai wa waɗanda ba firistoci ba. 14 Daga baya kuma suka shirya wa kansu da firistoci, saboda firistoci, 'ya'yan Haruna, maza, suna ta hidimar miƙa hadayu na ƙonawa, da kuma na kitse, har dare. Don haka Lawiyawa suka shirya wa kansu abinci, suka kuma shirya wa firistoci, 'ya'yan Haruna, maza. 15 Mawaƙa, 'ya'yan Asaf, maza, suna wurinsu bisa ga umarnin Dawuda, da Asaf, da Heman, da kuma Yedutun maigani na sarki, matsaran ƙofofi kuma suna a kowace ƙofa, ba lalle sai su bar wurin hidimarsu gama 'yan'uwansu Lawiyawa sun shirya musu nasu. 16 Haka fa aka shirya dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Idin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda Yosiya sarki ya umarta. 17 Jama'ar Isra'ila waɗanda suke wurin, suka kiyaye Idin Ƙetarewa, da kuma idin abinci marar yisti har kwana bakwai. 18 Ba a taɓa yin Idin Ƙetarewa irin wannan ba tun kwanakin annabi Sama'ila, ba wani kuma daga cikin sarakunan Isra'ila da ya kiyaye Idin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya kiyaye shi tare da firistoci, da Lawiyawa, da dukan mutanen Yahuza da na Isra'ila, waɗanda suke a wurin, da kuma mazaunan Urushalima. 19 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya aka yi Idin Ƙetarewa.

Rasuwar Yosiya

20 Bayan wannan duka, sa'ad da Yosiya ya shirya Haikali, sai Neko Sarkin Masar, ya zo don ya yi yaƙi a Karkemish wadda take a Yufiretis, sai Yosiya ya fito don ya kara da shi. 21 Amma Neko ya aika 'yan saƙo su faɗa masa su ce, “Me ya gama mu da juna, ya Sarkin Yahuza? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da Sarkin Assuriya! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada ya hallaka ka.” 22 Duk da haka Yosiya bai yarda ya koma ba, sai ya ɓad da kama don ya yi yaƙi da shi. Bai yarda da magana wadda Allah ya faɗa wa Neko ba, sai suka kama yaƙi a filin Magiddo. 23 Maharba suka harbi sarki Yosiya, sai ya ce wa barorinsa, “Ku ɗauke ni ku tafi da ni, gama an yi mini mummunan rauni.” 24 Barorinsa kuwa suka ɗauke shi daga cikin karusa, suka sa shi a karusa ta biyu, suka kawo shi Urushalima, sai ya rasu. Aka binne shi a hurumin kakanninsa. Yahuza da Urushalima fa suka yi makoki domin Yosiya. 25 Irmiya kuma ya hurta makoki domin Yosiya. Hakanan kuma dukan mawaƙa mata da maza, suka ambaci Yosiya cikin makokinsu har yau. Suka sa waɗannan su zama farali a Isra'ila, ga shi kuma, an rubuta su a Littafin Makoki. 26 Sauran ayyukan Yosiya, da kyawawan ayyukansa, waɗanda ya yi bisa ga abin da aka rubuta a Shari'ar Ubangiji, 27 ayyukansa na fari da na ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila da na Yahuza.

2 Tarihi 36

Sarki Yehowahaz na Yahuza

1 Jama'ar ƙasa kuwa suka ɗauki Yehowahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki. Ya gaji tsohonsa a Urushalima. 2 Yehowahaz yana da shekara ashirin da uku sa'ad da ya ci sarauta, ya kuwa yi mulki a Urushalima wata uku. 3 Sai Sarkin Masar ya tuɓe shi daga sarautarsa ta Urushalima, ya sa su biya gandu, su ba da azurfa talanti ɗari, da zinariya talanti guda. 4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan'uwansa, sarki a Yahuza da Urushalima. Ya sa masa sabon suna Yehoyakim. Amma Neko ya ɗauko Yehowahaz ɗan'uwan Eliyakim ya kai shi Masar.

Sarki Yehoyakim na Yahuza

5 Yehoyakim yana da shekara ashirin da biyar sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi shekara goma sha ɗaya yana sarauta a Urushalima. Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnsa. 6 Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya ɗaure shi da sarƙoƙi, ya kai shi Babila. 7 Nebukadnezzar kuma ya kwaso waɗansu tasoshi da tukwane na Haikalin Ubangiji, ya kai Babila, ya ajiye su a fādar Babila. 8 Sauran ayyukan Yehoyakim da irin abubuwan da ya yi na banƙyama, da irin laifofinsa, suna nan, an rubuta su a littafin sarakunan Isra'ila da na Yahuza. Ɗansa Yekoniya kuwa ya gāji gadon sarautarsa.

An Kama Sarki Yekoniya

9 Yekoniya yana da shekara takwas sa'ad da ya ci sarauta, ya yi sarauta a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji. 10 Da bazara sai sarki Nebukadnezzar ya aika aka kawo shi Babila tare da kayayyaki masu daraja na Haikalin Ubangiji. Ya kuma naɗa Zadakiya ɗan'uwan Yekoniya ya zama Sarkin Yahuza da Urushalima.

Sarki Zadakiya na Yahuza

11 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya ci sarauta, ya yi shekara goma sha ɗaya yana sarautar Urushalima. 12 Ya aikata mugunta a gaban Ubangiji Allahnsa. Bai nuna ladabi a gaban annabi Irmiya ba, wanda ya faɗa masa abin da Ubangiji ya ce.

Fāɗuwar Urushalima

13 Ya kuwa tayar wa sarki Nebukadnezzar wanda ya rantsar da shi da Allah. Amma ya ƙi kula, ya taurare zuciyarsa gāba da Ubangiji, Allah na Isra'ila. 14 Dukan manyan firistoci da sauran jama'a gaba ɗaya, sun zama marasa aminci ƙwarai suna aikata dukan abubuwan banƙyama da al'ummai suke yi. Suka ƙazantar da Haikalin Ubangiji wanda ya tsarkake a Urushalima. 15 Sai Ubangiji, Allah na kakanninsu, ya yi ta aika musu da manzanni saboda yana juyayin jama'arsa da wurin zaman zatinsa. 16 Sai suka yi ta yi wa manzannin Allah ba'a, suka raina maganarsa, suka yi wa annabawansa ba'a, sai Ubangiji ya husata da jama'arsa don abin ya kai intaha.

An Kai Yahuza Bautar Talala

17 Don haka Ubangiji ya bashe su ga Sarkin Kaldiyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a Haikali, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka a hannunsa. 18 Ya kwaso dukan kayayyakin da suke a Haikalin Allah, manya da ƙanana, da dukiyar da take a Haikalin Allah, da ta sarki, da ta sarakunansa ya kai su Babila. 19 Suka ƙone Haikalin Allah suke rushe garun Urushalima, suka ƙone dukan fādodinta, suka lalatar da dukan kayanta masu daraja. 20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa ya kwashe su, ya kai Babila, suka zama bayinsa da na 'ya'yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa, 21 don maganar ta cika wadda Ubangiji ya faɗa ta bakin Irmiya, har lokacin da ƙasar take shan hutawar asabatanta na zamanta kango har shekara saba'in, ta kiyaye asabatai. 22 Ubangiji kuwa ya iza Sairus Sarkin Farisa a shekarar da ya ci sarauta, domin a cika maganar da Ubangiji ya faɗa wa Irmiya. Sai ya yi shela a dukan ƙasar mulkinsa, aka kuma rubuta shelar. 23 Ga shelar, “In ji Sairus Sarkin Farisa, Ubangiji, Allah na samaniya ya ba ni sarautar dukan duniya, ya kuma umarce ni in gina masa Haikali a Urushalima, ta ƙasar Yahuza. Duk wanda yake na mutanensa da yake nan, Ubangiji Allahnsa ya kasance tare da shi, bari ya haura zuwa can Urushalima.”

Ezra 1

Umarnin Sarki Sairus Yahudawa su Koma

1 Ubangiji kuwa ya iza Sairus Sarkin Farisa a shekarar da ya ci sarauta, domin a cika maganar da Ubangiji ya faɗa wa Irmiya. Sai ya yi shela a dukan ƙasar mulkinsa, aka kuma rubuta shelar. 2 Ga shelar, “In ji Sairus Sarkin Farisa, Ubangiji, Allah na samaniya ya ba ni sarautar dukan duniya, ya kuma umarce ni in gina masa Haikali a Urushalima, ta ƙasar Yahuza. 3 Duk wanda yake na mutanensa da yake nan Ubangiji Allahnsa ya kasance tare da shi, bari ya haura zuwa can Urushalima ta ƙasar Yahuza don ya sāke gina Haikalin Ubangiji, Allah na Isra'ila, shi ne Allah wanda ake masa sujada a Urushalima. 4 A duk inda akwai wani Bayahude, sai mutanen wurin su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da dabbobi, tare da waɗansu kyautai na yardar rai saboda Haikalin Ubangiji wanda yake a Urushalima.”

Komowar Kamammu zuwa Urushalima

5 Shugabannin gidajen kakanni na Yahuza kuwa, da na Biliyaminu, da firistoci, da Lawiyawa, da duk wanda Ubangiji ya taɓa shi, suka tashi don su tafi su sāke gina Haikalin Ubangiji wanda yake a Urushalima. 6 Dukan waɗanda suke kewaye da su, suka taimake su da azurfa, da zinariya, da kayayyaki, da dabbobi, da abubuwa masu daraja, da kyautai na yardar rai. 7 Sarki Sairus kuma ya fito da kayayyakin Haikalin Ubangiji, waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya ajiye su a haikalin gumakansa. 8 Sairus Sarkin Farisa ya sa ma'aji, Mitredat, ya fito da kayayyakin, ya ƙidaya wa Sheshbazzar, shugaban Yahuza. 9 Yawan kayayyakin ke nan, kwanonin zinariya guda talatin, da kwanonin azurfa guda dubu (1,000 ), da wuƙaƙe guda ashirin da tara, 10 da finjalai na zinariya guda talatin, da tasoshi na azurfa ɗari huɗu da goma, da waɗansu kayayyaki guda dubu (1,000 ). 11 Jimillar kayayyakin duka, na zinariya da na azurfa, dubu biyar da arbaminya (5,400 ). Sheshbazzar ya tafi da waɗannan kayayyaki duka tare da kamammun da suka komo daga Babila. 2 .1 Yawan Kamammu da suka Komo. Yawan Kamammu da suka Komo.

Ezra 2

1 Waɗannan su ne mutanen da suka bar lardin Babila suka komo Urushalima da Yahuza daga bautar talala da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kai su Babila. Kowa ya koma garinsu. 2 Sun komo tare da Zarubabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Seraiya, da Re'elaya, da Mordekai, da Bilshan, Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba'ana. Ga jerin iyalan Isra'ila, da yawan waɗanda suka komo na kowane iyali daga zaman talala. 3-20 Zuriyar Farosh, mutum dubu biyu da ɗari da saba'in da biyu (2,172 ) Zuriyar Shefatiya, mutum ɗari uku da saba'in da biyu Zuriyar Ara, mutum ɗari bakwai da saba'in da biyar Zuriyar Fahat-mowab na zuriyar Yeshuwa da Yowab, mutum dubu biyu da ɗari takwas da goma sha biyu (2,812 ) Zuriyar Elam, mutum dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254 ) Zuriyar Zattu, mutum ɗari tara da arba'in da biyar Zuriyar Zakkai, mutum ɗari bakwai da sittin Zuriyar Bani, mutum ɗari shida da arba'in da biyu Zuriyar Bebai, mutum ɗari shida da ashirin da uku Zuriyar Azgad, mutum dubu da ɗari biyu da ashirin da biyu (1,222 ) Zuriyar Adonikam, mutum ɗari shida da sittin da shida Zuriyar Bigwai, mutum dubu biyu da hamsin da shida (2,056 ) Zuriyar Adin, mutum ɗari huɗu da hamsin da huɗu Zuriyar Ater na Hezekiya, mutum tasa'in da takwas Zuriyar Bezai, mutum ɗari uku da ashirin da uku Zuriyar Yora, mutum ɗari da goma sha biyu Zuriyar Hashum, mutum ɗari biyu da ashirin da uku Zuriyar Gibeyon, mutum tasa'in da biyar. 21-35 Mutanen da suke a garuruwan nan, su ma suka komo. Mutanen Baitalami, mutum ɗari da ashirin da uku Mutanen Netofa, mutum hamsin da shida Mutanen Anatot, mutum ɗari da ashirin da takwas Zuriyar Azmawet, mutum arba'in da biyu Zuriyar Kiriyat-yeyarim, da Kefira, da Biyerot, mutum ɗari bakwai da arba'in da uku Zuriyar Rama da Geba, mutum ɗari shida da ashirin da ɗaya Mutanen Mikmash, mutum ɗari da ashirin da biyu Mutanen Betel da Ai, mutum ɗari biyu da ashirin da uku Zuriyar Nebo, mutum hamsin da biyu Zuriyar Magbish, mutum ɗari da hamsin da shida Zuriyar wancan Elam, mutum dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254 ) Zuriyar Harim, mutum ɗari uku da ashirin Zuriyar Lod, da Hadid, da Ono, mutum ɗari bakwai da ashirin da biyar Mutanen Yariko, mutum ɗari uku da arba'in da biyar Zuriyar Senaya, mutum dubu uku da ɗari shida da talatin (3,630 ). 36-39 Ga kuma lissafin iyalan firistocin da suka komo, Zuriyar Yedaiya na gidan Yeshuwa, mutum ɗari da saba'in da uku Zuriyar Immer, mutum dubu da hamsin da biyu (1,052 ) Zuriyar Fashur, mutum dubu da ɗari biyu da arba'in da bakwai (1,247 ) Zuriyar Harim, mutum dubu da goma sha bakwai (1,017 ). 40 Lawiyawa na zuriyar Yeshuwa da Kadmiyel na Hodawiya mutum saba'in da huɗu. 41 Mawaƙa na zuriyar Asaf, mutum ɗari da ashirin da takwas. 42 Zuriyar Shallum, da ta Ater, da ta Talmon, da ta Akkub, da ta Hatita, da ta Shobai, su ne zuriyar matsaran ƙofa, yawan mutanensu duka ɗari da talatin da tara. 43-54 Ga lissafin ma'aikatan Haikali da suka komo. Zuriyar Ziha, da zuriyar Hasufa, da zuriyar Tabbawot Zuriyar Keros, da zuriyar Siyaha, da zuriyar Fadon Zuriyar Lebana, da zuriyar Hagaba, da zuriyar Akkub Zuriyar Hagab, da zuriyar Shamlai, da zuriyar Hanan Zuriyar Giddel, da zuriyar Gahar, da zuriyar Rewaiya Zuriyar Rezin, da zuriyar Nekoda, da zuriyar Gazam Zuriyar Ussa, da zuriyar Faseya, da zuriyar Besai Zuriyar Asna, da Me'uniyawa, da Nefushiyawa Zuriyar Bakbuk, da zuriyar Hakufa da zuriyar Harhur Zuriyar Bazlut, da zuriyar Mehida, da zuriyar Harsha Zuriyar Barkos, da zuriyar Sisera, da zuriyar Tema Zuriyar Neziya, da zuriyar Hatifa 55-57 Zuriyar barorin Sulemanu, su ne Zuriyar Sotai, da zuriyar Hassoferet, da zuriyar Feruda Zuriyar Yawala, da zuriyar Darkon, da zuriyar Giddel Zuriyar Shefatiya, da zuriyar Hattil, da zuriyar Fokeret-hazzebayim, da zuriyar Ami. 58 Dukan zuriyar ma'aikatan Haikali da zuriyar barorin Sulemanu su ɗari uku da tasa'in da biyu ne. 59 Waɗannan su ne waɗanda suka zo daga Tel-mela, da Tel-harsha, da Kerub, da Addan, da Immer, amma ba su iya tabbatar da gidajen kakanninsu da asalinsu ba, ko su na Isra'ila ne. 60 Su ne zuriyar Delaiya, da zuriyar Tobiya, da zuriyar Nekoda. Su ɗari shida da hamsin da biyu ne. 61 Sai kuma zuriyar firistoci, wato zuriyar Habaya, da zuriyar Hakkoz, da zuriyar Barzillai, wanda ya auri mata daga cikin 'ya'yan Barzillai, mata, mutumin Gileyad, aka kira shi da sunnansu, 62 suka bincika littafin asalin kakanninsu, amma suka ga ba su a ciki. Don haka aka mai da su ƙazantattu, ba a yarda musu su yi aikin firist ba. 63 Sai mai mulki ya ce ba za su ci abinci mafi tsarki ba, sai firist ya shawarci Urim da Tummim tukuna, wato kamar kuri'a ke nan. 64-67 Yawan taron jama'a su dubu arba'in da biyu da ɗari uku da sittin (42,360 ). Barorinsu maza da mata, dubu bakwai da ɗari uku da talatin da bakwai (7,337 ) Mawaƙa ɗari biyu mata da maza Dawakansu ɗari bakwai da talatin da shida Alfadaransu ɗari biyu da arba'in da biyar Raƙumansu kuma ɗari huɗu da talatin da biyar ne Jakunansu kuwa dubu shida da ɗari bakwai da ashirin (6,720 ). 68 Waɗansu shugabannin gidajen kakanninsu, sa'ad da suka isa Haikalin Ubangiji a Urushalima, sai suka bayar da kyautai da yardar rai don a sāke gina Haikalin Ubangiji a wurin da yake dā. 69 Gwargwadon arzikinsu suka ba da darik dubu sittin da dubu ɗaya (61,000 ) na zinariya, da maina dubu biyar (5,000 ) na azurfa, da tufafin firistoci guda ɗari. 70 Firistoci, da Lawiyawa, da waɗansu mutane da suke zaune a Urushalima da kewayenta, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da ma'aikatan Haikalin, da dukan mutanen Isra'ila suka zauna a garuruwansu.

Ezra 3

An Komo da Yin Sujada

1 Da tsayawar watan bakwai, sai mutanen Isra'ila waɗanda suka riga suka koma garuruwansu, suka taru gaba ɗaya a Urushalima. 2 Sai Yeshuwa ɗan Yehozadak tare da 'yan'uwansa, firistoci, da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel tare da 'yan'uwansu, suka tashi suka gina bagaden Allah na Isra'ila domin a miƙa hadayu na ƙonawa kamar yadda aka rubuta a dokokin Musa, mutumin Allah. 3 Suka ta da bagaden a wurinsa domin suna jin tsoron mutanen ƙasar. Suka miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa safe da yamma. 4 Suka kuma kiyaye Idin Bukkoki kamar yadda aka rubuta, suna miƙa hadayu na ƙonawa kowace rana bisa ga yawan adadin hadayun da ake bukata. 5 Daga baya kuma suka miƙa hadayun ƙonawa na yau da kullum, da hadayu na amaryar wata, da ƙayyadaddun hadayu na idodin Ubangiji, da hadayu na amaryar wata, da ƙayyadaddun Ubangiji. 6 Tun daga rana ta fari ga watan bakwai, suka fara miƙa wa Ubangiji hadayu na ƙonawa, amma ba a riga an aza harsashin Haikalin Ubangiji ba.

An fara Gina Haikali

7 Sai suka ba magina da masassaƙa kuɗin, suka kuma ba Sidoniyawa da mutanen Taya abinci, da abin sha, da mai don su kawo itacen al'ul daga Lebanon zuwa teku a Yafa bisa ga izinin da suka samu daga wurin sarki Sairus. 8 A watan biyu na shekararsu ta biyu da suka komo wurin Haikalin Allah a Urushalima, sai Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, da Yeshuwa ɗan Yehozadak, da sauran 'yan'uwansu firistoci, da Lawiyawa da dukan waɗanda suka komo Urushalima daga bauta suka fara aikin ginin. Suka sa Lawiyawa 'yan shekara ashirin zuwa gaba su yi shugabancin aikin ginin Haikalin Ubangiji. 9 Sai Yeshuwa da 'ya'yansa da danginsa, da Kadmiyel da 'ya'yansa, da 'ya'yan Hodawiya, da 'ya'yan Henadad, duk Lawiyawa ne, suka yi shugabancin aikin ginin Haikalin Allah. 10 Sa'ad da maginan suka aza harsashin ginin Haikalin Ubangiji, firistoci suna nan tsaye saye da rigunansu, suna riƙe da ƙahoni, Lawiyawa kuma 'ya'yan Asaf, suna riƙe da kuge domin su yabi Ubangiji, bisa ga umarnin Dawuda, Sarkin Isra'ila. 11 Da bangirma suka raira waƙa ta yabo da godiya ga ubangiji, suna cewa, “Ubangiji nagari ne, Gama ƙaunarsa marar matuƙa ce, Ta tabbata har abada ga Isra'ila.” Sai mutane duka suka ɗaga murya da ƙarfi suka yabi Ubangiji, saboda an aza harsashin ginin Haikalin Ubangiji. 12 Amma da yawa daga cikin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin gidajen kakanni, wato tsofaffi waɗanda suka ga Haikali na farko, suka yi kuka da babbar murya a sa'ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan Haikali. Waɗansu kuwa suka yi sowa don farin ciki. 13 Saboda haka mutane ba su iya rarrabe amon muryar murna da ta kuka ba, gama mutanen suka ɗaga murya da ƙarfi har aka ji su daga nesa.

Ezra 4

Magabta suna Hana Aiki

1 Sa'ad da abokan gāban Yahuza da Biliyaminu suka ji waɗanda suka komo daga bauta suna gina Haikalin Ubangiji Allah na Isra'ila, 2 sai suka tafi wurin Zarubabel, da shugabannin gidajen kakanni, suka ce musu, “Ku yarda mana mu yi ginin tare, gama muna yi wa Allahnku sujada kamar yadda kuke yi, muna kuma ta miƙa masa sadaka tun kwanakin Esar-haddon, Sarkin Assuriya, wanda ya kawo mu nan.” 3 Amma Zarubabel, da Yeshuwa, da shugabannin gidajen kakannin Isra'ila suka ce musu, “Ba abin da za ku yi tare da mu na ginin Haikalin Allahnmu, amma mu kaɗai za mu yi wa Ubangiji Allah na Isra'ila, gini kamar yadda sarki Sairus, wato Sarkin Farisa, ya umarce mu.” 4 Sai mutanen ƙasar suka shiga karya zuciyar jama'ar Yahuza, su kuwa suka ji tsoron yin gini. 5 Mutanen kuwa suka yi ijara da mashawarta, da za su sa niyyarsu ta shiririce tun daga zamanin Sairus, Sarkin Farisa, har zuwa zamanin Dariyus, Sarkin Farisa. 6 A farkon sarautar Ahasurus, sai suka rubuta takarda ƙara a kan mazaunan Yahuza, da Urushalima.

Takarda Zuwa ga Sarki

7 A zamanin Artashate kuma sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da magoya bayansu suka rubuta wa Artashate Sarkin Farisa takarda da harufan Suriya, aka fassara ta. 8 Rehum shugaban sojoji, da Shimshai magatakarda, suka rubuta takardar ƙara a kan Urushalima zuwa Sarki Artashate. 9 Sa'an nan Rehum shugaban sojoji ya rubuta tare da Shimshai magatakarda, da abokansu, da alƙalai, da masu mulkin larduna, da ma'aikatan hukumomi, wato mutanen Farisa, da na Erek, da na Babila, da na Shusha a ƙasar Elam, 10 da sauran al'ummai, waɗanda mai girma, Asnaffar, ya kwaso, ya zaunar da su a biranen Samiriya, da sauran wurare na Yammacin Kogi. 11 Ga abin da suka rubuta. “Gaisuwa daga talakawanka, mutane na hayin Kogin zuwa ga sarki Artashate. 12 “Muna sanar da sarki, cewa Yahudawan nan waɗanda suka fito daga gare ka suka zo wurinmu, sun tafi Urushalima, suna sāke gina mugun birnin nan na tawaye, sun fara gina garun, ba da jimawa ba za su gama ginin. 13 Sarki ya sani fa, idan an sāke gina birnin, aka kuma gama garun, ba za su biya haraji ko kuɗin shiga da fita na kaya ko kuɗin fito ba, baitulmalin sarki za ta rasa kuɗi ke nan. 14 Da yake muke cin moriyar fāda, ba daidai ba ne mu bari a raina sarki. Saboda haka muke sanar da sarki, 15 domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka gani a littattafan tarihi, cewa wannan birni na tayarwa ne, mai yin ta'adi ga sarakuna da larduna. A nan ne aka ta da hargitsi a dā. Shi ya sa aka lalatar da shi. 16 Muna sanar da sarki fa, idan aka sāke gina wannan birni da garunsa, ba za ka sami abin mallaka a lardin Yammacin Kogi ba.”

Amsar Sarki

17 Sarki kuma ya aika musu da amsa ya ce, “Gaisuwa zuwa ga Rehum shugaban sojoji, da Shimshai magatakarda, da abokansu waɗanda suke zaune a Samariya da lardin Yammacin Kogi. 18 “An karanta mini wasiƙar da kuka aiko mana, filla filla. 19 Na ba da umarni, aka bincika, aka kuwa tarar, cewa wannan birni ya tayar wa sarakuna a dā, an yi tawaye da hargitsi cikinsa. 20 Manya manyan sarakuna sun yi sarauta a Urushalima, waɗanda suka yi mulki a kan dukan lardin Yammacin Kogi, waɗanda aka biya su haraji, da kuɗin shiga da fita na kaya, da kuɗin fito. 21 Saboda haka sai ka umarci waɗannan mutane su daina gina birnin nan, sai lokacin da na ba da umarni. 22 Ka kula fa, kada ka yi kasala a wannan al'amari, don me ɓarna za ta bunƙasa har ta cuci sarki?” 23 Sa'ad da aka karanta wa Rehum, da Shamshai magatakarda, da abokansu, wasiƙar sarki Artashate, suka hanzarta suka tafi wurin Yahudawa a Urushalima, suka gwada musu iko, suka tilasta musu su daina ginin. 24 An tsai da aikin Haikalin Allah a Urushalima, sai a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus Sarkin Farisa.

Ezra 5

An Sāke Kama Aikin Gina Haikali

1 Haggai kuwa, da Zakariya ɗan Iddo, annabawa, suka yi wa Yahudawan da suke a Yahuza da Urushalima wa'azi da sunan Allah na Isra'ila wanda yake iko da su. 2 Sai Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, da Yeshuwa ɗan Yehozodak, suka tashi suka sāke kama aikin gina Haikalin Allah wanda yake a Urushalima. Annabawan Allah suna tare da su, suna taimakonsu. 3 A wannan lokaci kuma, sai Tatenai, mai mulkin lardin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu suka je wurinsu suka yi magana da su, suka ce, “Wa ya ba ku izini ku gina Haikalin nan, har ku gama wannan garu?” 4 Suka kuma tambaye su, “Ina sunayen waɗanda suke yin wannan gini?” 5 Amma ikon Allah yana kan dattawan Yahudawa, saboda haka ba su hana su yin ginin ba, sai sun kai wa Dariyus labari, sun sami amsa a rubuce tukuna. 6 Wannan ita ce wasiƙar da Tattenai mai mulkin lardin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu ma'aikatan hukuma waɗanda suke Yammacin Kogi, suka aika wa sarki Dariyus. 7 “Zuwa ga sarki Dariyus, salama gare ka. 8 Muna sanar da sarki, cewa mun tafi lardin Yahuza a wurin Haikalin Allah Mai Girma. Ana ginin Haikalin da manyan duwatsu, ana kuma sa katakai a bango. Aikin yana ci gaba sosai a hannunsu. 9 “Mun yi magana da dattawan, muka tambaye su wanene ya ba su izini su gina wannan Haikali har su gama bangonsa. 10 Mun kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta maka sunayen mutanen da suke shugabanninsu. 11 To, sai suka ce mana, ‘Mu bayin Allah ne wanda yake da sama da ƙasa, muna sāke gina Haikalin da wani babban sarki na Isra'ila ya gina tun shekaru da yawa da suka wuce. 12 Amma saboda kakanninmu suka tsokani Allah na Sama, sai ya bashe su a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, mutumin Kaldiya. Shi ne ya lalatar da Haikalin nan, ya kuma kwashe jama'a zuwa Babila. 13 Amma a shekara ta fari ta sarautar Sairus, Sarkin Babila, sai ya ba da izini a sāke gina wannan Haikali na Allah. 14 Kwanonin zinariya da na azurfa na Haikalin Allah, waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga cikin Haikalin da yake Urushalima, zuwa haikalin gumaka na Babila, sarki Sairus ya ɗauke su daga haikalin Babila ya ba wani mai suna Sheshbazzar wanda ya naɗa shi mai mulki. 15 Ya ce masa, ya ɗauki waɗannan kwanoni, ya tafi, ya sa su cikin Haikalin da yake a Urushalima, a sāke gina Haikalin Allah a wurin da yake a dā.’ 16 Sheshbazzar kuwa ya zo ya aza harsashin ginin Haikalin Allah wanda yake a Urushalima. Tun daga wannan lokaci, har yanzu ana ta gininsa, har yanzu kuma ba a gama ba. 17 Domin haka in ya gamshi sarki, sai a bincike ɗakin littattafan da yake Babila don a gani ko sarki Sairus ya ba da izini a sāke gina wanna Haikalin Allah a Urushalima. Bari sarki ya aiko mana da abin da ya gani a kan wannan al'amari.”

Ezra 6

A Gano Umarnin Sarki Sairus

1 Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincike ɗakin littattafai na Babila, inda aka ajiye takardun shaida. 2 Sai aka sami takarda a Ekbatana, babban lardin Mediya. A cikin takardar aka iske rubutu don tunawa. 3 “A shekara ta fari ta sarautar sarki Sairus, sai ya ba da izini a sāke gina Haikalin Allah da yake a Urushalima, wurin da za a miƙa sadaka da hadayu na ƙonawa. Sai a aza harsashi da ƙarfi. Tsayinsa zai zama kamu sittin, fāɗinsa kuwa kamu sittin. 4 Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako, a kuma biya kuɗin aikin daga baitulmalin sarki. 5 A kuma kawo kwanonin nan na zinariya da na azurfa cikin Haikalin Allah, waɗanda Nebukadnezzar ya kwaso daga cikin Haikali a Urushalima ya kawo Babila, a komar da su, a mayar da su a Haikali a Urushalima, a ajiye kowanne a wurinsa a Haikalin Allah.”

Sarki Dariyus ya Umarta a Ci gaba da Aiki

6 Sarki Dariyus ya ce, “Zuwa ga Tattenai, mai mulkin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu, wato ma'aikatan hukuma na lardin Yammacin Kogi, ku nisance su. 7 “Ku ƙyale aikin Haikalin nan na Allah kawai, ku ƙyale masu mulkin Yahudawa da dattawan Yahudawa, su sāke gina Haikalin Allah a wurin da yake a dā. 8 Ina umartarku ku biya wa dattawan Yahuza kuɗin sāke ginin Haikalin nan na Allah, a biya mutanen nan cikakken kuɗin aiki daga baitulmalin sarki, wanda yake a lardin Yammacin Kogi, ba tare da ɓata lokaci ba. 9 A ba su duk abin da suke bukata, wato kamar 'yan bijimai, da raguna, da 'yan tumaki domin yi wa Allah na Sama hadayun ƙonawa, da alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da man naɗawa yadda firistoci a Urushalima suke bukata, sai a ba su kowace rana banda fashi, 10 domin su miƙa wa Allah na Sama sadaka mai daɗin ƙanshi, su kuma yi addu'a saboda sarki da 'ya'yansa. 11 Na kuma umarta, cewa duk wanda ya karya wannan doka, sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa'an nan a mai da gidansa juji. 12 Allah wanda ya sa sunansa ya kasance a Urushalima, ya hamɓarar da kowane sarki, ko al'umma waɗanda za su sāke wannan doka don su lalatar da Haikalin Allah da yake a Urushalima. Ni Dariyus na kafa wannan doka. Lalle ne a kiyaye dokata sarai.”

An Ƙeɓe Haikalin

13 Saboda maganar sarki Dariyus, sai Tattenai mai mulkin lardin Yammacin Kogi, da Shetar-bozenai, da abokansu suka aikata abin da sarki Dariyus ya umarta da aniya. 14 Dattawan Yahuza suka yi nasarar ginin ta wurin wa'azin annabi Haggai da Zakariya ɗan Iddo. Suka gama ginin bisa ga umarnin Allah na Isra'ila, da umarnin Sairus, da Dariyus, da Artashate sarakunan Farisa. 15 An gama ginin Haikali a ran ashirin da uku ga watan Adar, a shekara ta shida ta sarautar sarki Dariyus. 16 Sai mutanen Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa, da sauran waɗanda suka komo daga bauta, suka yi bikin keɓe Haikalin Allah da murna. 17 A bikin keɓe Haikalin Allah, suka miƙa bijimai ɗari, da raguna ɗari biyu, da 'yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra'ila, bunsurai goma sha biyu, bisa ga yawan kabilan Isra'ila. 18 Sai suka karkasa firistoci da Lawiyawa ƙungiya domin yin aikin Ubangiji a Urushalima kamar yadda aka rubuta a Attaura ta Musa.

An yi Idin Ƙetarewa

19 A rana ta goma sha huɗu ga watan fari, sai waɗanda suka komo daga bauta suka kiyaye Idin Ƙetarewa. 20 Gama firistoci da Lawiyawa sun tsarkake kansu, suka kuwa tsarkaka, sai suka yanka ragon Idin Ƙetarewa saboda dukan waɗanda suka komo daga bauta, da kuma saboda 'yan'uwansu firistoci, da su kansu. 21 Mutanen Isra'ila waɗanda suka komo daga zaman talala suka ci tare da kowane mutumin da ya haɗa kai da su, ya kuma keɓe kansa daga ƙazantar al'umman ƙasar, domin ya bi Ubangiji Allah na Isra'ila. 22 Suka kuma kiyaye idin abinci marar yisti kwana bakwai da murna, gama Ubangiji ya sa su yi murna, ya kuma juyo da zuciyar Sarkin Assuriya wajensu, saboda haka ya taimake su da aikin Haikalin Allah, Allah na Isra'ila.

Ezra 7

Ezra da Ƙungiyarsa sun Iso Urushalima

1 Bayan wannan a zamanin Artashate Sarkin Farisa, sai Ezra ya gane da asalinsa, wato shi na ɗan Seraiya, da Azariya, da Hilkiya, 2 da Shallum, da Zadok, da Ahitub, 3 da Amariya, da Azariya, da Merayot, 4 da Zarahiya, da Uzzi, da Bukki, 5 da Abishuwa da Finehas, da Ele'azara, da Haruna babban firist. 6 Ezra ɗin ya taho daga Babila. Shi malami ne, masanin shari'ar Musa, wadda Ubangiji Allah na Isra'ila ya bayar. Sarki kuwa ya ba shi dukan abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi. 7 A shekara ta bakwai kuma ta sarautar sarki Artashate, waɗansu mutanen Isra'ila, da waɗansu firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da matsaran ƙofa, da ma'aikatan Haikali, suka taho Urushalima. 8 Ezra kuma tare da su, suka iso Urushalima a watan biyar na shekara ta bakwai ta sarautar sarkin. 9 Suka taso daga Babila a rana ta fari ga watan fari, suka iso Urushalima a rana ta fari ga watan biyar, Allah kuwa yana tare da su. 10 Gama Ezra ya ba da kansa ga yin nazarin dokokin Allah, ya kiyaye su, ya kuma koyar wa Isra'ilawa dokoki da farillan Allah.

Takardar da Sarki Artashate ya Ba Ezra

11 Wannan ita ce takardar doka da sarki Artashate ya ba Ezra, wanda yake firist da magatakarda, ƙwararre cikin sha'anin dokoki da umarnan Ubangiji a cikin Isra'ilawa. 12 Ta ce, “Daga Artashate, sarkin sarakuna, zuwa ga Ezra firist, masanin shari'ar Allah na Sama. 13 “Yanzu na yi doka, cewa kowane mutum daga cikin mutanen Isra'ila, da firistocinsu, da Lawiyawansu da suke cikin mulkina wanda yake so ya koma Urushalima, sai ya tafi tare da kai. 14 Gama sarki ne da 'yan majalisarsa guda bakwai suka aike ka don ka san irin zaman mutanen Yahuza da na Urushalima game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka, 15 domin kuma ka ba da azurfa da zinariya waɗanda sarki da 'yan majalisarsa suka ba Allah na Isra'ila da yardar ransu, wato Allah wanda Haikalinsa yake a Urushalima, 16 da kuma azurfa da zinariya da za ka samu a dukan lardin Babila tare da hadayu na yardar rai daga mutane da firistoci, hadayun da suka yi wa'adi su bayar da yardar ransu domin Haikalin Allahnsu, da yake a Urushalima. 17 “Da wannan kuɗi ne za ka himmatu, ka sayi bijimai, da raguna, da 'yan raguna, da hadayunsu na gari, da na sha. Za ka miƙa su a bisa bagaden Haikalin Allah da yake a Urushalima. 18 Duk abin da kai da 'yan'uwanka kuka ga ya dace ku yi, sai ku yi shi da sauran azurfa da zinariya bisa ga nufin Allahnku. 19 Kwanonin da aka ba ka domin hidima a Haikalin Allah, sai ka ajiye su a gaban Allah a Urushalima. 20 Dukan abin da ake bukata domin Haikalin Allah, abin nan kuwa ya kamata a yi shi, sai ka yi shi da kuɗin baitulmalin sarki. 21 “Ni, sarki Artashate, ina umartar kowane ma'aji na Yammacin Kogin Yufiretis, cewa duk abin da Ezra, firist, masanin dokokin Allah na Sama, zai bukata a gare ka, sai ka himmatu ka yi. 22 Sai ku ba shi abin da ya kai talanti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari ta ruwan inabi, mai kuma garwa ɗari. Gishiri kuwa a bayar da yawa, kada a iyakance. 23 Dukan abin da Allah na Sama ya umarta, sai a yi shi sosai domin Haikalin Allah na Sama, domin kada ya yi fushi da mulkin sarki da 'ya'yansa. 24 Muna kuma sanar da ku, cewa ba daidai ba ne ku karɓi haraji, da kuɗin shiga da fita, daga wurin firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da matsaran ƙofa, da masu lura da Haikali, da ma'aikatan wannan Haikali na Allah. 25 “Kai kuma, Ezra, bisa ga hikimar da Allahnka ya ba ka, sai ka naɗa mahukunta da alƙalai waɗanda za su yi wa mutanen da suke a lardin Yammacin Kogi shari'a, wato dukan waɗanda suka san shari'a. Waɗanda ba su san shari'a ba kuwa, sai ka koya musu. 26 Duk wanda bai yi biyayya da shari'ar Allahnka ba, ko shari'ar sarki, sai a yi masa hukunci mai tsanani, ko na mutuwa, ko na kora, ko na ƙwace dukiyarsa, ko na kurkuku.”

Ezra ya Yi Yabon Allah

27 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na kakanninmu, wanda ya sa a zuciyar sarki ya ƙawata Haikalin Ubangiji da yake a Urushalima. 28 Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a wurin sarki, da 'yan majalisarsa, da manyan ma'aikatansa. Na sami ƙarfin hali, gama Ubangiji Allahna yana tare da ni. Sai na tattara manyan mutane na Isra'ila don mu tafi tare.

Ezra 8

Waɗanda suka Komo daga Zaman Talala

1 Waɗannan su ne shugabannin gidajen kakanninsu. Wannan kuwa shi ne lissafin asalin waɗanda suka komo tare da ni daga Babila a zamanin sarautar sarki Artashate. 2-14 Gershom shi ne shugaban iyalin Finehas, Daniyel shi ne na iyalin Itamar, Hattush ɗan Shekaniya, shi ne na iyalin Dawuda. Zakariya shi ne na iyalin Farosh, ya zo da iyalinsa mutum ɗari da hamsin. Eliyehoyenai ɗan Zarahiya, shi ne na iyalin Fahat-mowab, tare da shi kuma akwai mutum ɗari biyu. Shekaniya ɗan Yahaziyel, shi ne na iyalin Zattu, tare da shi akwai mutum ɗari uku. Ebed ɗan Jonatan, shi ne na iyalin Adin, tare da shi akwai mutum hamsin. Yeshaya ɗan Ataliya, shi ne na iyalin Elam, yana tare da mutum saba'in. Zabadiya ɗan Maikel, shi ne na iyalin Shefatiya, yana tare da mutum tamanin. Obadiya ɗan Yehiyel, shi ne na iyalin Yowab, yana tare da mutum ɗari biyu da goma sha takwas. Shelomit ɗan Yosifiya, shi ne na iyalin Bani, yana tare da mutum ɗari da sittin. Zakariya ɗan Bebai, shi ne na iyalin Bebai, yana tare da mutum ashirin da takwas. Yohenan ɗan Hakkatan, shi ne na iyalin Azgad, yana tare da mutum ɗari da goma. Elifelet, da Yehiyel, da Shemaiya, su ne na iyalin Adonikam (su ne suka zo daga baya), suna tare da mutum sittin. Utai da Zabbud, su ne na iyalin Bigwai, suna tare da mutum saba'in.

Ezra ya Sami Lawiyawa domin Haikali

15 Na kuma tara mutanen a bakin rafin da yake gudu zuwa Ahawa. A nan muka yi zango kwana uku. Sa'ad da na duba jama'a, da firistoci, sai na tarar ba 'ya'yan Lawi. 16 Sai na sa a kirawo Eliyezer, da Ariyel, da Shemaiya, da Elnatan, da Yarib, da Elnatan, da Natan, da Zakariya, da Mehullam waɗanda suke shugabanni, a kuma kirawo Yoyarib da Elnatan masu hikima. 17 Na kuma aike su zuwa wurin Iddo, shugaba a Kasifiya. Na faɗa musu abin da za su faɗa wa Iddo a Kasifiya da 'yan'uwansa ma'aikatan Haikali, wato ya aiko mana waɗanda za su yi hidima a Haikalin Allahnmu. 18 Da yake Allah yana tare da mu, sai suka kawo mana mutum mai ganewa gada 'ya'yan Mali ɗan Lawi, ɗan Isra'ila. Sunan mutumin Sherebiya, da 'ya'yansa da 'yan'uwansa, su goma sha takwas ne. 19 Suka kuma kawo Hashabiya tare da Yeshaya daga 'ya'yan Merari. 'Yan'uwansa da 'ya'yansu su ashirin ne. 20 Da kuma ma'aikatan Haikali mutum ɗari biyu da ashirin, waɗanda Dawuda da ma'aikatansa suka keɓe domin su taimaki Lawiyawa. Aka ambaci waɗannan da sunayensu.

Ezra ya Bi da Jama'a da Azumi da Addu'a

21 Na kuma yi shelar azumi a bakin rafin Ahawa don mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu roƙe shi ya kiyaye mu, da 'ya'yanmu, da kayanmu a hanya. 22 Gama na ji kunya in roƙi sarki ya ba mu sojojin ƙasa da na doki su kāre mu daga maƙiya a hanya, da yake na riga na faɗa masa cewa, “Allah yana tare da dukan waɗanda suke nemansa, ikonsa da fushinsa mai zafi kuwa yana kan dukan waɗanda suke mantawa da shi.” 23 Don haka muka yi azumi, muka roƙi Allah saboda wannan, shi kuwa ya ji roƙonmu.

Kyautai domin Haikalin

24 Sai na keɓe goma sha biyu daga cikin manyan firistoci, wato Sherebiya, da Hashabiya, da waɗansu goma daga cikin danginsu. 25 Na auna musu azurfa, da zinariya, da kwanoni waɗanda sarki da fādawansa, da manyan mutanensa, da Isra'ilawa duka suka kawo suka miƙa domin Haikalin Allahnmu. 26-27 Ga abin da na auna na ba su, talanti ɗari shida da hamsin na azurfa kayan azurfa na talanti ɗari kayan zinariya na talanti ɗari kwanonin zinariya guda ashirin na darik dubu (1,000 ) kwanoni guda biyu na tatacciyar tagulla, darajarsu daidai da kwanon zinariya. 28 Na ce musu, “Ku tsarkaka ne ga Ubangiji, kayayyakin kuma tsarkaka ne, azurfa da zinariya sadaka ce ta yardar rai ga Ubangiji Allah na kakanninku. 29 Ku riƙe su, ku yi tsaronsu, har lokacin da za ku kai su a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin gidajen kakanninku na Isra'ila a Urushalima, a shirayin Haikalin Ubangiji.” 30 Sai firistoci da Lawiyawa suka ɗauki azurfa, da zinariya, da kwanoni waɗanda aka auna, zuwa Urushalima, zuwa Haikalin Allahnmu.

Komowar Urushalima

31 Muka kuwa tashi daga kogin Ahawa a ran goma sha biyu ga watan ɗaya, don mu tafi Urushalima, Allahnmu kuma yana tare da mu, ya kuwa cece mu daga hannun maƙiyanmu, da mafasa a hanya. 32 Muka iso Urushalima, muka yi kwana uku. 33 A rana ta huɗu, a Haikalin Allah, sai aka ba da azurfa, da zinariya, da kwanoni ga Meremot ɗan Uriya, firist, da Ele'azara ɗan Finehas, da Lawiyawa, wato Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi. 34 Aka ƙidaya dukan kome aka kuma auna, sa'an nan aka rubuta yawan nauyin. 35 Waɗanda fa suka komo daga zaman talala, suka miƙa wa Allah na Isra'ila hadaya ta ƙonawa, da bijimai goma sha biyu domin dukan Isra'ila, da raguna tasa'in da shida, da 'yan raguna saba'in da bakwai. Suka kuma miƙa hadaya don zunubi da bunsurai goma sha biyu. Dukan wannan ya zama hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. 36 Suka faɗa wa wakilan sarki da masu mulkin Yammacin Kogin Yufiretis umarnan sarki. Su kuwa suka taimaki mutane, da kuma Haikalin Allah.

Ezra 9

Addu'ar Ezra da Faɗar Laifi

1 Bayan da aka gama waɗannan abubuwa, sai shugabanni suka zo wurina, suka ce, “Mutanen Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa ba su keɓe kansu daga ƙazantar mutanen ƙasar ba, wato su Kan'aniyawa, da Hittiyawa, da Ferizziyawa, da Yebusiyawa, da Ammonawa, da Mowabawa, da Masarawa, da Amoriyawa. 2 Gama sun auro wa kansu da 'ya'yansu 'yan matan mutanen nan. Yanzu tsattsarkar zuriya ta cuɗanya da mutanen ƙasashe. Shugabanni da magabata sun fi kowa laifi kan wannan rashin gaskiya.” 3 Sa'ad da na ji wannan, sai na yayyage rigata da alkyabbata, na tsittsiga gashin kaina da na gemuna, na zauna a ruɗe. 4 Sa'an nan dukan waɗanda suka yi rawar jiki saboda maganar Allah na Isra'ila, saboda rashin aminci na waɗanda suka komo daga zaman talala, suka taru, suka kewaye ni sa'ad da nake zaune a ruɗe, har lokacin yin sadakar yamma. 5 A lokacin sadakar yamma ɗin, sai na tashi daga yin azumi, da rigata da alkyabbata yagaggu. Na rusuna a gwiwoyina, na ɗaga hannuwana zuwa ga Ubangiji Allahna. 6 Na ce, “Ya Allahna, kunya ta rufe fuskata, ban iya in ko ɗaga idanuna wajenka ba, gama muguntarmu ta sha kanmu, tsibin zunubanmu kuma ya kai har sammai. 7 Tun daga zamanin kakanninmu muna da babban laifi. Saboda zunubanmu, mu da sarakunanmu, da firistocinmu, aka bashe mu a hannun sarakunan waɗansu ƙasashe, aka bashe mu ga takobi, aka kai mu bauta, aka washe mu, aka kunyatar da mu kamar yadda yake a yau. 8 Amma a yanzu a wannan ɗan lokaci Ubangiji Allahnmu ya yi mana alheri da ya bar mana ringi, ya kuma ba mu wuri a wurinsa mai tsarki, inda za mu zauna lafiya domin Allahnmu ya waye mana ido, ya kuma ba mu 'yar wartsakewa daga bautarmu. 9 Gama mu bayi ne, duk da haka Allahnmu bai manta da mu a bautarmu ba, amma ya sa muka sami tagomashi a wurin sarakunan Farisa, suka iza mu domin mu gina Haikalin Allahnmu, mu sāke gyaransa, mu kuma gina garu a Yahuza da Urushalima. 10 “Yanzu, me za mu ce bayan wannan, ya Allahnmu, gama mun manta da umarnanka. 11 Umarnan da ka umarta ta bakin bayinka annabawa cewa, ‘Ƙasar da kuke shiga don ku mallake ta, ta ƙazantu da ƙazantar al'umman da suke cikinta. Ƙazantarsu ta cika dukan ƙasar. 12 Domin haka kada ku aurar musu da 'ya'yanku mata, kada kuma ku auro wa 'ya'yanku 'yan matansu, kada kuma ku nemi zaman arziki da su. Idan kun yi biyayya za ku yi ƙarfi, ku ci albarkar ƙasar, har ku bar ta gādo ga 'ya'yanku har abada.’ 13 Bayan wannan dukan abubuwan nan suka same mu saboda mugayen ayyukanmu da zunubanmu masu yawa. Ya Allahnmu, ga shi ma, ka hukunta mu kaɗan bisa ga yawan zunubanmu, ka kuma bar mana wannan ringi. 14 Za mu sake ƙetare umarninka, mu yi aurayya da mutanen da suke yin waɗannan ƙazanta? Ba za ka yi fushi da mu, ka ƙone mu da fushinka har babu ringi ba? 15 Ya Ubangiji Allah na Isra'ila, kai mai adalci ne, gama ka bar mana ringin da ya tsira kamar yadda yake a yau. Ga mu nan gabanka da zunubinmu, gama ba wanda zai iya tsayawa a gabanka saboda wannan.”

Ezra 10

An Shirya yadda za a Rabu da Aurayya da Arna

1 Sa'ad da Ezra yake yin addu'a, yana hurta laifi, yana kuka, yana a durƙushe gaban Haikalin Allah, sai babban taron jama'a, mata, da maza, da yara daga Isra'ila suka taru wurinsa. Mutane suka yi kuka mai zafi. 2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam, ya yi wa Ezra magana, ya ce, “Mun yi wa Allahnmu rashin aminci, gama mun auri mata baƙi daga mutanen ƙasar, amma duk da haka akwai sauran bege ga Isra'ila. 3 Bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori dukan waɗannan mata da 'ya'yansu, bisa ga shawarar shugabanni da waɗanda suke rawar jiki saboda umarnin Allah. Bari mu yi alkawari bisa ga doka. 4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, mu kuwa muna tare da kai. Sai dai ka yi ƙarfin hali, ka yi shi.” 5 Ezra kuwa ya tashi, ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra'ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar. 6 Sa'an nan Ezra ya tashi daga Haikalin Allah, ya tafi gidan Yohenan ɗan Eliyashib, amma ko da ya tafi can bai ci abinci ba, bai kuma sha ruwa ba, gama yana baƙin ciki saboda rashin aminci na waɗanda suka dawo daga zaman talala. 7 Sai aka yi shela a dukan Yahuza da Urushalima, cewa dukan waɗanda suka komo daga zaman talala, su hallara a Urushalima. 8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama'ar da suka dawo daga zaman talala. Haka shugabanni da dattawa suka umarta. 9 Sai dukan mutanen Yahuza da na Biliyaminu, suka hallara a Urushalima kafin kwana uku, a ran ashirin ga watan tara. Mutanen suka zauna a dandalin Haikali, suna rawar jiki saboda al'amarin, da kuma saboda babban ruwan sama. 10 Ezra firist kuwa ya miƙe tsaye ya ce wa jama'a, “Kun yi rashin aminci, kun auri mata baƙi, ta haka kuka ƙara zunubin Isra'ila. 11 Yanzu sai ku hurta wa Ubangiji Allah na kakanninku, laifinku, ku kuma aikata nufinsa. Ku ware kanku daga mutanen ƙasar da mata baƙi.” 12 Dukan taron jama'a suka amsa da babbar murya, suka ce, “Hakanan ne, hakanan ne, dole ne mu yi yadda ka faɗa. 13 Amma mutane suna da yawa, a lokacin kuwa ana marka, ba za mu iya tsayawa a fili ba, aikin nan kuma ba na kwana ɗaya, ko biyu ba ne, gama mun yi laifi sosai wajen wannan al'amari. 14 Bari shugabanninmu su wakilci dukan taron jama'a, bari kuma dukan waɗanda suke garuruwanmu da suka auri mata baƙi su zo a ƙayyadadden lokaci tare da dattawa da alƙalan garuruwansu, har lokacin da Allah ya huce daga fushinsa a kanmu saboda al'amarin nan.” 15 Jonatan ɗan Asahel da Yazeya ɗan Tikwa ne kaɗai ba su yarda da wannan ba, Meshullam da Shabbetai suka goyi bayansu. 16 Waɗanda suka komo daga zaman talala kuwa suka yi haka. Sai Ezra firist ya zaɓi mutanen da suke shugabannin gidajen kakanninsu. Aka rubuta sunan kowa. Sai suka taru ran ɗaya ga watan goma, don su bincika al'amarin. 17 Suka gama binciken dukan mutanen da suka auri mata baƙi ran ɗaya ga watan fari.

Mazajen da suke da Mata Baƙi

18 Ma'aseya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya iyalin Yeshuwa ɗan Yehozadak, su ne firistocin da suka auri mata baƙi. 19 Sai suka yi alkawari, cewa za su saki matansu. Suka ba da rago don yin hadaya saboda laifinsu. 20-24 Na iyalin Immer, Hanani, da Zabadiya Na iyalin Harim, Ma'aseya, da Iliya, da Shemaiya, da Yehiyel, da Uzziya Na iyalin Fashur, Eliyehoyenai, da Ma'aseya, da Isma'ilu, da Netanel, da Yozabad, da Elasa Na Lawiyawa, Yozabad, da Shimai, da Kelaya, wato Kelita, da Fetahiya, da Yahuza, da Eliyezer Na mawaƙa, Eliyashib Na masu tsaron ƙofa, Shallum, da Telem, da Uri 25-33 Akwai kuma waɗansu na Isra'ila. Na iyalin Farosh, Ramiya, da Izziya, da Malkiya, da Miyamin, da Ele'azara, da Malkiya, da Benaiya Na iyalin Elam, Mattaniya, da Zakariya, da Yehiyel, da Abdi, da Yeremot, da Iliya Na iyalin Zattu, Eliyehoyenai, da Eliyashib, da Mattaniya, da Yeremot, da Zabad, da Aziza Na iyalin Bebai, Yehohanan, da Hananiya, da Zabbai, da Atlai Na iyalin Bani, Meshullam, da Malluki, da Adaya, da Yashub, da Sheyal, da Yeremot Na iyalin Fahat-mowab, Adana, da Kelal, da Benaiya, da Ma'aseya, da Mattaniya, da Bezalel, da Binnuyi, da Manassa Na iyalin Harim, Eliyezer, da Isshiya, da Malkiya, da Shemaiya, da Shimeyon, da Biliyaminu, da Malluki, da Shemariya Na iyalin Hashum, Mattenai, da Mattatta, da Zabad, da Elifelet, da Yeremai, da Manassa, da Shimai 34-37 Na iyalin Bani, Mayadi, da Amram, da Yuwel, da Benaiya, da Bedeya, da Keluhi, da Waniya, da Meremot, da Eliyashib, da Mattaniya, da Mattenai, da Yawasu 38-42 Na iyalin Binnuyi, Shimai, da Shelemiya, da Natan, da Adaya, da Maknadebai, da Shashai, Sharai, da Azarel, da Shelemiya, da Shemariya, da Shallum, da Amariya, da Yusufu 43 Na iyalin Nebo, Yehiyel, da Mattitiya, da Zabad, da Zebina, da Yaddai, da Yowel, da Benaiya. 44 Waɗannan duk sun auro mata baƙi. Sai suka sake su da 'ya'yansu.

Nehemiya 1

Addu'ar Nehemiya domin Urushalima

1 Labarin Nehemiya ɗan Hakaliya ke nan. Ya zama fa a watan Kisle a shekara ta ashirin, sa'ad da ni Nehemiya nake a fādar Shushan, wato alkarya, 2 sai Hanani, ɗaya daga cikin 'yan'uwana, ya zo tare da waɗansu mutanen Yahuza. Na kuwa tambaye shi labarin Yahudawan da suka tsira, suka koma daga zaman talala, da labarin Urushalima. 3 Sai suka ce mini, “Waɗanda suka tsira, suka koma daga zaman talala, da suke can lardin, suna cikin wahala ƙwarai, suna kuma shan kunya. Garun Urushalima kuma ya rushe, ƙofofi sun ƙone.” 4 Da na ji wannan labari, sai na zauna, na yi kuka. Na yi kwanaki ina baƙin ciki, na yi ta azumi da addu'a a gaban Allah na Sama. 5 Na ce, “Ya Ubangiji Allah na Sama, Allah mai girma, mai banrazana, mai cika alkawari, mai nuna madawwamiyar ƙauna ga waɗanda suke ƙaunarka, wato masu kiyaye umarnanka, 6 ina roƙonka ka kasa kunne, ka kuma buɗe idanunka, ka ji addu'ar bawanka, wadda nake yi a gabanka dare da rana saboda bayinka, mutanen Isra'ila. Ina hurta zunubanmu, mu mutanen Isra'ila, da muka yi maka. Ni da gidan ubana mun yi zunubi. 7 Mun kangare maka, ba mu kiyaye umarnai, da dokoki, da ka'idodi waɗanda ka ba bawanka Musa ba. 8 Ka tuna da maganar da ka umarci bawanka Musa cewa, ‘Idan kun yi rashin aminci, zan warwatsa ku cikin al'ummai. 9 Amma idan kun juyo wurina, kun kiyaye umarnaina, kun aikata su, ko da yake an warsatsar da ku can nesa, zan tattaro ku, in kawo ku wurin da na zaɓa domin in sa sunana ya kahu a wurin.’ 10 “Su bayinka ne, mutanenka ne kuma, waɗanda ka fansa da ikonka. 11 Ya Ubangiji, ka kasa kunne ga addu'ar bawanka, da addu'o'in bayinka, waɗanda suke jin daɗin girmama sunanka. Ka ba bawanka nasara yau ka sa ya sami tagomashi a gaban mutumin nan.”

Nehemiya 2

An Aika da Nehemiya ya Tafi Urushalima

1 Ni kuwa ina riƙe da finjalin sarki. Wata rana a watan Nisan, a shekara ta ashirin ta sarautar sarki Artashate, sa'ad da na kai masa ruwan inabi, sai na ɗauki ruwan inabin, na ba shi. Ni ban taɓa ɓata fuskata a gabansa a dā ba, sai wannan karo. 2 Sai sarki ya tambaye ni, ya ce, “Me ya sa fuskarka ta ɓaci, ga shi, ba ciwo kake yi ba. Ba abin da ya kawo wannan, sai lalle kana baƙin ciki.” Sai na tsorata ƙwarai, 3 na ce wa sarki, “Ranka ya daɗe, me zai hana fuskata ta ɓaci, da yake birni inda makabartar kakannina take ya zama kango, an kuma ƙone ƙofofinsa da wuta?” 4 Sa'an nan sarki ya ce mini, “To, me kake so?” Sai na yi addu'a ga Allah na Sama, 5 sa'an nan na ce wa sarki, “Idan ka yarda, idan kuma na sami tagomashi a wurinka, ya sarki, ka yardar mini in tafi Yahuza, birnin kakannina, inda makabartarsu take domin in sāke gina shi.” 6 Sarki kuwa, a sa'an nan sarauniya tana zaune kusa da shi, ya ce mini, “Kwana nawa za ka yi, yaushe kuma za ka dawo?” Sai na faɗa masa, ya kuwa yardar mini in tafi, ni kuwa na yanka masa kwanakin da zan yi. 7 Sa'an nan na ce wa sarki, “Idan sarki ya yarda, sai a ba ni takarda zuwa ga masu mulki da suke a lardin Yammacin Kogin Yufiretis domin su yardar mini in wuce zuwa Yahuza. 8 A kuma ba ni takarda zuwa ga Asaf, sarkin daji, domin ya ba ni katakan da zan yi jigajigan ƙofofin kagarar Haikali, da na garun birnin, da na gidan da zan zauna.” Sarki kuwa ya ba ni abin da na roƙa, gama Allah yana tare da ni. 9 Da na zo wurin masu mulkin Yammacin Kogin Yufiretis, sai na miƙa musu takardar sarki. Sarki ya haɗa ni da sarkin yaƙi da mahayan dawakai. 10 Amma Sanballat Bahorone, da Tobiya, Ba'ammone, bawa, ba su ji daɗi ba ko kaɗan sa'ad da suka ji labari, cewa wani ya zo domin ya inganta zaman lafiyar mutanen Isra'ila.

Nehemiya ya Ƙarfafa Maginan Garu

11 Da na iso Urushalima na yi kwana uku, 12 sai na fita da dare tare da waɗansu mutane kima, ban faɗa wa kowa abin da Allahna ya sa a zuciyata in yi wa Urushalima ba. Ba waɗansu dabbobi kuma tare da ni, sai dai dabbar da na hau. 13 Da na fita, sai na bi ta Ƙofar Kwari zuwa Rijiyar Dila da Ƙofar Juji, na dudduba garun Urushalima, wanda aka rushe, da ƙofofinsa da wuta ta cinye. 14 Na yi gaba zuwa Ƙofar Maɓuɓɓuga da Tafkin Sarki, amma dabbar da na hau ba ta sami wurin wucewa ba. 15 Haka kuwa na fita da dare ta hanyar kwari na dudduba garun, sa'an nan na koma ta Ƙofar Kwari. 16 Shugabanni ba su san inda na tafi, ko abin da na yi ba, gama ban riga na faɗa wa Yahudawa, da firistoci, da manyan gari, da shugabanni, da sauran waɗanda za su yi aikin ba. 17 Sa'an nan na ce musu, “Kun ga irin wahalar da muke ciki, yadda Urushalima ta zama kango, an kuma ƙone ƙofofinta. Ku zo, mu sāke gina garun Urushalima don mu fita kunya.” 18 Na kuma faɗa musu yadda Allah yana tare da ni, ya kuma taimake ni, da maganar da sarki ya faɗa mini. Sai suka ce, “Mu tashi, mu kama gini.” Suka himmatu su yi wannan aiki nagari. 19 Amma sa'ad da Sanballat Bahorone, da Tobiya Ba'ammone, bawa, da Geshem Balarabe, suka ji labari, sai suka yi mana ba'a, suka raina mu, suka ce, “Me kuke yi? Kuna yi wa sarki tayarwa ne?” 20 Ni kuwa sai na amsa musu, na ce, “Allah na Sama zai ba mu nasara, saboda haka mu mutanensa za mu tashe, mu kama gini, amma ba ruwanku, ba hakkinku, ba ku da wani abin tunawa a Urushalima.”

Nehemiya 3

An Raba wa Mutane Wuraren da za su Gina

1 Eliyashib, babban firist kuwa, tare da 'yan'uwansa firistoci, suka tashi suka gina Ƙofar Tumaki. Suka tsarkake ta, suka sa mata ƙyamarenta. Suka tsarkake garun zuwa Hasumiyar Ɗari da Hasumiyar Hananel. 2 Mutanen Yariko suka kama gini kusa da shi. Sai kuma Zakkur ɗan Imri ya kama gini kusa da na mutanen Yariko. 3 Iyalin Hassenaya suka gina Ƙofar Kifi, suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. 4 Kusa da su kuma, sai Meremot ɗan Uriya, wato j�kan Hakkoz ya yi gyare-gyare. Kusa da shi kuma sai Meshullam ɗan Berikiya jikan Meshezabel ya yi gyare-gyare. Kusa da shi kuma sai Zadok ɗan Ba'ana ya yi gyare-gyare. 5 Kusa da Zadok kuwa mutanen Tekowa suka yi nasu gyare-gyare, amma manyansu ba su sa hannu ga aikin shugabanninsu ba. 6 Yoyada ɗan Faseya, da Meshullam ɗan Besodeya, suka gyara Tsohuwar Ƙofa, suka kafa katakanta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. 7 Kusa da su kuma sai Melatiya Bagibeyone, da Yadon Bameronote, da mutanen Gibeyon, da na Mizfa waɗanda suke a ƙarƙashin mulkin Yammacin Kogin Yufiretis suka yi gyare-gyare. 8 Kusa da su kuma sai Uzziyel ɗan Harhaya, maƙerin zinariya, ya yi gyare-gyare. Kusa da Uzziyel kuma sai Hananiya, ɗaya daga cikin masu yin turare, ya yi gyare-gyare. Suka gyare Urushalima har zuwa Garu Mai Faɗi. 9 Kusa da su kuma sai Refaya ɗan Hur, mai mulkin rabin yankin Urushalima, ya yi gyare-gyare. 10 Kusa da Refaya kuma, sai Yedaiya ɗan Harumaf ya yi gyare-gyare daura da gidansa. Kusa da Yedaiya sai Hattush ɗan Hashabnaiya ya yi gyare-gyare. 11 Malkiya ɗan Harim, da Hasshub ɗan Fahat-mowab suka gyara wani sashi da kuma Hasumiyar Tanderu. 12 Kusa da su kuma, sai Shallum ɗan Hallohesh mai mulkin rabin yankin Urushalima ya yi gyare-gyare tare da 'ya'yansa mata. 13 Hanun da mazaunan Zanowa suka gyara Ƙofar Kwari. Sun gina ta, suka sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta, da ƙyamarenta, suka gyara garun kamu dubu, har zuwa Ƙofar Juji. 14 Malkiya ɗan Rekab, mai mulkin yankin Bet-akkerem, ya gyara Ƙofar Juji. Ya gina ta, ya sa ƙyamarenta da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. 15 Sai Shallum ɗan Kolhoze, mai mulkin yankin Mizfa ya gyara Ƙofar Maɓuɓɓuga, ya gina ta, ya rufe ta, ya sa ƙyamarenta, da sandunan ƙarfe na kulle ƙofofinta. Ya kuma gina garun Tafkin Siluwam na gonar sarki, har zuwa matakan da suka gangaro daga Birnin Dawuda. 16 Bayansa kuma Nehemiya, ɗan Azbuk, mai mulkin yankin Bet-zur ya yi gyare-gyare, har zuwa wani wuri daura da kabarin Dawuda, har zuwa haƙaƙƙen tafki da gidan masu tsaro.

Lawiyawan da suka Yi Aikin Garu

17 Waɗannan Lawiyawa sun yi gyare-gyare a ƙarƙashin shugabancin Rehum ɗan Bani. Kusa da su kuma, sai Hashabiya mai mulkin rabin yankin Kaila, ya yi gyare-gyare domin yankinsa. 18 Bayansa kuma, sai 'yan'uwansu suka yi gyare-gyare a ƙarƙashin shugabancin Bawwai ɗan Henadad, mai mulkin rabin yankin Kaila. 19 Kusa da su kuma sai Ezer ɗan Yeshuwa, mai mulkin Mizfa, ya gyara wani sashi a gaban gidan makamai a wajen kusurwa. 20 Bayansa kuma, Baruk ɗan Zabbai, ya gyara wani sashi daga wajen kusurwar, har ya zuwa ƙofar gidan Eliyashib babban firist. 21 Bayansa kuma Meremot ɗan Uriya, ɗan Hakkoz, ya gyara wani sashi daga ƙofar gidan Eliyashib, zuwa ƙarshen gidan.

Firistocin da suka yi Aikin Garu

22 Bayansa kuma sai firistoci, mutanen filin kwari, suka yi gyare-gyare. 23 Bayansu kuma Biliyaminu da Hasshub suka yi gyara daura da gidansu. Bayansu kuma Azariya, ɗan Ma'aseya, wato jikan Ananiya, ya yi gyara kusa da gidansa. 24 Bayansa kuma Binnuyi, ɗan Henadad, ya gyara wani sashi daga gidan Azariya zuwa kusurwar garun. 25 Falal ɗan Uzai, ya gyara wani sashi daga kusurwar da hasumiyar benen gidan sarki a wajen shirayin matsara. Bayansa kuma sai Fedaiya ɗan Farosh ya yi gyare-gyare. 26 Ma'aikatan Haikali da suke zaune a Ofel suka yi gyare-gyare zuwa wani wuri daura da Ƙofar Ruwa wajen gabas, har zuwa wata doguwar hasumiya.

Sauran Masu Gini

27 Bayansu kuma mutanen Tekowa suka gyara wani sashi daura da babbar doguwar hasumiya, har zuwa garun Ofel. 28 Daga Ƙofar Dawaki, firistoci suka yi gyare-gyare, kowa ya yi gyara daura da gidansa. 29 Bayansu kuma Zadok, ɗan Immer, ya gyara wani sashi daura da gidansa. Bayansa kuma Shemaiya, ɗan Shekaniya, mai tsaron Ƙofar Gabas ya yi gyare-gyare. 30 Bayansa kuma Hananiya ɗan Shelemiya, da Hanun, ɗa na shida na Zalaf, suka gyara wani sashi, kashi na biyu. Bayansu kuma Meshullam, ɗan Berikiya, ya gyara wani sashi daura da gidansa. 31 Bayansa kuma, Malkiya, ɗaya daga cikin maƙeran zinariya ya yi gyare-gyare, har zuwa gidan ma'aikatan Haikali da na 'yan kasuwa, daura da Ƙofar Taruwa, har zuwa soron bene a wajen kusurwa. 32 Maƙeran zinariya da 'yan kasuwa suka gyara wani sashi tsakanin soron bene daga kusurwa da Ƙofar Tumaki.

Nehemiya 4

Ma'aikata sun Tsare Kansu

1 Sa'ad da Sanballat ya ji muna ginin garun, sai ya husata ƙwarai, ya yi wa Yahudawa ba'a. 2 Ya yi magana a gaban 'yan'uwansa da sojojin Samariya ya ce, “Menene waɗannan Yahudawa kumamai suke yi? Za su mai da abubuwa yadda suka a dā ne? Za su miƙa hadayu ne? Za su gama ginin a rana ɗaya ne? Za su iya samun duwatsun gini daga tsibin matattun duwatsu?” 3 Tobiya Ba'ammone yana kusa da shi, ya ce, “Ai, garun da suke ginawa da duwatsu, ko dila ya hau, sai ya rushe shi!” 4 Sai ni, Nehemiya, na yi addu'a, na ce, “Ka ji, ya Allahnmu, gama ana raina mu, ka sa ba'arsu ta koma kansu, ka sa a washe su a kai su ƙasar bauta. 5 Kada ka shafe laifinsu, kada kuwa ka gafarta musu, gama sun ci mutuncinmu, mu da muke gini.” 6 Muka gina garun, har ya kai rabin tsayinta, domin mutane sun himmatu da aikin. 7 Amma sa'ad da Sanballat, da Tobiya, da Larabawa, da Ammonawa, da mutanen Ashdod, suka ji yadda ginin garun Urushalima yake ci gaba, ana kuma tattoshe tsattsaguwa, sai suka husata. 8 Dukansu suka ƙulla za su zo, su yi yaƙi da Urushalima, su ta da hankali a cikinta. 9 Sai muka yi addu'a ga Allahnmu, muka sa masu tsaro su yi mana tsaro dare da rana saboda su. 10 Mutanen Yahuza kuwa suka ce, “Ƙarfin ma'aikata yana kāsawa, Akwai komatsai da yawa da za a kwashe, Yaya za mu iya gina garun yau?” 11 Abokan gābanmu kuma suka ce, “Ba za su sani ba, ba kuwa za su gan mu ba, sai dai kawai su gan mu a cikinsu, za mu karkashe su, mu tsai da aikin.” 12 Da Yahudawan da suke zaune kusa da su suka zo, suka yi ta nanata mana irin shirin abokan gabanmu, wato za su zo su fāɗa mana. 13 Saboda haka na sa jama'a su ja ɗamara bisa ga iyalinsu a bayan garu, a wuraren da ba a gina ba. Suna riƙe da takuba, da māsu, da bakuna. 14 Da na ga mutane sun damu, sai na tashi na yi magana da shugabanni, da sauran jama'a, na ce, “Kada ku ji tsoro, ku tuna da Ubangiji mai iko, mai banrazana, ku yi yaƙi domin 'yan'uwanku, da 'ya'yanku mata da maza, da matanku, da gidajenku.” 15 Da abokan gābanmu suka ji mun san shirinsu, Ubangiji kuwa ya wargaje shirinsu, sai dukanmu muka koma wurin garun, kowa ya kama aikinsa. 16 Daga wannan rana, sai rabin barorina suka yi ta gini, rabi kuwa suna riƙe da māsu, da garkuwoyi, da bakuna, da sulke. Shugabannin kuwa suka goyi bayan dukan Yahudawa sosai. 17 Masu ginin garun da masu ɗaukan kaya suna yi da hannu ɗaya, hannu ɗaya kuma na riƙe da makami. 18 Kowane magini yana rataye da takobinsa sa'ad da yake gini. Mai busa ƙaho yana kusa da ni. 19 Sai na ce wa manya da shugabanni, da sauran jama'a, “Aikin nan babba ne, mai yawa kuma, ga shikuwa, muna rarrabe a kan garun nesa da juna. 20 Duk inda kuka ji an busa ƙaho, sai ku taru a wurin. Allahnmu zai yi yaƙi dominmu.” 21 Haka kuwa muka yi aikin, rabinmu na riƙe da māsu tun daga wayewar gari har zuwa fitowar taurari. 22 A wannan lokaci kuma na ce wa jama'a, kowane mutum tare da baransa ya kwana a Urushalima domin a yi tsaro da dare, da safe kuma a kama aiki. 23 Saboda haka ni, da 'yan'uwana, da barorina, da matsaran da suke tare da ni, ba wanda ya tuɓe tufafinsa. Kowa yana riƙe da makami.

Nehemiya 5

An Hana Ba da Kuɗi da Ruwa

1 Sai mata da maza suka yi ta kuka ƙwarai saboda 'yan'uwansu Yahudawa. 2 Akwai waɗanda suka ce, “Mu da 'ya'yanmu mata da maza muna da yawa, sai mu sami hatsi don mu ci mu rayu.” 3 Waɗansu kuma suka ce, “Saboda yunwa mun jinginar da gonakinmu, da gonakin inabinmu, da gidajenmu don mu sami hatsi.” 4 Akwai waɗansu kuma da suka ce, “Mun ci bashin kuɗi don mu biya haraji a kan gonakinmu, da gonakin inabinmu. 5 Ga shi kuwa, mu da su dangin juna ne, 'ya'yanmu da nasu kuma ɗaya ne, duka da haka muna tilasta wa 'ya'yanmu mata da maza su zama bayi. Har ma waɗansu daga cikin 'ya'yanmu mata an riga an bautar da su, amma ba mu da iko mu ce kome, domin gonakinmu da gonakin inabinmu suna a hannun waɗansu mutane.” 6 Ni Nehemiya na husata ƙwarai, sa'ad da na ji kukansu da wannan magana. 7 Sai na yi shawara a zuciyata, na yi wa manya da shugabanni faɗa, na ce musu, “Kuna musguna wa 'yan'uwanku da yake kuna ba su rance da ruwa.” Sa'an nan na kira babban taro saboda su. 8 Na ce musu, “Da iyakacin ƙoƙarinmu mun fanshi 'yan'uwanmu Yahudawa waɗanda aka sayar wa al'ummai, amma ga shi, kuna tilasta wa 'yan'uwanku su sayar da kansu ga 'yan'uwansu.” Sai suka yi tsit, suka rasa abin da za su ce. 9 Na kuma ce musu, “Abin da kuke yi ba shi da kyau. Ya kamata ku yi tsoron Allah don ku hana al'ummai, abokan gabanmu, yi mana ba'a. 10 Ni ma da 'yan'uwana da barorina muna ba da rancen kuɗi da hatsi. Sai mu daina sha'anin ba da rance da ruwa. 11 Yau sai ku mayar musu da gonakinsu, da gonakin inabinsu, da na zaitunsu, da gidajensu, da kashi ɗaya bisa ɗari na kuɗi, da na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, waɗanda kuka karɓa a wurinsu.” 12 Sa'an nan suka ce, “Za mu mayar musu da waɗannan abubuwa, ba kuwa za mu bukaci wani abu a gare su ba. Za mu yi abin da ka faɗa.” Sai na kira firistoci su rantsar da su, cewa za su yi yadda suka alkawarta. 13 Sai kuma na kakkaɓe hannuna, na ce, “Duk wanda ya karya wannan alkawari, haka Allah zai kakkaɓe shi daga gidansa da aikinsa. Allah zai kakkaɓe shi, ya wofintar da shi.” Sai dukan taron suka amsa, “Amin, amin.” Suka kuma yabi Ubangiji. Suka kuwa cika alkawarin da suka yi.

Rashin Sonkan Nehemiya

14 Tun kuma lokacin da na yi mulkin ƙasar Yahuza, a shekara ta ashirin zuwa shekara ta talatin da biyu ta sarautar sarki Artashate, shekara goma sha biyu ke nan, ni ko 'yan'uwana, ba wanda ya karɓi albashin da akan ba mai mulki. 15 Waɗanda suka riga ni mulki sun nawaita wa mutane. Sun yi ta karɓar abinci da ruwan inabi daga gare su, banda shekel arba'in kowace rana domin abinci da ruwan inabi. Har ma barorin masu mulki sun nawaya wa mutane. Amma ni ban yi haka ba, saboda ina tsoron Allah. 16 Na mai da hankali ga aikin garu, ban samar wa kaina gonaki ba. Barorina duka suka haɗa kai da ni a kan aikin gini. 17 Duk da haka akwai Yahudawa da shugabanni ɗari da hamsin waɗanda suke cin abinci a teburina, banda waɗanda sukan zo wurinmu daga al'umman da suke kewaye da mu. 18 Ga abincin da ake shiryawa kowace rana, sa ɗaya, da tumaki shida kyawawa, da kuma kaji. A kowace rana ta goma akan kawo salkunan ruwan inabi masu yawa, amma duk da haka ban karɓi albashin da akan ba mai mulki ba, domin wahala ta yi wa mutane yawa. 19 Ya Allahna, ka tuna da alherin da na yi wa mutanen nan.

Nehemiya 6

Sharrin 'Yan Hammayya

1 Sa'ad da fa aka sanar da Sanballat, da Tobiya, da Geshem Balarabe, da sauran abokan gābanmu, cewa na gina garun, har ba sauran tsaguwa da ta ragu, ko da yake a lokacin ban riga na sa wa ƙofofi ƙyamare ba, 2 sai Sanballat da Geshem suka aika wurina cewa, “Ka zo mu sadu a wani ƙauye a filin Ono,” amma da nufin su cuce ni. 3 Sai na aika musu da manzanni, na ce, “Ina fama da babban aiki, ba ni da damar zuwa wurinku. Don me zan bar aiki in gangaro zuwa wurinku?” 4 Suka yi ta aiko mini da wannan saƙo har sau huɗu, ni kuwa na yi ta ba su amsa irin ta dā. 5 A karo na biyar sai Sanballat ya aiko da buɗaɗɗiyar wasiƙa ta hannun baransa, da irin maganar dā. 6 Ga abin da yake cikin wasiƙar, “Geshem ya faɗa mini, ana ta ji jita jita wurin maƙwabta, cewa kai da Yahuduwa kuna niyyar tayarwar, don haka kake ginin garun, kana so kuma ka naɗa kanka sarki. 7 Ga shi, ka sa annabawa su yi shelarka a Urushalima cewa, ‘Akwai sarki a Yahuza.’ To, za a faɗa wa sarki wannan magana, sai ka zo mu yi shawara tare a kan wannan al'amari.” 8 Sai na mayar masa da amsa cewa, “Faufau, ba a yi wani abu haka kamar yadda ka faɗa ba, kai ne ka ƙaga wannan a zuciyarka.” 9 Gama dukansu so suke su tsoratar da mu, suna cewa, “Za su daina aikin.” Amma na yi addu'a, na ce, “Ya Allah, ka ƙarfafa ni.” 10 Sa'ad da na ziyarci Shemaiya ɗan Delaiya, wato jikan wanda aka hana shi fita, sai ya ce mini, “Bari mu tafi cikin Haikalin Allah, mu rufe ƙofofin Haikalin, gama suna zuwa su kashe ka, za su iya zuwa a wani dare su kashe ka.” 11 Sai na ce, “Mutum kamata ne, zai gudu? Mutum irina zai shiga Haikali don ya tsere? To, ba zan tafi ba.” 12 Na gane Allah bai aike shi wurina ba. Ya yi mini wannan magana domin Tobiya da Sanballat sun haɗa baki da shi. 13 Gama da wannan nufi ne suka haɗa baki, don in ji tsoro, in yi yadda suke so, in yi zunubi, da haka za su ba ni mugun suna, su yi mini ba'a. 14 “Ya Allahna, ka tuna da Tobiya da Sanballat bisa ga abubuwan nan da suka yi, da annabiya Nowadiya, da sauran annabawa waɗanda suka so su tsoratar da ni.”

Gamawar Aikin

15 A cikin kwana hamsin da biyu aka gama garun, ran ashirin da biyar ga watan Elul. 16 Sa'ad da abokan gābanmu da dukan al'umman da suke kewaye da mu suka ji, sai suka ji tsoro, gabansu kuma ya faɗi, gama sun gane, da taimakon Allahnmu muka yi wannan aiki. 17 A kwanakin nan kuma shugabannin Yahuza suka yi ta aika wa Tobiya da wasiƙu, shi kuma Tobiya yana ta aika musu da nasa wasiƙu. 18 Mutane da yawa a Yahuza sun rantse za su goyi bayan Tobiya, domin ya auri 'yar Shekaniya, ɗan Ara. Ɗansa kuma, wato Yohenan, ya auri 'yar Meshullam, ɗan Berikiya. 19 Mutane suka yi magana a kan ayyukan kirki na Tobiya a gabana. Suka kuma kai maganata a wurinsa, sai Tobiya ya yi ta aika mini da wasiƙu don ya tsoratar da ni.

Nehemiya 7

Nehemiya ya Zaɓi Masarautan Urushalima

1 Sa'ad da aka gina garun, aka sa ƙofofinsa, aka kuma sa matsaran ƙofofi, da mawaƙa, da Lawiyawa, 2 sai na ba ɗan'uwana, Hanani, da Hananiya, shugaban kagara, aikin riƙon Urushalima. Shi Hananiya mai aminci ne, mai tsoron Allah, fiye da sauran mutane. 3 Sa'an nan na ce musu, kada su buɗe ƙofofin Urushalima da sassafe, sai rana ta cira sosai, su kuma kulle ƙofofin da ƙarfe kafin matsara su tashi wajen faɗuwar rana. Su samo matsara daga mazaunan Urushalima, su sa su tsaye a muhimman wurare, waɗansunsu kuma suna zaga gidaje.

Lissafin Mutane

4 Birnin yana da faɗi da girma, amma mutanen da suke ciki kaɗan ne, ba a kuma gina gidaje ba tukuna. 5 Allahna kuwa ya sa a zuciyata in tara manya da shugabanni, da sauran jama'a don a rubuta su bisa ga asalinsu. Na sami littafin asali na waɗanda suka fara komowa. Ga abin da na tarar aka rubuta ciki. 6 Waɗannan su ne mutanen lardin Yahuza, waɗanda suka komo daga zaman talala da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kai mutane. Sun komo Urushalima da Yahuza. Kowa ya tafi garinsu. 7 Sun komo tare da Zarubabel, da Yeshuwa, da Nehemiya, da Seraiya, da Re'elaya, da Nahamani, da Mordekai, da Bilshan, da Misfar, da Bigwai, da Rehum, da Ba'ana. 8-25 Ga jerin iyalan Isra'ila da adadin waɗanda suka komo daga zaman dole iyalin Farosh, dubu biyu da ɗari da saba'in da biyu (2,172 ) iyalin Shefatiya, ɗari uku da saba'in da biyu iyalin Ara, ɗari shida da hamsin da biyu iyalin Fahat-mowab, wato zuriyar Yeshuwa da Yowab, dubu biyu da ɗari takwas da goma sha takwas (2,818 ) iyalin Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254 ) iyalin Zattu, ɗari takwas da arba'in da biyar iyalin Zakkai, ɗari bakwai da sittin iyalin Bani, ɗari shida da arba'in da takwas iyalin Bebai, ɗari shida da ashirin da takwas iyalin Azgad, dubu biyu da ɗari uku da ashirin da biyu (2,322 ) iyalin Adonikam, ɗari shida da sittin da bakwai iyalin Bigwai, dubu biyu da sittin da bakwai (2,067 ) iyalin Adin, ɗari shida da hamsin da biyar iyalin Ater (na Hezekiya), tasa'in da takwas iyalin Hashum, ɗari uku da ashirin da takwas iyalin Bezai, ɗari uku da ashirin da huɗu iyalin Yora, ɗari da goma sha biyu iyalin Gibeyon, tasa'in da biyar 26-38 Mutanen da kakanninsu suka zauna a waɗannan garuruwa, su ma sun komo daga zaman talala. Baitalami da Netofa, ɗari da tamanin da takwas Anatot, ɗari da ashirin da takwas Azmawet, arba'in da biyu Kiriyat-yeyarim da Kefira, da Biyerot, ɗari bakwai da arba'in da uku Rama da Geba, ɗari shida da ashirin da ɗaya Mikmash, ɗari da ashirin da biyu Betel da Ai, ɗari da ashirin da uku Da wani Nebo, hamsin da biyu Da wani Elam, dubu da ɗari biyu da hamsin da huɗu (1,254 ) Harim, ɗari uku da ashirin Yariko, ɗari uku da arba'in da biyar Lod, da Hadid, da Ono, ɗari bakwai da ashirin da ɗaya Senaya, dubu uku da ɗari tara da talatin (3,930 ) 39-42 Ga lissafin iyalin firistoci da suka komo daga zaman talala. Yedaiya, na zuriyar Yeshuwa, ɗari tara da saba'in da uku Immer, dubu ɗaya da hamsin da biyu (1,052 ) Fashur, dubu da ɗari biyu da arba'in da bakwai (1,247 ) Harim, dubu ɗaya da goma sha bakwai (1,017 ) 43 Lawiyawan da suka komo daga zaman talala, Yeshuwa da Kadmiyel na zuriyar Hodawiya, saba'in da huɗu. 44 Mawaƙa, na zuriyar Asaf, ɗari da arba'in da takwas. 45 Masu tsaron Haikali su ne zuriyar Shallum, da Ater, da Talmon, da Akkub, da Hatita, da Shobai, ɗari da talatin da takwas. 46-56 Ma'aikatan Haikali da suka komo daga zaman talala, su ne Zuriyar Ziha, da Hasufa, da Tabbawot, Keros, da Siyaha, da Fadon, Lebana, da Hagaba, da Shamlai, Hanan, da Giddel, da Gahar, Rewaiya, da Rezin, da Nekoda, Gazam, da Uzza, da Faseya, Besai, da Me'uniyawa, da Nefushiyawa, Bakbuk, da Hakufa, da Harkur, Bazlut, da Mehida, da Harsha, Barkos, da Sisera, da Tema, Neziya, da Hatifa. 57-59 Iyalan barorin Sulemanu da suka komo daga zaman talala, su ne na Sotai, da Hassoferet, da Feruda, Yawala, da Darkon, da Giddel, Shefatiya, da Hattil, da Fokeret-hazzebayim, da Ami. 60 Jimillar zuriyar ma'aikatan Haikali da na Sulemanu, su ɗari uku da tasa'in da biyu ne. 61-62 Waɗannan su ne daga zuriyar Delaiya, da Tobiya, da Nekoda, waɗanda suka zo daga garuruwan Telmela, da Tel-harsha, da Kerub, da Addan, da Immer, amma ba su iya nuna gidajen kakanninsu, ko zuriyarsu a cikin Isra'ilawa ba, su ɗari shida ne da arba'in da biyu. 63 Na wajen firistoci kuma su ne zuriyar Habaya, da na Hakkoz, da na Barzillai, wanda ya auri 'yar Barzillai mutumin Gileyad, aka kira shi da sunan zuriyar surukinsa. 64 Waɗannan suka nema a rubuta su tare da waɗanda aka rubuta jerin sunayen asalinsu, amma ba a same su a ciki ba, saboda haka aka hana su shiga cikin firistoci, sun zama kamar marasa tsarki. 65 Sai mai mulki ya faɗa musu kada su ci abinci mafi tsarki, sai an sami firist wanda zai yi tambaya ta wurin Urim da Tummin tukuna. 66-69 Jimillar waɗanda suka komo duka su dubu arba'in da dubu biyu da ɗari uku da sittin ne (42,360 ) barorinsu mata da maza, waɗanda yawansu ya kai dubu bakwai da ɗari uku da talatin da bakwai (7,337 ) mawaƙa ɗari biyu da arba'in da biyar mata da maza dawakansu kuma ɗari bakwai da talatin da shida ne alfadaransu kuma ɗari biyu da arba'in da biyar ne raƙumansu ɗari huɗu da talatin da biyar ne jakunansu dubu shida da ɗari bakwai da ashirin (6,720 ) 70-72 Da yawa daga cikin jama'a suka ba da taimako domin biyan aikin gyaran Haikali. Mai mulki ya ba da zinariya darik dubu (1,000 ) kwanonin wanke hannu guda hamsin rigunan firistoci ɗari biyar da talatin Shugabannin iyali suka ba da zinariya darik dubu ashirin (20,000 ) azurfa maina dubu biyu da ɗari biyu (2,200 ) Sauran jama'a suka ba da zinariya darik dubu ashirin (20,000 ) azurfa maina dubu biyu (2,000 ) rigunan firistoci guda sittin da bakwai. 73 Sa'an nan firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron Haikali, da mawaƙa da waɗansu da dama daga cikin jama'a, da ma'aikatan Haikali, da dukan Isra'ilawa suka zauna a garuruwansu.

Ezra ya Karanta wa Jama'a Attaura

8 Da amaryar watan bakwai mutanen Isra'ila duk sun riga sun zauna a garuruwansu. 1 Dukan jama'a suka taru wuri ɗaya a filin Ƙofar Ruwa, suka faɗa wa Ezra, magatakarda, ya kawo Attaura ta Musa wanda Ubangiji ya ba Isra'ilawa. 2 A ran ɗaya ga watan bakwai, sai Ezra, firist, ya kawo Attaura a gaban taron jama'a, mata da maza, da dukan waɗanda za su ji, su fahimta. 3 Ya karanta Littafin, yana fuskantar filin Ƙofar Ruwa, a gaban mata da maza, da waɗanda za su iya fahimta. Mutane duka kuwa suka kasa kunne ga karatun Attaura, tun da sassafe har zuwa rana tsaka. 4 Sai Ezra, magatakarda, ya tsaya a wani dakali na itace, wanda suka shirya musamman domin wannan hidima. Sai Mattitiya, da Shema, da Anaya, da Uriya, da Hilkiya, da Ma'aseya, suka tsaya a wajen damansa, a wajen hagunsa kuwa Fedaiya, da Mishayel, da Malkiya, da Hashum, da Hashbaddana, da Zakariya, da Meshullam suka tsaya. 5 Ezra kuwa ya buɗe Littafin a gaban jama'a duka, domin yana sama da jama'a. Sa'ad da ya buɗe Littafin, sai jama'a duka suka miƙe tsaye. 6 Sai Ezra ya yabi Ubangiji Allah Maɗaukaki. Jama'a duka suka amsa, “Amin, amin!” Suna ɗaga hannuwansu. Suka sunkuyar da kansu har ƙasa, suka yi wa Ubangiji sujada. 7 Sa'ad da jama'a suke tsaye a wurarensu, sai Lawiyawa, wato su Yeshuwa, da Bani, da Sherebiya, da Yamin, da Akkub, da Shabbetai, da Hodiya, da Ma'aseya, da Kelita, da Azariya, da Yozabad, da Hanan, da Felaya, suka fassara musu dokokin. 8 Suka karanta daga littafin dokokin Allah sosai, suka fassara musu, saboda haka jama'a suka fahimci karatun. 9 Nehemiya kuwa wanda yake mai mulki, da Ezra, firist da magatakarda, da Lawiyawa waɗanda suka fassara wa jama'a dokokin, suka ce wa dukan jama'a, “Wannan rana tsattsarka ce, ta Ubangiji Allahnku, kada ku yi baƙin ciki ko kuka.” Gama mutane duka sai kuka suke sa'ad da aka karanta musu dokokin. 10 Sa'an nan ya ce musu, “Ku koma gidajenku ku ci abinci mai kyau, ku sha ruwan inabi mai zaƙi, ku kuma aika wa wanda ba shi da shi, gama wannan rana tsattsarka ce ta Ubangijinmu. Kada ku yi baƙin ciki, gama farin cikin da Ubangiji ya ba ku shi ne ƙarfinku.” 11 Lawiyawa kuma suka bi suna rarrashin jama'a, suna cewa, “Ku yi shiru, gama wannan rana tsattsarka ce, kada ku yi baƙin ciki.” 12 Sai jama'a duka suka koma gidajensu suka ci, suka sha, suka aika wa wanda ba shi da abinci. Suka yi murna ƙwarai domin sun fahimta dokokin da aka karanta musu.

Idin Bukkoki

13 Kashegari kuma sai shugabannin kakannin gidajen jama'a duka, tare da firistoci, da Lawiyawa, suka je wurin Ezra, magatakarda, domin su yi nazarin dokokin. 14 Sai suka iske an rubuta a cikin dokokin da Ubangiji ya umarta ta hannun Musa, cewa sai jama'ar Isra'ila su zauna a bukkoki a lokacin idi na watan bakwai. 15 Saboda haka sai suka yi shela a garuruwansu duka da a Urushalima cewa, “Ku fita zuwa tuddai ku kawo rassan zaitun, da na kadanya, da na dargaza, da na dabino, da sauran rassan itatuwa masu gazari, domin a yi bukkoki kamar yadda aka rubuta.” 16 Sai suka tafi suka kawo rassan, suka yi wa kansu bukkoki a kan rufin sorayensu, da a dandalinsu, da cikin harabar Haikalin Allah, da a dandalin Ƙofar Ruwa, da a dandalin Ƙofar Ifraimu. 17 Dukan taron jama'ar da suka komo daga zaman talala suka yi wa kansu bakkoki, suka zauna cikinsu, gama tun daga kwanakin Joshuwa ɗan Nun, har zuwa wannan rana, jama'ar Isra'ila ba su yin haka. Aka kuwa yi farin ciki mai yawa. 18 Kowace rana, tun daga rana ta fari zuwa rana ta ƙarshe, Ezra yakan karanta musu daga cikin littafin dokokin Allah. Suka kiyaye idin har kwana bakwai. A rana ta takwas kuma suka muhimmin taro bisa ga ka'ida.

Nehemiya 9

Jama'a sun Hurta Laifofinsu

1 A rana ta ashirin da huɗu ga watan nan, sai jama'ar Isra'ila suka taru, suna azumi, suna saye da tufafin makoki, suna zuba toka a kansu. 2 Suka ware kansu daga bāre duka, suka tsaya, suna hurta laifofinsu da na kakanninsu. 3 Sa'ad da suke tsaye a inda suke, sai suka ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu na yini, suna karanta littafin dokokin Ubangiji Allahnsu. Suka kuma ɗauki kashi ɗaya daga cikin huɗu ɗin na yinin, suna ta hurta laifofi suna kuma yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. 4 Sai Yeshuwa, da Bani, da Kadmiyel, da Shebaniya, da Bunni, da Sherebiya, da Bani, da Kenani suka tsaya a kan dakalin Lawiyawa, suka ta da murya da ƙarfi ga Ubangiji Allahnsu. 5 Waɗannan Lawiyawa kuma, wato Yeshuwa, da Kadmiyel, da Bani, da Hashabnaiya, da Sherebiya, da Hodiya, da Shebaniya, da Fetahiya su ne suka yi kiran sujada, suka ce, “Ku miƙe tsaye, ku yabi Ubangiji Allahnku, Ku yabe shi har abada abadin. Bari kowa ya yabi maɗaukakin sunanka, ya Ubangijii, Ko da yake ba yabon da ɗan adam zai yi har ya isa.”

Addu'ar Hurta Laifi

6 Sa'an nan suka yi wannan addu'a, suka ce, “Kai kaɗai ne Ubangiji, ya Ubangiji, Kai ne ka yi samaniya da taurari da sararin sama. Kai ne ka yi ƙasa, da teku, da kowane abu da yake cikinsu, Ka ba dukansu rai, Ikokin samaniya sun rusuna suna maka sujada. 7 Kai ne, ya Ubangiji Allah, ka zaɓi Abram, Ka fito da shi daga Ur ta Kaldiyawa, Ka sāke sunansa ya zama Ibrahim. 8 Ka iske shi amintacce a gare ka, Ka kuwa yi masa alkawari. Ka yi alkawari za ka ba shi ƙasar Kan'ana, Da ta Hittiyawa, da ta Amoriyawa, da ta Ferizziyawa, Da ta Yebusiyawa, da ta Girgashiyawa, Ta zama inda zuriyarsa za su zauna. Ka kuwa cika alkawarinka, gama kai mai aminci ne. 9 Ka ga wahalar kakanninmu a Masar, Ka ji kukansu a Bahar Maliya. 10 Ka kuma aikata alamu da al'ajabai a kan Fir'auna, Da fadawansa duka, da mutanen ƙasarsa, Gama ka san yadda suka yi wa jama'arka danniya. Ta haka ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau. 11 Ka yi hanya ta cikin teku domin jama'arka, Ka sa su bi ta ciki a kan sandararriyar ƙasa. Ka sa waɗanda suke fafararsu suka hallaka cikin zurfin teku, Suka nutse kamar dutse. 12 Da rana ka bishe su da al'amudin girgije, Da dare ka bishe su da al'amudin wuta. 13 Ka kuma sauka a bisa Dutsen Sinai, Ka yi magana da jama'arka a can, Ka ba su ka'idodin da suka dace, Da dokoki, da kyakkyawar koyarwa. 14 Ka koya musu su kiyaye Asabar ɗinka tsattsarka, Ka kuma ba su dokokinka ta hannun Musa bawanka. 15 Ka ba su abinci daga sama sa'ad da suka ji yunwa, Ruwa kuma daga dutse sa'ad da suka ji ƙishi, Ka faɗa musu su shiga su mallaki ƙasar da ka yi alkawari za ka ba su. 16 Amma kakanninmu suka yi fāriya, suka taurare, Suka ƙi yin biyayya da umarnanka. 17 Suka ƙi yin biyayya, Suka manta da dukan abin da ka yi, Suka manta da al'ajaban da ka aikata. Cikin fāriyarsu suka zaɓi shugaba, Don su koma cikin bauta a Masar. Amma kai Allah ne mai gafartawa, Kai mai alheri ne, mai ƙauna, Jinƙanka da girma yake, ba ka yashe su ba. 18 Ko sa'ad da suka yi wa kansu ɗan marakin zubi, Suka ce shi ne allahn da ya fisshe su daga Masar, Ai, sun yi maka ɓatanci, ya Ubangiji. 19 Amma ba ka rabu da su a hamada ba, Saboda jinƙanka mai girma ne. Ba ka kuwa kawar da girgije da wuta ba, Waɗanda suke nuna musu hanya dare da rana. 20 Ta wurin alherinka ka faɗa musu abin da ya kamata su yi, Ka ciyar da su da manna, ka ba su ruwa su sha. 21 Ka taimake su a jeji shekara arba'in, Ka ba su dukan abin da suke bukata, Ƙafafunsu ba su kumbura su yi musu ciwo ba. 22 “Ka sa sun ci al'ummai da mulkoki da yaƙi, Ƙasashen da suke maƙwabtaka da tasu. Suka ci ƙasar Sihon, Sarkin Heshbon, Da ƙasar Bashan, inda Og yake sarki. 23 Ka riɓaɓɓanya zuriyarsu kamar taurarin sararin sama, Ka sa suka ci ƙasar, suka zauna cikinta, Ƙasar da aka yi wa kakanninsu alkawari za ka ba su. 24 Saboda haka zuriyarsu suka shiga, suka mallaki ƙasar Kan'ana. Ka rinjayi mutanen da suke zama a can. Ka ba jama'arka iko su yi yadda suke so Da mutane, da sarakunan ƙasar Kan'ana. 25 Sun ci birane masu garu, da ƙasa mai dausayi, Da gidaje cike da dukiya, da rijiyoyi, da gonakin inabi, Da itatuwan zaitun, da itatuwa masu 'ya'ya. Suka ci dukan abin da suke so, suka yi taiɓa, Suka mori dukan kyawawan abubuwan da ka ba su. 26 “Amma suka yi maka rashin biyayya, suka tayar maka, Suka juya wa dokokinka baya, Suka karkashe anna bawan da suka faɗakar da su, Waɗanda suka faɗa musu su juyo gare ka. Suka yi ta saɓa maka lokaci lokaci. 27 Saboda haka ka bar abokan gābansu su ci su, mallake su. A wahalarsu sun yi kira gare ka domin taimako, Ka kuwa amsa musu daga Sama. Ta wurin jinƙanka mai yawa ka aiko musu da shugabanni, Waɗanda suka kuɓutar da su daga maƙiyansu. 28 Sa'ad da zaman salama ya komo, sai kuma su yi zunubi, Kai kuma sai ka bar abokan gabansu su ci su. Duk da haka idan sun tuba, suka roƙe ka ka cece su, Kakan ji daga Sama, sau da yawa, Ka cece su da jinƙanka mai yawa. 29 Ka gargaɗe su su yi biyayya da koyarwarka, Amma sun bijire wa dokoki saboda girmankai, Ko da yake kiyaye dokarka ita ce hanyar rai. Masu taurinkai sun taurare, sun ƙi yin biyayya. 30 “Ka yi haƙuri da su shekaru da yawa, ka gargaɗe su, Annabawanka sun yi musu magana, amma sun toshe kunne. Saboda haka ka sa waɗansu al'ummai su mallaki jama'arka. 31 Duk da haka, saboda yawan jinƙanka, Ba ka yashe su ko ka hallaka su ba. Kai Allah mai alheri ne mai jinƙai! 32 “Ya Allah, Allahnmu, da girma kake! Kai mai banrazana ne, cike da iko! Da aminci ka cika alkawaranka da ka alkawarta. Daga lokacin da Sarkin Assuriya ya danne mu, Har yanzu ma, wace wahala ce ba mu sha ba! Sarakunanmu, da shugabanninmu, da firistocinmu, Da annabawanmu, da kakanninmu, Da dukan sauran jama'arka sun sha wahala. Ka san irin wahalar da muka sha. 33 Ka yi daidai da ka hukunta mu haka! Kai mai aminci ne, mu kuwa mun yi zunubi. 34 Gama kakanninmu, da sarakunanmu, Da shugabanninmu, da firistocinmu, Ba su kiyaye dokarka ba. Ba su kasakunne ga umarnanka da gargaɗinka ba. Da waɗannan ne kake zarginsu. 35 Da albarkacinka sarakuna suke mulkin jama'arka, Sa'ad da suke ƙasashen waje, ƙasa mai dausayi ka ba su, Amma ba su juyo su bar zunubi, su bauta maka ba. 36 Ga shi, a yau mu bayi ne a ƙasar da ka ba mu, Wannan ƙasa mai dausayi wadda take ba mu abinci. 37 Amfanin ƙasa duk yana tafiya ga sarakunan Da ka ɗora su a kanmu saboda mun yi zunubi. Suna yi mana yadda suka ga dama, mu da dabbobinmu, Muna cikin baƙin ciki.”

Jama'a sun Sa Hannu a Yarjejeniya

38 “Saboda wannan duka muke yin alkawari mai ƙarfi a rubuce. Shugabanninmu kuwa, da Lawiyawanmu, da firistocinmu, suka buga hatimi, suka sa hannu.”

Nehemiya 10

1 Waɗanda suka fara sa hannu a takardar alkawarin, su ne mai mulki, wato Nehemiya ɗan Hakaliya, da Zadakiya, nan firistoci, wato Seraiya, da Azariya, da Irmiya, Fashur, da Amariya, da Malkiya, Hattush, da Shebaniya, da Malluki, Harim, da Meremot, da Obadiya, Daniyel, da Ginneton, da Baruk, Meshullam, da Abaija, da Miyamin, Mawaziya, da Bilgai, da Shemaiya. 9-13 Wajen Lawiyawa kuwa, su ne Yeshuwa ɗan Azaniya, da Binnuyi daga zuriyar Henadad da Kadmiyel. 'Yan'uwansu kuwa su ne Shebaniya, da Hodiya, Kelita, da Felaya, da Hanan, Mika, da Rehob, da Hashabiya, Zakkur, da Sherebiya, da Shebaniya, Hodiya, da Bani, da Beninu. 14-27 Shugabannin jama'a kuwa, su ne Farosh, da Fahat-mowab, Elam, da Zattu, da Bani, Bunni, da Azgad, da Bebai, Adonaija, da Bigwai, da Adin, Ater, da Hezekiya, da Azzur, Hodiya, da Hashum, da Bezai, Harif, da Anatot, da Nebai, Magfiyash, da Meshullam, da Hezir, Meshezabel, da Zadok, da Yadduwa, Felatiya, da Hanan, da Anaya, Hosheya, da Hananiya, da Hasshub, Hallohesh, da Filha, da Shobek, Rehum, da Hashabna, da Ma'aseya, Ahaija, da Hanan, da Anan, Malluki, da Harim, da Ba'ana.

Alkawarin da aka Yi

28 Jama'ar Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa, da ma'aikatan Haikali, da dukan waɗanda suka ware kansu daga sauran al'umman waɗansu ƙasashe, domin su bi dokokin Allah, su da matansu, da 'ya'yansu mata da maza, da dai duk waɗanda suke da sani da fahimta, 29 suka haɗa kai da 'yan'uwansu, da shugabanninsu, suka rantse, cewa la'ana ta same su idan ba su kiyaye dokokin Allah waɗanda ya ba bawansa Musa ba. Suka rantse za su kiyaye, su aikata umarnai, da ka'idodi, da dokokin Ubangijinmu. 30 Suka ce, “Ba za mu aurar wa mutanen ƙasar da 'ya'yanmu mata ba. Ba kuma za mu auro wa 'ya'yanmu maza 'ya'yansu mata ba. 31 “Idan kuma mutanen ƙasar sun kawo kayayyaki da hatsi don sayarwa a ranar Asabar, ba za mu saya ba, ko kuma a wata tsattsarkar rana. “A kowace shekara ta bakwai ba za mu girbe amfanin gonakinmu ba, za mu kuma yafe kowane irin bashi. 32 “Muka kuma anita kowannenmu zai riƙa ba da sulusin shekel a shekara domin aikin Haikalin Allahnmu. 33 “Za mu tanadi gurasar ajiyewa, da hadayar gāri ta kullum, da ta ranakun Asabar, da ta amaryar wata, da ta ƙayyadaddun idodi, da abubuwa masu tsarki, da hadaya don zunubi saboda yi wa jama'ar Isra'ila kafara, da dukan aiki na Haikalin Allahnmu. 34 “Muka kuma jefa kuri'a wato firistoci, da Lawiyawa, da jama'a a kan kawo itacen hadaya a Haikalin Allahnmu, bisa ga gidajen kakanninmu, a kan ƙayyadaddun lokatai a shekara, don a ƙona hadayu a bisa bagaden Ubangiji Allahnmu, kamar yadda aka rubuta a dokoki. 35 “Wajibi ne kuma mu kawo nunan fari na gonakinmu, da nunan fari na 'ya'yan itatuwanmu kowace shekara zuwa Haikalin Ubangiji. 36 “Za mu kuma kawo 'ya'yan farinmu maza, da na shanunmu, da na tumaki, da awaki, kamar dai yadda aka rubuta a dokoki, haka za mu kawo su a Haikalin Allahnmu, da gaban firistocin da suke hidima a Haikalin Allahnmu. 37 “Za mu kuma kawo hatsinmu na fari kullum, da sadakokinmu, da 'ya'yan itatuwanmu, da sabon ruwan inabi, da mai, a gaban firistoci, a shirayin Haikalin Allahnmu. “Za mu kuma ba Lawiyawa zakar amfanin gonakinmu, gama Lawiyawa ne suke tara zaka a garuruwanmu na karkara. 38 Firist kuwa daga zuriyar Haruna zai kasance tare da Lawiyawa sa'ad da suke karɓar zakar. Lawiyawa kuma za su fid da zaka daga cikin zakar da aka tara musu, su kawo ɗakin ajiya na Haikalin Allah. 39 Gama jama'ar Isra'ila da Lawiyawa za su kawo sadakoki na hatsi, da na ruwan inabi, da na mai, a ɗakin ajiya inda tasoshin Haikali suke, da gaban firistocin da suke hidima, da masu tsaron ƙofofi, da mawaƙa. “Ba za mu ƙyale Haikalin Allahnmu ba.”

Nehemiya 11

Mazaunan Urushalima

1 Shugabannin jama'a kuwa suka zauna a Urushalima. Sauran jama'a kuma suka jefa kuri'a don a sami mutum guda daga cikin goma wanda zai zauna a Urushalima, wato tsattsarkan birni, sauran tara kuwa su yi zamansu a sauran garuruwa. 2 Jama'a suka sa wa dukan waɗanda suka tafi su zauna a Urushalima da yardar ransu albarka. 3 Waɗannan su ne shugabannin lardi waɗanda suka zauna a Urushalima, amma a garuruwan Yahuza kowa ya zauna a mahallinsa a garuruwansu, wato Isra'ila, da firistoci, da Lawiyawa, da ma'aikatan Haikali, da zuriyar barorin Sulemanu. 4 Waɗansu mutanen Yahuza da na Biliyaminu suka zauna a Urushalima. Daga cikin mutanen Yahuza akwai Ataya ɗan Azariya, wato j�kan Zakariya ɗan Amariya. Sauran kakanninsa su ne Shefatiya, da Mahalalel, zuriyar Feresa ɗan Yahuza. 5 Akwai kuma Ma'aseya ɗan Baruk, j�kan Kolhoze. Sauran kakanninsa su ne Hazaiya, da Adaya, da Yoyarib, da Zakariya, zuriyar Shela ɗan Yahuza. 6 Dukan mutanen Feresa da suka zauna Urushalima su ɗari huɗu da sittin da takwas ne, dukansu kuwa muhimman mutane ne. 7 Waɗannan su ne mutanen Biliyaminu, Sallai ɗan Meshullam, j�kan Yowed. Sauran kakanninsa su ne Fedaiya, da Kolaiya, da Ma'aseya, da Itiyel da Yeshaya. 8 Sa'an nan kuma ga Gabbai da Sallai danginsa, mutum ɗari tara da ashirin da takwas. 9 Yowel ɗan Zikri shi ne shugabansu, Yahuza ɗan Hassenuwa shi ne shugaba na biyu cikin birnin. 10 Na wajen firistoci, su ne Yedaiya ɗan Yoyarib, da Yakin, 11 da Seraiya ɗan Hilkiya, j�kan Shallum. Sauran kakanninsa, su ne Zadok, da Merayot, da Ahitub, mai lura da Haikalin Allah. 12 Tare da 'yan'uwansu waɗanda suka yi aiki a Haikali, su ɗari takwas da ashirin da biyu ne. Akwai kuma Adaya ɗan Yeroham, j�kan Felaliya. Sauran kakanninsa su ne Amzi, da Zakariya, da Fashur, da Malkiya. 13 Tare da 'yan'uwansu shugabannin gidajen kakanni, su ɗari da arba'in da biyu. Sai kuma Amashai ɗan Azarel, j�kan Azai. Sauran kakanninsa su ne Meshillemot, da Immer. 14 Tare da 'yan'uwansu, su ɗari da ashirin da takwas ne gwarzayen sojoji ne. Shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim. 15 Na wajen Lawiyawa kuwa su ne Shemaiya ɗan Hasshub, j�kan Azrikam. Sauran kakanninsa su ne Hashabiya, da Bunni, 16 da Shabbetai, da Yozabad, ɗaya daga cikin manyan shugabanni na Lawiyawa, waɗanda suke lura da kewayen Haikalin Allah. 17 Da kuma Mattaniya ɗan Mika, j�kan Zikri, zuriyar Asaf, shi ne shugaba na farko na mawaƙan addu'a ta godiya. Bakbukiya, shi ne mataimakin Mattaniya. Ga kuma Obadiya ɗan Shemaiya, j�kan zuriyar Galal, zuriyar Yedutun. 18 Dukan Lawiyawa da suke a tsattsarkan birni su ɗari biyu da tamanin da huɗu ne. 19 Masu tsaron ƙofofi kuma su ne Akkub, da Talmon, da 'yan'uwansu, su ɗari da saba'in da biyu ne. 20 Sauran jama'ar Isra'ila kuwa, da firistoci, da Lawiyawa suka zauna a dukan garuruwan Yahuza, kowa ya zauna a gādonsa. 21 Amma ma'aikatan Haikali suka zauna a Ofel. Ziha da Gishfa, su ne shugabannin ma'aikatan Haikali. 22 Shugaban Lawiyawan da yake a Urushalima, shi ne Uzzi ɗan Bani, j�kan Hashabiya. Sauran kakanninsa su ne Mattaniya, ɗan Mika daga zuriyar Asaf. Su ne mawaƙa a Haikalin Allah. 23 Sarki ya yi wa shugabannin mawaƙa umarni da ƙarfi a kan abin da za su yi kowace rana. 24 Fetahiya ɗan Meshezabel, daga zuriyar Zera na kabilar Yahuza, shi ne wakilin sarki a kan dukan abin da ya shafi jama'a.

Mutanen da suke a Sauran Garuruwa da Birane

25 Game da ƙauyuka da gonakinsu kuma, waɗansu mutanen Yahuza suka zauna a Kiriyat-arba, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta, 26 da a biranen Yeshuwa, da Molada, da Bet-felet, 27 da Hazar-shuwal, da Biyer-sheba da ƙauyukanta, 28 da Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta, 29 da En-rimmon, da Zora, da Yarmut, 30 da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da Azeka da ƙauyukanta. Haka suka yi zango daga Biyer-sheba zuwa kwarin Hinnom. 31 Mutanen kabilar Biliyaminu suka zauna a Geba, da Mikmash, da Ayya, da Betel da sauran ƙauyuka na kewaye, 32 da Anatot, da Nob, da Ananiya, 33 da Hazor, da Rama, da Gittayim, 34 da Hadid, da Zeboyim, da Neballat, 35 da Lod, da Ono, wato kwarin masu sana'a. 36 Waɗansu kashi na Lawiyawan da suke a Yahuza, aka sa su zauna a yankin ƙasar Biliyaminu.

Nehemiya 12

Firistoci da Lawiyawa

1 Firistoci da Lawiyawa da suka komo tare da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, da Yeshuwa, su ne Seraiya, da Irmiya, da Ezra, 2-7 Amariya, da Malluki, da Hattush, Shekaniya, da Rehum, da Meremot, Iddo, da Ginneton, da Abaija, Miyamin, da Mawadiya, da Bilga, Shemaiya, da Yoyarib, da Yedaiya, Sallai, da Amok, da Halkiya, da Yedaiya. Waɗannan su ne shugabannin firistoci da 'yan'uwansu a zamanin Yeshuwa. 8-9 Lawiyawa su ne, Yeshuwa, da Binnuyi, da Kadmiyel, Sherebiya, da Yahuza, da Mattaniya wanda yake lura da waƙoƙin godiya, da shi da 'yan'uwansa. Bukbukiya da Unno, 'yan'uwansu, suka tsaya daura da su a taron sujada.

Zuriyar Yeshuwa Firist

10 Yeshuwa shi ne ya haifi Yoyakim, Yoyakim ya haifi Eliyashib, Eliyashib ya haifi Yoyada. 11 Yoyada ya haifi Jonatan, Jonatan ya haifi Yadduwa.

Shugabannin Iyalin Firistoci

12-21 A zamanin Yoyakim babban firist, waɗannan su ne shugabannin iyalin firistoci, na wajen Seraiya, Meraiya ne na wajen Irmiya, Hananiya ne na wajen Ezra, Meshullam ne na wajen Amariya, Yehohanan ne na wajen Malluki, Jonatan ne na wajen Shebaniya, Yusufu ne na wajen Harim, Adana ne na wajen Merayot, Helkai ne na wajen Iddo, Zakariya ne na wajen Ginneton, Meshullam ne na wajen Abaija, Zikri ne na wajen Miniyamin da Mowadiya, Filtai ne na wajen Bilga, Shimeya ne na wajen Shemaiya, Yehonatan ne na wajen Yoyarib, Mattenai ne na wajen Yedaiya, Uzzi ne na wajen Sallai, Kallai ne na wajen Amok, Eber ne na wajen Hilkiya, Hashabiya ne na wajen Yedaiya, Netanel ne.

Lissafin Manya na Iyalin Firistoci da Lawiyawa

22 A zamanin Eliyashib, da Yoyada, da Yohenan, da Yadduwa, Lawiyawa, har zuwa zamanin mulkin Dariyus, mutumin Farisa, aka rubuta shugabannin gidajen kakannin Lawiyawa da firistoci. 23 Aka kuma rubuta shugabannin gidajen kakannin zuriyar Lawi a tarihi, har zuwa zamanin Yohenan ɗan Eliyashib.

An Rarraba Ayyukan Haikali

24 Shugabannin Lawiyawa kuwa, su ne Hashabiya, da Sherebiya, da Yeshuwa, da Kadmiyel. 'Yan'uwansu suna tsaye kusa da su daki daki domin su yi yabo, su yi godiya kamar yadda Dawuda mutumin Allah ya umarta. 25 Mattaniya, da Bakbukiya, da Obadiya, da Meshullam, da Talmon, da Akkub su ne masu tsaron ƙofofi, suna tsaron ɗakunan ajiya na wajen ƙofofi. 26 Waɗannan suna nan a zamanin Yoyakim ɗan Yeshuwa, jikan Yehozadak, da zamanin mai mulki Nehemiya, da Ezra, firist da magatakarda.

An Keɓe Garun Birni

27 A lokacin keɓe garun Urushalima, sai aka nemo Lawiyawa a wurarensu duka don a kawo su Urushalima, su yi bikin keɓewa da farin ciki da godiya, da raira waƙoƙi da kuge, da garaya, da molo. 28 Aka tattara mawaƙa daga kewayen Urushalima da ƙauyukan Netofatiyawa. 29 Da kuma daga Betgilgal da karkarar Geba, da Azmawet, gama mawaƙan sun gina wa kansu ƙauyuka kewaye da Urushalima. 30 Sai firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma tsarkake jama'a, da ƙofofi, da garun. 31 Sai na sa shugabannin Yahuza su hawo garu, sa'an nan na sa manyan ƙungiyoyi biyu waɗanda za su yi godiya, su tafi a jere. Ƙungiya guda ta bi wajen dama a kan garun zuwa Ƙofar Juji. 32 Hoshaiya da rabin sugabannin Yahuza suka bi bayansu, 33 tare da Azariya, da Ezra, da Meshullam, 34 da Yahuza, da Biliyaminu, da Shemaiya, da Irmiya. 35 Sa'an nan waɗansu 'ya'yan firistoci, masu busar ƙaho, su ne Zakariya ɗan Jonatan, j�kan Shemaiya. Sauran kakanninsa su ne Mattaniya, da Mikaiya, da Zakkur, daga zuriyar Asaf. 36 Sauran 'yan'uwansa su ne Shemaiya, da Azarel, da Milalai, da Gilalai, da Ma'ai, da Netanel, da Yahuza, da Hanani. Suna da kayayyakin bushe-bushe da na kaɗekaɗe. Ezra magatakarda ne yake gabansu. 37 A Ƙofar Maɓuɓɓuga kuwa, sai suka yi gaba sosai wajen matakan birnin Dawuda, wajen hawan garu, daga bisa gidan Dawuda, zuwa Ƙofar Ruwa wajen gabas. 38 Ƙungiyar jama'a ta biyu ta masu yin waƙoƙin godiya, ta bi ta wajen hagu. Na bi su tare da rabin jama'a a kan garu, sama da Hasumiyar Tanderu zuwa garu mai fādi, 39 da Kuma sama da Ƙofar Ifraimu da wajen Tsohuwar Ƙofar, da wajen Ƙofar Kifi, da Hasumiyar Hananel, da Hasumiyar Ɗari zuwa Ƙofar Tumaki, sai suka tsaya a Ƙofar Tsaro. 40 Haka fa ƙungiyoyi biyu ɗin nan masu raira waƙoƙin godiya suka tsaya a Haikalin Allah. Ni da rabin shugabanni muna tare da su. 41 Tare da firistoci kuma, wato su Eliyakim, da Ma'aseya, da Miniyamin, da Mikaiya, da Eliyehoyenai, da Zakariya, da Hananiya, suna busa ƙaho, 42 da kuma Ma'aseya, da Shemaiya, da Ele'azara, da Uzzi, da Yehohanan, da Malkiya, da Elam, da Ezer, suna raira waƙoƙi, Yezrahiya kuma shi ne shugabansu. 43 Jama'a suka miƙa hadayu da yawa a wannan rana, suka yi murna, gama Allah ya faranta musu zuciya ƙwarai. Mata da yara kuma suka yi murna. Aka ji muryar murnar mutanen Urushalima daga nesa.

Shiri don Firistoci da Lawiyawa

44 A ran nan aka sa mutanen da za su lura da ɗakunan ajiya, da sadakoki, da nunan fari, da zaka. Su ne za su tara nunan fari daga gonakin da suke kusa da garuruwa, bisa ga yadda doka ta ce, saboda firistoci da Lawiyawa, gama mutanen Yahuza sun yi murna saboda hidimar da firistoci da Lawiyawa suka yi. 45 Sun yi wa Allahnsu sujada, sun yi hidimar tsarkakewa tare da mawaƙa da masu tsaron ƙofofi kamar yadda Dawuda da ɗansa Sulemanu suka umarta. 46 A dā a zamanin Dawuda da Asaf akwai shugaban mawaƙa, akwai kuma waƙoƙin yabo da na godiya ga Allah. 47 A zamanin Zarubabel da zamanin Nehemiya dukan jama'ar Isra'ila suka biya wa mawaƙa da masu tsaron ƙofofi bukatarsu ta kowace rana. Sun kuma ba Lawiyawa sadokoki, su Lawiyawa kuma suka ba zuriyar Haruna nasu rabo.

Nehemiya 13

Gyare-gyaren da Nehemiya ya Yi

1 A wannan rana aka karanta daga littafin Musa a kunnuwan jama'a. A cikinsa aka tarar da inda aka rubuta, cewa kada Ba'ammone, ko mutumin Mowab ya shiga taron jama'ar Allah. 2 Gama ba su taryi jama'ar Isra'ila da abinci da abin sha ba, amma suka yi ijara da Bal'amu ya zo ya la'anta musu su, amma Allahnmu ya juyar da la'anar ta zama albarka. 3 Da mutane suka ji dokokin, sai suka ware dukan waɗanda suke ba Isra'ilawa ba. 4 Kafin wannan lokaci Eliyashib, firist, wanda aka sa shi shugaban ɗakunan ajiya na Haikalin Allahnmu, wanda yake da dangantaka da Tobiya, 5 ya shirya wa Tobiya babban ɗaki inda dā aka ajiye hadaya ta gari, da turare, da tasoshi, da zakar hatsi, da ruwan inabi, da mai, waɗanda aka umarta a ba Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da inda aka ajiye sadakokin da ake ba firistoci. 6 Ba na nan a Urushalima sa'ad da wannan abu ya faru, gama a shekara ta talatin da biyu ta sarautar Artashate, Sarkin Babila, na tafi wurin sarki. Daga baya sarki ya ba ni izini in koma. 7 Da na komo Urushalima, sai na ga mugun abin da Eliyashib ya yi domin Tobiya, yadda ya shirya masa ɗaki a filin Haikalin Allah. 8 Sai na husata ƙwarai, na fitar da kayan ɗakin Tobiya a waje. 9 Sai na umarta, suka kuwa tsarkake ɗakunan, sa'an nan na mayar da tasoshin Haikalin Allah, da hadaya ta gari, turare a ciki. 10 Na kuma iske ba a ba Lawiyawa rabonsu ba. Saboda wannan Lawiyawa da mawaƙa masu hidima suka watse zuwa gonakinsu. 11 Sai na yi wa shugabanni faɗa, na ce, “Me ya sa aka ƙi kula da Haikalin Allah?” Sa'an nan na tara Lawiyawa da mawaƙa, na sa su a wuraren aikinsu. 12 Sai dukan mutanen Yahuza suka kawo zakar hatsi, da ta ruwan inabi, da ta mai, a ɗakunan ajiya. 13 Sai na sa Shelemiya, firist, da Zadok, magatakarda, da Fedaiya daga cikin Lawiyawa su zama masu lura da ɗakunan ajiya. Na kuma sa Hanan ɗan Zakkur, jikan Mattaniya ya yi aiki tare da su, gama su amintattu ne. Aikinsu shi ne su raba wa 'yan'uwansu abin da aka kawo. 14 “Ka tuna da ni, ya Allahna, saboda wannan. Kada ka manta da ayyukan kirki da na yi a Haikalin Allah da kuma na hidimarsa.” 15 A kwanakin nan na ga mutane a Yahuza suna matse ruwan inabi, suna labta wa jakunansu buhunan hatsi, da ruwan inabi, da 'ya'yan inabi, da ɓaure, da kaya iri iri, suna kawo su cikin Urushalima a ran Asabar. Sai na yi musu faɗa a kan sayar da abinci a wannan rana. 16 Mutanen Taya da suke zaune a birnin sukan kawo kifi da kaya iri iri, su sayar wa mutanen Yahuza a Urushalima a ranar Asabar. 17 Sai na tsauta wa manyan mutanen Yahuza, na ce musu, “Wane irin mugun abu ne kuke yi haka, kuna ɓata ranar Asabar? 18 Ashe, ba haka kakanninku suka yi ba, har wannan ya sa Allahnmu ya kawo mana masifa, mu da dukan birnin? Duk da haka kuna ƙara kawo wa Isra'ila hasala saboda kuna ɓata ranar Asabar.” 19 Magariba na yi kafin ranar Asabar, sai na yi umarni a rufe ƙofofin Urushalima, kada a buɗe su sai Asabar ta wuce. Na sa waɗansu barorina a ƙofofin, don kada su bari a shigo da kaya ran Asabar. 20 Sau ɗaya ko sau biyu, 'yan kasuwa da masu sayar da abubuwa iri iri suka kwana a bayan Urushalima. 21 Amma na tsauta musu, na ce, “Me ya sa kuka kwana a bayan garu? Idan kun ƙara yin haka zan kama ku.” Tun daga wannan lokaci ba su ƙara zuwa a ranar Asabar ba. 22 Sai kuma na umarci Lawiyawa su tsarkake kansu, su yi tsaron ƙofofin don a kiyaye ranar Asabar da tsarki. “Ya Allahna, ka tuna da wannan aiki nawa, ka rayar da ni saboda girman madawwamiyar ƙaunarka.” 23 A waɗannan kwanaki kuma na ga waɗansu Yahudawa waɗanda suka auro mata daga Ashdod, da Ammon, da Mowab. 24 Rabin 'ya'yansu suna magana da harshen Ashdod, ko wani harshe dabam, amma ba su iya yin magana da harshen Yahuza ba. 25 Sai na yi musu faɗa na la'ance su, na bugi waɗansu daga cikinsu, na ciccire gashin kansu, na sa su rantse da Allah, cewa ba za su aurar da 'ya'yansu mata ga 'ya'yan maza na bare ba, ko kuma su auro wa 'ya'yansu maza 'yan matan bare, ko su auro wa kansu. 26 Na faɗa musu cewa, “Ba a kan irin wannan ba ne Sulemanu Sarkin Isra'ila ya yi laifi? A al'ummai, ba sarki kamarsa. Allahnsa ya ƙaunace shi, ya sarautar da shi a Isra'ila, duk da haka baren mata suka sa shi ya yi zunubi. 27 Ba za mu yarda da abin da kuke yi ba, har mu aikata wannan mugunta ta rashin aminci ga Allahnmu, da za mu auro baren mata.” 28 Ɗaya daga cikin 'ya'yan Yoyada ɗan Eliyashib, babban firist, surukin Sanballat ne, Bahorone, saboda haka sai na kore shi daga wurina. 29 “Ka tuna da su, ya Allahna don sun ƙazantar da aikin firistoci da alkawarin zama firist da Lawiyawa.” 30 Da haka na tsarkake su daga kowane baƙon abu, na sa firistoci da Lawiyawa cikin aiki, kowa ya kama aikinsa. 31 Na kuma shirya yadda za a tara itace domin yin hadaya a kan kari, da kuma lokacin da za a kawo nunan fari. “Ya Allahna, ka tuna da ni, ka yi mini alheri.”

Esta 1

Sarauniya Bashti ta Raina sarki Ahasurus

1 Ahasurus ya yi sarauta daga Hindu har zuwa Habasha, ya mallaki larduna ɗari da ashirin da bakwai. 2 A waɗannan kwanaki, sarki Ahasurus yake zaune a gadon sarautarsa a Shushan, masarauta. 3 A shekara ta uku ta sarautarsa, sai ya yi biki saboda sarakunansa, da barorinsa, da sarakuna yaƙin Farisa da Mediya, da manyan mutane, da hakiman larduna. 4 Sai ya nuna wadatar mulkinsa, da martabarsa, da darajarsa har kwanaki masu yawa, wato kwana ɗari da tamanin. 5 Bayan da waɗannan kwanaki sun cika, sai sarki ya yi wa manya da ƙanana waɗanda suke a Shushan, wato masarauta, biki, har na kwana bakwai a filin lambun fādar sarki. 6 Aka kewaye wurin da fararen labule da na shunayya na lallausan lilin, aka ɗaure da kirtani na lallausan lilin mai launin shunayya haɗe da zobban azurfa da ginshiƙai na sassaƙaƙƙun duwatsu masu daraja. Akwai gadaje na zinariya da na azurfa a kan daɓen da aka yi da duwatsu masu daraja, masu launi iri iri. 7 Aka ba da sha a finjalai iri iri na zinariya. Aka shayar da su da ruwan inabi irin na sarauta a yalwace bisa ga wadatar sarki. 8 Aka yi ta sha bisa ga doka, ba wanda aka matsa masa, gama sarki ya umarci fādawansa su yi wa kowa yadda yake so. 9 Sarauniya Bashti kuma ta yi wa mata babban biki a fādar sarki Ahasurus. 10 A rana ta bakwai sa'ad da zuciyar sarki take murna saboda ruwan inabi, sai ya umarta bābāninsa guda bakwai, waɗanda suke yi masa hidima, wato Mehuman, da Bizta, da Harbona, da Bigta, da Abagta, da Zetar, da Karkas, 11 su kirawo sarauniya Bashti ta zo wurinsa da kambin sarauta, don ya nuna wa jama'a da shugabanni kyanta, gama ita kyakkyawa ce. 12 Amma sarauniya Bashti ta ƙi zuwa kamar yadda sarki ya umarci bābānin su faɗa mata. Wannan ya sa sarki ya husata ƙwarai. 13 Sarki kuwa ya nemi shawara ga masu hikima waɗanda suka ƙware zamani, gama sarki ya saba da yin haka ga waɗanda suka san doka da shari'a. 14 Su ne mutanen da suke kusa da shi, wato Karshena, da Shetar, da Admata, da Tarshish, da Meres, da Marsena, da Memukan. Su ne sarakuna bakwai na Farisa da Mediya, su ne masu zuwa wurin sarki, su ne kuma na fari a mulkin. 15 Sarki ya ce, “Bisa ga doka, me za a yi da sarauniya Bashti da yake ba ta yi biyayya da umarnin da na aika ta hannun babani ba?” 16 Sai Memukan ya amsa a gaban sarki da sauran sarakai, ya ce, “Ba sarki ne kaɗai sarauniya Bashti ta yi wa laifi ba, amma har dukan sarakai, da sauran jama'a da suke cikin dukan lardunan sarki Ahasurus. 17 Gama za a sanar wa dukan mata abin da sarauniya ta yi, gama abin da ta yi zai sa su raina mazansu, gama za su ce, ‘Sarki Ahasurus ya umarta a kirawo masa sarauniya Bashti, amma ta ki.’ 18 Yau ma matan Farisa da Mediya waɗanda suka ji abin da sarauniya ta yi, haka za su faɗa wa dukan hakimai. Wannan zai kawo raini da fushi mai yawa. 19 Idan sarki ya yarda, bari ya yi doka, a kuma rubuta ta cikin dokokin Farisa da Mediya don kada a sāke ta, cewa Bashti ba za ta ƙara zuwa wurin sarki Ahasurus ba. Bari sarki ya ba da matsayinta na sarauta ga wata wadda ta fi ta. 20 Sa'ad da aka ji dokar sarki, wadda zai yi a dukan babbar ƙasarsa, dukan mata za su girmama mazansu, ƙanana da manya.” 21 Wannan shawara ta gamshi sarki da sauran sarakai, sarki ya yi kamar yadda Memukan ya shawarta. 22 Sai ya aika da takardu zuwa dukan lardunan sarki, kowane lardi da irin rubutunsa, kowaɗanne mutane kuma da harshensu, domin kowane namiji ya zama shugaban gidansa, ya kuma zama mai faɗa a ji.

Esta 2

Esta ta Zama Sarauniya

1 Bayan waɗannan abubuwa, sa'ad da sarki Ahasurus ya huce daga fushinsa, sai ya tuna da abin da Bashti ta yi, da dokar da aka yi a kanta. 2 Sa'an nan barorin sarki waɗanda suke yi masa hidima suka ce masa, “Bari a samo wa sarki 'yan mata, budurwai, kyawawa. 3 Bari kuma sarki ya sa shugabanni a cikin dukan lardunan mulkinsa su tara dukan kyawawan 'yan mata, budurwai, a gidan matan kulle a masarauta a Shushan, ƙarƙashin Hegai bābā na sarki, wanda yake lura da mata. A riƙa ba budurwan man shafawa. 4 Bari sarki ya zaɓi budurwar da ta gamshe shi, ta zama sarauniya maimakon Bashti.” Sarki fa ya ji daɗin wannan shawara, ya kuwa yi haka ɗin. 5 Akwai wani Bayahude a masarauta a Shushan, mai suna Mordekai ɗan Yayir, ɗan Shimai, ɗan Kish mutumin Biliyaminu. 6 An kamo shi a Urushalima tare 'yan zaman talala waɗanda aka kwashe tare da Yekoniya Sarkin Yahuza, wanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kai su zaman talala. 7 Mordekai ne ya goyi Hadassa, wato Esta, 'yar kawunsa, gama ita marainiya ce. Ita kuwa kyakkyawa ce. Sa'ad da iyayenta suka rasu, sai Mordekai ya karɓe ta tankar 'yarsa. 8 Sa'ad da aka yi shelar dokar sarki, aka kuma tattara 'yan mata a masarauta a Shushan, a hannun Hegai, sai aka ɗauko Esta zuwa fādar sarki, aka sa ta a hannun Hegai wanda yake lura da mata. 9 Esta kuwa ta gamshi Hegai, ta kuma sami farin jini a wurinsa, sai nan da nan ya ba ta man shafawa, da rabon abincinta, da zaɓaɓɓun kuyangi guda bakwai daga fādar sarki. Ya kuma kai ta da kuyanginta a wuri mafi kyau na gidan matan kulle. 10 Esta ba ta riga ta bayyana asalin mutanenta, da danginta ba, gama Mordekai ya umarce ta kada ta yi. 11 Kowace rana Mordekai yakan zo shirayin gidan matan kulle don ya san yadda Esta take. 12 Sa'ad da lokacin kowace budurwa ya yi da za ta shiga wurin sarki Ahasurus, bayan da ta riga ta yi wata goma sha biyu na ka'idar yin kwalliyar mata, wato takan shafe jiki da man ƙanshi wata shida, ta kuma shafe jiki da turare da man shafawa wata shida, 13 sa'an nan budurwar za ta shiga wurin sarki, sai a ba ta dukan abin da take bukata ta ɗauko daga gidan matan kullen zuwa fādar sarki. 14 Takan tafi da yamma, ta koma gidan matan kulle na biyu da safe, a hannun Shawashgaz, bābā na sarki, wanda yake lura da ƙwaraƙwarai. Ba za ta ƙara zuwa wurin sarki ba, sai ko ta sami farin jini a wurin sarki sa'an nan a kirawo ta. 15 Sa'ad da lokacin Esta 'yar Abihail, kawun Mordekai, wadda Mordekai ya karɓe ta tankar 'yarsa, ya yi da za ta shiga wurin sarki, ba ta bukaci kome ba, sai dai abin da Hegai, bābā na sarki, wanda yake lura da mata, ya ce. Esta kuwa tana da farin jini a idon duk wanda ya gan ta. 16 Sa'ad da aka kai Esta wurin sarki Ahasurus a fādarsa a wata na goma, wato watan Tebet, a shekara ta bakwai ta sarautarsa, 17 sai sarki ya ƙaunaci Esta fiye da dukan sauran matan. Ta kuwa sami alheri da farin jini a wurinsa fiye da sauran budurwan, saboda haka ya sa kambin sarauta a kanta. Ya naɗa ta sarauniya maimakon Bashti. 18 Sarki kuwa ya yi wa sarakunansa da barorinsa ƙasaitaccen biki saboda Esta. Ya kuma ba larduna hutu, ya ba da kyautai da yawa irin na sarauta.

Mordekai ya Ceci Ran Sarki

19 Sa'ad da aka tara budurwai a karo na biyu, Mordekai yana zaune a ƙofar sarki. 20 Har yanzu dai Esta ba ta bayyana asalin danginta da mutanenta ba, kamar yadda Mordekai ya umarce ta, gama Esta tana yi wa Mordekai biyayya kamar ta yi tun lokacin da yake renonta. 21 A kwanakin nan sa'ad da Mordekai yake zaune a ƙofar sarki, sai babani biyu na sarki, wato Bigtana da Teresh waɗanda suke tsaron ƙofar, suka yi fushi, har suka nema su kashe sarki Ahasurus. 22 Wannan maƙarƙashiya ta sanu ga Mordekai, shi kuwa ya faɗa wa sarauniya Esta. Esta kuma ta faɗa wa sarki da sunan Mordekai. 23 Sa'ad da aka bincika al'amarin aka tarar haka yake. Sai aka rataye mutum biyu ɗin a kan gumagumai. Aka kuma rubuta labarin a littafin tarihi a gaban sarki.

Esta 3

Maƙaƙashiyar Haman don ya Hallaka Yahudawa

1 Bayan waɗannan abubuwa, sai sarki Ahasurus ya gabatar da Haman ɗan Hammedata Ba'agage. Ya f�fita shi bisa dukan sarakunan da suke tare da shi. 2 Dukan barorin sarki waɗanda suke a bakin ƙofar sarki suka rusuna suka yi wa Haman mubaya'a, gama sarki ya umarta a yi masa haka. Amma Mordekai bai rusuna ya yi masa mubaya'a ba. 3 Sai barorin sarki waɗanda suke a bakin ƙofar sarki suka ce wa Mordekai, “Me ya sa ka karya dokar sarki?” 4 Sa'ad da suka yi ta yi masa magana kowace rana, shi kuwa bai kasa kunne gare su ba, sai suka faɗa wa Haman, don su gani ko maganar Mordekai za ta tabbata, gama ya faɗa musu shi Bayahude ne. 5 Sa'ad da Haman ya ga Mordekai bai rusuna ya yi masa mubaya'a ba, sai ya husata. 6 Har ma ya ga a kashe Mordekai kaɗai, wannan bai isa ba. Da yake an faɗa masa asalin Mordekai, sai ya nema ya hallaka dukan Yahudawa, wato kabilar Mordekai, waɗanda suke a dukan mulkin Ahasurus. 7 A watan fari, wato watan Nisan, a shekara ta goma sha biyu ta sarautar sarki Ahasurus, sai suka yi ta jefa Fur, wato kuri'a, a gaban Haman kowace rana da kowane wata har kuri'a ta faɗo a kan watan goma sha biyu, wato watan Adar. 8 Sa'an nan Haman ya ce wa sarki Ahasurus, “Akwai waɗansu mutane da suke warwatse a jama'ar dukan lardunan mulkinka. Dokokinsu sun sha bambam da na sauran mutane, ba su kuma kiyaye dokokin sarki, don haka ba shi da amfani a wurin sarki ya yi ta haƙuri da su. 9 Idan ya gamshi sarki, bari a yi doka a hallaka su, ni kuwa zan ba waɗanda suke tafiyar da aikin sarki, talanti dubu goma (10,000 ) na azurfa, don su sa a baitulmalin sarki.” 10 Sarki kuwa ya zare zobensa na hatimi daga hannunsa ya ba Haman Ba'agage, ɗan Hammedata, maƙiyin Yahudawa. 11 Sa'an nan ya ce masa, “Da kuɗin, da mutanen duk an ba ka, ka yi yadda ka ga dama da su.” 12 Sai aka kirawo magatakardun sarki a rana ta goma sha uku ga watan fari. Bisa ga umarnin Haman aka rubuta doka zuwa ga shugabannin mahukuntai na sarki, da masu mulkin dukan larduna, da sarakunan shugabannin jama'a. Aka rubuta zuwa kowane lardi da irin rubutunsa, da kowaɗanne mutane kuma da harshensu da sunan sarki Ahasurus. Aka hatimce ta da hatimin zoben sarki. 13 Aka ba 'yankada-ta-kwana takardun zuwa dukan lardunan sarki don a hallaka Yahudawa, a karkashe, a ƙarasa su, ƙanana da manya, mata da maza, duk a rana ɗaya, wato ran goma sha uku ga watan goma sha biyu, wato watan Adar, a kuma washe dukiyoyinsu. 14 Sai a ba kowane lardi fassarar dokar, don a yi shelarta ga dukan mutane, su kasance a shirye don ranar. 15 Bisa ga umarnin sarki, sai 'yankada-ta-kwana, suka tafi da sauri. Aka ba da umarni a Shushan, masarauta. Sarki da Haman kuwa suka zauna don su sha, amma birnin Shushan ya ruɗe.

Esta 4

Esta za ta yi Roƙo don Mutanenta

1 Da Mordekai ya ji dukan abin da aka yi, sai ya yage tufafinsa, sa'an nan ya sa rigar makoki, ya zuba toka a kā. Ya fita zuwa tsakiyar birni, yana ta rusa kuka da ƙarfi. 2 Ya tafi kusa da ƙofar sarki, gama ba a yarda wani ya shiga ƙofar sarki da rigar makoki ba. 3 A kowane lardi inda aka kai umarni da dokar sarki, Yahudawa suka yi babban baƙin ciki, da azumi, da kuka, da makoki. Waɗansu da yawa da rigunan makoki a cikin toka suka kwanta. 4 Sa'ad da kuyangin Esta da bābāninta suka tafi suka faɗa mata abin da Mordekai yake yi, sai sarauniya Esta ta damu ƙwarai, ta aika da riguna a sa wa Mordekai, ya tuɓe rigar makokinsa, amma Mordekai ya ƙi, bai yarda ba. 5 Sai Esta ta kirawo Hatak, ɗaya daga cikin bābānin sarki, wanda aka sa ya yi mata hidima, ta aike shi wurin Mordekai, don ya ji abin da ya faru, har ya sa yake yin haka. 6 Hatak kuwa ya tafi wurin Mordekai a dandalin birnin, a gaban ƙofar sarki. 7 Sai Mordekai ya faɗa masa dukan abin da ya faru da shi, da yawan ƙudin da Haman ya ce zai biya a sa a baitulmalin sarki don a hallaka Yahudawa. 8 Mordekai kuma ya ba Hatak takardar dokar da aka yi a Shushan don a hallaka Yahudawa domin ya tafi ya nuna wa Esta ya sanar da ita, ya kuma umarce ta ta tafi wurin sarki don ta roƙi arziki ga sarki saboda mutanenta. 9 Sai Hatak ya tafi, ya faɗa wa Esta abin da Mordekai ya ce. 10 Esta kuma ta yi magana da Hatak sa'an nan ta aike shi da saƙo a wurin Mordekai cewa, 11 “Dukan barorin sarki da mutanen lardunan sarki sun sani duk wanda ya tafi wurin sarki a shirayi na ciki, ba tare da an kira shi ba, to, doka ɗaya ce ke kan mutum, wato kisa, ko mace ko namiji, sai dai wanda sarki ya miƙa wa sandan sarauta na zinariya don ya rayu. Kwana talatin ke nan ba a kira ni in tafi wurin sarki ba.” 12 Hatak ya tafi ya faɗa wa Mordekai abin da Esta ta ce. 13 Sai Mordekai ya ce masa ya je ya faɗa wa Esta haka, “Kada ki yi tsammani za ki tsira a fādar sarki fiye da sauran Yahudawa. 14 Gama idan kin yi shiru a irin wannan lokaci, to, taimako da ceto za su zo wa Yahudawa ta wata hanya dabam, amma ke da gidan iyayenki za ku hallaka. Wa ya sani ko saboda irin wannan lokaci ne kika sami wannan maƙami?” 15 Sa'an nan Esta ta ce masa ya je ya faɗa wa Mordekai cewa, 16 “Ka tattara dukan Yahudawan da suke a Shushan, su yi domin, kada su ci ko su sha dare da rana, har kwana uku. Ni kuma da kuyangina za mu yi hakanan. Sa'an nan zan tafi wurin sarki, ko da yake ba bisa ga doka ba, idan na hallaka, na hallaka ke nan.” 17 Sai Mordekai ya tafi ya yi abin da Esta ta umarce shi.

Esta 5

Esta ta Yi wa Sarki da Haman Liyafa

1 A kan rana ta uku sai Esta ta sa rigunan, ta tafi, ta tsaya a shirayi na ciki na fādar sarki, kusa da ɗakin sarki. Sarki kuwa yana zaune a gadon sarautarsa, a gidan sarautarsa, daura da ƙofar shiga fāda. 2 Sa'ad da ya ga Esta tana tsaye a shirayin, sai ya miƙa mata sandan zinariya na sarauta, gama ta sami kwarjini a wurinsa. Sai Esta ta matsa kusa ta taɓa kan sandan. 3 Sarki ya ce mata, “Mene ne, sarauniya Esta? Me kike so? Za a ba ki, ko rabin mulkina ma.” 4 Sai Esta ta ce, “Idan sarki ya yarda, bari sarki ya zo tare da Haman yau wurin liyafa da na shirya wa sarki.” 5 Sarki kuwa ya ce, “A zo da Haman maza, mu yi abin da Esta take so.” Sai sarki da Haman suka tafi liyafar da Esta ta shirya. 6 Sa'ad da suke shan ruwan inabi, sai sarki ya tambayi Esta, “Mece ce bukatarki? Za a biya miki ko da rabin mulkina ne.” 7 Sai Esta ta ce, “Bukatata, da roƙona ke nan, 8 idan na sami tagomashi a wurin sarki, idan kuma sarki ya yarda ya biya bukatata da roƙona, to, bari sarki da Haman su zo liyafar da zan yi musu, gobe kuwa zan yi abin da sarki ya faɗa.”

Haman ya Yi Shirin Kashe Mordekai

9 Ran nan Haman ya fita da murna da farin ciki, amma da ya ga Mordekai a ƙofar sarki, Mordekai kuwa bai tashi ba, bai kuma yi rawar jiki a gabansa ba, sai ya husata ƙwarai. 10 Duk da haka Haman ya cije, ya tafi gida. Ya aika a kirawo abokansa da matarsa, Zeresh. 11 Ya faɗa musu darajar wadatarsa, da yawan 'ya'yansa, da yawan matsayin da sarki ya girmama shi da su, da yadda sarki ya ciyar da shi gaba fiye da sarakuna da barorin sarki. 12 Ya ƙara da cewa, “Har ma sarauniya Esta ma ba ta yarda kowa ya tafi tare da sarki wurin liyafar da ta shirya ba, sai ni. Gobe ma ta gayyace ni tare da sarki. 13 Duk da haka wannan bai yi mini daɗi ba, muddin Mordekai, Bayahuden nan, yana zaune a ƙofar sarki.” 14 Matarsa, Zeresh kuwa, da abokansa duka suka ce, “Ka sa a shirya gungumen itace mai tsayi kamu hamsin, sa'an nan da safe ka faɗa wa sarki a rataye Mordekai a kai, sa'an nan ka tafi wurin liyafar tare da sarki da murna.” Haman kuwa ya ji daɗin wannan shawara, sai ya sa aka shirya gungumen itacen.

Esta 6

Haman ya Girmama Mordekai Tilas

1 A wannan dare kuwa sarki ya kasa yin barci, sai ya umarta a kawo littafin da aka rubuta al'amuran da suke faruwa don tunawa. Aka kuwa kawo, aka karanta wa sarki. 2 Sai aka tarar an rubuta yadda Mordekai ya gano maƙarƙashiyar Bigtana da Teresh, biyu daga cikin bābāni na sarki, masu tsaron ƙofa, waɗanda suka yi niyya su kashe sarki Ahasurus. 3 Sai sarki ya ce, “To, wace irin daraja ko girma aka ba Mordekai saboda wannan?” Barorin sarki waɗanda suke yi masa hidima suka ce, “Ba a yi masa kome ba.” 4 Sarki kuwa ya ce, “Wane ne yake a shirayi?” Daidai lokacin ne kuwa Haman ya shigo shirayi na fari na fādar sarki, don ya yi magana da sarki a kan a rataye Mordekai a gungumen itace da ya shirya. 5 Barorin sarki suka ce, “Ai, Haman ne yake tsaye a shirayi.” Sai sarki ya ce ya shigo. 6 Da shigowar Haman, sai sarki ya ce masa, “Me za a yi wa mutumin da sarki yake so ya ɗaukaka?” Haman ya yi tunani ya ce a ransa, “Wanene sarki yake so ya ɗaukaka, in banda ni?” 7 Sai Haman ya ce wa sarki, “Abin da za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka ka nan. 8 Bari a kawo rigunan sarautar da sarki ya taɓa sawa, da dokin da sarki ya taɓa hawa, a kuma sa kambin sarauta a kansa. 9 Sa'an nan a ba ɗaya daga cikin manyan sarakunanka rigunan ya sa wa wanda kake so ka ɗaukaka, ya kuma hawa da shi kan dokin, sa'an nan ya zagaya da shi a dandalin birni, yana shelar a gabansa yana cewa, ‘Haka za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka.’ ” 10 Sai sarki ya ce wa Haman, “Yi maza, ka ɗauki rigunan da dokin, ka tafi wurin Mordekai, Bayahuden nan, wanda yakan zauna a ƙofar sarki ka yi masa kamar yadda ka faɗa. Kada ka kasa yin kome daga cikin abin da ka faɗa.” 11 Haman kuwa ya ɗauki rigunan da dokin. Ya sa wa Mordekai riguna, ya hawar da shi kan dokin, ya zagaya da shi a dandalin birnin, yana cewa, “Haka za a yi wa wanda sarki yake so ya ɗaukaka.” 12 Sa'an nan Mordekai ya koma ƙofar sarki, Haman kuwa ya gaggauta zuwa gidansa, yana baƙin ciki, kunya ta rufe shi. 13 Da ya koma gida, sai ya faɗa wa Zeresh, matarsa, da dukan abokansa, duk abin da ya same shi. Sai mutanensa masu hikima da Zeresh, matarsa, suka ce masa, “Idan Mordekai, wanda ka fara faɗuwa a gabansa, in dai daga zuriyar Yahudawa yake, to, ba za ka yi nasara a kansa ba, amma hakika za ka fāɗi a gabansa.” 14 Suna magana ke nan, sai bābānin sarki suka iso, suka tafi da Haman a gaggauce zuwa wurin liyafar da Esta ta shirya.

Esta 7

Haman ya Fāɗa a Ramin da ya Haƙa

1 Sarki da Haman kuwa suka tafi wurin Esta, gun liyafa. 2 A rana ta biyu, sa'ad da suke shan ruwan inabi, sai sarki ya sāke ce wa Esta, “Mece ce bukatarki, sarauniya Esta? Za a yi miki. Mene ne roƙonki? Za a ba ki, ko da rabin mulkina ne.” 3 Sai Esta ta ce, “Ya sarki, idan na sami tagomashi a wurinka, idan kuma sarki ya yarda, bukatata ita ce a bar ni da raina, roƙona kuma shi ne a bar mutanena. 4 Gama an sayar da mu, ni da mutanena, don a hallaka mu, a karkashe, a ƙarasa mu. Da a ce an sayar da mu mu zama bayi, mata da maza, da na yi shiru, gama ba za a kwatanta wahalarmu da hasarar da sarki zai sha ba.” 5 Sarki Ahasurus ya ce wa sarauniya Esta, “Wanene shi, ina yake, wanda zai yi karambanin yin wannan?” 6 Esta ta ce, “Haman ne, magabci, maƙiyi, mugu!” Sai tsoro ya kama Haman a gaban sarki da sarauniya. 7 Sarki kuwa ya tashi da fushi, ya tafi lambun fāda. Amma Haman ya tsaya don ya roƙi sarauniya Esta ta ceci ransa, gama ya ga sarki yana niyyar hukunta shi. 8 Da sarki ya koma daga lambun fāda zuwa inda suke shan ruwan inabi, sai ga Haman ya fāɗi a kan shimfiɗar da Esta take zaune. Sai sarki ya ce, “Har ma zai ci mutuncin sarauniya a gabana, a gidana?” Da dai sarki ya faɗi haka, sai bābāni suka cafe Haman. 9 Sa'an nan Harbona, ɗaya daga cikin bābānin da suke yi wa sarki hidima ya ce, “Ga shi ma, Haman ya riga ya shirya gungumen itace a gidansa, mai tsayi kamu hamsin, inda zai rataye Mordekai wanda ya ceci sarki ta wurin maganarsa.” Sai sarki ya ce, “A rataye Haman a gungumen.” 10 Aka kuwa rataye Haman a gungumen itace da ya shirya zai rataye Mordekai. Sa'an nan sarki ya huce.

Esta 8

An Ba Yahudawa Izini kada su Miƙa Wuya

1 A wannan rana sai sarki Ahasurus ya ba Esta gidan Haman, maƙiyin Yahudawa, da duk dukiyar Haman. Mordekai kuwa ya zo gaban sarki, gama Esta ta bayyana yadda yake a gare ta. 2 Sa'an nan sarki ya ɗauki zobensa na hatimi, wanda ya karɓe a wurin Haman, ya ba Mordekai. Esta kuma ta ba Mordekai gidan Haman. 3 Sa'an nan kuma Esta ta faɗi a wajen ƙafafun sarki, ta roƙe shi da hawaye ya kawar da mugun shirin da Haman Ba'agage ya shirya wa Yahudawa. 4 Sai sarki ya miƙo wa Esta sandan sarauta na zinariya. 5 Esta kuwa ta miƙe tsaye a gaban sarki, ta ce, “Idan sarki ya yarda, idan kuma na sami tagomashi a wurinka, idan ya yi wa sarki kyau, idan kuma sarki yana jin daɗina, bari a yi rubutu a soke wasiƙun da Haman Ba'agage ɗan Hammedata ya rubuta don a hallaka Yahudawan da suke cikin dukan lardunan sarki. 6 Gama ƙaƙa zan iya daurewa da ganin masifa da hallaka na mutanena da dangina?” 7 Sai sarki Ahasurus ya ce wa sarauniya da Mordekai, Bayahude, “Ga shi, na riga na ba Esta gidan Haman, an kuma riga an rataye shi a bisa gungume domin ya so ya taɓa Yahudawa. 8 Sai ku rubuta doka yadda kuke so da sunan sarki zuwa ga Yahudawa. Ku hatimce ta da hatimin zoben sarki, gama dokar da aka rubuta da sunan sarki, aka kuma hatimce ta da hatimin zoben sarki, ba za a iya a soke ta ba.” 9 A wannan lokaci aka kirawo magatakardun sarki ran ashirin da uku ga watan uku, wato watan Siwan. Bisa ga umarnin Mordekai aka rubuta doka zuwa ga Yahudawa, da shugabannin mahukunta, da masu mulki, da shugabannin larduna, tun daga Hindu har zuwa Habasha, wato lardi ɗari da ashirin da bakwai. Aka rubuta wa kowane lardi da irin rubutunsa, kowaɗanne mutane kuma da irin harshensu, zuwa ga Yahudawa kuma da irin rubutunsu da harshensu. 10 An yi rubutu da sunan sarki Ahasurus, aka kuma hatimce shi da hatimin zoben sarki. Aka aika da wasiƙun ta hannun 'yan-kada-ta-kwana, waɗanda suka hau dawakai masu zafin gudu da akan mora a aikin sarki. 11 A wasiƙun, sarki ya yardar wa Yahudawan da suke a kowane birni su taru, su kāre rayukansu, su kuma hallaka kowace rundunar mutane da kowane lardi da zai tasar musu, da 'ya'yansu, da matansu, su karkashe su, su rurrushe su, su kuma washe dukiyarsu. 12 Za a yi wannan a dukan lardunan sarki Ahasurus ran goma sha uku ga watan goma sha biyu, wato watan Adar. 13 Sai a ba kowane lardi fassarar dokar, don a yi shelarta ga dukan mutane, Yahudawa kuwa su yi shiri saboda wannan rana, domin su ɗau fansa a kan maƙiyansu. 14 Sai 'yan-kada-ta-kwana suka hau dawakai masu zafin gudu waɗanda akan mora a aikin sarki, suka tafi da gaggawa don su iyar da dokar sarki. Aka yi shelar dokar a Shushan, masarauta. 15 Mordekai kuwa ya fita a gaban sarki da rigunan sarauta, masu launin shuɗi, da fari, da babban kambi na zinariya, da alkyabba ta lilin mai launin shunayya. Aka yi sowa don murna a birnin Shushan. 16 Yahudawa suka sami haske, da farin ciki, da murna, da daraja. 17 A kowane lardi da birni inda maganar sarki da dokarsa suka kai, Yahudawa suka yi farin ciki da murna, suka yi biki, suka yi hutu. Mutane da yawa daga cikin mutanen ƙasar suka zama Yahudawa, gama tsoron Yahudawa ya kama su.

Esta 9

Yahudawa sun Hallaka Maƙiyansu

1 A kan rana ta goma sha uku ga watan sha biyu, wato watan Adar, a ranar da za a aikata maganar sarki da dokarsa, wato a ranar da maƙiyan Yahudawa za su fāɗa musu, sai ranar ta zama ranar da Yahudawa ne za su tasar wa maƙiyansu. 2 Sai Yahudawa suka taru a biranensu a dukan lardunan sarki Ahasurus, don su tasar wa waɗanda suke so su yi musu ɓarna. Ba wanda ya tasar musu gama tsoronsu ya kama mutane. 3 Dukan sarakunan larduna, da hakimai, da masu mulki, da ma'aikatan sarki, suka taimaki Yahudawa, gama tsoron Mordekai ya kama su. 4 Gama Mordekai ya zama babban mutum a gidan sarki, ya kuma yi suna a dukan larduna, gama ya yi ta ƙasaita gaba gaba. 5 Yahudawa kuwa suka kashe dukan maƙiyansu da takobi. Suka hallaka maƙiyansu yadda suke so. 6 A Shushan, masarauta kanta, Yahudawa suka hallaka mutum ɗari biyar. 7 Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata, 8 da Forata, da Adaliya, da Aridata, 9 da Farmashta, da Arisai, da Aridai, da Waizata. 10 Su ne 'ya'ya goma na Haman, ɗan Hammedata, maƙiyin Yahudawa, amma ba su washe dukiyarsu ba. 11 A ranar ce aka faɗa wa sarki yawan mutanen da aka kashe a Shushan, masarauta. 12 Sai sarki ya ce wa sarauniya Esta, “A Shushan, masarauta, Yahudawa sun kashe mutum ɗari biyar da kuma 'ya'yan Haman guda goma. Mene ne suka yi a sauran lardunan sarki? Mece ce kuma bukatarki? Za a yi miki. Mene ne kuma roƙonki? Za a ba ki.” 13 Esta ta ce, “Idan sarki ya yarda, bari a yardar wa Yahudawan da suke Shushan su yi haka gobe, kamar yadda suka yi yau. Bari a rataye gawawwakin 'ya'yan Haman guda goma a bisa gumagumai.” 14 Sarki kuwa ya ce a yi haka ɗin. Sai aka yi doka a Shushan, aka kuwa rataye gawawwakin 'ya'yan Haman guda goma. 15 Yahudawan da suke Shushan kuwa suka taru a rana ta goma sha huɗu ga watan Adar, suka kashe mutum ɗari uku a Shushan, amma ba su washe dukiyarsu ba.

Bikin Furim

16 Yahudawan da suke cikin lardunan sarki kuma suka taru, suka kāre rayukansu, suka ƙwaci kansu daga maƙiyansu. Suka kashe mutum dubu saba'in da dubu biyar (75,000 ) daga cikin maƙiyansu, amma ba su washe dukiyarsu ba. 17 A rana ta goma sha uku ga watan Adar ne suka aikata wannan abu. A rana ta goma sha huɗu suka huta, suka mai da ranar ta zama ta biki, da farin ciki. 18 Amma Yahudawan da suke a Shushan suka taru a rana ta goma sha uku, da rana ta goma sha huɗu, suka huta ran goma sha biyar, suna biki da murna. 19 Yahudawan da suke zaune a ƙauyuka, da karkara, suka mai da rana ta goma sha huɗu ga watan Adar, ranar farin ciki, da biki, da hutu, da ranar aika wa juna da abinci. 20 Mordekai kuwa ya rubuta abubuwan nan da suka faru, ya aika da takardun zuwa ga dukan Yahudawa waɗanda suke a dukan lardunan sarki Ahasurus, na kusa da na nesa. 21 Ya yi musu umarni, cewa su kiyaye rana ta goma sha huɗu da ta goma sha biyar na watan Adar a kowace shekara. 22 Su ne ranakun da Yahudawa suka sami kuɓuta daga abokan gābansu. A wannan wata ne kuma baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama hutawa. Sai su maishe su ranakun biki da farin ciki, da aika wa juna da abinci, da kuma ba da kyautai ga matalauta. 23 Sai Yahudawa suka ɗauka su yi kamar yadda suka fara, da kuma yadda Mordekai ya rubuta musu. 24 Haman Ba'agage, ɗan Hammedata, maƙiyin dukan Yahudawa, ya ƙulla wa Yahudawa makirci don ya hallaka su. Ya jefa Fur, wato kuri'a don ya hallaka su. 25 Amma da Esta ta zo wurin sarki, sai sarki ya ba da umarni a rubuce, cewa mugun makircin nan da Haman ya shirya wa Yahudawa ya koma a kansa. Shi da 'ya'yansa maza aka rataye su a bisa gumagumai. 26 Saboda haka suka sa wa ranakun nan suna Furim, wanda asalinsu daga Fur ne, wato kuri'a. Domin haka dukan abin da aka rubuta a wannan takarda, da abin da suka gani a wannan al'amari, da abin da ya same su, 27 sai Yahudawa suka ga wajibi ne a gare su, da zuriyarsu, da waɗanda suka tare da su, su kiyaye ranaku biyu ɗin nan ba fashi kowace shekara, bisa ga abin da aka rubuta. 28 Za a tuna da ranakun nan, a kiyaye su a kowane zamani, da kowane iyali, da lardi, da birni. Ranakun Furim ɗin nan, Yahudawa ba za su daina tunawa da su ba, zuriyarsu kuma ba za ta daina tunawa da su ba. 29 Sa'an nan sarauniya Esta 'yar Abihail, da Mordekai Bayahude, ta ba da cikakken iko a rubuce don ta tabbatar da takardan nan ta biyu game da Furim. 30 Aka aika da takardun zuwa ga dukan Yahudawa da suke a lardi ɗari da ashirin da bakwai na mulkin Ahasurus, da kalmomin salama da na gaskiya, 31 da cewa a kiyaye ranakun Furim a lokacinsu, kamar yadda Mordekai Bayahude, da sarauniya Esta, suka umarci Yahudawa, kamar yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu lokacin tunawa da azuminsu da baƙin cikinsu. 32 Da umarnin Esta aka kafa ka'idodin Furim, aka kuwa rubuta su a littafi.

Esta 10

Ƙasaitar Mordekai

1 Sarki Ahasurus ya fasa haraji a ƙasar tudu da ta bakin teku. 2 An rubuta a littafin tarihin sarakunan Mediya da na Farisa, dukan ayyukan iko, da isa, da cikakken labarin darajar Mordekai, wadda sarki ya ba shi. 3 Gama sarki Ahasurus kaɗai yake gaba da Mordekai Bayahude, Mordekai kuma yana da girma a wurin Yahudawa, yana kuma da farin jini a wurin taron jama'ar 'yan'uwansa, gama ya nemi lafiyar jama'arsa, yana kuma maganar alheri ga dukan mutane.

Ayuba 1

Shaiɗan ya Jarraba Ayuba

1 Akwai wani mutum a ƙasar Uz, mai suna Ayuba, amintacce ne, mai tsoron Allah. Shi mutumin kirki ne, natsattse, yana ƙin aikata kowace irin mugunta. 2 Yana da 'ya'ya bakwai maza, uku mata. 3 Yana da tumaki dubu bakwai (7,000 ), da raƙuma dubu uku (3,000 ), da shanu dubu guda (1,000 ), da jakuna ɗari biyar. Yana kuma da barori masu yawan gaske, don haka ya fi kowa a ƙasar gabas arziki nesa. 4 'Ya'yansa maza sukan yi liyafa bi da bi a gidajen junansu, inda su duka sukan taru koyaushe, sukan gayyaci 'yan'uwan nan nasu mata su halarci liyafar. 5 A kowane lokacin da aka gama da liyafar, Ayuba yakan tashi da sassafe, kashegarin liyafar, ya miƙa hadayu don ya tsarkake 'ya'yansa. Haka yake yi kullum, don yana zaton mai yiwuwa ne ɗaya daga cikin 'ya'yan ya yi zunubi, ya saɓi Allah a ɓoye. 6 Sa'ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta yi, Shaiɗan ma ya zo tare da su. 7 Sai Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Kai fa me kake yi?” Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, a ko'ina a duniya.” 8 Ubangiji ya ce masa, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta.” 9 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “A banza Ayuba yake yi maka sujada? 10 Ai, don ka kiyaye shi ne, shi da iyalinsa, da dukan abin da yake da shi. Ka kuma sa wa duk abin da yake yi albarka, ka kuwa ba shi shanun da suka isa su cika dukan ƙasar nan. 11 Amma da a ce za ka raba shi da dukan abin hannunsa, to, da zai fito fili ya zage ka ƙiri ƙiri.” 12 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “To, shi ke nan, dukan abin hannunsa yana cikin ikonka, amma shi kansa kada ka cuce shi.” Sai Shaiɗan ya tafi.

An Hallaka 'Ya'yan Ayuba da Dukiyarsa

13 Wata rana 'ya'yan Ayuba suna shagali a gidan wansu, 14 sai ga jakada ya zo wurin Ayuba a guje, ya ce, “Muna huɗar gona da shanu, jakuna suna kiwo a makiyayar da take kusa da wurin, 15 sai Sabiyawa suka auka musu farat ɗaya, suka sace su duka, suka kuma karkashe duk barorinka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.” 16 Kafin ya gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Tsawa ta kashe tumaki da makiyayansu duka, ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.” 17 Kafin ya gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Ƙungiyoyin mahara uku na Kaldiyawa suka auka mana, suka kwashe raƙuma duka, suka kuma karkashe barorinka duka, sai ni kaɗai na tsira, na zo in faɗa maka.” 18 Kafin ya gama magana, sai wani bara ya zo, ya ce, “Sa'ad da 'ya'yanka suke liyafa a gidan wansu, 19 sai hadiri ya taso daga hamada, ya rushe gidan, ya kashe 'ya'yanka duka, ni kaɗai na tsira na zo in faɗa maka.” 20 Sai Ayuba ya tashi, ya kyakkece tufafinsa don baƙin ciki. Ya aske kansa, ya fāɗi ƙasa, 21 ya ce, “Ban shigo duniya da kome ba, ba kuma zan fita cikinta da kome ba. Ubangiji ya bayar, shi ne kuma ya karɓe, yabo ya tabbata ga sunansa.” 22 Ko da yake waɗannan al'amura duka sun faru, duk da haka Ayuba bai sa wa Allah laifi ba.

Ayuba 2

Shaiɗan ya Sāke Jarraba Ayuba

1 Sa'ad da ranar da talikan sama masu rai sukan hallara gaban Ubangiji ta sāke yi, Shaiɗan shi ma ya zo tare da su. 2 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ina ka fito?” Sai Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Ina ta kaiwa da kawowa ne, ko'ina a duniya.” 3 Ubangiji ya tambaye shi, ya ce, “Ko ka lura da bawana Ayuba? Ba wani mutumin kirki, mai aminci, kamarsa a duniya. Yana yi mini sujada, natsattse ne, yana ƙin aikata kowace irin mugunta. Kai ka sa na yardar maka ka far masa, ba tare da wani dalili ba. Amma duk da haka Ayuba yana nan da amincinsa kamar yadda yake.” 4 Shaiɗan ya amsa, ya ce, “Mutum ya iya rabuwa da dukan abin da yake da shi don ya ceci ransa. 5 Amma yanzu da a ce za ka taɓa lafiyar jikinsa, da sai ya fito fili ya zage ka.” 6 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Shi ke nan, yana cikin ikonka, amma fa, kada ka kashe shi.” 7 Sa'an nan Shaiɗan ya rabu da Ubangiji, ya je ya sa ƙuraje su fito ko'ina a jikin Ayuba. 8 Ayuba ya je ya zauna kusa da juji ya ɗauki tsingaro ya yi ta sosa ƙurajen. 9 Sai matarsa ta ce masa, “Har yanzu kana da amincin nan naka? Don me ba za ka zagi Allah ka mutu ba?” 10 Ayuba ya amsa, ya ce mata, “Wace irin maganar gāɓanci ce haka? Lokacin da Allah ya aiko mana da alheri, mukan yi na'am da shi, to, me zai sa sa'ad da ya aiko mana da wahala za mu yi gunaguni?” Cikin dukan wahalar da Ayuba ya sha, bai sa wa Allah laifi ba.

Abokan Ayuba sun Zo

11 Sa'ad da uku daga cikin abokan Ayuba, wato Elifaz daga birnin Teman, da Bildad daga ƙasar Shuwa, da Zofar daga ƙasar Na'ama, suka ji labarin irin yawan wahalar da Ayuba yake sha, sai suka kama hanya suka tafi su ziyarce shi, su ta'azantar da shi. 12 Suka hango Ayuba tun daga nesa, amma ba su gane shi ba. Da suka gane shi sai suka fara kuka da murya mai ƙarfi. Suka kyakkece tufafinsu saboda baƙin ciki, suka ɗibi ƙura suka watsa a kawunansu. 13 Sa'an nan suka zauna a ƙasa tare da shi, har kwana bakwai, amma ba wanda ya ce uffan, saboda ganin irin yawan wahalar da yake sha.

Ayuba 3

Ayuba ya Kai Kuka ga Allah

1 Ayuba ya yi magana ya la'anci ranar da aka haife shi. 2 Ya ce, “Ya Ubangiji, ka la'anci ranar nan da aka haife ni. 3 Ka la'anci daren nan da aka yi cikina. 4 Ka mai da ranar nan ta zama duhu, ya Allah. Kada a ƙara tunawa da wannan rana, Kada haske ya ƙara haskakata. 5 Ka sa ta zama ranar duhu baƙi ƙirin. Ka rufe ta da gizagizai, kada hasken rana ya haskaka ta. 6 Ka shafe wannan dare daga cikin shekara, Kada kuma a ƙara lasafta shi. 7 Ka sa daren ya zama marar amfani, daren baƙin ciki. 8 Ka faɗa wa masu sihiri su la'anci wannan rana, Su waɗanda suke umartar dodon ruwa. 9 Ka hana gamzaki haskakawa, Kada ka bar daren nan ya sa zuciya ga wayewar gari, 10 Ka la'anci daren nan da aka haife ni, Da ya jefa ni a baƙin ciki da wahala. 11 “Da ma na mutu tun a cikin cikin uwata, Ko kuwa da haihuwata in mutu. 12 Me ma ya sa uwata ta rungume ni a ƙirjinta, Ta shayar da ni kuma da mamanta? 13 Da a ce na mutu a lokacin, da yanzu ina huce, 14 Da ina ta barcina kamar sarakuna da masu mulki Waɗanda suka sāke gina fādodi na dā, 15 Da ina ta sharar barcina kamar shugabanni Waɗanda suka cika gidajensu da zinariya da azurfa, 16 In yi ta sharar barci kamar jariran da aka haifa matattu. 17 Mugaye za su daina muguntarsu a kabari, Ma'aikatan da suka gaji da aiki su ma za su huta, 18 Har 'yan sarƙa ma za su ji daɗin salama, Su huta daga tsautawa da umarnai masu tsanani. 19 Kowa da kowa yana wurin, babba da ƙarami duk ɗaya ne, Bayi ma sun sami 'yanci. 20 “Me ya sa ake barin mutane su yi ta zama cikin damuwa? Me ya sa ake ba da haske ga waɗanda suke baƙin ciki? 21 Sun jira mutuwa, amma ta ƙi samuwa, Sun fi son kabari da kowace irin dukiya. 22 Ba su da farin ciki, sai sun mutu an binne su tukuna. 23 Allah ya ɓoye musu sanin abin da zai faru nan gaba, Ya kalmashe su kowane gefe. 24 A maimakon cin abinci, sai baƙin ciki nake yi, Ba kuma zan daina yin nishi ba, 25 Dukan abin da nake jin tsoro ko fargaba ya faru. 26 Ba ni da salama, ba ni da hutawa, Wahala ba za ta taɓa ƙarewa ba.”

Ayuba 4

Elifaz ya Tsauta wa Ayuba

1 Elifaz ya yi magana. 2 “Ayuba, za ka ji haushi in na yi magana? Ba zan iya kannewa, in yi shiru ba. 3 Ka koya wa mutane da yawa, Ka kuma ƙarfafa hannuwan marasa ƙarfi. 4 Idan wani ya yi tuntuɓe, Ya gaji, ya rasa ƙarfi, Kalmominka suka ƙarfafa zuciyarsa, Har ya iya tsayawa kyam. 5 Yanzu naka lokacin wahala ya zo, Kai kuwa ka rikice, ka kasa ɗaurewa, 6 Kana yi wa Allah sujada, Ba wani laifi a zamanka, Ya kamata ka amince ka sa zuciya. 7 “Yanzu fa sai ka yi tunani. Ka faɗi bala'i ɗaya wanda ya taɓa fāɗa wa adalin mutum. 8 Na taɓa ganin mutane suna huɗe gonar mugunta, Suna shuka mugunta, Suka kuwa girbe mugunta. 9 A cikin fushinsa Allah yakan hallaka su kamar hadiri. 10 Mugaye sukan yi ruri suna gurnani kamar zakoki, Amma Allah yakan sa su yi tsit, Ya kakkarya haƙoransu. 11 Kamar zakoki da ba su da abin da za su kashe su ci, Hakanan za su mutu, 'ya'yansu kuwa su warwatse duka. 12 “Wata rana wani saƙo ya zo a hankali, Har da ƙyar nake iya ji, 13 Kamar wani irin mafarki mai razanarwa yake, Wanda ya hana ni jin daɗin barcina. 14 Na yi rawar jiki ina makyarkyata, Duk jikina yana ta ɓare-ɓare don tsoro. 15 Wata iska marar ƙarfi ta taɓa fuskata, Sai fatar jikina ta yanƙwane saboda fargaba. 16 Na ga wani abu can yana tsaye, Na zura ido, amma ban san kowane irin abu ba ne, Ina cikin wannan hali sai na ji murya, 17 Ta ce, ‘Mutum yana iya zama adali a gaban Allah? Akwai kuma wanda yake mai tsarki a gaban Mahaliccinsa? 18 Allah ba ya amince wa barorinsa na cikin sammai, Yakan sami laifi a wurin mala'ikunsa. 19 Ta ƙaƙa zai amince da talikinsa wanda aka yi da ƙasa, Abin da yake na ƙura, ana kuwa iya murƙushe shi kamar asu. 20 Mai yiwuwa ne mutum yana raye da safe Amma ya mutu ba a sani ba kafin maraice. 21 Duk abin da ya mallaka an ɗauke, Duk da haka ya mutu cikin rashin hikima.’ ”

Ayuba 5

1 “Ka yi kira, ya Ayuba, ka gani, ko wani zai amsa! Akwai wani mala'ika da za ka juya zuwa gare shi? 2 Ba shi da amfani ka dami kanka Har ka mutu, saboda tsarguwa, gama wannan wawanci ne, Da aikin rashin hankali. 3 Na ga waɗansu wawaye waɗanda ake gani kamar suna zaune lafiya, Amma nan da nan sai na la'anci gidajensu. 4 Ko kaɗan, 'ya'yansu maza ba za su taɓa zama lafiya ba. Ba wanda zai tsaya musu a ɗakin shari'a. 5 Mayunwata za su ci amfanin gonar wawa, Har da hatsin da yake girma cikin ƙayayuwa, Waɗanda suke jin ƙishirwa za su ji ƙyashin dukiyarsa. 6 Zunubi ba ya tsirowa daga ƙasa, Haka ma wahala ba ta tsirowa daga ƙasa. 7 Ai, an haifi mutum domin wahala ne, Tabbatacce ne kamar yadda tartsatsin wuta yake tashi. 8 “In da ni ne kai, da sai in juya wurin Allah, In kai ƙarata a wurinsa. 9 Ba za mu iya fahimtar manyan abubuwa da yake yi ba, Al'ajabansa kuwa ba su da iyaka. 10 Yakan aiko da ruwan sama, Ya shayar da gonaki. 11 I, Allah ne yake ɗaukaka masu tawali'u, Shi yake kuɓutar da dukan waɗanda suke makoki. 12 Yakan birkitar da shirye-shiryen masu wayo. 13 Yakan sa wa masu wayo tarko cikin dabarunsu, Har ba za su yi nasara a dukan abin da suke yi ba. 14 Da rana sukan yi karo da duhu, Ko da tsakar rana ma lalube suke kamar ana duhu. 15 Amma Allah yakan ceci matalauta daga mutuwa, Yakan kuma ceci masu bukata daga zalunci. 16 Yakan sa matalauta su sa zuciya, Ya sa mugaye su yi shiru. 17 “Mai farin ciki ne mutumin da Allah ya hora, Kada ka tsargu sa'ad da ya tsauta maka. 18 Allah yakan yi maganin raunin da ya yi maka, Ciwon da ya ji maka da hannunsa, Da hannunsa yakan warkar. 19 Yakan tsare ka daga cuta sau shida har sau bakwai, Ba muguntar da za ta taɓa ka. 20 Yakan kiyaye ka da rai a lokacin yunwa, A yaƙi kuma yakan tsare ka daga mutuwa. 21 Allah yakan kuɓutar da kai daga ƙarairayi da ɓata suna, Yakan cece ka daga hallaka. 22 Aikin kama-karya da yunwa za su zama abin dariya a gare ka, Ba kuwa za ka ji tsoron namomin jeji ba. 23 Ba za a sami duwatsu a gonakin da kake nomawa ba, Mugayen namomin jeji ba za su far maka ba. 24 Sa'an nan za ka zauna lafiya a alfarwanka, A sa'ad da ka dubi tumakinka, za ka tarar suna nan lafiya. 25 'Ya'yanka za su yi yawa kamar ciyawa, Kamar yadda alkama take a lokacin kakarta. 26 Haka kai ma za ka rayu, har ka tsufa da kyakkyawan tsufa. 27 Kai, Ayuba, mun koyi wannan don mun daɗe muna nazari, Gaskiya ce, don haka ka yarda da wannan.”

Ayuba 6

Ayuba ya Zargi Abokansa

1 Ayuba ya amsa. 2 “In da za a auna wahalata da ɓacin raina da ma'auni, 3 Da sun fi yashin teku nauyi. Kada ka yi mamaki da maganganun da nake yi. 4 Allah Maɗaukaki ya harbe ni da kibau, Dafinsu kuwa ya ratsa jikina. Allah ya jera mini abubuwa masu banrazana. 5 “Idan jaki ya sami ciyawar ci, muradinsa ya biya, In ka ji saniya ta yi shiru, tana cin ingirici ne. 6 Amma wane ne zai iya cin abinci ba gishiri? Akwai daɗin ɗanɗano ga farin ruwan ƙwai? 7 Ba na jin marmarin cin abinci irin haka, Kowane irin abu da na ci yakan sa mini cuta. 8 “Me ya sa Allah ya ƙi ba ni abin da nake roƙo? Me ya sa ya ƙi yin abin da nake so? 9 Da ma ya ci gaba kawai ya kashe ni, Ko ya sake ikonsa ya datse ni! 10 Da na san zai yi haka, da sai in yi tsalle don murna, Da ba zan kula da tsananin azabar da nake ciki ba. Ba taɓa yin gāba da umarnan Allah ba. 11 Wane ƙarfi ne nake da shi na rayuwa? Wane sa zuciya kuma nake da ita, tun da na tabbata mutuwa zan yi? 12 Da dutse aka yi ni? Ko da tagulla aka yi jikina? 13 Ba ni da sauran ƙarfi da zan ceci kaina, Ba inda zan juya in nemi taimako. 14 “A cikin irin wannan wahala Ina bukatar amintattun abokai, Ko da na rabu da Allah, ko 'ina tare da shi. 15 Amma ku abokaina, kun ruɗe ni, Kamar rafi wanda yakan ƙafe da rani. 16-17 Rafin yana cike da iska mai laima da ƙanƙara, Amma lokacin zafi sai su ɓace, Kwacciyar rafin, sai ta bushe ba kome. 18 Ayari sukan ɓata garin neman ruwa, Su yi ta gilo, har su marmace a hamada. 19 Ayari daga Sheba da Tema suka yi ta nema, 20 Amma sa zuciyarsu ta ƙare a gefen busassun rafuffuka, 21 Kamar rafuffukan nan kuke a gare ni, Kun ga abin da ya same ni, kun gigita. 22 Na roƙe ku ku ba ni kyauta ne? Ko kuwa na roƙe ku ku ba wani rashawa domina? 23 Ko kuma na roƙe ku ku cece ni daga maƙiyi ko azzalumi ne? 24 “To, sai ku koya mini, ku bayyana mini laifofina, Zan yi shiru in kasa kunne gare ku. 25 Kila muhawara mai ma'ana ta rinjaye ni, Amma yanzu duk maganar shirme kuke yi. 26 Kuna so ku amsa maganganuna? Don me? Mutumin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi, Ba wata maganar da zai yi in ba shirme ba. 27 Kukan jefa wa bayi da marayu kuri'a, Kukan arzuta kanku daga abokanku na kurkusa. 28 Ku dubi fuskata, Lalle ba zan faɗi ƙarya ba. 29 Kai, kun zaƙe, ku daina aikata rashin adalci, Kada ku sa mini laifi, nake da gaskiya. 30 Amma duk da haka kuna tsammani ƙarya nake yi. Kuna tsammani ba zan iya rarrabe tsakanin gaskiya da ƙarya ba.”

Ayuba 7

Ayuba ya Damu da Abin da Allah ya Yi

1 “Kamar kamen soja na tilas, Haka zaman 'yan adam take, Kamar zaman mai aikin bauta. 2 Kamar bawa ne wanda yake sa zuciya ga inuwa mai sanyi, Kamar ma'aikaci wanda yake sa zuciya ga lokacin biya. 3 Wata da watanni ina ta aikin banza, Kowane dare ɓacin rai yake kawo mini. 4 Sa'ad da na kwanta barci, sai daren ya daɗa tsawo In yi ta jujjuyawa duk dare, in ƙosa gari ya waye. 5 Jikina cike yake da tsutsotsi, Ƙuraje duka sun rufe shi, Daga miyakuna mugunya tana ta zuba. 6 Kwanakina sun wuce ba sa zuciya, Sun wuce da sauri kamar ƙoshiyar saƙa. 7 “Ka tuna, ya Ubangiji, raina iska ne kawai, Farin cikina ya riga ya ƙare. 8 Kuna ganina yanzu, amma ba za ku sāke ganina ba. Idan kuka neme ni, za ku tarar ba na nan. 9 Kamar girgijen da yake bajewa ya tafi, Hakanan mutum yake mutuwa. 10 Ba kuwa zai ƙara komowa ba, Mutanen da suka san shi, duka za su manta da shi. 11 A'a, ko kaɗan ba zan yi shiru ba! Haushi nake ji, zuciyata ta ɓaci, Dole ne in yi magana. 12 “Ya Ubangiji, don me ka sa ni a waƙafi? Kana tsammani ni dodon ruwa ne? 13 Na kwanta ina ƙoƙari in huta, Ina neman taimako don azabar da nake sha. 14 Amma kai kana firgita ni da mafarkai, Kana aiko mini da wahayi da ganegane, 15 Har nakan fi so a rataye ni, Gara in mutu da in rayu a wannan hali. 16 Na fid da zuciya. Na gaji da rayuwa. Ku rabu da ni. Rayuwa ba ta da wata ma'ana. 17 “Ya Ubangiji, me ya sa mutum yake da daraja haka a gare ka? Me ya sa kake lura da abin da yake yi? 18 Kakan dube shi kowace safiya. Kana jarraba shi a kowane daƙiƙa. 19 Ba za ka ko ɗan kawar da kai ba, Don in samu in haɗiye yau? 20 Ko na yi zunubi ina ruwanka, Kai mai ɗaure mutane? Me ya sa ka maishe ni abin bārata? Ni wani babban kaya mai nauyi ne a gare ka? 21 Ba za ka iya gafarta mini zunubina ba? Ba za ka kawar da kai ga muguntar da na aikata ba? Ba da daɗewa ba zan rasu in koma a ƙura, Lokacin da ka neme ni ba za ka same ni ba.”

Ayuba 8

Bildad ya Ƙarfafa Hukuncin Allah Daidai Ne

1 Sai Bildad ya yi magana. 2 “Ka gama maganganunka marasa kan gado duka? 3 Allah bai taɓa yin danniya ba, Bai kuma taɓa fāsa aikata abin da yake daidai ba. 4 Lalle 'ya'yanka sun yi wa Allah zunubi, Don haka ya hukunta su yadda ya cancanta. 5 Amma sai ka juyo ka yi roƙo ga Allah Maɗaukaki. 6 Idan kana da tsarki da aminci, Allah zai taimake ka, Ya maido da iyalin gidanka, ya yi maka sakayya. 7 Duk hasarar dukiyar nan da ka yi, ba kome ba ne In aka gwada da abin da Allah zai ba ka nan gaba. 8 “Ka tsai da zuciyarka a kan hikima irin ta zamanin dā. Ka kuma yi ta yin tunani a kan gaskiyar da kakanninmu suka koya. 9 Kwanakinmu 'yan kaɗan ne kawai, Ba mu san kome ba, Mu inuwa ne kawai a fuskar duniya. 10 Amma ka yarda masu hikima na zamanin dā su koya maka, Ka kasa kunne ga abin da za su faɗa. 11 “Iwa ba ta tsirowa inda ba ruwa, Ba a taɓa samunta a ko'ina ba sai a fadama. 12 In ruwan ta ƙafe, ita ce za ta fara bushewa, Tun tana ƙanƙana ba ta isa a yanke a yi amfani da ita ba. 13 Marasa tsoron Allah kamar iwan nan suke, Ba su da sa zuciya muddin sun rabu da Allah. 14 Suna dogara ga silin zare, murjin gizo-gizo. 15 Idan suka jingina ga saƙar gizo-gizo, za ta iya tokare su? Idan sun kama ta, za ta taimake su tsayawa? 16 “Mugaye sukan tsiro kamar ciyayi a hasken rana, Ciyayin da sukan yaɗu su cinye gona duka. 17 Saiwoyinsu sukan nannaɗe duwatsu, Su riƙe kowane dutse da ƙarfi. 18 Amma idan aka tumɓuke su, Ba wanda zai taɓa cewa sun kasance a wurin. 19 Hakika matuƙar murnar da mugaye suke da ita ke nan, Yanzu waɗansu ne za su zo su gāje wurarensu. 20 “Amma daɗai Allah ba zai rabu da amintattu ba, Ba kuwa zai taɓa taimakon mugun mutum ba. 21 Zai sāke barinka ka yi dariya ka ƙyalƙyata kamar dā, Ka kuma yi sowa da murna matuƙa. 22 Amma zai sa maƙiyanka su sha kunya, Za a shafe gidajen mugaye.”

Ayuba 9

Ayuba ya Kasa Amsa wa Allah

1 Ayuba ya amsa. 2 “Ai, na taɓa jin waɗannan duka, Amma ta ƙaƙa mutum zai yi jayayya da Allah har ya yi nasara? 3 Ta ƙaƙa za ka iya jayayya da shi? Yana yiwuwa ya yi maka tambayoyi guda dubu Waɗanda ba wanda zai iya ba da amsarsu. 4 Allah mai hikima ne, mai iko, Ba wanda zai iya ja in ja da shi. 5 Yakan kawar da manyan duwatsu farat ɗaya, Ya hallaka su da fushinsa, 6 Allah yakan aiko da girgizar ƙasa, ya girgiza duniya, Yakan jijjiga ginshiƙan da duniya take zaune a kansu. 7 Allah yana da iko ya hana rana fitowa, Ko kuma ya hana taurari haskakawa da dare. 8 Ba wanda ya taimaki Allah shimfiɗa sammai, Wanda yake taka raƙuman ruwan teku, ya kuma kwantar da su. 9 Allah ya rataye taurari a sararin sama, Wato su mafarauci da kare da zomo, Da kaza da 'ya'yanta da taurarin kudu. 10 Ba shi yiwuwa mu gane manyan abubuwa da yake yi. Ayyukan al'ajabansa ba su da iyaka. 11 “Allah yana wucewa kusa da ni, Amma ba na ganinsa. 12 Yakan ɗauki abin da yake so, ba wanda yake hana shi, Ba wanda yake tambayarsa cewa, ‘Me kake yi?’ 13 “Allah ba zai huce fushinsa ba. Ya murƙushe maƙiyansa waɗanda suka taimaki dodon ruwan nan da ake kira Rahab, wanda ya tayar masa. 14 To, ƙaƙa zan yi in samo kalmomin da zan amsa wa Allah? 15 Ko da yake ba ni da laifi, Duk da haka iyakar abin da zan iya yi ke nan, In roƙi Allah ya yi mini jinƙai, Shi da yake alƙalina. 16 Amma duk da haka ko ya yardar mini in yi magana ma, Ban yi tsammani zai saurare ni ba. 17 Shi ya aiko da hadura, suka yi kacakaca da ni, Suka ƙuƙƙuje ni, ga shi kuwa, ba wani dalilin da ya sa ya yi mini rauni. 18 Ya hana ni in ko shaƙata, Ina jin haushin dukan abin da yake yi mini. 19 In gwada ƙarfi ne? To, a iya gwada wa Allah ƙarfi? In kai shi ƙara ne? Wa zai sa shi ya je? 20 Ni ba ni da laifin kome, amintacce ne ni, A kunne sai a ji kalmomina kamar na marar gaskiya ne. Kowane abu da na fāɗa, kā da ni yake yi. 21 Ba ni da laifin kome, amma ba na ƙara damuwa. Na gaji da rayuwa. 22 Don haka ban damu da kome ba. Da marar laifin da mai laifin duk, Allah zai hallaka mu. 23 Sa'ad da marar laifi ya mutu farat ɗaya, Allah yakan yi dariya. 24 Allah ya ba da duniya ga mugaye, Ya makantar da dukan alƙalai, Idan ba Allah ne ya yi hakanan ba, to, wa ya yi? 25 “Kwanakina suna shuɗewa da sauri, ba mai kyau ko ɗaya. 26 Raina na wucewa kamar jirgin ruwa mafi sauri, Da sauri ƙwarai kamar juhurma ya kai wa zomo sura. 27 Idan an yi murmushi, Ina ƙoƙari in manta da azabata, 28 Sai dukan wahalar da nake sha ta yi ta firgita ni, Na sani Allah ya ɗauke ni mai laifi. 29 Tun da yake Allah ya ɗauka, ni mai laifi ne, To, me zai sa in damu? 30 Ba sabulun da zai iya wanke zunubaina. 31 Allah ya jefa ni a kwatami, Har tufafina ma suna jin kunyata. 32 Da a ce Allah mutum ne, Da sai in mayar masa da magana, Da sai mun je ɗakin shari'a a yanka mana shari'a. 33 Amma ga shi, ba wanda zai shiga tsakaninmu, Ba wanda zai shara'anta tsakanina da Allah. 34 Ka daina hukunta ni, ya Allah! Ka daina razanar da ni. 35 Ba na jin tsoro, Zan yi magana, domin na san zuciyata.”

Ayuba ya yi Kukan Matsayin da yake Ciki

Ayuba 10

1 “Na gaji da rayuwa, Ku ji ina fama da baƙin ciki. 2 Kada ka hukunta ni, ya Allah. Ka faɗa mini laifin da kake tuhumata da shi. 3 Daidai ne a gare ka ka yi mugunta? Ka wulakanta abin da kai da kanka ka yi? Sa'an nan ka yi murmushi saboda dabarun mugaye? 4 Yadda mutane suke duban abu, haka kake duba? 5 Kai ma ranka gajere ne kamar namu? 6 In haka ne, me ya sa kake bin diddigin dukan laifofina, Kana farautar dukan abin da na yi? 7 Ka sani, ba ni da laifi, Kakuma sani, ba wanda zai cece ni daga gare ka. 8 “Da ikonka ne ka yi ni, ka siffata ni, Yanzu kuma da ikon nan naka ne za ka hallaka ni. 9 Ka tuna, ya Allah, kai ka halicce ni, da yumɓu kuwa ka yi ni. Za ka murtsuke ni ne, in kuma koma ƙura? 10 Kai ne ka ba mahaifina ƙarfin da zai haife ni, Kai ne ka sa na yi firma a cikin cikin mahaifiyata. 11 Kai ne ka siffata jikina da ƙasusuwa da jijiyoyi, Ka rufe ƙasusuwan da nama, naman kuma ka rufe da fata. 12 Kai ne ka ba ni rai da madawwamiyar ƙauna, Kulawarka ce ta sa ni rayuwa. 13 Amma yanzu na sani, Dukan lokacin nan kana da wani nufi a ɓoye game da ni. 14 Jira kake ka ga ko zan yi zunubi, Don ka ƙi gafarta mini. 15 Da cewa na yi zunubi, na shiga uku ke nan a wurinka. Amma sa'ad da na yi abin kirki ba na samun yabo. Ina baƙin ciki ƙwarai, kunya ta rufe ni. 16 Da zan ci nasara a kan kowane abu, Da sai ka yi ta farautata kamar zaki, Kana aikata al'ajabai don ka cuce ni. 17 A koyaushe kakan karɓi shaida gāba da ni, Fushinka sai gaba gaba yake yi a kaina, Kakan yi mini farmaki a koyaushe. 18 “Ya Allah, me ya sa ka bari aka haife ni? Da ma na mutu tun kafin wani ya gan ni! 19 Da a ce daga cikin cikin mahaifiyata an wuce da ni zuwa kabari Da ya fi mini kyau bisa ga kasancewata. 20 Raina bai kusa ƙarewa ba? A bar ni kawai! Bari in ci moriyar lokacin da ya rage mini. 21 An jima kaɗan zan tafi, ba kuwa zan komo ba faufau, Zan tafi ƙasa mai duhu, inda ba haske, 22 Ƙasa mai duhu, da inuwoyi da ɗimuwa Inda ko haske ma kansa duhu ne.”

Ayuba 11

Zofar ya Zargi Ayuba a kan Aikata Laifi

1 Zofar ya amsa. 2 “Ba wanda zai amsa dukan wannan surutu? Yawan magana yakan sa mutum ya zama daidai? 3 Ayuba, kana tsammani ba za mu iya ba ka amsa ba? Kana tsammani maganganunka na ba'a Za su sa mu rasa abin da za mu mayar maka? 4 Ka ɗauka duk abin da kake faɗa gaskiya ne, Ka kuma mai da kanka kai mai tsarki ne a gaban Allah. 5 Da ma Allah zai amsa maka, Ya yi magana gāba da kai, 6 Da ya faɗa maka hikima tana da fannoni da yawa. Akwai abubuwa waɗanda suka fi ƙarfin ganewar ɗan adam. Duba, Allah ya ƙyale wani ɓangare na laifinka. 7 “Kana iya gane matuƙa da iyakar Girman Allah da na ikonsa? 8 Sararin sama ba shi ne matuƙa a wurin Allah ba, Amma ga shi, yana can nesa da kai, Allah ya san lahira, Amma kai ba ka sani ba. 9 Fāɗin girman Allah ya fi duniya Ya kuma fi teku fāɗi. 10 Idan Allah ya kama ka ya gurfanar da kai gaban shari'a, Wa zai iya hana shi? 11 Allah ya san irin mutanen da ba su da amfani, Domin yana ganin dukan mugayen ayyukansu. 12 Idan dakikan mutane sa yi hikima, To, jakunan jeji ma sa yi irin hali na gida. 13 “Ayuba, ka shirya zuciyarka, Ka ɗaga hannuwanka zuwa wurin Allah. 14 Ka kawar da mugunta da kuskure daga gidanka. 15 Sa'an nan ka sāke shan ɗamarar zaman duniya, Da ƙarfi da rashin tsoro. 16 Duk wahalarka za ta gushe daga tunaninka, Kamar yadda rigyawa takan wuce, ba a ƙara tunawa da ita. 17 Ranka zai yi haske fiye da hasken rana da tsakar rana. Kwanakin ranka mafiya duhu Za su yi haske kamar ketowar alfijir. 18 Za ka yi zaman lafiya, cike da sa zuciya, Allah zai kiyaye ka, ya ba ka hutawa. 19 Ba za ka ji tsoron kowane maƙiyi ba, Mutane da yawa za su nemi taimako daga gare ka. 20 Amma mugaye za su dudduba ko'ina da fid da zuciya, Ba su da wata hanyar da za su kuɓuta. Sauraronsu kaɗai shi ne mutuwa.”

Ayuba 12

Ayuba ya Ƙarfafa Ikon Allah da Hikimar Allah

1 Ayuba ya amsa. 2 “Aha! Ashe, kai ne muryar jama'a, Idan ka mutu hikima ta mutu ke nan tare da kai. 3 Amma ni ma ina da hankali gwargwado, kamar yadda kake da shi, Ban ga yadda ka fi ni ba. Kowa ya san sukan abin da ka faɗa. 4 Har abokaina ma, suna ta yi mini dariya yanzu, Suna ta dariya ko da yake ni adali ne marar laifi, Amma akwai lokacin da Allah ya amsa addu'o'ina. 5 Ba ka shan wahalar kome, duk da haka ka maishe ni abin dariya. Ka bugi mutumin da yake gab da fāɗuwa. 6 Amma ɓarayi da marasa tsoron Allah suna zaune cikin salama, Ko da yake ƙarfinsu ne kaɗai allahnsu. 7 “Don haka tsuntsaye da dabbobi sun fi ka sani, Suna da abu mai yawa da za su koya maka. 8 Ka roƙi talikan da suke a duniya, da a cikin teku, hikimar da suke da ita. 9 Dukansu sun sani ikon Ubangiji ne ya yi su. 10 Allah shi ne yake bi da rayukan talikansa. Numfashin dukan mutane kuwa a ikonsa yake. 11 Amma kamar yadda harsunanku suke jin daɗin ɗanɗanar abinci, Hakanan kuma kunnuwanku suke jin daɗin sauraren kalmomi. 12-13 “Tsofaffi suna da hikima, Amma Allah yana da hikima da iko. Tsofaffi suna da tsinkaya, Amma Allah yana da tsinkaya da ikon aikatawa. 14 Sa'ad da Allah ya rurrushe, wa zai iya sāke ginawa? Wa kuma zai iya fitar da mutumin da Allah ya sa a kurkuku? 15 Akan yi fari sa'ad da Allah ya hana ruwan sama, Rigyawa takan zo sa'ad da ya kwararo ruwa. 16 Allah mai iko ne a kullum kuwa cikin nasara yake Da macuci, da wanda aka cutar, duk ƙarƙashin ikon Allah suke. 17 Yakan mai da hikimar masu mulki wauta, Yakan mai da shugabanni marasa tunani. 18 Yakan tuɓe sarakuna ya sa su kurkuku. 19 Yakan ƙasƙantar da firistoci da mutane masu iko. 20 Yakan rufe bakin waɗanda aka amince da su. Yakan kawar da hikimar tsofaffi. 21 Yakan kunyatar da masu iko, Ya hana wa masu mulki ƙarfi. 22 Yakan aika da haske a wuraren da suke da duhu kamar mutuwa. 23 Yakan sa sauran al'ummai su yi ƙarfi su ƙasaita, Sa'an nan ya fatattaka su, ya hallaka su. 24 Yakan sa shugabanninsu su zama wawaye, Ya bar su su yi ta makuwa, su ruɗe, su ɓata, 25 Su yi ta lalube cikin duhu, su yi ta tangaɗi kamar bugaggu.”

Ayuba 13

Ayuba ya Kāre Mutuncinsa

1-2 “Duk abin da ka hurta, na taɓa jinsa, Na gane da shi sarai. Iyakar abin da kuka sani, ni ma na sani. Ba ku fi ni da kome ba. 3 Amma da Allah nake jayayya, ba da ku ba, Ina so in yi muhawara da shi a kan ƙarar da nake da ita. 4 Kun ɓoye jahilcinku da ƙarairayi. Kun zama kamar likitoci waɗanda ba su iya warkar da kowa ba. 5 Kada ku faɗi kome, Wani sai ya ce kuna da hikima! 6 “Ku saurara mini, zan faɗi ƙarata. 7 Me ya sa kuke yin ƙarya? Kuna tsammani ƙarairayinku za su taimaki Allah? 8 Son zuciya kuke yi, ko ba haka ba? Kuna goyon bayan Allah? Za ku goyi bayan Allah sa'ad da aka gurfanar da ko gaban shari'a? 9 Da Allah ya bincike ku sosai, Zai iske wani abin kirki ne a cikinku? Kuna tsammani za ku ruɗi Allah, kamar yadda kuke ruɗin mutane? 10 Ko da yake kun ɓoye son zuciyarku, Duk da haka zai tsauta muku, 11 Ikonsa kuwa zai razana ku. 12 Karin maganarku da muhawararku ba su da ƙarfi ƙwarai. 13 “Ku yi shiru ku ba ni zarafi in yi magana. Duk abin da zai faru, ya faru. 14 A shirye nake in yi kasai da raina. 15 Na fid da zuciya ɗungum. To, in Allah ya kashe ni, sai me? Zan faɗa masa ƙarata. 16 Mai yiwuwa ne ƙarfin halina ya cece ni, Tun da yake ba wani mugun mutumin da zai iya zuwa gaban Allah. 17 Sai a saurari bayanin da zan yi. 18 A shirye nake in faɗi ƙarata, Domin na sani ina da gaskiya. 19 “Ya Allah, za ka yi ƙarata? Idan kuwa ka yi, to, a shirye nake in yi shiru in mutu. 20 Ina da abu biyu da zan yi maka roƙo, Ka yarda da su, sa'an nan ba zan yi ƙoƙari in ɓoye ba. 21 Wato ka daina hukuncin da kake yi mini, Kada ka sa razanarka ta ragargaza ni. 22 “Ka fara yin magana, ya Allah, ni kuwa zan amsa. Ko kuma ka bari in yi magana, sa'an nan ka amsa mini. 23 Kuskure da laifi guda nawa na yi? Waɗanne irin laifofi ake tuhumata da su? 24 Me ya sa kake guduna? Me ya sa ka maishe ni kamar maƙiyi? 25 Ƙoƙari kake ka firgita ni? Ni ba wani abu ba ne, ganye ne kawai, Ka fāɗa wa tattaka da yaƙi ne kawai. 26 Ka kawo mugayen ƙararraki a kaina, Har da laifofin da na yi na ƙuruciya. 27 Ka ɗaure ƙafata da sarƙoƙi, Kakan lura da kowace takawata, Har kana bin diddigin sawayena. 28 Saboda wannan na zama abin kallo, ni kuwa kamar ragargazajjen itace ne, ko diddigaggiyar riga.”

Ayuba 14

Ayuba ya yi Tunani a kan Rashin Tsawon Rai

1 “Mutum duka kwanakin ransa gajere ne, kwanakin wahala kuwa. 2 Sukan yi firma su bushe nan da nan kamar furanni, Sukan shuɗe kamar inuwa. 3 Na ma isa ka dube ni ne, ya Allah? Ko ka gabatar da ni a gabanka, Ka yi mini shari'a? 4 Ba wani abu tsarkakakke Da zai fito daga cikin kowane marar tsarki, kamar mutum. 5 Tsawon kwanakin ransa, an ƙayyade su tun can, An ƙayyade yawan watannin da zai yi, Ka riga ka yanke haka ya Allah, ba su sākuwa. 6 Ka kawar da fuska daga gare shi, ka rabu da shi, Ka bar shi ya ji daɗin kwanakinsa na fama da aiki idan zai iya. 7 “Akwai sa zuciya ga itacen da aka sare, Yana iya sāke rayuwa ya yi toho. 8 Ko da yake saiwoyinsa sun tsufa, Kututturensa kuma ya ruɓe a ƙasa, 9 In aka zuba ruwa, sai ya toho kamar sabon tsiro. 10 Amma ɗan mutum ya mutu, ƙarshensa ke nan, Ya mutu, a ina yake a lokacin nan? 11 “Mai yiwuwa ne koguna za su daina gudu, Har tekuna kuma su ƙafe. 12 Amma matattu ba za su tashi ba daɗai, Ba za su ƙara tashi ba sam, muddin sararin sama na nan. Sam, ba za a dame su cikin barcinsu ba. 13 “Ya Allah, da ma a ce ka ɓoye ni a lahira, Ka bar ni a ɓoye, har fushinka ya huce, Sa'an nan ka lokacin da za ka tuna da ni! 14 Idan mutum ya mutu, zai sāke rayuwa kuma? Amma zan jira lokaci mafi kyau, In jira sai lokacin wahala ya wuce. 15 Sa'an nan za ka yi kira, ni kuwa zan amsa, Za ka yi murna da ni, ni talikinka. 16 Sa'an nan za ka lura da kowace takawata Amma ba za ka bi diddigin zunubaina ba. 17 Za ka soke zunubaina ka kawar da su, Za ka shafe dukan kurakuran da na taɓa yi. 18 “Lokaci na zuwa sa'ad da duwatsu za su fāɗi, Har ma za a kawar da duwatsun bakin teku. 19 Ruwa zai zozaye duwatsu, su ragu, Ruwan sama mai ƙarfi zai kwashe jigawa, Kai ma ka bar mutane, ba su da sauran sa zuciya ko kaɗan. 20 Ka fi ƙarfin mutum, ka kore shi har abada, Fuskarsa ta rikiɗe sa'ad da ya mutu. 21 'Ya'yansa maza za su sami girma, amma sam, ba zai sani ba, Sam, ba wanda zai faɗa masa sa'ad da aka kunyatar da su. 22 Ciwon jikinsa da ɓacin zuciyarsa kaɗai yake ji.”

Ayuba 15

Elifaz ya Tsauta wa Ayuba

1 Elifaz ya yi magana. 2 “Surutai, Ayuba! Surutai! 3 Ba wani mai hikima wanda zai yi magana irin taka, Ko kuma ya kāre kansa da irin maganganun da ba su da ma'ana. 4 Kana karya jama'a, kana hana su jin tsoron Allah, Kana hana su yin addu'a gare shi. 5 Mugun lamirinka shi ne yake magana yanzu, Kana ƙoƙari ka ɓuya a bayan maganganunka na wayo. 6 Ba na bukata in kā da kai, Kowace kalma da ka hurta ta kā da ka. 7 “Kana tsammani kai ne mutumin da aka haifa na farko? Sa'ad da Allah ya yi duwatsu kana nan? 8 Ko ka taɓa jin shirye-shiryen da Allah ya yi? Ko kai kaɗai kake da hikima a cikin mutane? 9 Ba wani abu da ka sani da mu ba mu sani ba. 10 Daga wurin mutanen da suka yi furfura muka koyi hikimarmu. Mun koyi hikimarmu daga mutane waɗanda aka haife su Tun kafin a haifi mahaifinka. 11 “Allah yana ta'azantar da kai, Me ya sa har yanzu ka ƙi kulawa da shi? Mun yi magana a madadinsa a natse da lafazi mai daɗi. 12 Amma ka ta da hankalinka, Kana ta zazzare mana ido da fushi. 13 Fushi kake yi da Allah, kana ƙinsa. 14 Akwai mutumin da yake tsarkakakke sarai? Akwai mutumin da yake cikakke a wurin Allah? 15 Me ya sa Allah bai sakar wa mala'ikunsa kome ba? Har su ma ba tsarkaka suke a gare shi ba. 16 Mutum yakan sha mugunta kamar yadda yake shan ruwa, Hakika mutum ya lalace, ya zama mai rainako. 17 “Yanzu ka saurara, ya Ayuba, ga abin da na sani. 18 Mutane masu hikima sun koya mini gaskiya Wadda suka koya daga wurin kakanninsu, Ba su kuwa ɓoye mini asirin kome ba. 19 Ƙasaru 'yantacciya ce daga baƙi Ba wanda zai raba su da Allah. 20 “Mugun mutum mai zaluntar sauran mutane Zai kasance da wahala muddin ransa. 21 Zai ji ƙarar muryoyi masu firgitarwa a kunnuwansa. 'Yan fashi za su fāɗa masa Sa'ad da yake tsammani ba abin da zai same shi. 22 Bai sa zuciya zai kuɓuta daga duhu ba, Gama takobi yana jiransa a wani wuri don ya kashe shi. 23 Yana ta yawon neman abinci, yana ta cewa, ‘Ina yake?’ Ya sani baƙin ciki ne yake jiransa a nan gaba. Kamar sarki mai iko, 24 Haka masifa take shirin fāɗa masa. 25 “Wannan shi ne ƙaddarar mutum, Wanda ya nuna wa Allah yatsa, Ya kuwa raina Mai Iko Dukka. 26 Wannan mutum mai girmankai ne, ɗan tawaye. 27 Ya ɗauki garkuwarsa kamar ɗan yaƙi, Ya ruga don ya yi yaƙi da Allah. 28 Shi ne mutumin da ya ci birane da yaƙi, Ya ƙwace gidajen waɗanda suka tsere, Amma yaƙi ne zai hallaka birane da gidaje. 29 Arzikinsa ba zai daɗe ba, Duk abin da ya mallaka ba zai daɗe ba. Har inuwarsa ma za ta shuɗe, 30 Ba kuwa zai kuɓuta daga duhu ba. Zai zama kamar itacen da wuta ta ƙone rassansa, Kamar itace kuma da iska ta kaɗe furensa. 31 Idan wauta tasa ta kai shi ga dogara ga mugunta, To, mugunta ce kaɗai zai samu. 32 Kafin kwanakinsa su cika zai bushe, Zai bushe kamar reshe, ba zai ƙara yin ganye ba. 33 Zai ama kamar itacen inabi Wanda 'ya'yansa suka kakkaɓe tun kafin su nuna, Kamar itacen zaitun wanda bai taɓa yin 'ya'ya ba. 34 Marasa tsoron Allah ba za su sami zuriya ba, Wuta za ta cinye gidajen da aka gina da dukiyar rashawa. 35 Waɗannan su ne irin mutanen da suke shirya tarzoma, su aikata mugunta. Kullum zuciyarsu cike take da ruɗarwa.”

Ayuba 16

Ayuba ya yi Kukan abin da Allah yake Yi

1 Ayuba ya yi magana. 2 “Ai, na taɓa jin magana irin wannan, Ta'aziyyar da kake yi azaba ce kawai. 3 Ka dinga yin magana ke nan har abada? A kullum maganarka ita ce dahir? 4 In da a ce a matsayina kake, ni kuma ina a naka, Ina iya faɗar duk abin da kake faɗa yanzu. Da sai in kaɗa kaina da hikima, In dulmuyar da kai a cikin rigyawar maganganu. 5 Da sai in ba ka shawara ta ƙarfafawa, In yi ta yi maka maganar ta'azantarwa. 6 “Amma ba abin da zan faɗa wanda zai taimaka, Yin shiru kuma ba zai raba ni da azaba ba. 7 Ka gajiyar da ni, ya Allah, Ka shafe iyalina. 8 Ka kama ni, kai maƙiyina ne. Na zama daga fata sai ƙasusuwa, Mutane suka ɗauka, cewa wannan ya tabbatar ni mai laifi ne. 9 Allah ya kakkarya gaɓoɓina da fushinsa, Yana dubana da ƙiyayya. 10 Mutane sun buɗe baki don su haɗiye ni Suna kewaye ni suna ta marina. 11 Allah ya bashe ni ha mugaye. 12 Dā ina zamana da salama, Allah Allah ya maƙare ni, Ya fyaɗa ni ƙasa ya ragargaza ni. Allah ya maishe ni abin bārata. 13 Ya harbe ni da kibau daga kowane gefe. Kiban sun ratsa jikina sun yi mini rauni, Duk da haka bai nuna tausayi ba! 14 Ya yi ta yi mini rauni a kai a kai, Ya fāɗa mini kamar soja da ƙiyayya ta haukata. 15 “Ina makoki saye da tsummoki, Ina zaune cikin ƙura a kunyace. 16 Na yi ta kuka har fuskata ta zama ja wur, Idanuna kuma suka yi luhuluhu. 17 Amma ban yi wani aikin kama-karya ba, Addu'ata ga Allah kuwa ta gaskiya ce. 18 “Duniya, kada ki ɓoye laifofin da aka yi mini! Kada ki yi shiru da roƙon da nake yi na neman adalci! 19 Akwai wani a Sama Wanda zai tsaya mini ya goyi bayana. 20 Ina so Allah ya ga hawayena, Ya kuma ji addu'ata. 21 “Ina so wanda zai yi roƙo ga Allah domina, Kamar yadda mutum yakan yi roƙo domin abokinsa. 22 Yanzu shekaruna wucewa suke yi, Ina bin hanyar da ba a komawa.”

Ayuba 17

1 “Ƙarshen raina ya gabato, da ƙyar nake numfashi, Ba abin da ya rage mini sai kabari. 2 Na lura da yadda mutane suke yi mini mummunar ba'a. 3 Ni amintacce ne, ya Allah, ka yarda da maganata. Ba wanda zai goyi bayan abin da nake faɗa. 4 Ka baƙantar da hankalinsu, ya Allah, Kada ka bar su su yi mini duban wulakanci yanzu. 5 A karin maganar mutanen dā an ce, ‘Kowa ya ci amanar abokinsa saboda kuɗi, 'Ya'yansa sā sha wahala!’ 6 Yanzu kuwa sun mai da wannan karin magana a kaina. Da mutane suka ji, Suka zo suka yi ta tofa mini yau a fuska. 7 Baƙin cikina ya kusa makantar da ni, Hannuwana da ƙafafuna sun rame, sun zama kamar kyauro. 8 Duk waɗanda suka zaci su adalai ne sun razana. Dukansu sun kāshe ni, cewa ni ba mai tsoron Allah ba ne. 9 Har su ma da suke cewa su mutanen kirki ne Suna ƙara tabbatarwa ba su yi kuskure ba. 10 Amma da a ce dukansu za su zo su tsaya a gabana, Da ba zan sami mai hikima ko ɗaya daga cikinsu ba. 11 “Kwanakina sun ƙare, shirye-shiryena sun kāsa, Ba ni da sauran sa zuciya. 12 Amma abokaina sun ce dare shi ne hasken rana, Sun kuma ce haske yana kusa, Ko da yake ina cikin duhu. 13 Ba ni da sauran sa zuciya, Gidana yana lahira, Inda zan kwanta in yi ta barci cikin duhu. 14 Zan ce kabari shi ne mahaifina, Tsutsotsin da suke cinye ni su ne mahaifiyata, da 'yan'uwana mata. 15 Ina ne zan sa zuciyata? Wane ne ya ga inda zan sa ta? 16 Akwai wanda ya yi shiri a binne shi tare da ni, Mu tafi tare da shi zuwa lahira?”

Ayuba 18

Bildad ya Bayyana abin da za a Yi wa Mugun Mutum

1 Bildad ya amsa. 2 “Ayuba, mutane kamarka sun taɓa yin shiru? Da ka yi ƙoƙari ka kasa kunne da mun yi magana da kai. 3 Me ya sa kake tsammani mu dakikai ne kamar shanu? 4 Cutar kanka kake yi saboda fushin da kake ji. Duniya za ta ƙare ne sabili da kai? Za a kawar da duwatsu sabili da kai? 5 “Za a kashe hasken mugun mutum, Harshen wutarsa ba zai ƙara ci ba. 6 Fitilar da take cikin alfarwarsa ba za ta ba da haske ba. 7 A dā gagau yake tafiya, amma yanzu ɗingishi yake yi, Shawararsa ta kāshe shi. 8 Yana tafiya, sai ya fāɗa cikin tarko. Tarkon ya kama ƙafafunsa. 9 Tarko ya kama diddigensa ya riƙe shi, 10 An binne masa tarko a ƙasa, An kafa masa tarko a hanyarsa. 11 “Kewaye da shi duka razana tana jiransa, Duk inda ya nufa tana biye da shi, 12 Dā attajiri ne, amma yanzu ya talauce, Kusa da shi bala'i na tsaye yana jiransa. 13 Mummunan ciwo ya bazu ko'ina a jikinsa, Yana sa hannuwansa da ƙafafunsa su ruɓe, 14 Dā yana zaune lafiya, Sai razana ta tatike shi, Ta jawo shi zuwa ga Sarkin Mutuwa. 15 Yanzu kowa zai iya zama a alfarwarsa, Bayan da an karkashe ƙwayoyin cuta da farar wuta. 16 Saiwoyinsa da rassansa suka yi yaushi suka bushe. 17 Sunansa ya ƙare a gida da a jeji, Ba wanda yake ƙara tunawa da shi. 18 Za a kore shi daga ƙasar masu rai, Za a kore shi daga haske zuwa duhu. 19 Ba shi da zuriya, da sauran waɗanda suka ragu da rai. 20 Daga gabas zuwa yamma, duk wanda ya ji labarin ƙaddarar da ta same shi, Zai yi makyarkyata, ya yi rawar jiki don tsoro. 21 Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wannan ita ce ƙaddarar mutane waɗanda ba su damu da kome na Allah ba.”

Ayuba 19

Bangaskiyar Ayuba ta sa Allah zai Goyi Bayansa

1 Ayuba ya amsa. 2 “Me ya sa kuke azabta ni da maganganu? 3 A kowane lokaci kuna wulakanta ni, Ba kwa jin kunya yadda kuke zagina. 4 Da a ce ma na aikata abin da yake ba daidai ba ne, Da me ya cuce ku? 5 Tsammani kuke kun fi ni ne, Kuna ɗauka cewa wahalar da nake sha Ta tabbatar ni mai laifi ne. 6 Ba ku iya ganin abin da Allah ya yi mini, Ya kafa tarko don ya kama ni. 7 Na ce ban yarda da kama-karyarsa ba, Amma ba wanda ya kasa kunne. Na nema a aikata gaskiya, amma sam, babu. 8 Allah ya rufe hanya, na kasa wucewa, Ya rufe hanyata da duhu, 9 Gama ya kwashe dukiyata duka, Ya ɓata mini suna. 10 Ya mammangare ni, Ya tumɓuke sa zuciyata, Ya bar ni in yi yaushi, in mutu. 11 Allah ya zaburo mini da fushi, Ya maishe ni kamar mafi mugunta daga cikin maƙiyansa. 12 Ya aiko da rundunar sojansa don ta fāɗa mini, Suka haƙa ramummuka kewaye da alfarwata inda za su yi kwanto. 13 “Yan'uwana sun yashe ni, Na zama baƙo ga idon sanina. 14 Dangina da abokaina sun tafi. 15 Waɗanda sukan ziyarce gidana sun manta da ni. Barorina mata na gidana sun maishe ni kamar baƙo daga wata ƙasa. 16 Sa'ad da na kira barana, ba ya amsawa, Ko a lokacin da na roƙe shi ya taimake ni. 17 Har matata ma ba ta iya jurewa da ɗoyin numfashina, 'Yan'uwana maza kuwa ba su ko zuwa kusa da ni. 18 'Yan yara sukan raina ni su yi mini dariya sa'ad da suka gan ni. 19 Aminaina na kusa sukan dube ni, duban ƙyama, Waɗanda na fi ƙaunarsu duka sun zama maƙiyana. 20 Fatar jikina ta saki, ba ƙarfi, Da ƙyar na kuɓuta. 21 Ku abokaina ne! Ku ji tausayina! Ikon Allah ya fyaɗa ni ƙasa. 22 Me ya sa kuke ɓata mini rai kamar yadda Allah ya yi? Azabar da kuka yi mini har yanzu ba ta isa ba? 23 “Da ma a ce wani zai rubuta abin da nake faɗa, Ya rubuta shi a littafi! 24 Ko kuwa ya zana kalmomina da kurfi a kan dutse, Ya rubuta su don su tabbata har abada! 25 Amma na sani akwai wani a Samaniya Wanda a ƙarshe zai zo ya tsaya mini. 26 Ko da yake ciwo ya riga ya cinye fatata, A wannan jiki zan ga Allah. 27 Zan gan shi ido da ido, Ba kuwa zai zama baƙo a gare ni ba. “Zuciyata ta karai saboda ku mutane kun ce, 28 ‘Ta ƙaƙa za mu yi masa azaba?’ Kuna neman sanadin da za ku fāɗa mini. 29 Amma yanzu, sai ku ji tsoron takobi, Ku ji tsoron takobin da yake kawo hasalar Allah a kan zunubi. Don haka za ku sani akwai wani mai yin shari'a.”

Ayuba 20

Zofar ya Nuna Rabon Mugu

1 Zofar ya amsa. 2 “Ayuba, ka ɓata mini rai, Ba zan yi haƙuri ba, sai na ba ka amsa. 3 Abin da ka faɗa raini ne, Amma na san yadda zan ba ka amsa. 4 “Hakika ka sani tun daga zamanin dā, Sa'ad da aka fara sa mutum a duniya, 5 Ba wani mugun mutum wanda ya taɓa daɗewa da farin ciki. 6 Mai yiwuwa ne ya ƙasaita, ya zama kamar hasumiya a sararin sama. Ya ƙasaita har kansa ya taɓa gizagizai. 7 Amma zai shuɗe kamar ƙura. Waɗanda dā suka san shi, Za su yi mamaki saboda rashin sanin inda ya tafi. 8 Zai ɓace kamar mafarki, kamar wahayi da dad dare, Ba kuwa zai a ƙara ganinsa ba. 9 Ba za a ƙara ganinsa a wurin zamansa ba. 10 Tilas 'ya'yansa maza su biya zambar da ya yi wa matalauta, Tilas hannuwansa subiya dukiyar da ya ƙwace. 11 Ko da yake gagau yake, ma'aikaci ne kuma sa'ad da yake yaro, Duk da haka ba da jimawa ba, zai zama ƙura. 12-13 Ɗanɗana mugunta yana da daɗi a gare shi ƙwarai, Yakan sa wata a bakinsa don ya riƙa jin daɗin tsotsanta. 14 Amma a cikinsa wannan abinci yakan zama da ɗaci, Ɗacinsa kamar na kowane irin dafi mai ɗaci ne. 15 Mugun mutum yakan harar da dukiyar da ya samu ta hanyar zamba, Allah zai karɓe ta har da wadda ya ci a cikin cikinsa. 16 Abin da mugu ya haɗiye kamar dafi yake, Yakan kashe shi kamar saran maciji mai mugu dafi. 17 Zai mutu bai ga kogunan man zaitun ba, Ba kuwa zai ga rafuffukan da suke da yalwar albarka ba. 18 Tilas ya rabu da dukan abin da ya yi wahalarsa. Ba dama ya mori dukiyarsa, 19 Saboda zalunci da rashin kula da matalauta, Da ƙwace gidajen da waɗansu suka gina. 20 “Har abada ba zai kai ga samun abin da yake wahala ba. 21 Sa'ad da ya ci ba zai yi saura ba, Gama yanzu dukiyarsa ta ƙare. 22 A lokacin da yake gaɓar samunsa, Baƙin ciki mai nauyin gaske zai ragargaza shi. 23 Bari ya ci duk irin abin da yake so! Allah zaihukunta shi da hasala da fushi. 24 Lokacin da yake ƙoƙari ya kuɓuta daga takobin baƙin ƙarfe, Za a harbe shi da bakan tagulla ya fāɗi warwar. 25 Kibiya za ya kafe a jikinsa Tsininta zai yi ta ɗiɗɗiga da jini, Razana ta kama zuciyarsa. 26 Aka hallaka dukan abin da ya tattara, Wutar da ba hannun mutum ya kunna ba Ta ƙone shi, shi da iyalinsa duka. 27 Samaniya ta bayyana zunubin wannan mutum, Duniya kuma ta ba da shaida gāba da shi. 28 Dukan dukiyarsa za a hallaka ta a rigyawar fushin Allah. 29 “Wannan ita ce ƙaddarar mugaye, Wadda Allah ya ƙayyade musu.”

Ayuba 21

Ayuba ya yi Magana a kan Wadatar Mugaye

1 Ayuba ya amsa. 2 “Ku kasa kunne ya abin da nake faɗa, Wannan ita ce ta'aziyyar da nake nema a gare ku. 3 Ku ba ni zarafi in yi magana, sa'an nan in na gama ku amsa in kun ga dama. 4 “Ba da 'yan adam nake faɗa ba, Ina da isasshen hanzarin da za sa in yi fushi. 5 Ku dube ni, ashe, wannan bai isa ya sa ku yi zuru, Ku firgita, ku yi shiru ba? 6 Sa'ad da na tuna da abin da ya same ni, Sai jikina ya yi suwu, in yi ta makyarkyata in rawar jiki. 7 Me ya sa Allah yake barin mugaye Har su tsufa su kuma yi arziki? 8 'Ya'yansu da jikokinsu sukan girma a idonsu. 9 Allah bai taɓa aukar wa gidajensu da bala'i ba, Ba su taɓa zama a razane ba. 10 Hakika shanunsu suna ta hayayyafa, Suna haihuwa ba wahala. 11 'Ya'yansu suna guje-guje, Suna tsalle kamar 'yan raguna, 12 Suna rawa ana kaɗa garaya, Ana busa sarewa. 13 Suka yi zamansu da salama, Su mutu shiru ba tare da shan wahala ba. 14 Mugaye sukan ce wa Allah ya ƙyale su kurum, Ba su so su san nufinsa game da hanyoyinsu. 15 Suna tsammani ba amfani a bauta wa Allah, Ko a yi addu'a gare shi domin samun wata fa'ida. 16 Sukan ce ta wurin ƙarfinsu ne suka yi nasara, Amma ban yarda da irin tunaninsu ba. 17 “An taɓa kashe hasken mugun mutum? Ko masifa ta taɓa fāɗa wa wani daga cikinsu? Allah ya taɓa hukunta wa mugu da fushi, 18 Ya kuma sa su zama kamar tattakar da iska yake kwashewa? Ko kuma kamar ƙura wadda hadiri yake kwashewa? 19 “Kukan ce Allah yakan hukunta yaro saboda zunuban mahaifinsa. A'a! Allah dai yakan hukunta wa masu zunubi. Ya kuma nuna ya yi haka saboda zunubansu ne. 20 Bari dai a hukunta masu zunubi Su kuma ga hasalar Allah. 21 Bayan rasuwar mutum, Ruwansa ne ya sani ko 'ya'yansa suna jin daɗi? 22 Mutum zai iya koya wa Allah? Mutum zai iya shara'anta wa Allah Mai Iko Dukka? 23 “Waɗansu mutane sukan yi zamansu ba ciwon kome har ranar mutuwarsu, Suna cikin farin ciki da jin daɗi, 24 Jikunansu kuwa sun yi ɓulɓul. 25 Waɗansu kuwa ba su taɓa sanin farin ciki ba. Sukan yi dukan kwanakinsu su mutu da baƙin ciki. 26 Amma duk abu guda ne su, mutuwa za su yi, a binne, Tsutsotsi su lulluɓe su duka. 27 “Na san irin tunaninku na hassada, 28 Kuna ta tambaya, ‘Ina ne gidan babban mutumin nan yanzu, Wato mutumin da yake aikata mugunta?’ 29 “Ashe, ba ku yi magana da matafiya ba? Ba ku kuma san rahoton da suka kawo ba? 30 A ranar da Allah ya yi fushi, ya yi hukunci, A kullum mugun na kaɗai yakan kuɓuta. 31 Ba wanda zai fito fili ya zargi mugun, Ko ya mayar masa da martani. 32 Sa'ad da aka ɗauke shi zuwa hurumi, A inda ake tsaron kabarinsa, 33 Dubban mutane sukan tafi wurin jana'izarsa, Akan mai da ƙasa a kan gawarsa a hankali. 34 “Amma ku, ƙoƙari kuke yi ku ta'azantar da ni da maganganun banza. Duk abinda kuka faɗa ƙarya ne!”

Ayuba 22

Elifaz ya Zargi Ayuba a kan Aikata Mugunta

1 Elifaz ya yi magana. 2 “Akwai wani mutum, ko mafi hikima, Wanda zai amfani Allah? 3 Gaskiyar da kake yi za ta amfani Allah? Ko kuwa abin kirki da kake yi zai taimake shi? 4 Ai, ba don tsoron Allah da kake yi ba ne, Ya sa wannan tsautawa da jarrabawa suka same ka. 5 Ko kusa ba haka ba ne, Amma saboda zunubi mai yawa da ka yi ne. Saboda kuma dukan muguntar da ka aikata. 6 Don ka sa ɗan'uwanka ya biya ka bashin da kake binsa, Ka ƙwace tufafinsa, ka bar shi huntu. 7 Ka hana wa waɗanda suke ji ƙishi ruwan sha, Ka hana waɗanda suke jin yunwa abinci. 8 Ka mori ikonka da matsayinka, Don ka mallaki dukan ƙasar. 9 Ba ƙin taimako kaɗai ka yi ba, Amma har marayu ma ka yi musu ƙwace, ka wulakanta su. 10 Don haka ne yanzu akwai ramummuka ko'ina kewaye da kai, Tsoro ya kama ka nan da nan. 11 An yi duhu ƙwarai, har ba ka iya gani, Rigyawa ta sha kanka. 12 “Ashe, ba a can saman sammai Allah yake zaune ba? Sai ya sunkuya ya dubi taurari, ko da yake suna can sama ne. 13 Duk da haka ka ce, ‘Allah bai san kome ba. Gizagizai sun lulluɓe shi, ƙaƙa zai iya yi mana shari'a?’ 14 Kana tsammani gizagizai masu duhu sun hana shi gani, A lokacin da yake tafiya a kan iyakar da ke tsakanin duniya da sararin sama. 15 “Ka ɗauka a ranka ka bi gurbin da mugaye suke bi kullum? 16 Kafin ma su kai ga kwanakinsu, Sai rigyawa ta shafe su. 17 Su ne mutanen da suka ƙi Allah, Suka kuwa gaskata ba shi da ikon yi musu kome, 18 Ko da yake Allah ne ya arzuta su. Ba na iya gane tunanin mugaye. 19 Mutanen kirki suna murna, Marasa laifi kuma suna dariya Sa'ad da suka ga ana hukunta mugaye. 20 Duk abin da mugu ya mallaka ya hallaka, Wuta kuwa ta lashe kowane abu da ya ragu. 21 “Yanzu fa, Ayuba, sai ka yi sulhu da Allah, Ka daina ɗaukarsa kamar maƙiyinka, In ka yi haka, to, za ka sami albarka. 22 Ka karɓi koyarwar da yake yi, Ka riƙe kalmominsa a zuciyarka. 23 Hakika sai ka yi tawali'u, ka koma wurin Allah, Ka kawar da dukan muguntar da ake yi a gidanka. 24 Ka jefar da zinariyarka, zinariyarka mafi kyau, Ka jefar da ita kamar dutse ko ƙura. 25 Bari Allah Mai Iko Dukka ya zama zinariyarka, Ya zama azurfa, wadda aka tula dominka. 26 Sa'an nan za ka dogara ga Allah kullayaumin, Ka kuma tarar shi ne asalin farin cikinka. 27 Sa'ad da ka yi addu'a zai amsa maka, Za ka kuwa kiyaye alkawaran da ka yi. 28 Za ka yi nasara a kowane abu da za ka yi, Haske kuma zai haskaka hanyarka. 29 Allah yakan ƙasƙantar da mai girmankai, Yakan ceci mai tawali'u. 30 Zai ceci wanda yake da laifi, Idan abin da kake yi daidai ne.”

Ayuba 23

Ayuba yana Marmarin kai Ƙara gaban Allah

1 Ayuba ya amsa. 2 “Duk da haka zan yi tawaye in yi wa Allah gunaguni, In dinga yin nishi. 3 Da ma na san inda zan same shi, In kuma san yadda zan kai wurinsa, 4 Da zan kai ƙarata a gare shi, in faɗa masa duk muhawarata, in kāre kaina ne. 5 Ina so in san irin amsar da zai mayar mini, Ina kuma so in san yadda zai amsa mini. 6 Allah kuwa da dukan ƙarfinsa zai yi gāba da ni? A'a, zai saurara in na yi magana. 7 Ina da aminci, zan faɗa wa Allah ra'ayina, Zai tabbatar da amincina duka. 8 “Na nemi Allah a gaba, amma ban same shi a can ba, Ban kuwa same shi a baya ba sa'ad da na neme shi. 9 Allah ya tafi wurin aiki a dama, Ya kuma tafi hagu, amma har yanzu ban gan shi ba. 10 Duk da haka Allah ya san kowane irin hali da nake ciki. Idan ya jarraba ni zai tarar ni tsattsarka ne. 11 Da aminci ina bin hanyar da ya zaɓa, Ban kuwa taɓa kaucewa daga wannan gefe zuwa wancan ba. 12 A kullum ina aikata abin da Allah ya umarta, Ina bin nufinsa, ba nufin kaina ba. 13 “Bai taɓa sākewa ba. Ba wanda zai iya gāba da shi, Ko kuma ya hana shi yin abin da yake so ya aikata. 14 Zai tabbatar da abin da ya shirya domina, Wannan ma ɗaya daga cikin shiryeshiryen da ya yi ne. 15 Don haka in rawar jiki a gabansa saboda tsoro. 16 Allah Mai Iko Dukka ya lalatar da ƙarfin halina. Allah ne ya tsorata ni, 17 Amma ban damu da damu ba, Ko da yake duhu ya dunɗe idanuna.”

Ayuba 24

Ayuba ya yi Kuka da yake Allah bai Kula da Mugunta Ba

1 “Me ya sa Allah bai tsai da ranar da zai yi shari'a ba? Me ya sa ba ya tsai da ranar adalci ga Waɗanda suka bauta masa? 2 Mugaye sukan ci iyaka, Don su ƙara yawan gonarsu. Sukan saci tumaki su zuba cikin garkunansu. 3 Sukan saci jakunan marayu, Su kama san gwauruwa, Su ce sai ta biya basusuwanta. 4 Sukan hana matalauta samun halaliyarsu, Sukan tilasta wa masu bukata su gudu su ɓuya. 5 Kamar jakunan jeji waɗanda sukan nemi abinci a busasshen jeji, Haka matalauta suke, Ba inda za su iya samo wa 'ya'yansu abinci. 6 Ya zama tilas a gare su su girbe gonakin da ba nasu ba, Su tattara 'ya'yan inabi daga gonakin mugaye. 7 Da dare sukan kwanta, ba su da abin rufa, Ba su da abin da zai hana su jin sanyi. 8 Sukan jiƙe sharkaf da ruwan sama wanda ka kwararowa daga kan duwatsu. Sun takure a gefen duwatsu neman mafaka. 9 “Mugaye sukan bautar da yara marayu, Sukan kama 'ya'ya matalauta a bakin bashin da suke bi. 10 Amma tilas matalauta su fita huntaye, ba sa da abin sutura. Tilas su girbi alkama suna kuwa jin yunwa. 11 Suna matse mai daga 'ya'yan zaitun. Suna kuma matse ruwan inabi daga 'ya'yan inabi, Amma su kansu suna fama da ƙishi. 12 Kana jin kukan waɗanda suka yi rauni da Waɗanda suke baƙin mutuwa a birni, Amma Allah bai kula da addu'o'insu ba. 13 “Akwai mugaye waɗanda suke ƙin haske, Ba su fahimce shi ba, suka ƙi bin hanyarsa. 14 Da asuba mai kisankai yakan fita ya kashe matalauci, Da dare kuma ya yi fashi. 15 Mazinaci yakan jira sai da magariba, Sa'an nan ya ɓoye fuskarsa don kada a gane shi. 16 Da dare ɓarayi sukan kutsa kai cikin gidaje, Amma da rana sukan ɓuya, su guje wa haske. 17 Gama tsananin duhu kamar safiya yake gare su, Sun saba da razanar duhu. 18 “Rigyawa takan ci mugun mutum, Ƙasar da ya mallaka kuwa tana ƙarƙashin la'anar Allah. Ba ya kuma iya zuwa aiki a gonar inabinsa. 19 Kamar dusar ƙanƙara take a lokacin zafi da a lokacin fari, Haka mai zunubi yakan shuɗe daga ƙasar masu rai. 20 Ba wanda zai tuna da shi, mahaifiyarsa ma ba za ta lura da shi ba. Tsutotsi sukan ci shi su hallaka shi sarai. Za a sare mugunta kamar itace. 21 Haka yake samun wanda ya wulakanta gwauraye. Bai kuma nuna alheri ga matan da ba su haihu ba. 22 Allah, da ikonsa, yakan hallaka masu ƙarfi, Allah yakan aikata, sai mugun mutum ya mutu. 23 Ya yiwu Allah ya bar shi ya yi zamansa lafiya, Amma a kowane lokaci zai sa ido a kansa. 24 Mugun mutum yakan ci nasara ɗan lokaci, Daga nan sai ya yi yaushi kamar tsiro, Ya yi yaushi kamar karan dawa da aka yanke. 25 Akwai wanda zai iya cewa, ba haka ba ne? Akwai wanda zai tabbatar da cewa kalmomina ba gaskiya ba ne?”

Ayuba 25

Bildad bai Yarda Allah zai Baratar da Mutum Ba

1 Bildad ya amsa. 2 “Allah mai iko ne, duka sai a ji tsoronsa, A samaniya yake tafiya da mulkinsa da salama. 3 Akwai wanda zai iya ƙidaya mala'ikun da suke masa hidima? Akwai wurin da hasken Allah bai haskaka ba? 4 Akwai wanda ya isa ya zama adali, Ko mai tsarki a gaban Allah? 5 Hasken wata ba haske ba ne a gare shi, Ko taurari ma ba su da tsarki a gabansa. 6 To, mutum fa? Ai, wannan tsutsa ne, ɗan ƙwaro kawai. Me mutum ya daɗa a gaban Allah?”

Ayuba 26

Ayuba ya Hurta Sarautar Allah

1 Ayuba ya amsa. 2 “Kai ne mai taimakon marar ƙarfi, Kai ne mai ceton rarrauna! 3 Kai ne kake ba marar hikima shawara, Kai kake sanar da ilimi mai ma'ana a wadace! 4 Kana tsammani wane ne zai ji maganganunka duka? Wane ne ya iza ka ka yi irin wannan magana? 5 “Lahira tana rawa, Mazaunanta suna rawar jiki don tsoro. 6 Lahira tsirara take a gaban Allah, Haka kuma Hallaka take a gaban Allah. 7 Allah ne ya shimfiɗa arewa a sarari kurum, Ya rataya duniya ba bisa kan kome ba. 8 Allah ne ya cika gizagizai masu duhu da ruwa, Girgijen kuwa bai kece ba. 9 Ya rufe kursiyinsa, ya shimfiɗa girgije a kansa. 10 Ya shata da'ira a kan fuskar teku, A kan iyakar da take tsakanin haske da duhu. 11 Ginshiƙan samaniya sun girgiza, Sun firgita saboda tsautawarsa. 12 Ta wurin ƙarfinsa ya kwantar da teku, Da saninsa ya hallaka dodon ruwan nan, wato Rahab. 13 Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi garau, Ikonsa ne kuma ya sha zarar macijin nan mai gudu. 14 Amma waɗannan kaɗan ne kawai daga cikin al'amuransa. Ɗan ƙis kaɗai muke ji a kansa. Amma wa zai iya fahimtar ikon tsawarsa?”

Ayuba 27

Ayuba ya Bayyana Rabon Mugaye

1 Ayuba ya amsa. 2 “Na rantse da Allah Mai Iko Dukka, Wanda ya ƙwace mini halaliyata, Wanda ya ɓata mini rai. 3 Muddin ina numfashi, Ruhun Allah kuma yana cikin hancina 4 Bakina ba zai faɗi ƙarya ba, Harshen kuma ba zai hurta maganganun yaudara ba. 5 Allah ya sawwaƙa in ce kun yi daidai, Har in mutu ba zan daina tsare mutuncina ba. 6 Ina riƙe da adalci kam, ba kuwa zan sake shi ba, Zuciyata ba ta zarge ko ɗaya daga cikin kwanakin raina ba. 7 “Bari maƙiyina ya zama kamar mugun mutum, Wanda ya tashi gāba da ni ya zama kamar marar adalci. 8 Wace sa zuciya take ga marar tsoron Allah? Sa'ad da Allah ya datse shi, ya ɗauke ransa? 9 Allah kuwa zai ji kukansa sa'ad da wahala ta same shi? 10 Ko Mai Iko Dukka zai zama abin farin ciki a gare shi? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci? 11 “Zan koya muku zancen ikon Allah, Abin da yake na wajen Mai Iko Dukka ba zan ɓoye ba. 12 Ga shi kuwa, dukanku kun gani da kanku, Me ya sa kuka zama wawaye? 13 “Wannan shi ne rabon mugaye daga wurin Allah, Gādo ne kuma wanda azzalumai za su karɓa daga wurin Mai Iko Dukka. 14 Idan 'ya'yansu sun riɓaɓɓanya za su zama rabon takobi, Zuriyarsu kuwa ba za su sami isasshen abinci ba. 15 Waɗanda suka tsira, annoba za ta kashe su, Matansu ba za su yi makokin mutuwarsu ba. 16 Koda yake sun tsibe azurfa kamar turɓaya, Sun tara tufafi kamar ƙasa, 17 Za su tara, amma adalai za su sa, Marasa laifi ne za su raba azurfar. 18 Sun gina gidajensu kamar saƙar gizo-gizo, Kamar bukkar mai tsaro. 19 Attajirai za su kwanta, amma daga wannan shi ke nan, Za su buɗe ido su ga dukiyar nan ba ta. 20 Razana za ta auka musu kamar rigyawa. Da dare iska za ta tafi da su. 21 Iskar gabas za ta fauce su su tafi, Ta share su ta raba su da wurin zamansu. 22 Za ta murɗe su ba tausayi, Hakika za su yi ƙoƙari su tsere daga ikonsa, Sai su yi ƙundumbala. 23 Kowa zai tafa hannu ya yi musu tsaki har su tashi daga wurin da suke.”

Ayuba 28

Samun Hikima yana da Wuya

1 “Hakika akwai ma'adinai na azurfa, Da wuraren da ake tace zinariya. 2 Mutane sukan haƙo baƙin ƙarfe daga ƙasa, Sukan narkar da tagulla daga dutse. 3 Mutane sukan kawar da duhu, Sukan kuma bincike zuzzurfar iyaka, Sukan haƙo duwatsun da suke cikin duhu, duhu baƙi ƙirin. 4 Sukan haƙa loto a fadama nesa da mutane, Sukan kafa abin lilo su yi ta lilo nesa da mutane. 5 “Daga cikin ƙasa ake samun abinci, Amma a ƙarƙashinta yakan zama kamar wuta. 6 Akwai duwatsu masu daraja cikin duwatsunta, Akwai zinariya a ƙurarta. 7 Tsuntsu mai cin nama bai san wannan hanya ba. Shaho ma bai gan ta ba. 8 Namomin jeji ba su taɓa bin hanyar ba, Ko zaki ma bai taɓa binta ba. 9 “Mutane sun iya sarrafa ƙanƙarar dutse, Suna kuma iya tumɓuke tushen duwatsu. 10 Sukan haƙa magudanar ruwa cikin duwatsu, Idanunsu sukan ga kowane abu mai daraja. 11 Sukan datse rafuffuka su hana su gudu, Su binciko abin da yake ɓoye, ya fito sarari. 12 Amma ina, a ina za a iya samun hikima? A ina za a samo haziƙanci? 13 Mutane ba su san darajar hikima ba, Ba a samunta a ƙasar masu rai. 14 Zurfafa sun ce, ‘Ba ta a cikinmu,’ Tekuna kuma sun ce, ‘Ba ta tare da mu.’ 15 Ba za a saye ta da zinariya tsantsa ba. Azurfa ba za ta iya biyan tamaninta ba. 16 Ko zinariyar Ofir, ko onis, Ko saffir, wato duwatsu masu daraja, ba za su iya biyan tamaninta ba. 17 Ba daidai take da zinariya ko madubi ba, Ba za a iya musayarta da kayayyakin da aka yi da zinariya tsantsa ba. 18 Kada ma a ko ambaci murjani, Da duwatsu masu walƙiya. Gama tamanin hikima ya fi na lu'ulu'ai mafiya daraja duka. 19 Ba za a daidaita tamaninta da na duwatsun tofaz na Habasha ba. Tamaninta ya fi na zinariya tsantsa. 20 “To, daga in a hikima ta fito? A wane wuri kuma haziƙanci yake? 21 Ba talikin da ya iya ganinta, Ko tsuntsun da yake tashi sama. 22 Hallaka da Mutuwa sun ce, ‘Da kunnuwanmu mun ji ƙishinƙishin a kanta.’ 23 “Allah ne kaɗai ya san hanya zuwa gare ta, Ya san inda hikima take, 24 Saboda yana ganin duniya ɗungum, Yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sararin sama. 25 Sa'ad da Allah ya sa iska ta hura, Ya yi wa tekuna iyaka. 26 Sa'ad da ya ba da umarni ga ruwan sama, Da kuma hanyar da tsawa za ta bi, 27 Shi ya san hikimar, shi ya sanar, Ya tabbatar da ita, ya bincike ta sarai. 28 “Allah ya ce wa mutane, ‘Duba, tsoron Ubangiji shi ne hikima, Rabuwa da mugunta kuma, ita ce haziƙanci.’ ”

Ayuba 29

Ayuba ya Tuno da Farin Cikinsa na Dā

1 Ayuba ya ci gaba da magana. 2 Da ma ina cikin lokacin da ya wuce ne, Lokacin da Allah yake lura da ni, 3 Sa'ad da fitilarsa take haskaka mini, Ta wurin haskensa kuma nake tafiya da duhu, 4 Kwanakin da nake gaɓar raina, Lokacin da ni'imar Allah take kan gidana, 5 Sa'ad da Mai Iko Dukka take tare da ni, 'Ya'yana duka kuma suka kewaye ni, 6 Sa'ad da aka wanke ƙafafuna da madara, Duwatsu kama suna ɓulɓulo mini da rafuffukan mai! 7 A sa'ad da nakan tafi kofar birni, In shirya wurin zamana a dandali, 8 Da samari sun gan ni, sai su kawar da jiki, Tsofaffi kuma su miƙe tsaye, 9 Sarakuna sun yi shiru sun kame bakinsu. 10 Manyan mutane sukan yi shiru, harshensu ya liƙe a dasashi. 11 Waɗanda suka ji labarina sukan sa mini albarka, Waɗanda suka gan ni sukan yi na'am da ni. 12 Domin sa'ad da matalauta suka yi kuka, ni nake cetonsu, Nakan taimaki marayu waɗanda ba su da mai taimako. 13 Waɗanda suke bakin mutuwa sukan sa mini albarka, Na taimaki gwaurayen da mazansu suka mutu, Su raira waƙa don murna. 14 Adalci shi ne suturata, Gaskiya ita ce rigata da rawanina. 15 Ni ne idon makafi, guragu kuma, ni ne ƙafarsu. 16 Ni mahaifi ne ga matalauta, Nakan bincika don in warware al'amarin da ya dami baƙi. 17 Nakan karya muƙamuƙin marar adalci, In sa ya saki ganimar da ya kama. 18 “Da na zaci zan mutu cikin sutura, Kwanakina kuma suriɓaɓɓanya, su yi yawa kamar yashi, 19 Saiwoyina a shimfiɗe suke cikin ruwa, Dukan dare raɓa na sauka a kan rassana. 20 Darajata garau take a gare ni, Bakana kullum sabo yake a hannuna. 21 Mutane sukan kasa kunne su jira, su yi shiru Sa'ad da nake ba da shawara. 22 Bayan na gama magana ba wanda zai ƙara wata magana. Maganata takan shige su. 23 Suna jirana kamar yadda ake jiran ruwan sama, Da baki buɗe, kamar yadda ake jiran ruwan bazara. 24 Nakan yi musu murmushi sa'ad da suka fid da zuciya, Ba su yi watsi da fara'ata ba. 25 Nakan zaɓar musu hanyar da za su bi, Ina zaune kamar sarki a tsakanin mayaƙansu, Kamar mai ta'azantar da masu makoki.”

Ayuba 30

Ayuba ya yi Kuka saboda Masifunsa

1 “Amma yanzu waɗanda na girme su, sai ba'a suke mini, Waɗanda iyayensu maza ba su fi karnukan da suke kiwon garken tumakina ba. 2 Wace riba zan samu ta wurin ƙarfin hannuwansu waɗanda ba su da sauran kuzari? 3 Saboda rashi da matsananciyar yunwa sun rame, Sai gaigayar ƙasa suke yi da dare, a cikin kufai. 4 Sukan tsinki ganyaye masu ɗaci na jeji su ci, Sukan ci doyar jeji. 5 Aka kore su daga cikin mutane, Suka yi ta binsu da ihu kamar yadda ake yi wa ɓarawo, 6 Sai a kwazazzabai suke zama Da a ramummuka da kogwannin duwatsu. 7 Suka yi ta kuka a jeji, Suka taru wuri ɗaya a cikin sarƙaƙƙiya. 8 Mutane ne marasa hankali marasa suna! Aka kore su daga ƙasar. 9 “Yanzu na zama abin waƙa gare su, Abin ba'a kuma a gare su. 10 Suna ƙyamata, guduna suke yi, Da ganina, sai su tofa mini yau. 11 Domin Allah ya katse lakata, ya ƙasƙanta ni, Saboda haka sun raba ni da zuriyata, 12 A hannun dama 'yan tā da zaune tsaye sun taso mini, Sun runtume ni, sun tura ni a hanyarsu ta hallakarwa. 13 Sun datse hanyata, Sun jawo mini bala'i, Ba kuwa wanda ya hana su. 14 Sun kutsa kamar waɗanda suka karya doka, Sun auka mini da dukan ƙarfinsu kamar yadda suka yi nufi. 15 Sun firgita ni, Sun kori darajata kamar da iska, Wadatata kuma ta shuɗe kamar girgije. 16 “Yanzu zuciyata ta narke Kwanakin wahala sun same ni. 17 Da dare ƙasusuwana karkaɗuwa suke, Azaba tana ta gaigayata ba hutawa. 18 An yi mini kamun kama-karya, An ci wuyan rigata. 19 Allah ya jefar da ni cikin laka, Na zama kamar ƙura ko toka, 20 “Na yi kira gare ka, ya Allah, amma ba ka amsa mini ba, Na yi addu'a kuma, amma ba ka kula da ni ba. 21 Ka zama mugu a gare ni, Da ƙarfin dantsenka ka tsananta mini. 22 Ka jefa ni cikin guguwa, ka sa ni in hau ta, Ka yi ta shillo da ni cikin rugugin hadiri. 23 Hakika na sani za ka kai ni ga mutuwa, Gidan da aka ƙaddara wa kowane mai rai. 24 “Ashe, wanda yake gab da gagarumar hallaka, Ba zai miƙa hannu ya roƙi taimako a masifar da yake sha ba? 25 Ashe, ban yi kuka saboda wanda yake shan wahala ba? Ashe, ban yi ɓacin rai saboda matalauta ba? 26 Amma sa'ad da na sa zuciya ga alheri, sai ga mugunta, Sa'ad da nake jiran haske, sai ga duhu ya zo. 27 Zuciyata tana tafasa, ba ta kwanciya, Kwanakin wahala sun auko mini. 28 Na yanƙwane, amma ba yanƙwanewar rana ba, Na tsaya a gaban taron jama'a, ina roƙon taimako. 29 “Na zama ɗan'uwan dila, Na kuma zama aminin jiminai. 30 Fatata ta takura, ta zama baƙa, Ƙasusuwana suna zogi saboda zafi, 31 Saboda haka garayata ta zama ta makoki, Sarewata kuma ta zama muryar masu kuka.”

Ayuba 31

Ayuba ya Tabbatar da Mutuncinsa

1 “Na yi alkawari da idanuna, Me zai sa in ƙyafaci budurwa? 2 Wane rabo zan samu daga wurin Allah a Sama? Wane gādo kuma zan samu daga wurin Mai Iko Dukka a can samaniya? 3 Yakan aika da masifa da lalacewa Ga waɗanda suke aikata abin da ba daidai ba. 4 Allah ya san dukan abin da nake yi, Yana ƙididdige dukan takawata. 5 “Idan ina tafiya da rashin gaskiya, Ina hanzari don in aikata yaudara, 6 Bari Allah ya auna ni da ma'aunin da yake daidai, Zai kuwa san mutuncina. 7 Idan dai na kauce daga hanya, Ko kuwa zuciyata ta bi sha'awar idanuna, Idan akwai ko ɗan sofane a hannuna, 8 To, bari in shuka, wani ya ci amfanin, Bari a tumɓuke amfanin gonata. 9 “Idan na yi sha'awar wata mace, Har na je na laɓe a ƙofar maƙwabcina, 10 To, bari matata ta yi wa wani abinci, Bari waɗansu su kwana da ita. 11 Gama wannan mugun laifi ne ƙwarai, Wanda alƙalai ne za su hukunta. 12 Za ta zama wuta mai ci har ta hallaka, Za ta cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus. 13 “Idan a ce ban kasa kunne ga kukan barorina mata da maza ba, Sa'ad da suka kawo koke-kokensu a kaina, 14 To, wace amsa zan ba Allah sa'ad da ya tashi don ya hukuntar? Me zan iya faɗa sa'ad da Allah ya zo yi mini shari'a? 15 Ashe, shi wanda ya halicce ni a cikin mahaifa, Ba shi ne ya halicce su ba? Shi wanda ya siffata mu a cikin mahaifa? 16 “Ban taɓa ƙin taimakon matalauta ba, Ban kuma taɓa sa gwauruwar da mijinta ya mutu ta yi kuka ba, 17 Kokuwa in bar marayu da yunwa sa'ad da nake cin abincina, 18 Tun suna yara nake goyonsu, Ina lura da su kamar 'ya'yan cikina. 19 “Amma idan na ga wani yana lalacewa saboda rashin sutura, Ko wani matalauci matar abin rufa, 20 Idan a zuciyarsa bai sa mini albarka ba, Ko bai ji ɗumi da ulun tumakina ba, 21 Ko na ɗaga hannuna don in cuci maraya, Don na ga ina da kafar kuɓuta, 22 To, ka sa kafaɗuna su ɓaɓɓalle daga inda suke. Ka kakkarya gwiwoyin hannuna. 23 Gama bala'i daga wurin Allah ya razanar da ni, Saboda ɗaukakarsa ba zan iya yin kome ba. 24 “Idan na ce ga zinariya na dogara, ko zinariya tsantsa ita ce jigona, 25 Idan kuma saboda yawan dukiyata nake fariya, Ko saboda abin da na mallaka ne, 26 Idan ga hasken rana nake zuba ido, Ko ga hasken farin wata ne, 27 Zuciyata ta jarabtu ke nan a asirce, Ni da kaina ina sumbatar hannuna, 28 Wannan ma zai zama laifi ne wanda alƙalai za su hukunta, Gama na zama munafukin Allah Mai Iko Dukka ke nan. 29 “Idan na yi murna saboda wahala ta sami maƙiyana, Ko na yi fariya saboda mugun abu ya same shi, 30 Ban yi zunubi da bakina ba, Ban nemi ran wani ta wurin la'anta shi ba. 31 Ko mutanen da suke cikin alfarwata ba wanda zai ce, Ga wani can da bai ƙoshi da nama ba. 32 Ban bar baƙi su kwana a titi ba, Ƙofar gidana a buɗe take ga matafiya. 33 Idan na ɓoye laifofina a zuciyata, 34 Ko na tsaya shiru saboda tsoron taron jama'a, Saboda kuma baƙar maganar mutane ta razanar da ni, 35 Da a ce ina da wanda zai kasa kunne gare ni, Da sai in sa hannu a kan abin da na faɗa, Allah kuwa Mai Iko Dukka ya amsa mini. “Da ƙarar da maƙiyana suke kai ni, a rubuce ne, 36 Hakika da sai in ɗauke ta a kafaɗata, In kuwa naɗa ta a kaina kamar rawani. 37 Da na ba Allah dukan lissafin abin da na taɓa yi, In tinƙare shi kamar ni basarauce ne. 38 “Idan ƙasata tana kuka da ni, Ita da kunyoyinta, 39 Ko na ci amfaninta ban biya ba, Ko na yi sanadin mutuwar mai ita, 40 Ka sa ƙayayuwa su tsiro maimakon alkama, Tsire-tsire marasa amfani kuma maimakon sha'ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.

Ayuba 32

Jawaban Elihu

1 Mutanen nan uku sun daina ba Ayuba amsa, saboda yana ganin kansa adali ne. 2 Sai Elihu, ɗan Barakel, mutumin Buz, daga cikin iyalin Arama, ya husata, yana fushi da Ayuba saboda ya baratar da kansa, bai bari Allah ya baratar da shi ba. 3 Yana kuma fushi da abokan nan uku na Ayuba, domin sun rasa amsar da za su ba Ayuba, ko da yake sun hurta Ayuba ne yake da laifi. 4 Elihu ya jira sai a wannan lokaci ne ya yi magana da Ayuba, don shi ne yaro a cikinsu duka. 5 Sa'ad da Elihu ya ga mutanen nan uku ba su da wata amsa da za su ba Ayuba, sai ya yi fushi. 6 Elihu ɗan Barakel, mutumin Buz, ya fara magana, ya ce, “A shekaru dai ni yaro ne ku kuwa manya ne, Don haka ina jin nauyi, Ina kuma jin tsoro in faɗa muku ra'ayina. 7 Na ce wa kaina, ‘Ya kamata kwanaki su yi magana, Yawan shekaru kuma su koyar da hikima.’ 8 Amma Ruhun Allah Mai Iko Dukka ne wanda yake cikin mutum, Yakan ba mutane basira. 9 Ba tsofaffi ne masu wayo ba, Ba kuma masu yawan shekaru kaɗai suke gane abin da yake daidai ba. 10 Don haka na ce ku kasa kunne gare ni, Bari in faɗa muku nawa ra'ayi. 11 “Ga shi, na dakata na ji maganarku, Na kasa kunne ga maganarku ta hikima, Tun kuna tunani a kan abin da za ku faɗa. 12 Na kasa kunne gare ku sosai, Amma ko ɗaya ba wanda ya kā da Ayuba. Ba kuma wanda ya ba shi amsar tambayarsa. 13 Ku lura kada ku ce kuna da hikima, Allah ne kaɗai yake da iko ya kā da shi, ba mutum ba. 14 Ba da ni Ayuba yake magana ba, Saboda haka ba zan amsa masa da irin amsarku ba. 15 “Abin ya cika musu ciki, ba su ƙara amsawa ba, Wato ba su da ta cewa. 16 Ni kuma sai in tsaya don ba su ce kome ba? Sun tsaya kurum, don ba su da ta cewa? 17 A'a, ni kuma zan ba da tawa amsa, In kuma faɗi ra'ayina. 18 Cike nake da magana, Ruhun da ka cikina ya iza ni. 19 Ga zuciya tana kama da ruwan inabin da ba shi da mafitar iska, Kamar sabuwar salkar ruwan inabi wadda take shirin fashewa. 20 Tilas in yi magana don in huce, Dole in ba da amsa. 21 Ba zan yi wa kowa son zuciya ba, Ko kuma in yi wa wani fādanci. 22 Gama ni ban iya fādanci ba, Idan na yi haka kuwa Mahaliccina zai kashe ni nan da nan.”

Ayuba 33

Elihu ya Tsauta wa Ayuba

1 “Amma yanzu, kai Ayuba, ka yarda ka ji maganata, Ka kasa kunne ga dukan abin da zan faɗa. 2 Ga shi, na buɗe baki in yi magana. 3 Maganar da zan hurta ainihin gaskiya da take a zuciyata ce, Abin da zan faɗa kuma dahir ne. 4 Ruhun Allah ne ya yi ni, Mai Iko Dukka ya hura mini rai. 5 “Ka amsa mini, in ka iya, Ka shirya abubuwan da za ka faɗa mini, ka yi tsaye a kansu. 6 Duba, ni da kai ɗaya muke a wajen Allah, Dukanmu biyu kuma daga yumɓu aka siffata mu. 7 Don haka kada ka razana saboda ni, Abin da zan faɗa maka, ba abin da zai fi ƙarfinka. 8 “Hakika na ji maganar da ka yi, Na kuwa ji amon maganganunka, 9 Ka ce kai tsattsarka ne, ba ka da laifi, Kai tsabtatacce ne, ba ka da wata ƙazanta. 10 Ka ce Allah ya zarge ka ya ɗauke ka tankar maƙiyansa, 11 Ya saka ka a turu, Yana duban dukan al'amuranka. 12 “Amma a kan wannan, Ayuba, ka yi kuskure, zan ba ka amsa, Gama Allah ya fi kowane mutum girma. 13 Me ya sa kake yi wa Allah gunaguni, Cewa ba ya karɓar maganarka ko ɗaya? 14 Gama Allah yakan yi magana sau ɗaya ne, I, har sau biyu, duk da haka mutum ba ya lura. 15 Yakan sanar a mafarkai ko a wahayi Sa'ad da barci mai nauyi ya ɗauke su, A sa'ad da suke barci a gadajensu. 16 Yakan buɗe kunnuwan mutane, Ya tsorata su da faɗakarwarsa, 17 Domin ya kawar da su daga aikin da suke yi, Ya kuma kawar musu da girmankai. 18 Yakan hana su zuwa kabari, Ya hana ransu hallaka da takobi. 19 “Akan hori mutum da cuta mai zafi a gadonsa, Ya yi ta fama da azaba a cikin ƙasusuwansa, 20 Ransa yana ƙyamar abinci, Yana ƙyamarsa kome daɗinsa kuwa. 21 Yakan rame ƙangayau, ƙasusuwansa duk a waje. 22 Yana gab da shiga kabari, Ransa yana hannun mala'ikun mutuwa. 23 “Da a ce akwai wani mala'ika mai sulhuntawa a tsakani, Ko da ɗaya daga cikin dubu ne wanda zai faɗa wa mutum, 24 Mala'ikan da zai yi masa alheri ya ce, ‘Ka cece shi daga gangarawa zuwa cikin kabari, Na sami abin da zai fanshe shi!’ 25 Naman jikinsa zai koma kamar na saurayi, Zai komo kamar lokacin da yake gaɓar ƙarfinsa. 26 Sa'an nan ne mutum zai yi addu'a ga Allah, ya karɓe shi, Ya zo gabansa da murna, Allah zai komar wa mutum da adalcinsa. 27 Zai raira waƙa a gaban jama'a, ya ce, ‘Na yi zunubi. Ban yi daidai ba, Amma ba a sa ni in biya ba. 28 Allah ya fanshe ni daga gangarawa zuwa kabari, Raina kuwa zai ga haske.’ 29 “Ga shi kuwa, Allah ya yi dukan waɗannan abubuwa sau biyu, har ma sau uku ga mutum, 30 Don ya komo da ran mutum daga kabari, Domin a haskaka shi da hasken rai. 31 “Haba Ayuba, ka kula fa, ka kasa kunne, Ga abin da nake faɗa, Ka yi shiru, zan yi magana. 32 Amma idan kana da ta cewa, to, amsa, Yi magana, gama ina so in kuɓutar da kai. 33 In kuwa ba haka ba, sai ka yi shiru, Ka kasa kunne gare ni, Zan kuwa koya maka hikima.”

Ayuba 34

Elihu ya ga Allah ya yi Daidai

1 Elihu ya ci gaba. 2 “Ku mutane masu hikima, ku ji maganata, Ku kasa kunne ga abin da zan faɗa, ku masana. 3 Kunne yake rarrabewa da magana, Kamar yadda harshe yake rarrabewa da ɗanɗanar abinci. 4 Bari mu zaɓi abin da yake daidai, Bari kuma mu daidaita abin da yake mai kyau tsakanin junanmu. 5 Gama Ayuba ya ce, ‘Ni marar laifi ne, Amma Allah ya ƙwace mini halaliyata. 6 Duk da rashin laifina an ɗauke ni a maƙaryaci, Raunina ba ya warkuwa ko da yake ba ni da laifin kome.’ 7 “Wane irin mutum ne kai, Ayuba, Da kake shan raini kamar yadda kake shan ruwa, 8 Wanda yake cuɗanya da ƙungiyar masu aikata laifi, Kana yawo tare da mugaye? 9 Gama ka ce, ‘Bai amfana wa mutum kome ba Ya yi murna da Allah.’ 10 “Saboda haka ku kasa kunne gare ni, ku da kuke haziƙai, Sam, Allah ba mai aikata mugunta ba ne, A wurin Mai Iko Dukka ba kuskure, 11 Gama bisa ga aikin mutum yake sāka masa, Yana sa aniyarsa ta bi shi. 12 Gaskiya ce, Allah ba zai aikata mugunta ba, Mai Iko Dukka ba zai kauce wa adalci ba. 13 Wa ya shugabantar da shi a kan duniya? Wa ya mallakar masa da duniya duka? 14 Da zai amshe ruhu da numfashin da ya hura wa mutum, 15 Da duk mai rai ya hallaka, Mutum kuma ya koma ƙura. 16 “Idan kai haziƙi ne, to, ji wannan, Kasa kunne ga abin da zan faɗa. 17 Da Allah maƙiyin adalci ne, da ya yi mallaka? Ka iya sa wa Adali, Mai Iko Dukka laifi? 18 Ka iya sa wa Allah laifi, Shi da ya ce, ‘Sarki marar amfani ne, Hakimai kuma mugaye?’ 19 Ba ya nuna sonkai ga sarakuna, Ko kuma ya fi kulawa da attajira fiye da matalauta, Gama shi ya halicce su duka. 20 Sukan mutu nan da nan, Da tsakar dare manya da ƙanana sukan shuɗe farat ɗaya, An kawar da su ba da hannun mutum ba. 21 “Gama yana ganin al'amuran mutum, Yana kuma ganin dukan manufarsa. 22 Ba wani duhu, ko duhu baƙi ƙirin Inda masu aikata mugunta za su ɓuya. 23 Ba ajiyayyen lokacin da ya ajiye wa kowane mutum Da zai je shari'a a gaban Allah. 24 Yakan ragargaza ƙarfafa ba tare da wani bincike ba, Ya sa waɗansu a madadinsu. 25 Saboda sanin ayyukansu, Yakan kaɓantar da su da dare ya ragargaza su, 26 Yakan buge su a gaban mutane saboda muguntarsu, 27 Don sun daina binsa, ba su kula da ko ɗaya Daga cikin umarnansa ba. 28 Suka sa matalauta su yi kuka ga Allah, Ya kuwa ji kukan waɗanda ake tsananta wa. 29 Idan Allah zai yi shiru, da wa zai sa wa wani laifi? Idan ya ɓoye fuskarsa, wa zai iya ganinsa, Ko aka yi wa al'umma ko ga mutum? 30 Bai kamata marar tsoron Allah ya yi mulki ba, Don kada ya tura jama'a cikin tarko. 31 “Akwai wanda zai ce wa Allah, ‘Ni horarre ne, Ba zan ƙara yin laifi ba? 32 Ka koya mini abin da ban sani ba, Idan na yi laifi, ba zan ƙara yi ba.’ 33 Zai kuɓutar domin ya gamshe ka saboda ka ƙi yarda? Tilas kai za ka zaɓa, ba ni ba, Saboda haka sai ka hurta abin da ka sani. 34 “Haziƙan mutane da mutum mai hikima da suka ji ni za su ce, 35 ‘Ayuba yakan yi magana ne ba tare da sanin abin da yake yi ba, Maganarsa ba ta mai hangen nesa ba ce. 36 Da ma a gwada Ayuba har ƙarshe, Saboda amsar da yake bayarwa ta mugaye. 37 Gama ya ƙara zunubinsa da tayarwa, Yana tafa hannunsa a tsakaninmu, Yana yawaita maganganunsa gāba da Allah.’ ”

Ayuba 35

1 Elihu kuwa ya yi magana. 2 “Ayuba, ba daidai ba ne, ka ce, Ba ka yi laifi a gaban Allah ba, 3 Ka kuwa ce, ‘Wace riba na ci? Wane fifiko nake da shi fiye da idan na yi zunubi?’ 4 Zan ba ka amsa, kai da abokanka. 5 Ka duba sama, Ka dubi gizagizai waɗanda suke can sama da kai. 6 Idan ka yi zunubi, da me ka cuci Allah? Idan ka aikata laifofi da yawa, wace cuta ka yi masa? 7 Idan kai adali ne da me ka ƙara masa, Ko kuwa me ya samu daga gare ka? 8 Muguntarka ta shafi mutum ne kamarka, Haka kuma adalcinka ya shafi ɗan adam ne kawai. 9 “Saboda yawan zalunci, jama'a sukan yi kuka, Suka nemi taimako, saboda matsin masu ƙarfi. 10 Amma ba su juyo wurin Allah Mahaliccinsu ba, Wanda yakan sa a raira wanda da dare, 11 Wanda yake koya mana fiye da namomin jeji da suke a duniya, Wanda ya sa muka fi tsuntsayen sama hikima. 12 Suka yi kira don taimako, amma Allah bai amsa ba, Saboda suna da girmankan mugaye. 13 Hakika Allah bai ji holoƙon kukansu ba, Allah Mai Iko Dukka kuwa bai kula da shi ba. 14 “Ayuba, kai wane ne da za ka ce ba ka gan shi ba? Da kake cewa ƙararka tana gabansa, Jiransa kake yi? 15 Yanzu fa saboda bai yi hukunci da fushinsa ba, Kamar kuma bai kula da laifi ba, 16 Ayuba, maganarka marar ma'ana ce, Ka yi ta maganganu marasa hikima.”

Ayuba 36

Elihu ya Ɗaukaka Girman Allah

1 Elihu ya ci gaba da magana. 2 “Ka yi mini haƙuri kaɗan, ni kuwa zan nuna maka, Gama har yanzu ina da abin da zan faɗa in kāre Allah. 3 Zan tattaro ilimina daga nesa, In bayyana adalcin Mahaliccina. 4 Gaskiya nake faɗa ba ƙarya ba, Wanda yake da cikakken sani yana tare da kai. 5 “Ga shi kuwa, Allah Mai Girma, ba ya raina kowa, Shi mai girma ne, mai cikakkiyar basira. 6 Ba ya rayar da masu laifi, Amma yakan ba waɗanda ake tsananta wa halaliyarsu. 7 Yakan kiyaye waɗanda suke aikata gaskiya, Yakan kafa su har abada tare da sarakuna, A gadon sarauta, ya ɗaukaka su. 8 Amma idan aka ɗaure su da sarƙoƙi, Da kuma igiyar wahala, 9 Sa'an nan yakan sanar da su aikinsu Da laifofin da suke yi na ganganci. 10 Yakan sa su saurari koyarwa, Da umarnai, cewa su juya, su bar mugunta. 11 Idan suka kasa kunne suka bauta masa, Za su cika kwanakinsu da wadata, Shekarunsu kuma da jin daɗi. 12 Amma idan ba su kasa kunne ba, Za a hallaka su da takobi, Su mutu jahilai. 13 “Waɗanda ba su da tsoron Allah a zuciyarsu, Suna tanada wa kansu fushi, Ba su neman taimako sa'ad da ya ɗaure su. 14 Sukan yi mutuwar ƙuruciya, Sukan ƙare kwanakinsu da kunya. 15 Zai kuɓutar da waɗanda suke shan tsanani, Ta wurin tsananin da suke sha, Yakan buɗe kunnuwansu ta wurin shan wahala. 16 Allah ya tsamo ka daga cikin wahala, Ya kawo ka yalwataccen wuri inda ba matsi, Abincin da aka yi na addaras aka jera maka a kan tebur. 17 “Ka damu ƙwarai don ka ga an hukunta mugaye, Amma hukunci da adalci sun kama ka. 18 Ka lura kada ka bar hasalarka ta sa ka raina Allah, Kada kuma ka bar wahalar da kake sha ta sa ka ɓata da mai fansarka. 19 Kukanka ya iya raba ka da wahala, Ko kuwa dukan ƙarfin da kake da shi? 20 Kada ka ƙosa dare ya yi, Domin a lokacin nan ne mutane sukan watse, Kowa ya kama gabansa. 21 Ka lura kada ka rinjayu a kan aikata mugunta, Gama saboda haka kake shan wannan tsanani, Don a tsare ka daga aikata mugunta. 22 “Duba, Allah Maɗaukaki ne cikin ikonsa, Wa ya iya koyarwa kamarsa? 23 Ba wanda zai iya tsara wa Allah abin da zai yi, Wa ya isa ya ce masa ya yi kuskure? 24 “Ka tuna ka girmama aikinsa, Wanda mutane suke yabo. 25 Dukan mutane sun ga ayyukansa, Sun hango shi daga nesa. 26 Ga shi kuwa, Allah Maɗaukaki ne, Ba mu kuwa san iyakar ɗaukakarsa ba, Yawan shekarunsa ba su bincikuwa. 27 “Allah yakan sa ruwa ya zama tururi, Ya maishe shi ruwan sama, 28 Wanda yakan kwararo daga sama, Ya zubo wa ɗan adam a yalwace. 29 Wa zai iya gane yadda gizagizai suke shimfiɗe a sararin sama, Da tsawar da ake yi a cikinsu? 30 Ga shi, yakan baza waƙiya kewaye da shi, Yakan rufe ƙwanƙolin duwatsu. Zurfin teku yana nan da duhunsa. 31 Gama ta haka yakan shara'anta mutane, Yakan ba da abinci a yalwace. 32 Ya cika hannunsa da walƙiya, Yakan sa ta faɗa a kan abin da ya bārata. 33 Tsawarta tana nuna kasancewar Allah, Ko shanu sun san da zuwan hadiri.”

Ayuba 37

1 “Saboda wannan zuciyata takan kaɗu, Kamar ta yi tsalle daga inda take. 2 Ku kasa kunne ga tsawar muryarsa, Ku saurara ga maganarsa mai ƙarfi. 3 Yakan sako ta a ƙarƙashin samaniya duka, Walƙiyarsa takan zagaya dukan kusurwoyin duniya. 4 Bayan walƙiyar akan ji rugugin muryarsa, Ya yi tsawa da muryarsa ta ɗaukaka, Ko da yake an ji muryarsa bai dakatar da tsawar ba. 5 Muryar tsawar Allah mai banmamaki ce, Yana aikata manyan abubuwa da suka fi ƙarfin ganewarmu. 6 Yakan umarci dusar ƙanƙara ta fāɗo bisa duniya, Yayyafi da ruwan sama kuwa su yi ƙarfi. 7 Yakan tsai da kowane mutum daga aikinsa, Domin dukan mutane su san aikinsa. 8 Namomin jeji sukan shiga wurin kwanciyarsu, Su yi zamansu a ciki. 9 Guguwa takan taso daga inda take, Sanyi kuma daga cikin iska mai hurawa. 10 Numfashin Allah yakan sa ƙanƙara, Yakan sa manyan ruwaye su daskare farat ɗaya. 11 Yakan cika girgije mai duhu da ruwa, Gizagizai sukan baza walƙiyarsa. 12 Sukan yi ta kewayawa ta yadda ya bishe su, Don su cika dukan abin da ya umarce su a duniya da ake zaune a ciki. 13 Allah yakan aiko da ruwan sama ya shayar da duniya, Saboda tsautawa, ko saboda ƙasa, ko saboda ƙauna. 14 “Ka ji wannan, ya Ayuba, Tsaya ka tuna da ayyukan Allah masu banmamaki. 15 Koka san yadda Allah yakan ba su umarni, Ya sa walƙiyar girgijensa ta haskaka? 16 Ko kuma ka san yadda gizagizai suke tsaye daram a sararin sama? Ayyukan banmamaki na Allah, cikakken masani! 17 Ko ka san abin da yake sa ka jin gumi Sa'ad da iskar kudu take hurowa? 18 Ka iya yin yadda ya yi, Kamar yadda ya shimfiɗa sararin sama daram, Kamar narkakken madubi? 19 Ka koya mana abin da za mu faɗa masa, Ba za mu iya gabatar da ƙararrakinmu ba, gama mu dolaye ne. 20 A iya faɗa masa, cewa zan yi magana? Mutum ya taɓa so a haɗiye shi da rai? 21 “A yanzu dai mutane ba su iya duban haske, Sa'ad da yake haskakawa a sararin sama, Bayan da iska ta hura ta share gizagizai sarai. 22 Daga arewa wani haske kamar na zinariya ya fito mai banmamaki, Allah yana saye da ɗaukaka mai bantsoro. 23 Mai Iko Dukka, ya fi ƙarfin ganewarmu, Shi mai girma ne, da iko, da gaskiya, Da yalwataccen adalci, Ba ya garari. 24 Saboda haka mutane suke tsoronsa, Bai kula da waɗanda suke ɗaukar kansu su masu hikima ba ne.”

Ayuba 38

Ubangiji ya Tabbatar da Jahilcin Ayuba

1 Ubangiji ya yi magana da Ayuba ta cikin guguwa. 2 “Wane ne wannan da yake ɓāta shawara Da maganganu marasa ma'ana? 3 Ka tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji, Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa. 4 A ina kaka sa'ad da na aza harsashin gina duniya? Faɗa mini idan ka sani. 5 Wane ne ya zayyana kusurwoyinta? Hakika ka sani. Wane ne kuma ya auna ta? 6 A kan me aka kafa tushenta? Wa ya aza dutsen kan kusurwarta? 7 Sa'ad da taurarin asuba suka raira waƙa tare, Sai mala'iku duka suka yi sowa saboda murna. 8 “Wa ya yi wa teku iyaka Sa'ad da ta tumbatso daga zurfafa? 9 Sa'ad da na suturta ta da gizagizai, Na yi mata maɗauri da duhu ƙirin. 10 Na sa mata iyakoki, Na sa mata ƙyamare da ƙofofi, 11 Na ce mata, ‘Iyakar inda za ki tsaya ke nan, Ba za ki wuce ba. Nan raƙuman ruwanki masu tumbatsa za su tsaya.’ 12 “Ayuba, a dukan kwanakinka Ka taɓa umartar wayewar gari, Ko ka sa alfijir ya keto? 13 Da gari ya waye, Ka kawar da muguntar da ake yi da dare? 14 Yakan sāke kamar lakar da take ƙarƙashin hatimi, Yakan rine kamar riga. 15 Akan hana wa mugaye haske, Sa'ad da sukan ɗaga hannuwansu sama akan kakkarya su. 16 “Ko ka taɓa shiga cikin maɓuɓɓugan teku? Ka taɓa yin tafiya a cikin zurfin lallokin teku? 17 An taɓa nuna maka ƙofofin mutuwa? Ko kuwa ka taɓa ganin ƙofofin duhu ƙirin? 18 Ko ka san iyakar fāɗin duniya? Ka amsa mini in ka san dukan waɗannan. 19 “Ina hanya zuwa wurin da haske yake? A ina kuma duhu yake? 20 Ka san iyakarsa ko mafarinsa? 21 Ka sani, gama a lokacin nan an haife ka, Shekarunka kuwa suna da yawa. 22 “Ka taɓa shiga rumbunan dusar ƙanƙara? Ko kuwa ka taɓa shiga rumbunan ajiyar ƙanƙara? 23 Na adana su ne don lokacin wahala, Domin ranar faɗa da ta yaƙi. 24 Ina hanya zuwa inda rana take fitowa, Ko kuma ta inda iskar gabas take hurowa ta māmaye ko'ina? 25 “Wa ya haƙa hanyar da ruwan sama mai kwararowa zai bi? Da kuma hanyar da gatarin aradu zai bi? 26 Wa ya kuma kawo ruwan sama a ƙasar da ba mutane, Da a cikin hamada inda ba kowa, 27 Don a shayar da zozayar ƙasa inda ba kowa, Har ta tsiro da ciyayi? 28 “Ruwan sama yana da mahaifi? Wa ya haifi ɗiɗɗigar raɓa? 29 Wace ce mahaifiyar ƙanƙara? Wace ce kuma ta haifi jaura? 30 Ruwa ya daskare ya yi ƙarfi kamar dutse, Teku ta daskare. 31 “Za ka iya ɗaure sarƙoƙin kaza-da-'ya'yanta? Ko ka iya kwance igiyoyin mafarauci-da-kare-da-zomo? 32 Za ka iya bi da yaneyanen sararin sama bisa ga fasalinsu? 33 Ka san ka'idodin sammai? Ko ka iya faɗar yadda suka danganta da duniya? 34 “Kana iya yi wa gizagizai tsawa, Don su kwararo ruwan sama, ya rufe ka? 35 Ka iya aikar walƙiyoyi su tafi, Sa'an nan su ce maka, ‘Ga mu mun zo?’ 36 Wa ya sa hikima a gizagizai, Ko kuma wa ya ba da ganewa ga kāsashi? 37 Akwai mai hikimar da zai iya ƙidaya gizagizai? Ko kuwa wa zai iya karkato da salkunan ruwan sammai, 38 Sa'ad da ƙura ta murtuke ta taru jingim, ta game kam? 39 “Ka iya farauto wa zakoki abinci? Ko ka ƙosar da yunwar sagarun zakoki, 40 Sa'ad da suke fako a kogwanninsu, Ko suna kwance suna jira a maɓoyarsu? 41 Wa yake tanada wa hankaka abincinsa, Sa'ad da 'ya'yansa suke kuka ga Allah, Suna kai da kawowa saboda rashin abinci?”

Ayuba 39

1 “Ka san lokacin da awakan dutse suke haihuwa? Ka taɓa lura da yadda batsiya take haihuwa? 2 Ka san ko watanni nawa suke yi kafin su haihu? Ka san lokacin haihuwarsu? 3 Ka san lokacin naƙudarsu, sa'ad da suke haihuwar 'ya'yansu, Lokacin da 'ya'yansu suke fita cikinsu? 4 'Ya'yansu sukan yi ƙarfi su girma a fili cikin saura, Sukan yi tafiyarsu ba su komawa wurin iyayensu. 5 “Wa ya bar jakin jeji ya yi yadda yake so? Wa ya ɓalle dabaibayin jaki mai sauri, 6 Wanda na ba fili fetal ya zama gidansa, Da ƙasa mai gishiri a wurin zamansa? 7 Yakan yi wa hayaniyar birane ba'a, Ba ruwansa da tsawar masu kora. 8 Tsaunukan duwatsu ne wurin kiwonsa, A can yake neman kowane ɗanyen abu. 9 “Kutunkun ɓauna zai yarda ya yi maka aiki? Zai yarda ya kwana ɗaya a dangwalinka? 10 Ka iya ɗaure shi da igiya a kwarin kunya? Ko kuwa zai yi maka kaftu a fadamarka? 11 Za ka dogara gare shi saboda tsananin ƙarfinsa? Za ka kuma bar masa aikinka? 12 Ka gaskata zai komo, Ya kawo maka hatsi a masussukarka? 13 “Jimina takan karkaɗa fikafikanta da alfarma! Amma ba su ne gashin fikafikan ƙauna ba. 14 Jimina takan bar wa ƙasa ƙwayayenta, Ta bar ƙasa ta ɗumama su. 15 Takan manta wani ya iya taka su su fashe, Ya yiwu kuma wani naman jeji ya tattake su. 16 Takan yi wa 'ya'yanta mugunta, Sai ka ce ba nata ba ne, Ko da yake ta sha wahala a banza, Duk da haka ba ta damu ba. 17 Gama Allah bai ba ta hikima ba, Bai kuwa ba ta fahimi ba. 18 Amma sa'ad da ta sheƙa a guje, Takan yi wa doki maguji da mahayinsa dariya. 19 “Kai ka yi wa doki ƙarfinsa? Kai ne kuma ka daje wuyansa da geza? 20 Kai ne ka sa shi tsalle kamar ɗango? Kwarjinin firjinsa yana da bantsoro. 21 Yakan yi nishi a fadama, Yana murna saboda ƙarfinsa, A wurin yaƙi ba ya ja da baya, ba ya jin tsoron kibau. 22 Tsoro abin dariya ne a gare shi, bai damu ba. Ba ya da baya ga takobi, 23 Kibau na ta shillo a kansa, Māsu suna ta gilmawa a gabansa. 24 Da tsananin fushi da hasala yana kartar ƙasa, Da jin ƙarar ƙaho, sai ya yi ta zabura. 25 Sa'ad da aka busa ƙaho yana ce, ‘Madalla.’ Yakan ji warin yaƙi daga nesa, da hargowar sarakunan yaƙi da ihunsu. 26 “Ta wurin hikimarka ne shirwa take tashi, Ta buɗe fikafikanta ta nufi kudu? 27 Ta wurin umarninka ne gaggafa take tashi sama Ta yi sheƙarta can ƙwanƙoli? 28 A kan dutse take zaune, a can take gidanta, Cikin ruƙuƙin duwatsu. 29 Daga can takan tsinkayi abincinta Idanunta sukan hango shi tun daga nesa. 30 'Yayanta sukan tsotsi jini, A inda kisassu suke, can take.”

Ayuba 40

1 Ubangiji ya yi wa Ayuba magana. 2 “Mai neman sa wa wani laifi ya jā da Mai Iko Dukka? Wanda yake gardama da Allah, bari ya ba da amsa.” 3 Ayuba ya amsa wa Ubangiji ya ce, 4 “Ai, ni ba a bakin kome nake ba, Wace amsa zan ba ka? Na rufe bakina na yi gam. 5 Ai, na riga na yi magana sau ɗaya, har ma sau biyu, Ba zan amsa ba, ba zan ƙara cewa kome ba.”

Bayyanuwar Ikon Allah

6 Sa'an nan Ubangiji ya amsa wa Ayuba daga cikin guguwa, ya ce, 7 “Tashi tsaye ka sha ɗamara kamar namiji, Zan yi maka tambaya, kai kuwa ka ba ni amsa. 8 Kai kanka za ka sa mini laifi? Za ka kā da ni don kai ka barata? 9 Kana da ƙarfi kamar na Allah? Kana iya tsawa da murya kamar tasa? 10 “Ka caɓa ado da kwarjini da ɗaukaka, Ka yafa daraja da maƙami. 11 Ka kwararar da rigyawar fushinka, Ka dubi dukan wanda yake alfarma, a wulakance. 12 Ka dubi dukan wanda yake alfarma ka ƙasƙantar da shi, Ka tattake mugaye a inda suke. 13 Dukansu ka binne su a ƙasa, Ka ɗaure fuskokinsu, ka jefa su a lahira. 14 Sa'an nan ni kaina kuma zan sanar da kai, Cewa da hannun damanka za ka yi nasara. 15 “Ga dorina wanda ni na halicce ta, Kamar yadda na halicce ka, Tana cin ciyawa kamar sa. 16 Ga shi, ƙarfinta yana cikin ƙugunta, Ikonta yana cikin tsakar cikinta. 17 Na yi mata wutsiya miƙaƙƙiya, mai ƙarfi kamar itacen al'ul, Jijiyoyin cinyoyinta suna haɗe wuri ɗaya 18 Ƙasusuwanta bututun tagulla ne, Gaɓoɓinta kamar sandunan ƙarfe ne. 19 “Ita ce ta farko cikin ayyukan Allah, Sai Mahaliccinta kaɗai yake iya tunkararta da takobi! 20 Gama duwatsu suke ba ta abinci, A inda dukan namomin jeji suke wasa. 21 Takan kwanta a inuwar ƙaddaji, Ta ɓuya a cikin iwa, da a fadama. 22 Gama inuwar da take rufe ta ta ƙaddaji ce, Itatuwan wardi na rafi, sun kewaye ta. 23 Ga shi, ba ta jin tsoron tumbatsar kogi, A natse take, ko da ta bakinta rigyawar Urdun take wucewa. 24 Akwai wanda zai iya kama ta da ƙugiya, Ko ya sa mata asirka?”

Ayuba 41

1 “Ka iya kama dodon ruwa da ƙugiyar kama kifi? Ko kuma ka iya zarge harshensa da igiya? 2 Ka iya sa wa hancinsa asirka? Ko ka iya huda muƙamuƙinsa da ƙugiya? 3 Zai ta yi maka godo? Zai yi maka magana da tattausar murya? 4 Zai ƙulla alkawari da kai, Cewa zai zama baranka har abada? 5 Za ka yi wasa da shi kamar yadda za ka yi da tsuntsu? Ko za ka ɗaure shi da tsarkiya domin barorinka mata? 6 'Yan kasuwa za su saye shi? Za su karkasa shi ga fatake? 7 Za ka iya huhhuda fatarsa da zaguna? Kokuwa kansa da māsu? 8 In ka kama shi, ka daɗe kana tunawa da yaƙin da ba za ka ƙara marmarin yi ba! 9 Ba ma amfani a yi ƙoƙarin kama shi, Tunanin yin haka ma abin tsoro ne. 10 Ba wani mai zafin hali da zai kuskura ya tsokane shi. Wane ne wannan da zai iya tsayawa a gabana? 11 Wa ya ba ni har da zan biya shi? Dukan abin da yake cikin duniyar nan nawa ne. 12 “Ba zan yi shiru a kan zancen gaɓoɓinsa ba, Ko babban ƙarfinsa, ko kyan ƙirarsa. 13 Wa zai iya yaga babbar rigarsa? Kokuwa ya kware sulkensa da aka ninka biyu? 14 Wa zai iya buɗe leɓunansa? Gama haƙoransa masu bantsoro ne. 15 An yi gadon bayansa da jerin garkuwoyi ne, An haɗa su daɓa-daɓa kamar an liƙe. 16 Suna haɗe da juna gam, Ko iska ba ta iya ratsa tsakaninsu. 17 Sun manne da juna har ba su rabuwa. 18 Atishawarsa takan walƙata walƙiya, Idanunsa kuma kamar ketowar alfijir. 19 Harsunan wuta kamar jiniya suna fitowa daga bakinsa, Tartsatsin wuta suna ta fitowa. 20 Hayaƙi na fita daga hancins Kamar tururi daga tukunya mai tafasa, Ko bāgar da ta kama wuta. 21 Numfashinsa yakan kunna gawayi, Harshen wuta yana fita daga bakinsa. 22 A wuyansa ƙarfi yake zaune, Razana tana rausaya a gabansa. 23 Namansa yana ninke, manne da juna, Gama ba ya motsi. 24 Zuciyarsa tana da ƙarfi kamar dutse, Ƙaƙƙarfa kamar dutsen niƙa. 25 Sa'ad da ya miƙe tsaye, ƙarfafa sukan tsorata, Su yi ta tutturmushe juna. 26 Ko an sare shi da takobi, Ko an nashe shi da māshi ko hargi, ko an jefe shi, Ba sa yi masa kome. 27 Kamar ciyawa baƙin ƙarfe yake a gare shi, Tagulla ma kamar ruɓaɓɓen itace take. 28 Kibiya ba za ta sa ya gudu ba, Jifar majajjawa a gare shi kamar jifa da tushiyoyi ce. 29 A gare shi kulake kamar tushiyoyi ne, Kwaranniyar karugga takan ba shi dariya. 30 Kaifin ƙamborin cikinsa kamar tsingaro ne. Yana jan ciki a cikin laka kamar lular ƙarfe. 31 Yakansa zurfafa su tafasa kamar tukunya, Teku kuwa kamar kwalabar man shafawarsa. 32 Idan yana wucewa sai a ga hasken dārewar ruwa, Yakansa zurfafa su yi kumfa. 33 A duniya ba kamarsa, Taliki ne wanda ba shi da tsoro. 34 Yakan dubi kowane abu da yake mai alfarma, Shi sarki ne a bisa dukan masu girmankai.”

Ayuba 42

Ayuba ya Tuba aka kuma Karɓe Shi

1 Ayuba ya amsa wa Ubangiji. 2 “Na sani kai kake da ikon yin dukan abu, Ba wanda ya isa ya hana ka yin abin da ka nufa. 3 Wane ne wannan marar ilimi da zai ɓoye shawara? Saboda haka na hurta abin da ban gane ba, Abubuwa waɗanda ban gane ba suna banmamaki ƙwarai. 4 Ka ce, ‘Kasa kunne, zan yi magana da kai, Zan yi maka tambaya, ka ba ni amsa.’ 5 Dā jin labarinka nake, Amma yanzu na gan ka ido da ido. 6 Saboda haka na ga ni ba kome ba ne, Na tuba, ina hurwa da ƙura da toka.”

Ƙarshen Magana

7 Bayan da Ubangiji ya gama faɗa wa Ayuba waɗannan magana, sai ya ce wa Elifaz, mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokan nan naka biyu, gama ba ku faɗi gaskiya game da ni, kamar yadda bawana Ayuba ya yi ba. 8 Yanzu fa, sai ku kama bijimai bakwai da raguna bakwai, ku kai wa Ayuba, ku miƙa su hadaya ta ƙonawa domin kanku. Ayuba zai yi addu'a dominku, ni kuwa zan amsa addu'arsa don kada in sāka muku bisa ga wautarku. Gama ba ku faɗi gaskiya game da ni kamar yadda bawana Ayuba ya yi ba.” 9 Sai Elifaz mutumin Teman, da Bildad mutumin Shuwa, da Zofar mutumin Na'ama suka tafi suka yi kamar yadda Ubangiji ya faɗa musu, Ubangiji kuwa ya karɓi addu'ar Ayuba.

Allah ya Mayar wa Ayuba da Wadatarsa

10 Ubangiji kuwa ya mayar wa Ayuba da dukiyarsa, sa'ad da ya yi addu'a domin abokansa, sai Ubangiji ya mayar masa da riɓin abin da yake da shi dā. 11 Sa'an nan dukan 'yan'uwan Ayuba mata da maza da dukan waɗanda suka san shi a dā, suka zo gidansa suka ci abinci tare da shi, suka yi juyayin abin da ya same shi, suka ta'azantar da shi, saboda dukan wahalar da Ubangiji ya aukar masa. Kowannensu ya ba shi 'yan kuɗi da zoben zinariya. 12 Ubangiji ya sa wa wannan zamani na Ayuba albarka, har fiye da na farko. An ba shi tumaki dubu goma sha huɗu (14,000 ), da raƙuma dubu shida (6,000 ), da takarkari dubu biyu (2,000 ), da jakai mata dubu ɗaya (1,000 ). 13 Ya kuma haifi 'ya'ya maza bakwai, mata uku. 14 Ya raɗa wa ta farin suna Yemima, da ta biyun Keziya, da ta ukun Keren-Haffuk. 15 Duk ƙasar ba 'yan mata kyawawa kamar 'ya'yan Ayuba. Mahaifinsu kuwa ya ba su gādo tare da 'yan'uwansu maza. 16 Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba'in bayan wannan, ya ga 'ya'yansa, ya ga jikokin jikokinsa har tsara ta huɗu. 17 Sa'an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.

Zabura 1

Farin Ciki na Gaskiya

1 Albarka ta tabbata ga mutumim da Ba ya karɓar shawarar mugaye, Wanda ba ya bin al'amuran masu zunubi, Ko ya haɗa kai da masu wasa da Allah. 2 Maimakon haka, yana in daɗin karanta shari'ar Allah, Yana ta nazarinta dare da rana. 3 Yana kama da itacen da yake a gefen ƙorama, Yakan ba da 'ya'ya a kan kari, Ganyayensa ba sa yin yaushi, Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi. 4 Amma mugaye ba haka suke ba, Su kamar yayi suke wanda iska take kwashewa. 5 Allah kuwa zai hukunta mugaye, Masu zunubi kuwa za a ware su daga adalai. 6 Gama Ubangiji yana lura da al'amuran adalai, Amma al'amuran mugaye za su watse.

Zabura 2

Mulkin sarkin da Ubangiji ya Zaɓ

1 Don me al'ummai suke shirin tayarwa? Don me waɗannan mutane suke ƙulla shawarwarin banza? 2 Sarakunan duniya sun yi tayarwa, Masu mulkinsu suna shirya maƙarƙashiya tare, Gāba da Ubangiji da zaɓaɓɓen sarkinsa. 3 Suna cewa, “Bari mu 'yantar da kanmu daga mulkinsu, Bari mu fice daga ƙarƙashinsu!” 4 Ubangiji ya yi dariya daga kan kursiyinsa can Sama, Ya mai da su abin dariya. 5 Ya yi musu magana da fushi, Ya razanar da su da hasalarsa, 6 Ya ce, “A bisa Sihiyona, dutsena tsattsarka, Na naɗa sarkina.” 7 Sarkin ya ce, “Zan yi shelar abin da Ubangiji ya hurta. Ubangiji ya ce mini, ‘Kai ɗana ne, Yau ne na zama mahaifinka. 8 Ka yi roƙo, zan kuwa ba ka dukan al'ummai, Dukan duniya kuma za ta zama taka. 9 Za ka mallake su da sandan ƙarfe, Za ka farfashe su kamar tukunyar yumɓu.’ ” 10 Yanzu ku kasa kunne gare ni, ku sarakuna, Ku mai da hankali, ku mahukunta! 11 Ku bauta wa Ubangiji da tsoro, Ku yi rawar jiki, ku rusuna masa, 12 Ku yi mubaya'a da Ɗan, Idan kuwa ba haka ba zai yi fushi da ku, za ku kuwa mutu, Gama yakan yi fushi da sauri. Albarka ta tabbata ga dukan masu zuwa gare shi neman mafaka!

Zabura 3

Addu'ar Safe ta Dogara ga Alla

1 Ina da maƙiya da yawa, ya Ubangiji, Da yawa kuma sun juya, suna gāba da ni! 2 Suna magana a kaina, suna cewa, “Allah ba zai taimake shi ba!” 3 Amma kai, ya Ubangiji, kullum kana kiyaye ni daga hatsari, Kana ba ni nasara, Kana kuma maido mini da ƙarfin halina. 4 Na yi kira wurin Ubangiji domin taimako, Ya kuwa amsa mini daga tsattsarkan dutsensa. 5 Na kwanta na yi barci, Na kuwa tashi lafiya lau, Gama Ubangiji yana kiyaye ni. 6 Ba na jin tsoron dubban abokan gāba Waɗanda suka kewaye ni ta kowane gefe. 7 Ka zo, ya Ubangiji! Ka cece ni, ya Allahna! Ka yi nasara a kan dukan abokan gābana, Ka hallakar da dukan mugaye. 8 Ceto yana zuwa daga wurin Ubangiji, Bari ya sa wa jama'arsa albarka!

Zabura 4

Addu'ar Maraice ta Dogara ga Alla

1 Ka amsa mini sa'ad da na yi kira, Ya Allah, madogarata! Lokacin da nake shan wahala, ka zama mai taimakona. Ka yi mini alheri, ka kuma saurari addu'ata! 2 Ku mutanen nan, sai yaushe za ku daina zagina? Sai yaushe za ku daina ƙaunar abubuwan banza, Da bin abin da yake na ƙarya? 3 Ku tuna fa, Ubangiji ne ya zaɓe ni domin in zama nasa, Ya kuma ji ni lokacin da na yi kira gare shi. 4 Ku ji tsoro, ku daina aikata zunubinku, Ku yi tunani da gaske a kan wannan A kaɗaice, shiru, a ɗakunanku. 5 Ku miƙa wa Ubangiji hadayun da suka dace, Ku kuma dogara gare shi. 6 Akwai mutane da yawa da suke cewa, “Da ma a sa mana albarka!” Ka dube mu da alheri, ya Ubangiji! 7 Farin cikin da ka ba ni mai yawa ne, Fiye da na waɗanda suke da wadataccen hatsi da ruwan inabi. 8 Da zarar na kwanta, sai barci ya kwashe ni, Kai kaɗai kake kiyaye ni sosai, ya Ubangiji.

Zabura 5

Addu'ar Neman Tsari daga Mugay

1 Ka kasa kunne ga kalmomina, ya Ubangiji, Ka kuma ji ajiyar zuciyata. 2 Ya Sarkina, Allahna, Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako. 3 A gare ka zan yi addu'a, ya Ubangiji, Da safe za ka ji muryata, Da hantsi zan yi addu'ata, In kuma jira amsa. 4 Kai ba Allah mai yarda da aikin kuskure ba ne, Ba ka yarda da mugunta a gabanka. 5 Ba ka jurewa da ganin mutane masu fāriya, Kana ƙin mugaye. 6 Kakan hallakar da duk maƙaryata, Kakan raina masu ta da hankali da masu ruɗi. 7 Amma ni, ina iya zuwa wurinka, Saboda ƙaunarka mai girma, In yi sujada a tsattsarkan Haikalinka, In kuma rusuna maka da bangirma. 8 Ina da abokan gāba da yawa, ya Ubangiji, Ka bi da ni in aikata nufinka, Ka kuma fayyace mini hanyarka domin in bi ta! 9 Abin da maƙiyana suke faɗa, Ba abin da za a yarda da shi ba ne, Su dai, so suke su hallakar kawai, Bakinsu kamar buɗaɗɗen kabari yake, Maganganunsu kuwa suna da taushi da kuma yaudara. 10 Ka kāshe su, ka hukunta su, ya Allah Ka watsar da mugayen shirye-shiryensu, Ka kore su daga gabanka sabili da yawan zunubansu, Da kuma tayarwar da suke yi maka. 11 Duk waɗanda suka fake gare ka za su yi farin ciki, Kullum za su yi ta raira waƙa domin murna. Kana kiyaye waɗanda suke ƙaunarka, Suna kuwa matuƙar murna saboda kai. 12 Ka sa wa masu yi maka biyayya albarka, ya Ubangiji, Alherinka yana kāre su kamar gārkuwa.

Zabura 6

Addu'ar Neman Jinƙai a Lokacin Wahal

1 Ya Ubangiji, kada ka yi fushi, ka kuma tsauta mini! Kada ka hukunta ni da fushinka! 2 Ka ji tausayina, gama na gaji tiƙis, Ka wartsarkar da ni, gama na tafke sarai. 3 Duk na damu ƙwarai da gaske. Sai yaushe wannan zai ƙare, ya Ubangiji? 4 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni, Gama kana ƙaunata, ka kuɓutar da ni daga mutuwa. 5 Ba za a tuna da kai a lahira ba, Ba wanda zai yabe ka a can! 6 Na gaji tiƙis saboda baƙin ciki, Kowane dare gadona yakan jiƙe saboda kukana. Matashin kaina ya yi sharkaf da hawaye. 7 Idanuna sun yi kumburi saboda yawan kuka, Har da ƙyar nake iya gani, Duk kuwa saboda abokan gābana! 8 Ku tafi daga nan, ku masu aikin mugunta! Ubangiji yana jin kukana. 9 Yana kasa kunne ga kukana na neman taimako, Yana kuwa amsa addu'o'ina. 10 Abokan gābana duka za su sha kunyar fāɗuwarsu, Suna cikin matsanancin ruɗami, Za a kwashe su farat ɗaya.

Zabura 7

Addu'ar Neman a Yi Adalc

1 Ya Ubangiji, Allahna, na sami mafaka a wurinka, Ka cece ni, ka tserar da ni daga dukan masu fafarata, 2 Idan ba haka ba kuwa, za su ɗauke ni, Su tafi da ni zuwa wurin da ba wanda zai cece ni, A can za su yayyage ni kamar zaki. 3 Ya Ubangiji, Allahna, idan na aikata ɗaya daga cikin waɗannan, Wato idan na yi wa wani laifi, 4 Idan na ci amanar abokina, Ko kuwa in na gwada wa maƙiyi fin ƙarfi ba dalili, 5 To, bari abokan gābana su fafare ni, su kama ni, Bari su datse ni har ƙasa, su kuma kashe ni, Su bar ni ƙasa, matacce! 6 Ka tashi da fushinka, ya Ubangiji, Ka kuma tashi ka yi gāba da hasalar abokan gābana! Ka tashi, ka taimake ni, gama adalci kake so a yi. 7 Ka tattaro dukan kabilun da suke kewaye da kai, Ka yi mulki a kansu daga Sama. 8 Ya Ubangiji, kai ne alƙalin dukan mutane. Ka shara'anta mini bisa ga adalcina, Gama ba ni da laifi, ina kuma da kirki. 9 Ka tsai da muguntar mugaye, Ina roƙonka, ka sāka wa mutanen kirki. Kai Allah mai adalci ne, Kana kuwa auna tunanin mutane, da marmarinsu. 10 Allah ne mai kiyaye ni, Yakan ceci waɗanda suke yi masa biyayya. 11 Allah alƙali ne mai adalci, Kullum kuwa yana kā da mugaye. 12 Idan mutane ba su tuba ba, Allah zai wasa takobinsa, 13 Zai ɗana bakansa ya shirya shi, Zai ɗauki makamansa masu dafi, Ya kuma auna kibansa masu wuta. 14 Ka duba, yadda mugu yake tunanin mugunta a ransa, Yana shisshirya wahala, yana kuma aikata ruɗi. 15 Yana haƙa rami mai zurfi a ƙasa, Sa'an nan ya fāɗa ramin da ya haƙa! 16 Saboda haka muguntarsa ta hukunta shi ke nan, Rikicin kansa ya yi masa lahani. 17 Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa, Zan raira yabbai ga Ubangiji, Maɗaukaki.

Zabura 8

Ɗaukakar Allah da Martabar Mutu

1 Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya. Yabonka ya kai har sammai, 2 Yara da jarirai suna raira shi, Ka gina kagara saboda magabtanka, Domin ka tsai da maƙiyanka da abokan gābanka. 3 Sa'ad da na duba sararin sama, wanda ka yi, Da wata da taurari waɗanda ka sa a wuraren zamansu, 4 Wane ne mutum, har da kake tunawa da shi, Mutum kurum, har da kake lura da shi? 5 Duk da haka in banda kai ba wanda ya fi shi, Ka naɗa shi da daraja da girma! 6 Ka sa shi ya yi mulkin dukan abin da ka halitta, Ka ɗora shi a kan dukan abubuwa, 7 Tumaki da shanu, har ma da namomin jeji, 8 Da tsuntsaye da kifaye, Da dukan halittar da take cikin tekuna. 9 Ya Ubangiji, Ubangijinmu, An san girmanka ko'ina a dukan duniya!

Zabura 9

Godiya ga Allah saboda Adalcinsa

1 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji, Zan hurta dukan abubuwa masu banmamaki da ka yi. 2 Zan raira waƙa da farin ciki sabili da kai, Zan raira yabo gare ka, ya Maɗaukaki! 3 Magabtana sun jā da baya da suka gan ka, Suka faɗi, suka mutu. 4 Kai da kake alƙali mai adalci Ka zauna a kursiyinka, Ka kuwa yi shari'ar da ta yi mini daidai. 5 Ka kā da arna, Ka kumar hallakar da mugaye, Ba kuwa za a ƙara tunawa da su ba. 6 An hallaka abokan gābanmu har abada, Ka lalatar da biranensu, An kuma manta da su sarai. 7 Amma Ubangiji sarki ne har abada, Ya kafa kursiyinsa domin yin shari'a. 8 Yana mulkin duniya da adalci, Yana yi wa mutane shari'a da gaskiya. 9 Ubangiji mafaka ne ga waɗanda ake zalunta, Wurin ɓuya a lokatan wahala. 10 Waɗanda suka san ka za su amince da kai, ya Ubangiji, Ba za ka ƙyale duk wanda ya zo gare ka ba. 11 Ku yabi Ubangiji, shi da yake mulki a Sihiyona! Ku faɗa wa kowace al'umma abin da ya yi! 12 Allah yana tunawa da waɗanda suke shan wuya, Ba ya mantawa da kukansu, Yana kuma hukunta waɗanda suke cutarsu. 13 Ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai! Ka dubi irin wulakancin da maƙiya suka yi mini! Ka kuɓutar da ni daga mutuwa, ya Ubangiji, 14 Domin in iya tsayawa a gaban jama'ar Urushalima, In faɗa musu dukan abin da ya sa nake yabonka. Zan yi farin ciki saboda ka cece ni. 15 Arna sun haƙa rami sun kuwa fāɗa ciki, Sun ɗana tarko, ya kuwa kama su. 16 Ubangiji ya bayyana kansa ta wurin shari'arsa mai adalci, Mugaye sun kama kansu da abubuwan da suka aikata. 17 Mutuwa ce maƙarar dukan mugaye, Da dukan waɗanda suke ƙin Allah. 18 Ba kullum ne ake ƙyale masu bukata ba, Ba za a danne sa zuciyar waɗanda ake zalunta ba har abada. 19 Ka zo, ya Ubangiji! Kada ka bari mutane su gagare ka! Ka kawo arna a gabanka, ka hukunta su. 20 Ka sa su ji tsoro, ya Ubangiji, Ka sa su sani su mutane ne kawai.

Zabura 10

Addu'ar Neman Hamɓare Mugaye

1 Ya Ubangiji, me ya sa kake can nesa? Me ya sa ka ɓoye kanka a lokacin wahala? 2 Mugaye suna fāriya, suna kuma tsananta wa matalauta, Ɗana tarkon da suka yi ya kama su. 3 Mugun mutum yana fāriya da mugayen manufofinsa, Mai haɗama yakan zagi Ubangiji ya kuma ƙi shi. 4 Mugun mutum da girmankansa yana cewa, “Ba Allah!” Wannan ne abin da mugu yake tunani. 5 Yakan yi nasara a dukan abin da yake yi. Ba zai fahimci hukuncin Allah ba, Yana yi wa abokan gābansa duban raini. 6 Yana ce wa “Ba zan taɓa fāɗuwa ba, Ba zan taɓa shan wahala ba.” 7 Maganganunsa suna cike da zage-zage, da ƙarairayi, da barazana, Yana da saurin faɗar maganganun ƙiyayya da na mugunta. 8 Yakan ɓuya cikin ƙauyuka, Ya jira a can har ya kashe marasa laifi. Yakan yi sanɗa, ya kama kāsassu, 9 Yakan jira a inda ya ɓuya kamar zaki. Yakan kwanta yana fakon wanda zai kama, Har ya kama shi da tarkonsa ya tafi da shi! 10 Yakan ragargaza kāsasshe, Ya gwada masa ƙarfi, ya ci nasara a kansa. 11 Mugun mutum yakan ce wa kansa, “Allah bai kula ba! Ya rufe idonsa, ba zai taɓa ganina ba.” 12 Ya Ubangiji, ka zo ka cece ni! Kada ka manta da waɗanda ake zaluntarsu, ya Allah! 13 Yaya mugun zai riƙa raina Allah, Har ya riƙa ce wa kansa, “Ba zai hukunta ni ba?” 14 Amma kana gani, kana kuma lura da masu shan wuya, da masu ɓacin rai, Koyaushe kuma a shirye kake ka yi taimako. Mutum wanda ba shi da mai taimako yakan danka kansa gare ka, Gama kullum kakan taimaki masu bukata. 15 Ka karya ikon mugaye, masu mugunta, Ka hukunta su saboda muguntarsu, Har hukuncinsu ya cika sarai. 16 Ubangiji sarki ne har abada abadin, Arna kuma za su ɓace daga ƙasarsa. 17 Za ka saurara ga addu'o'in masu kaɗaici, ya Ubangiji, Za ka ba su ƙarfin hali. 18 Za ka ji koke-koken waɗanda ake zalunta da na marayu, Ka yi shari'ar da za su ji daɗi, Domin kada 'yan adam su ƙara haddasa wata razana.

Zabura 11

Mafakar Adalai

1 Na dogara ga Ubangiji domin zaman lafiya, Wauta ce idan kun ce mini, “Ka yi firiya kamar tsuntsu zuwa duwatsu, 2 Domin mugaye sun ja bakkunansu, Sun kuma ɗana kibansu Domin su harbi mutanen kirki a duhu. 3 Ba abin da mutumin kirki zai iya yi Sa'ad da kome ya lalace.” 4 Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Yana da kursiyinsa a Sama. Yana kallon dukan mutane Yana sane da abin da suke yi. 5 Yana auna masu kirki da mugaye dukka, Yana ƙin marar bin doka gaba ɗaya. 6 Yakan aukar da garwashin wuta Da kibritu mai cin wuta a kan mugaye, Yakan hukunta su da harshen wuta mai ƙuna. 7 Ubangiji mai adalci ne, yana ƙaunar kyawawan ayyuka, Masu yi masa biyayya za su zauna a gabansa.

Zabura 12

Addu'ar Neman Taimako

1 Ka cece ni, ya Ubangiji, Ba sauran mutanen kirki, Ba kuma za a sami amintattun mutane ba. 2 Dukan mutane suna yi wa juna ƙarya, Suna ruɗin junansu da yaudara. 3 Ka sa harsunan nan masu yaudara su yi shiru, Ya Ubangiji, ka rufe bakunan nan masu fāriya! 4 Sukan ce, “Za mu yi magana yadda muka ga dama, Ba kuwa wanda zai hana mu. Wane ne yake da ikon faɗa mana abin da za mu faɗa?” 5 Ubangiji ya ce, “Amma zan zo yanzu, Domin ana zaluntar masu bukata, Waɗanda aka tsananta musu kuma, suna nishi don zafi. Zan ba su zaman lafiya da suke nema!” 6 Alkawaran Ubangiji abin dogara ne, Alkawarai ne na ainihi kamar azurfa Da aka tace har sau bakwai cikin matoya. 7 Ka kiyaye lafiyarmu, ya Ubangiji, Ka kiyaye mu daga irin waɗannan mutane. 8 Akwai mugaye ko'ina, suna ta yanga, Suna ta yabon abin da yake mugunta.

Zabura 13

Addu'ar Neman Taimako daga Wahala

1 Har yaushe za ka manta da ni, ya Ubangiji? Har abada ne? Har yaushe za ka ɓoye mini fuskarka? 2 Har yaushe raina zai jure da shan wahala? Har yaushe zan yi ta ɓacin rai dare da rana? Har yaushe maƙiyana za su riƙa cin nasara a kaina? 3 Ka dube ni, ya Ubangiji Allahna, ka amsa mini, Ka mayar mini da ƙarfina, don kada in mutu. 4 Sa'an nan maƙiyana ba za su ce, “Ai, mun yi nasara da shi” ba! Ba za su iya yin murna saboda fāɗuwata ba. 5 Amma ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarka, Zan yi murna gama za ka cece ni. 6 Zan raira waƙa ga Ubangiji, Gama ya kyautata mini.

Zabura 14

Muguntar 'Yan Adam da Wautarsu

1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah!” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai. 2 Daga Sama Ubangiji ya dubi mutane, Ya ga ko da akwai masu hikima Waɗanda suke yi masa sujada. 3 Amma dukansu sun koma baya, Su duka mugaye ne, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai, Babu ko ɗaya. 4 Ubangiji ya ce, “Ba su sani ba? Duk waɗannan masu aikin mugunta jahilai ne? Ta wurin yi wa jama'ata fashi suke zaman gari, Ba su yin addu'a gare ni.” 5 Amma za su razana, Gama Allah yana tare da masu yi masa biyayya. 6 Suna yi wa shirye-shiryen kāsasshe dariya, Saboda yana dogara ga Ubangiji. 7 Ina addu'a matuƙa domin ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona! Sa'ad da Ubangiji ya sāke arzuta jama'arsa, Zuriyar Yakubu za su yi farin ciki, Jama'ar Isra'ila za su yi murna.

Zabura 15

Mazauna a Tudun Allah Mai Tsarki

1 Wane ne zai iya zama cikin Haikalinka? Wa zai iya tsayawa a Sihiyona, wato tudunka tsattsarka? 2 Sai dai mutumin da yake biyayya ga Allah da kowane abu, Yana kuwa aikata abin da yake daidai, Wanda yake faɗar gaskiya da zuciya ɗaya, 3 Wanda kuma ba ya ɓāta sunan waɗansu. Ba ya zargin abokansa, Ba ya kuwa baza jita-jita a kan maƙwabtansa. 4 Yakan raina waɗanda Allah ya ƙi su, Amma yana girmama waɗanda suke yi wa Ubangiji biyayya, KUllum yana cika alkawaran da ya yi ko ta halin ƙaƙa, 5 Yana ba da rance ba ruwa, Ba ya karɓar hanci don ya yi shaidar zur a kan marar laifi. Wanda ya aikata waɗannan abubuwa ba zai taɓa fāɗuwa ba.

Zabura 16

Gādon Alheri

1 Ya Allah, ka kiyaye ni, gama na zo gare ka neman mafaka. 2 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Ubangijina, Dukan kyawawan abubuwan da nake da su Daga gare ka suke.” 3 Dubi irin martabar da amintattun jama'ar Ubangiji suke da ita! Ba abin da raina ya fi so, Sai in zauna tare da su. 4 Waɗanda suke hanzari zuwa ga gumaka, Za su jawo wa kansu wahala. Ba zan yi tarayya da su da hadayarsu ba. Ba zan yi sujada ga gumakansu ba. 5 Kai ne kaɗai, nake da shi, ya Ubangiji, Kai ne kake biyan dukan bukatata, Raina yana hannunka. 6 Kyautanka zuwa gare ni da bansha'awa suke, Kyawawa ne kuwa ƙwarai! 7 Na yabi Ubangiji saboda yana bi da ni, Da dare kuma lamirina yana yi mini fadaka. 8 A kullum ina jin Ubangiji yana tare da ni, Yana nan kusa, ba abin da zai girgiza ni. 9 Don haka cike nake na murna da farin ciki, Kullum kuwa ina jin kome lafiya yake, 10 Saboda ba za ka yarda in shiga lahira ba, Ba za ka bar wanda kake ƙauna a zurfafa daga ƙarƙas ba. 11 Za ka nuna mini hanyar rai, Kasancewarka takan sa in cika da farin ciki, Taimakonka kuwa yana kawo jin daɗi har abada.

Zabura 17

Addu'ar Neman Tsari daga Azzalumai

1 Ka kasa kunne ga roƙona, ni adalin mutum, Ka lura da kukana na neman taimako! Ka kasa kunne ga addu'ata, Gama ni ba mayaudari ba ne. 2 Za ka shara'anta shari'ar da za ta gamshe ni, Saboda ka san abin da yake daidai. 3 Ka san zuciyata, Kakan zo gare ni da dare, Ka riga ka jarraba ni sarai, Ba ka kuwa sami mugun nufi a cikina ba. Na ƙudurta kuma bakina ba zai yi saɓo ba. 4 Zancen aikin sauran mutane, Na yi biyayya ga umarninka Ban bi hanyar rashin hankali ba. 5 Ina tafiya a kan tafarkinka kullum, Ban kuwa kauce ba. 6 Ina addu'a gare ka, ya Allah, Domin kakan amsa mini, Don haka ka juyo wurina ka kasa kunne ga maganata. 7 Ka bayyana ƙaunarka mai banmamaki, Ya Mai Ceto, Muddin muna kusa da kai mun tsira daga maƙiyanmu. 8 Ka kiyaye ni kamar yadda ake kiyaye idanu, Ka ɓoye ni a inuwar fikafikanka, 9 Daga hare-hare na mugaye. Maƙiyana cike da ƙiyayya sun kewaye ni. 10 Ba su jin tausayi, suna magana da girmankai, 11 Yanzu suna kewaye da ni duk inda na juya, Suna jira su sami dama su fyaɗa ni ƙasa. 12 Kamar zakoki suke nema su yayyage ni kaca-kaca, Kamar sagarun zakoki suna fakona a wurin ɓuyarsu. 13 Ka zo, ya Ubangiji, Ka yi yaƙi da maƙiyana, ka yi nasara da su! Ka cece ni da takobinka daga mugaye, 14 Ka cece ni daga gare su da ikonka, Ka cece ni daga waɗanda suke da duk abin da suke so a duniyar nan, Ka hukunta su da wahalar da ka shirya musu, Ka sa har 'ya'yansu, su ma, ta ishe su, Wahalar da ta ragu kuma, ta sami jikokinsu! 15 Zan gan ka domin ni adali ne, Sa'ad da na farka, kasancewarka tana cika ni da farin ciki.

Zabura 18

Waƙar Dawuda ta Nasara

1 Ina ƙaunarka ƙwarai, ya Ubangiji! Kai ne mai kāre ni. 2 Ubangiji ne Mai Cetona, Shi ne garkuwata mai ƙarfi. Allahna, shi ne yake kiyaye ni, Lafiya nake sa'ad da nake tare da shi, Yana kiyaye ni kamar garkuwa, Yana kāre ni, ya ba ni lafiya. 3 Na yi kira ga Ubangiji, Yakan cece ni daga magabtana, Yabo ya tabbata ga Ubangiji! 4 Mutuwa ta ɗaure ni kam da igiyoyinta, Hallaka ta auko mini a kai a kai. 5 Mutuwa ta ɗaure ni kam da igiyoyinta, Kabari kuma ya ɗana mini tarko. 6 A shan wahalata na kira ga Ubangiji, Na yi kira ga Allahna domin neman taimako. A Haikalinsa ya ji muryata, Kukana na neman taimako ya kai kunnensa. 7 Sai duniya ta raurawa ta girgiza, Harsashin duwatsu suka jijjigu, suka girgiza Saboda Allah ya husata! 8 Hayaƙi ya yi ta tuƙaƙowa daga hancinsa, Harshen wuta da garwashi suna fitowa daga bakinsa. 9 Ya buɗe sararin sama, ya sauko ƙasa, Tare da girgije mai duhu a ƙarƙashin ƙafafunsa. 10 Ya sauko ta bisa bayan kerubobi, Yana tafe da sauri a kan fikafikan iska. 11 Ya rufe kansa da duhu, Gizagizai masu duhu cike da ruwa, suna kewaye da shi. 12 Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko Daga cikin walƙiya da take gabansa, Suka keto ta cikin gizagizai masu duhu. 13 Sa'an nan Ubangiji ya yi tsawa daga sararin sama, Aka ji muryar Maɗaukaki. Ƙanƙara da garwashin wuta suka sauko. 14 Ya harba kibansa, ya watsa magabtana, Da walƙiya ya kore su. 15 Kashiyar teku ta bayyana, Tussan duniya sun bayyana, Sa'ad da ka tsauta wa magabtana ya Ubangiji, Sa'ad da kuma ka yi musu tsawa da fushi. 16 Ubangiji ya miƙa hannunsa daga samaniya ya ɗauke ni, Ya tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi. 17 Ya cece ni daga magabtana masu ƙarfi, Daga kuma dukan masu ƙina, Gama sun fi ƙarfina! 18 Sa'ad da nake shan wahala suka auka mini, Amma Ubangiji ya kiyaye ni. 19 Ya fisshe ni daga cikin hatsari, Ya cece ni, don yana jin daɗina. 20 Ubangiji yakan sāka mini, saboda ni adali ne, Yakan sa mini albarka, don ni marar laifi ne. 21 Na yi biyayya da umarnan Ubangiji, Ban yi wa Ubangiji Allahna tawaye ba. 22 Na kiyaye dukan dokokinsa, Ban yi rashin biyayya da umarnansa ba. 23 Ya sani ba ni da laifi, Domin na kiyaye kaina daga mugunta. 24 Don haka ya sāka mini, domin ni adali ne, Gama ya sani ni marar laifi ne. 25 Kai, ya Ubangiji, mai aminci ne ga masu aminci, Kai nagari ne, cikakke ga kamilai. 26 Kai Mai Tsarki ne ga waɗanda suke tsarkaka, Amma kana gāba da mugaye. 27 Kakan ceci masu tawali'u, Amma kakan ƙasƙantar da masu girmankai. 28 Ubangiji yakan ba ni haske, Allah yakan kawar da duhuna. 29 Yakan ba ni ƙarfin da zan fāɗa wa magabtana, Da ikon rinjayar kagararsu. 30 Wannan Allah dai! Ayyukansa kamiltattu ne ƙwarai, Maganarsa abar dogara ce! Kamar garkuwa yake, ga duk mai neman taimako a wurinsa. 31 Ubangiji shi kaɗai ne Allah, Allah ne kaɗai kāriyamu. 32 Shi ne Allahn da yake ƙarfafa ni, Yana kiyaye lafiyata a kan hanya. 33 Yana sa in tabbata lafiya nake tafiya, kamar barewa. Yana kiyaye ni lafiya a kan duwatsu. 34 Yakan horar da ni don yaƙi, Domin in iya amfani da baka mafi ƙarfi. 35 Ya Ubangiji ka kiyaye ni, ka cece ni, Na zama babban mutum saboda kana lura da ni, Ikonka kuma ya kiyaye lafiyata. 36 Ka tsare ni, ba a kama ni ba, Ban kuwa taɓa fāɗuwa ba. 37 Na kori magabtana, har na kama su, Ba zan tsaya ba, sai na yi nasara da su. 38 Zan buge su har ƙasa, ba kuwa za su tashi ba, Za su fāɗi ƙarƙashin ƙafafuna. 39 Kakan ba ni ƙarfin yin yaƙi, Kakan ba ni nasara a kan magabtana. 40 Ka kori magabtana daga gare ni, Zan hallaka waɗanda suke ƙina. 41 Suna kukan neman taimako, amma ba wanda zai iya cetonsu, Za su yi kira ga Ubangiji, amma ba zai amsa ba. 42 Zan murƙushe su har su zama ƙura Wadda iska take kwashewa, Zan tattake su kamar caɓi a titi. 43 Ka cece ni daga mutane masu tawaye, Ka naɗa ni in yi mulkin sauran al'umma, Jama'ar da ban san ta ba, ta zama abin mulkina. 44 Za su yi biyayya sa'ad da suka ji ni, Baƙi za su rusuna mini, 45 Za su karai, Su fita, suna rawar jiki daga kagaransu. 46 Ubangiji mai rai ne! Yabo ya tabbata ga mai kāre ni! Allah ne, Mai Cetona! A yi shelar girmansa! 47 Yakan ba ni nasara a kan magabtana, Yakan sa jama'a a ƙarƙashina, 48 Yakan cece ni daga maƙiyana. Ka ba ni nasara a kan magabtana, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga mutane masu kama-karya, 49 Don haka zan yabe ka a cikin al'ummai, Zan raira maka yabo. 50 Kullayaumi Allah yakan ba sarkin da ya naɗa babbar nasara. Yakan nuna madawwamiyar ƙauna ga wanda ya zaɓa, Wato Dawuda da zuriyarsa har abada.

Zabura 19

Ayyukan Allah da Shari'arsa

1 Dubi yadda sararin sama yake bayyana ɗaukakar Allah! Dubi yadda suke bayyana a fili ayyukansa da ya yi! 2 Kowace rana tana shelar ɗaukakarsa ga ranar da take biye, Kowane dare yana nanata ɗaukakarsa ga daren da yake biye. 3 Ba magana ko kalma da aka hurta, Ba wani amon da aka ji, 4 Duk da haka muryarsu ta game duniya duka, Saƙonsu ya kai ko'ina a duniya. Allah ya kafa wa rana alfarwa a sararin sama, 5 Tana fitowa kamar ango yana taƙama daga gidansa, Kamar ɗan wasan da ya ƙosa ya yi tsere. 6 Takan fara daga wannan ƙarshen sararin sama, ta kewaye zuwa wancan. Ba abin da zai iya ɓuya daga zafinta. 7 Dokar Ubangiji cikakkiya ce, Tana wartsakar da rai. Umarnan Ubangiji abin dogara ne, Sukan ba da hikima ga wanda ba shi da ita. 8 Ka'idodin Ubangiji daidai suke, Waɗanda suke biyayya da su sun ji daɗi. Umarnan Ubangiji daidai suke, Sukan ba da fahimi ga zuciya. 9 Daidai ne a bauta wa Ubangiji, A ci gaba da yi har abada. Duk abin da Ubangiji ya hukunta daidai ne, A kullum hukuntan Ubangiji daidai suke. 10 Abin da ake so ne fiye da zinariya, I, fiye da tatacciyar zinariya ma, Sun fi zuma zaƙi, I, fiye da tatacciyar zuma ma. 11 Suna ba ni ilimi, ni baranka, Ina samun ladan yin biyayya da su. 12 Ba mai iya ganin kuskuren kansa, Ka cece ni daga ɓoyayyun laifofi! 13 Ka tsare ni kuma daga laifofi na fili, Kada ka bari su mallake ni. Sa'an nan zan zama kamili, In kuɓuta daga mugun zunubi. 14 Ka sa maganata da tunanina su zama abin karɓa a gare ka, Ya Ubangiji, Mafakata da Mai Fansata!

Zabura 20

Addu'ar Neman Nasara

1 Ubangiji ya amsa maka a ranar wahala! Allah na Yakubu ya kiyaye ka! 2 Ya aiko maka da taimako daga Haikalinsa, Ya kawo maka gudunmawa daga Sihiyona. 3 Ya karɓi hadayunka, Ya kuma ji daɗin dukan sadakokinka. 4 Ya ba ka abin da kake bukata, Ya sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara. 5 Mu kuma, sai mu yi sowa ta farin ciki saboda ka ci nasara, Mu yi bikin cin nasara da ka yi, Da yabon Ubangiji Allahnmu. Allah ya amsa dukan roƙe-roƙenka! 6 Yanzu dai na sani Ubangiji yakan ba da nasara ga zaɓaɓɓen sarkinsa, Yakan amsa masa daga samaniyarsa mai tsarki, Da ikonsa mai girma yakan sa shi ya yi nasara. 7 Waɗansu ga karusan yaƙinsu suke dogara, Waɗansu kuwa ga dawakansu, Amma mu, ga ikon Ubangiji Allahnmu muke dogara! 8 Za su yi tuntuɓe su fāɗi, Amma mu za mu tashi mu tsaya daram! 9 Ka ba sarki nasara, ya Ubangiji, Ubangiji zai amsa mana sa'ad da muka yi kira.

Zabura 21

Yabo saboda Nasara

1 Sarki yana murna, ya Ubangiji, Domin ka ba shi ƙarfi, Yana cike da farin ciki, Don ka sa ya ci nasara. 2 Ka biya masa bukatarsa, Ka amsa roƙonsa. 3 Ka zo gare shi da albarka mai yawa, Ka sa kambin zinariya a kansa. 4 Ya roƙi rai, ka kuwa ba shi mai tsawo, Da yawan kwanaki. 5 Darajarsa tana da girma saboda taimakonka, Ka sa ya yi suna da martaba. 6 Albarkarka tana a kansa har abada, Kasancewarka tare da shi, takan cika shi da murna. 7 Sarki yana dogara ga Maɗaukaki, Saboda madawwamiyar ƙaunar Ubangiji Zai zama sarki har abada. 8 Sarki zai kakkama dukan magabtansa, Zai kakkama duk waɗanda suke ƙinsa. 9 Ubangiji zai hallaka su kamar harshen wuta, sa'ad da ya bayyana. Ubangiji zai cinye su a cikin fushinsa, Wuta kuma za ta cinye su ƙurmus. 10 Sarki zai karkashe 'ya'yansu duka, Zai yanyanke dukan zuriyarsu. 11 Sun ƙulla mugayen dabaru, suna fakonsa, Amma ba za su yi nasara ba. 12 Zai harba kibansa a kansu, Ya sa su juya su gudu. 13 Ya Ubangiji, ka zo da ƙarfinka! Za mu raira waƙa mu yabi ikonka.

Zabura 22

Kukan Azaba da Waƙar Yabo

1 Ya Allahna, ya Allahna, Don me ka yashe ni? Na yi kuka mai tsanani, ina neman taimako, Amma har yanzu ba ka zo ba! 2 Da rana na yi kira a gare ka, ya Allahna, Amma ba ka amsa ba. Da dare kuma na yi kira, Duk da haka ban sami hutawa ba. 3 Amma an naɗa ka Mai Tsarki, Wanda Isra'ila take yabonsa. 4 Kakanninmu suka dogara gare ka, Sun dogara gare ka, ka kuwa cece su. 5 Suka yi kira gare ka, suka tsira daga hatsari, Suka dogara gare ka, ba su kuwa kunyata ba. 6 A yanzu dai ni ba mutum ba ne, tsutsa ne kawai, Rainanne, abin ba'a ga kowa da kowa! 7 Duk wanda ya gan ni Sai ya maishe ni abin dariya, Suna zunɗena da harshensu suna kaɗa kai. 8 Suke ce, “Ka dogara ga Ubangiji, Me ya sa bai cece ka ba? Idan Ubangiji na sonka, Don me bai taimake ka ba?” 9 Kai ne ka fito da ni lafiya a lokacin da aka haife ni, A lokacin da nake jariri ka kiyaye ni. 10 Tun daga lokacin da aka haife ni nake dogara gare ka, Kai ne Allahna tun daga ran da aka haife ni. 11 Kada ka yi nisa da ni! Wahala ta gabato, Ba kuwa mai taimako. 12 Magabta da yawa sun kewaye ni kamar bijimai, Dukansu suna kewaye da ni, Kamar bijimai masu faɗa na ƙasar Bashan. 13 Sun buɗe bakinsu kamar zakoki, Suna ruri, suna ta bina a guje. 14 Ƙarfina ya ƙare, Ya rabu da ni kamar ruwan da ya zube ƙasa. Dukan gaɓoɓina sun guggulle, Zuciyata ta narke kamar narkakken kākin zuma. 15 Maƙogwarona ya bushe kamar ƙura, Harshena kuma na liƙe wa dasashina na sama. Ka bar ni matacce cikin ƙura. 16 Ƙungiyar mugaye na kewaye da ni, Suka taso mini kamar garken karnuka, Suka soke hannuwana da ƙafafuna. 17 Ana iya ganin ƙasusuwana duka. Magabtana suka dube ni, suka zura mini ido. 18 Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, Suka jefa kuri'a a kan babbar rigata. 19 Kada ka yi nisa da ni, ya Ubangiji! Ka gaggauta ka cece ni, ya Mai Cetona! 20 Ka cece ni daga takobi, Ka ceci raina daga waɗannan karnuka. 21 Ka kuɓutar da ni daga waɗancan zakoki, Ba ni da mataimaki a gaban bijimai masu mugun hali. 22 Zan faɗa wa mutanena abin da ka yi, Zan yabe ka cikin taronsu. 23 “Ku yabe shi, ku bayin Ubangiji! Ku girmama shi, ku zuriyar Yakubu! Ku yi masa sujada, ku jama'ar Isra'ila! 24 Ba ya ƙyale matalauta, Ko ya ƙi kulawa da wahalarsu, Ba ya rabuwa da su, Amma yakan amsa lokacin da suka nemi taimako.” 25 Zan yabe ka a gaban babban taron jama'a Saboda abin da ka yi, A gaban sukan masu yi maka biyayya, Zan miƙa sadakokin da na alkawarta. 26 Matalauta za su ci yadda suke so, Masu zuwa wurin Ubangiji za su yabe shi, Su arzuta har abada! 27 Dukan al'ummai za su tuna da Ubangiji, Za su zo gare shi daga ko'ina a duniya, Dukan kabilai za su yi masa sujada. 28 Ubangiji Sarki ne, Yana mulki a kan al'ummai. 29 Masu girmankai duka za su rusuna masa, 'Yan adam duka za su rusuna masa, Dukan waɗanda aka ƙaddara musu mutuwa. 30 Zuriya masu zuwa za su bauta masa, Mutane za su ambaci Ubangiji ga zuriya mai zuwa. 31 Mutanen da ba a haifa ba tukuna, za a faɗa musu, “Ubangiji ya ceci jama'arsa!”

Zabura 23

Ubangiji Makiyayina Ne

1 Ubangiji makiyayina ne, Ba zan rasa kome ba. 2 Yana sa ni in huta a saura mai ɗanyar ciyawa, Yana bi da ni a tafkuna masu daɗin ruwa, suna kwance lif. 3 Yana ba ni sabon ƙarfi. Yana bi da ni a hanyar da yake daidai kamar yadda ya alkawarta. 4 Ko da hanyan nan ta bi ta tsakiyar duhu na mutuwa, Ba zan ji tsoro ba, ya Ubangiji, Gama kana tare da ni! Sandanka na makiyayi da kerenka Suna kiyaye lafiyata. 5 Ka shirya mini liyafa Inda maƙiyana duk za su iya ganina, Ka marabce ni, ka shafe kaina da mai, Ka cika tanduna fal da mai. 6 Hakika, alherinka da ƙaunarka Za su kasance tare da ni muddin raina. Haikalinka zai zama gidana har abada.

Zabura 24

Sarkin Ɗaukaka

1 Duniya da dukan abin da yake cikinta na Ubangiji ne, Duniya da dukan mazaunanta nasa ne. 2 Ya gina ta a bisa ruwa mai zurfi na ƙarƙashin ƙasa, Ya kuma kafa harsashinta a zurfin teku. 3 Wa yake da iko ya hau tudun Ubangiji? Wa yake da iko ya shiga Haikalinsa tsattsarka? 4 Sai wanda yake da tsarki cikin aiki, da tunani, Wanda ba ya yi wa gumaka sujada, Ko kuma ya yi alkawarin ƙarya. 5 Ubangiji zai sa masa albarka, Allah Mai Cetonsa zai kuɓutar da shi. 6 Su ne irin mutanen da suke zuwa wurin Allah, Waɗanda suke zuwa a gaban Allah na Yakubu. 7 A buɗe ƙofofi sosai, A buɗe daɗaɗɗun ƙofofi, Babban Sarki kuwa zai shigo! 8 Wane ne wannan babban Sarki? Ubangiji ne mai ƙarfi mai iko, Ubangiji mai nasara cikin yaƙi! 9 A buɗe ƙofofi sosai, A buɗe daɗaɗɗun ƙofofi, Babban Sarki kuwa zai shigo! 10 Wane ne wannan babban Sarki? Ubangiji Mai Runduna, shi ne babban Sarki!

Zabura 25

Addu'a don Biyarwa, da Gafartawa, da Kiyayewa

1 A gare ka nake yin addu'a, ya Ubangiji, 2 A gare ka nake dogara, ya Allah. Ka cece ni daga shan kunyar fāɗuwa, Kada ka bar magabtana su yi mini duban wulakanci! 3 Waɗanda suke dogara gare ka, Ba za su kāsa yin nasara ba, Sai dai waɗanda suke gaggawa su yi maka tayarwa. 4 Ka koya mini al'amuranka, ya Ubangiji, Ka sa su zama sanannu a gare ni. 5 Ka koya mini in yi zamana bisa ga gaskiyarka, Gama kai Mai Cetona ne. Dukan yini ina dogara a gare ka. 6 Ya Ubangiji, ka tuna da alherinka da madawwamiyar ƙaunarka, Waɗanda ka nuna tun a dā. 7 Ka gafarta zunubaina da kurakuraina masu yawa na ƙuruciyata. Saboda madawwamiyar ƙaunarka da alherinka, Ka tuna da ni, ya Ubangiji! 8 Ubangiji mai adalci ne, mai alheri, Yana koya wa masu zunubi tafarkin da za su bi. 9 Yana bi da masu tawali'u a tafarkin da yake daidai, Yana koya musu nufinsa. 10 Da ƙauna da aminci yana bi da dukan waɗanda suke biyayya da alkawarinsa da umarnansa. 11 Ka cika alkawarinka, ya Ubangiji, ka gafarta zunubaina, gama suna da yawa. 12 Waɗanda suke biyayya da Ubangiji Za su koyi hanyar da za su bi daga gare shi. 13 Kullayaumi za su arzuta, 'Ya'yansu kuma za su zauna lafiya a ƙasar. 14 Ubangiji yakan amince da waɗanda suke biyayya da shi, Yakan koya musu alkawarinsa. 15 A koyaushe ga Ubangiji nake neman taimako, Yakan kuɓutar da ni daga hatsari. 16 Ka juyo wajena, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai, Gama ina zaman kaɗaici da rashin ƙarfi. 17 Damuwar zuciyata ta yi yawa, Ka raba ni da dukan damuwa, Ka cece ni daga dukan wahalata. 18 Ka kula da wahalata da azabata, Ka gafarta dukan zunubaina. 19 Ka duba yawan magabtan da nake da su, Dubi irin ƙiyayyar da suke yi mini! 20 Ka yi mini kāriya, ka cece ni, Gama na zo wurinka neman kāriya. 21 Ka sa nagartata da amincina su kiyaye ni, Gama na dogara gare ka. 22 Ka fanshi jama'arka daga dukan wahalarsu, ya Allah!

Zabura 26

Addu'ar Neman Tsare Mutunci

1 Ka hurta rashin laifina, ya Ubangiji, Gama na yi abin da yake daidai, Na dogara gare ka gaba ɗaya. 2 Ka jarraba ni ka auna ni, ya Ubangiji, Ka gwada muradina da tunanina. 3 Madawwamiyar ƙaunarka tana bi da ni, Amincinka yake yi mini jagora kullayaumin. 4 Ba na tarayya da mutanen banza, Ba abin da ya gama ni da masu riya. 5 Ina ƙin tarayya da masu mugunta, Nakan kauce wa mugaye. 6 Ya Ubangiji, na wanke hannuwana Don in nuna ba ni da laifi, Da ibada nakan taka, ina kewaya bagadenka. 7 Na raira waƙar godiya, Na faɗi dukan ayyukanka masu banmamaki. 8 Ya Ubangiji, ina ƙaunar Haikali inda zatinka yake, Inda ɗaukakarka take zaune. 9 Kada ka hallaka ni tare da masu zunubi, Ka cece ni daga ƙaddarar masu kisankai, 10 Mutanen da suke aikata mugunta a dukan lokaci, A koyaushe suna shirye don su ba da rashawa. 11 Amma ni, ina yin abin da yake daidai, Ka yi mini jinƙai ka fanshe ni! 12 Na kuɓuta daga dukan hatsarori, A taron sujada na yabi Ubangiji!

Zabura 27

Ubangiji ne Haskena da Cetona

1 Ubangiji ne haskena da cetona, Ba zan ji tsoron kowa ba. Ubangiji yana kiyaye ni daga dukan hatsari, Ba zan ji tsoro ba. 2 Sa'ad da mugaye suka tasar mini, Suna ƙoƙari su kashe ni, Za su yi tuntuɓe su fāɗi. 3 Ko da rundunar mayaƙa ta kewaye ni, Ba zan ji tsoro ba. Ko da magabtana sun tasar mini, Zan dogara ga Allah. 4 Abu guda nake roƙo a wurin Ubangiji, Abu ɗaya kaɗai nake bukata, Shi ne in zauna a masujadar Ubangiji, In yi ta al'ajabin alherinsa Dukan kwanakin raina, In roƙi biyarwarsa a can. 5 A lokatan wahala zai kiyaye ni a inuwarsa, Zai kiyaye ni lafiya a Haikalinsa, Zai ɗora ni a kan dutse mai tsayi, ya kiyaye ni. 6 Ta haka zan ci nasara a kan magabtana da suke kewaye da ni. Da sowar farin ciki mai yawa zan miƙa sadakoki a Haikalinsa! Zan raira waƙa, in yabi Ubangiji! 7 Ka ji ni, ya Ubangiji, sa'ad da na ya yi kira gare ka! Ka yi mini jinƙai ka amsa mini! 8 Ka ce, “Zo wurina,” Zan kuwa zo gare ka, ya Ubangiji, 9 Kada ka ɓoye mini fuskarka, ya Ubangiji! Kada ka yi fushi da ni, Kada kuwa ka kori bawanka. Kai ne kake taimakona, tun dā ma, Kada ka bar ni, kada ka yashe ni, Ya Allahna, Mai Cetona! 10 Mai yiwuwa ne ubana da uwata su yashe ni, Amma Ubangiji zai lura da ni. 11 Ka koya mini abin da ya kamata in yi, ya Ubangiji, Ka bi da ni kan lafiyyiyar hanya, Domin ina da magabta da yawa. 12 Kada ka bar ni a hannun magabtana, Waɗanda suke fāɗa mini da ƙarairayi da kurari. 13 Hakika zan rayu domin in ga alherin Ubangiji Da zai yi wa jama'arsa. 14 Ka dogara ga Ubangiji! Ka yi imani, kada ka karai. Ka dogara ga Ubangiji!

Zabura 28

Addu'ar Roƙo da Yabo

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji mai kāre ni, Ka ji kukana! In kuwa ba ka amsa mini ba, Zan zama ɗaya daga cikin waɗanda suka gangara zuwa lahira. 2 Ka ji ni lokacin da na yi kuka gare ka neman taimako, Ina ɗaga hannuwana wajen tsattsarkan Haikalinka. 3 Kada ka kāshe ni tare da mugaye, Tare da masu aikata mugunta, Mutane waɗanda maganarsu kamar ta zumunci ce, Amma zukatansu cike suke da ƙiyayya. 4 Ka hukunta su saboda abin da suka aikata. Ka hukunta su saboda dukan ayyukansu, Ka ba su abin da ya cancance su! 5 Ba su kula da abin da Ubangiji ya yi ba, Ko kuma abin da ya halitta, Don haka zai hukunta su, ya hallaka su har abada. 6 A yabi Ubangiji, Gama ya ji kukana na neman taimako! 7 Ubangiji yakan kiyaye ni, ya tsare ni. Na dogara gare shi. Ya taimake ni, don haka ina murna, Ina raira masa waƙoƙin yabo. 8 Ubangiji yana kiyaye jama'arsa, Yakan kiyaye sarkinsa da ya zaɓa, ya kuma cece shi. 9 Ka ceci jama'arka, ya Ubangiji, Ka sa wa waɗanda suke naka albarka! Ka zama makiyayinsu, Ka lura da su har abada.

Zabura 29

Muryar Ubangiji a cikin Hadiri

1 Ku yabi Ubangiji, ku alloli, Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa. 2 Ku yabi sunan Ubangiji mai daraja, Ku rusuna a gaban Mai Tsarki sa'ad da ya bayyana. 3 An ji muryar Ubangiji a kan tekuna, Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Tsawar muryarsa kuwa ta yi amsa kuwa a bisa teku. 4 An ji muryar Ubangiji A dukan ikonsa da zatinsa! 5 Muryar Ubangiji takan karya itatuwan al'ul, Har ma da itatuwan al'ul na Lebanon. 6 Yakan sa duwatsun Lebanon su yi tsalle kamar 'yan maruƙa, Ya kuma sa Dutsen Harmon ya yi tsalle kamar ɗan maraƙi. 7 Muryar Ubangiji ta sa walƙiya ta walƙata. 8 Muryarsa ta sa hamada ta girgiza, Ta girgiza hamadar Kadesh. 9 Muryar Ubangiji ta sa barewa ta haihu, Ta sa itatuwa su kakkaɓe, Sa'ad da aka yi sowa a cikin Haikalinsa, Aka ce, “'Daukaka ga Allah!” 10 Ubangiji yana sarautar ruwa mai zurfi, Yana sarauta kamar sarki har abada. 11 Ubangiji yana ba jama'arsa ƙarfi, Ya sa musu albarka da salama.

Zabura 30

Addu'ar Godiya domin Kuɓuta daga Mutuwa

1 Ina yabonka, ya Ubangiji saboda ka cece ni, Ka kuwa hana magabtana su haɗiye ni. 2 Na roƙi taimako a gare ka, ya Ubangiji Allahna, Ka kuwa warƙar da ni. 3 Ka dawo da ni daga lahira. Na gangara tare da waɗanda suke gangarawa cikin zurfafa a ƙasa, Amma ka ceci raina. 4 Ku raira yabo ga Ubangiji, Ku amintattun jama'arsa! Ku tuna da abin da Mai Tsarki ya aikata, Ku yi masa godiya! 5 Fushinsa ba ya daɗewa, Alherinsa kuwa har matuƙa ne. Mai yiwuwa ne ya zama ana kuka da dare, Amma a yi murna da safe. 6 Ina zaune jalisan, na ce wa kaina, “Faufau ba za a taɓa cin nasara a kaina ba.” 7 Kana yi mini alheri, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni kamar a kagarar dutse. Amma sa'ad da ka ɓoye mini fuskarka, Sai in cika da tsoro. 8 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Ina roƙon taimakonka. 9 Wane amfani za a samu daga mutuwata? Ina ribar da za a samu daga zuwana kabari? Ko matattu suna iya yabonka? Za su iya shelar madawwamin alherinka? 10 Ka ji ni, ya Ubangiji, ka yi mini jinƙai! Ka taimake ni, ya Ubangiji! 11 Ka mai da baƙin cikina Ya zama rawar farin ciki, Ka tuɓe mini tufafin makoki, Ka sa mini na farin ciki. 12 Don haka ba zan yi shiru ba, Zan raira maka yabo, Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan gode maka har abada.

Zabura 31

Addu'ar Dogara ga Allah

1 Na zo gare ka, ya Ubangiji, domin ka kiyaye ni. Kada ka bari a yi nasara da ni. Kai Allah mai adalci ne, Ka cece ni, ina roƙonka! 2 Ka ji ni! Ka cece ni yanzu! Ka zama mafakata, don ka kiyaye ni, Ka zama mai kāre ni, don ka cece ni. 3 Kai ne mafakata da kariyata, Ka bi da ni yadda ka alkawarta. 4 Ka kiyaye ni daga tarkon da aka kafa domina, Kai ne inuwata. 5 Ina ba da kaina gare ka domin ka kiyaye ni. Za ka fanshe ni, ya Ubangiji, Kai Allah mai aminci ne. 6 Kana ƙin waɗanda suke yi wa gumaka sujada, Amma ni na dogara gare ka. 7 Zan yi murna da farin ciki, Saboda madawwamiyar ƙaunarka. Ka ga wahalata, Ka kuwa san damuwata. 8 Ba ka bar magabtana su kama ni ba, Ba kiyaye ni. 9 Ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, Gama ina shan wahala, Idanuna sun gaji saboda yawan kuka, Na kuwa tafke ƙwarai! 10 Baƙin ciki ya gajerta kwanakina, Kuka kuma ya rage shekaruna. Na raunana saboda yawan wahalata, Har ƙasusuwana suna zozayewa! 11 Magabtana duka suna mini ba'a, Maƙwabtana sun raina ni, Waɗanda suka san ni kuwa suna jin tsorona, Sa'ad da suka gan ni a kan titi sukan guje mini. 12 Duk an manta da ni kamar matacce, Na zama kamar abin da aka jefar. 13 Na ji magabtana da yawa suna raɗa, Razana ta kewaye ni! Suna ƙulla maƙarƙashiya don su kashe ni. 14 Amma a gare ka na dogara, ya Ubangiji, Kai ne Allahna. 15 Kana lura da ni kullum, Ka cece ni daga magabtana, Daga waɗanda suke tsananta mini. 16 Ni, bawanka ne, Ka dube ni da alherinka, Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka! 17 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Kada ka bari a ci nasara a kaina! Ka sa a ci nasara a kan mugaye, Ka sa su yi shiru a lahira. 18 Ka rufe bakin maƙaryatan can Dukan masu girmankai da masu fāriya, Waɗanda suke wa adalai maganar raini! 19 Abin al'ajabi ne irin tanadin da ka yi wa masu tsoronka! Abin da kake aikatawa a gaban kowa kuma, Yana da banmamaki. Kana kiyaye waɗanda suke amincewa da kai. 20 Ka ɓoye su a wurinka lafiya daga makircin mutane, A inuwa mai lafiya ka ɓoye su daga zargin magabtansu. 21 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Gama ya nuna mini ƙaunarsa mai ban al'ajabi, Sa'ad da aka kewaye ni, aka fāɗa mini! 22 Na ji tsoro, na zaci ka jefar da ni ne daga gabanka. Amma ka ji kukana sa'ad da na yi kira gare ka neman taimako. 23 Ku ƙaunaci Ubangiji, ku amintattun jama'arsa duka! Ubangiji yana kiyaye masu aminci, Amma yakan hukunta masu girmankai da tsanani. 24 Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali, Dukanku da kuke sa zuciya ga Ubangiji!

Zabura 32

Albarkar Gafarar Zunubi

1 Mai farin ciki ne mutumin da aka gafarta masa zunubansa, Mai farin ciki ne kuma wanda aka gafarta masa laifofinsa. 2 Mai farin ciki ne wanda Ubangiji bai zarge shi a kan wani laifi ba, Wanda ba algus ko kaɗan a cikinsa. 3 Sa'ad da ban hurta zunubaina ba, Na gajiyar da kaina da yawan kuka dukan yini. 4 Ka hukunta ni dare da rana, ya Ubangiji, Ƙarfina duka ya ƙare sarai, Kamar yadda laima take bushewa, Saboda zafin bazara. 5 Sa'an nan na hurta zunubaina gare ka, Ban ɓoye laifofina ba. Na ƙudurta in hurta su gare ka, Ka kuwa gafarta dukan laifofina. 6 Saboda haka dukan jama'arka masu biyayya, Za su yi addu'a gare ka, lokacin bukata. Sa'ad da babbar rigyawa ta malalo, Ba za ta kai wurinsu ba. 7 Kai ne maɓoyata, Za ka cece ni daga wahala. Ina raira waƙa da ƙarfi saboda cetonka, Domin ka kiyaye ni. 8 Ubangiji ya ce, “Zan koya maka hanyar da za ka bi, Zan koya maka, in kuma ba ka shawara. 9 Kada ka zama wawa kamar doki ko alfadari, Wanda dole sai da linzami, da ragama za a sarrafa shi, Sa'an nan ya yi maka biyayya.” 10 Tilas ne mugu ya sha wahala, Amma masu dogara ga Ubangiji, Madawwamiyar ƙaunarsa tana kiyaye su. 11 Dukanku adalai, ku yi murna, Ku yi farin ciki, Saboda abin da Ubangiji ya yi! Dukanku da kuke yi masa biyayya, Ku yi sowa ta farin ciki!

Zabura 33

Waƙar Yabo

1 Dukanku adalai ku yi murna, A kan abin da Ubangiji ya yi, Ku yabe shi, ku da kuke masa biyayya! 2 Ku kaɗa garaya, kuna yi wa Ubangiji godiya. Ku raira masa waƙa, da kayan kaɗe-kaɗe masu tsarkiya. 3 Ku raira masa sabuwar waƙa, Ku kaɗa garaya da gwaninta, Ku kuma raira waƙa da ƙarfi! 4 Kalmomin Ubangiji gaskiya ne, Ayyukansa duka kuwa abin dogara ne. 5 Ubangiji yana ƙaunar abin da yake na adalci da gaskiya, Madawwamiyar ƙaunarsa ta cika duniya. 6 Ubangiji ya halicci duniya da umarninsa, Rana, da wata, da taurari kuma bisa ga maganarsa. 7 Ya tattara tekuna wuri ɗaya. Ya rurrufe zurfafan teku a ɗakunan ajiya. 8 Bari duk duniya ta ji tsoron Ubangiji! Ku ji tsoronsa ku mutanen duniya! 9 Da magana ya halicci duniya, Ta wurin umarninsa kowane abu ya bayyana. 10 Ubangiji yakan sassoke manufofin sauran al'umma, Yakan hana su aikata shirye-shiryensu. 11 Amma shirye-shiryensa sukan tabbata har abada. Nufe-nufensa kuma dawwamammu ne har abada. 12 Mai farin ciki ce al'ummar da Ubangiji yake Allahnta, Masu farin ciki ne jama'ar da Ubangiji ya zaɓo wa kansa! 13 Daga Sama Ubangiji ya dubo dukan 'yan adam. 14 Daga inda yake mulki, yakan dubo dukan mazaunan duniya. 15 Shi ya siffata tunaninsu, yana sane da dukan abin da suke yi. 16 Ba saboda ƙarfin mayaƙa sarki yakan ci nasara ba, Mayaƙi ba yakan yi rinjaye saboda ƙarfinsa ba. 17 Dawakan yaƙi ba su da amfani don cin nasara, Ƙarfin nan nasu ba zai iya ceto ba. 18 Ubangiji yana kiyaye masu tsoronsa, Waɗanda suke dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa. 19 Yakan cece su daga mutuwa, Yakan rayar da su a lokacin yunwa. 20 Ga Ubangiji muke sa zuciya, Shi mai taimakonmu ne, mai kiyaye mu. 21 Saboda da shi muke murna, Muna dogara ga sunansa mai tsarki. 22 Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji, Da yake a gare ka muke sa zuciya.

Zabura 34

Yabo domin Kuɓuta

1 Zan yi godiya ga Ubangiji kullayaumin, Faufau ba zan taɓa fasa yabonsa ba. 2 Zan yabe shi saboda abin da ya yi, Da ma dukan waɗanda suke da tawali'u su kasa kunne, su yi murna! 3 Ku yi shelar girman Ubangiji tare da ni, Mu yabi sunansa tare! 4 Na yi addu'a ga Ubangiji, ya kuwa amsa mini, Ya kuɓutar da ni daga dukan tsorona. 5 Waɗanda ake zalunta suka dube shi suka yi murna, Ba za su ƙara ɓacin rai ba. 6 Marasa galihu suka yi kira gare shi, ya kuwa amsa. Ya cece su daga dukan wahalarsu. 7 Mala'ikansa yana tsaron waɗanda suke tsoron Ubangiji, Ya cece su daga hatsari. 8 Ku gane da kanku yadda Ubangiji yake da alheri! Mai farin ciki ne mutumin da ya sami kwanciyar rai a wurinsa! 9 Ku yi tsoron Ubangiji ku jama'arsa duka, Masu tsoronsa suna da dukan abin da suke bukata. 10 Har zakoki sukan rasa abinci su ji yunwa, Amma masu biyayya ga Ubangiji, Ba abu mai kyau da sukan rasa. 11 Ku zo, ku abokaina, ku kasa kunne gare ni, Zan koya muku ku ji tsoron Ubangiji. 12 Kuna so ku ji daɗin rai? Kuna son tsawon rai da farin ciki? 13 To, ku yi nisa da mugun baki, Da faɗar ƙarairayi. 14 Ku rabu da mugunta, ku aikata alheri, Ku yi marmarin salama, ku yi ƙoƙarin samunta. 15 Ubangiji yana lura da adalai, Yana kasa kunne ga koke-kokensu, 16 Amma yana ƙin masu aikata mugunta, Saboda haka har mutanensu sukan manta da su. 17 Adalai sukan yi kira ga Ubangiji, yakan kuwa kasa kunne, Yakan cece su daga dukan wahalarsu. 18 Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai, Yakan ceci waɗanda suka fid da zuciya. 19 Mutumin kirki yakan sha wahala da yawa, Amma Ubangiji yakan cece shi daga cikinsu duka. 20 Ubangiji yakan kiyaye shi sosai, Ba ko ɗaya daga cikin ƙasusuwansa da zai karye ba. 21 Mugunta za ta kashe mugu, Waɗanda suke ƙin adalai za a hukunta su. 22 Ubangiji zai fanshi bayinsa, Waɗanda suka tafi wurinsa neman mafaka Za a bar su da rai.

Zabura 35

Addu'ar Kuɓuta daga Maƙiya

1 Ka yi hamayya da masu hamayya da ni, ya Ubangiji, Ka yi faɗa da masu faɗa da ni! 2 Ɗauki garkuwa da makamanka, ka zo ka taimake ni. 3 Ka daga mashin yaƙinka sama, da gatarinka, Ka yi gaba da masu fafarata. Ka faɗa mini kai ne Mai Cetona! 4 Ka sa a kori waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni, a kunyatar da su! Ka sa waɗanda suke mini maƙarƙashiya su juya da baya, su ruɗe! 5 Ka sa su zama kamar tattakar da iska take kwashewa, Kamar waɗanda mala'ikan Ubangiji yake korarsu! 6 Ka sa hanyarsu ta duhunta, ta yi santsi, A sa'ad da mala'ikan Ubangiji yake fyaɗe su ƙasa! 7 Suka kafa mini tarko ba dalili, Sun kuma haƙa rami mai zurfi don in faɗa ciki. 8 Amma kafin su farga, hallaka za ta kama su. Tarkunan da suka kafa za su kama su, Su kuma fāɗa cikin ramin da suka haƙa! 9 Sa'an nan zan yi murna saboda Ubangiji, Zan yi murna, gama ya cece ni. 10 Da zuciya ɗaya zan ce wa Ubangiji, “Ba wani kamarka! Kakan kāre marasa ƙarfi daga masu ƙarfi, Talaka da matalauci kuma daga azzalumai!” 11 Mugaye suna ba da muguwar shaida a kaina, Suna kai ƙarata a kan laifofin da ban san kome a kansa ba. 12 Sun sāka mini alheri da mugunta, Cike nake da nadama. 13 Amma sa'ad da suke ciwo, nakan sa tufafin makoki, Na ƙi cin abinci, Na yi addu'a da kaina a sunkuye, 14 Kamar yadda zan yi wa aboki ko ɗan'uwa addu'a. Ina tafe a takure saboda makoki, Kamar wanda yake makoki domin mahaifiyarsa. 15 Sa'ad da nake shan wahala, Murna suke yi duka, Sun kewaye ni, suna ta yi mini dariya, Baƙi sun duke ni, suna ta buguna. 16 Suka wahalshe ni, suka yi mini dariya, Suna hararata da ƙiyayya. 17 Sai yaushe, za ka duba, ya Ubangiji? Ka kuɓutar da ni daga farmakinsu, Ka ceci raina daga waɗannan zakoki! 18 Sa'an nan zan yi maka godiya a gaban babban taron jama'a. Zan yabe ka a gaban babban taro. 19 Kada ka bar maƙiyana, maƙaryatan nan, su ga fāɗuwata! Kada ka bar waɗanda suke ƙina ba dalili, Su ƙyaface ni, su yi murna saboda baƙin cikina! 20 Ba su yin maganar zumunci, A maimakon haka sukan ƙaga ƙarairayi a kan masu ƙaunar limana. 21 Sukan zarge ni da kakkausan harshe, Su ce, “Mun ga abin da ka yi!” 22 Amma kai, ya Ubangiji ka ga wannan. Saboda haka kada ka ƙyale su, ya Ubangiji, Kada ka yi nisa! 23 Ka tashi, ya Ubangiji, ka kāre ni. Ya Allah ka tashi, ka bi mini hakkina. 24 Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, ka shaida rashin laifina, Kada ka bar maƙiyana su ƙyaface ni, ya Allahna! 25 Kada ka bar su su ce ce wa kansu, “Madalla! Da ma abin da muke so ke nan!” Kada ka bar su su ce, “Mun rinjaye shi!” 26 Ka sa waɗanda suka ƙyaface ni a wahalata, A rinjaye su, su ruɗe. Ka sa waɗanda suke ɗaukar kansu sun fi ni, Su sha kunya da wulakanci! 27 Ka sa waɗanda suke murna da kuɓutata Su yi ta sowa ta murna, suna cewa, “Ubangiji mai girma ne! Yana murna da cin nasarar bawansa!” 28 Sa'an nan zan yi shelar adalcinka, Dukan yini kuwa zan yi ta yabonka.

Zabura 36

Madawwamiyar Ƙaunar Allah

1 Zunubi yakan yi magana da mugun daga can gindin zuciyarsa, Yakan ƙi Allah, ba ya jin tsoronsa. 2 Domin yana ganin kansa shi wani abu ne, A tsammaninsa Allah ba zai tona asirinsa ba, Ya hukunta zunubinsa. 3 Maganarsa mugunta ce cike da ƙarairayi, Ba shi da sauran isasshiyar hikima da zai aikata nagarta. 4 Yana ƙulla mugunta lokacin da yake kwance a gadonsa, Halinsa ba shi da kyau, Ba ya ƙin abin da yake mugu. 5 Madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ta kai har sammai, Amincinka ya kai sararin sammai. 6 Adalcinka kafaffe ne, Kamar namyan duwatsu. Hukuntanka kamar teku mai zurfi suke. Ya Ubangiji, kai kake lura da mutane da dabbobi. 7 Ina misalin darajar madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji! Mutane sukan sami mafarka a ƙarƙashin fikafikanka. 8 Sukan yi biki da yalwataccen abincin da yake Haikalinka, Kakan shayar da su daga koginka na alheri. 9 Kai ne mafarin dukan rai, Saboda haskenka ne kuma, muke ganin haske, 10 Ka yi ta ƙaunar waɗanda suka san ka, Ka yi wa adalai alheri. 11 Kada ka bar masu girmankai su fāɗa mini, Kada ka bar mugaye su kore ni. 12 Dubi inda mugaye suka fāɗi! Can suka kwanta, ba su iya tashi.

Zabura 37

Makomar Mugaye da ta Nagargaru

1 Kada ka damu saboda mugaye, Kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba. 2 Za su shuɗe kamar busasshiyar ciyawa, Za su mutu kamar yadda tsire-tsire yake bushewa. 3 Ka dogara ga Ubangiji ka aikata nagarta, Ka zauna a ƙasar, ka sami lafiya. 4 Ka nemi farin cikinka a wurin Ubangiji, Zai kuwa biya maka bukatarka. 5 Ka miƙa kanka ga Ubangiji, Ka dogara gare shi, zai kuwa taimake ka. 6 Zai sa nagartarka ta haskaka kamar haske, Adalcinka kuma ya haskaka kamar tsakar rana. 7 Ka natsu a gaban Ubangiji, Ka yi haƙuri, ka jira shi, Kada ka damu da waɗanda suke da dukiya, Ko su da suka yi nasara da aikata mugayen shirye-shiryensu. 8 Kada ka yi fushi, kada ka hasala! Kada ka damu! Gama ba zai yi maka amfanin kome ba. 9 Waɗanda suka dogara ga Ubangiji, Za su yi zamansu lafiya a ƙasar, Amma za a kori mugaye. 10 A ɗan ƙanƙanen lokaci mugaye za su shuɗe, Za ka neme su, amma ba za a same su ba, 11 Amma masu ladabi za su zauna lafiya a ƙasar, Su ji daɗin cikakkiyar salama. 12 Mugu yakan yi wa mutumin kirki makarƙashiya, Yana harararsa da ƙiyayya. 13 Ubangiji yana yi wa mugu dariya, Domin Ubangiji ya sani ba da daɗewa ba mugun zai hallaka. 14 Mugaye sun zare takuba, Sun tanƙware bakkunansu Don su kashe matalauta da masu bukata, Su karkashe mutanen kirki. 15 Amma takubansu za su sassoke su, Za a kakkarya bakkunansu. 16 Ƙanƙanen abin da mutumin kirki yake da shi, Ya fi dukan dukiyar mugaye amfani, 17 Gama Ubangiji zai raba mugaye da ƙarfinsu, Amma zai kiyaye mutanen kirki. 18 Ubangiji yana kula da masu yi masa biyayya, Ƙasar kuwa za tama tasu har abada. 19 Ba za su sha wahala a lokacin tsanani ba, Za su sami yalwa a lokacin yunwa. 20 Amma mugaye za su mutu, Magabtan Ubangiji kuwa za su shuɗe kamar furen jeji, Za su ɓace kamar hayaƙi. 21 Mugu yakan ci bashi, ya ƙi biya, Amma mutumin kirki mai alheri ne, Mai bayarwa hannu sake. 22 Waɗanda Ubangiji ya sa wa albarka, Za su zauna lafiya lau a ƙasar, Amma waɗanda ya la'anta Za a kore su su fita. 23 Ubangiji yakan bi da mutum lafiya A hanyar da ya kamata ya bi, Yakan ji daɗin halinsa, 24 In ya fāɗi, ba zai yi warwar ba, Gama Ubangiji zai taimake shi Ya tashi tsaye. 25 Yanzu dai na tsufa, ni ba yaro ba ne, Amma ban taɓa ganin Ubangiji ya yar da mutumin kirki ba, Ko kuma a ga 'ya'yansa suna barar abinci. 26 A koyaushe yakan bayar a sake, Yana ba da rance ga waɗansu, 'Ya'yansa kuwa dalilin albarka ne. 27 Ka rabu da mugunta ka aikata nagarta, Za ka kuwa zauna a ƙasar har abada, 28 Gama Ubangiji yana ƙaunar abin da yake daidai, Ba ya rabuwa da amintattun jama'arsa, Yana kiyaye su koyaushe, Amma za a kori zuriyar mugaye. 29 Adalai za su yi zamansu lafiya a ƙasar, Su gāje ta har abada. 30 Kalmomin mutumin kirki suna da hikima, Yana faɗar abin da yake daidai. 31 Yakan riƙe dokar Allahnsa a zuciyarsa, Ba ya kauce mata, faufau. 32 Mugu yakan yi fakon mutumin kirki, Ya yi ƙoƙari ya kashe shi, 33 Amma Ubangiji ba zai bar shi a hannun magabtansa ba, Ko kuwa ya bari a kāshe shi Sa'ad da ake masa shari'a. 34 Ka sa zuciyarka ga Ubangiji Ka kiyaye dokokinsa, Shi zai ba ka ƙarfin da za ka mallaki ƙasar, Za ka kuwa ga an kori mugaye. 35 Na ga wani mugu, azzalumi, Ya fi kowa tsayi, Kamar itacen al'ul na Lebanon, 36 Amma bayan ƙanƙanen lokaci, Da na zaga, ban gan shi ba, Na neme shi, amma ban same shi ba. 37 Dubi mutumin kirki, ka lura da adali, Mutumin salama yakan sami zuriya, 38 Amma za a hallaka masu zunubi ƙaƙaf, Za a kuma shafe zuriyarsu. 39 Ubangiji yakan ceci adalai, Ya kiyaye su a lokatan wahala. 40 Yakan taimake su, ya kuɓutar da su, Yakan cece su daga mugaye, Gama sukan zo wurinsa don ya kāre su.

Zabura 38

Addu'ar Mai Shan Wuya

1 Kada ka yi fushi har ka tsauta mini, ya Ubangiji! Kada ka hukunta ni da fushinka! 2 Ka hukunta ni, ka kuwa yi mini rauni, Ka kuma buge ni har ƙasa. 3 Saboda fushinka ina ciwo mai tsanani, Duk jikina ya kamu da ciwo saboda zunubina. 4 Ina nutsewa cikin ambaliyar zunubaina, Ina jin nauyinsu, sun danne ni ƙasa. 5 Saboda wawancina, miyakuna sun ruɓe, suna wari, 6 An tanƙware ni, an ragargaza ni, Ina ta kuka dukan yini. 7 Ina fama da zazzaɓi, Ina rashin lafiya ƙwarai. 8 An ragargaza ni sarai, an kuwa ci nasara a kaina, Na damu a zuciyata, ina nishi don zafi. 9 Ka san bukatata, ya Ubangiji, Kana jin dukan nishe-nishena. 10 Zuciyata tana ɗar, ƙarfina ya ƙāre, Idanuna sun dushe. 11 Abokaina da maƙwabtana ba su ko zuwa kusa da ni, saboda miyakuna, Har iyalina ma sun guje mini. 12 Masu son kashe ni, sun haƙa mini tarkuna, Masu so su cuce ni, suna barazanar lalatar da ni, Yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya. 13 Kamar kurma nake, ba na iya ji, Kamar kuma bebe, ba na iya magana. 14 Ni kamar mutumin da ba ya iya amsawa nake, don ba na ji. 15 Na dogara gare ka, ya Ubangiji, Kai za ka amsa mini, ya Ubangiji Allahna. 16 Kada ka bar magabtana su yi murna saboda wahalata. Kada ka bar su su yi kirari a kan fāɗuwata! 17 Ina gab da fāɗuwa, Ina cikin azaba kullum. 18 Na hurta zunubaina, Sun cika ni da taraddadi. 19 Magabtana lafiyayyu ne masu ƙarfi. Waɗanda suke ƙina ba dalili, suna da yawa. 20 Masu rama nagarta da mugunta, Suna gāba da ni, Domin ina ƙoƙarin aikata abin da yake daidai. 21 Kada ka yashe ni, ya Ubangiji, Kada ka rabu da ni, ya Allahna! 22 Sai ka taimake ni yanzu, ya Ubangiji, Mai Cetona!

Zabura 39

Rai Mai Halin Shuɗewa

1 Na ce, “Zan yi hankali da abin da nake yi, Don kada harshena ya sa ni zunubi, Ba zan ce kome ba sa'ad da mugaye suke kusa.” 2 Na yi shiru, ban ce kome ba, Ko a kan abin da yake da kyau! Amma duk da haka wahalata sai ƙaruwa take yi, 3 Zuciyata kuwa ta cika da taraddadi, Bisa ga yawan tunanina, haka yawan wahalata zai zama, Dole ne in yi ta tambaya, 4 “Ya Ubangiji, kwana nawa zan yi a duniya? Yaushe zan mutu? Ka koya mini ranar da ajalina zai auko. 5 “Ga shi, ka gajerta yawan kwanakina! Yawan kwanakina a wurinka kamar ba kome ba ne. Hakika duk mutum mai rai, Bai fi shaƙar iska ba. 6 Bai kuma fi inuwa ba! Duk abin da yake yi banza ne, Yakan tara dukiya, amma bai san wanda zai more ta ba! 7 “A kan me zan sa zuciya, ya Ubangiji? A gare ka nake dogara. 8 Ka cece ni daga dukan zunubaina, Kada ka bar wawaye su yi mini ba'a. 9 Zan yi shiru, ba zan ce kome ba, Saboda ka sa na sha wahala haka. 10 Kada ka ƙara hukunta ni! Na kusa mutuwa saboda bugun da kake yi mini! 11 Kakan hukunta zunuban mutum ta wurin tsautawarka, Kamar yadda asu yake lalata abu. Hakika mutum bai fi shaƙar iska ba! 12 “Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka kuma kasa kunne ga roƙona, Kada ka yi shiru sa'ad da na yi kuka gare ka! Yadda dukan kakannina suka yi, Ni baƙonka ne na ɗan lokaci. 13 Ka ƙyale ni ko zan sami kwanciyar rai, Kafin in tafi, ai, tawa ta ƙāre.”

Zabura 40

Wakar Yabo

1 Na yi ta jiran taimakon Ubangiji, Sa'an nan ya kasa kunne gare ni, ya ji kukana. 2 Ya fisshe ni daga rami mai hatsari! Ya aza ni a kan dutse lafiya lau. Ya kawar mini da tsoro. 3 Ya koya mini raira sabuwar waƙa, Waƙar yabon Allahnmu. Da yawa idan suka ga wannan za su tsorata, Za su kuwa dogara ga Ubangiji. 4 Mai farin ciki ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, Wanda bai juya ga gumaka ba, Ko ya haɗa kai da masu sujada ga allolin karya. 5 Ka yi mana abubuwa masu yawa, ya Ubangiji Allahna. Ba wani kamarka! Idan na yi ƙoƙari in faɗe su duka, Sun fi ƙarfin in faɗa. 6 Ba ka bukatar bayebaye da hadayu, Ba ka so a miƙa maka hadayun ƙonawa Na dabbobi a bisa bagade ba, Ko bayabaye don a kawar da zunubai. A maimakon haka, ka ba ni kunnuwan da zan saurare ka. 7 Sai na amsa, “Ga ni, umarnanka zuwa gare ni Suna a Littafin Shari'a. 8 Ina ƙaunar in aikata nufinka sosai, ya Allah! Ina riƙe da koyarwarka a zuciyata.” 9 A taron dukan jama'arka, ya Ubangiji, Na ba da albishir na cetonka. Ka sani ba zan fasa hurta shi ba. 10 Ban riƙe labarin cetonka don kaina kaɗai ba, Nakan yi maganar amincinka, da taimakonka a koyaushe. Ba na yin shiru a taron dukan jama'arka, Amma ina ta shaida madawwamiyar ƙaunarka da amincinka. 11 Ya Ubangiji, na sani ba za ka fasa yi mini jinƙai ba! Ƙaunarka da amincinka za su kiyaye lafiyata kullum. 12 Wahalai iri iri sun kewaye ni, har ba su ƙidayuwa! Alhakin zunubaina ya tarar da ni, Har ba na iya gani, Sun fi gashin kaina yawa, na karaya. 13 Ka cece ni, ya Allah, Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni! 14 Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina Su koma baya, su sha kunya! 15 Ka sa waɗanda suke mini ba'a Su razana sabili da fāɗuwarsu! 16 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka Su yi murna, su yi farin ciki! Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!” 17 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki, Ya Allah, ka zo wurina da hanzari. Kai ne mataimakina da Mai Cetona, Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!

Zabura 41

Addu'ar Roƙon Warkewa

1 Mai farin ciki ne wanda yake kula da matalauta, Ubangiji zai taimake shi sa'ad da yake shan wahala. 2 Ubangiji zai kiyaye shi, ya keɓe ransa. Ubangiji zai sa ya ji daɗi a ƙasar, Ba zai bar shi a hannun magabtansa ba. 3 Ubangiji zai taimake shi sa'ad da yake ciwo Ya mayar masa da lafiyarsa. 4 Na ce, “Na yi maka zunubi, ya Ubangiji, Ka yi mini jinƙai ka warkar da ni!” 5 Magabtana suna mugayen maganganu a kaina, Suna cewa, “Yaushe ne zai mutu a manta da shi?” 6 Masu zuwa su gaishe ni ba da zuciya ɗaya suke zuwa ba, Sukan tattara duk mugun labari a kaina Sa'an nan su je su yi ta bazawa ko'ina. 7 Maƙiyana duk suna raɗa da junansu a kaina, Sukan ɗauka na fi kowa mugunta. 8 Suna cewa, “Yana ciwon ajali, Ba zai taɓa tashi daga gadonsa ba.” 9 Har da shaƙiƙin abokina, Wanda na fi amincewa da shi. Wanda muke ci tare, ya juya yana gāba da ni. 10 Ka ji ƙaina ya Ubangiji, ka maido mini da lafiyata, Zan kuwa sāka wa magabtana! 11 Zan sani kana jin daɗina, Domin ba za su rinjaye ni ba, 12 Za ka taimake ni domin ina yin abin da yake daidai, Za ka sa ni a gabanka har abada. 13 Bari mu yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila. Ku yabe shi yanzu da har abada! Amin! Amin!

Zabura 42

Kewar Allah a Baƙuwar Ƙasa

1 Kamar yadda kishimi yake marmarin ruwan sanyi daga rafi, Haka nake marmarinka, ya Allah. 2 Ina jin ƙishinka, ya Allah, ya Allah Mai Rai, Yaushe zan tafi in yi sujada a gabanka? 3 Dare da rana ina kuka, Hawayena kaɗai su ne abincina, A kowane lokaci maƙiyana suna ta tambayata, “Ina Allahnka?” 4 Zuciyata takan ɓaci in na tuna da abin da ya wuce, Sa'ad da nakan tafi tare da taron jama'a zuwa Haikalin Allah, Ina bishe su a jere. Taron jama'a masu farin ciki, suna raira waƙa, Suna ta da murya, suna yabon Allah. 5 Me ya sa nake baƙin ciki haka? Me ya sa nake damuwa ƙwarai? Zan dogara ga Allah, Zan sāke yin yabonsa, Mai Cetona, Allahna. 6 Zuciyata ta karai Saboda haka zan tuna da kai A wajen Urdun, da kusa da Dutsen Harmon, da na Mizar, Zan tuna da kai. 7 Zurfafan tekuna suna kiran junansu, Matsirgar ruwa na Allah kuwa suna ta ruri! Igiyoyin ruwa na baƙin ciki Suka yi wa raina ambaliya. 8 Ubangiji ya nuna madawwamiyar ƙaunarsa kowace rana! Ni ma in raira yabo gare shi kowane dare, In yi addu'a ga Allah, wanda ya ba ni rai. 9 Ga Allah wanda yake tsarona yana ce, “Me ya sa ka manta da ni? Me ya sa nake ta shan wahala Saboda muguntar maƙiyana?” 10 An ragargaza ni da zargin maƙiyana Waɗanda suke tambayata kullum, “Ina Allahnka?” 11 Me ya sa ni ɓacin rai haka? Me ya sa ni damuwa? Zan dogara ga Allah. Har yanzu ma zan yabe shi, Mai Cetona, Allahna.

Zabura 43

Addu'ar Wanda aka Kai Baƙuwar Ƙasa ala Tilas

1 Ya Allah, ka kuɓutar da ni, Ka kiyaye al'amarina daga marasa tsoronka, Ka cece ni daga ƙaryar mugaye! 2 Ya Allah, kai ne kake kāre ni, Me ya sa ka yashe ni? Me ya sa nake ta shan wahala saboda muguntar maƙiyana? 3 Ka aiko da haskenka, da gaskiyarka, Bari su bishe ni, Su kawo ni Sihiyona, tsattsarkan tudunka, Su kawo ni Haikalinka, inda zatinka yake! 4 Sa'an nan zan tafi wurin bagadenka, ya Allah, Zuwa gare ka, kai wanda kake sa ni in yi murna da farin ciki, In raira waƙar yabo a gare ka da garayata, Ya Allah, Allahna! 5 Me ya sa nake baƙin ciki? Me ya sa nake damuwa? Zan dogara ga Allah, Zan ƙara yabonsa, Mai Cetona, Allahna.

Zabura 44

Addu'ar Neman Ceto

1 Da kunnuwanmu muka ji, ya Allah, Kakanninmu suka faɗa mana, Manya manyan abubuwa da ka aikata a lokacinsu, A zamanin dā, 2 Yadda kai da kanka ka kori arna, Ka dasa jama'arka a ƙasaru, Yadda ka hori sauran al'umma, Amma ka sa jama'arka su wadata. 3 Ba da takubansu suka ci ƙasar ba, Ba kuwa da ikonsu suka rinjayi ƙasar ba, Amma da ikonka ne da kuma ƙarfinka, Ta wurin tabbatar musu kana tare da su, Kana nuna musu kana ƙaunarsu. 4 “Ya Allah, kai ne Sarkina, Ka ba jama'arka nasara. 5 Da ikonka muka kori abokan gābanmu, Saboda kasancewarka tare da mu Muka rinjayi magabtanmu. 6 Ban dogara ga bakana ba, Takobina kuwa ba zai cece ni ba. 7 Amma ka cece mu daga abokan gābanmu, Ka kori waɗanda suke ƙinmu. 8 Za mu yabe ka kullum, Mu yi maka godiya har abada.” 9 Amma yanzu, ya Allah, ka yashe mu, Ka bari aka kore mu, Ba ka ƙara fita ka yi tafiya tare da sojojinmu ba. 10 Ka sa muka gudu daga gaban abokan gābanmu, Suka ƙwace abin da muke da shi. 11 Ka bari aka yanyanka mu kamar tumaki, Ka warwatsar da mu a baƙuwar ƙasa. 12 Ka sayar da jama'arka A bakin 'yan kuɗi ƙalilan, Ba ka ci ribar cinikin ba. 13 Maƙwabtanmu suna yi mana dariya saboda kai, Suna yi mana ba'a, sun maishe mu abin wasa. 14 Ka maishe mu abin raini a wurin arna, Suna kaɗa mana kai, suna raina mu. 15 Kullum a cikin kunya nake, Kunya ta lulluɓe ni ɗungum, 16 Saboda dukan wulakanci, Da zagin da nake sha daga maƙiyana da abokan gābana. 17 Dukan wannan ya same mu, Ko da yake ba mu manta da kai ba, Ba mu kuma ta da alkawarin da ka yi da mu ba. 18 Ba mu ci amanarka ba, Ba mu ƙi yin biyayya da umarnanka ba. 19 Duk da haka ka ƙi taimakonmu da namomin jejin nan, Ka bar mu a cikin duhu baƙi ƙirin. 20 Da a ce mun daina yin sujada ga Allahnmu, Muka yi addu'a ga gumaka, 21 Hakika ka gane, Domin ka san asirin tunanin mutane. 22 Ya Allah, saboda kai ne ake karkashe mu a kowane lokaci, Ake kuma maishe mu kamar tumakin da za a yanyanka. 23 Ka tashi, ya Ubangiji! Me ya sa kake zama kamar mai barci? Ka tashi! Kada ka yashe mu har abada! 24 Me ya sa ka ɓuya mana? Kada ka manta da ƙuncinmu da wahalarmu! 25 Mun fāɗi, an turmushe mu a ƙasa, An bar mu kwance cikin ƙura. 26 Ka tashi ka taimake mu! Ka fanshe mu saboda madawwamiyar ƙaunarka!

Zabura 45

Waƙar Ɗaurin Auren Sarki

1 Kwanyata ta cika da kyawawan kalmomi, Lokacin da nake tsara waƙar sarki, Harshena kuwa kamar alkalami ne na ƙwararren marubuci. 2 Kai ne mafi kyau a cikin dukan mutane, Kai mai kyakkyawan lafazi ne, Kullum Allah yakan sa maka albarka! 3 Ka sha ɗamara da takobinka, ya Maɗaukakin Sarki, Kai mai iko ne, Maɗaukaki! 4 Ka yi hawan ɗaukaka zuwa nasara, Domin ka tsare gaskiya da adalci. Saboda ikonka za ka yi babban rinjaye. 5 Kibanka suna da tsini, Suna huda zuciyar abokan gābanka, Al'ummai suna fāɗuwa ƙasa a ƙafafunka. 6 Kursiyinka, ya Allah, zai dawwama har abada abadin! Kana mulkin mallakarka da adalci. 7 Kana ƙaunar abin da yake daidai, Kana ƙin abin da yake mugu. Saboda haka Allah, Allahnka, ya zaɓe ka, Ya kuwa kwararo maka farin ciki mai yawa fiye da kowa. 8 Tufafinka suna ƙanshin turaren mur, da na al'ul, da na kashiya, A kowace fādar hauren giwa, mawaƙa suna yi maka waƙar. 9 Daga cikin matan da suke fādarka, har da 'ya'yan sarakuna. A daman kursiyinka kuwa ga sarauniya a tsaye. Tana saye da kayan ado na zinariya mafi kyau duka. 10 Ki ji abin da zan faɗa, ya ke amaryar sarki, Ki manta da mutanenki da danginki. 11 Saboda ke kyakkyawa ce sarki zai so ki, Shi ne maigidanki, sai ki yi masa biyayya. 12 Mutanen Taya za su kawo miki kyautai, Attajirai za su zo su sami farin jini a gare ki. 13 Gimbiya tana fāda, kyakkyawa ce ainun, Da zaren zinariya aka saƙa rigarta, 14 Aka kai ta wurin sarki tana saye da riga mai ado. Ga 'yan matanta a biye, Aka kawo su wurin sarki. 15 Da farin ciki da murna suka zo, Suka shiga fādar sarki. 16 Za ka haifi 'ya'ya maza da yawa, Waɗanda za su maye matsayin kakanninka, Za ka sa su zama masu mulkin duniya duka. 17 Waƙata za ta sa a yi ta tunawa da sunanka har abada, Dukan jama'a za su yabe ka a dukan zamanai masu zuwa.

Zabura 46

Allah ne Mafakarmu da Ƙarfinmu

1 Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, Kullum a shirye yake ya yi taimako a lokacin wahala. 2 Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, Ko da duniya za ta girgiza, Duwatsu kuma su fāɗa cikin zurfafan teku, 3 Ko da a ce tekuna za su yi ruri su tumbatsa, Tuddai kuma su girgiza saboda tangaɗin tekun. 4 Akwai kogin da yake kawo farin ciki a birnin Allah, Da cikin tsattsarkan Haikali na Maɗaukaki. 5 Allah yana zaune cikin birnin, Ba kuwa za a hallaka birnin ba, faufau. Da asuba Allah zai kawo musu gudunmawa. 6 An kaɓantar da sauran al'umma, mulkoki suka girgiza, Allah ya yi tsawa, duniya kuwa ta narke. 7 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu! 8 Zo ku ga abin da Ubangiji ya yi! Dubi irin ayyukan al'ajabi da ya yi a duniya! 9 Ya hana yaƙoƙi ko'ina a duniya, Yana karya bakkuna, yana lalatar da māsu, Yana ƙone karusai da wuta. 10 Ya ce, “Ku yi shiru, ku sani ni ne Allah, Maɗaukaki ne cikin sauran al'umma, Maɗaukaki kuma a duniya!” 11 Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu, Allah na Yakubu shi ne mafakarmu!

Zabura 47

Allah ne Mai Mulkin Duka

1 Ku yi tāfi saboda farin ciki, Ya ku jama'a duka! Ku raira waƙoƙi da karfi, ku yabi Allah! 2 A ji tsoron Ubangiji Mai Iko Dukka, Shi babban Sarki ne, ya mallaki dukan duniya. 3 Ya ba mu nasara a bisa jama'o'i, Ya sa muka yi mulkin al'ummai, 4 Ya zaɓar mana ƙasar da muke zaune, Wadda take mallaka ce ta fāriya, ta jama'arsa Wadda yake ƙauna. 5 Allah ya hau kan kursiyinsa! Aka yi ta sowa ta murna, ana ta busa ƙahoni, Lokacin da Ubangiji yake hawa! 6 Ku raira yabbai ga Allah, Ku raira yabbai ga sarkinmu! 7 Allah sarki ne na duniya duka, Ku yabe shi da waƙoƙi! 8 Allah yana zaune kan kursiyinsa mai tsarki, Yana mulkin al'ummai, 9 Masu mulkin al'ummai suka tattaru Tare da jama'ar Allah na Ibrahim. Allah shi ne garkuwar jarumawa, Yana mulkin duka!

Zabura 48

Sihiyona Mai Daraja, Birnin Allah

1 Ubangiji mai girma ne, Dole kuwa a yabe shi da girmamawa a birnin Allahnmu, A kan tsattsarkan dutsensa. 2 Dutsen Sihiyona, dutse mai tsawo, Mai kyan gani ne na Allah, Birnin babban Sarki. Yakan kawo farin ciki ga dukan duniya! 3 Allah ya nuna akwai zaman lafiya a wurinsa, A kagarar birnin. 4 Sarakuna suka tattaru, Suka zo Dutsen Sihiyona, 5 Da suka gan shi sai suka yi mamaki, Suka tsorata suka gudu. 6 Tsoro ya kama su suka razana, Kamar mace wadda take gab da haihuwa. 7 Allah yakan hallaka manyan jiragen ruwa da iskar gabas. 8 Mun ji labarin waɗannan al'amura, Yanzu kuwa mun gan su A birnin Allahnmu, Mai Runduna, Zai kiyaye birnin lafiya har abada. 9 A cikin Haikalinka, ya Allah, Muna tunanin madawwamiyar ƙaunarka. 10 A ko'ina jama'a suna yabonka, Sunanka ya game duniya duka. Kana mulki da adalci. 11 Bari jama'ar Sihiyona su yi murna! Gama kana shari'a ta gaskiya, Bari biranen Yahuza su yi farin ciki. 12 Ku tafi ku kewaye Dutsen Sihiyona, Ku ƙirga yawan hasumiyarsa. 13 Ku lura da garukanta, ku bincike kagaranta, Saboda ku iya faɗa wa tsara mai zuwa, 14 Cewa wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin, Shi ne zai bishe mu a dukan zamanai masu zuwa.

Zabura 49

Dogara ga Dukiya Wauta Ce

1 Ku ji wannan, ko wannenku, Ku saurara jama'a duka na ko'ina, 2 Da manya da ƙanana duka ɗaya, Da attajirai da matalauta baki ɗaya. 3 Zan yi magana da hikima, Zan yi tunani mai ma'ana. 4 Zan mai da hankalina ga ka-cici-ka-cici, In bayyana ma'anarsa sa'ad da nake kaɗa molo. 5 Don me zan ji tsoro a lokacin hatsari, Sa'ad da mugaye suka kewaye ni, 6 Mutanen da suke dogara ga dukiyarsu, Waɗanda suke fāriya saboda yawan wadatarsu? 7 Har abada mutum ba zai iya fansar wani ba, Ba kuwa zai iya biyan kuɗin ransa ga Allah ba. 8 Gama kuɗin biyan ran mutum ba shi da iyaka. Abin da zai iya biya, sam ba zai isa ba, 9 Ba kuwa zai rayar da shi, Ko ya hana shi mutuwa har abada ba. 10 Yakan sa masu hikima su ma su mutu, Hakanan ma wawaye da mutanen banza, Za su mutu su bar dukiyarsu ga zuriyarsu. 11 Kaburburansu za su zama gidajensu har abada, Can za su kasance kullum, Ko da yake a dā suna da ƙasa ta kansu. 12 Girman mutum ba zai hana shi mutuwa ba, Zai mutu kamar dabba. 13 Dubi abin da zai faru ga waɗanda suke dogara ga kansu, Da irin ƙaddarar waɗanda dukiya ta ishe su. 14 Za a ƙaddara su ga mutuwa kamar tumaki, Mutuwa ce za ta yi kiwonsu. Da safe adalai za su ci nasara a kansu, Sa'ad da gawawwakinsu suke ruɓewa a ƙasar matattu, Nesa da gidajensu. 15 Amma Allah zai fanshe ni, Zai ɗauke ni daga ikon mutuwa. 16 Kada ka damu sa'ad da mutum ya zama attajiri, Ko kuwa dukiyarsa ta ƙasaita, 17 Domin ba zai ɗauke ta a lokacin mutuwarsa ba, Dukiyarsa ba za ta shiga kabari tare da shi ba. 18 Ko da a ce mutum ya sami falalar wannan rai, Ana kuwa ta yabonsa saboda nasarar da ya ci, 19 Duk da haka zai tarar da kakanninsa waɗanda suka mutu, Inda duhu ya dawwama har abada. 20 Girman mutum ba zai hana shi mutuwa ba, Zai mutu kamar dabba.

Zabura 50

Allah ne Mai Shari'a

1 Allah Maɗaukaki, Ubangiji, ya yi magana, Yana kiran dukan duniya, daga gabas zuwa yamma. 2 Allah yana haskakawa daga Sihiyona, Da cikar jamalin Sihiyona. 3 Allahnmu ya zo, ba a ɓoye yake ba, Wuta mai cinyewa na tafe a gabansa, Babban hadiri kuwa na kewaye da shi. 4 Ya kira sammai da duniya su zama shaidu, Su ga yadda yake shara'anta jama'arsa. 5 Ya ce, “Ku tattaro mini amintattuna, Waɗanda suka cika alkawarin da yake tsakanina da su, Ta wurin miƙa hadaya.” 6 Sammai suna shelar adalcin Allah, Domin shi yake yin shari'a! 7 “Ku ji, ya ku jama'ata, zan kuwa yi magana, Zan ba da shaida gāba da ku, ya Isra'ila. Ni ne Allah, Allahnku. 8 Ban tsauta muku saboda hadayunku ba, Ko saboda hadayu na ƙonawa da kuke ta miƙa mini kullum. 9 Ba na bukatar bijimai daga gonakinku, Ko awaki daga garkunanku. 10 Gama namomin jeji nawa ne, Dubban shanu da suke kan tuddai kuma nawa ne. 11 Dukan tsuntsayen da suke tashi a sararin sama nawa ne, Da dukan masu rai da suke ƙasa. 12 “Da ina jin yunwa ba sai na faɗa muku ba, Gama da duniya da dukan abin da yake cikinta nawa ne. 13 Nakan ci naman bijimai ne? Ko nakan sha jinin awaki? 14 Bari ku miƙa wa Allah hadayarku ta godiya, Ku ba Mai Iko Dukka, dukan hadayun da kuka alkawarta. 15 Ku yi kira gare ni sa'ad da wahala ta zo, Zan cece ku, Ku kuwa za ku yabe ni.” 16 Amma Allah ya ce wa mugaye, “Don me za ku haddace umarnaina? Don me za ku yi magana a kan alkawaraina? 17 Kun ƙi in tsauta muku, Kun yi watsi da umarnaina. 18 Sa'ad da kuka ga ɓarawo kukan yi abuta da shi. Kuna haɗa kai da mazinata. 19 “Kullum a shirye kuke ku hurta mugunta, Ba ku jin nauyin faɗar ƙarya. 20 A shirye kuke ku sari 'yan'uwanku, Ku sa musu laifi. 21 Kun aikata waɗannan duka, ni kuwa ban ce kome ba, Saboda haka kuka zaci ni kamar ku nake. Amma yanzu zan tsauta muku, In bayyana muku al'amarin a fili. 22 “Ku ji wannan ku da kuke ƙyale ni, In ba haka ba zan hallaka ku, Ba wanda zai cece ku. 23 Wanda yake yin godiya a sa'ad da yake miƙa hadayarsa, yana girmama ni, Da wanda yake yi mini biyayya kuma, zan nuna masa cetona.”

Zabura 51

Addu'ar Roƙon Gafara

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, Sabili da madawwamiyar ƙaunarka. Ka shafe zunubaina, Saboda jinƙanka mai girma! 2 Ka wanke muguntata sarai, Ka tsarkake ni daga zunubina! 3 Na gane laifina, Kullum ina sane da zunubina. 4 Na yi maka zunubi, kai kaɗai na yi wa, Na kuwa aikata mugunta a gare ka. Daidai ne shari'ar da ka yi mini, Daidai ne ka hukunta ni. 5 Mugu ne ni tun lokacin da aka haife ni, Mai zunubi ne ni tun daga ranar da aka haife ni. 6 Amintacciyar zuciya ita kake so, Ka cika tunanina da hikimarka. 7 Ka kawar da zunubina, zan kuwa tsarkaka, Ka wanke ni, zan kuwa fi auduga fari. 8 Bari in ji sowa ta farin ciki da murna. Ko da yake ka ragargaza ni, Ka kakkarya ni, duk da haka zan sāke yin murna. 9 Ka kawar da fuskarka daga zunubaina, Ka shafe duk muguntata. 10 Ka halitta tsarkakakkiyar zuciya a cikina, ya Allah, Ka sa sabon halin biyayya a cikina. 11 Kada ka kore ni daga gabanka, Kada ka ɗauke mini Ruhunka Mai Tsarki. 12 Ka sāke mayar mini da farin ciki na cetonka, Ka ƙarfafa ni da zuciya ta biyayya. 13 Sa'an nan zan koya wa masu zunubi umarnanka, Za su kuwa komo wurinka. 14 Ka rayar da raina, ya Allah Mai Cetona, Zan kuwa yi shelar adalcinka da farin ciki. 15 Ka taimake ni in yi magana, ya Ubangiji, Zan kuwa yabe ka. 16 Ba ka son sadakoki, ai, da na ba ka, Ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa. 17 Hadayata, ita ce halin ladabi, ya Allah, Zuciya mai ladabi da biyayya, Ba za ka ƙi ba, ya Allah. 18 Ya Allah, ka yi wa Sihiyona alheri, ka taimake ta, Ka sāke gina garun Urushalima. 19 Sa'an nan za ka ji daɗin hadaya ta ainihi, Da dukan hadayun ƙonawa. Za a miƙa bijimai hadayu a bisa bagadenka.

Zabura 52

Hukuncin Allah da Alherinsa

1 Me ya sa kake fāriya da muguntarka, Ya kai, babban mutum? Ƙaunar Allah tana nan a koyaushe. 2 Kana shirya maƙarƙashiya don ka lalatar da waɗansu, Harshenka kamar aska mai kaifi yake. Kana ƙirƙiro ƙarairayi kullum. 3 Kana ƙaunar mugunta fiye da nagarta, Kana kuwa ƙaunar faɗar ƙarya fiye da gaskiya. 4 Kana jin daɗin cutar mutane da maganganunka, Ya kai, maƙaryaci! 5 Don haka Allah zai ɓata ka har abada, Zai kama ka, ya jawo ka daga alfarwarka, Zai kawar da kai daga ƙasar masu rai. 6 Adalai za su ga wannan, su ji tsoro, Za su yi maka dariya, su ce, 7 “Duba, ga mutumin da bai dogara ga Allah Don ya sami zaman lafiyarsa ba. A maimakon haka, sai ya dogara ga wadatarsa. Yana neman zaman lafiyarsa ta wurin muguntarsa.” 8 Amma ni, kamar itacen zaitun nake, wanda yake girma kusa da Haikalin Allah, Ina dogara ga madawwamiyar ƙaunarsa har abada abadin. 9 Zan gode maka, ya Ubangiji, Saboda abin da ka aikata. Zan dogara gare ka, Sa'ad da nake sujada tare da jama'arka, Domin kai mai alheri ne.

Zabura 53

Muguntar Mutane

1 Wawaye sukan ce wa kansu, “Ba Allah.” Dukansu sun lalace, sun aikata mugayen al'amura, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai. 2 Daga Sama Allah ya dubi mutane, Ya ga ko akwai masu hikima Waɗanda suke yi masa sujada. 3 Amma dukansu sun koma baya, Su duka mugaye ne, Ba wanda yake aikata abin da yake daidai, Babu ko ɗaya. 4 Allah ya ce, “Ashe, ba su sani ba? Ashe, mugayen nan jahilai ne? Ta wurin yi wa jama'arta fashi suke rayuwa, Ba sa yin addu'a gare ni.” 5 Amma sa'an nan za su firgita ƙwarai, Irin yadda ba su taɓa yi ba, Gama Allah ya warwatsa ƙasusuwan maƙiyanka. Ya kore su sarai, saboda ya ƙi su. 6 Dā ma ceto ya zo ga Isra'ila daga Sihiyona! Sa'ad da Allah ya sāke arzuta jama'arsa, Zuriyar Yakubu za ta yi farin ciki, Jama'ar Isra'ila kuwa za ta yi murna.

Zabura 54

Addu'ar Neman Tsari daga Maƙiyi

1 Ka cece ni ta wurin ikonka, ya Allah, Ka cece ni ta wurin ƙarfinka! 2 Ka ji addu'ata, ya Allah, Ka saurari kalmomina! 3 Masu girmankai sun tasar mini, Mugaye suna nema su kashe ni, Mutanen da ba su kula da Allah ba. 4 Na sani Allah ne mai taimakona, Na sani Ubangiji shi ne mai tsarona! 5 Ubangiji ya hukunta wa maƙiyana da irin muguntarsu! Gama zai hallaka su saboda shi mai aminci ne. 6 Da murna zan miƙa maka hadaya, Zan yi maka godiya, ya Ubangiji, Domin kai mai alheri ne. 7 Ka cece ni daga dukan wahalaina, Na kuwa ga an kori maƙiyana.

Zabura 55

Addu'ar Neman Taimako

1 Ka ji addu'ata, ya Allah, Kada ka ƙi jin roƙona! 2 Ka saurare ni, ka amsa mini, Gama damuwata ta gajiyar da ni tiƙis. 3 Hankalina ya tashi saboda yawan kurarin maƙiyana, Saboda danniyar mugaye. Sukan jawo mini wahala, Suna jin haushina suna ƙina. 4 Azaba ta cika zuciyata, Tsorace-tsoracen mutuwa sun yi mini nauyi. 5 Tsoro da rawar jiki sun kama ni, Na cika da razana. 6 Na ce, “Da a ce ina da fikafikai kamar kurciya, Da sai in tashi, in tafi, in nemi wurin hutawa! 7 In tafi can nesa, In yi wurin zamana a hamada. 8 Zan hanzarta in nemi mafaka Daga iska mai ƙarfi da hadiri.” 9 Ka hallaka su, ya Ubangiji, ka birkitar da maganarsu, Gama na ga hargitsi da tawaye a birni. 10 Dare da rana suna ta yawo a kan garu suna ta kewaye birnin, Birnin kuwa cike yake da laifi da wahala. 11 Akwai hallaka a ko'ina, Tituna suna cike da azzalumai da 'yan danfara. 12 Da a ce maƙiyina ne yake mini ba'a, Da sai in jure. Da a ce abokin gābana ne yake shugabancina, Da sai in ɓuya masa. 13 Amma kai ne, aminina, Abokin aikina ne, abokina ne kuma! 14 Dā mukan yi taɗi da juna ƙwarai, Mukan tafi Haikali tare da sauran jama'a. 15 Allah ya sa mutuwa ta auko wa maƙiyana ba labari, Allah ya sa su gangara ƙasar matattu da ransu! Mugunta tana cikin gidajensu da zukatansu. 16 Amma ina kira ga Allah, ya taimake ni, Ubangiji kuwa zai cece ni. 17 Koke-kokena da nishe-nishena Suna hawa zuwa gare shi da safe, da tsakar rana, da dad dare, Zai kuwa ji muryata. 18 Zai fisshe ni lafiya Daga yaƙe-yaken da nakan yi da magabtana masu yawa. 19 Allah, shi wanda yake mulki tun fil azal, Zai ji ni, zai kore su. Ba abin da suka iya yi a kai, Domin ba su tsoron Allah. 20 Abokina na dā, Ya yi wa abokansa faɗa, Ya ta da alkawarinsa. 21 Kalmominsa sun fi mai taushi, Amma ƙiyayya tana a zuciyarsa, Kalmominsa sun fi mai sulɓi, Amma suna yanka kamar kakkaifan takobi. 22 Ka gabatar da wahalarka ga Ubangiji, Zai kuwa taimake ka, Ba zai bari a ci nasara a kan mutumin kirki ba, faufau. 23 Amma kai, ya Allah, za ka jefar da masu kisankai, da maƙaryata can ƙasa cikin zurfafa, Kafin su kai rabin kwanakinsu a duniya. Amma ni, zan dogara gare ka.

Zabura 56

Addu'ar Dogara ga Allah

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, Gama mutane sun tasar mini, Maƙiyana suna tsananta mini koyaushe! 2 Dukan yini maƙiyana suna tasar mini, Waɗanda suke faɗa da ni sun cika yawa. 3 Sa'ad da nake jin tsoro, ya Maɗaukaki, A gare ka nake dogara. 4 Ga Allah nake dogara, ina yabon alkawarinsa, Gare shi na dogara, ba zan ji tsoro ba. Me mutum kawai zai yi mini? 5 Maƙiyana suke ta wahalshe ni dukan yini, A kan kowane abu da nake yi, Kullum suna ta tunanin yadda za su cuce ni! 6 Sukan taru a ɓoye, Suna kallon duk abin da nake yi. Suna sa zuciya za su iya kashe ni. 7 Ka hukunta su, ya Allah saboda muguntarsu, Da fushinka ka kori waɗannan mutane! 8 Ka san irin wahalar da nake sha, Kana riƙe da lissafin yawan hawayena. Ashe, ba a rubuce suke a littafinka ba? 9 A ranar da na yi kira gare ka, Za a komar da abokan gābana baya, Gama na sani Allah yana tare da ni! 10 Ina dogara ga Allah, ina yabon alkawarinsa, Ina dogara ga Ubangiji, ina yabon alkawarinsa. 11 A gare shi nake dogara, Ba zan ji tsoro ba. Me mutum kawai zai yi mini? 12 Zan miƙa maka abin da na yi alkawari, ya Allah, Zan miƙa maka hadaya ta godiya. 13 Domin ka cece ni daga mutuwa, Ka hana a ci nasara a kaina. Saboda haka a gaban Allah nake tafiya A hasken da yake haskaka wa masu rai.

Zabura 57

Addu'ar Neman Kuɓuta daga Tsanani

1 Ka yi mini jinƙai, ya Allah, ka yi jinƙai, Gama na zo gare ka neman tsira. Zan sami kāriya a ƙarƙashin fikafikanka, Sai dukan hatsari ya wuce. 2 Zan yi kira ga Allah, Maɗaukaki, Zan yi kira ga Allah, mai biyan dukan bukatata. 3 Daga sammai Allah zai amsa mini, Zai kori waɗanda suka tasar mini, Allah zai nuna mini madawwamiyar ƙaunarsa da amincinsa. 4 Raina yana tsakiyar zakoki, Na kwanta a tsakiyar waɗanda suka yi niyyar cinye mutane. Haƙoransu kamar māsu da kibau suke, Harsunansu masu kaifi ne kamar takobi. 5 Ka bayyana girmanka ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya! 6 Maƙiyana sun kafa tarko don su kama ni, Damuwa ta fi ƙarfina. Sun yi wushefe a kan hanyata, Amma su da kansu suka fāɗa a ciki. 7 A shirye nake, ya Allah, Na shirya sosai! Zan raira waƙoƙi in yabe ka! 8 Ka farka, ya raina! Ku farka, molona da garayata! Zan sa rana ta farka! 9 Zan gode maka a cikin sauran al'umma, ya Ubangiji! Zan yabe ka a cikin jama'a! 10 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har sammai, Amincinka kuma har sararin sammai. 11 Ka bayyana girmanka, ya Allah, a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya!

Zabura 58

Addu'ar don a Hukunta Mugaye

1 Hakika za ku yanka daidai, ku manya? Za ku shara'anta wa mutane daidai? 2 A'a, tunanin muguntar da za ku aikata kaɗai kuke yi, Kuna aikata laifofin ta da hargitsi a ƙasar. 3 Mugaye, laifi suke yi dukan kwanakinsu, Tun daga ranar da aka haife su suke ta faɗar ƙarya. 4 Cike suke da dafi kamar macizai, Sukan toshe kunnuwansu kamar kuraman gamsheƙa, 5 Wanda ba ya jin muryar gardi, Ko kuma waƙar gwanin sihiri. 6 Ka kakkarya haƙoransu, ya Allah, Ka ciccire fiƙoƙin waɗannan zakoki masu zafin rai, ya Ubangiji! 7 Bari su ɓace kamar ruwan da ya tsanye, Bari a murtsuke su kamar ciyayi a hanya. 8 Bari su zama kamar katantanwu waɗanda sukan narke su yi yauƙi, Allah ya sa su zama kamar jinjirin da aka haifa matacce. Wanda bai taɓa ganin hasken rana ba. 9 Kafin tukunya ta ji zafin wuta, Da zafin fushi, Allah zai watsar da su tun suna da rai. 10 Adalai za su yi murna sa'ad da suka ga an hukunta masu zunubi, Za su wanke ƙafafunsu cikin jinin mugaye. 11 Mutane za su ce, “Hakika an sāka wa adalai, Hakika akwai Allah wanda yake shara'anta duniya!”

Zabura 59

Addu'ar Neman Ceto daga Maƙiya

1 Ka cece ni daga maƙiyana, ya Allahna, Ka kiyaye ni daga waɗanda suka tasar mini! 2 Ka cece ni daga waɗannan mugaye, Ka tsirar da ni daga masu kisankan nan! 3 Duba! Suna jira su auka mini, Mugaye suna taruwa gāba da ni, Ba domin wani zunubi ko wani laifin da na yi ba, 4 Ba domin na yi wani laifi ba, ya Ubangiji, Har da suka gaggauta gāba da ni. Kai da kanka ka gani, ya Allah na Isra'ila! Ka tashi ka taimake ni. 5 Ka tashi, ya Ubangiji, Allah Maɗaukaki, ka taimake ni, Ka tashi ka hukunta al'ummai, Kada ka yi wa waɗannan mugaye, maciya amana, jinƙai! 6 Da maraice suka komo, Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni. 7 Ji abin da suke fada! Harsunansu suna kama da takuba a bakinsu, Duk da haka suna ta tambaya, suna cewa, “Wa zai ji mu?” 8 Amma kai dariya kake yi musu, ya Ubangiji, Ka mai da al'ummai duka abin bandariya! 9 Mai tsarona, kai ne kake kiyaye ni, Kai ne mafakata, ya Allah. 10 Allahna wanda yake ƙaunata, zai zo gare ni, Zai sa in ga an kori magabtana. 11 Kada ka kashe su, ya Allah, don kada jama'ata su manta. Ka watsar da su da ikonka, ka hallaka su ya Ubangiji mai kiyaye mu! 12 Zunubi na cikin leɓunansu, maganganunsu na zunubi ne, Da ma a kama su saboda girmankansu, Domin suna la'antarwa, suna ƙarya! 13 Da fushinka ka hallaka su, Ka hallaka su ɗungum. Sa'an nan jama'a za su sani Allah yana mulkin Isra'ila, Mulkinsa ya kai ko'ina a duniya! 14 Da maraice maƙiyana suka komo, Suna yaƙe haƙora kamar karnukan da suke yawo ko'ina a birni. 15 Suna kai da kawowa ko'ina neman abinci, In ba su sami abin da ya ishe su ba, Sukan yi gunaguni. 16 Amma zan raira waƙa a kan ikonka, Kowace safiya zan raira waƙa da ƙarfi Ga zancen madawwamiyar ƙaunarka. Kai mafaka ne a gare ni, Wurin ɓuya a kwanakin wahala. 17 Zan yabe ka, mai tsarona, Allah ne mafakata, Allah wanda ya ƙaunace ni.

Zabura 60

Addu'ar Neman Taimako

1 Ka rabu da mu, ya Allah, har aka ci nasara a kanmu, Ka yi fushi da mu, amma yanzu sai ka juyo wurinmu! 2 Ka sa ƙasar ta girgiza, ka tsaga ta. Yanzu sai ka warkar da tsaguwarta, gama tana gab da fāɗuwa! 3 Ka sa jama'arka su sha wahala ƙwarai, Ka ba mu ruwan inabin da ya bugar da mu. 4 Ka ta da tuta ga masu tsoronka, Domin su juya su gudu daga abokin gāba. 5 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu'ata, Domin jama'ar da kake ƙauna ta sami cetonka. 6 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce, “Da nasara zan raba Shekem, Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama'ata. 7 Gilyad tawa ce, har da Manassa ma, Ifraimu ne kwalkwalina, Yahuza kuma sandana ne na sarauta. 8 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki, Edom kuwa kamar akwatin takalmina. Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.” 9 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara? Wa zai kai ni Edom? 10 Da gaske ka yashe mu ke nan? Ba za ka yi tafiya tare da sojojinmu ba? 11 Ka taimake mu, mu yaƙi abokan gāba, Domin taimako irin na mutum banza ne! 12 Idan Allah yana wajenmu, Za mu yi nasara, Zai kori abokan gābanmu.

Zabura 61

Dogara ga Kiyayewar Allah

1 Ya Allah, ka ji kukana, Ka ji addu'ata! 2 Sa'ad da nake nesa da gida, zuciyata ta karai, Zan yi kira gare ka! Ka kai ni lafiyayyiyar mafaka. 3 Kai ne kāriyata mai ƙarfi Da take kiyaye ni daga maƙiyana. 4 Ka yarda in zauna a alfarwarka dukan kwanakin raina, Ka yarda in sami zaman lafiya a ƙarƙashin fikafikanka. 5 Ya Allah, kā ji alkawaraina, Kā kuwa ba ni abin da ya dace, Tare da waɗanda suke ɗaukaka ka. 6 Ka ƙara wa sarki tsawon rai, Ka sa ya rayu dukan lokaci! 7 Ka sa ya yi mulki har abada a gabanka, ya Allah, Ka tsare shi da madawwamiyar ƙaunarka, da amincinka. 8 Don haka zan yi ta raira waƙar yabonka kullayaumin, A sa'ad da nake miƙa maka abin da na alkawarta.

Zabura 62

Allah ne kaɗai Mafaka

1 Ga Allah kaɗai na dogara, Cetona daga gare shi yake fitowa. 2 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona, Shi ne kariyata, Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam. 3 Har yaushe dukanku za ku fāɗa wa wani don ku yi nasara da shi, Kamar rusasshen garu, Ko kuma dangar da ta fāɗi? 4 Ba abin da kuke so, sai ku ƙasƙantar da shi daga maƙaminsa na daraja, Kuna jin daɗin yin ƙarairayi. Kuna sa masa albarka, Amma a zuciyarku la'antarwa kuke yi. 5 Ga Allah kaɗai na dogara, A gare shi na sa zuciyata. 6 Shi kaɗai ne mai kiyaye ni, Mai Cetona, Shi ne kariyata, Ba kuwa za a yi nasara da ni ba sam. 7 Cetona da darajata daga Allah ne, Shi ne ƙaƙƙarfan makiyayina, Shi ne mafakata. 8 Ya jama'ata, ku dogara ya Allah a kowane lokaci! Ku faɗa masa dukan wahalarku, Gama shi ne mafakarmu. 9 Talakawa kamar shaƙar numfashi suke, Manyan mutane, su ma haka suke marasa amfani. Ko an auna su a ma'auni, sam ba su da nauyin kome, Sun fi numfashi shakaf. 10 Kada ku dogara da aikin kama-karya. Kada ku sa zuciya za ku ci ribar kome ta wurin fashi. In kuwa dukiyarku ta ƙaru, Kada ku dogara gare ta. 11 Sau ɗaya Allah ya faɗa, Sau biyu na ji, cewa Allah yake da iko. 12 Madawwamiyar ƙauna, ta Ubangiji ce. Kai kanka, ya Ubangiji, kake sāka wa Kowane mutum bisa ga ayyukansa.

Zabura 63

Sa Zuciya ga Allah

1 Ya Allah, kai ne Allahna, Ina sa zuciya gare ka. Duk niyyata ta nemanka ce, Raina yana ƙishinka, Kamar bussasshiyar ƙasa, Wadda ta zozaye, ba ta da ruwa. 2 Bari in gan ka a tsattsarkan wurinka, In dubi ɗaukakarka da darajarka. 3 Madawwamiyar ƙaunarka ta fi rai kansa, Saboda wannan zan yabe ka. 4 Muddin raina, zan yi maka godiya, Zan ta da hannuwana sama, in yi addu'a gare ka. 5 Raina zai yi liyafa, ya ƙoshi sosai, Ni kuwa zan raira waƙoƙin murna na yabo a gare ka. 6 Sa'ad da nake kwance a gadona na tuna da kai, Dare farai ina ta tunawa da kai, 7 Domin kai kake taimakonka kullayaumin. Da murna, nake raira waƙa, A inuwar fikafikanka, 8 Raina yana manne maka, Ikonka yana riƙe da ni. 9 Waɗanda suke ƙoƙari su kashe ni, Za su gangara zuwa lahira, 10 Za a kashe su cikin yaƙi, Kyarketai kuwa za su cinye gawawwakinsu. 11 Sarki zai yi farin ciki ga Allah, Duk waɗanda suka yi alkawarai da sunan Allah Za su yi murna, Amma za a rufe bakunan maƙaryata.

Zabura 64

Addu'ar Neman Tsari

1 Ina shan wahala, ya Allah, ka ji addu'ata! Ina jin tsoro, ka cece ni daga maƙiyana! 2 Ka kiyaye ni daga ƙulle-ƙullen mugaye, Da iskancin mugayen mutane. 3 Sukan wasa harsunansu kamar takuba, Sukan kai bāra da mugayen maganganu kamar kibau. 4 Sukan yi kwanto su harbi mutanen kirki da kibau, Nan da nan sukan yi harbi, ba su kuwa jin tsoro. 5 Suna ƙarfafa junansu cikin yin mugayen ƙulle-ƙullensu, Sukan yi ta taɗi a kan inda za su kafa tarkunansu. “Ba wanda zai ga mu,” in ji su. 6 Sukan shirya maƙarƙashiya, su ce, “Ai, mun gama shirin aikata laifi sarai.” Zuciyar mutum da tunaninsa, suna da wuyar ganewa! 7 Amma Allah zai harbe su da kibansa, Za a yi musu rauni nan da nan. 8 Zai hallaka su saboda maganganunsu, Duk wanda ya gan su zai kaɗa kansa. 9 Dukansu za su ji tsoro, Za su faɗi abin da Allah ya aikata, Su yi tunani a kan ayyukansa. 10 Dukan masu adalci za su yi murna, Saboda abin da Ubangiji ya aikata. Za su sami mafaka a gare shi, Dukan mutanen kirki za su yabe shi.

Zabura 65

Yabo da Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ya Allah, dole mutane su yabe ka a Sihiyona, Tilas su ba ka abin da suka alkawarta. 2 Saboda kakan amsa addu'o'i, Dukan mutane za su zo wurinka. 3 Zunubanmu sun kāshe mu, Amma za ka gafarta zunubanmu. 4 Masu farin ciki ne waɗanda ka zaɓe su Su zauna a tsattsarkan wurinka! Za mu ƙoshi da kyawawan abubuwa da suke wurin zamanka, Da albarkun tsattsarkan Haikalinka! 5 Ka amsa mana, ya Allah Mai Cetonmu, Ka kuma cece mu ta wurin aikata al'amuran banmamaki. Mutane daga ko'ina a duniya, Har da waɗanda suke can nesa a hayin tekuna, Sun dogara gare ka. 6 Ka kakkafa duwatsu ta wurin ikonka, Ka bayyana ƙarfin ikonka. 7 Kakan kwantar da rurin tekuna, Kakan kwantar da rurin igiyar ruwa, Kakan kwantar da tarzomar jama'a. 8 Dukan duniya ta tsorata, Saboda manyan ayyuka da ka aikata. Ayyukanka sukan kawo sowa ta farin ciki Daga wannan iyakar duniya zuwa wancan. 9 Kakan nuna kana kulawa da ƙasar, Ta wurin aiko mata da ruwa. Ka arzuta ta, ta zama dausayi. Rafuffukan da ka bayar ba su taɓa ƙafewa ba, Sun sa ƙasar ta ba da amfanin gonaki, Abubuwan da ka aikata ke nan. 10 Ka kwarara ruwa mai yawa a gonakin da aka nome, Ka jiƙe su da ruwa, Ka tausasa ƙasar da yayyafi, Ka sa ƙananan tsire-tsire su yi girma. 11 Saboda alherinka, ya Allah, an sami kaka mai albarka! Inda ka tafi duka akwai wadata! 12 Makiyaya suna cike da tumaki masu ƙiba, Tuddai kuma suna cike da farin ciki. 13 Sauruka suna cike da tumaki, Kwaruruka suna cike da alkama, Suna sowa suna raira waƙa ta farin ciki!

Zabura 66

Waƙar Yabo da Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ku yabi Allah da babbar murya ta farin ciki, Ya jama'a duka! 2 Ku raira waƙar darajar sunansa, Ku yabe shi da ɗaukaka! 3 Ku faɗa wa Allah cewa, “Al'amuran da kake aikatawa Suna da banmamaki ƙwarai! Ikonka yana da girma ƙwarai, Har maƙiyanka sukan durƙusa a gabanka don tsoro. 4 Duk wanda yake a duniya, yana yi maka sujada, Yana raira maka waƙar yabbai, Yana raira yabbai ga sunanka.” 5 Zo, ka ga abin da Allah ya yi, Ayyukansa masu ban al'ajabi Waɗanda ya aikata ga mutane. 6 Ya sa teku ta zama busasshiyar ƙasa, Kakanninmu suka haye kogi da ƙafa. A can muka yi farin ciki saboda abin da ya yi. 7 Har abada yana mulki ta wurin ƙarfinsa, Yana duban al'ummai, Don kada 'yan tawaye su tayar masa! 8 Ku yabi Allahnmu, ya ku dukan al'ummai, Bari a ji yabon da kuke yi masa. 9 Shi ne yake rayar da mu, Bai kuwa yarda mu fāɗi ba. 10 Ka jarraba mu, ya Allah, Kamar yadda ake tace azurfa da wuta, Hakanan ka jarraba mu. 11 Ka bar mu muka fāɗa a tarko, Ka ɗora mana kaya masu nauyi. 12 Ka bar maƙiyanmu suka tattaka mu, Mun ratsa ta cikin wuta da rigyawa, Amma yanzu ka kawo mu a lafiyayyen wuri. 13 Zan kawo hadayun ƙonawa a ɗakinka, Zan miƙa maka abin da na alkawarta. 14 Zan ba ka abin da na ce zan bayar, A lokacin da nake shan wahala. 15 Zan miƙa tumaki don a ƙona a kan bagade, Nan za a ji ƙanshi mai daɗi na ƙonannun awaki, Zan miƙa hadayu na bijimai da na awaki. 16 Ku zo ku ji, dukanku, ku da kuke girmama Allah, Ni kuwa zan faɗa muku abin da ya yi mini. 17 Na yi kira gare shi neman taimako, A shirye nake in yabe shi da waƙoƙi. 18 Da ban watsar da zunubaina ba, Da Ubangiji bai ji ni ba. 19 Amma hakika Allah ya ji ni, Ya saurari addu'ata. 20 Ina yabon Allah, Domin bai ƙi addu'ata ba, Bai kuwa hana mini madawwamiyar ƙaunarsa ba.

Zabura 67

Waƙar Miƙa Hadaya ta Godiya

1 Ka yi mana jinƙai, ya Allah, ka sa mana albarka, Ka dube mu da idon rahama, 2 Domin dukan duniya ta san nufinka, Dukan sauran al'umma kuma su san cetonka. 3 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka! 4 Da ma sauran al'umma su yi murna, su raira waƙa ta farin ciki, Domin kana yi wa jama'a shari'a ta adalci, Kana kuma bi da dukan sauran al'umma. 5 Da ma dukan mutane su yabe ka, ya Allah, Da ma dukan mutane su yabe ka! 6 Ƙasa ta ba da amfaninta, Allah, wanda yake Allahnmu ne, ya sa mana albarka. 7 Allah ya sa mana albarka, Da ma dukan jama'a ko'ina su girmama shi.

Zabura 68

Waƙar Nasara ta Al'ummar Ƙasar

1 Da ma Allah ya tashi ya warwatsa maƙiyansa! Da ma su waɗanda suke ƙinsa su gudu! 2 Kamar yadda iska take korar hayaƙi, Hakanan zai kore su, Kamar yadda kākin zuma yakan narke a gaban wuta, Hakanan mugaye za su hallaka a gaban Allah. 3 Amma adalai za su yi murna, Su kuma yi farin ciki a gaban Allah, Za su yi murna ƙwarai da gaske. 4 Ku raira waƙa ga Allah, Ku raira waƙar yabo ga sunansa, Ku yi hanya ga wanda yake ratsa gizagizai. Sunansa kuwa Ubangiji ne, ku yi murna a gabansa! 5 Allah, wanda yake zaune a tsattsarkan Haikalinsa, Yana lura da marayu, yana kuwa kiyaye gwauraye, Wato matan da mazansu suka mutu. 6 Yakan ba waɗanda suke da kewa gida, su zauna a ciki, Yakan fitar da 'yan sarƙa ya kai su 'yanci mai daɗi, Amma 'yan tawaye za su zauna a ƙasar da ba kowa a ciki. 7 Sa'ad da ka bi da jama'arka, ya Allah, Sa'ad da ka yi tafiya a hamada, 8 Duniya ta girgiza, sararin sama ya kwararo ruwa, Saboda bayyanar Allah, har Dutsen Sinai ya girgiza, Saboda bayyanar Allah na Isra'ila. 9 Ka sa aka yi ruwan sama mai yawa, ya Allah, Ka rayar da ƙasarka wadda ta zozaye. 10 Jama'arka suka gina gidajensu a can, Ta wurin alherinka ka yi wa matalauta tanadi. 11 Ubangiji ya ba da umarni, Sai mata masu yawa suka baza labari cewa, 12 “Sarakuna da rundunan sojojinsu suna gudu! Matan da suke a gida suka rarraba ganima.” 13 Suna kamar kurciyoyin da aka dalaye da azurfa, Waɗanda fikafikansu suna ƙyalli kamar kyakkyawar zinariya. (Me ya sa waɗansunku suke zaune cikin shingen tumaki?) 14 Sa'ad da Allah Mai Iko Dukka Ya warwatsar da sarakuna a dutsen Zalmon, Sai ya sa dusar ƙanƙara ta sauka a wurin. 15 Wane irin babban dutse ne wannan dutsen Bashan? Tulluwarka nawa, dutsen Bashan? 16 Me ya sa, daga manyan kawunanka Kake yi wa dutsen da Allah ya zaɓa Ya zauna a kai, duban raini? A nan Ubangiji zai zauna har abada! 17 Daga Sinai da dubban manyan karusansa, Ubangiji ya zo tsattsarkan Haikalinsa. 18 Ya hau kan tsaunuka Tare da ɗumbun waɗanda ya kamo daga yaƙi, Yana karɓar kyautai daga wurin mutane, Daga wurin 'yan tawaye kuma. Ubangiji Allah zai zauna a can. 19 Ku yabi Ubangiji, Wanda yake ɗaukar nawayarmu ta yau da kullum, Shi ne Allah wanda ya cece mu. 20 Allahnmu, Allah Mai Ceto ne, Shi ne Ubangiji, Ubangijinmu, Wanda yake cetonmu daga mutuwa. 21 Hakika Allah zai farfashe kawunan abokan gābansa, Da na waɗanda suka nace bin hanyoyinsu na zunubi. 22 Ubangiji ya ce, “Zan komo da su daga Bashan, Zan komo da su daga zurfin teku, 23 Don ku wanke sawayenku a cikin jinin maƙiyanku, Karnukanku kuwa za su lashe iyakar abin da suke so.” 24 Ya Allah, jama'a duka sun ga irin tafiyarka ta nasara, Irin tafiyar Allah, Sarkina, zuwa tsattsarkan wurinsa. 25 Mawaƙa suna kan gaba, mabusa suna biye, A tsakiya kuwa 'yan mata suna kaɗa bandiri. 26 “Ku jama'ar Allah, ku yabe shi cikin taronku, Ku yabi Ubangiji, dukanku, ku zuriyar Isra'ila!” 27 Ga Biliyaminu mafi ƙanƙanta Cikin kabilai, a kan gaba, Sa'an nan shugabannin Yahuza da ƙungiyarsu, Daganan sai shugabannin Zabaluna da na Naftali suna biye da su. 28 Ka nuna ikonka, ya Allah, Ikon nan da ka nuna saboda mu. 29 Daga Haikalinka a Urushalima, Sarakuna sukan kawo maka kyautai. 30 Ka tsauta wa Masar, naman jejin nan Mai zafin hali da yake cikin iwa, Ka tsauta wa sauran al'umma, taron bijiman nan da 'yan maruƙansu, Har dukansu su durƙusa, su miƙa maka azurfarsu. Ka warwatsar da jama'ar nan Masu son yin yaƙi! 31 Wakilai za su zo daga Masar, Habashawa za su miƙa hannuwansu sama, Su yi addu'a ga Allah. 32 Ku raira waƙa ga Allah, ku mulkokin duniya, Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji, 33 Shi wanda ya hau cikin sararin sama, Daɗaɗɗen sararin sama! Ku kasa kunne ga muryarsa mai ƙarfi! 34 Ku yi shelar ikon Allah, Ɗaukakarsa tana bisa kan Isra'ila, Ikonsa yana cikin sararin sama. 35 Allah al'ajabi ne a tsattsarkan wurinsa, Allah na Isra'ila! Yana ba da ƙarfi da iko ga jama'arsa. Ku yabi Allah!

Zabura 69

Kukan Neman Taimako

1 Ka cece ni, ya Allah! Ruwa ya sha kaina. 2 Ina nutsewa cikin laka mai zurfi, Ba kuwa ƙasa mai ƙarfi, Na tsunduma cikin ruwa mai zurfi, Raƙuman ruwa kuwa sun kusa kashe ni. 3 Na gaji da kira, ina neman taimako, Maƙogwarona yana yi mini ciwo, Idanuna duka sun gaji, Saboda ina zuba ido ga taimakonka. 4 Waɗanda suke ƙina ba dalili Sun fi gashin kaina yawa, Waɗanda suke baza ƙarya suke ƙina, Suna da ƙarfi, suna kuwa so su kashe ni. Suka tilasta ni in mayar da abubuwan da ba satarsu na yi ba. 5 Zunubaina ba a ɓoye suke a gare ka ba ya Allah, Ka san irin wawancin da na yi! 6 Kada ka bar ni in jawo kunya ga waɗanda suka dogara gare ka, Ya Ubangiji Allah Mai Iko Dukka! Kada ka bar ni in jawo abin kunya Ga waɗanda suke maka sujada, ya Allah na Isra'ila! 7 Sabili da kai ne aka ci mutuncina, Kunya ta rufe ni. 8 Kamar baƙo nake ga 'yan'uwana, Haka ma ga iyalina, kamar baƙo nake. 9 Ƙaunar da nake da ita ta yin ibada a Haikalinka Tana iza ni a ciki kamar wuta, Zargin da suke yi a kanka, ya fāɗa a kaina. 10 Na ƙasƙantar da kaina ta wurin yin azumi, Jama'a kuwa suka ci mutuncina. 11 Na sa tufafin makoki, Sai suka maishe ni abin dariya. 12 A tituna suna ta magana a kaina, Bugaggu da giya kuwa suna raira waƙa a kaina. 13 Amma ni, za yi addu'a gare ka, ya Ubangiji, Ka amsa mini, ya Allah, a lokacin da ka zaɓa, Sabili da muhimmiyar ƙaunarka, Saboda kana cika alkawarinka na yin ceto. 14 Ka cece ni daga nutsewa cikin wannan laka, Ka kiyaye ni daga maƙiyana, Daga kuma wannan ruwa mai zurfi. 15 Kada ka bar ambaliyar ruwa ta rufe ni. Kada ka bar ni in mutu cikin zurfafa, Ko in nutse a cikin kabari. 16 Sabili da madawwamiyar ƙaunarka, ka amsa mini, ya Ubangiji, Ka juyo wurina, saboda juyayinka mai girma! 17 Kada ka ɓoye kanka daga bawanka, Ina shan babbar wahala, ka yi hanzari ka amsa mini! 18 Ka zo ka fanshe ni, Ka kuɓutar da ni daga abokan gābana. 19 Ka san yadda ake cin mutuncina, Da yadda ake kunyata ni, ake ƙasƙantar da ni, Kana ganin dukan abokan gābana. 20 Zuciyata ta karai saboda cin mutuncin da ake ci mini, Ni kuwa ba ni da mataimaki, Na sa zuciya za a kula da ni, Amma babu. Na sa zuciya zan sami ta'aziyya, Amma ban samu ba. 21 Sa'ad da na ji yunwa, sai suka ba ni dafi, Sa'ad da na ji ƙishi, sai suka ba ni ruwan tsami. 22 Allah ya sa bukukuwansu su zama lalacewarsu, Shagulgulansu kuma su zama sanadin fāɗuwarsu! 23 Ka makantar da su, har da ba za su iya gani ba, Kullum ka sa bayansu ya ƙage! 24 Ka kwarara musu fushinka, Bari zafin fushinka ya ci musu! 25 Allah ya sa su gudu su bar sansaninsu, Kada wani ya ragu da rai cikin alfarwansu! 26 Sun tsananta wa waɗanda ka hukunta, Suna taɗin shan wuyar waɗanda ka aukar wa cutar. 27 Ka riɓaɓɓanya zunubansu, Kada ka bar su su sami rabon kome daga cikin cetonka. 28 Ka sa a goge sunansu daga cikin littafin rai, Kada a sa su a lissafin jama'arka. 29 Amma ni mai bukata ne, ina shan wahala, Ka tsame ni, ya Allah, ka cece ni! 30 Zan raira waƙar yabo ga Allah, Zan yi shelar girmansa ta wurin yi masa godiya, 31 Wannan zai daɗaɗa wa Ubangiji rai Fiye da hadayar bijimi, Fiye da a ba shi bijimi bana bakwai. 32 Sa'ad da masu bukata suka ga wannan za su yi murna, Waɗanda suke yi wa Allah sujada kuwa za a ƙarfafa su. 33 Ubangiji yana kasa kunne ga masu bukata, Bai manta da jama'arsa da suke a kurkuku ba. 34 Ku yabi Allah, ku al'arshi da duniya, ku yabi Allah, Tekuna da dukan talikan da suke cikinsu! 35 Gama zai ceci Sihiyona, Ya sāke gina garuruwan Yahuza, Jama'arsa za su zauna a wurin, su mallaki ƙasar. 36 Zuriyar bayinsa za su gāje ta, Masu ƙaunarsa za su zauna a wurin.

Zabura 70

Addu'ar Neman Kuɓuta

1 Ka cece ni, ya Allah! Ya Ubangiji, ka yi hanzari ka taimake ni! 2 Ka sa masu so su kashe ni, A ci nasara a kansu, su ruɗe! Ka sa waɗanda suke murna saboda wahalaina, su koma baya, su sha kunya! 3 Ka sa waɗanda suke mini ba'a Su razana sabili da fāɗuwarsu! 4 Ka sa dukan waɗanda suke zuwa gare ka Su yi murna, su yi farin ciki! Ka sa waɗanda suke ƙaunar cetonka Kullayaumi su ce, “Allah da girma yake!” 5 Ba ni da ƙarfi, ba mataimaki, Ya Allah, ka zo wurina da hanzari. Kai ne mataimakina da Mai Cetona, Kada ka yi jinkiri, ya Ubangiji!

Zabura 71

Addu'ar Tsoho

1 A gare ka, ya Ubangiji, lafiya lau nake, Faufau kada ka bari a yi nasara da ni! 2 Sabili da kai adali ne ka taimake ni, ka cece ni. Ka kasa kunne gare ni, ka cece ni! 3 Ka zama mini lafiyayyiyar mafaka, Da kagara mai ƙarfi, domin ka tsare ni, Kai ne mafakata da kāriyata. 4 Ya Allahna, ka cece ni daga mugaye, Daga ikon mugga, wato mugayen mutane. 5 Ya Ubangiji, a gare ka nake sa zuciya, Tun ina yaro, nake dogara gare ka. 6 A duk kwanakina a gare ka nake dogara, Kana kiyaye ni tun da aka haife ni, Kullayaumi zan yabe ka! 7 Raina abin damuwa ne ga mutane da yawa, Amma kai ne kāriyata mai ƙarfi. 8 Ina yabonka dukan yini, Ina shelar darajarka. 9 Yanzu da na tsufa, kada ka yashe ni, Yanzu da ƙarfina ya ƙare kuma, kada ka rabu da ni! 10 Maƙiyana, waɗanda suke so su kashe ni, Suna magana, suna ƙulle-ƙulle gāba da ni. 11 Suna cewa, “Ai, Allah ya rabu da shi, Gama ba wanda zai cece shi!” 12 Kada ka yi nisa da ni haka, ya Allah, Ka yi hanzari ka taimake ni, ya Allahna! 13 Ka sa a kori waɗanda suka tasar mini, A hallaka su! Ka sa a kunyata waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni, A wulakanta su sarai! 14 A koyaushe zan sa zuciya gare ka, Zan yi ta yabonka. 15 Zan ba da labarin adalcinka, Zan yi magana a kan cetonka duk yini, Ko da yake ya fi ƙarfin in san shi duka. 16 Zan tafi in yi yabon ikonka, ya Ubangiji Allah, Zan yi shelar adalcinka, Naka, kai kaɗai. 17 Kai ne ka koya mini, ya Allah, tun lokacin da nake yaro, Har wa yau kuwa ina ba da labarin ayyukanka masu banmamaki. 18 Yanzu da na tsufa, na kuma yi furfura, Kada ka rabu da ni, ya Allah! Ka kasance tare da ni sa'ad da nake shelar ikonka da ƙarfinka ga mutanen dukan zamanai masu zuwa. 19 Adalcinka, ya Allah, ya kai har sammai. Ka aikata manyan ayyuka, Ba waninka! 20 Ka aiko mini da wahala da azaba, Amma za ka mayar mini da ƙarfina, Za ka tashe ni daga kabari. 21 Za ka girmama ni har abada, Za ka sāke ta'azantar da ni. 22 Hakika zan yabe ka da garaya, Zan yabi amincinka, ya Allahna. Da garayata zan yi maka waƙoƙi, Ya Mai Tsarki na Isra'ila. 23 Zan ta da muryar farin ciki Sa'ad da nake raira maka waƙar yabbai, Zan raira waƙa da zuciya ɗaya, Gama dā ka fanshe ni. 24 Zan yi magana a kan adalcinka dukan yini, Saboda an yi nasara da waɗanda suke ƙoƙari su cuce ni, sun ruɗe.

Zabura 72

Mulkin Sarki Mai Adalci

1 Ka koya wa sarki ya yi shari'a Da adalcinka, ya Allah, Ka kuma ba shi shari'arka, 2 Don ya yi mulkin jama'arka bisa kan shari'a, Ya kuma bi da mulki da adalci. 3 Ka sa ƙasar ta mori wadatarta, Ka sa al'ummar ta san adalci. 4 Ka sa sarki ya yi wa talakawa shari'ar gaskiya, Ya taimaki waɗanda suke da bukata, Ya kuma hukunta azzalumai! 5 Ka sa su girmama ka Muddin rana tana haskakawa, Muddin wata yana ba da haske dukan lokaci. 6 Ka sa sarki ya zama kamar ruwan sama a gonaki, Ya zama kamar yayyafi a bisa ƙasa. 7 Ka sa adalci ya bunƙasa a zamaninsa, Wadata ta dawwama muddin wata na haskakawa. 8 Mulkinsa ya kai daga teku zuwa teku, Daga Kogin Yufiretis, har zuwa iyakar duniya. 9 Kabilan hamada za su durƙusa a gabansa, Abokan gābansa za su kwanta warwar a cikin ƙura. 10 Sarakunan Esbanya da na tsibirai, Za su ba shi kyautai, Sarakunan Arabiya da na Habasha Za su kawo masa kyautai. 11 Dukan sarakuna za su durƙusa a gabansa, Dukan sauran al'umma za su bauta masa! 12 Yakan ceci matalauta waɗanda suka yi kira gare shi, Da waɗanda suke da bukata, Da waɗanda ba a kula da su. 13 Yakan ji tausayin gajiyayyu da matalauta, Yakan ceci rayukan waɗanda suke da bukata. 14 Yakan cece su daga zalunci da kama-karya, Rayukansu suna da daraja a gare shi. 15 Ran sarki ya daɗe! Da ma a ba shi zinariya daga Arabiya, Da ma a yi masa addu'a dukan lokaci, Allah ya sa masa albarka kullum! 16 Da ma a sami hatsi mai yawa a ƙasar, Da ma amfanin gona ya cika tuddan, Ya yi yawa kamar itatuwan al'ul na Lebanon, Da ma birane su cika da mutane, Kamar ciyayin da suke girma a sauruka. 17 Da ma a yi ta tunawa da sunansa har abada, Da ma shahararsa ta ɗore muddin rana tana haskakawa. Da ma dukan sauran al'umma su yabi sarkin, Dukan jama'a su roƙi Allah ya sa musu albarka, Kamar yadda ya sa wa sarki albarka. 18 Ku yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila, Wanda shi kaɗai ne yake aikata al'amuran nan masu banmamaki! 19 Ku yabi sunansa mai daraja har abada, Allah ya sa ɗaukakarsa ta cika dukan duniya! Amin! Amin! 20 Ƙarshen addu'o'in Dawuda, ɗan Yesse ke nan.

Zabura 73

Ƙarshen Mugaye

1 Hakika, Allah yana yi wa Isra'ila alheri, Da waɗanda suke da tsarkin zuciya! 2 Amma ina gab da fāɗuwa, Ƙafafuna sun kusa zamewa, 3 Saboda na ji kishin masu girmankai, Sa'ad da na ga mugaye suna arziki. 4 Ba su jin zafin ciwo, Su ƙarfafa ne, lafiyayyu. 5 Ba su shan wahala yadda sauran mutane suke sha, Ba su da wahala kamar sauran mutane, 6 Don haka suka ɗaura girmankai kamar dutsen wuya, Suka sa hargitsi kuma kamar riga. 7 Zuciyarsu, cike take da mugunta, Tunaninsu kuma cike suke da mugayen ƙulle-ƙulle. 8 Sukan yi wa waɗansu ba'a, Suna faɗar mugayen abubuwa, Masu girmankai ne su, suna shawara A kan yadda za su zalunci waɗansu. 9 Sukan faɗi baƙar magana a kan Allah na Sama, Su ba da umarnai na girmankai ga mutane a duniya, 10 Har jama'ar Allah ma sukan koma wurinsu, Suna ɗokin gaskata dukan abin da suke faɗa musu. 11 Sukan ce, “Ai, Allah ba zai sani ba, Maɗaukaki ba zai bincika ba!” 12 Haka mugaye suke. Suna da dukiya da yawa, amma sai ƙaruwa suke ta yi. 13 Ashe, a banza nake kiyaye kaina da tsarki, Hannuwana kuma a tsabtace daga zunubi? 14 Ya Allah, ka sa ina shan wahala dukan yini, Kana horona kowace safiya! 15 Da na faɗi waɗannan abubuwa, Da na zama marar gaskiya ga jama'arka. 16 Don haka na yi iyakar ƙoƙari in fahimci wannan, Ko da yake ya cika wuya, 17 Sai sa'ad da na shiga Haikalinka, Sa'an nan na fahimci abin da zai sami mugaye. 18 Hakika ka sa su a wurare masu santsi, Ka sa su su fāɗi su hallaka sarai! 19 Cikin ƙyaftawar ido aka hallaka su, Suka yi mummunan ƙarshe! 20 Ya Ubangiji, kamar mafarki suke Wanda akan manta da shi da safe, Sa'ad da mutum ya farka yakan manta da kamanninsa. 21 Sa'ad da zuciyata ta ɓaci, Hankalina ya tashi, 22 Sai na zama wawa, ban fahimta ba, Na nuna halin dabba a gabanka. 23 Duk da haka ina tare da kai kullayaumin, Kana riƙe da hannuna. 24 Shawararka, tana bi da ni, Daga ƙarshe kuma za ka karɓe ni da daraja. 25 In banda kai, wa nake da shi a Sama? Tun da yake ina da kai, me kuwa nake bukata a duniya? 26 Kwanyata da jikina za su raunana, Amma Allah ne ƙarfina, Shi nake so har abada! 27 Hakika waɗanda za su rabu da kai za su mutu, Za ka hallakar da marasa aminci gare ka. 28 Amma a gare ni, ya fi mini kyau, in kasance kusa da Allah! Na sami mafaka a wurin Ubangiji Allah, Da zan yi shelar dukan abin da ya aikata.

Zabura 74

Addu'ar Neman Ceton Al'ummar Allah

1 Don me ka yashe mu haka, ya Allah? Za ka yi ta fushi da jama'arka har abada ne? 2 Ka tuna da jama'arka waɗanda ka zaɓa su zama naka tuntuni, Ka tuna da jama'arka waɗanda ka fansa, Don su zama kabilarka. Ka tuna da Dutsen Sihiyona, inda zatinka yake! 3 Ka zo, ka yi yawo a wannan kufai, Abokan gābanmu sun lalatar da kome na cikin Haikali! 4 Abokan gābanka suka yi sowa ta nasara A inda akan sadu da kai, Sun ƙwace Haikalin. 5 Suna kama da masu saran itace, Suna saran itatuwa da gaturansu. 6 Da gaturansu da gudumarsu, Sun ragargaje ƙyamaren da aka yi da katako. 7 Sun sa wa Haikalinka wuta, Sun ƙazantar da wurin da akan yi maka sujada, Sun farfashe shi duk. 8 Sun yi niyya su murƙushe mu sarai, Sun ƙone kowane tsattsarkan wuri na ƙasar. 9 Ba sauran tsarkakan alamu, Ba sauran annabawan da suka ragu, Ba kuwa wanda ya san ƙarewar wannan. 10 Ya Allah, har yaushe abokan gābanmu za su yi ta yi mana ba'a? Za su yi ta zargin sunanka har abada ne? 11 Me ya sa ka ƙi taimakonmu? Ka tasar musu ka hallaka su! 12 Amma ya Allah, kai ne Sarkinmu tun daga farko, Ka yi nasara da duniya. 13 Da ƙarfin ikonka ka raba teku, Ka farfashe kawunan dodannin ruwa, 14 Ka ragargaje kawunan kadduna, Ka kuwa ba mutanen hamada su ci. 15 Ka sa ruwan maɓuɓɓugai ya yi gudu, Ka sa manyan koguna sa ƙafe. 16 Ka halicci yini da dare, Ka sa rana da wata a wurarensu. 17 Ka yi wa duniya kan iyaka, Ka kuwa yi lokatan damuna da na rani. 18 Amma ka tuna fa, ya Ubangiji, abokan gābanka suna yi maka ba'a, Su wawaye ne waɗanda suke raina ka. 19 Kada ka ba da jama'arka marasa taimako A hannun mugayen maƙiyansu, Kada ka manta da jama'arka waɗanda ake tsananta musu! 20 Ka tuna da alkawarin da ka yi mana, Akwai tashin hankali a kowane lungu mai duhu na ƙasar! 21 Kada ka bari a kori waɗanda ake zalunta, Amma bari matalauta da masu mayata su yabe ka. 22 Ka tashi, ya Allah, ka kāre kanka! Ka tuna fa, marasa tsoronka suna ta yi maka ba'a dukan yini! 23 Kada ka manta da hargowar maƙiyanka, Kada ka manta da hayaniyar da magabtanka suke ta yi.

Zabura 75

Allah ya Ƙasƙantar da Mugaye, ya Ɗaukaka Adalai

1 Muna yabonka, ya Allah, muna yabonka! Muna shelar sunanka mai girma, Muna kuwa faɗa abubuwan banmamaki da ka aikata! 2 “Na ƙayyade lokacin yin shari'a,” in ji Ubangiji Allah, “Zan kuwa yi shari'ar gaskiya. 3 Ko da duniya da dukan waɗanda suke zaune cikinta za su ɓace, Zan ƙarfafa harsashin gininta. 4 Na faɗa wa masu girmankai kada su yi taƙama, Na kuma faɗa wa mugaye kada su yi fāriya, 5 Na dai faɗa musu su daina yanga, Su daina yin taƙama.” 6 Hukunci ba daga gabas, ko yamma, Ko daga kudu, ko arewa yake zuwa ba. 7 Allah yake yin shari'a, Yana ƙasƙantar da waɗansu, ya kuma ɗaukaka waɗansu. 8 Ubangiji yana riƙe da ƙoƙo, Cike da sabon ruwan inabi mai ƙarfi, Yana zuba shi, dukan mugaye kuwa suna ta sha, Suka shanye shi ƙaƙaf. 9 Amma har abada ba zan daina yin magana a kan Allah na Yakubu ba, Ko in daina raira yabbai gare shi. 10 Shi zai karya ikon mugaye, Amma za a ƙara wa masu adalci ƙarfi.

Zabura 76

Allah Mai Nasara Mai Hukunci

1 Allah sananne ne a Yahuza, Mashahuri ne kuma a Isra'ila. 2 Wurin zamansa yana Urushalima, A dutsen Sihiyona zatinsa yake. 3 A can yake kakkarya kiban abokan gāba, Da garkuwoyinsu, da takubansu, i, har da dukan makamansu. 4 Ina misalin darajarka, ya Allah! Ina misalin ɗaukakarka a sa'ad da ka komo daga kan duwatsu, Daga korar abokan gābanka! 5 An kwashe ganimar sojojinsu masu ƙarfin hali, Yanzu suna barci, barcin matattu, Ba waninsu da ya ragu, Da zai yi amfani da makamansa. 6 Sa'ad da ka fafare su, ya Allah na Yakubu, Dawakansu da mahayansu suka fāɗi matattu. 7 Amma mutane suna jin tsoronka! Wa zai iya tsayawa a gabanka Sa'ad da ka yi fushi? 8 Daga Sama ka sanar da shari'arka, Duniya ta tsorata, ta yi tsit, 9 Sa'ad da ka tashi domin ka yanke hukunci, Domin ka ceci waɗanda ake zalunta a duniya. 10 Hasalar mutane ba ta ƙara kome, sai dai ta ƙara maka yabo. Waɗanda suka tsira daga yaƙe-yaƙe za su kiyaye idodinka. 11 Ku ba Ubangiji Allahnku abin da kuka alkawarta masa, Dukanku sauran al'umma da kuke kusa, ku kawo masa kyautai. Allah yakan sa mutane su ji tsoronsa, 12 Yakan ƙasƙantar da shugabanni masu girmankai, Ya tsoratar da manyan sarakuna.

Zabura 77

Ta'aziyya a Lokacin Damuwa

1 Na ta da murya, na yi kuka ga Allah, Na ta da murya, na yi kuka, ya kuwa ji ni. 2 A lokacin wahala, nakan yi addu'a ga Ubangiji, Dukan dare nakan ɗaga hannuwana sama in yi addu'a, Amma ban sami ta'aziyya ba. 3 Lokacin da na tuna da Allah na yi ajiyar zuciya. Sa'ad da nake tunani, Nakan ji kamar in fid da zuciya. 4 Ba ya barina in yi barci, Na damu har na kāsa magana. 5 Na yi tunanin kwanakin da suka wuce, Nakan kuma tuna da shekarun da suka wuce da daɗewa. 6 Dare farai ina ta tunani mai zurfi, A cikin tunani nakan yi wa kaina tambaya. 7 A kullum ne Ubangiji zai yashe ni? Ba kuma zai ƙara yin murna da ni ba? 8 Ya daina ƙaunata ke nan? Alkawarinsa ba shi da wani amfani? 9 Allah ya manta da yin jinƙai ne? Fushinsa ya maye matsayin juyayinsa ne? 10 Sa'an nan sai na ce, “Abin da ya fi mini zafi duka, Shi ne ikon Maɗaukaki ya ragu.” 11 Zan tuna da manyan ayyukanka, ya Ubangiji, Zan tuna da al'amura masu banmamaki da ka aikata a dā. 12 Zan tuna da dukan abubuwan da ka yi, Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka. 13 Dukan abin da kake yi mai tsarki ne, ya Allah! Ba wani allah mai girma kamarka! 14 Kai ne Allah wanda kake aikata al'ajabai, Ka nuna ikonka cikin sauran al'umma. 15 Ta wurin ikonka ka fanshi jama'arka, Zuriyar Yakubu da ta Yusufu. 16 Ya Allah, sa'ad da ruwaye suka gan ka, sai su tsorata, Zurfafan teku kuma suka yi rawar jiki. 17 Gizagizai suka zubo da ruwa, Aka buga tsawa daga sama, Aka kuwa yi walƙiya ko'ina. 18 Bugawar tsawarka ta gama ko'ina, Hasken walƙiya ya haskaka dukan duniya, Duniya ta yi rawa, ta girgiza, ta kaɗu. 19 Ka yi tafiya a teku, Ka haye teku mai zurfi, Amma ba a ga shaida inda ka taka ba. 20 Ka bi da jama'arka yadda makiyayi yake yi, Musa da Haruna suke lura da su.

Zabura 78

Amincin Allah ga Jama'arsa

1 Ku kasa kunne ga koyarwata, ya ku jama'ata, Ku kula da abin da nake faɗa. 2 Zan yi magana da ku, In faɗa muku asirai na dā, 3 Abubuwan da muka ji muka kuwa sani, Waɗanda kakanninmu suka faɗa mana. 4 Ba za mu ɓoye waɗannan abubuwa daga 'ya'yanmu ba, Amma za mu faɗa wa tsara mai zuwa Labarin ikon Ubangiji, da manya manyan ayyukansa, Da abubuwan banmamaki waɗanda ya aikata. 5 Ya ba da dokoki ga jama'ar Isra'ila, Da umarnai ga zuriyar Yakubu. Ya ba kakanninmu ka'idodi, Don su koya wa 'ya'yansu dokokinsa, 6 Saboda tsara mai zuwa ta koye su, Su kuma su koya wa 'ya'yansu. 7 Ta haka su ma za su dogara ga Allah, Ba za su manta da abin da ya yi ba, Amma a kullum za su riƙa biyayya da umarnansa. 8 Kada su zama kamar kakanninsu, Jama'ar 'yan tawaye marasa biyayya. Ba su taɓa dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya ba, Ba su kuwa yi masa aminci ba. 9 Ifraimawa waɗanda suka yi yaƙi da bakkuna da kibau Suka gudu a ranar yaƙi. 10 Ba su kiyaye alkawarinsu da Allah ba, Sun ƙi biyayya da dokokinsa. 11 Sun manta da abin da ya aikata, Da mu'ujizan nan da ya nuna musu. 12 Kakanninsu na kallo sa'ad da Allah ya aikata wata mu'ujiza A filin Zowan a ƙasar Masar. 13 Ya raba teku, ya ratsa da su ta cikinta, Ya sa ruwa ya tsaya kamar bango. 14 Da rana sai ya bi da su da girgije, Da dare kuwa ya bi da su da hasken wuta. 15 Ya tsaga duwatsu, suke buɗe a hamada, Ya ba su ruwa daga cikin zurfafa. 16 Ya sa rafi ya fito daga cikin dutse, Ya sa ruwan ya yi gudu kamar a kogi. 17 Amma sun ci gaba da yi wa Allah zunubi, A hamada suka yi wa Maɗaukaki tawaye. 18 Da gangan suka jarraba Allah, Da suka ce ya ba su irin abincin da suke so. 19 Suka yi magana gāba da Allah, suka ce, “Ko Allah yana da iko ya ba mu abinci a hamada? 20 Gaskiya ce, ya bugi dutse, Ruwa kuwa ya fito a yalwace, Amma ko yana da iko ya ba da abinci da nama ga jama'arsa?” 21 Saboda haka Allah ya yi fushi sa'ad da ya ji su, Ya aukar wa jama'arsa da wuta, Fushinsa ya haɓaka a kansu, 22 Saboda ba su amince da shi ba, Ba su kuma gaskata yana da ikon cetonsu ba. 23 Amma ya yi magana da sararin sama, Ya umarci ƙofofinsa su buɗe, 24 Ya ba su tsaba daga sama, Da ya sauko musu da manna, su ci. 25 Ta haka suka ci abincin mala'iku. Allah ya ba su iyakar abin da za su iya ci. 26 Sa'an nan sai ya sa iskar gabas ta hura, Da ikonsa kuma ya sa iskar kudu ta tashi. 27 Ya aika da tsuntsaye bisansu kamar ƙura, Yawansu kamar yashi a gaɓa, 28 Sai suka fāɗo a zango, Kewaye da alfarwai ko'ina. 29 Sai mutane suka ci suka ƙoshi, Allah ya ba su iyakar abin da suke bukata. 30 Amma sa'ad da suke cikin ci, Tun ba su ƙoshi ba, 31 Sai Allah ya yi fushi da su. Ya karkashe ƙarfafan mutane, Da samarin Isra'ila na gaske! 32 Ko da yake ya aikata mu'ujizai da yawa, Duk da haka jama'a suka ci gaba da yin zunubi, Ba su kuwa gaskata shi ba. 33 Ta haka ya ƙare kwanakinsu kamar fitar numfashi, Bala'i ya aukar wa rayukansu farat ɗaya. 34 Amma sa'ad da ya kashe waɗansunsu, Sai sauran suka juyo gare shi suka tuba, Suka yi addu'a sosai a gare shi. 35 Sun tuna, ashe, Allah ne mai kiyaye su, Sun tuna Maɗaukaki shi ne Mai Fansarsu. 36 Amma maganganunsu duka ƙarya ne, Dukan abin da suka faɗa kuwa daɗin baki ne kawai. 37 Ba su yi masa biyayya ba, Ba su yi aminci game da alkawarin da suka yi da shi ba. 38 Amma Allah ya yi wa jama'arsa jinƙai, Ya gafarta zunubansu, Bai hallaka su ba. Sau da yawa yakan kanne fushinsa, Ya dakatar da hasalarsa. 39 Yakan tuna su mutane ne kawai, Kamar iskar da take hurawa ta wuce. 40 Sau da yawa suka tayar masa a hamada. Sau da yawa suka sa shi yin ɓacin rai! 41 Suka yi ta jarraba Allah a kai a kai, Suka kuwa sa Mai Tsarki na Isra'ila yin fushi. 42 Suka manta da ikonsa mai girma. Suka manta da lokacin da ya cece su daga abokan gābansu, 43 Lokacin da ya aikata manyan ayyuka da mu'ujizai A filin Zowan, ta ƙasar Masar. 44 Ya mai da koguna su zama jini, Masarawa kuwa suka kasa sha daga rafuffukansu. 45 Ya aiko da ƙudaje gare su, suka wahalshe su, Kwaɗi suka lalata filayensu. 46 Ya aiko da gamzari don su ci amfanin gonakinsu, Ya aiko da ɗango su lalata gonakinsu. 47 Ya kashe kurangar inabinsu da ƙanƙara, Ya kuma kashe itatuwan ɓaurensu da jaura. 48 Ya karkashe shanunsu da ƙanƙara, Ya kuma karkashe garkunan tumakinsu da na awakinsu da tsawa. 49 Ya buge su da fushinsa mai zafi, da hasalarsa, Ya sa su damuwa ƙwarai, Da ya aiko da mala'iku masu hallakarwa. 50 Bai kanne fushinsa ba, Bai bar su da rai ba, Amma ya karkashe su da annoba. 51 Ya karkashe 'yan fari maza Na dukan iyalan da suke Masar. 52 Sa'an nan ya bi da jama'arsa Kamar makiyayi, ya fito da su, Ya yi musu jagora cikin hamada. 53 Ya bi da su lafiya, ba su kuwa ji tsoro ba, Amma teku ta cinye abokan gābansu. 54 Ya kawo su tsattsarkar ƙasarsa, Ya kawo su a duwatsun da shi kansa ya ci da yaƙi. 55 Ya kori mazaunan wurin sa'ad da jama'arsa suka dirkako, Ya rarraba ƙasar ga kabilan Isra'ila, A nan ya ba su izini su zauna a wurin, a cikin alfarwansu. 56 Amma sai suka yi wa Allah Mai Iko Dukka tawaye, Suka jarraba shi. Ba su kiyaye dokokinsa ba, 57 Amma suka yi tawaye da rashin aminci Kamar kakanninsu, Kamar kiban da aka harba da tanƙwararren baka, Waɗanda ba su da tabbas. 58 Suka sa shi ya yi fushi saboda Masujadansu na arnanci. Suka sa ya ji kishi saboda gumakansu. 59 Allah ya yi fushi sa'ad da ya ga haka, Don haka ya rabu da jama'arsa ɗungum. 60 Ya bar alfarwarsa da take a Shilo, Wato wurin da yake zaune a dā, a tsakiyar mutane. 61 Ya yardar wa abokan gāba su ƙwace akwatin alkawari, Inda aka ga ikonsa da darajarsa, 62 Ya ji fushi da jama'arsa, Ya bar abokan gābansu su karkashe su. 63 Aka karkashe samari a cikin yaƙi, 'Yan mata kuma suka rasa ma'aura. 64 Aka karkashe firistoci da takuba, Matansu ba su yi makoki dominsu ba. 65 Daga bisani sai Ubangiji ya tashi Kamar wanda ya farka daga barci, Kamar jarumi wanda ya bugu da ruwan inabi. 66 Ya tura abokan gābansa baya, Da mummunar kora mai bankunya Da ba za su sāke tashi ba. 67 Ubangiji ya rabu da zuriyar Yusufu, Bai kuma zaɓi kabilar Ifraimu ba. 68 A maimakonsu sai ya zaɓi kabilar Yahuza, Ya zaɓi Dutsen Sihiyona, wanda yake ƙauna ƙwarai. 69 A can ya gina Haikalinsa, Kamar wurin zamansa a Sama. Ya kafa shi da ƙarfi kamar duniya, Tabbatacce a kowane lokaci. 70 Ya zaɓi bawansa Dawuda, Ya ɗauko shi daga wurin kiwon tumaki, 71 Ya ɗauko shi daga inda yake lura da 'yan raguna. Ya naɗa shi Sarkin Isra'ila, Ya naɗa shi makiyayin jama'ar Allah. 72 Dawuda kuwa ya lura da su da zuciya ɗaya, Da gwaninta kuma ya bi da su.

Zabura 79

Makoki Saboda an Lalatar da Urushalima

1 Ya Allah, arna sun fāɗa wa ƙasar jama'arka! Sun ƙazantar da Haikalinka tsattsarka, Sun bar Urushalima kufai. 2 Suka bar wa ta tsuntsaye gawawwakin jama'arka su ci, Suka bar wa namomin jeji gawawwakin bayinka. 3 Suka zubar da jinin jama'arka kamar ruwa. Jini ya yi ta gudu kamar ruwa Ko'ina a Urushalima, Ba ma wanda ya ragu don ya binne gawawwaki. 4 Sauran al'umma da suke kewaye da mu, Suka maishe mu abin ba'a, suka yi mana dariya, Suka yi mana ba'a. 5 Har yaushe za ka yi ta fushi da mu, ya Ubangiji? Har abada ne? Kullum ne fushinka zai yi ta ci kamar wuta? 6 Ka yi fushi da al'umman da ba su yi maka sujada, Ka yi fushi da jama'ar da suka ƙi ka! 7 Sun karkashe mutanenmu, Sun kuwa lalatar da ƙasarmu. 8 Kada ka hukunta mu saboda zunuban kakanninmu, Amma ka yi mana jinƙai yanzu, Gama mun fid da zuciya sarai. 9 Ka taimake mu, ya Allah Mai Cetonmu, Saboda girmanka. Ka cece mu, ka gafarta mana zunubanmu, Don mutane su yabe ka. 10 Don me al'ummai za su tambaye mu cewa, “Ina Allahnku?” Bari mu ga ka hukunta al'ummai Saboda sun zubar da jinin bayinka! 11 Ka kasa kunne ga nishin 'yan sarƙa, Ka kuɓutar da waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa, Ta wurin ikonka mai girma. 12 Ya Ubangiji, ka rama wa al'umman nan har sau bakwai, Saboda tsiwace-tsiwacen da suka yi maka. 13 Mu waɗanda muke jama'arka, tumakin garkenka, Za mu gode maka, mu yabe ka har abada.

Zabura 80

Addu'ar Komo da Al'umma

1 Ka kasa kunne gare mu, ya Makiyayin Isra'ila, Ka ji mu, kai da kake shugaban garkenka, Da kake zaune a kan kursiyinka, a bisa kerubobi. 2 Ka bayyana ƙaunarka ga kabilar Ifraimu, Da ta Biliyaminu, da ta Manassa! Ka nuna mana ikonka, Ka zo ka cece mu! 3 Ka komo da mu, ya Allah! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu! 4 Har yaushe ke nan ya Ubangiji Allah Mai Runduna, Za ka yi ta fushi da addu'o'in jama'arka? 5 Ka ciyar da mu da hawaye, Ka shayar da mu da babban ƙoƙo na hawaye. 6 Ka bar al'umman da suke maƙwabtaka da mu Su yi ta faɗa a kan ƙasarmu, Abokan gābanmu kuma suna yi mana ba'a. 7 Ka komo da mu, ya Allah Mai Runduna! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu! 8 Ka fito da kurangar inabi daga cikin Masar, Ka kori sauran al'umma, Ka dasa kurangar a ƙasarsu. 9 Ka gyara mata wuri don ta yi girma, Saiwoyinta suka shiga ƙasa sosai, Ta yaɗu, ta rufe dukan ƙasar. 10 Ta rufe tuddai da inuwarta, Ta rufe manya manyan itatuwan al'ul da rassanta. 11 Rassanta sun miƙe har Bahar Rum, Har zuwa Kogin Yufiretis. 12 Me ya sa ka rushe shingen da yake kewaye da ita? Ga shi yanzu, duk mai wucewa yana iya satar 'ya'yanta. 13 Aladen jeji kuma za su tattake ta, Namomin jeji duka za su cinye ta. 14 Ka juyo wurinmu, ya Allah Mai Runduna! Daga Sama, ka dube mu, Ka zo ka ceci kurangar inabinka! 15 Ka zo ka ceci kurangar inabin nan Wadda kai da kanka ka dasa, Wannan ƙaramar kuranga, Ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai! 16 Abokan gābanmu sun sa mata wuta, sun sare ta, Ka yi fushi da su, ka hallaka su! 17 Ka kiyaye jama'arka wadda ka zaɓa, Ka keɓe ta. Al'umman nan wadda ka sa ta yi girma, ta yi ƙarfi sosai! 18 Ba za mu ƙara rabuwa da kai ba, Ka rayar da mu, mu kuwa za mu yabe ka. 19 Ka komo da mu, ya Ubangiji Allah Mai Runduna! Ka nuna mana ƙaunarka, za mu kuwa cetu!

Zabura 81

Waƙar Idi

1 Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah Mai Cetonmu, Ku raira yabbai ga Allah na Yakubu! 2 A fara waƙa, ku buga bandiri, Ku yi waƙoƙi masu daɗi da molaye, da garayu. 3 Ku busa ƙaho domin idin, A amaryar wata, Da a tsakiyar farin wata. 4 Wannan doka ce a Isra'ila, Umarni ne kuma daga Allah na Yakubu. 5 Ya ba da wannan umarni ga jama'ar Isra'ila, A lokacin da ya fita gāba da ƙasar Masar. Na ji wata murya da ban saba ji ba tana cewa, 6 “Na ɗauke muku kayayyaki masu nauyi da kuke ɗauke da su a kā, Na sa kuka ajiye kwandunan aikinku. 7 Sa'ad da kuke shan wahala Kuka yi kira a gare ni, na kuwa cece ku. Daga maɓuyata cikin hadiri, na amsa muku, Na jarraba ku a maɓuɓɓugan Meriba. 8 “Ya kuma jama'ata Isra'ila ku kasa kunne, Ina kuwa so ku saurara gare ni. 9 Faufau kada ku bauta wa gumaka, Ko ku yi sujada ga wanina. 10 Ni ne Ubangiji Allahnku, Wanda ya fisshe ku daga ƙasar Masar. Ku buɗe bakinku, zan ciyar da ku. 11 “Amma jama'ata ba sa kasa kunne gare ni ba. Isra'ila ta ƙi yi mini biyayya. 12 Saboda haka na bar su su yi ta kangarewarsu, Su aikata duk irin abin da suka ga dama. 13 Ina kuwa so jama'ata su kasa kunne gare ni, Su kuwa yi mini biyayya! 14 Da sai in kori abokan gābansu nan da nan, In yi nasara da dukan maƙiyansu. 15 Maƙiyana, za su sunkuya a gabana saboda tsoro, Hukuncinsu na har abada ne. 16 Zan ciyar da ku da kyakkyawar alkama, In ƙosar da ku da zuma.”

Zabura 82

Tsautawa a kan Muguwar Shari'a

1 Allah yana matsayinsa a taron jama'arsa, Yakan zartar da nufinsa a taron alloli. 2 Tilas ku daina yin rashin gaskiya a shari'a, Ku daina goyon bayan mugaye! 3 Ku kāre hakkin talakawa da na marayu, Ku yi adalci ga matalauta, Da waɗanda ba su da mataimaki. 4 Ku kuɓutar da talakawa da matalauta, Ku cece su daga ikon mugaye! 5 “Waɗanne irin jahilai ne ku, wawaye! Kuna zaune cikin duhu, Ga shi, ba adalci a duniya sam! 6 Na faɗa muku, ku alloli ne, Cewa dukanku 'ya'ya ne na Maɗaukaki. 7 Amma za ku mutu kamar kowane mutum, Ku fāɗi kamar kowane basarauce.” 8 Ya Allah, ka zo, ka mallaki duniya, Dukan al'ummai naka ne.

Zabura 83

Addu'a don a Hallaka Abokan Gāban Isra'ila

1 Ya Allah, kada ka yi shiru, Kada ka tsaya cik, Ya Allah, kada kuma ka yi tsit! 2 Duba, abokan gābanka suna tawaye, Maƙiyanka sun tayar. 3 Suna ta ƙulle-ƙulle a asirce gaba da jama'arka, Suna shirya maƙarƙashiya gāba da waɗanda kake tsaronsu. 4 Suna cewa, “Ku zo, mu hallakar da al'ummarsu, Don a manta da Isra'ila har abada!” 5 Suka yarda a kan abin da suka shirya, Suka haɗa kai gāba da kai. 6 Su ne mutanen Edom, da Isma'ilawa, Da mutanen Mowab, da Hagarawa, 7 Da mutanen Gebal, da na Ammon, da na Amalek, Da na Filistiya, da na Taya. 8 Assuriya ma ta haɗa kai da su, Haɗa kai ke nan mai ƙarfi da zuriyar Lutu. 9 Ka yi musu yadda ka yi wa Madayanawa, Ka yi musu yadda ka yi wa Sisera Da Yabin a Kogin Kishon, 10 Waɗanda aka kora a Endor, Gawawwakinsu kuwa suka ruɓe a ƙasa. 11 Ka yi wa shugabannin yaƙinsu yadda ka yi wa Oreb da Ziyib, Ka kori dukan masu mulkinsu yadda ka kori Zeba da Zalmunna, 12 Waɗanda suka ce, “Za mu ƙwace ƙasar da take ta Allah, ta zama tamu.” 13 Ya Allahna, ka warwatsa su kamar ƙura, Ka warwatsa su kamar ciyayin da iska take hurawa. 14 Kamar yadda wuta take cin jeji, Kamar yadda harshen wuta yake ƙone tuddai, 15 Ka runtume su da hadirinka, Ka razanar da su da iskarka mai ƙarfi. 16 Ya Ubangiji, ka sa kunya ta rufe su, Don su so su bauta maka. 17 Ka sa a kore su, a razanar da su har abada, Ka sa su mutu, mutuwar ƙasƙanci! 18 Ka sa su sani kai kaɗai ne Ubangiji, Kai kaɗai ne mamallakin dukan duniya!

Zabura 84

Sa Zuciya ga Haikali

1 Ina ƙaunar Haikalinka ƙwarai, Ya Allah Mai Iko Dukka! 2 A can nake so in kasance! Ina marmarin farfajiyar Haikalin Ubangiji. Da farin ciki mai yawa zan raira waƙa ga Allah Mai Rai. 3 Har ba'u ma sukan yi sheƙa, Tsattsewa suna da sheƙunansu, A kusa da bagadanka suke kiwon 'ya'yansu. Ya Ubangiji Maɗaukaki, Sarkina, Allahna. 4 Masu murna ne waɗanda suke zaune a Haikalinka, Kullum suna raira yabonka! 5 Masu murna ne waɗanda suka sami ƙarfinsu daga gare ka, Su waɗanda suka ƙosa su kai ziyara a Dutsen Sihiyona. 6 Sa'ad da suke ratsa busasshen kwari, Sai ya zama maɓuɓɓugar ruwa, Ruwan sama na farko yakan rufe wurin da tafkuna. 7 Sukan yi ta ƙara jin ƙarfi a cikin tafiyarsu, Za su kuwa ga Allahn alloli a Sihiyona! 8 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji Allah Mai Runduna, Ka ji ni, ya Allah na Yakubu! 9 Duba, ya Allah, kai ne garkuwarmu, Ka dubi fuskar Sarkinmu, zaɓaɓɓenka. 10 Kwana guda da za a yi a Haikalinka, Ya fi kwana dubu da za a yi a wani wuri dabam. Na gwammace in tsaya a ƙofar Haikalin Allahna, Da in zauna a gidajen mugaye. 11 Ubangiji shi ne makiyayinmu, sarkinmu mai daraja, Yakan sa mana albarka, da alheri, da daraja, Ba ya hana kowane abu mai kyau ga waɗanda suke aikata abin da yake daidai. 12 Masu farin ciki ne waɗanda suka dogara gare ka, Ya Allah Mai Runduna!

Zabura 85

Addu'a don Lafiyar Al'ummar

1 Ya Ubangiji, ka yi wa ƙasarka alheri, Ka sāke arzuta Isra'ila kuma. 2 Ka gafarta wa jama'arka zunubansu, Ka kuwa gafarta musu dukan kuskurensu, 3 Ka daina yin fushi da su, Ka kuwa kawar da zafin fushinka. 4 Ka komo da mu, ya Allah Mai Cetonmu, Ka daina jin haushinmu! 5 Za ka yi fushi da mu har abada? Ba za ka taɓa hucewa ba? 6 Ka daɗa mana ƙarfi, ka yarda ka sabunta ƙarfinmu, Mu kuwa, jama'arka, za mu yabe ka. 7 Ka ƙaunace mu da madawwamiyar ƙaunarka, ya Ubangiji, Ka taimake mu da cetonka. 8 Ina kasa kunne ga abin da Ubangiji Allah yake cewa, Mu da muke mutanensa, ya alkawarta mana salama, Idan ba mu koma kan al'amuranmu na wauta ba. 9 Hakika a shirye yake ya ceci waɗanda suke girmama shi, Kasancewarsa a ƙasar, ceto ne ga ƙasar. 10 Ƙauna da aminci za su sadu wuri ɗaya, Adalci da salama za su gamu. 11 Amincin mutum zai yunƙura daga duniya, ya nufi sama. Adalcin Allah kuwa zai dubo daga Sama. 12 Ubangiji zai arzuta mu, Ƙasarmu kuwa za ta ba da amfanin gona mai yawa. 13 Adalci zai yi tafiya a gaban Ubangiji, Ya shirya masa tafarki.

Zabura 86

Addu'ar Neman Jinƙan Allah

1 Ka kasa kunne gare ni, ya Ubangiji, ka amsa mini, Gama ba ni da ƙarfi, ba ni kuwa da mataimaki. 2 Ka cece ni daga mutuwa, saboda ni mai aminci ne a gare ka, Ka cece ni saboda ni bawanka ne, ina kuwa dogara gare ka. 3 Kai ne Allahna, saboda haka ka yi mini jinƙai, ya Ubangiji, Ina yin addu'a a gare ka dukan yini. 4 Ka sa bawanka ya yi murna, ya Ubangiji, Saboda addu'o'ina sun hau zuwa gare ka. 5 Ya Ubangiji, kai managarci ne, mai yin gafara, Cike kake da madawwamiyar ƙauna ga dukan waɗanda suke yin addu'a gare ka. 6 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka ji kukana na neman taimako! 7 Nakan kira gare ka a lokacin wahala, Saboda kakan amsa addu'ata. 8 Ba wani allah kamarka, ya Ubangiji, Ba ko ɗaya, ba wanda zai iya aikata abin da kake aikatawa. 9 Dukan sauran al'umma da ka halitta Za su zo su rusuna har ƙasa a gabanka. Za su yabi girmanka, 10 Gama kai kaɗai ne maɗaukaki, ya Allah, Kai kaɗai ne ka aikata abubuwa na banmamaki. 11 Ya Ubangiji, ka koya mini abin da kake so in yi, Ni kuwa zan yi maka biyayya da aminci. Ka koya mini in bauta maka da zuciya ɗaya. 12 Zan yabe ka da zuciya ɗaya, ya Ubangiji Allahna, Zan riƙa shelar girmanka har abada. 13 Wane irin girma madawwamiyar ƙaunarka take da shi a gare ni! Gama ka cece ni daga zurfin kabari. 14 Masu girmankai sun tasar mini, ya Allah, Ƙungiyar mugaye tana ƙoƙari ta kashe ni, Mutanen da ba su kula da kai ba. 15 Ya Ubangiji, kai Allah ne mai jinƙai, mai ƙauna, Mai jinkirin fushi, kullum kai mai alheri ne, mai aminci. 16 Ka juyo gare ni, ka yi mini jinƙai, Ka ƙarfafa ni, ka cece ni, Gama ina bauta maka, kamar yadda mahaifiyata ta yi. 17 Ka nuna mini alherinka, ya Ubangiji, Sa'an nan su waɗanda suke ƙina za su sha kunya, Sa'ad da suka ga ka ta'azantar da ni, Ka kuma taimake ni.

Zabura 87

Fa'idar Zama a Urushalima

1 Allah ya gina birninsa a bisa tsarkakan tuddai, 2 Yana ƙaunar birnin Urushalima fiye da kowane wuri a Isra'ila. 3 Ya birnin Allah, ka kasa kunne, Ga abubuwan banmamaki da ya faɗa a kanka. 4 “Sa'ad da na lasafta sauran al'umma da suke yi mini biyayya, Zan sa Masar da Babila a cikinsu, Zan ce da Filistiya, da Taya, da Habasha, Su ma na Urushalima ne.” 5 A kan Sihiyona kuwa za a ce, “Dukan sauran al'umma nata ne.” Maɗaukaki kuwa zai ƙarfafa ta. 6 Ubangiji zai rubuta lissafin jama'o'i, Ya sa su duka cikin jimilla ta Urushalima. 7 Duk mazauna a wurin za su raira waƙa, su yi rawa, Su ce, “Dukan maɓuɓɓugaina suna cikinka.”

Zabura 88

Kukan Neman Taimako

1 Ya Ubangiji Allah, Mai Cetona, Duk yini ina ta kuka, Da dare kuma na zo gare ka. 2 Ka ji addu'ata, Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako! 3 Wahala mai yawa ta auko mini, Har ina gab da mutuwa. 4 Ina daidai da sauran mutanen da suke gab da mutuwa, Dukan ƙarfina ya ƙare. 5 An yashe ni a cikin matattu, Kamar waɗanda aka karkashe, Suna kuma kwance cikin kaburburansu, Waɗanda ka manta da su ɗungum, Waɗanda taimakonka ya yi musu nisa. 6 Ka jefar da ni cikin zurfin kabari, Da cikin rami mafi zurfi, mafi duhu. 7 Fushinka yana da nauyi a kaina, An turmushe ni a cikin tuƙuƙinka. 8 Ka sa abokaina su yashe ni, Ka sa sun ware ni. An kange ni, ba yadda zan kuɓuta. 9 Idanuna sun raunana saboda wahala. Ya Ubangiji, kowace rana ina kira gare ka, Ina ta da hannuwana zuwa gare ka da addu'a! 10 Kakan yi wa matattu mu'ujizai ne? Sukan tashi su yabe ka? 11 Akan yi maganar madawwamiyar ƙaunarka a kabari? Ko amincinka a inda ake hallaka? 12 Za a iya ganin mu'ujizanka a cikin duhu? Ko kuwa alherinka a lahira? 13 Ya Ubangiji, ina kira gare ka, neman taimako, Kowace safiya nakan yi addu'a gare ka. 14 Me ya sa ka yashe ni, ya Ubangiji? Me ya sa ka ɓoye kanka daga gare ni? 15 Tun ina ƙarami nake shan wahala, Har ma na kusa mutuwa, Na tafke saboda nauyin hukuncinka. 16 Hasalarka ta bi ta kaina, Tasar mini da kake ta yi, ta hallaka ni. 17 Dukan yini sun kewaye ni kamar rigyawa, Ta kowace fuska, sun rufe ni. 18 Ka sa har abokaina na kusa sun yashe ni, Duhu ne kaɗai abokin zamana.

Zabura 89

Alkawarin Allah da Dawuda

1 Ya Ubangiji zan raira waƙar Madawwamiyar ƙaunarka koyaushe, Zan yi shelar amincinka a dukan lokaci. 2 Na sani ƙaunarka za ta dawwama har abada, Amincinka kuma tabbatacce ne kamar sararin sama. 3 Ka ce, “Na yi alkawari da mutumin da na zaɓa, Na yi wa bawana Dawuda alkawari cewa, 4 ‘Daga zuriyarka kullum za a sami sarki, Zan kiyaye mulkinka har abada.’ ” 5 Talikan da suke Sama suna raira waƙa a kan Abubuwan banmamaki da kake yi, Suna raira waƙa kan amincinka, ya Ubangiji. 6 Ba wani kamarka a Sama, ya Ubangiji, Ba wani daga su cikin talikai da yake daidai da kai. 7 Ana girmama ka a cikin majalisar talikai, Duk waɗanda suke kewaye da kai suna jin tsoronka ƙwarai. 8 Ya Ubangiji Allah, Mai Runduna, Ba wani mai iko kamarka, Kai mai aminci ne a kowane abu. 9 Kai kake mulkin haukan teku, Kakan kwantar da haukan raƙuman ruwa. 10 Ka ragargaza dodon nan Rahab, ka kashe shi, Da ƙarfin ikonka ka cinye maƙiyanka. 11 Duniya taka ce, haka ma samaniya taka ce, Kai ne ka halicci duniya da dukan abin da yake cikinta. 12 Kai ne ka yi kudu da arewa, Dutsen Tabor da Dutsen Harmon Suna raira waƙa gare ka don farin ciki. 13 Kai kake da iko! Kai kake da ƙarfi! 14 A gaskiya da adalci aka kafa mulkinka, Akwai ƙauna da aminci a dukan abin da kake yi. 15 Masu farin ciki ne jama'ar da suke yi maka sujada, suna raira waƙoƙi, Waɗanda suke zaune a hasken alherinka. 16 Suna murna dukan yini saboda da kai, Suna kuwa yabonka saboda alherinka. 17 Kana sa mu ci babbar nasara, Da alherinka kakan sa mu yi rinjaye, 18 Sabili da ka zaɓar mana mai kāre mu, Kai, Mai Tsarki na Isra'ila, Kai ne ka ba mu sarkinmu. 19 Ka faɗa wa amintattun bayinka a wahayin da ka nuna musu tun da daɗewa, ka ce, “Na sa kambin sarauta a kan shahararren soja, Na ba da gadon sarauta ga wanda aka zaɓa daga cikin jama'a. 20 Na zaɓi bawana Dawuda, Na naɗa shi sarkinku. 21 Ƙarfina zai kasance tare da shi, Ikona kuma zai ƙarfafa shi. 22 Abokan gābansa ba za su taɓa cin nasara a kansa ba, Mugaye ba za su kore shi ba. 23 Zan ragargaza magabtansa, In karkashe duk waɗanda suke ƙinsa. 24 Zan ƙaunace shi kullum, in amince da shi, Zan sa ya yi nasara kullayaumin. 25 Zan faɗaɗa mulkinsa tun daga Bahar Rum, Har zuwa Kogin Yufiretis. 26 Zai ce mini, ‘Kai ubana ne da Allahna, Kai ne kake kiyaye ni, kai ne Mai Cetona.’ 27 Zan maishe shi ɗan farina, Mafi girma daga cikin dukan sarakuna. 28 Zan riƙa ƙaunarsa har abada, Alkawarin da na yi da shi kuma zai tabbata har abada. 29 A kullayaumin daga cikin zuriyarsa ne za a naɗa sarki, Mulkinsa zai dawwama kamar sararin sama. 30 “Amma idan zuriyarsa sun ƙi yin biyayya da shari'ata, Ba sa kuwa zauna cikin ka'idodina ba, 31 In sun ƙyale koyarwata, Ba su kiyaye umarnaina ba, 32 To, sai in hukunta su saboda zunubansu, Zan bulale su saboda laifofinsu. 33 Amma fa, ba zan daina ƙaunar Dawuda ba, Ba kuwa zan rasa cika alkawarin da na yi masa ba. 34 Ba zan keta alkawarin da na yi masa ba, Ba zan soke ko ɗaya daga cikin alkawaran da na yi masa ba. 35 “Da sunana mai tsarki na yi alkawari sau ɗaya tak, Ba zan yi wa Dawuda ƙarya ba! 36 Zuriyarsa za ta kasance kullum, Zan lura da mulkinsa muddin rana tana haskakawa. 37 Zai dawwama kamar wata, Kamar amintaccen mashaidin nan da yake a sararin sama.” 38 Amma kana fushi da zaɓaɓɓen sarkinka, Ka rabu da shi, ka yashe shi. 39 Ka soke alkawarinka wanda ka yi wa bawanka, Ka jefar da kambinsa a cikin ƙazanta. 40 Ka rurrushe garun birninsa, Ka mai da sansaninsa mai kagara kufai. 41 Dukan waɗanda suke wucewa za su sace masa kayansa, Maƙwabtansa duka suna yi masa ba'a. 42 Ka ba maƙiyansa nasara, Ka sa dukansu su yi murna. 43 Ka sa makamansa su zama marasa amfani, Ka bari a ci shi da yaƙi. 44 Ka ƙwace masa sandan sarautarsa, Ka buge gadon sarautarsa ƙasa. 45 Ka sa shi ya tsofe kafin lokacinsa, Ka rufe shi da kunya. 46 Har yaushe za ka ɓoye kanka, ya Ubangiji? Har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta? 47 Ka tuna kwanakin mutum kaɗan ne, ya Ubangiji, Ka tuna yadda ka halicci mutane duka masu mutuwa ne! 48 Wa zai rayu har abada, ba zai mutu ba? Ƙaƙa mutum zai hana kansa shiga kabari? 49 Ya Ubangiji, ina ƙaunarka ta dā? Ina alkawaran nan waɗanda ka yi wa Dawuda? 50 Kada ka manta da yadda aka ci mutuncina, ni da nake bawanka, Da yadda na daure da dukan cin mutuncin da arna suka yi mini. 51 Ya Ubangiji, kada ka manta da yadda maƙiyanka suka ci mutuncin zaɓaɓɓen sarki da ka naɗa! Suka yi ta cin mutuncinsa duk inda ya tafi. 52 Mu yabi Ubangiji har abada! Amin! Amin!

Zabura 90

Allah Madawwami, Mutum mai Shuɗewa

1 Ya Ubangiji, a koyaushe kai ne wurin zamanmu. 2 Kafin a kafa tuddai, Kafin kuma ka sa duniya ta kasance, Kai Allah ne, Madawwami. Ba ka da farko, ba ka da ƙarshe. 3 Kakan sa mutane su koma yadda suke, Su zama ƙura. 4 A gare ka shekara dubu kamar kwana ɗaya ne, Kamar jiya ce wadda ta shige, Gajeruwa ce kamar sa'a guda ta dare. 5 Kakan kwashe mutane kamar yadda ambaliyar ruwa take yi, Kamar mafarki suke, ba su daɗewa. Kamar tsire-tsire suke waɗanda suke tsirowa da safe, 6 Su yi girma har su yi huda, Sa'an nan su yi yaushi su bushe da yamma. 7 Mun hallaka ta wurin fushinka, Mun razana saboda hasalarka. 8 Ka jera zunubanmu a gabanka, Zunubanmu na ɓoye kuwa, Ka sa su a inda za ka gan su. 9 Fushinka ya gajerta tsawon ranmu, Ranmu ya ƙare kamar ajiyar zuciya. 10 Tsawon kwanakin ranmu duka a ƙalla shekara ce saba'in, In kuwa muna da ƙarfi, shekara tamanin ne. Duk da haka iyakar abin da waɗannan shekaru Suke kawo mana, damuwa ce da wahala, Nan da nan sukan wuce, Tamu da ƙare. 11 Wa ya san iyakar ikon fushinka? Wa ya san irin tsoron da hasalarka za ta kawo? 12 Ka koya mana mu sani ranmu na ɗan lokaci ne, Domin mu zama masu hikima. 13 Ya Ubangiji, sai yaushe za ka ji tausayinmu? Ka ji tausayin bayinka! 14 Ka cika mu da madawwamiyar ƙaunarka a kowace safiya, Don mu raira waƙoƙin murna dukan kwanakin ranmu. 15 Yanzu sai ka sa mu yi farin ciki mai yawa, Kamar yadda ka sa muka yi baƙin ciki A dukan shekarun nan da muka sha wahala. 16 Ka yarda mana, mu bayinka, mu ga ayyukanka masu girma, Ka yardar wa zuriyarmu su ga ikonka mai girma. 17 Ka yarda, albarkarka ta kasance tare da mu, ya Ubangiji Allahnmu. Ka sa mu yi nasara game da dukan abin da za mu yi! I, ka ba mu nasara a dukan abin da muke yi!

Zabura 91

Zama a Inuwar Mai Iko Dukka

1 Duk wanda ya je wurin Maɗaukaki Zai zauna lafiya, Duk wanda yake zaune a inuwar Mai Iko Dukka, 2 Ya iya ce wa Ubangiji, “Kai ne kāriyata, da mai kiyaye ni! Kai ne Allahna, a gare ka nake dogara!” 3 Hakika zai kiyaye ka Daga dukan hatsarorin da ka ɓoye, Daga kuma dukan mugayen cuce-cuce. 4 Zai rufe ka da fikafikansa, Za ka zauna lafiya a ƙarƙashinsu. Amincinsa zai tsare ka, ya kiyaye ka. 5 Ba za ka ji tsoron hatsarori da dare ba, Ko fāɗawar da za a yi maka da rana, 6 Ko annobar da take aukowa da dare, Ko mugayen da suke kisa da tsakar rana. 7 Mutum dubu za su fāɗi daura da kai, Dubu goma kuma za su fāɗi dama da kai, Amma kai, ba za a cuce ka ba. 8 Da idonka za ka duba, Ka ga yadda ake hukunta wa mugaye. 9 Domin ka ɗauka Ubangiji yake kiyaye ka, Maɗaukaki ne yake tsaronka, 10 To, ba bala'in da zai same ka, Ba za a yi wa gidanka aikin ƙarfi da yaji ba. 11 Allah zai sa mala'ikunsa su lura da kai, Za su kiyaye ka duk inda za ka tafi. 12 Za su ɗauke ka a hannuwansu, Don kada ka buga ƙafarka a dutse. 13 Za ka tattake zakoki da macizai, Za ka tattake zakoki masu zafin rai Da macizai masu dafi. 14 Allah ya ce, “Zan ceci waɗanda suke ƙaunata, Zan kiyaye waɗanda suka san ni. 15 Sa'ad da suka kira gare ni, zan amsa musu, Zan kasance tare da su sa'ad da suke shan wahala, Zan cece su in girmama su. 16 Zan ba su tsawon rai lada, Hakika kuwa zan cece su.”

Zabura 92

Waƙar Yabo

1 Abu mai kyau ne a yi wa Ubangiji godiya, A raira waƙa don girmansa, Allah mafi ɗaukaka, 2 A yi shelar madawwamiyar ƙaunarka kowace safiya, Amincinka kuma kowane maraice, 3 Da abubuwan kaɗe-kaɗe masu tsarkiya, Da amon garaya mai daɗi. 4 Ya Ubangiji, Ayyukanka masu iko suna sa ni murna, Saboda abin da ka aikata Ina raira waƙa domin farin ciki. 5 Ayyukanka da girma suke, ya Ubangiji! Tunaninka da zurfi suke! 6 Ga wani abin da wawa ba zai iya sani ba, Dakiki kuma ba zai iya ganewa ba, 7 Shi ne mai yiwuwa ne mugu ya yi girma kamar tsire-tsire, Masu aikata mugayen ayyuka kuma su arzuta, Duk da haka za a hallaka su ɗungum. 8 Gama kai, ya Ubangiji, Maɗaukaki ne har abada. 9 Mun sani maƙiyanka za su mutu, Dukan mugaye kuwa za a yi nasara da su. 10 Ka sa ni na yi ƙarfi kamar bijimi mai faɗa, Ka sa mini albarka da farin ciki. 11 Na ga fāɗuwar maƙiyana, Na ji kukan mugaye. 12 Adalai za su yi yabanya Kamar itatuwan giginya, Za su yi girma kamar itatuwan al'ul na Lebanon. 13 Za su zama kamar itatuwan da aka daddasa a Haikalin Ubangiji, Suna ta yabanya a Haikalin Allahnmu. 14 Waɗanda suke yin 'ya'ya da tsufansu, A kullum kuwa kore shar suke, Suna da ƙarfinsu kuma. 15 Wannan ya nuna Ubangiji adali ne, Shi wanda yake kāre ni, Ba kuskure a gare shi.

Zabura 93

Allah Sarki Ne

1 Ubangiji sarki ne! Yana saye da ɗaukaka, suturarsa ƙarfi ne. Hakika duniya ta kahu sosai a inda take, Ba kuwa za ta jijjigu ba. 2 Kursiyinka, ya Ubangiji, ya kahu tun daga farko, Kana nan tun fil azal. 3 Ya Ubangiji, zurfafan teku suna ta da muryarsu, Suna ta da muryarsu da ruri. 4 Ubangiji yana mulki cikin Sama, Mulkinsa mafifici ne, Fiye da rurin teku, Fiye da ikon raƙuman ruwan teku. 5 Dokokinka dawwamammu ne, ya Ubangiji, Haikalinka kuwa tsattsarka ne ƙwarai, Har abada abadin.

Zabura 94

Addu'ar Neman Sakayya

1 Ya Ubangiji, kai Allah ne wanda yake yin hukunci, Ka bayyana fushinka! 2 Kai ne mai yi wa dukan mutane shari'a, Ka tashi, ka sāka wa masu girmankai Abin da ya dace da su! 3 Har yaushe mugaye za su yi ta murna? Har yaushe ne, ya Ubangiji? 4 Har yaushe za su yi shakiyanci, Su yi ta ɗaga kai? Har yaushe, ya Ubangiji? 5 Suna ragargaza jama'arka, ya Ubangiji, Suna zaluntar waɗanda suke naka. 6 Suna karkashe gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, Da kuma baƙin da suke zaune a ƙasarmu. 7 Suna cewa, “Ai, Ubangiji ba ya ganinmu, Allah na Isra'ila ba ya lura da abin da yake faruwa!” 8 Ya jama'ata, ƙaƙa kuka zama dakikai, wawaye haka? Sai yaushe za ku koya? 9 Allah ya yi mana kunnuwa, shi ba zai ji ba? Allah ya yi mana idanu, shi ba zai gani ba? 10 Shi ne yake shugabancin sauran al'umma, ba zai hukunta su ba? Shi ne yake koya wa dukan mutane, shi ba shi da sani ne? 11 Ubangiji ya san tunaninsu, Ya san kuma hujjojinsu na rashin hankali. 12 Ya Ubangiji, mai farin ciki ne mutumin da kake koya wa, Mutumin da kake koya masa shari'arka. 13 Don ka ba shi hutawa a kwanakin wahala, Kafin a haƙa wa mugaye kabari. 14 Ubangiji ba zai rabu da jama'arsa ba, Ba zai rabu da waɗanda suke nasa ba. 15 Adalci kuma zai sāke dawowa cikin majalisun alƙalai, Dukan adalai kuwa za su yi na'am da shi. 16 Wa zai tsaya mini gāba da mugaye? Wa zai goyi bayana gāba da masu aikata mugunta? 17 Da ba domin Ubangiji ya taimake ni ba, Ai, da tuni na kai ƙasar da ba a motsi. 18 Na ce, “Ina kan fāɗuwa,” Amma, ya Ubangiji, madawwamiyar ƙaunarka ta riƙe ni. 19 Sa'ad da nake alhini, ina cikin damuwa, Ka ta'azantar da ni, ka sa in yi murna. 20 Ba ruwanka da alƙalai azzalumai, marasa gaskiya, Waɗanda suka mai da rashin gaskiya ita ce gaskiyarsu, 21 Sukan shirya wa mutanen kirki maƙarƙashiya, Sukan yanke wa marar laifi hukuncin kisa. 22 Amma Ubangiji yakan kāre ni, Allahna yakan kiyaye ni. 23 Shi zai hukunta su saboda muguntarsu, Ya hallaka su saboda zunubansu. Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

Zabura 95

Waƙar Yabo da Sujada

1 Ku zo mu yabi Ubangiji! Mu raira waƙa domin farin ciki ga mai kiyaye mu, Da Mai Cetonmu! 2 Mu zo gabansa da godiya, Mu raira waƙoƙin farin ciki na yabo! 3 Gama Ubangiji Allah ne mai iko, Shi yake mulki bisa sauran alloli duka. 4 Yana mulki bisa dukan duniya, Daga zurfafan kogwannin duwatsu zuwa tuddai mafiya tsayi. 5 Yana mulki bisa tekun da ya yi, Da kuma bisa ƙasar da ya siffata. 6 Ku zo, mu durƙusa, mu yi masa sujada, Mu durƙusa a gaban Ubangiji, Mahaliccinmu! 7 Shi ne Allahnmu, Mu ne jama'ar da yake lura da ita, Mu ne kuma garken da yake ciyarwa. Yau ku ji abin da yake faɗa. 8 “Kada ku taurare zuciyarku yadda kakanninku suka yi a Meriba, Kamar yadda suka yi a jeji a Masaha, a wancan rana. 9 A can suka gwada ni suka jarraba ni, Ko da yake da idanunsu suka ga abin da na yi dominsu. 10 A shekara arba'in ɗin nan, Jama'ar nan ta zama abar ƙyama gare ni, ‘Su marasa biyayya ne,’ in ji ni, ‘Gama sun ƙi bin umarnaina!’ 11 Sai na ji haushi, na yi musu alkawari mai nauyi. Na ce, ‘Faufau ba za ku shiga ƙasar da zan ba ku hutawa a ciki ba.’ ”

Zabura 96

Allah Maɗaukakin Sarki Ne

1 Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji! Ku raira waƙa ga Ubangiji, ya duniya duka! 2 Ku raira waƙa ga Ubangiji, ku yabe shi! Kowace rana ku ba da labari mai daɗi cewa, “Ya cece mu!” 3 Ku yi shelar ɗaukakar Ubangiji ga sauran al'umma, Ku yi shelar ayyukansa masu girma ga dukan kabilai. 4 Ubangiji da girma yake, tilas a ɗaukaka shi, Tilas a fi jin tsoronsa fiye da dukan alloli. 5 Allolin dukan al'ummai, gumaka ne kawai, Amma Ubangiji ne ya yi sammai. 6 Daraja da ɗaukaka suna kewaye da shi, Girma da jamali suna cikin Haikalinsa. 7 Dukan jama'ar da ke bisa duniya su yabi Ubangiji! Ku yabi ɗaukakarsa da ikonsa! 8 Ku yabi sunan Ubangiji mai ɗaukaka, Ku kawo sadaka, ku shiga Haikalinsa. 9 Ku durƙusa a gaban Mai Tsarki, sa'ad da ya bayyana, Ku yi rawar jiki a gabansa, ku duniya duka! 10 A faɗa wa dukan sauran al'umma, “Ubangiji Sarki ne! Duniya ta kahu da ƙarfi a wurin zamanta, Ba za a iya kaushe ta ba, Shi zai shara'anta dukan jama'a da adalci.” 11 Duniya da sararin sama, ku yi murna! Ki yi ruri, ya ke teku da dukan masu rai da suke cikinki. 12 Ku yi murna ya ku filaye da dukan abubuwan da suke cikinku! Sa'an nan itatuwan da suke cikin kurama Za su ta da murya saboda farin ciki 13 A gaban Ubangiji, gama ya zo ne ya mallaki duniya. Zai mallaki dukan jama'ar duniya Da adalci da gaskiya.

Zabura 97

Allah ne Mai Mulkin Dukka

1 Ubangiji Sarki ne! Ki yi murna ke duniya! Ku yi murna, dukanku tsibiran da kuke cikin tekuna! 2 Gajimare da duhu sun kewaye shi. A kan adalci da gaskiya ya kafa mulkinsa. 3 Wuta tana tafe a gabansa, tana cinye maƙiyansa Waɗanda suke kewaye da shi. 4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya, Duniya kuwa ta gani ta yi ta rawar jiki. 5 Tuddai sun narke a gaban Ubangiji kamar kākin zuma, A gaban Ubangijin dukan duniya. 6 Sammai suna shelar adalcinsa, Dukan kabilai kuwa, sun ga ɗaukakarsa. 7 Dukan waɗanda suke yi wa siffofi sujada za su sha kunya, Haka kuma waɗanda suke fāriya da gumakansu. Dukan alloli za su rusuna a gabansa. 8 Jama'ar Sihiyona suna murna, Garuruwan Yahuza kuma suna farin ciki, Sabili da irin shari'unka, ya Ubangiji! 9 Ya Ubangiji Mai Iko Dukka, kai kake mulkin dukan duniya, Ka fi sauran alloli duka girma. 10 Ubangiji yana ƙaunar masu ƙin mugunta. Yakan kiyaye rayukan jama'arsa, Yakan cece su daga ikon mugaye. 11 Haske yakan haskaka adalai, Haka kuma murna ta cika ga masu nagarta. 12 Dukanku adalai ku yi murna, Saboda abin da Ubangiji ya yi! Ku tuna da abin da Mai Tsarki ya yi, Ku yi masa godiya!

Zabura 98

Yabo Saboda Adalcin Allah

1 Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji, Gama ya aikata ayyuka masu banmamaki! Ta wurin ikonsa, da ƙarfinsa mai tsarki ya yi nasara. 2 Ubangiji ya bayyana cin nasararsa, Ya sanar da ikonsa na ceto ga sauran al'umma. 3 Ya cika alkawarinsa wanda ya yi wa jama'ar Isra'ila, Da tabbatacciyar ƙauna da aminci. Dukan mutane ko'ina sun ga nasarar Allahnmu! 4 Ku raira waƙa ta farin ciki ga Ubangiji. Dukanku waɗanda kuke a duniya, Ku yabe shi da waƙoƙi, kuna ta da murya da ƙarfi, Saboda farin ciki! 5 Ku raira yabbai ga Ubangiji da garayu, Ku kaɗa garayu! 6 Ku busa kakaki da ƙahoni, Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, Sarki! 7 Ki yi ruri, ya ke teku, Ke da dukan masu rai waɗanda suke cikinki, Ki raira waƙa, ke duniya, Da dukan waɗanda suke zaune cikinki! 8 Ku yi tāfi, ya ku tekuna, Ku raira waƙa tare, ya ku tuddai, don farin ciki. 9 A gaban Ubangiji, gama ya zo ne ya yi mulki bisa duniya! Zai yi mulki bisa dukan jama'ar duniya da adalci da gaskiya.

Zabura 99

Amincin Allah ga Isra'ila

1 Ubangiji Sarki ne, Mutane suna rawar jiki, Yana zaune a bisa kursiyinsa a bisa kerubobi, Duniya ta girgiza. 2 Ubangiji mai iko ne a Sihiyona, Shi ne yake mulki a bisa dukan sauran al'umma. 3 Kowa da kowa zai yabi sunansa mai girma, Maɗaukaki, Mai Tsarki ne shi! 4 Maɗaukaki kana ƙaunar abin da yake daidai, Ka kawo adalci cikin Isra'ila, Ka kawo adalci da gaskiya. 5 Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a gaban kursiyinsa! Mai Tsarki ne shi! 6 Musa da Haruna firistocinsa ne, Sama'ila kuma mai yi masa sujada ne. Suka yi kira ga Ubangiji, ya kuwa amsa musu. 7 Ya yi magana da su daga girgije, Suka yi biyayya da dokoki da umarnai da ya ba su. 8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa wa jama'arka, Ka nuna musu, kai Allah ne mai yin gafara, Amma kakan hukunta su saboda zunubansu. 9 Ku yabi Ubangiji Allahnmu, Ku yi sujada a bisa dutsensa mai tsarki! Ubangiji Allahnmu Mai Tsarki ne!

Zabura 100

Waƙar Yabo

1 Bari dukan duniya ta raira waƙar farin ciki ga Ubangiji! 2 Ku yi wa Ubangiji sujada da murna, Ku zo gabansa, kuna raira waƙoƙin farin ciki! 3 Kada fa a manta da cewa, Ubangiji shi ne Allah! Shi ne ya yi mu, mu kuwa nasa ne, Mu jama'arsa ne, mu garkensa ne. 4 Ku shiga Haikalinsa da godiya, Ku shiga wurinsa mai tsarki, ku yabe shi! Ku gode masa, ku yabe shi! 5 Ubangiji nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce, Amincinsa kuwa har abada abadin ne.

Zabura 101

Alkawarin Sarki don Zaman Adalci

1 Waƙata ta aminci ce da gaskiya. Ina raira maka ita, ya Ubangiji. 2 Abin da nake yi ba zai zama laifi ba, Yaushe za ka zo wurina? Da zuciya mai tsabta zan zauna a gidana. 3 Ba zan jure da mugunta ba ko kaɗan. Na ƙi jinin ayyukan waɗanda suka bijire wa Allah, Ba ruwana da su. 4 Ba zan yi rashin aminci ba, Ba kuwa zan yi tunanin mugunta ba. 5 Zan hallakar da mai raɗar abokinsa, Ba zan jure da mutum mai girmankai, Ko mai alfarma ba. 6 Zan yarda da waɗanda suke amincewa da Allah, Zan yardar musu si yi zamansu a fādata, Zan yarda wa waɗanda suke da tabbataccen aminci Su yi mini hidima. 7 Maƙaryaci ba zai zauna a fādata ba, Ba zan yarda munafuki ya yi zamansa a wurina ba. 8 A kowace rana zan yi ta karkashe dukan mugayen da suke cikin ƙasarmu, Zan kori dukan mugaye daga birnin Ubangiji.

Zabura 102

Addu'ar Wanda yake Shan Wahala

1 Ka ji addu'ata, ya Ubangiji, Ka ji kukana na neman taimako! 2 Kada ka ɓoye mini sa'ad da nake shan wahala! Ka ji ni, ka amsa mini da sauri sa'ad da na yi kira! 3 Raina ya ɓace kamar hayaƙi, Jikina yana ƙuna kamar wuta. 4 An tattake ni kamar busasshiyar ciyarwa, Ba ni da marmarin cin abinci. 5 Ina nishi da ƙarfi, Ba abin da ya ragu gare ni, In banda ƙashi da fata. 6 Ni kamar tsuntsu nake cikin hamada, Kamar mujiya a kufai. 7 Kwana nake ba barci, Na zama kamar tsuntsun da yake fama da kewa A bisa kan daƙi. 8 Maƙiyana suna cin mutuncina dukan yini. Waɗanda suke mini ba'a, Suna la'antarwa da sunana. 9 Toka ce abincina, Hawayena kuwa sun gauraya da abin da nike sha, 10 Sabili da fushinka da hasalarka. Ka ɗauke ni, ka jefar da ni. 11 Raina kamar inuwar maraice yake, Kamar busasshiyar ciyawa nake. 12 Amma kai, ya Ubangiji, sarki ne kai har abada, Dukan zamanai masu zuwa za su tuna da kai. 13 Za ka tashi ka ji tausayin Sihiyona, Lokaci ya yi da za ka yi mata jinƙai, Wannan shi ne lokacin! 14 Bayinka suna ƙaunarta, Ko da yake an hallakar da ita, Suna jin tausayinta, Ko da yake ta zama kufai. 15 Sauran al'umma za su ji tsoron Ubangiji, Dukan sarakunan duniya za su ji tsoron ikonsa. 16 Sa'ad da Ubangiji ya sāke gina Sihiyona Zai bayyana girmansa. 17 Zai saurari jama'arsa wadda ya rabu da ita, Zai kuwa ji addu'arta. 18 Ku rubuta abin da Ubangiji ya aikata don zamani mai zuwa, Don waɗanda ba a haife su ba tukuna, Su ma su yabe shi. 19 Ubangiji ya duba ƙasa Daga Sama, tsattsarkan wurinsa, Daga Sama ya dubi duniya, 20 Don ya ji nishin ɗaurarru, Don ya saki waɗanda aka yanke musu hukuncin kisa. 21 Saboda wannan mutane za su yi shelar sunan Ubangiji a Sihiyona, Za su yi masa godiya a Urushalima, 22 Sa'ad da sauran al'umma da mulkoki suka taru Don su yi wa Ubangiji sujada. 23 Tun ina ƙaramin yaro Ubangiji ya sa na rasa ƙarfi, Ya gajerta kwanakina. 24 Ya Allahna, kada ka ɗauke ni a yanzu, Tun da yake ban tsufa ba tukuna! Ya Ubangiji har abada kake. 25 Ka halicci duniya tun tuntuni, Da ikonka ne ka yi sammai. 26 Su za su ɓace duka, amma kai za ka dawwama, Za su ƙare kamar yadda tufafi suke ƙarewa, Za ka sāke su kamar tufafi, za su kuwa ɓace. 27 Amma kai, kana yadda kake kullayaumin, Har abada kake. 28 'Ya'yanmu za su yi zaman lafiya, Zuriyarsu kuma za su zauna cikin kiyayewarka kullayaumin.

Zabura 103

Yabon Ƙaunar Allah

1 Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ka yabi sunansa mai tsarki! 2 Ka yabi Ubangiji, ya raina, Kada ka manta da yawan alherinsa. 3 Ya gafarta dukan zunubaina, Ya kuma warkar da dukan cuce-cucena. 4 Ya cece ni daga kabari, Ya sa mini albarka da ƙauna da jinƙai. 5 Ya cika raina da kyawawan abubuwa, Don in zauna gagau, Ƙaƙƙarfa kamar gaggafa. 6 Ubangiji yakan yi wa waɗanda ake zalunta shari'a ta gaskiya. Yakan ba su hakkinsu. 7 Ya faɗa wa Musa shirye-shiryensa. Ya yardar wa jama'ar Isra'ila su ga manyan ayyukansa. 8 Ubangiji mai jinƙai ne, mai ƙauna ne kuma, Mai jinƙirin fushi ne, cike yake da madawwamiyar ƙauna. 9 Ba zai yi ta tsautawa kullum ba, Ba zai yi ta jin haushi har abada ba. 10 Yakan yi mana rangwame sa'ad da yake hukunta mu, Ko sa'ad da yake sāka mana saboda zunubanmu da laifofinmu. 11 Kamar yadda nisan sararin sama yake bisa kan duniya, Haka kuma girman ƙaunarsa yake ga waɗanda suke tsoronsa. 12 Kamar yadda gabas take nesa da yamma, Hakanan ne ya nisantar da zunubanmu daga gare mu. 13 Kamar yadda uba yake yi wa 'ya'yansa alheri, Hakanan kuwa Ubangiji yake yi wa masu tsoronsa alheri. 14 Ubangiji ya san abin da aka yi mu da shi, Yakan tuna, da ƙura aka yi mu. 15 Mutum fa, ransa kamar ciyawa ne, Yakan yi girma, ya yi yabanya kamar furen jeji. 16 Sa'an nan iska ta bi ta kansa, yakan ɓace, Ba mai ƙara ganinsa. 17 Amma ƙaunar Ubangiji ga waɗanda suke girmama shi har abada ce. Alherinsa kuwa tabbatacce ne har dukan zamanai, 18 Ga waɗanda suke riƙe da alkawarinsa da gaskiya, Waɗanda suke biyayya da umarnansa da aminci. 19 Ubangiji ya kafa kursiyinsa a Sama, Shi yake sarautar duka. 20 Ku yabi Ubangiji, ku ƙarfafa, ku manyan mala'iku, Ku da kuke biyayya da umarnansa, Kuna kasa kunne ga maganarsa! 21 Ku yabi Ubangiji, ku dukan ikokin da kuke a Sama, Ku yabi Ubangiji, ku bayinsa masu aikata abin da yake so! 22 Ku yabi Ubangiji, dukanku da kuke halittattunsa, A duk inda yake mulki! Ka yabi Ubangiji, ya raina!

Zabura 104

Ubangiji yana Kula da Halittarsa

1 Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ya Ubangiji Allahna, mai girma ne kai! Kana saye da ɗaukaka da daraja, 2 Ka yi lulluɓi da haske. Ka shimfiɗa sammai kamar alfarwa. 3 Ka gina wurin zamanka a bisa kan ruwan da yake sama. Gajimare ne karusanka, A bisa kan fikafikan iska kake tafiya. 4 Iska ce jakadanka, Walƙiya kuwa ita ce baiwarka. 5 Ka sa duniya ta kahu sosai a bisa harsashin gininta, Ba kuwa za a iya kawar da ita ba har abada. 6 Ka sa teku a bisanta kamar alkyabba, Ruwan kuwa ya rufe manyan duwatsu. 7 Amma sa'ad da ka tsauta wa ruwa, Sai ya tsere, Sa'ad da ya ji ka daka tsawa, Sai ya sheƙa a guje. 8 Ya haura kan duwatsu, ya gangara cikin kwaruruka, Wurin da ka shirya masa. 9 Ka ƙayyade masa kan iyaka da ba zai taɓa ƙetarewa ba, Don kada ya sāke rufe duniya. 10 Ka sa maɓuɓɓugai suka gudano cikin kwaruruka, Ka sa ruwa yana gudu tsakanin tuddai. 11 Su ne suke shayar da namomin jeji, Jakunan jeji kuma, a nan sukan kashe ƙishinsu. 12 A itatuwan da suke kusa da wurin, Tsuntsaye suke yin sheƙunansu suna ta raira waƙa. 13 Daga sararin sama kakan aiko da ruwa bisa duwatsu, Ƙasa kuwa takan cika da albarkunka. 14 Kakan sa ciyawa ta yi girma don shanu, Tsire-tsire kuma don amfanin mutum, Saboda haka mutum zai iya shuka amfanin gona, 15 Don ya yi ruwan inabin da zai sa shi farin ciki, Ya sami man zaitun wanda zai sa shi fara'a, Da abincin da zai ba shi ƙarfi. 16 Itatuwan al'ul na Lebanon sukan sami isasshen ruwan sama, Itatuwa ne na Ubangiji kansa, waɗanda shi ya dasa. 17 A nan tsuntsaye suke yin sheƙunansu, A bisa itatuwan fir shamuwa take yin sheƙa. 18 A kan duwatsu masu tsayi awakin jeji suke zama, Remaye sukan ɓuya a kan tsaunukan bakin teku. 19 Ka halicci wata don ƙididdigar lokatai, Rana kuwa ta san daidai lokacin fāɗuwarta. 20 Ka halicci dare, da duhu inda namomin jeji suke fitowa. 21 Sagarun zakoki sukan yi ruri sa'ad da suke farauta, Suna neman abincin da Allah zai ba su. 22 Sa'ad da rana ta fito, Sai su koma su kwanta a kogwanninsu. 23 Sa'an nan mutane sukan fita su yi aikinsu, Su yi ta aiki har maraice ya yi. 24 Ya Ubangiji, ka halicci abubuwa masu yawa! Da hikima ƙwarai ka halicce su! Duniya cike take da talikanka. 25 Ga babbar teku mai fāɗi, Inda talikai da ba su ƙidayuwa suke zaune, Manya da ƙanana gaba ɗaya. 26 Jiragen ruwa suna tafiya a kansa, Dodon ruwa wanda ka halitta, a ciki yake wasa. 27 Dukansu a gare ka suke dogara, Don ka ba su abinci sa'ad da suke bukata. 28 Ka ba su, sun ci, Ka tanada musu abinci, sun ƙoshi. 29 Sa'ad da ka rabu da su sukan tsorata, In ka zare numfashin da ka ba su, sai su mutu, Su koma turɓaya, da ma da ita aka yi su. 30 Amma sa'ad da ka hura musu numfashi, sai su rayu, Kakan sabunta fuskar duniya. 31 Da ma darajar Ubangiji ta dawwama har abada! Da ma Ubangiji ya yi farin ciki da abin da ya halitta! 32 Ya dubi duniya, sai ta girgiza, Ya taɓa duwatsu, sai suka tuɗaɗo da hayaƙi. 33 Zan raira waƙa ga Ubangiji dukan raina, Zan raira yabbai ga Allah muddin raina. 34 Da ma ya ji daɗin waƙata, Saboda yakan sa ni in yi murna. 35 Da ma a hallakar da masu zunubi daga duniya, Da ma mugaye su ƙare ƙaƙaf! Ka yabi Ubangiji, ya raina! Ka yabi Ubangiji!

Zabura 105

Allah da Jama'arsa

1 Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar girmansa, Ku sanar wa sauran al'umma abubuwan da ya yi! 2 Ku raira masa waƙa, ku raira yabo gare shi, Ku faɗi dukan abubuwa masu banmamaki da ya yi! 3 Ku yi murna saboda mu nasa ne, Ku yi murna dukanku da kuke bauta wa Ubangiji! 4 Ku je wurin Ubangiji neman taimako, Ku tsaya a gabansa koyaushe. 5-6 Ya ku zuriyar bawansa Ibrahim, Ya ku zuriyar zaɓaɓɓensa Yakubu, Ku tuna da mu'ujizansa masu girma, masu banmamaki, Ku tuna kuma da hukuntai waɗanda ya yanke. 7 Shi Ubangiji, shi ne Allahnmu, Umarnansa domin dukan duniya ne. 8 Zai cika alkawarinsa har abada, Alkawaransa kuma don dubban zamanai, 9 Yarjejeniyar da ya yi da Ibrahim, Da alkawarin da ya yi wa Ishaku. 10 Ubangiji ya yi madawwamin alkawari da Isra'ila, Ya yi madawwamiyar yarjejeniya da Yakubu sa'ad da ya ce, 11 “Zan ba ka ƙasar Kan'ana, Za ta zama mallakarka.” 12 Jama'ar Ubangiji kima ne, Baƙi ne kuwa a ƙasar. 13 Suka yi ta yawo daga ƙasa zuwa ƙasa, Daga wannan mulki zuwa wancan, 14 Amma bai yarda kowa ya zalunce su ba, Ya tsauta wa sarakuna da yawa saboda su. 15 Ya ce, “Kada ku taɓi bayina, zaɓaɓɓu, Kada ku cuci annabawana!” 16 Sa'ad da Ubangiji ya aukar da yunwa a ƙasarsu, Ya kuma sa abincinsu duka ya ƙare, 17 Sai ya aika da Yusufu ya riga su zuwa, Shi wanda aka sayar da shi kamar bawa. 18 Ƙafafunsa suka yi rauni saboda an ɗaure su da sarƙa, Aka kuma sa wa wuyansa ƙuƙumi na baƙin ƙarfe, 19 Har kafin faɗar da ya yi, ta cika. Maganar Ubangiji ta tabbatar da gaskiyar abin da ya faɗa. 20 Sa'an nan Sarkin Masar ya sake shi, Mai mulkin dukan sauran al'umma ya 'yantar da shi. 21 Ya sa shi ya lura da mulkinsa, Ya sa shi ya yi mulki a bisa dukan ƙasar. 22 Ya ba shi cikakken iko bisa dukan ma'aikatan hukuma. Ya ba shi ikon umartar mashawartansa. 23 Sa'an nan Yakubu ya tafi Masar, Ya zauna a ƙasar. 24 Ubangiji ya sa jama'arsa suka hayayyafa da yawa, Ya sa su fi ƙarfin maƙiyansu. 25 Ya sa Masarawa suka ƙi jinin jama'arsa, Suka yi wa bayinsa munafunci. 26 Sai ya aiki bayinsa Musa da Haruna, waɗanda ya zaɓa. 27 Suka aikata manya manyan ayyuka na Allah, Suka kuma yi ayyukan al'ajabi a Masar. 28 Ya aika da duhu a bisa ƙasar. Musa da Haruna ba su tayar wa umarnansa ba. 29 Ya mai da ruwan kogunansu su zama jini, Ya karkashe kifayensu duka. 30 Ƙasarsu ta cika da kwaɗi, Har a fādar sarki. 31 Allah ya ba da umarni, sai ƙudaje da ƙwari Suka cika dukan ƙasar. 32 Ya aiki ƙanƙara da tsawa a bisa ƙasarsu Maimakon ruwan sama. 33 Ya lalatar da 'ya'yan inabinsu da itatuwan ɓaurensu, Ya kakkarya itatuwansu. 34 Ya ba da umarni, sai fāri suka zo, Dubun dubbai da ba su ƙidayuwa. 35 Suka cinye dukan tsire-tsire na ƙasa. Suka cinye dukan amfanin gonaki. 36 Ya karkashe dukan 'ya'yan fari maza Na dukan iyalan Masarawa. 37 Sa'an nan ya bi da Isra'ilawa, suka fita, Suka kwashi azurfa da zinariya, Dukansu kuma ƙarfafa ne lafiyayyu. 38 Masarawa suka yi murna da fitarsu, Gama sun tsoratar da su. 39 Ya sa girgije ya yi wa jama'arsa inuwa, Da dare kuma wuta ta haskaka musu. 40 Suka roƙa, sai aka ba su makware, Ya ba su abinci daga sama da za su ci su ƙoshi. 41 Ya buɗe dutse, sai ruwa ya bulbulo, Yana gudu cikin hamada kamar kogi. 42 Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki Wanda ya yi wa bawansa Ibrahim. 43 Haka kuwa ya bi da jama'arsa, suka fita suna raira waƙa, Ya bi da zaɓaɓɓun jama'arsa, suna sowa ta farin ciki. 44 Ya ba su ƙasar baƙi, Ya sa su gāje gonakinsu, 45 Don jama'arsa su yi biyayya da dokokinsa, Su kuma kiyaye umarninsa. Ku yabi Ubangiji!

Zabura 106

Tawayen Isra'ila

1 Ku yabi Ubangiji! Ku yi wa Ubangiji godiya, gama nagari ne shi, Ƙaunarsa madawwamiya ce. 2 Wa zai iya faɗar dukan manya manyan ayyuka da ya yi? Wa zai iya yi masa isasshen yabo? 3 Masu farin ciki ne waɗanda suke biyayya da umarnansa, Waɗanda kullayaumi suke aikata abin da yake daidai! 4 Ka tuna da ni sa'ad da za ka taimaki jama'arka, ya Ubangiji! Ka sa ni cikinsu, sa'ad da za ka cece su. 5 Ka yardar mini in ga wadatar jama'arka, In yi tarayya da jama'arka da farin cikinsu, In yi farin ciki tare da waɗanda suke murna ta fāriya domin su naka ne. 6 Mun yi zunubi yadda kakanninmu suka yi, Mugaye ne, mun aikata mugunta. 7 Kakanninmu a Masar Ba su fahimci ayyukan Allah masu banmamaki ba, Sau da yawa sukan manta da irin ƙaunar da ya nuna musu, Suka tayar wa Mai Iko Dukka a Bahar Maliya. 8 Amma duk da haka ya cece su, kamar yadda ya alkawarta, Domin ya nuna ikonsa mai girma. 9 Ya tsauta wa Bahar Maliya, ta ƙafe, Har ya bi da jama'arsa su haye Kamar a bisa busasshiyar ƙasa. 10 Ya cece su daga maƙiyansu, Ya ƙwato su daga wurin abokan gābansu. 11 Ruwa ya cinye maƙiyansu, Ba wanda ya tsira. 12 Sa'an nan jama'arsa suka gaskata alkawarinsa, Suka raira yabo gare shi. 13 Amma nan da nan, suka manta da abin da ya yi, Suka aikata, ba su jira shawararsa ba. 14 Suka cika da sha'awa cikin hamada, Suka jarraba Allah, 15 Sai ya ba su abin da suke roƙa, Amma ya aukar musu da muguwar cuta. 16 Can cikin hamada suka ji kishin Musa Da Haruna, bayin Ubangiji, tsarkaka, 17 Sai ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan, Ta binne Abiram da iyalinsa. 18 Wuta ta sauko bisa magoya bayansu, Ta ƙone mugayen mutanen nan. 19 Suka ƙera ɗan maraƙi da zinariya a Horeb, Suka yi masa sujada. 20 Suka musaya ɗaukakar Allah Da siffar dabba mai cin ciyawa. 21 Suka manta da Allah wanda ya cece su, Ta wurin manyan ayyuka da ya yi a Masar. 22 Kai, Allah ya aikata abubuwa masu ban al'ajabi a can! Ga kuma abubuwa masu banmamaki da ya aikata a Bahar Maliya! 23 Saboda wannan Allah ya ce zai hallaka jama'arsa, Amma Musa, zaɓaɓɓen bawansa, ya yi godo ga Allah, Allah kuwa ya huce, bai hallaka su ba. 24 Sai suka ƙi ƙasar nan mai ni'ima, Saboda ba su gaskata alkawarin Allah ba. 25 Suka zauna cikin alfarwansu suna ta gunaguni, Sun ƙi su saurari Ubangiji. 26 Saboda haka ya yi musu kakkausan kashedi, Cewa shi zai sa su duka su mutu a jejin, 27 Zai warwatsa zuriyarsu a cikin arna, Ya bar su su mutu a baƙuwar ƙasa. 28 Sai jama'ar Allah suka taru suka shiga yi wa Ba'al sujada, a Feyor, Suka ci hadayun da aka miƙa wa matattun alloli. 29 Suka tsokani Ubangiji, ya yi fushi saboda ayyukansu, Mugawar cuta ta auka musu, 30 Amma Finehas ya tashi, ya yanke hukunci a kan laifin, Aka kuwa kawar da annobar. 31 Tun daga lokacin nan ake ta tunawa da shi, Saboda abin da ya yi. Za a yi ta tunawa da shi a dukan zamanai masu zuwa. 32 Jama'ar Ubangiji suka sa ya yi fushi. A maɓuɓɓugan Meriba, Musa ya shiga uku saboda su. 33 Suka sa Musa ya husata ƙwarai, Har ya faɗi abubuwan da bai kamata ya faɗa ba. 34 Suka ƙi su kashe arna, Yadda Ubangiji ya umarta, 35 Amma suka yi aurayya da su, Suka kwaikwayi halayen arnan. 36 Jama'ar Allah suka yi wa gumaka sujada. Wannan kuwa ya jawo musu hallaka. 37 Suka miƙa 'ya'yansu mata da maza hadaya ga allolin arna. 38 Suka karkashe mutane marasa laifi, Wato 'ya'yansu mata da maza. Suka miƙa su hadaya ga gumakan Kan'ana, Suka ƙazantar da ƙasar saboda kashe-kashenkan da suke yi. 39 Ta wurin ayyukansu, suka ƙazantar da kansu, Suka zama marasa aminci ga Allah. 40 Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da jama'arsa, Ransa bai ji daɗinsu ba. 41 Sai ya bar su ƙarƙashin ikon arna, Abokan gābansu suka mallake su. 42 Abokan gābansu suka zalunce su, Suka tilasta su, su yi musu biyayya. 43 Sau da yawa Ubangiji yakan ceci jama'arsa, Amma sun fi so su yi masa tawaye, Suna ta nutsawa can cikin zunubi. 44 Duka da haka Ubangiji ya ji su sa'ad da suka yi kira gare shi, Ya kula da wahalarsu. 45 Saboda su ne ya tuna da alkawarinsa, Ya sāke ra'ayinsa saboda ƙaunarsa mai yawa. 46 Ubangiji ya sa waɗanda suka kama su Su ji tausayinsu. 47 Ka cece mu, ya Ubangiji Allahnmu, Ka komo da ma daga cikin sauran al'umma, Domin mu yabi sunanka mai tsarki, Mu kuma yi murna mu yi maka godiya. 48 Sai mu yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila, Mu yabe shi yanzu da har abada kuma! Dukan jama'a za su amsa su ce, “Amin! Amin!” Ku yabi Ubangiji!

Zabura 107

Ubangiji ne Mai Kuɓutarwa daga Wahala

1 Ku gode wa Ubangiji, gama shi nagari ne, Ƙaunarsa madawwamiya ce! 2 Ku zo mu yabi Ubangiji tare, Dukanku waɗanda ya fansa, Gama ya ƙwato ku daga maƙiyanku. 3 Ya komo da ku daga ƙasashen waje, Daga gabas da yamma, kudu da arewa. 4 Waɗansu suka yi ta kai da kawowa a hamada inda ba hanya, Sun kasa samun hanyar da za ta kai su garin da za su zauna a ciki. 5 Suka yi ta fama da yunwa, da ƙishirwa, Suka fid da zuciya ga kome. 6 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga wahalarsu. 7 Ya fisshe su, ya bi da su sosai, Zuwa birnin da za su zauna. 8 Dole ne su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu! 9 Ya shayar da waɗanda suke jin ƙishirwa, Ya kuma ƙosar da mayunwata da alheransa. 10 Waɗansu suna zaune cikin duhu da inuwar mutuwa, 'Yan sarƙa suna shan wahala da sarƙoƙi, 11 Saboda sun tayar, sun ƙi bin umarnan Allah Maɗaukaki, Sun kuwa ƙi koyarwarsa. 12 Suka gaji tiƙis saboda tsananin aiki, Za su faɗi ƙasa, ba mataimaki. 13 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga wahalarsu. 14 Ya fisshe su daga cikin duhu da inuwar mutuwa, Ya tsintsinka sarƙoƙinsu. 15 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu. 16 Ya kakkarya ƙofofin da aka yi da tagulla. Ya kuma ragargaza ƙyamaren da aka yi da baƙin ƙarfe. 17 Waɗansu suka yi ciwo sabili da zunubansu, Suna ta shan wahala saboda muguntarsu. 18 Ba su so su ga abinci, Sun kusa mutuwa. 19 A cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga azabar da suke sha. 20 Da umarninsa ya warkar da su, Ya cece su daga kabari. 21 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu. 22 Dole su gode masa, su miƙa masa hadayu, Su raira waƙoƙin murna, Su faɗi dukan abin da ya yi! 23 Waɗansu suka yi tafiya a teku da jirage, Suna samun abin zaman garinsu daga tekuna. 24 Suka ga abin da Ubangiji ya aikata, Ayyukansa masu banmamaki waɗanda ya yi a tekuna. 25 Ya ba da umarni, sai babbar iska ta tashi, Ta fara hurowa, ta sa raƙuman ruwa su tashi. 26 Aka ɗaga jiragen ruwa sama, Sa'an nan suka tsinduma cikin zurfafa. Da mutanen suka ga irin hatsarin da suke ciki, Sai zuciyarsu ta karai. 27 Suka yi ta tuntuɓe suna ta tangaɗi kamar bugaggu, Gwanintarsu duka ta zama ta banza. 28 Cikin wahalarsu suka yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa cece su daga azabarsu. 29 Ya sa hadiri ya yi tsit, Raƙuman ruwa kuma suka yi shiru. 30 Suka yi murna saboda wurin ya yi shiru, Ya kuma kai su kwatar jiragen ruwa lafiya, Wurin da suke so. 31 Dole su gode wa Ubangiji saboda madawwamiyar ƙaunarsa, Sabili da abubuwa masu banmamaki waɗanda ya aikata dominsu. 32 Dole su yi shelar girmansa cikin taron jama'a, Su kuma yabe shi a gaban majalisar dattawa. 33 Ubangiji ya sa koguna suka ƙafe ƙaƙaf, Ya hana maɓuɓɓugai su gudana. 34 Ya mai da ƙasa mai dausayi ta zama mai gishiri, marar amfani, Saboda muguntar waɗanda suke zaune a can. 35 Ya sāke hamada ta zama tafkunan ruwa, Ya kuma mai da busasshiyar ƙasa ta zama maɓuɓɓugai masu gudana. 36 Ya bar mayunwata su zauna a can, Suka kuwa gina birni don su zauna a ciki. 37 Suka shuka gonaki suka dasa kurangar inabi, Waɗanda suka ba da amfani mai yawan gaske. 38 Ya sa wa jama'arsa albarka, Suka kuwa haifi 'ya'ya da yawa. Bai bar garkunan shanunsu su ragu ba. 39 Sa'ad da aka ci nasara a kan jama'ar Allah, Aka ƙasƙantar da su ta wurin mugun zalunci, Da wahalar da aka yi musu. 40 Sai Allah ya wulakanta waɗanda suka zalunci jama'arsa. Ya sa su suka yi ta kai da kawowa A hamada inda ba hanya. 41 Ya tsamo masu bukata daga cikin baƙin cikinsu, Ya sa iyalansu su riɓaɓɓanya kamar garkunan tumaki. 42 Da adalai suka ga wannan, sai suka yi murna, Mugaye kuwa aka rufe bakinsu. 43 Da ma a ce masu hikima Za su yi tunani a kan waɗannan abubuwa, Da ma kuma su yarda Da madawwamiyar ƙaunar Ubangiji.

Zabura 108

Addu'ar Neman Tsari daga Maƙiya

1 A shirye nake, ya Allah, Na shirya sosai! Zan raira waƙa in yabe ka! Ka farka, ya raina! 2 Ku farka, ya molona da garayata! Zan farkar da rana! 3 Zan yi maka godiya a tsakiyar sauran al'umma, ya Ubangiji! Zan yabe ka a tsakiyar kabilai! 4 Madawwamiyar ƙaunarka ta kai har can saman sammai, Amincinka kuma ya kai sararin sammai. 5 Ya Allah, ka bayyana girmanka a sararin sama, Ɗaukakarka kuma a bisa dukan duniya! 6 Ka cece mu da ƙarfinka, ka amsa addu'ata, Domin jama'ar da kake ƙauna ta sai cetonka. 7 A tsattsarkan wurinsa, Allah ya faɗa ya ce, “Da nasara zan raba Shekem, Da nasara kuma zan rarraba Sukkot ga jama'ata. 8 Gileyad tawa ce, har da Manassa ma, Ifraimu ne kwalkwalina, Yahuza kuma sandana ne na sarauta. 9 Amma zan yi amfani da Mowab kamar kwanon wanki, Edom kuwa kamar akwatin takalmina. Zan yi sowar nasara a kan Filistiyawa.” 10 Ya Allah, wa zai kai ni birni mai kagara? Wa zai kai ni Edom? 11 Da gaske ka yashe mu ke nan? Ba za ka yi tafiya Tare da sojojinmu ba? 12 Ka taimake mu, mu yaƙi abokin gāba, Domin taimako irin na mutum banza ne! 13 Idan Allah yana wajenmu, Za mu yi nasara, Zai kori abokan gābanmu.

Zabura 109

Kukan Mutumin da yake Shan Wahala

1 Ina yabonka, ya Allah, kada ka yi shiru! 2 Mugaye da maƙaryata sun tasar mini, Suna ta faɗar ƙarairayi a kaina. 3 Suna faɗar mugayen abubuwa a kaina. Suna tasar mini ba dalili. 4 Suna ƙina ko da yake ina ƙaunarsu, Har ina yi musu addu'a. 5 Sukan sāka mini alheri da mugunta, Sukan sāka mini ƙauna da ƙiyayya. 6 Ka zaɓi lalataccen mutum ya shara'anta maƙiyina, Ka sa ɗaya daga cikin maƙiyansa Ya gabatar da ƙararsa. 7 Ka sa a same shi da laifi a shari'ar da ake yi masa, Ka sa har addu'ar da yake yi Ta zama babban laifi! 8 Ka aukar masa da ajalinsa nan da nan, Ka sa wani ya ɗauki matsayinsa! 9 Ka sa 'ya'yansa su zama marayu, Matarsa kuwa ta zama gwauruwa! 10 Ka sa 'ya'yansa su rasa gidan zama, su riƙa yawon bara. Ka sa a kore su daga kufan da suke zaune! 11 Ka sa waɗanda suke binsa bashi su kwashe Dukan abin da yake da shi. Ka sa baƙi su kwashe dukan abin da ya sha wahalar nema. 12 Ka sa kada kowa ya yi masa alheri sam, Kada ka bar kowa ya lura da marayunsa. 13 Ka sa dukan zuriyarsa su mutu, Har a manta da sunansa a tsara mai zuwa. 14 Sai ka tuna, ya Ubangiji, da muguntar kakanninsa, Kada ka manta da zunuban mahaifiyarsa. 15 Ka tuna da zunubansu kullayaumin, ya Ubangiji, Amma su kansu a manta da su ɗungum! 16 Gama mutumin nan bai taɓa tunanin yin alheri ba, Yakan tsananta wa talakawa, da matalauta, da kasassu, har ya kashe su. 17 Yana jin daɗin la'antarwa, ka sa a la'anta shi! Ba ya son sa albarka, ka sa kada kowa ya sa masa albarka! 18 Yakan la'antar a sawwaƙe kamar yadda yake sa tufafinsa. Ka sa la'antarwa da yake yi Su jiƙa shi kamar ruwa, Su shiga har ƙasusuwansa kamar mai, 19 Su lulluɓe shi kamar tufa, Su kuma kewaye shi kamar ɗamara. 20 Ya Ubangiji, ka sa haka, Wato ya zama yadda za a hukunta wa maƙiyana ke nan, Waɗanda suke faɗar mugayen abubuwa a kaina! 21 Amma ya Ubangiji, Allahna, ka taimake ni, Yadda ka alkawarta, Ka cece ni sabili da alherin ƙaunarka. 22 Ni talaka ne, matalauci, Na ji zafi ƙwarai a can zuciyata. 23 Na kusa ɓacewa kamar inuwar maraice, An hurar da ni can kumar ƙwaro. 24 Gwiwoyina sun yi suwu saboda rashin abinci, Jikina kuma ya rame, ba shi da ƙarfi. 25 Sa'ad da mutane suka gan ni sun yi mini ba'a, Suna kaɗa kai saboda raini. 26 Ka taimake ni, ya Ubangiji Allahna, Ka cece ni saboda madawwamiyar ƙaunarka! 27 Ka sa maƙiyana su sani, Kai ne Mai Cetona. 28 Watakila su la'anta ni, Amma kai za ka sa mini albarka, Ka sa a kori waɗanda suke tsananta mini. Da ma ka sa ni da nake bawanka, in yi murna. 29 Ka sa kunya ta rufe maƙiyana, Ka sa su sa kunyarsu kamar riga. 30 Da murya mai ƙarfi zan yi wa Ubangiji godiya. Zan yabe shi a taron jama'a, 31 Saboda yakan kāre talaka, Domin ya cece shi daga waɗanda Suka sa masa laifin mutuwa.

Zabura 110

Ubangiji ya Ba Sarkin da ya Zaɓa Iko

1 Ubangiji ya ce wa Mai Girma, Sarkina, “Zauna nan a damana, Har in sa maƙiyanka a ƙarƙashin sawayenka.” 2 Tun daga Sihiyona Ubangiji zai faɗaɗa sarautarka, ya ce, “Ka yi mulki bisa maƙiyanka.” 3 A ranar da za ka yi yaƙi da maƙiyanka, Jama'arka za su kawo maka gudunmawa don kansu. Kamar yadda raɓa take da sassafe, Haka samarinka za su zo wurinka a tsarkakan tsaunuka. 4 Ubangiji ya yi muhimmin alkawari, Ba kuwa zai fasa ba! “Za ka zama firist har abada Bisa ga tsabi'ar Malkisadik firist.” 5 Ubangiji yana damanka, Zai kori sarakuna a ranar da ya husata. 6 Zai shara'anta wa dukan sauran al'umma, Ya rufe fagen fama da gawawwaki, Zai kori sarakunan duk duniya. 7 Sarkin zai sha ruwan rafin da yake kan hanya, Ya wartsake ya sami ƙarfi. Zai yi tsayawar nasara.

Zabura 111

Kiyayewar Ubangiji ga Jama'arsa

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Zan yi wa Ubangiji godiya da zuciya ɗaya, A cikin taron jama'arsa. 2 Abubuwan banmamaki ne Ubangiji yake aikatawa! Duk waɗanda suke murna da su Suna so su fahimce su. 3 Dukan abin da yake yi, Cike yake da girma da ɗaukaka, Adalcinsa har abada ne. 4 Ubangiji ba zai bar mu mu manta da ayyukansa masu banmamaki ba, Shi mai alheri ne, mai jinƙai kuma. 5 Yakan tanada wa masu tsoronsa abinci, Bai taɓa mantawa da alkawarinsa ba. 6 Ya nuna ikonsa ga jama'arsa Saboda ya ba su ƙasashen baƙi. 7 Iyakar abin da yake yi duka, da aminci da adalci ne. Dukan umarnansa, abin dogara ne. 8 Sukan tabbata har abada, Da gaskiya da adalci aka ba da su. 9 Ya kawo wa jama'arsa ceto, Ya kuma yi musu madawwamin alkawari. Mai Tsarki ne shi, Maɗaukaki! 10 Hanyar samun hikima, ita ce tsoron Ubangiji, Yakan ba da kyakkyawar ganewa Ga dukan waɗanda suke bin umarnansa, Sai ku yabe shi har abada!

Zabura 112

Wadatar Mai Tsoron Allah

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Mai farin ciki ne mutumin da yake tsoron Ubangiji, Mai farin ciki ne shi wanda yake jin daɗin yin biyayya da umarnansa. 2 'Ya'yansa za su zama manyan ƙasar, Zuriyar mutumin kirki za ta yi albarka. 3 Iyalinsa za su zama attajirai masu dukiya, Adalcinsa zai tabbata har abada. 4 Haske yakan haskaka wa mutanen kirki a cikin duhu, Da waɗanda suke yin alheri, da jinƙai, da gaskiya. 5 Mai farin ciki ne mutumin da yakan ba da rance hannu sake, Wato wanda yake yin harkarsa da gaskiya. 6 Mutumin kirki ba zai kāsa ba daɗai, Ba za a taɓa mantawa da shi ba. 7 Ba ya tsoron jin mugun labari, Bangaskiyarsa tana da ƙarfi, Ga Ubangiji yake dogara. 8 Ba shi da damuwa ko tsoro, Ya tabbata zai ga fāɗuwar maƙiyansa. 9 Yakan bayar ga matalauta hannu sake, Alherinsa kuwa dawwamamme ne. Zai zama mai iko wanda ake girmamawa. 10 Sa'ad da mugaye suka ga wannan, Sai suka tunzura, suka harare shi da fushi, suka ɓace, Sa zuciyarsu ta ƙare har abada.

Zabura 113

Yabon Alherin Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku bayin Ubangiji, Ku yabi sunansa! 2 Za a yabi sunansa yanzu da har abada! 3 Daga gabas zuwa yamma a yabi sunan Ubangiji! 4 Ubangiji yake mulkin dukan sauran al'umma, Ɗaukakarsa tana bisa kan sammai. 5 Ba wani kamar Ubangiji Allahnmu. Yana zaune a can ƙwanƙolin sama, 6 Amma ya duba ƙasa, Ya dubi sammai da duniya. 7 Yakan ɗaga talakawa daga ƙura, Yakan ɗaga matalauta daga cikin azabarsu. 8 Yakan sa su zama abokan sarakuna, Sarakunan jama'arsa. 9 Yakan girmama matar da ba ta haihuwa a gidanta, Yakan sa ta yi farin ciki ta wurin ba ta 'ya'ya. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 114

Waƙar Idin Ƙetarewa

1 Sa'ad da jama'ar Isra'ila suka bar Masar, Sa'ad da zuriyar Yakubu suka bar baƙuwar ƙasar nan, 2 Yahuza ya zama tsattsarkar jama'ar Ubangiji, Isra'ila ya zama abin mallakarsa. 3 Bahar Maliya da ya duba, sai ya gudu, Kogin Urdun ya daina gudu. 4 Duwatsu suka yi ta tsalle kamar awaki, Tuddai kuwa suka yi ta tsalle suna kewayawa kamar tumaki. 5 Me ya faru ne, ya teku, da ya sa ki gudu? Kai fa Urdun, me ya sa ka daina gudu? 6 Ku fa duwatsu, me ya sa kuka yi ta tsalle kamar awaki? Tuddai, me ya sa kuka yi ta tsalle, Kuna kewayawa kamar tumaki? 7 Ki yi rawar jiki, yake duniya, Saboda zuwan Ubangiji, A gaban Allah na Yakubu, 8 Wanda ya sa duwatsu su zama tafkunan ruwa, Ya kuma sa kogwannin duwatsu su zama maɓuɓɓugai, Masu bulbulo da ruwa.

Zabura 115

Allah Mai Gaskiya Makaɗaici

1 A gare ka kaɗai, ya Ubangiji, A gare ka kaɗai, ba a gare mu ba, Dole a girmama ka, Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka. 2 Me ya sa sauran al'umma suke tambayarmu, “Ina Allahnku?” 3 Allahnmu yana Sama, Yana aikata yadda yake so. 4 Amma nasu alloli na azurfa da zinariya ne, Da hannu aka siffata su. 5 Suna da baki, amma ba sa magana, Suna da idanu, amma ba sa gani. 6 Suna da kunnuwa, amma ba sa ji, Suna da hanci, amma ba sa jin ƙanshi. 7 Suna da hannuwa, amma ba sa iya riƙon kome, Suna da ƙafafu, amma ba sa iya tafiya. Ba su da murya sam. 8 Ka sa waɗanda suka yi su, Da dukan masu dogara gare su, Su zama kamar gumakan da suka yi! 9 Ku dogara ga Ubangiji, ya ku jama'ar Isra'ila! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku. 10 Ku dogara ga Ubangiji, ya ku firistoci na Allah! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku. 11 Ku dogara ga Ubangiji, dukanku waɗanda kuke tsoronsa! Shi yake taimakonku, yana kiyaye ku. 12 Ubangiji yana tuna da mu, zai kuwa sa mana albarka, Zai sa wa jama'ar Isra'ila albarka, Da dukan firistoci na Allah. 13 Zai sa wa dukan waɗanda suke tsoronsa albarka. Babba da yaro. 14 Ubangiji ya ba ku 'ya'ya, Ku da zuriyarku. 15 Ubangiji, wanda ya yi sama da ƙasa Ya sa muku albarka! 16 Samaniya ta Ubangiji ce kaɗai, Amma ya ba mutane duniya. 17 Matacce ba ya yabon Ubangiji, Ko wanda ya gangara zuwa cikin kabari. 18 Amma mu da muke rayayyu, za mu yi masa godiya. A yanzu da har abada. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 116

Mutumin da aka Cece shi daga Mutuwa

1 Ina ƙaunar Ubangiji, saboda yana jina, Yana kasa kunne ga addu'o'ina. 2 Yakan kasa kunne gare ni, A duk lokacin da na yi kira gare shi. 3 Mutuwa ta ɗaure ni da da igiyarta tam, Razanar kabari ta auka mini, Na cika da tsoro da alhini. 4 Sa'an nan sai na yi kira ga Ubangiji, na ce, “Ina roƙonka, ya Ubangiji, ka cece ni!” 5 Ubangiji mai jinƙai ne, mai alheri, Allahnmu mai rahama ne. 6 Ubangiji yakan kiyaye kāsassu, Sa'ad da na shiga hatsari ya cece ni. 7 Kada ki yi shakka, ya zuciyata, Gama Ubangiji yana yi mini alheri. 8 Ubangiji ya cece ni daga mutuwa, Ya share hawayena, Bai bari a kāshe ni ba. 9 Don haka nake tafiya a gaban Ubangiji A duniyar masu rai. 10 Na dai yi ta gaskatawa, ko da yake Na ce, “An ragargaza ni sarai.” 11 Sa'ad da na ji tsoro na ce, “Ba wanda za a iya dogara gare shi.” 12 Me zan bayar ga Ubangiji Saboda sukan alheransa gare ni? 13 Zan miƙa hadaya ta sha ga Ubangiji, Ina gode masa domin dā ya cece ni. 14 Zan ba shi abin da na alkawarta A taron dukan jama'arsa. 15 Mutuwar ɗaya daga cikin tsarkakansa, Abu mai daraja ne! 16 Ni bawanka ne, ya Ubangiji, Ina bauta maka yadda mahaifiyata ta yi, Ka 'yantar da ni. 17 Zan miƙa maka hadaya ta godiya, Zan yi addu'ata a gare ka. 18-19 A taron dukan jama'arka, A shirayun Haikalinka, A Urushalima, zan ba ka abin da na alkawarta. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 117

Yabo ga Ubangiji saboda Madawwamiyar Ƙaunarsa

1 Ku yabi Ubangiji, ku dukan sauran al'ummai! Ku yabe shi, ku dukan kabilai! 2 Madawwamiyar ƙaunarsa, da ƙarfi take, Amincinsa kuma tabbatacce ne har abada. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 118

Addu'ar Godiyar don Cin Nasara

1 Ku gode wa Ubangiji, Domin shi mai alheri ne, Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce. 2 Bari jama'ar Isra'ila su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.” 3 Bari dukan firistoci na Allah su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.” 4 Bari dukan waɗanda suke tsoronsa su ce, “Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.” 5 A cikin wahalata na yi kira ga Ubangiji Ya kuwa amsa mini, ya kuɓutar da ni. 6 Ubangiji yana tare da ni, ba zan ji tsoro ba. Me mutane za su iya yi mini? 7 Ubangiji ne yake taimakona, Zan kuwa ga fāɗuwar maƙiyana da idona. 8 Gwamma a dogara ga Ubangiji, Da a dogara ga mutane. 9 Gwamma a dogara ga Ubangiji, Da a dogara ga shugabanni na mutane kawai. 10 Maƙiya da yawa sun kewaye ni, Amma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji! 11 Suka kewaye ni a kowane gefe Amma na hallaka su ta wurin ikon Ubangiji! 12 Suka rufe ni kamar ƙudan zuma, Amma suka ƙone nan da nan kamar wutar jeji, Ta wurin ikon Ubangiji na hallaka su! 13 Aka auko mini da tsanani, Har aka kore ni, Amma Ubangiji ya taimake ni. 14 Ubangiji yakan ba ni iko, ya ƙarfafa ni, Shi ne Mai Cetona! 15 Ku kasa kunne ga sowar murna ta nasara A cikin alfarwan jama'ar Allah. “Ikon Ubangiji mai girma ne ya aikata wannan! 16 Ikonsa ne ya kawo mana nasara, Babban ikonsa a wurin yaƙi!” 17 Ba zan mutu ba, amma rayuwa zan yi, Don in ba da labarin abin da Ubangiji ya yi. 18 Ya hukunta ni da hukunci mai tsanani, Amma bai kashe ni ba. 19 A buɗe mini ƙofofin Haikali, Zan shiga ciki in yabi Ubangiji! 20 Wannan ƙofar Ubangiji ce, Sai adalai kaɗai suke shiga ciki! 21 Ina yabonka, ya Ubangiji, domin ka ji ni, Domin ka ba ni nasara! 22 Dutsen da magina suka ƙi, wai ba shi da amfani, Sai ya zama shi ya fi duka amfani. 23 Ubangiji ne ya yi haka, Wannan kuwa abin banmamaki ne! 24 Wace irin rana ce haka da Ubangiji ya ba mu! Bari mu yi farin ciki, mu yi biki! 25 Ka cece mu, ya Ubangiji, ka cece mu! Ka ba mu nasara, ya Ubangiji! 26 Allah yakan sa wa wanda ya zo da sunan Ubangiji albarka! Daga Haikalin Ubangiji muke yabonka! 27 Ubangiji shi ne Allah, yana yi mana alheri, Ku ɗauki hadayunku ku yi ta idi, Ku ɗaura su a zankayen bagade. 28 Kai ne Allahna, kai nake yi wa godiya, Zan yi shelar girmanka. 29 Ku gode wa Ubangiji, gama nagari ne, Ƙaunarsa kuwa tabbatacciya ce.

Zabura 119

Mafificiyar Shari'ar Ubangiji

1 Masu farin ciki ne marasa laifi cikin zamansu, Waɗanda suke zamansu bisa ga dokar Ubangiji. 2 Masu farin ciki ne waɗanda suke bin umarnansa, Waɗanda suke yi masa biyayya da zuciya ɗaya. 3 Hakika ba su yin laifi, Sukan yi tafiya a hanyoyin Ubangiji. 4 Kai ka ba mu dokokinka, Ka kuwa faɗa mana mu kiyaye su da aminci. 5 Na sa zuciya zan yi aminci, Game da kiyaye dokokinka! 6 Idan na kula da dukan umarnanka, To, ba zan kasa kaiwa ga burina ba. 7 Zan yabe ka da tsattsarkar zuciya, A sa'ad da na fahimci ka'idodinka masu adalci. 8 Zan yi biyayya da dokokinka, Ko kusa kada ka kashe ni!

Biyayya ga Shari'ar Ubangiji

9 Ƙaƙa saurayi zai kiyaye ransa da tsarki? Sai ta wurin biyayya da umarnanka. 10 Da zuciya ɗaya nake ƙoƙarin bauta maka, Ka kiyaye ni daga rashin biyayya da umarnanka! 11 Na riƙe maganarka a zuciyata, Don kada in yi maka zunubi. 12 Ina yabonka, Ya Ubangiji, Ka koya mini ka'idodinka! 13 Zan ta da murya, In maimaita dukan dokokin da ka bayar. 14 Ina murna da bin umarnanka, Fiye da samun dukiya mai yawa. 15 Nakan yi nazarin umarnanka, Nakan kuma yi bimbinin koyarwarka. 16 Ina murna da dokokinka, Ba zan manta da umarnanka ba.

Farin Ciki da Dokar Ubangiji

17 Ka yi mini alheri, ni bawanka, Domin in rayu in yi biyayya da koyarwarka. 18 Ka buɗe idona Domin in ga gaskiyar shari'arka mai banmamaki. 19 Zamana a nan duniya na ɗan lokaci kaɗan ne. Kada ka ɓoye mini umarnanka! 20 Zuciyata ta ƙosa saboda marmari, A kowane lokaci ina so in san hukuntanka. 21 Kakan tsauta wa masu girmankai, La'anannu ne waɗanda suka ƙi bin umarnanka. 22 Ka kuɓutar da ni daga cin mutuncinsu da raininsu, Domin na kiyaye dokokinka. 23 Ko da sarakuna za su taru Su shirya mini maƙarƙashiya, Duka da haka, ni bawanka, Zan yi nazarin ka'idodinka. 24 Umarnanka suna faranta mini rai, Su ne mashawartana.

Ƙudurin yin Biyayya ga Dokar Ubangiji

25 Ina kwance cikin ƙura, an yi nasara da ni, Ka wartsakar da ni kamar yadda ka alkawarta! 26 Na hurta dukan abin da na aikata, ka kuwa amsa mini, Ka koya mini ka'idodinka! 27 Ka koya mini yadda zan yi biyayya da dokokinka, In kuma yi nazarin koyarwarka mai banmamaki. 28 Ɓacin rai ya ci ƙarfina, Ka ƙarfafa ni, kamar yadda ka alkawarta. 29 Ka kiyaye ni daga bin muguwar hanya, Ta wurin alherinka, ka koya mini dokarka. 30 Na yi niyya in yi biyayya, Na mai da hankali ga ka'idodinka. 31 Na bi umarnanka, ya Ubangiji, Kada ka sa in kasa ci wa burina! 32 Ina ɗokin yin biyayya da umarnanka, Gama za ka ƙara mini fahimi.

Addu'ar Neman Fahimi

33 Ka koya mini ma'anar dokokinka, ya Ubangiji, Zan kuwa yi biyayya da su a kowane lokaci. 34 Ka fassara mini dokarka, ni kuwa zan yi biyayya da ita, Zan kiyaye ta da zuciya ɗaya. 35 Ka bishe ni a hanyar umarnanka, Domin a cikinsu nakan sami fari ciki 36 Ka sa ni in so yin biyayya da ka'idodinka, Fiye da samun dukiya. 37 Ka kiyaye ni daga mai da hankali ga abin da yake marar amfani, Ka yi mini alheri kamar yadda ka alkawarta. 38 Ka tabbatar da alkawarin da ka yi mini, ni bawanka, Irin wanda kakan yi wa waɗanda suke tsoronka. 39 Ka kiyaye ni daga cin mutuncin da nake tsoro, Ka'idodinka suna da amfani ƙwarai! 40 Ina so in yi biyayya da umarnanka, Gama kai mai adalci ne, Ka yi mini alheri!

Dogara ga Dokar Ubangiji

41 Ka nuna mini yawan ƙaunar da kake yi mini, ya Ubangiji, Ka cece ni bisa ga alkawarinka. 42 Sa'an nan zan amsa wa waɗanda suke cin mutuncina, Domin na dogara ga maganarka. 43 Ka ba ni iko in iyar da saƙonka na gaskiya a kowane lokaci, Gama sa zuciyata tana ga hukuntanka. 44 Kullum zan yi biyayya da dokarka har abada abadin! 45 Zan rayu da cikakken 'yanci, Gama na yi ƙoƙari in kiyaye ka'idodinka. 46 Zan hurta umarnanka ga sarakuna, Ba kuwa zan ji kunya ba. 47 Ina murna in yi biyayya da umarnanka, Saboda in ƙaunarsu. 48 Ina girmama umarnanka, ina kuwa ƙaunarsu, Zan yi ta tunani a kan koyarwarka.

Amincewa da Shari'ar Ubangiji

49 Ka tuna da alkawarin da ka yi mini, ni bawanka, Ka ƙarfafa zuciyata. 50 Ko ina shan wahala, ana ta'azantar da ni, Saboda alkawarinka yana rayar da ni. 51 Masu girmankai suna raina ni, Amma ban rabu da dokarka ba. 52 Na tuna da koyarwar da ka yi mini a dā, Sukan kuwa ta'azantar da ni, ya Ubangiji. 53 Haushi ya kama ni sosai, Sa'ad da na ga mugaye suna keta dokarka. 54 Ina zaune can nesa da gidana na ainihi, Sai na ƙago waƙoƙi a kan umarnanka. 55 Da dare nakan tuna da kai, ya Ubangiji, Ina kuwa kiyaye dokarka. 56 Wannan shi ne farin cikina, In yi biyayya da umarnanka.

Tunani a kan Shari'ar Ubangiji

57 Kai kaɗai nake so, ya Ubangiji, Na yi alkawari in yi biyayya da dokokinka. 58 Ina roƙonka da zuciya ɗaya, Ka yi mini jinƙai kamar yadda ka alkawarta! 59 Na yi tunani a kan ayyukana, Na yi alkawari in bi ka'idodinka. 60 Ba tare da ɓata lokaci ba, Zan gaggauta in kiyaye umarnanka. 61 Mugaye sun ɗaure ni tam da igiyoyi, Amma ba zan manta da dokarka ba. 62 Da tsakar dare nakan farka, In yabe ka saboda hukuntanka masu adalci. 63 Ina abuta da duk waɗanda suke bauta maka, Da duk waɗanda suke kiyaye dokokinka. 64 Ya Ubangiji, duniya ta cika da madawwamiyar ƙaunarka, Ka koya mini umarnanka!

Amfanin Shari'ar Ubangiji

65 Kana cika alkawarinka, ya Ubangiji, Kana kuwa yi mini alheri, ni bawanka. 66 Ka ba ni hikima da ilimi Domin ina dogara ga umarnanka. 67 Kafin ka hore ni nakan yi kuskure, Amma yanzu ina biyayya da maganarka. 68 Managarci ne kai, mai alheri ne kuma, Ka koya mini umarnanka! 69 Masu girmankai sun faɗi ƙarairayi a kaina, Amma da zuciya ɗaya nake biyayya da ka'idodinka. 70 Waɗannan mutane ba su da ganewa, Amma ni ina murna da dokarka. 71 Horon da aka yi mini ya yi kyau, Domin ya sa na koyi umarnanka. 72 Dokar da ka yi Muhimmiya ce a gare ni, Fiye da dukan dukiyar duniya.

Adalcin Shari'ar Ubangiji

73 Kai ne ka halicce ni, ka kuma kiyaye ni lafiya, Ka ba ni ganewa, don in koyi dokokinka. 74 Waɗanda suke tsoronka za su yi murna sa'ad da suka gan ni, Saboda ina dogara ga alkawarinka. 75 Na sani ka'idodinka na adalci ne, ya Ubangiji, Ka hore ni, domin kai mai aminci ne. 76 Ka sa madawwamiyar ƙaunarka ta ta'azantar da ni, Kamar yadda ka alkawarta mini, ni bawanka. 77 Ka yi mini jinƙai, zan rayu, Saboda ina murna da dokarka. 78 Ka kunyatar da masu girmankai Saboda sun ba da shaidar zur a kaina, Amma ni, zan yi tunani a kan ka'idodinka. 79 Ka sa waɗanda suke tsoronka su zo gare ni, Da waɗanda suka san umarnanka. 80 Ka sa in yi cikakkiyar biyayya da umarnanka, Sa'an nan zan tsere wa shan kunyar fāɗuwa.

Addu'ar Neman Ceto

81 Na tafke, ya Ubangiji, jira nake ka cece ni, Na dogara ga maganarka. 82 Idanuna sun gaji da zuba ido ga alkawarinka. Roƙo nake, “Sai yaushe za ka taimake ni?” 83 Na zama marar amfani kamar salkar ruwan inabi wanda aka jefar da ita, Duk da haka ban manta da umarnanka ba. 84 Har yaushe zan yi ta jira? Yaushe za ka yi wa waɗanda suke tsananta mini hukunci? 85 Masu girmankai, waɗanda ba su biyayya da dokarka, Sun haƙa wushefe don su kama ni. 86 Umarnanka duka, abin dogara ne, Mutane suna tsananta mini da ƙarairayi, Ka taimake ni! 87 Sun kusa ci wa burinsu na su kashe ni, Amma ban raina ka'idodinka ba. 88 Saboda madawwamiyar ƙaunarka, ka yi mini alheri, Domin in yi biyayya da dokokinka.

Gaskata Shari'ar Ubangiji

89 Maganarka tabbatacciya ce, ya Ubangiji, A kafe take a Sama. 90 Amincinka ya tabbata har abada, Ka kafa duniya a inda take, tana nan kuwa a wurin. 91 Dukan abubuwa suna nan har wa yau saboda umarninka, Domin su duka bayinka ne. 92 Da ba domin dokarka ita ce sanadin farin cikina ba, Da na mutu saboda hukuncin da na sha. 93 Faufau ba zan raina ka'idodinka ba, Gama saboda su ka bar ni da rai. 94 Ni naka ne, ka cece ni! Na yi ƙoƙari in yi biyayya da umarnanka. 95 Mugaye suna jira su kashe ni, Amma zan yi ta tunani a kan dokokinka. 96 Na koya, cewa ba wani abu da yake cikakke, Amma umarninka ba shi da iyaka.

Ƙaunar Shari'ar Ubangiji

97 Ga yadda nake ƙaunar dokarka! Ina ta tunani a kanta dukan yini. 98 Umarninka yana tare da ni a kowane lokaci, Ya sa ni in yi hikima fiye da dukan maƙiyana. 99 Ganewata ta fi ta dukan malamaina, Saboda ina ta tunani a kan koyarwarka. 100 Na fi tsofaffi hikima, Saboda ina biyayya da umarnanka. 101 Nakan guje wa halin mugunta Saboda ina so in yi biyayya da maganarka. 102 Ban raina koyarwarka ba Saboda kai ne ka koya mini. 103 Ɗanɗanon ka'idodinka akwai zaƙi, Har sun fi zuma zaƙi! 104 Na ƙaru da hikima daga dokokinka, Saboda haka ina ƙin dukan halin da yake ba daidai ba.

Haske daga Shari'ar Ubangiji

105 Maganarka fitila ce wadda za ta bi da ni, Haske ne kuma a kan hanyata. 106 Zan cika muhimmin alkawarina, In yi biyayya da koyarwarka mai adalci. 107 Azabaina, ya Ubangiji, suna da yawa, Ka rayar da ni kamar yadda ka alkawarta! 108 Ka karɓi addu'ata ta godiya, ya Ubangiji, Ka koya mini umarnanka. 109 Kullum a shirye nake in kasai da raina, Ban manta da umarninka ba. 110 Mugaye sun kafa mini tarko, Amma ban yi rashin biyayya da umarnanka ba. 111 Umarnanka nawa ne har abada, Su ne murnar zuciyata. 112 Na ƙudura zan yi biyayya da ka'idodinka, Har ranar mutuwata.

Akwai Lafiya ga Bin Shari'ar Ubangiji

113 Ina ƙin waɗanda ba su yi maka aminci, Amma ina ƙaunar dokarka. 114 Kai ne kake kāre ni, kake kuma kiyaye ni, Ina sa zuciya ga alkawarinka. 115 Ku rabu da ni, ku masu zunubi! Zan yi biyayya da umarnan Allahna. 116 Ka ƙarfafa ni kamar yadda ka alkawarta, zan kuwa rayu, Kada ka bar ni in kasa ci wa burina! 117 Ka riƙe ni, sai in zauna lafiya, Koyaushe zan mai da hankali ga umarnanka. 118 Ka rabu da dukan waɗanda ba su biyayya da dokokinka, Dabarunsu na yaudara banza ne. 119 Kakan yi banza da duk mai mugunta, Don haka ina ƙaunar koyarwarka. 120 Saboda kai, nake jin tsoro, Na cika da tsoro saboda shari'unka.

Biyayya da Shari'ar Ubangiji

121 Na yi abin da yake daidai mai kyau, Kada ka bar ni a hannun maƙiyana! 122 Sai ka yi alkawari za ka taimaki bawanka, Kada ka bar masu girmankai su wahalshe ni! 123 Idanuna sun gaji da duban hanyar cetonka, Ceton da ka alkawarta. 124 Ka bi da ni bisa ga tabbatacciyar ƙaunarka, Ka koya mini umarnanka. 125 Ni bawanka ne, don haka ka ba ni ganewa, Don in san koyarwarka. 126 Ya Ubangiji, lokaci ya yi da za ka yi wani abu, Saboda mutane sun ƙi yin biyayya da dokarka! 127 Ina ƙaunar umarnanka, fiye da zinariya, Fiye da zinariya tsantsa. 128 Saboda haka ina bin dukan koyarwarka, Ina kuwa ƙin dukan mugayen al'amura.

Niyyar yin Biyayya da Shari'ar

129 Koyarwarka tana da ban al'ajabi, Da zuciya ɗaya nake biyayya da su. 130 Fassarar koyarwarka takan da ba haske, Takan ba da hikima ga wanda bai ƙware ba. 131 Ina haki da baki a buɗe, Saboda marmarin da nake yi wa umarnanka. 132 Ka juyo wurina ka yi mini jinƙai, Kamar yadda kakan yi wa masu ƙaunarka. 133 Kada ka bar ni in fāɗi kamar yadda ka alkawarta, Kada ka bar mugunta ta rinjaye ni. 134 Ka cece ni daga waɗanda suke zaluntata, Domin in yi biyayya da umarnanka. 135 Ka sa mini albarka da kasancewarka tare da ni, Ka koya mini dokokinka. 136 Hawayena suna malalowa kamar kogi, Saboda jama'a ba su biyayya da shari'arka ba.

Adalcin Shari'ar Ubangiji

137 Kai mai adalci ne, ya Ubangiji, Dokokinka kuma daidai ne, 138 Ka'idodin da ka bayar kuwa dukansu masu kyau ne, Daidai ne kuwa. 139 Fushi yana cina kamar wuta, Saboda maƙiyana ba su kula da umarnanka ba. 140 Alkawarinka ba ya tashi! Bawanka yana ƙaunar alkawarinka ƙwarai! 141 Ni ba kome ba ne, rainanne ne, Amma ban ƙi kula da ka'idodinka ba. 142 Adalcinka zai tabbata har abada, Dokarka gaskiya ce koyaushe. 143 A cike nake da wahala da damuwa, Amma umarnanka suna faranta zuciyata. 144 Koyarwarka masu adalci ne har abada, Ka ba ni ganewa domin in rayu.

Addu'ar Neman Kuɓutarwa

145 Ina kira gare ka da zuciya ɗaya, Ka amsa mini, ya Ubangiji, Zan yi biyayya da umarnanka! 146 Ina kira gare ka, Ka cece ni, zan bi ka'idodinka! 147 Tun kafin fitowar rana ina kira gare ka neman taimako, Na sa zuciya ga alkawarinka. 148 Dare farai ban yi barci ba, Ina ta bimbini a kan koyarwarka. 149 Ka ji ni, ya Ubangiji, bisa ga madawwamiyar ƙaunarka, Ka kiyaye raina bisa ga alherinka! 150 Mugayen nan waɗanda suke tsananta mini sun matso kusa, Mutanen da ba su taɓa kiyaye dokarka ba. 151 Amma kana kusa da ni, ya Ubangiji, Dukan alkawaranka gaskiya ne. 152 Tuntuni na ji labarin koyarwarka, Ka sa su tabbata har abada.

Roƙo domin Ceto

153 Ka dubi wahalata, ka cece ni, Gama ban ƙi kulawa da dokarka ba. 154 Ka kāre manufata, ka kuɓutar da ni, Ka cece ni kamar yadda ka alkawarta! 155 Ba za a ceci mugaye ba, Saboda ba su yi biyayya da dokokinka ba. 156 Amma juyayinka yana da girma, ya Ubangiji, Saboda haka ka cece ni yadda ka yi niyya. 157 Maƙiyana da masu zaluntata, suna da yawa, Amma ban fasa yin biyayya da dokokinka ba. 158 Sa'ad da na dubi waɗannan maciya amana, Sai in ji ƙyama ƙwarai, Domin ba su yi biyayya da umarninka ba. 159 Ka dubi yadda nake ƙaunar koyarwarka, ya Ubangiji! Ka cece ni bisa ga madawwamiyar ƙaunarka. 160 Cibiyar dokarka gaskiya ce, Dukan ka'idodinka na adalci tabbatattu ne.

Duƙufa da Bin Dokar Ubangiji

161 Ƙarfafan mutane sun auka mini ba dalili, Amma maganarka ce nake girmamawa. 162 In farin ciki ƙwarai saboda alkawaranka, Farin cikina kamar na wanda ya sami dukiya mai yawa ne. 163 Ina ƙin ƙarairayi, ba na jin daɗinsu, Amma ina ƙaunar dokarka. 164 A kowace rana nakan gode maka sau bakwai, Saboda shari'unka masu adalci ne. 165 Waɗanda suke ƙaunar dokarka sun sami cikakken zaman lafiya, Ba wani abin da zai sa su fāɗi. 166 Ina jiranka ka cece ni, ya Ubangiji, Ina aikata abin da ka umarta. 167 Ina biyayya da ka'idodinka, Ina ƙaunarsu da zuciya ɗaya. 168 Ina biyayya da umarnanka da koyarwarka, Kana kuwa ganin dukan abin da nake yi.

Addu'ar Neman Taimako

169 Bari kukana ya kai gare ka, ya Ubangiji! Ka ganar da ni kamar yadda ka alkawarta. 170 Bari addu'ata ta zo gare ka, Ka cece ni kamar yadda ka alkawarta! 171 Zan yabe ka kullayaumin Domin ka koya mini ka'idodinka. 172 Zan raira waƙa a kan alkawarinka, Domin umarnanka a gaskiya ne. 173 Kullum a shirye kake domin ka taimake ni, Saboda ina bin umarnanka. 174 Ina sa zuciya ga cetonka ƙwarai, ya Ubangiji! Ina samun farin ciki ga dokarka. 175 Ka rayar da ni don in yabe ka, Ka sa koyarwarka su taimake ni! 176 Ina kai da kawowa kamar ɓatacciyar tunkiya, Ka zo ka neme ni, ni bawanka, Saboda ban ƙi kulawa da dokokinka ba.

Zabura 120

Addu'ar Neman Taimako

1 Sa'ad da nake shan wahala, Na yi kira ga Ubangiji, Ya kuwa amsa mini. 2 Ka cece ni, ya Ubangiji, Daga maƙaryata da masu ruɗi! 3 Ku maƙaryata, me Allah zai yi da ku? Yaya zai hukunta ku? 4 Da kibau masu tsini na mayaƙa, Da garwashin wuta zai hukunta ku! 5 Zama tare da ku mugun abu ne, kamar zama a Meshek, Ko tare da mutanen Kedar! 6 Na daɗe ƙwarai ina zama tare da mutane marasa son salama! 7 Sa'ad da nake maganar salama, Su sai su yi ta yaƙi.

Zabura 121

Ubangiji ne yake Kiyaye Ku

1 Na duba wajen duwatsu, Daga ina taimakona zai zo? 2 Taimakona zai zo daga wurin Ubangiji, Wanda ya yi sama da ƙasa. 3 Ba zai bar ka ka fāɗi ba, Makiyayinka, ba zai yi barci ba! 4 Makiyayin Isra'ila, Ba ya gyangyaɗi ko barci! 5 Ubangiji zai lura da kai, Yana kusa da kai domin ya kiyaye ka. 6 Ba za ka sha rana ba, Ko farin wata da dare. 7 Ubangiji zai kiyaye ka daga dukan hatsari, Zai sa ka zauna lafiya. 8 Zai kiyaye shigarka da fitarka, Tun daga yanzu har abada.

Zabura 122

Yabon Urushalima

1 Na yi murna sa'ad da suka ce mini, “Tashi mu tafi Haikalin Ubangiji!” 2 Ga shi kuwa, mun iso, Muna tsaye a ƙofofin Urushalima! 3 Urushalima birni ce wadda aka maido ta yadda take dā, Da kyakkyawan tsari, a shirye! 4 A nan kabilai sukan zo, Kabilan Isra'ila, Domin su yi godiya ga Ubangiji, Kamar yadda ya umarce su. 5 A nan majalisu suke, Wurin da sarki yake yi wa jama'arsa shari'a. 6 Ku yi wa Urushalima addu'ar salama! “Allah ya sa masu ƙaunarki su arzuta! 7 Salama ta samu a garukanki, Da zaman lafiya kuma a fādodinki.” 8 Saboda abokaina da aminaina, Na ce wa Urushalima, “Salama a gare ki!” 9 Saboda Haikalin Ubangiji, Allahnmu, Ina addu'a domin ki arzuta.

Zabura 123

Addu'ar Neman Jinƙai

1 Ya Ubangiji, ina zuba ido gare ka, A Sama inda kake mulki. 2 Kamar yadda bara yake dogara ga maigidansa, Baranya kuma ga uwargijiyarta, Hakanan muke zuba ido gare ka, ya Ubangiji Allahnmu, Har mu sami jinƙanka. 3 Ka yi mana jinƙai, ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, An gwada mana wulakanci matuƙa! 4 Attajirai sun daɗe suna ta yi mana ba'a, Azzalumai masu girmankai sun raina mu!

Zabura 124

Allah ne Mai Ceton Jama'arsa

1 Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu, Da me zai faru? Ba da amsa, ya Isra'ila! 2 “Da a ce Ubangiji ba ya tare da mu, A lokacin da abokan gābanmu suka auka mana, 3 Da sun haɗiye mu da rai a lokacin nan, Saboda zafin fushi da suke yi da mu, 4 Da rigyawa ta kwashe mu, Da ruwa yi ci mu, 5 Kwararowar ruwa da nutsar da mu.” 6 Sai mu gode wa Ubangiji, Da bai bar abokan gābanmu su hallaka mu ba. 7 Mun kuɓuta kamar tsuntsu daga tarkon mai farauta, Tarkon ya tsinke, mun 'yantu! 8 Taimakonmu daga wurin Ubangiji yake zuwa, Shi wanda ya yi sama da duniya.

Zabura 125

Zaman Lafiyar Jama'ar Allah

1 Waɗanda suke dogara ga Ubangiji, Suna kama da Dutsen Sihiyona, Wanda ba zai jijjigu ba, faufau. Faufau kuma ba za a kawar da shi ba. 2 Kamar yadda duwatsu suka kewaye Urushalima, Hakanan Ubangiji zai kewaye jama'arsa, Daga yanzu har abada. 3 Ba a koyaushe mugaye za su yi mulki a ƙasar jama'ar Allah ba, Idan kuwa suka yi, to, ya yiwu jama'ar Allah su yi laifi. 4 Ya Ubangiji, ka yi wa mutanen kirki alheri, Su waɗanda suke biyayya da umarnanka! 5 Amma ka hukunta waɗanda suke bin mugayen al'amuransu, Sa'ad da kake hukunta wa masu aikata mugunta! Salama ta kasance tare da Isra'ila!

Zabura 126

Godiyar Samun Ceto

1 Sa'ad da Ubangiji ya komar da mu cikin Sihiyona, Sai abin ya zama kamar mafarki! 2 Muka kece da dariya, muka raira waƙa don farin ciki, Sa'an nan sai sauran al'umma suka ambace mu, suka ce, “Ubangiji ya yi manyan al'amura masu girma, sabili da su!” 3 Hakika ya aikata manyan al'amura sabili da mu, Mun kuwa yi farin ciki ƙwarai! 4 Ya Ubangiji, ka komar da mu ƙasarmu Kamar yadda ruwan da kake yi yakan koma cikin busassun koguna, 5 Ka sa waɗanda suke kuka a lokacin da suke dashe, Su tattara albarkar kaka da farin ciki! 6 Su waɗanda suka yi kuka a sa'ad da suka fita suna ɗauke da iri, Za su komo ɗauke da albarkar kaka, Suna raira waƙa don farin ciki!

Zabura 127

Yabon Alherin Ubangiji

1 Idan ba Ubangiji ne ya gina gidan ba, Aikin magina banza ne. Idan ba Ubangiji ne ya tsare birnin ba, Ba wani amfani a sa matsara su yi tsaro. 2 Ba wani amfani a sha wahalar aiki saboda abinci, A yi asubancin tashi, a yi makarar kwanciya, Gama Ubangiji yakan hutar da waɗanda yake ƙauna. 3 'Ya'ya kyauta ne daga wurin Ubangiji, Albarka ce ta musamman. 4 'Ya'ya maza da mutum ya haifa a lokacin ƙuruciyarsa Kamar kibau suke a hannun mayaƙi. 5 Mai farin ciki ne mutumin da yake da irin waɗannan kibau da yawa! Faufau ba za a ci nasara a kansa ba, Sa'ad da ya kara da maƙiyansa a wurin shari'a.

Zabura 128

Albarkar Mai Tsoron Ubangiji

1 Mai farin ciki ne wanda yake tsoron Ubangiji, Wanda yake zamansa bisa ga umarnansa! 2 Za ka sami isasshen abin biyan bukatarka, Za ka yi farin ciki ka arzuta. 3 Matarka za ta zama kamar kurangar inabi Mai 'ya'ya a gidanka, 'Ya'yanka maza kuma kamar dashen zaitun Suna kewaye da teburinka. 4 Mutumin da yake yi wa Ubangiji biyayya, Hakika za a sa masa albarka kamar haka. 5 Ubangiji ya sa maka albarka daga Sihiyona! Ya sa ka ga Urushalima ta arzuta Dukan kwanakinka! 6 Ya kuma sa ka ka ga jikokinka! Salama ta kasance ga Isra'ila!

Zabura 129

Addu'a a kan Maƙiyan Isra'ila

1 Isra'ila, sai ka faɗi irin muguntar Da maƙiyanka suka tsananta maka da ita, Tun kana ƙarami! 2 “Maƙiyana suka tsananta mini da mugunta, Tun ina ƙarami, Amma ba su yi nasara da ni ba. 3 Suka sa mini raunuka masu zurfi a bayana, Suka mai da shi kamar gonar da aka nome. 4 Amma Ubangiji mai adalci, Ya 'yantar da ni daga bauta.” 5 Allah ya sa duk waɗanda suke ƙin Sihiyona, A yi nasara da su a kuma kore su! 6 Allah ya sa su zama kamar ciyawar da take girma a kan soraye, Ta kuwa bushe kafin ta isa yanka. 7 Ba wanda zai tattara ta, Ya ɗaure ta dami dami. 8 Duk waɗanda suke wucewa a hanya ba za su ce, “Ubangiji ya sa maka albarka!” ba, Ko su ce, “Muna sa maka albarka da sunan Ubangiji!”

Zabura 130

Sa Zuciya ga Ceton Allah

1 A cikin fid da zuciyata, Na yi kira gare ka, ya Ubangiji. 2 Ka ji kukana, ya Ubangiji, Ka kasa kunne ga kiran da nake yi na neman taimako! 3 Idan kana yin lissafin zunubanmu, Wa zai kuɓuta daga hukunci? 4 Amma kakan gafarta mana, Domin mu zama masu tsoronka. 5 Na zaƙu, ina jiran taimako daga Ubangiji, Ga maganarsa na dogara. 6 Ina jiran Ubangiji, Na zaƙu ƙwarai, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir, I, fiye da matsara waɗanda suke jiran ketowar alfijir. 7 Ya Isra'ila, ki dogara ga Ubangiji, Saboda ƙaunarsa madawwamiya ce, A koyaushe yana da nufin yin gafara. 8 Zai fanshi jama'arsa Isra'ila Daga dukan zunubansu.

Zabura 131

Addu'ar Tawali'u

1 'Ya Ubangiji, na rabu da girmankai, Na bar yin fāriya, Ba ruwana da manyan al'amura, Ba ruwana kuma da zantuttukan da suka fi ƙarfina. 2 Amma na haƙura, raina a kwance, Kamar jinjirin da yake kwance jalisan a hannun mahaifiyarsa, Haka zuciyata take kwance. 3 Ya Isra'ila, ka dogara ga Ubangiji, Daga yanzu har abada!

Zabura 132

Yabo saboda Tsattsarkan Wuri

1 Ya Ubangiji, kada ka manta da Dawuda Da dukan irin aikin da ya yi. 2 Ka tuna, ya Ubangiji, da alkawarin da ya yi, Da rantsuwar da ya yi maka, ya Maɗaukaki, Allah na Isra'ila, 3 “Ba zan tafi gida ko in kwanta ba, 4 Ba zan huta, ko in yi barci ba, 5 Sai sa'ad da na shirya wa Ubangiji wuri, Wato Haikali domin Maɗaukaki, Allah na Isra'ila.” 6 Mun ji labari akwatin alkawari yana Baitalami, Amma muka same shi a kurmi. 7 Muka ce, “Bari mu tafi Haikalin Ubangiji, Mu yi sujada a gaban kursiyinsa!” 8 Ka zo wurin hutawarka, ya Ubangiji, Tare da akwatin alkawari, Alama ce ta ikonka. 9 Ka suturta firistoci da adalci, Ka sa dukan jama'arka su yi sowa ta farin ciki! 10 Ka yi wa bawanka Dawuda alkawari, Kada ka rabu da zaɓaɓɓen sarkinka, ya Ubangiji! 11 Ka yi wa Dawuda muhimmin alkawari, Ba kuwa za ka ta da alkawarin ba. Ka ce, “Za naɗa ɗaya daga cikin 'ya'yanka maza ya zama sarki, Zai yi mulki a bayanka. 12 Idan 'ya'yanka maza za su amince da alkawarina, Da umarnan da na yi musu, 'Ya'yansu maza kuma za su bi bayanka su zama sarakuna, A dukan lokaci.” 13 Ubangiji za yaɓi Sihiyona, A can yake so ya gina Haikalinsa, ya ce, 14 “A nan zan zauna har abada. A nan kuma nake so in yi mulki. 15 Zan tanada wa Sihiyona dukan abin da take bukata a yalwace, Zan ƙosar da matalautanta da abinci. 16 Zan sa firistocinta su yi shela, Cewa ina yin ceto, Jama'ata kuma za su raira waƙa, Suna sowa don farin ciki. 17 A nan ne zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyar Dawuda Ya zama babban sarki, A nan ne kuma zan wanzar da Mulkin zaɓaɓɓen sarkina. 18 Zan sa maƙiyansa su sha kunya, Amma mulkinsa zai arzuta. Ya kuma kahu.”

Zabura 133

Yaba Ƙaunar 'Yan'uwanci

1 Abu mai kyau ne, mai daɗi kuma, Ga jama'ar Allah su zauna tare kamar 'yan'uwa! 2 Yana kama da man zaitun mai daraja, Wanda yake naso daga bisa kan Haruna zuwa gemunsa, Har zuwa wuyan riganunsa. 3 Kamar raɓa a bisa Dutsen Harmon, Wadda take zubowa a bisa tuddan Sihiyona. A can ne Ubangiji ya alkawarta albarkarsa, Rai na har abada.

Zabura 134

Kira a Yabi Allah

1 Ku zo mu yabi Ubangiji, Dukanku bayinsa, Dukanku waɗanda kuke yi masa hidima, A cikin Haikalinsa da dare. 2 Ku ɗaga hannuwanku sama, ku yi addu'a a Haikali, Ku yabi Ubangiji! 3 Ubangiji wanda ya yi sama da duniya, Ya sa muku albarka daga Sihiyona.

Zabura 135

Waƙar Yabon Girman Ubangiji

1 Ku yabi Ubangiji! Ku yabi sunansa, ku bayin Ubangiji, 2 Ku da kuke tsaye a Haikalin Ubangiji, A wuri mai tsarki na Allahnmu. 3 Ku yabi Ubangiji, domin nagari ne shi, Ku raira yabbai ga sunansa, domin shi mai alheri ne. 4 Ya zaɓar wa kansa Yakubu, Jama'ar Isra'ila kuwa tasa ce. 5 Na sani Ubangijinmu mai girma ne, Ya fi dukan alloli girma. 6 Yana aikata dukan abin da ya ga dama a Sama ko a duniya, A tekuna, da kuma zurfafan da ke ƙarƙas. 7 Yakan kawo gizagizan hadiri daga bangayen duniya, Yakan yi walƙiya domin hadura, Yakan fito da iska daga cikin taskarsa. 8 A Masar ne ya karkashe 'ya'yan fari na mutane da na dabbobi. 9 A can ne ya aikata mu'ujizai da al'ajabai, Domin ya hukunta Fir'auna da dukan hukumar ƙasarsa. 10 Ya hallakar da sauran al'umma masu yawa, Ya karkashe sarakuna masu iko, wato 11 Sihon, Sarkin Amoriyawa, da Og, Sarkin Bashan, Da dukan sarakunan Kan'ana. 12 Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa, Ya ba da ita ga Isra'ila. 13 Ya Ubangiji, kullayaumi mutane za su sani kai ne Allah, Dukan tsararraki za su tuna da kai. 14 Ubangiji zai ji juyayin mutanensa, Zai 'yantar da bayinsa. 15 Gumakan al'ummai, da azurfa da zinariya aka yi su, Hannuwan mutane ne suka siffata su. 16 Suna da bakuna, amma ba sa magana, Da idanu, amma ba sa gani. 17 Suna da kunnuwa, amma ba sa ji, Ba kuma numfashi a bakinsu. 18 Ka sa su waɗanda suka yi su, Da dukan waɗanda suke dogara gare su, Su zama kamar gumakan da suka yi! 19 Ku yabi Ubangiji, ya jama'ar Isra'ila, Ku yabe shi, ya ku firistocin Allah! 20 Ku yabi Ubangiji, ya ku Lawiyawa, Ku yabe shi, dukanku da kuke tsoronsa! 21 Ku yabi Ubangiji a Sihiyona da a Urushalima, wato a Haikalinsa. Ku yabi Ubangiji!

Zabura 136

Waƙar Godiyar Ƙaunar Allah

1 Ku gode wa Ubangiji domin shi mai alheri ne, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 2 Ku gode wa Allahn da ya fi dukan alloli girma, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 3 Ku gode wa Ubangijin dukan iyayengiji, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 4 Shi kaɗai ne yake aikata mu'ujizai masu girma, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 5 Ta wurin hikimarsa ya halicci sammai, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 6 Ya kafa duniya a bisa kan ruwa mai zurfi, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 7 Shi ne ya halicci rana da wata, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce, 8 Rana don ta yi mulkin yini, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce, 9 Wata da taurari kuwa don su yi mulkin dare, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 10 Shi ya karkashe 'ya'yan fari maza, na Masarawa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 11 Shi ya fito da jama'ar Isra'ila daga cikin Masar, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 12 Da ƙarfinsa da ikonsa ya fito da su, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 13 Shi ne ya keta Bahar Maliya biyu, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 14 Shi ya bi da jama'arsa ta cikin tekun, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 15 Shi ne ya sa ruwa ya ci Fir'auna da rundunarsa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 16 Ya bi da jama'arsa cikin hamada, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 17 Ya karkashe sarakuna masu iko, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 18 Ya karkashe shahararrun sarakuna, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 19 Ya kashe Sihon, Sarkin Amoriyawa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 20 Ya kashe Og, Sarkin Bashan, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 21 Ya ba da ƙasarsu ga jama'arsa, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 22 Ya ba da ita ga bawansa Isra'ila, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 23 Bai manta da mu sa'ad da aka yi nasara da mu ba, Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce. 24 Ya 'yantar da mu daga abokan gābanmu, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 25 Yana ba da abinci ga dukan mutane da dabbobi, Gama ƙaunarsa madawwamiya ce. 26 Ku yi wa Allah sa Sama godiya, Gama ƙaunarsa madawwamiyar ce.

Zabura 137

Kukan Isra'ilawa a Baƙuwar Ƙasa

1 A bakin kogunan Babila Muka zauna muka yi ta kuka, Sa'ad da muka tuna da Sihiyona. 2 A rassan itatuwan wardi da suke kusa da mu Muka rataye garayunmu. 3 Waɗanda suka kama mu suka sa mu mu yi waƙa, Suka ce mana, “Ku yi mana shagali Da waƙar da aka raira wa Sihiyona!” 4 Kaƙa za mu raira waƙar Ubangiji A baƙuwar ƙasa? 5 Da ma kada in ƙara iya kaɗa garaya, Idan na manta da ke, Urushalima! 6 Da ma kada in ƙara iya raira waƙa, Idan na manta da ke, Idan ban tuna ke ce Babbar abar farin ciki ba! 7 Ka tuna, ya Ubangiji, da abin da Edomawa suka yi, A ranar da aka ci Urushalima. Ka tuna da yadda suka ce, “A ragargaza ta har ƙasa!” 8 Babila, za a hallaka ki! Mai farin ciki ne shi wanda ya sāka miki Bisa ga abin da kika yi mana. 9 Mai farin ciki ne shi wanda zai kwashi jariranki Yi fyaɗa su a kan duwatsu!

Zabura 138

Godiya domin Alherin Ubangiji

1 Da zuciya ɗaya nake gode maka, ya Ubangiji, Ina raira waƙar yabonka a gaban alloli. 2 Na durƙusa a gaban tsattsarkan Haikalinka Ina yabon sunanka. Sabili da madawwamiyar ƙaunarka da amincinka, Saboda ka nuna ɗaukakarka da umarnanka. 3 Ka amsa mini sa'ad da na yi kira gare ka, Da ƙarfinka ka ƙarfafa ni. 4 Dukan sarakunan duniyar nan za su yabe ka, ya Ubangiji, Gama sun riga sun ji alkawaranka. 5 Za su raira waƙa a kan abin da Ubangiji ya yi, Za su raira waƙa kuma a kan ɗaukakarsa mai girma. 6 Ko da yake Ubangiji yana can Sama, Duk da haka yana kulawa da masu kaɗaici. Masu girmankai kuwa ba za su iya ɓoye kansu daga gare shi ba. 7 Ko lokacin da nake tsakiyar wahala, Za ka kiyaye ni lafiya, Ka yi gāba da abokan gābana, waɗanda suka husata, Za ka kuwa cece ni da ikonka. 8 Za ka aikata kowane abu da ka alkawarta mini, Ya Ubangiji, ƙaunarka madawwamiya ce har abada. Ka cikasa aikin da ka fara.

Zabura 139

Cikakken Sanin Allah da Kulawarsa

1 Ya Ubangiji, ka jarraba ni, ka san ni. 2 Ka sa dukan abin da nake yi, Tun daga can nesa ka gane dukan tunanina. 3 Kana ganina, ko ina aiki, ko ina hutawa, Ka san dukan ayyukana. 4 Tun kafin in yi magana Ka riga ka san abin da zan faɗa. 5 Kana kewaye da ni a kowane sashe, Ka kiyaye ni da ikonka. 6 Yadda ka san ni ya fi ƙarfin magana, Ya yi mini zurfi, ya fi ƙarfin ganewata. 7 Ina zan tafi in tsere wa Ruhunka? Ina zan gudu in tsere maka? 8 Idan na hau cikin samaniya kana can, In na kwanta a lahira kana can, 9 In na tashi sama, na tafi, na wuce gabas, Ko kuma na zauna a can yamma da nisa, 10 Kana can domin ka bi da ni, Kana can domin ka taimake ni. 11 Da na iya roƙon duhu ya ɓoye ni, Ko haske da yake kewaye da ni Ya zama dare, 12 Amma har duhun ma, ba duhu ba ne a gare ka, Dare kuwa haskensa kamar na rana ne. Duhu da haske, duk ɗaya ne gare ka. 13 Kai ne ka halicci kowace gaɓa ta jikina, Kai ne ka harhaɗa ni a cikin mahaifiyata. 14 Ina yabonka gama kai abin tsoro ne, Dukan abin da ka yi sabo ne, mai banmamaki. Da zuciya ɗaya na san haka ne. 15 Ka ga lokacin da ƙasusuwana suke siffatuwa, Sa'ad da kuma ake harhaɗa su a hankali A cikin mahaifiyata, Lokacin da nake girma a asirce. 16 Ka gan ni kafin a haife ni. Ka ƙididdige kwanakin da ka ƙaddara mini, Duka an rubuta su a littafinka, Tun kafin faruwar ko wannensu. 17 Ya Allah, tunaninka suna da wuyar ganewa a gare ni, Ba su da iyaka! 18 In na ƙirga su, za su fi tsabar yashi, Sa'ad da na farka, har yanzu ina tare da kai. 19 Ya Allah, da yadda nake so ne, da sai ka karkashe mugaye! 'Yan ta da zaune tsaye kuma sai su rabu da ni! 20 Suna ambaton mugayen abubuwa a kanka, Suna faɗar mugayen abubuwa gāba da sunanka. 21 Ya Ubangiji, ga yadda nake ƙin waɗanda suke ƙinka, Da yadda nake raina waɗanda suke tayar maka! 22 Ƙiyayyar da nake yi musu ta kai intaha, Na ɗauke su, su abokan gābana ne. 23 Jarraba ni, ya Allah, ka san tunanina, Gwada ni, ka gane damuwata. 24 Ka bincike, ko akwai wani rashin gaskiya a gare ni, Ka bi da ni a madawwamiyar hanya.

Zabura 140

Addu'ar Neman Tsari daga Mugaye

1 Ka cece ni daga mugaye, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga mutane masu hargitsi. 2 Kullum suna shirya mugunta, Kullum suna kawo tashin hankali. 3 Harsunansu kamar macizai masu zafin dafi, Kalmominsu kuwa kamar dafin gamsheƙa ne. 4 Ka tsare ni daga ikon masu mugunta, ya Ubangiji, Ka kiyaye ni daga masu tashin hankali, Waɗanda suke shirya fāɗuwata. 5 Masu girmankai sun kafa mini tarko, Sun shimfiɗa ragar igiya, Sun kuma kakkafa tarkuna a hanya don su kama ni. 6 Na ce wa Ubangiji, “Kai ne Allahna. Ka ji kukana ne neman taimako, ya Ubangiji! 7 Ya Ubangiji, Allahna, Mai Cetona, mai ƙarfi, Kā kiyaye ni cikin yaƙi. 8 Ya Ubangiji, kada ka biya wa mugaye burinsu, Kada ka bar mugayen dabaru su yi nasara! 9 “Kada ka bar maƙiyana su sami nasara, Ka sa kashedin da suke yi mini ya koma kansu. 10 Ka sa garwashin wuta ya zubo a kansu, Ka sa a jefa su a rami, kada su ƙara fita. 11 Ka sa waɗanda suke saran waɗansu a ƙaryace, Kada su yi nasara. Ka sa mugunta ta hallaka mutumin da yake ta da zaune tsaye.” 12 Na sani kai, ya Ubangiji, kana kāre matsalar talakawa, Da hakkin matalauta. 13 Hakika adalai za su yabe ka, Za su zauna a gabanka.

Zabura 141

Addu'ar Maraice ta Neman Keɓewa daga Mugunta

1 Ina kira gare ka, ya Ubangiji, Ka taimake ni yanzu! Ka saurare ni sa'ad da na kira gare ka. 2 Ka karɓi addu'ata kamar turaren ƙonawa, Ka karɓi ɗaga hannuwa sama da na yi kamar hadayar maraice. 3 Ya Ubangiji, ka sa a yi tsaron bakina, Ka sa mai tsaro a leɓunana. 4 Ka tsare ni daga son yin mugunta, Ko kuma in haɗa kai da mugaye cikin muguntarsu, Ka sa kada in taɓa yin tarayya da su a bukukuwansu! 5 Nagarin mutum ya iya hukunta ni, ya tsauta mini da alheri, Zai zamar mini kamar an shafe kaina da mai, Domin kullayaumi ina addu'a gāba da mugayen ayyuka. 6 Mutane za su yarda, cewa maganata gaskiya ce, Sa'ad da aka jefo da masu mulkinsu ƙasa, daga ƙwanƙolin dutse, 7 Kamar itacen da aka faskare, aka daddatse, Haka aka watsar da ƙasusuwansu a gefen kabari. 8 Amma ni, ya Ubangiji Allah, da nake dogara a gare ka, Ina neman kiyayewarka, Kada ka bar ni in hallaka! 9 Ka kiyaye ni daga tarkunan da suka kafa mini, Daga ashibtar masu aikata mugunta. 10 Ka sa mugaye su fāɗa cikin tarkunansu, Ni kuwa in zo in wuce lafiya.

Zabura 142

Addu'ar Neman Taimako

1 Ina kira ga Ubangiji don neman taimako, Ina roƙonsa. 2 Na kawo masa dukan koke-kokena, Na faɗa masa dukan wahalaina. 3 Sa'ad da na yi niyyar fid da zuciya, Ya san abin da zan yi. A kan hanyar da zan bi Maƙiyana sun kafa mini tarko a ɓoye. 4 Na duba kewaye da ni, sai na ga ba ni da wanda zai taimake ni, Ba wanda zai kiyaye ni, Ba kuwa wanda ya kula da ni. 5 Ya Ubangiji, na kawo kuka gare ka na neman taimako, Ya Ubangiji, kai ne mai kiyaye ni, Kai kaɗai nake so a rayuwata duka. 6 Ka kasa kunne ga kukana na neman taimako, Gama na nutsa cikin fid da zuciya. Ka cece ni daga maƙiyana Waɗanda suka fi ƙarfina. 7 Ka cece ni daga cikin wahalata, Sa'an nan zan yabe ka cikin taron jama'arka, Domin ka yi mini alheri.

Zabura 143

Addu'ar Neman Ceto da Kiyayewa

1 Ya Ubangiji ka ji addu'ata, Ka kasa kunne ga roƙona! Kai adali ne mai aminci, Don haka ka amsa mini! 2 Ni bawanka, kada ka gabatar da ni a gaban shari'a, Gama ba wanda ba shi da laifi a gare ka. 3 Maƙiyina ya tsananta mini, Ya kore ni fata-fata. Ya sa ni a kurkuku mai duhu, Ina kama da waɗanda suka daɗe da mutuwa, 4 Don haka ina niyya in fid da zuciya, Ina cikin damuwa mai zurfi. 5 Na tuna kwanakin baya, Na tuna da dukan abin da ka yi, Na tuna da dukan ayyukanka. 6 Na ɗaga hannuwana sama, ina addu'a gare ka, Kamar busasshiyar ƙasa, raina yana jin ƙishinka. 7 Yanzu ka amsa mini, ya Ubangiji! Na fid da zuciya duka! Kada ka ɓuya mini, Don kada in zama cikin waɗanda suke gangarawa zuwa lahira. 8 A gare ka nake dogara, Da safe ka tuna mini da madawwamiyar ƙaunarka. Addu'ata ta hau zuwa gare ka, Ka nuna mini hanyar da zan bi. 9 Na tafi wurinka don ka kiyaye ni, ya Ubangiji, Ka cece ni daga maƙiyana. 10 Kai ne Allahna, Ka koya mini in aikata nufinka. Ka sa in sami alherin Ruhunka. Ka bi da ni a hanyar lafiya. 11 Ka cece ni, ya Ubangiji, kamar yadda ka alkawarta. Saboda alherinka ka tsamo ni daga wahalaina! 12 Saboda ƙaunar da kake yi mini, Ka kashe maƙiyana. Ka hallakar da dukan waɗanda suke zaluntata. Gama ni bawanka ne.

Zabura 144

Addu'ar Neman Ceto da Wadata

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji, mai kiyaye ni, Ya hore ni don yaƙi, Ya kuwa shirya ni don yaƙi. 2 Shi yake kiyaye ni, Shi yake kāre ni, Shi ne mafakata da Mai Cetona, Wanda nake dogara gare shi Don samun zaman lafiya. Shi ne ya ɗora ni a kan al'ummai. 3 Ya Ubangiji wane ne mutum, har da kake lura da shi? Wane ne ɗan adam kurum, har da kake kulawa da shi? 4 Shi kamar hucin iska yake, Kwanakinsa kuwa kamar inuwa mai wucewa ne. 5 Ya Ubangiji, ka kware sararin sama, ka sauko, Ka taɓa duwatsu, don su tuƙaƙo da hayaƙi. 6 Ka aiko da walƙiyar tsawa ta warwatsa maƙiyanka, Ka harba kibanka, ka sa su sheƙa a guje! 7 Ka sunkuyo daga Sama, Ka tsamo ni daga cikin ruwa mai zurfi, ka cece ni, Ka cece ni daga ikon baƙi, 8 Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya. 9 Zan raira maka sabuwar waƙa, ya Allah, Zan kaɗa garaya in raira maka waƙa. 10 Ka ba sarakuna nasara, Ka kuma ceci bawanka Dawuda. 11 Ka cece ni daga mugayen abokan gābana, Ka ƙwato ni daga ikon baƙi, Waɗanda ba su taɓa faɗar gaskiya ba, Sukan yi rantsuwar ƙarya. 12 Ka sa 'ya'yanmu maza waɗanda suke cikin samartaka, Su zama kamar itatuwan da suke girma da ƙarfi. Ka sa 'ya'yanmu mata Su zama kamar al'amudai, Waɗanda suke adanta kusurwoyin fāda. 13 Ka sa rumbunanmu su cika Da kowane irin amfanin gona. Ka sa tumakin da yake cikin saurukanmu Su hayayyafa dubu dubu har sau goma, 14 Ka sa shanunmu su hayayyafa, Kada su yi ɓari ko su ɓace. Ka sa kada a ji kukan damuwa a kan titunanmu! 15 Mai farin ciki ce al'ummar Da abin nan da aka faɗa ya zama gaskiya a gare ta. Masu farin ciki ne jama'ar da Allahnsu shi ne Ubangiji!

Zabura 145

Waƙar Yabon Allah domin Alherinsa da Ikonsa

1 Zan yi shelar girmanka, ya Allahna, Sarkina, Zan yi maka godiya har abada abadin. 2 Kowace rana zan yi maka godiya, Zan yabe ka har abada abadin. 3 Ubangiji mai girma ne, dole ne a fifita yabonsa, Girmansa ya fi ƙarfin ganewa. 4 Za a yabi abin da ka aikata daga tsara zuwa tsara, Za su yi shelar manya manyan ayyukanka. 5 Mutane za su yi magana a kan darajarka da ɗaukakarka, Ni kuwa zan yi ta tunani a kan ayyukanka masu banmamaki. 6 Mutane za su yi magana a kan manya manyan ayyukanka, Ni kuwa zan yi shelar girmanka. 7 Za su ba da labarin girmanka duka, Su kuma raira waƙa a kan alherinka. 8 Ubangiji mai ƙauna ne, mai jinƙai, mai jinkirin fushi, Cike da madawwamiyar ƙauna. 9 Shi mai alheri ne ga kowa, Yana juyayin dukan abin da ya halitta. 10 Ya Ubangiji, talikanka duka za su yabe ka, Jama'arka kuma za su yi maka godiya! 11 Za su yi maganar darajar mulkinka, Su ba da labarin ikonka, 12 Domin haka dukan mutane za su san manyan ayyukanka, Da kuma darajar ɗaukakar mulkinka. 13 Mulkinka, madawwamin mulki ne, Sarki ne kai har abada. 14 Ubangiji, yakan taimaki dukan waɗanda suke shan wahala, Yakan ta da waɗanda aka wulakanta. 15 Dukan masu rai suna sa zuciya gare shi, Yana ba su abinci a lokacin da suke bukata, 16 Yana kuwa ba su isasshe, Yakan biya bukatarsu duka. 17 Ubangiji mai adalci ne a abin da yake yi duka, Mai jinƙai ne a ayyukansa duka. 18 Yana kusa da dukan waɗanda suke kira gare shi, Waɗanda suke kiransa da zuciya ɗaya. 19 Yakan biya bukatar dukan waɗanda suke tsoronsa, Yakan ji kukansu, ya cece su. 20 Yakan kiyaye dukan waɗanda suke ƙaunarsa, Amma zai hallaka mugaye duka. 21 A kullum zan yabi Ubangiji, Bari talikai duka su yabi sunansa mai tsarki har abada!

Zabura 146

Yabon Allah Mai Ceto

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ka yabi Ubanigji, ya raina! 2 Zan yabe shi muddin raina. Zan raira waƙa ga Allahna dukan kwanakina. 3 Kada ka dogara ga shugabanni, Ko kowane mutum da ba zai iya cetonka ba. 4 Sa'ad da suka mutu sai su koma turɓaya, A wannan rana dukan shirye-shiryensu sun ƙare. 5 Mai farin ciki ne mutumin da Allah na Yakubu ne yake taimakonsa, Yana kuma dogara ga Ubangiji Allahnsa, 6 Wanda ya halicci sama, da duniya, da teku, Da dukan abin da yake cikinsu. Kullum yakan cika alkawaransa. 7 A yanke shari'arsa yakan ba wanda aka zalunta gaskiya. Yana ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan kuɓutar da ɗaurarru. 8 Yakan ba makafi ganin gari. Yakan ɗaukaka waɗanda aka wulakanta. Yana ƙaunar jama'arsa, adalai. 9 Yakan kiyaye baƙi waɗanda suke zaune a ƙasar. Yakan taimaki gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu. Yakan lalatar da dabarun mugaye. 10 Ubangiji Sarki ne har abada! Ya Sihiyona, Allahnki zai yi mulki har dukan zamanai! Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 147

Yabon Alherin Allah a kan Urushalima

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Abu mai kyau ne mu yabi Allahnmu, Abu mai daɗi ne, daidai ne kuma, a yabe shi. 2 Ubangiji yana rayar da Urushalima, Yana komo da waɗanda aka kai su baƙunci a wata ƙasa. 3 Yakan warkar da masu karyayyiyar zuciya, Yakan ɗaure raunukansu. 4 Ya ƙididdige yawan taurari, Yakan kira kowanne da sunansa. 5 Ubangijinmu mai girma ne, Mai Iko Dukka, Saninsa ya fi gaban aunawa. 6 Yakan ɗaukaka masu tawali'u, Amma yakan ragargaza mugaye har ƙasa. 7 Ku raira waƙar yabo ga Ubangiji, Ku yabi Allah da garaya. 8 Ya shimfiɗa gajimare a sararin al'arshi. Ya tanada wa duniya ruwan sama, Ya sa ciyayi su tsiro a kan tuddai. 9 Yakan ba dabbobi abincinsu, Yakan ciyar da 'ya'yan hankaki sa'ad da suka yi kuka gare shi. 10 Ba ya jin daɗin ƙarfafan dawakai, Ba ya murna da jarumawan mayaƙa. 11 Amma yana jin daɗin waɗanda suke tsoronsa, Yana jin daɗin waɗanda suke dogara da madawwamiyar ƙaunarsa. 12 Ya Urushalima, ki yabi Ubangiji, Ya Sihiyona, ki yabi Allahnki. 13 Shi yake riƙe da ƙofofinki da ƙarfi, Yakan sa wa jama'arki albarka. 14 Yakan kiyaye kan iyakar ƙasarki lafiya, Yakan kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau. 15 Yakan ba da umarni, Nan da nan umarnin yakan iso duniya. 16 Yakan aiko da dusar ƙanƙara mai kauri kamar ulu, Ya watsa jaura kamar ƙura. 17 Yakan aiko da ƙanƙara kamar duwatsu, Ba wanda yake iya jurewa da sanyin da yakan aiko! 18 Sa'an nan yakan ba da umarni, Ƙanƙara kuwa ta narke, Yakan aiko da iska, ruwa kuwa yakan gudu. 19 Yana ba Yakubu saƙonsa, Koyarwarsa da dokokinsa kuma ga Isra'ila. 20 Bai yi wa sauran al'umma wannan ba, Domin ba su san dokokinsa ba. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 148

Bari dukan Halittar Allah su yi Yabonsa

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji daga sama, Ku da kuke zaune a tuddan sama. 2 Ku yabe shi dukanku mala'ikunsa, Ku yabe shi, ku dukan rundunansa na sama! 3 Ku yabe shi, ku rana da wata, Ku yabe shi, ku taurari masu haskakawa! 4 Ku yabe shi, ku sammai mafi tsayi duka! Ku yabe shi, ku ruwayen da kuke bisa sararin sama! 5 Bari su duka su yabi sunan Ubangiji! Ya umarta, sai suka kasance. 6 Ta wurin umarninsa aka kafa su A wurarensu har abada, Ba su kuwa da ikon ƙi. 7 Ku yabi Ubangiji daga duniya, Ku yabi Ubangiji, ku dodanin ruwa da dukan zurfafan teku. 8 Ku yabe shi, ku walƙiya, da ƙanƙara, da dusar ƙanƙara, Da gizagizai, da ƙarfafan iska waɗanda suke biyayya da umarnansa! 9 Ku yabe shi, ku tuddai da duwatsu, Da itatuwa 'ya'ya da kurama. 10 Ku yabe shi dukanku dabbobi, na gida da na jeji, Masu rarrafe da tsuntsaye! 11 Ku yabe shi, ku sarakuna da dukan kabilai, Ku yabe shi, ku shugabanni da dukan hukumomi. 12 Ku yabe shi ku samari da 'yan mata! Ku yabe shi, ku tsoffafi da yara! 13 Bari dukansu su yabi sunan Ubangiji, Sunansa ya fi dukan sauran sunaye girma, Ɗaukakarsa kuwa tana bisa duniya da samaniya! 14 Ya sa al'ummarsa ta yi ƙarfi, Domin dukan jama'arsa su yabe shi Jama'arsa Isra'ila, wadda yake ƙauna ƙwarai! Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 149

Bari Isra'ilawa su Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji Ku yabe shi cikin taron jama'arsa masu aminci! 2 Ki yi murna, ke Isra'ila, sabili da Mahaliccinki, Ku yi farin ciki, ku jama'ar Sihiyona, sabili da Sarkinku! 3 Ku yabi sunansa, kuna taka rawa, Ku kaɗa bandiri da garayu, kuna yabonsa. 4 Ubangiji yana jin daɗin jama'arsa, Yakan girmama mai tawali'u ya sa ya ci nasara. 5 Bari jama'ar Allah su yi farin ciki saboda cin nasararsu, Su raira waƙa don farin ciki. 6 Bari su yi sowa da ƙarfi Sa'ad da suke yabon Allah, da takubansu masu kaifi. 7 Don su ci nasara bisa al'ummai, Su kuma hukunta wa jama'a, 8 Su ɗaure sarakunansu da sarƙoƙi, Su ɗaure shugabanninsu da sarƙoƙin baƙin ƙarfe, 9 Su hukunta wa al'ummai, kamar yadda Allah ya umarta. Wannan shi ne cin nasarar jama'ar Allah! Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Zabura 150

Ku Yabi Ubangiji

1 Yabo ya tabbata ga Ubangiji! Ku yabi Allah a cikin Haikalinsa! Ku yabi ƙarfinsa a sama! 2 Ku yabe shi saboda manyan abubuwa Waɗanda ya aikata! Ku yabi mafificin girmansa! 3 Ku yabe shi da kakaki! Ku yabe shi da garayu da molaye! 4 Ku yabe shi da bandiri kuna taka rawa! Ku yabe shi da garayu da sarewa! 5 Ku yabe shi da kuge! Ku yabe shi da kuge masu amo! 6 Ku yabi Ubangiji dukanku rayayyun talikai. Yabo ya tabbata ga Ubangiji!

Karin Magana 1

Amfanin Karin Magana

1 Karin maganar Sulemanu, ɗan Dawuda, Sarkin Isra'ila. 2 Ga Karin magana da za su taimake ka ka rarrabe da hikima, da kyakkyawar shawara, da fahimtar ma'anar zurfafan karin magana, 3 da yadda za ka karɓi koyarwa ta hanyar hikima, da adalci, da gaskiya, da sanin abin da yake daidai. 4 Sukan sa marar sani ya zama masani, sukan koya wa samari yadda za su zama masu amfani. 5 Waɗannan karin magana sukan ƙara wa masu ilimi hikima, sukan zama jagora ga masana, 6 don su fahimci ɓoyayyiyar ma'anar da take cikin karin magana, da mawuyatan al'amura waɗanda masu hikima suka ƙago. 7 In kana so ilimi dole ne ka fara da tsoron Ubangiji. Jahilai ba su san darajar hikima ba, sun kuwa ƙi su koya.

Gargaɗi da Faɗaka

8 Ɗana, ka kasa kunne ga koyarwar mahaifinka, ka mai da hankali ga abin da mahaifiyarka take faɗa. 9 Koyarwarsu za ta inganta halinka, ta zama kayan ado kamar kyakkyawan rawani a kanka, ko kyakkyawan abin wuya a wuyanka, don su ƙara maka kyau. 10 Ɗana sa'ad da masu zunubi suka jarabce ka, kada ka yarda 11 in suka ce maka, “Zo mu tafi mu nemi wani mutum mu kashe, mu je, mu fāɗa wa marasa laifi mu ji daɗi! 12 Ba mu damu da ransu da lafiyarsu ba, mu dai mu tafi mu kashe su, mu hallaka su ɗungum. 13 Za mu sami dukiya iri iri, mu cika gidajenmu da ganima! 14 Ka zo ka haɗa kai da mu, dukanmu kuwa za mu raba abin da muka sato.” 15 Ɗana, kada ka gama kanka da irin waɗannan mutane, ka yi nesa da su. 16 Ba su kasalar aikata mugunta, kullum a shirye suke su yi kisankai. 17 Ba shi da amfani a kafa tarko a idon tsuntsun da ake so a kama. 18 Amma waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko. Ba za su kama kome ba, sai rayukansu. 19 Yin fashi yakan zama sanadin mutuwar ɗan fashi a koyaushe. Wannan shi ne abin da yakan sami kowane mutum da ya kama sana'ar sata.

Hikima tana Kira

20 Ku kasa kunne! Hikima tana kira a tituna da a kasuwoyi. 21 Tana kira da ƙarfi a ƙofofin birni, a duk inda mutane suke tattaruwa. 22 Ta ce, “Wawayen mutane! Har yaushe za ku yi ta kasancewa haka? Har yaushe za ku daina jin daɗin yi wa mai ilimi ba'a? Faufau ba za ku taɓa koya ba? 23 Ku kasa kunne lokacin da nake tsauta muku, zan ba ku shawara mai kyau, mu yi tarayya cikin ilimina. 24 Ina ta kiranku ina gayyatarku ku zo, amma ba ku kula ba, ba ku mai da hankali gare ni ba. 25 Kun ƙi bin shawarwarina duka, ba ku yarda in gyara kuskurenku ba. 26 Saboda haka, lokacin da kuke shan wahala, zan yi muku dariya. Zan yi muku ba'a lokacin da razana ta auka muku, 27 sa'ad da ta zo muku kamar hadiri mai ƙaƙƙarfar iska mai wahalarwa, sa'ad da kuke shan azaba da damuwa. 28 Sa'an nan za ku kira gare ni, amma ba za ku same ni ba. Za ku neme ni a ko'ina, amma ba za ku same ni ba. 29 Domin ba ku taɓa sanin amfanin ilimi ba, kun ƙi tsoron Ubangiji a kullum. 30 Ba ku taɓa yarda da shawarata ba, ko ku yarda in gyara kuskurenku. 31 Saboda haka za ku karɓi sakayyarku, ayyukanku za su cuce ku. 32 Marasa sani sukan mutu saboda ba su yarda da hikima ba. Wawaye kuwa sukan hallaka saboda rashin kulawarsu. 33 Amma duk wanda ya kasa kunne gare ni, zai zauna lafiya. Ba abin da zai same shi, ba abin da zai tsorata shi.”

Karin Magana 2

Sakamakon Neman Hikima

1 Ɗana, ka koyi abin da nake koya maka, sam kada ka manta da abin da na faɗa maka ka yi. 2 Ka kasa kunne ga abin da yake na hikima, ka yi ƙoƙari ka fahimce shi. 3 I, ka roƙi ilimi da tsinkaya. 4 Ka nema da iyakar ƙoƙarinka kamar yadda za ka nemi azurfa, ko kowace irin ɓoyayyiyar dukiya. 5 Idan ka yi za ka san abin da ake nufi da tsoron Ubangiji. Za ka yi nasara a kan koyon sanin Allah. 6 Ubangiji ne yake ba da hikima. Ilimi da fahimi kuwa suna cikin kalmominsa. 7 Shi yake tanada wa adalai taimako da kiyayewa, wato mutane masu aminci. 8 Yakan kiyaye waɗanda suke lura da kyau, ya kiyaye waɗanda suke dogara gare shi. 9 Idan ka kasa kunne gare ni za ka san abin da yake daidai, da abin da yake gaskiya, da abin da yake na kirki. Za ka san abin da za ka yi. 10 Za ka zama mai hikima, iliminka zai faranta maka rai. 11 Tsinkayarka da fahiminka za su tsare ka. 12 Za su hana ka aikata mugayen ayyuka, za su nisantar da kai daga mutane masu ta da hargitsi da irin maganganunsu, 13 mutane waɗanda suka bar zaman adalci don su zauna cikin duhun zunubi, 14 waɗanda suke jin daɗin yin laifi, suna nishaɗi cikin mugunta. 15 Ba za a dogara da su ba, ba kuwa za a iya amincewa da su ba. 16 Za a nisantar da kai daga mazinaciya, wadda take ƙoƙari ta lalatar da kai da daɗin bakinta, 17 marar aminci ga mijinta, wadda ta manta da tsarkakan alkawaran da ta ɗauka. 18 Idan ka tafi gidanta ka kama hanyar mutuwa. Tafiya can kama hanyar zuwa lahira ne. 19 Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa. Ba zai ƙara komowa ga hanyar rai ba. 20 Saboda haka dole ka bi hanyar da mutanen kirki suka bi, ka bi gurbin adalai. 21 Mutane adalai, masu kamewa, su ne za su zauna ƙasarmu. 22 Amma Allah zai fizge mugaye daga ƙasar, ya kuma tumɓuke masu zunubi kamar yadda ake tumɓuke shuke-shuke daga ƙasa.

Karin Magana 3

Gargaɗin yin Biyayya

1 Ɗana kada ka manta da abin da na koya maka. Kullum ka tuna da abin da na faɗa maka ka yi. 2 Koyarwata za ta ba ka tsawon rai da wadata. 3 Kada ka yarda ka rabu da biyayya da aminci, ka ɗaura su a wuyanka, ka rubuta su kuma a zuciyarka. 4 Idan ka yi wannan kuwa, Allah zai yi murna da kai. Za ka yi nasara cikin hulɗar da kake yi da mutane. 5 Ka dogara ga Ubangiji da zuciya ɗaya, kada ka dogara ga abin da kake tsammani ka sani. 6 A cikin dukan abin da kake yi, ka tuna da Ubangiji, shi kuma zai nuna maka hanyar da yake daidai. 7 Sam, kada ka yarda ka ɗauki kanka kai mai hikima ne fiye da yadda kake, kai dai ka ji tsoron Ubangiji, ka rabu da aikata mugunta. 8 Idan ka kiyaye wannan, zai zama maka kamar magani mai kyau, ya warkar da raunukanka, ya kuma sawwaƙe maka azabar da kake sha. 9 Ka girmama Ubangiji ta wurin miƙa masa hadaya daga mafi kyau na amfanin gonarka. 10 Idan ka yi haka rumbunanka za su cika da hatsi. Za ka sami ruwan inabi mai yawa, har ka rasa wurin da za ka zuba shi duka. 11 Ɗana, sa'ad da Ubangiji ya tsauta maka ka mai da hankali sosai, ka kuma yarda da gargaɗinsa. 12 Ubangiji yana tsauta wa waɗanda yake ƙauna. Kamar yadda mahaifi yakan tsauta wa ɗan da yake fāriya da shi. 13 Mai farin ciki ne mutumin da ya zama mai hikima, ya kuma sami fahimi. 14 Yana da riba mai yawan gaske fiye da ta azurfa, tamaninta a gare ka ya fi na zinariya. 15 Tamanin hikima ya fi na lu'ulu'ai, ya kuma fi kowane irin abin da kake so tamani. 16 Hikima takan tsawanta ranka, ta kuma ba ka dukiya da daraja. 17 Hikima takan sa ka ji daɗin zama, ta kuma bi da kai lafiya a zamanka. 18 Masu farin ciki ne waɗanda suka sami hikima, hikima za ta ba su rai kamar yadda itace yakan ba da 'ya'ya. 19 Ubangiji ya halicci duniya ta wurin hikimarsa, Ya shimfiɗa sararin sama a inda yake ta wurin saninsa. 20 Hikimarsa ta sa ruwan koguna ya yi gudu, Gizagizai kuwa su zubo da ruwa bisa duniya. 21 Ɗana ka riƙe hikimarka da basirarka. Ko kusa kada ka bari su rabu da kai. 22 Za su tanada maka rai, rai mai daɗi da farin ciki. 23 Za ka bi hanyarka lafiya lau, ba ko tuntuɓe. 24 Ba za ka ji tsoro, sa'ad da kake kwance a gadonka ba, za ka yi ta sharar barci a dukan dare. 25 Ba za ka damu da masifar da za ta auko farat ɗaya ba, irin wadda takan auka wa mugaye kamar hadiri. 26 Ubangiji zai kiyaye ka. Ba zai bari ka fāɗa cikin tarko ba. 27 Ka yi wa masu bukata alheri a duk lokacin da kake iyawa. 28 Sam, kada ka ce wa maƙwabcinka ya dakata sai gobe, idan dai kana iya taimakonsa yanzu. 29 Kada ka shirya kome da zai cuci maƙwabcinka, gama yana zaune kusa da kai, yana kuwa amincewa da kai. 30 Kada ka yi jayayya ba dalili da wanda bai taɓa cutarka ba. 31 Kada ka ji kishin masu ta da zaune tsaye, ko ka yi sha'awar aikata ayyukansu, 32 gama Ubangiji yana ƙin mutanen da suke aikata mugunta, amma yakan rungumi adalai ya amince da su. 33 Ubangiji yakan la'antar da gidajen masu mugunta, amma yakan sa wa gidajen adalai albarka. 34 Ba ruwansa da masu girmankai, amma masu tawali'u sukan sami tagomashi a wurinsa. 35 Mutane masu hikima za su sami kyakkyawan suna, amma wawaye sukan ƙara wa kansu shan kunya.

Karin Magana 4

Fa'idodin Hikima

1 'Ya'yana ku kasa kunne ga koyarwar mahaifinku. Ku mai da hankali, za ku zama haziƙai. 2 Abin da nake koya muku, abu mai kyau ne, saboda haka ku tuna da shi duka. 3 Sa'ad da nake ɗan yaro tilo a wurin iyayena, 4 mahaifina yakan koya mini, yakan ce, “Ka tuna da abin da nake faɗa maka, kada ka manta. Ka yi abin da na faɗa maka za ka rayu. 5 Ka nemi hikima da basira! Kada ka manta ko ka ƙyale abin da na faɗa. 6 Kada ka rabu da hikima, gama za ta kiyaye ka, ka ƙaunace ta, za ta kiyaye lafiyarka. 7 Samun hikima shi ne mafificin abin da za ka yi. Kome za ka samu dai, ka sami basira. 8 Ka ƙaunaci hikima, za ta girmama ka. Ka rungume ta, za ta kawo maka daraja. 9 Za ta zamar maka rawanin daraja.” 10 Ɗana, ka kasa kunne gare ni. Ka ɗauki abin da nake faɗa maka, muhimmin abu ne, za ka yi tsawon rai. 11 Gama na koya maka hikima da hanyar zama mai kyau. 12 Idan ka yi tafiya da hikima ba abin da zai tsare maka hanya, sa'ad da kake gudu ba za ka yi tuntuɓe ba. 13 Kullum ka tuna da abin da ka koya, iliminka shi ne ranka, ka lura da shi da kyau. 14 Kada ka tafi inda mugaye suke tafiya, kada ka bi gurbin mugaye. 15 Kada ka yi mugunta! Ka nisance ta! Ka ƙi ta, yi tafiyarka. 16 Mugaye ba su iya yin barci, sai sun aikata ɓarna. Ba su barci sai sun cuci wani. 17 Mugunta da ta'adi kamar ci da sha suke a gare su. 18 Hanyar da adalai suke bi kamar fitowar rana ce, sai ta yi ta ƙara haske, har ta take tsaka. 19 Hanyar mugaye kuwa duhu ne baƙi ƙirin, kamar duhun dare. Sukan fāɗi, amma ba su san abin da ya sa suka yi tuntuɓe ba. 20 Ɗana, ka kula da abin da nake faɗa. Ka kasa kunne ga kalmomina. 21 Kada ka kuskura su rabu da kai, ka tuna da su, ka ƙaunace su. 22 Za su ba da rai da lafiya ga dukan wanda ya fahimce su. 23 Tunane-tunanenka mafarin rai ne kansa, ka kiyaye su abin mallakarka ne mafi daraja. 24 Kada ka faɗi kowane abu da yake ba na gaskiya ba, kada wani abu ya haɗa ka da ƙarya, ko maganganun ruɗawa. 25 Ka duba gaba sosai gabanka gaɗi, ba tsoro. 26 Ka tabbata ka san abin da kake yi, duk abin da kake yi kuma zai zama daidai. 27 Ka rabu da mugunta ka yi tafiyarka sosai, kada ka kauce ko da taki ɗaya daga hanyar da take daidai.

Karin Magana 5

Faɗakarwa a kan Fasikanci

1 Ɗana, ka mai da hankali, ka kasa kunne ga hikimata da basirata. 2 Sa'an nan ne za ka san yadda za ka yi kome daidai, kalmominka za su nuna kana da ilimi. 3 Leɓunan matar wani, mai yiwuwa ne, su yi zaƙi kamar zuma, sumbace-sumbacenta kuma su fi man zaitun taushi. 4 Amma bayan an gama duka, ba abin da za ta bar maka sai baƙin ciki, da azaba. 5 Za ta gangara da kai zuwa lahira, hanyar da take bi hanyar mutuwa ce. 6 Ba a kan hanyar rai take ba, tana ragaita nesa da hanyar, amma kai ba ka ankara ba. 7 'Ya'yana, ku kasa kunne gare ni yanzu, kada ko kusa ku manta da abin da nake faɗa. 8 Ku yi nesa da irin wannan mace! Kada ku yarda ku yi ko kusa da ƙofarta! 9 Idan kuwa kun yi, girmamawar da ake yi muku za ta zama ta waɗansu. Za ku yi mutuwar ƙuruciya ta hannun mutane marasa imani. 10 Hakika, baƙi za su kwashe dukan dukiyarku, abin da kuka sha wahalar samu kuma zai zama rabon wani dabam. 11 Za ku kwanta kuna nishi a kan gadon mutuwa, namanku da tsokokinku za su zagwanye. 12 Sa'an nan za ku ce, “Me ya sa ban taɓa koyo ba? Me ya sa ban yarda wani ya kwaɓe ni ba? 13 Ban kasa kunne ga malamaina ba. Ban mai da hankalina gare su ba. 14 Farat ɗaya sai aka kunyatar da ni a bainar jama'a.” 15 Ka yi aminci ga matarka, ka ƙaunace ta ita kaɗai. 16 Idan kuma waɗansu mata sun haifa maka 'ya'ya, 'ya'yan nan ba za su yi maka wani amfani ba. 17 'Ya'yanka za su yi girma su taimake ka, ba na baƙi ba. 18 Saboda haka ka yi farin ciki tare da matarka, ka yi murna da budurwa da ka auro, 19 kyakkyawa mai kyan gani kamar barewa. Bari kyanta ya ɗau hankalinka. Bari ƙaunarta ta kewaye ka. 20 Ɗana, don me za ka fi son matar wani? Don me za ka bar matar wani ta lallame ka da daɗin bakinta? 21 Ubangiji yana ganin dukan abin da kake yi. Inda ka shiga duk yana kallonka. 22 Zunuban mutum tarko ne, komar zunubinsa ce take kama shi. 23 Yakan mutu saboda rashin kamewarsa, cikakkiyar wautarsa za ta kai shi kabarinsa.

Karin Magana 6

Faɗakarwa a kan Ragwanci da Ƙarya

1 Ɗana, ka taɓa yin alkawari ka ɗaukar wa wani lamuni? 2 Maganganunka sun taɓa kama ka, ko alkawaranka sun taɓa zamar maka tarko? 3 To, ɗana, kana cikin ikon wannan mutum, amma ga yadda za ka yi ka fita, sheƙa zuwa wurinsa, ka roƙe shi ya sake ka. 4 Kada ka yarda ka yi barci ko ka huta. 5 Ka fita daga cikin tarkon kamar tsuntsu ko barewar da ta tsere wa maharbi. 6 Bari ragwaye su yi koyi da tururuwa. 7 Ba su da shugaba, ba su da sarki, ko mai mulki, 8 amma da kaka sukan tanada wa kansu abinci, domin kwanakin bazara. 9 Har yaushe rago zai yi ta ɓalɓalcewa? Yaushe zai farka? 10 Yakan ce, “Bari in ɗan ruruma, in naɗa hannuwana in shaƙata.” 11 Amma lokacin da yake sharar barci, tsiya za ta auka masa kamar ɗan fashi da makamai. 12 Sakarkari, wato mugaye sukan yi ta baza jita-jita. 13 Sukan yi ƙyifce, ko su yi nuni don su yaudare ka. 14 A kowane lokaci suna shirya mugunta a kangararren hankalinsu, suna kuta tashin hankali ko'ina. 15 Saboda wannan masifa za ta fāɗa musu farat ɗaya ba makawa, za a yi musu mummunan raini. 16-19 Akwai abu shida, i, har bakwai ma, waɗanda Ubangiji yake ƙi, waɗanda ba zai haƙura da su ba, duban raini, harshe mai faɗar ƙarya, hannuwan da suke kashe marasa laifi, kwanyar da take tunane-tunanen mugayen dabaru, mutum mai gaggawar aikata mugunta, mai yawan shaidar zur, mutum mai ta da fitina a tsakanin abokai.

Faɗakarwa a kan Zina

20 Ɗana, ka yi abin da mahaifinka ya faɗa maka, kada ka manta da koyarwar mahaifiyarka. 21 Kullum ka kiyaye abin da suke faɗa maka, ka kulle su kuma a zuciyarka. 22 Koyarwarsu za ta bi da kai sa'ad da kake tafiya, ta kiyaye ka da dare, ta kuma ba ka shawara da rana. 23 Doka da abubuwan da take koyarwa haske ne mai haskakawa. Tsautawa tana iya koya maka zaman duniya. 24 Za ta tsare ka daga mugayen mata, daga kalmomin alfasha da suke fitowa daga bakin matan waɗansu. 25 Kada kyansu ya jarabce ka, kada ka faɗa cikin tarkon feleƙensu. 26 Mutum ta dalilin karuwa zai sha hasarar abin da ya mallaka duka ta wurin zina. 27 Ka iya rungumar wuta a ƙirjinka sa'an nan ka ce ba za ta ƙone tufafinka ba? 28 Ka iya tafiya a kan garwashi sa'an nan ka ce ƙafafunka ba za su ƙone ba? 29 Haka yake da mutumin da ya kwana da matar wani. Duk wanda ya aikata wannan, zai sha wahala. 30 Mutane ba sukan raina wanda ya saci abinci don yana jin yunwa ba, 31 duk da haka in an kama shi, sai ya biya diyya sau bakwai, tilas kuwa ya ba da dukan abin da yake da shi. 32 Amma mazinaci marar hankali ne, gama hallaka kansa yake yi. 33 Zai sha d�ka, a wulakanta shi, zai dawwama cikin kunya. 34 Hasalar miji mai kishi babu irinta, ramawarsa ba dama. 35 Ba zai karɓi biya ba, ba kyautar da za a yi masa wadda za ta kwantar da fushinsa.

Karin Magana 7

Wayon Mazinaciya

1 Ɗana, ka tuna da abin da na faɗa, kada ka manta da abin da na ce maka ka yi. 2 Ka yi abin da na faɗa maka, za ka rayu. Ka natsu, ka bi koyarwata, ka tsare ta kamar ƙwayar idonka. 3 Kullayaumi ka riƙe koyarwata tare da kai, ka rubuta ta a zuciyarka. 4 Ka mai da hikima 'yar'uwarka, basira kuwa ta zama ƙawarka ta jikinka. 5 Za su nisanta ka da matan mutane, daga kuma mata masu maganganun alfasha. 6 Wata rana ina leƙawa ta tagar ɗakina, 7 sai na ga waɗansu samari masu yawa waɗanda ba su gogu da duniya ba, musamman sai na lura da wani dolo a cikinsu. 8 Yana tafe a kan titi kusa da kusurwar da take a zaune, yana wucewa kusa da gidanta, 9 da magariba cikin duhu. 10 Sai ta tarye shi, ta ci ado kamar karuwa, tana shirya yadda za ta yaudare shi. 11 (Ba ta jin tsoro, ba ta kuma jin kunya, koyaushe tana ta gantali a tituna. 12 Takan tsaya tana jira a kowace kusurwa, wani lokaci a tituna, wani lokaci kuma a kasuwa.) 13 Ta rungumi saurayin, ta sumbace shi, ta dubi tsabar idonsa ta ce, 14 “Na miƙa hadayu yau, ina da nama na hadayu. 15 Shi ya sa na fito ina nemanka, ina so in gan ka, ga shi kuwa, na gan ka! 16 Na lulluɓe gadona da zannuwan lilin masu launi iri iri daga Masar. 17 Na yayyafa musu turaren mur da na aloyes da na kirfa. 18 Ka zo mu sha daɗin ƙauna, mu more dukan dare, mu yi farin ciki rungume da juna. 19 Mijina ba ya gida, ya yi tafiya mai nisa. 20 Ya tafi da kuɗi masu yawa, ba zai komo ba sai bayan mako biyu.” 21 Ta jarabce shi da kwarkwasarta, sai ya ba da kai ga daɗin bakinta. 22 Nan da nan ya bi ta kamar sā zuwa mayanka, kamar barewa tana tsalle zuwa cikin tarko, 23 inda kibiya za ta soke zuciyarta. Yana kama da tsuntsun da yake zuwa cikin tarko, bai kuwa sani ransa yana cikin hatsari ba. 24 Yanzu fa 'ya'yana, ku kasa kunne gare ni, ku mai da hankali ga abin da nake faɗa. 25 Kada ku yarda irin wannan mace ta rinjayi zuciyarku, kada ku yi ta yawon nemanta. 26 Ita ce sanadin hallakar mutane da yawa, ta sa mutane da yawa mutuwa, har ba su ƙidayuwa. 27 Tafiya gidanta kuna kan hanya zuwa mutuwa ke nan, gajeruwar hanya ce zuwa lahira.

Yabon Hikima

Karin Magana 8

1 Ku kasa kunne! Hikima tana kira. Tana so a ji ta. 2 Tana tsaye bisa kan tuddai a bakin hanya Da a mararraban hanyoyi. 3 A ƙofofin shiga birni, tana kira, 4 “Ina roƙonku, ya ku, 'yan adam, Ina kiran kowane mutum da yake a duniya. 5 Ba ku balaga ba? To, ku balaga. Ku wawaye ne? Ku koyi hankali. 6 Ku kasa kunne ga jawabina mafi kyau, Dukan abin da na faɗa muku daidai ne. 7 Abin da na faɗa gaskiya ne, Ƙarairayi abin ƙi ne a gare ni. 8 Kowane abu da na faɗa gaskiya ne, Ba wani abu da yake na laifi ko na ruɗawa. 9 Ga mutum mai basira, dukan abu ne a sarari, Ga wanda aka sanar da shi sosai, abu ne a sawwaƙe. 10 Ka zaɓi koyarwata fiye da azurfa, Ka zaɓi ilimi fiye da zinariya tsantsa. 11 “Ni ce hikima, na fi lu'ulu'ai, Cikin dukan abin da kake so, ba kamata. 12 Ni ce hikima, ina da basira, Ina da ilimi da faɗar daidai. 13 Ƙin mugunta shi ne tsoron Ubangiji, Na ƙi girmankai, da fāriya, da mugayen hanyoyi, Da maganganu na ƙarya. 14 Nakan shirya abin da zan yi, in kuwa yi shi. Ina da fahimi, ina da ƙarfi. 15 Nakan taimaki sarakuna su yi mulki, Mahukunta kuma su tsara dokoki masu kyau. 16 Kowane mai mulki a duniya, da taimakona yake mulki, Ƙusoshin hukumomi da dattawan gari duka ɗaya. 17 Ina ƙaunar waɗanda ke ƙaunata, Dukan wanda ke nemana kuma zai same ni. 18 Ina da dukiya da daraja da zan bayar, Da wadata da nasara kuma. 19 Abin da za ka samu daga gare ni Ya fi zinariya kyau, da azurfa tsantsa. 20 A kan hanyar adalci nake tafiya, Rankai a kan hanyoyin gaskiya. 21 Ina ba da dukiya ga waɗanda suke ƙaunata, Ina kuma cika gidajensu da wadata. 22 “Ni ce halittar farko da Ubangiji Ya fara halittawa daga cikin ayyukansa tuntuni. 23 Da farkon farawa ni aka fara halittawa Kafin a yi duniya. 24 Ni aka fara yi kafin tekuna, A sa'ad da ba maɓuɓɓugan ruwa. 25 Ni aka fara yi kafin a yi duwatsu, Kafin a kafa tuddai a wurarensu, 26 Kafin Allah ya halicci duniya da filayenta, Ko ɗan ɓarɓashin ƙasa. 27 A can nake sa'ad da ya shata sararin sama, Da sa'ad da ya shimfiɗa al'arshi a hayin tekuna, 28 Da sa'ad da ya sa gizagizai a sararin sama, Ya buɗe maɓuɓɓugan teku, 29 Ya kuma umarci ruwan teku, kada ya zarce wurin da ya sa. Ina can sa'ad da ya kafa harsashin ginin duniya. 30 Ina kusa da shi kamar mai tsara fasalin gini, Ni ce abar murnarsa kowace rana, A koyaushe ina farin ciki a gabansa. 31 Ina farin ciki da duniya, Ina murna da 'yan adam. 32 “Yanzu ku matasa, ku kasa kunne gare ni, Ku yi abin da na ce, za ku yi farin ciki. 33 Ku saurari abin da aka koya muku, Ku zama masu hikima, kada ku yi sakaci da ita. 34 Mutumin da ya kasa kunne gare ni, zai yi farin ciki hakanan, Wato yakan tsaya a ƙofata koyaushe, Yana kuma jira a ƙofar shiga gidana. 35 Mutumin da ya same ni ya sami rai, Ubangiji zai ji daɗinsa. 36 Mutumin da bai same ni ba ya cuci kansa, Duk wanda yake ƙina mutuwa yake ƙauna.”

Karin Magana 9

Hikima da Dakikanci

1 Hikima ta gina gidanta, ta yi masa ginshiƙai bakwai. 2 Ta sa an yanka dabba don biki, ta gauraya ruwan inabi da kayan yaji, ta shirya tebur. 3 Ta aiki barorinta 'yan mata su je su hau wuri mafi tsayi a birni su yi kira. 4 “Ku shigo, ku jahilai!” Ga dolo kuwa ta ce, 5 “Zo ka ci abincina ka sha ruwan inabin da na gauraya. 6 Ka rabu da ƙungiyar jahilai, ka rayu, ka bi hanyar ilimi.” 7 Idan ka kwaɓi mai fāriya, za ka gamu da cin mutunci, idan ka tsauta wa mugu, kai ne za ka cutu. 8 Faufau kada ka kuskura ka kwaɓi mai fāriya, zai ƙi ka saboda wannan, amma idan ka kwaɓi mai hikima zai girmama ka. 9 Dukan abin da ka faɗa wa mutum mai hikima, zai ƙara masa hikima. Dukan abin da ka faɗa wa adali zai ƙara masa ilimi. 10 Domin ka zama mai hikima dole ka fara da tsoron Ubangiji. Idan ka san Mai Tsarki, ka sami ganewa. 11 Hikima za ta ƙara shekarunka. 12 Kai ne da riba in ka sami hikima. Kai za ka sha hasara in ka ƙi ta. 13 Wawanci kamar mace ce mai kwakwazo, jahila, marar kunya. 14 Takan zauna a ƙofar gidanta, ko a wurin da ya fi duka bisa a cikin gari. 15 Takan yi ta kiran masu wucewa waɗanda hankalinsu ke a kan ayyukansu, ta ce, 16 “Ku shigo, ku jahilai!” Takan ce wa dolo, 17 “Ruwan da aka sata ya fi daɗi, hakanan kuma abincin da ake satar ya fi daɗi.” 18 Waɗanda suka fāɗa a hannunta ba su sani mutuwa za su yi ba, waɗanda suka riga sun shiga kuwa suna can sun nutse cikin lahira.

Karin Magana 10

Adali da Mugu Dabam Suke

1 Karin maganar Sulemanu ke nan. Ɗa mai hikima abin fāriya ne ga mahaifinsa, amma wawa yakan jawo wa mahaifiyarsa baƙin ciki. 2 Abin da ka samu ta hanyar zamba ba zai yi albarka ba, amma gaskiya za ta cece ka. 3 Ubangiji ba zai bar mutumin kirki da yunwa ba, amma zai hana mugu ya kai ga biyan bukatarsa. 4 Ragwanci zai sa talauci, amma yin aiki sosai zai arzuta ka. 5 Mutum mai hankali yakan tattara amfanin gona da kaka, amma abin kunya ne a yi barci a lokacin girbi. 6 Mutumin kirki yakan karɓi albarka, maganganun mugun kuwa sukan ɓoye mugun halinsa. 7 Tunawa da mutumin kirki albarka ce, amma nan da nan za a manta da mugaye. 8 Mutane masu hankali sukan bi shawarar kirki, masu maganar wauta kuwa za su lalace. 9 Amintaccen mutum zai zauna lafiya ba abin da zai same shi, amma marasa aminci za a kama su. 10 Mutumin da ya ƙi faɗar gaskiya yana haddasa wahala, amma wanda ya bayyana gaskiya zai kawo salama. 11 Kalmomin mutumin kirki maɓuɓɓugan rai ne, amma kalmar mugun takan ɓoye makircinsa. 12 Ƙiyayya takan haddasa wahala, amma ƙauna takan ƙyale dukan laifofi. 13 Mutane masu fasaha sukan yi magana mai ma'ana, amma wawaye suna bukatar horo. 14 Mutane masu hikima sukan nemi ilimi iyakar iyawarsu, amma sa'ad da wawa ya yi magana, wahala tana kusa. 15 Wadata takan kiyaye attajiri, amma tsiya takan hallaka matalauci. 16 Sakayyar da za a yi wa mutumin kirki ta rai ce, amma zunubi yakan sa a ƙara yin wani zunubi. 17 Mutumin da ke kasa kunne sa'ad da ake kwaɓarsa zai rayu, amma duk wanda bai yarda da kuskurensa ba yana cikin hatsari. 18 Mutumin da ke faɗar ƙarairayi maƙiyi ne, dukan wanda ke baza jitajita wawa ne. 19 Bisa ga yawan surutunka, mai yiwuwa ne ƙwarai ka yi zunubi, amma idan kai mai la'akari ne, sai ka yi shiru. 20 Kalmomin mutumin kirki suna kama da azurfa tsantsa, amma shawarwarin mugu ba su da wani amfani. 21 Kalmomin mutumin kirki za su amfani mutane da yawa, amma kana iya hallaka kanka da wauta. 22 Albarkar Ubangiji takan arzuta mutum, amma yawan aiki ba shi yake kawo arziki ba. 23 Wawa ne ke jin daɗin aikata mugunta, amma mai fasaha yana jin daɗin hikima. 24 Abin da mugun yake tsoro, shi yakan auko masa, amma adali yakan sami biyan bukatarsa. 25 Hadiri yakan taso ya wargaza mugaye, amma amintattu lafiya lau suke a koyaushe. 26 Sam, kada ka sa malalaci ya yi maka wani abu, zai sa ka ka yi fushi, idanunka su cika da hawaye mai zafi. 27 Ka yi tsoron Ubangiji za ka rayu, ka yi tsawon rai, amma mugaye sukan mutu tun kwanansu bai ƙare ba. 28 Abin da mutanen kirki ke sa zuciya yakan kai su ga murna, amma mugaye ba su da wani abu da za su sa zuciya a kai. 29 Ubangiji yana kiyaye marasa laifi, amma yakan hallaka masu mugunta. 30 Kullayaumi adalai sukan yi zamansu lafiya, amma mugaye ba za su zauna a ƙasar ba. 31 Maganar adalai ta hikima ce, amma harshen da ke hurta mugunta, za a dakatar da shi. 32 Adalai sun san irin maganar da ta cancanta su faɗa, amma mugaye, kullum sukan faɗi maganar da za ta cutar.

Karin Magana 11

1 Ubangiji yana ƙin masu yin awo da ma'aunin zamba, amma yana farin ciki da masu yin awo da ma'auni na gaskiya. 2 Masu girmankai za a kunyatar da su nan da nan. Hikima ce mutum ya zama mai kamewa. 3 Mutanen kirki su ne gaskiya takan bi da su. Rashin aminci kuwa yana hallaka maciya amana. 4 Dukiya ba ta da wani amfani a ranar mutuwa, amma adalci zai hana ka mutuwa. 5 Gaskiya takan sa zaman mutanen kirki ya zama a sawwaƙe, amma mugun mutum shi yake kā da kansa da kansa. 6 Adalci yakan ceci amintaccen mutum, amma marar aminci, haɗamarsa ce take zamar masa tarko. 7 Mugun mutum yakan mutu da burinsa. Dogara ga dukiya bai amfana kome ba. 8 Akan kiyaye adali daga wahala, amma takan auko wa mugu. 9 Mutane sukan sha hasara ta wurin maganar marasa tsoron Allah, amma hikimar adalai takan yi ceto. 10 Birni yakan yi farin ciki saboda wadatar mutanen kirki, akwai kuma sowa ta farin ciki sa'ad da mugaye suka mutu. 11 Biranen da adalai ke cikinsu sukan ƙasaita, amma maganganun mugaye sukan hallakar da su. 12 Wauta ce a yi wa waɗansu maganar raini, amma mutum mai la'akari yakan kame bakinsa. 13 Ba wanda zai yarda ya faɗi asirinsa ga matsegunci, amma za ka amince wa amintaccen mutum. 14 Al'ummar da ba ta da masu ja mata gora, za ta fāɗi. Yawan mashawarta yake kawo zaman lafiya. 15 Wanda ya ɗaukar wa baƙo lamuni zai yi da na sani, zai fi maka sauƙi idan ba ruwanka. 16 Mace mai mutunci abar girmamawa ce, amma azzalumai za su sami dukiya. 17 In ka yi alheri, kanka ka samar wa tagomashi, in kuwa ka yi mugunta, kanka ka cutar. 18 A ainihi mugaye ba su cin ribar kome, amma idan ka yi abin da ke daidai, ka tabbata za a sāka maka da alheri. 19 Mutumin da ya yi niyyar aikata abin da ke daidai zai rayu, amma mutumin da ya dukufa ga aikata mugunta zai mutu. 20 Ubangiji yana ƙin masu muguwar niyya, amma yana murna da waɗanda ke aikata abin da ke daidai! 21 Ka tabbata fa za a hukunta mugaye, amma ba za a hukunta adalai ba. 22 Kome kyan mace idan ba ta da kangado, tana kamar zoben zinariya a hancin alade. 23 Abin da mutanen kirki suke so kullum yakan jawo alheri, idan mugaye sun sami biyan bukatarsu kowa zai yi ɓacin rai. 24 Waɗansu mutane sukan kashe kuɗinsu hannu sake, duk da haka arzikinsu sai ƙaruwa yake yi. Waɗansu kuwa saboda yawan tsumulmularsu sukan talauce. 25 Ka yi alheri za ka arzuta. Ka taimaki waɗansu, su kuma za su taimake ka. 26 Mutane sukan la'anci mai ɓoye hatsi, yana jira ya yi tsada, amma sukan yabi wanda yake sayar da nasa. 27 Idan nufe-nufenka na kirki ne za a girmama ka, amma idan kai mai neman tashin hankali ne, to, abin da zai same ka ke nan. 28 Adalai za su arzuta, kamar ganyaye da bazara, amma waɗanda ke dogara ga dukiyarsu za su karkaɗe kamar ganyaye da kaka. 29 Mutumin da ke jawo wa iyalinsa wahala, ƙarshensa talaucewa. Wawaye za su zama barorin masu hikima a koyaushe. 30 Adalci yana rayar da mutum, wanda yake da hikima kuma yakan ceci rayuka. 31 Idan an sāka wa mutumin kirki da alheri a duniya, hakika za a hukunta wa mugaye da masu zunubi.

Karin Magana 12

1 Mutumin da yake ƙaunar ilimi yakan so a faɗa masa kuskurensa, wauta ce mutum ya ƙi yarda a faɗa masa laifinsa. 2 Ubangiji yana murna da mutanen kirki, amma yakan hukunta masu shirya mugunta. 3 Mugunta ba ta kawo zaman lafiya, amma adalai sukan tsaya daram. 4 Matar kirki abar fāriya ce, abar murna ga mijinta, amma idan ta sa shi kunya, ta zama masa kamar ciwo a ƙashinsa. 5 Amintattun mutane za su yi maka abin da ke daidai, amma mugaye za su ruɗe ka. 6 Maganganun mugaye na kisankai ne, amma kalmomin adalai sukan ceci waɗanda ake neman ransu. 7 Mugaye sukan gamu da faɗuwarsu, ba magāda, amma iyalan adalai sukan dawwama. 8 Idan kai haziƙi ne, za a yabe ka, amma idan kai dakiki ne, mutane za su raina ka. 9 Gara kana talakanka, kana neman abinci, da ka mai da kanka kai wani abu ne, alhali kuwa abin da za ka ci ya fi ƙarfinka. 10 Mutumin kirki yakan lura da dabbobinsa, amma mugaye sukan yi wa nasu ƙeta. 11 Manomin da ke aiki ƙwarai yana da isasshen abinci. Wauta ce a ɓatar da lokaci a kan aikin banza. 12 Iyakar abin da mugaye suke so, shi ne su sami muguntar da za su yi, amma adalai suna tsaye daram. 13 Maganganun mugun sukan zamar masa tarko, amma amintacce yakan fid da kansa daga cikin wahala. 14 Sakayyar mutum ta rataya ne a kan maganarsa da aikinsa, zai sami abin da ya cancance shi. 15 Wawa a kullum tsammani yake abin da yake yi daidai ne, amma masu hikima sukan kasa kunne ga shawara. 16 Sa'ad da wawa ya hasala, nan da nan kowa zai sani, amma mai la'akari ba zai nuna ya kula ba. 17 Sa'ad da ka faɗi gaskiya, ka yi adalci, amma ƙarairayi su ne jagorar aikata rashin adalci. 18 Maganganun rashin tunani suke sa rauni mai zurfi kamar saran takobi, amma kalmomin mai hikima sukan warkar da raunuka. 19 Gaskiya dawwamammiya ce, amma ƙarya ƙurarriya ce. 20 Waɗanda ke shawarta mugunta za a auka musu farat ɗaya, amma waɗanda ke aikata alheri za su yi farin ciki. 21 Ba wani mugun abu da zai sami adali, amma mugaye ba za su sami kome ba, sai wahala. 22 Ubangiji yana ƙin maƙaryata, amma yana murna da masu faɗa da cikawa. 23 Mai la'akari zai bar wa cikinsa abin da ya sani, amma wawaye sukan yi ta tallar wautarsu. 24 Mutum mai mai da hankali ga aikinsa zai sami iko, amma ragwanci zai sa mutum ya zama bawa. 25 Damuwa takan hana wa mutum farin ciki, amma kalmomin alheri za su sa shi ya yi murna. 26 A koyaushe adalin mutum yakan gwada halinsa, amma mugaye sukan ɓata a hanya. 27 Rago ba zai kai ga biyan bukatarsa ba, amma mai ƙwazo zai sami dukiya. 28 Adalci hanyar rai ne, amma wauta hanyar mutuwa ce.

Karin Magana 13

1 Ɗa mai hikima yakan mai da hankali sa'ad da mahaifinsa yake kwaɓarsa, amma mutum mai girmankai ba ya yarda da kuskurensa. 2 Mutanen kirki za a sāka musu da alheri a kan abin da suke faɗa, amma mayaudara sukan ƙosa su ta da zaune tsaye. 3 Ka lura da irin abin da kake faɗa don ka kiyaye ranka. Mutumin da bai kula da maganarsa ba, yakan hallakar da kansa. 4 Rago yakan ƙosa ya sami wani abu ainun, amma sam, ba zai samu ba. Mai mai da hankali ga aikinsa zai sami kowane abu da yake bukata. 5 Masu aminci suna ƙin ƙarairayi, amma maganganun mugun abin kunya ne da ƙasƙanci. 6 Adalci yakan kiyaye marasa laifi, amma mugunta ita ce fāɗuwar masu zunubi. 7 Waɗansu mutane sukan nuna su attajirai ne, alhali kuwa ba su da kome. Waɗansu kuma sukan nuna su matalauta ne, alhali kuwa suna da dukiya. 8 Kuɗin attajiri suna iya ceton ransa, bai kyautu ba a razana matalauci. 9 Adalai suna kama da haske mai haskakawa ƙwarai, mugaye kuwa suna kamar fitilar da ke mutuwa. 10 Fāriya ba ta kawo kome sai wahala. Hikima ce a nemi shawara. 11 Dukiyar da aka same ta a sawwaƙe, za ka rasa ta da sauri, amma wanda ya same ta da wahala, za ta yi ta ƙaruwa. 12 Idan ba bege, sai zuciya ta karai, amma muradin da ya tabbata zai cika ka da sa zuciya. 13 Idan ka ƙi shawara mai kyau wahala kake nemar wa kanka, idan ka bi ta kuwa za ka zauna lafiya. 14 Koyarwar masu hikima maɓuɓɓugar rai ce, za ta taimake ka ka kuɓuta sa'ad da ranka yake cikin hatsari. 15 Basira takan sa a girmama ka, amma mutanen da ba za a iya amincewa da su ba, a kan hanyar hallaka suke. 16 Mutum mai hankali a koyaushe yakan yi tunani kafin ya aikata, amma wawa yakan tallata jahilcinsa. 17 Manzanni marasa aminci sukan haddasa wahala, amma waɗanda suke amintattu sukan kawo salama. 18 Mutumin da ba zai koya ba, zai talauce ya sha kunya, amma wanda ya kasa kunne ga tsautawa za a girmama shi. 19 Abu mai kyau ne mutum ya sami biyan bukatarsa! Wawaye sukan ƙi barin mugunta. 20 Ka koya daga wurin masu hikima, za ka zama mai hikima. Yi abuta da wawaye, za ka kuwa lalace. 21 Wahala tana bin masu zunubi ko'ina, amma za a sāka wa adalai da kyawawan abubuwa. 22 Mutumin kirki zai sami dukiya, har ya bar wa jikokinsa, amma dukiyar masu zunubi za ta zama ta adalai. 23 Saurukan da ba a aikatawa, za su ba da isasshen abinci ga matalauci, amma mutane marasa gaskiya sukan hana albarka. 24 Idan ba ka horon ɗanka, ba ka ƙaunarsa ke nan, amma idan kana ƙaunarsa za ka riƙa kwaɓarsa. 25 Adalai suna da isasshen abinci, amma mugaye fama suke da yunwa koyaushe.

Karin Magana 14

1 Hikimar mata takan gina gidaje, amma wauta takan rushe su. 2 Ka yi gaskiya, za ka nuna girmamawarka ga Ubangiji, amma idan ka yi rashin gaskiya, ka nuna rashin girmamawa ke nan ga Ubangiji. 3 Kalmomin mai hikima za su kiyaye shi, amma maganganun wawa za su jawo masa hukunci. 4 Idan ba ka da shanun noma ba za ka sami hatsi mai yawa ba, amma idan kana da su za ka sami hatsi mai yawan gaske. 5 Amintaccen mashaidi a koyaushe yana faɗar gaskiya, amma marar aminci ba ya faɗar kome, sai ƙarairayi. 6 Mutum mai fāriya ba zai taɓa zama mai hikima ba sam, amma mutum mai basira yakan koya a sawwaƙe. 7 Ka nisanci wawaye, gama ba su da abin da za su koya maka. 8 Me ya sa haziƙi yake da hikima? Domin ya san abin da zai yi. Me ya sa dakiki yake wauta? Domin yana ganin kansa masani ne. 9 Idan wawaye sun yi zunubi ba sukan kula ba, amma mutanen kirki sukan nemi gafara. 10 Ɓacin ranka naka ne, murnarka kuwa ba za ka raba da wani ba. 11 Gidan mutumin kirki ba zai rushe ba bayan da an lalatar da gidan mugun mutum. 12 Hanyar da kake tsammani ita ce daidai, za ta kai ka ga hallaka. 13 Dariyar mutum takan ɓoye baƙin cikinsa. Sa'ad da murna ta tafi, koyaushe baƙin ciki yana nan. 14 Mugu zai sami abin da ya cancance shi, mutumin kirki kuma zai sami sakayyar ayyukansa. 15 Wawa yakan gaskata kowane abu, amma mai la'akari yana lura da takawarsa. 16 Mutum mai hankali yana lura don ya kauce wa wahala, amma wawa rashin kula gare shi, yakan aikata kome da gaggawa. 17 Mutum mai zafin rai yakan yi aikin wauta, mai mugayen dabaru kuma abin ƙi ne. 18 Jahilai sukan sami abin da ya cancanci wautarsu, amma ilimi shi ne sakamakon masu azanci. 19 Tilas mugaye su rusuna wa adalai, su roƙe su tagomashi da tawali'u. 20 Ba wanda yake son matalauci, amma attajiri yana da abokai da yawa. 21 Idan kana so ka zama mai farin ciki, sai ka nuna alheri ga matalauci. Zunubi ne ka raina kowane mutum. 22 Waɗansu za su amince da kai, su girmama ka, idan ka aikata nagarta, idan kuwa ka aikata mugunta, to, ka yi babban kuskure. 23 Idan ka yi aiki za ka sami abin masarufi, idan kuwa ka zauna kana ta surutu kawai za ka zama matalauci. 24 Mutane masu hikima za a sāka musu da wadata, amma za a san wawa ta wurin wautarsa. 25 Sa'ad da mashaidi ya faɗi gaskiya zai ceci rayuka, amma maƙaryacin mashaidi yakan ci amanar mutane sa'ad da ya faɗi ƙarairayi. 26 Tsoron Ubangiji yakan ba da tabbatarwa, da zaman lafiya ga mutum da iyalinsa. 27 Kana so ka kauce wa mutuwa? To, tsoron Ubangiji shi ne maɓuɓɓugar rai. 28 Darajar sarki ta dogara ga irin yawan mutane da ya mallaka, idan ba su, shi ba kome ba ne. 29 Mutum mai kamewa yana da hikima, amma mai zafin rai yana bayyana wautarsa a fili. 30 Kwanciyar rai lafiya ce ga jiki, amma kishi yana kama da ciwon da yake cin ƙashi. 31 Wanda ya zalunci matalauci ya zargi Mahaliccinsa ke nan, amma nuna alheri ga matalauci yin sujada ne. 32 Muguntar mugun takan kawo hallakarsa, amma adalin mutum, an kiyaye shi ta wurin dattakonsa. 33 Hikima tana cikin kowane tunani na haziƙi, wawa bai san kome game da hikima ba. 34 Adalci yakan ɗaukaka al'umma, amma zunubi yakan kunyatar da al'umma. 35 Sarakuna suna jin daɗin ƙwararrun 'yan majalisarsu, amma sukan hukunta waɗanda suka ba su kunya.

Karin Magana 15

1 Amsa magana da tattausan harshe takan kwantar da hasala, amma magana da kakkausan harshe takan kuta fushi. 2 Sa'ad da mai hikima ya yi magana yakan sa ilimi ya yi bansha'awa, amma wawaye sukan yi ta sheƙa rashin hankali. 3 Ubangiji yana ganin abin da ke faruwa a ko'ina, yana lura da mu, ko muna aikata alheri ko mugunta. 4 Kalmomin alheri suna kawo rai, amma maganganun ƙiyayya suna karya zuciyar mutum. 5 Wauta ce mutum ya ƙi kulawa da abin da mahaifinsa ya koya masa, amma hikima ce idan ka karɓi tsautawarsa. 6 Adalai suna adana dukiyarsu, amma mugaye sukan rasa tasu dukiya sa'ad da wahala ta zo. 7 Mutane masu hikima suke yaɗa ilimi, amma banda wawaye. 8 Ubangiji yana murna sa'ad da adalai suke yin addu'a, amma yana ƙin hadayun da mugaye suke miƙa masa. 9 Ubangiji yana ƙin hanyoyin mugaye, amma yana ƙaunar mutumin da ke yin abin da ke daidai. 10 Idan ka yi abin da ba daidai ba, za ka sha hukunci sosai, za ka mutu idan ka ƙi yarda da tsautawa. 11 Ko lahira ba za ta hana Ubangiji ya san abin da ke can ba. Ƙaƙa fa mutum zai iya ɓoye wa Allah tunaninsa? 12 Mai girmankai ba ya so a tsauta masa. Faufau ba zai nemi shawara a wurin masu hikima ba. 13 Sa'ad da mutum yake murna yakan yi murmushi, amma sa'ad da yake baƙin ciki yakan yi nadama. 14 Mutum mai basira yana neman ilimi, amma dakikai, jahilcinsu ya wadace su. 15 Wahaltaccen mutum a koyaushe, fama yake yi a zamansa, amma masu farin ciki suna zama da daɗin rai. 16 Gara a zauna da talauci da tsoron Ubangiji, da a sami dukiya game da wahala. 17 Gara cin mabunƙusa tare da waɗanda kake ƙauna, da ka ci abinci mai romo a inda ƙiyayya take. 18 Zafin rai yakan kawo jayayya, amma haƙuri yana kawo salama. 19 Idan kai rago ne za ka gamu da wahala a ko'ina, amma idan kai amintacce ne, ba za ka sha wahala ba. 20 Ɗa mai hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa, amma wawa yana raina mahaifiyarsa. 21 Dakikai suna murna da wautarsu, amma mai hikima zai aikata abin da ke daidai. 22 Ka nemi dukan shawarwarin da ka iya ka samu, za ka yi nasara, idan ba tare da shawara ba, za ka fāɗi. 23 Me ya fi wannan zama abin murna? Mutum ya sami maganar da ke daidai a lokacin da ya dace! 24 Mutum mai hikima yakan kama hanya ya haura zuwa rai, ba ya bin hanyar da ta gangara zuwa mutuwa. 25 Ubangiji zai rushe gidajen masu girmankai, amma zai kiyaye dukiyar gwauruwa, wato mata wadda mijinta ya mutu. 26 Ubangiji yana ƙin tunanin mugaye, amma yana murna da kalmomi masu daɗi. 27 Mai ƙoƙarin cin ƙazamar riba yana jefa iyalinsa a wahala ke nan. Kada ka karɓi hanci, za ka yi tsawon rai. 28 Mutanen kirki sukan yi tunani kafin su ba da amsa. Mugaye suna da saurin ba da amsa, amma takan jawo wahala. 29 Sa'ad da mutanen kirki sukan yi addu'a, Ubangiji yakan kasa kunne, amma ba ya kulawa da mugaye. 30 Fuska mai fara'a takan sa ka yi murna, labari mai daɗi kuma yakan sa ka ji daɗi. 31 Idan ka mai da hakali sa'ad da ake tsauta maka kai mai hikima ne. 32 Idan ka ƙi koyo kana cutar kanka, idan ka karɓi tsautawa za ka zama mai hikima. 33 Tsoron Ubangiji koyarwa ce domin samun hikima. Sai ka zama mai tawali'u kafin ka sami girmamawa.

Karin Magana 16

Karin Magana Zancen Zaman Mutum

1 Mutane sun iya yin shirye-shiryensu, amma cikawa ta Ubangiji ce. 2 Za ka yi tsammani kowane abu da ka yi daidai ne, amma Ubangiji yana auna manufarka. 3 Ka roƙi Ubangiji, ya sa albarka ga shirye-shiryenka, za ka kuwa yi nasara cikin aikata su. 4 Kowane abu da Ubangiji ya yi yana da makoma, makomar mugun kuwa hallaka ce. 5 Ubangiji yana ƙin kowane mutum da ke fariya. Irin wannan mutum ba zai kuɓuta daga hukunci ba. 6 Ka zama mai biyayya da aminci, Allah kuwa zai gafarta maka zunubinka. Ka dogara ga Ubangiji, ba wani mugun abu da zai same ka. 7 Lokacin da ka yi abin da Ubangiji ke so, ka iya mai da maƙiyanka su zama abokai. 8 Gara ka sami kaɗan ta hanyar gaskiya, da ka tara abu mai yawa ta hanyar zamba. 9 Kana iya yin shirye-shiryenka, amma Allah ne ke bi da kai cikin ayyukanka. 10 Sarkin da yakan yi magana ta wurin ikon Allah, a koyaushe yakan yanke shawarar da ke daidai. 11 Ubangiji yana son ma'aunai su zama na gaskiya, kowane abin sayarwa kuma ya zama daidai. 12 Sarakuna ba za su iya jurewa da mugunta ba, gama adalci ke sa hukuma ta yi ƙarfi. 13 Sarki yana so ya ji gaskiya, zai kuwa ƙaunaci mutanen da ke faɗar gaskiya. 14 Mutum mai hikima yakan yi ƙoƙari ya faranta zuciyar sarki. Idan kuwa sarki ya hasala mai yiwuwa ne a kashe wani. 15 Alherin sarki kamar gizagizai ne masu kawo ruwan sama a lokacin bazara, akwai rai a ciki. 16 Yana da kyau, ya kuma fi kyau a sami hikima da ilimi fiye da zinariya da azurfa. 17 Mutumin kirki yana tafiya a hanyar da ta kauce wa mugunta, saboda haka ka kula da inda kake tafiya, za ta ceci ranka. 18 Girmankai jagora ne zuwa ga hallaka, fāriya kuwa zuwa ga fāɗuwa. 19 Gara ka zama ɗaya daga cikin matalauta masu tawali'u, da ka zama ɗaya daga cikin masu girmankai, har da za ka sami rabo daga cikin ganimarsu. 20 Ka mai da hankali ga abin da aka koya maka, za ka yi nasara. Ka dogara ga Ubangiji, za ka yi farin ciki. 21 Mutum mai hikima, wanda ya isa mutum, akan san shi ta wurin haziƙancinsa, kamar yadda kalmominsa suke da daɗi, haka ma rinjayarsa take. 22 Hikima maɓuɓɓugar rai ce ga mai hikima, amma ɓata lokaci ne a yi ƙoƙarin koya wa dakikai. 23 Mai hikima yakan yi tunani kafin ya yi magana, abin da ya faɗa yakan yi rinjaye ƙwarai. 24 Kalmomi masu daɗi suna kama da zuma, suna da daɗin ɗanɗana, suna kuma da amfani domin lafiyarka. 25 Hanyar da kake tsammani ita ce daidai, za ta kai ka ga hallaka. 26 Marmarin cin abinci yakan sa ɗan ƙodago ya yi aiki da ƙwazo, domin yana so ya ci ya ƙoshi. 27 Mutumin da yake jin daɗin yin mugunta yakan tafi yawon nemanta, mugayen maganganunsa ƙuna suke kamar wuta. 28 Mugaye sukan baza jita-jita, suna zuga tashin hankali, suna raba aminai. 29 Mutum mai ta da zaune tsaye yakan ruɗi abokansa, ya kai su ga bala'i. 30 Ka kula da mutane masu murguɗa baki suna kaɗa gira a kanka, sun yi tunanin wani mugun abu ke nan. 31 Furfurar tsufa rawanin daraja ce, sakamako ne ga ran mai adalci. 32 Ya fi kyau ka zama mai haƙuri da ka zama mai ƙarfi. Ya fi kyau ka iya mallakar kanka fiye da mallakar birane. 33 Mutane sukan jefa kuri'a don su san nufin Allah, amma Allah da kansa ne yake ba da amsa.

Karin Magana 17

1 Gara a ci ƙanzo da rai a kwance, da gida cike da liyafa, amma cike da tashin hankali. 2 Bara mai wayo yakan sami iko a kan shashashan ɗan maigidansa, har ya sami rabo a cikin gādon. 3 Zinariya da azurfa da wuta ake gwada su, zuciyar ɗan adam kuwa Ubangiji ne yake gwada ta. 4 Mugaye sukan kasa kunne ga mugayen dabaru, maƙaryata kuma sukan kasa kunne ga ƙarairayi. 5 Wanda ya yi wa matalauci ba'a, Mahaliccinsa yake yi wa zargi. Idan kana murna da hasarar wani, za a hukunta ka. 6 Tsofaffi suna fāriya da jikokinsu, kamar yadda samari suke alfarma da iyayensu maza. 7 Mutumin da yake kamili ba ya faɗar ƙarya, haka ma wawa ba zai faɗi wani abin kirki ba. 8 Waɗansu mutane suna tsammani cin rashawa yakan yi aiki kamar sihiri, sun gaskata zai iya yin kome. 9 Idan kana so mutane su so ka, ka riƙa yafe musu sa'ad da suka yi maka laifi. Mita takan raba abuta. 10 Mutum mai fasaha yakan koyi abu da yawa daga tsautawa ɗaya, fiye da abin da wawa zai koya ko da an d�ke shi sau ɗari. 11 Mutuwa za ta zo wa mugaye kamar mugun manzo wanda a koyaushe yana so ya kuta tashin hankali. 12 Gara mutum ya gamu da beyar ta mata wadda aka kwashe mata kwiyakwiyanta, da ka gamu da waɗansu wawaye suna aikin dakikancinsu. 13 Idan ka sāka alheri da mugunta, ba za ka iya raba gidanka da mugunta ba, faufau. 14 Mafarin jayayya kamar ɓarkewa madatsar ruwa ne, sai a tsai da ita tun ba ta haɓaka ba. 15 Da wanda ya baratar da mugun da wanda ya kā da adali, duk abin ƙi suke ga Ubangiji. 16 Kashe kuɗi saboda ilimi ba shi da amfanin kome ga wawa, domin ba shi da tunani. 17 A koyaushe abokai sukan nuna ƙaunarsu, 'yan'uwa kuma, ai, don su ɗauki nawayar juna suke. 18 Sai mutum marar tunani ne kaɗai zai ɗauki lamunin basusuwan maƙwabcinsa. 19 Shi wanda yake son zunubi, yana son wahala ke nan, wanda kuma yake yin fāriya a dukan lokaci yana neman tashin hankali ke nan. 20 Mutumin da yakan yi tunanin mugunta, ya kuma hurta ta, kada ya sa zuciya ga samun abin kirki, sai dai bala'i kaɗai. 21 Mahaifi wanda ɗansa yake yin abubuwan wauta, ba shi da kome sai ɓacin rai da baƙin ciki. 22 Kasancewa da murna yakan ba ka lafiya. Zama da baƙin rai dukan lokaci mutuwar tsaye ce. 23 Alƙalai marasa gaskiya suna cin hanci a ɓoye, sa'an nan ba za su aikata adalci ba. 24 Baligi da hikima yake aikinsa, amma wanda bai balaga ba, bai san abin da zai yi ba. 25 Wawan da yakan jawo wa mahaifinsa ɓacin rai, abin baƙin ciki yake ga mahaifiyarsa. 26 Ba daidai ba ne a ci marar laifi tara, yi wa mutumin kirki bulala kuwa rashin adalci ne. 27 Mutumin da ya tabbata yana da gaskiya ba zai cika yawan magana ba, natsattsen mutum yana da basira ƙwarai. 28 Banda haka ma, ko wawa in bai buɗe bakinsa ba, za a zaci shi mai hikima ne, mai basira.

Karin Magana 18

1 Mutumin da ya kula da kansa kaɗai ba ya jituwa da kowa, ko wani ya faɗi maganar da take daidai ba zai yarda ba. 2 Wawa bai kula ba, ko ya fahimci abu, ko bai fahimta ba. Abin da yake so ya yi kaɗai, shi ne ya nuna kuzarinsa. 3 Zunubi da kunya a tattare suke. Idan ka yar da mutuncinka za ka sha ba'a a maimakonsa. 4 Harshen ɗan adam yana iya zama shi ne asalin hikima mai zurfi kamar teku, sabo kamar ruwan rafi mai gudu. 5 Ba daidai ba ne a yi wa mugun mutum alheri, sa'an nan a ƙi yi wa marar laifi adalci. 6 Sa'ad da wawa ya fara jayayya, yana neman d�ka ne. 7 Sa'ad da wawa ya yi magana yana lalatar da kansa ne, maganarsa tarko ce, da ita ake kama shi. 8 Ɗanɗanar jita-jita daɗi gare ta, mukan ƙosa mu haɗiye ta. 9 Rago yana daidai da mutumin da yake lalatar da abubuwa. 10 Sunan Ubangiji kamar ƙaƙƙarfar hasumiya ne, inda adali yakan shiga ya zauna lafiya. 11 Attajirai suna zato dukiyarsu ita ce za ta kiyaye su kamar garuka masu tsayi da suke kewaye da birni. 12 Ba wanda za a girmama sai mai tawali'u, mutum mai girmankai kuwa yana kan hanyar hallaka. 13 Ka saurara kafin ka amsa, idan kuwa ba ka yi ba, ka zama dakiki mai bankunya. 14 Sa zuciya ga rai yakan taimaki mutum sa'ad da yake ciwo, amma idan ya karai, to, tasa ta ƙare. 15 Mutane masu basira, a koyaushe suna da himma, a shirye kuma suke domin su koya. 16 Kana so ka sadu da babban mutum? Ka kai masa kyauta, za ka gan shi a sawwaƙe. 17 Wanda ya fara mai da magana a majalisa yakan zama kamar shi ne mai gaskiya, sai abokin shari'arsa ya mai da tasa maganar tukuna. 18 Idan mutum biyu ƙarfafa suna jayayya da juna a gaban shari'a, kuri'a a asirce kaɗai take iya daidaita tsakaninsu. 19 Ɗan'uwan da ya ji haushinka zai gagare ka, idan ka yi faɗa da shi zai rufe maka ƙofarsa. 20 Bisa ga sakamakon hurcinka haka za ka rayu. 21 Abin da ka faɗa ya iya cetonka ko ya hallaka ka, saboda haka tilas ne ka karɓi sakamakon maganarka. 22 Idan ka sami mace ka sami abu mai kyau, wannan alheri ne wanda Ubangiji ya yi maka. 23 Matalauci yakan yi roƙo da taushi, maganar matalauci rarrashi ne, amma attajiri yakan yi magana garas. 24 Waɗansu abokai ba su sukan ɗore ba, amma waɗansu abokai sun fi 'yan'uwa aminci.

Karin Magana 19

1 Gara mutum ya zama matalauci amma mai aminci, da a ce ya zama maƙaryaci, wawa. 2 Yin ɗokin da ba ilimi ba shi da amfani, rashin haƙuri kuma zai jawo maka wahala. 3 Waɗansu mutane sukan lalatar da kansu ta wurin ayyukansu na jahilci, sa'an nan su sa wa Ubangiji laifi. 4 Attajirai sukan sami sababbin abokai a koyaushe, amma matalauta ba zu su iya riƙon 'yan kaɗan da suke da su ba. 5 Idan ka faɗi ƙarya a majalisa, za a hukunta ka, ba za ka kuɓuta ba. 6 Kowa na ƙoƙari ya sami farin jini wurin manyan mutane, kowa na so a ce shi abokin mutumin nan ne, mai yawan alheri. 7 'Yan'uwan matalauci ba su bukatarsa, ba abin mamaki ba ne ya rasa abokai. Kome ƙoƙarin da zai yi ba zai sami ko ɗaya ba. 8 Ka yi wa kanka gatanci, ka koyi dukan abin da kake iyawa, sa'an nan ka tuna da abin da ka koya, za ka arzuta. 9 Ba wanda zai faɗi ƙarya a majalisa ya rasa shan hukunci, maƙaryaci, tasa ta ƙare. 10 Ko kusa wawaye ba za su yi zaman jin daɗi ba, hakanan kuma bayi ba za su yi mulki a kan iyayengijinsu ba. 11 Mutum mai hankali yake danne fushinsa. Lokacin da wani ya cuce ka, abin kirki ne, ka yi kamar ba ka kula da shi ba. 12 Hasalar sarki kamar rurin zaki ne, amma alherinsa kamar saukar ruwan sama ne. 13 Dakikin ɗa yana jawo wa mahaifinsa lalacewa, mace mai mita tana kama da ɗiɗɗigar ruwa. 14 Mutum na iya cin gādon gida da kuɗi daga wurin iyayensa, amma Ubangiji ne kaɗai yake ba shi mace mai hankali. 15 Rago, yi ta ragwancinka ka yi ta sharar barci, amma kai za ka sha yunwa. 16 Ka kiyaye umarnai za ka rayu, in ka ƙi binsu kuwa za ka mutu. 17 Sa'ad da ka bayar ga matalauci kamar ka ba Ubangiji rance ne, gama Ubangiji zai sāka maka. 18 Ka yi wa 'ya'yanka tarbiyya tun suna ƙanana yadda za su iya koyo. Idan ba ka yi haka ba, ka taimaka wajen lalacewarsu ke nan. 19 Idan mutum mai zafin rai ne, ƙyale shi ya sha sakamakonsa. Idan ka fisshe shi daga cikin wahala sau ɗaya, sai ka sāke yi. 20 Ka saurari shawara, ka yarda ka koya, wata rana za ka zama mai hikima. 21 Mutum ya iya shirya dabaru iri iri, amma sai nufin Ubangiji ne zai tabbata. 22 Abin kunya ne mutum ya zama mai haɗama, matalauci kuma ya fi maƙaryaci. 23 Ka yi tsoron Ubangiji za ka yi tsawon rai, ka kuma sami biyan bukata, ba abin da zai cuce ka. 24 Waɗansu mutane sun cika lalaci, ko abincinsu ba su iya taunawa. 25 Za a hukunta mai fāriya saboda ya zama ishara ga mutanen da ba su san kome ba, mutum mai hikima yakan koya sa'ad da aka tsauta masa. 26 Sai marar kunya, marar mutunci yake wulakanta mahaifinsa, ko ya kori mahaifiyarsa daga gidansa. 27 Ɗana idan ka bar yin nazari za ka manta da abin da ka riga ka koya. 28 Ba gaskiya ga mashaidin da ya yi niyyar cutar wani. Mugaye suna ƙaunar yin mugunta. 29 Wawa mai fāriya hakika zai sha d�ka.

Karin Magana 20

1 Ruwan inabi da barasa sukan sa ka ka yi ta tā da murya, ka zama wawa. Wauta ce mutum ya bugu. 2 Ka ji tsoron fushin sarki kamar yadda za ka ji tsoron zaki mai ruri, sa shi ya yi fushi kashe kai ne. 3 Kowane wawa yakan fara yin jayayya, abin da ya fi daraja shi ne ka fita ka ware kanka. 4 Manomin da ya cika lalaci, ya kasa nome gonakinsa a kan kari, a lokacin girbi ba zai sami kome ba. 5 Tunanin mutum kamar ruwa yake a rijiya mai zurfi, sai mai basira ya iya ya jawo shi. 6 Kowa gani yake shi mai biyayya ne, mai aminci. Amma ina? Ko ka yi ƙoƙari ka sami amintacce ɗaya daga cikinsu, ba za ka samu ba. 7 'Ya'yan da mahaifinsu amintacce ne, wanda yake aikata abin da yake daidai, sun yi sa'a. 8 Sarkin da yake yin shari'a ta gaskiya, da ganin mugunta ya san ta. 9 Wane ne zai iya cewa lamirinsa garau yake, har da zai ce ya rabu da zunubinsa? 10 Allah yana ƙin masu ma'aunin algus. 11 Ayyukan da saurayi yake yi suke bayyana yadda yake, kana iya sani ko shi amintacce ne, mai nagarta. 12 Ubangiji ya ba mu ido don mu gani, ya ba mu kunne don mu ji. 13 Idan barci ne sana'arka za ka talauce. Ka yi ta aiki za ka sami wadataccen abinci. 14 Mai saye yakan yi kukan tsada a kullum, amma yakan tafi ya yi ta fāriya a kan ya iya ciniki. 15 In ka san abin da kake faɗa, kana da wani abu wanda ya fi zinariya da lu'ulu'ai tamani. 16 Sai wawa kaɗai yake ɗaukar lamunin biyan basusuwan da baƙo ya ci, ya kamata a karɓi dukiyarsa jingina. 17 Abin da ka samu ta hanyar zamba kakan ji daɗinsa kamar abinci mai kyau, amma ko ba jima ko ba daɗe zai zama kamar yashi cike da bakinka. 18 Ka nemi kyakkyawar shawara za ka yi nasara, kada ka jefa kanka cikin yaƙi ba tare da shiri ba. 19 Mai baza jita-jita ba shi da asiri, ka yi nesa da mai yawan surutu. 20 Idan ka zagi iyayenka, za ka mutu kamar fitilar da ta mutu cikin duhu. 21 Dukiyar da aka same ta a sawwaƙe, amfaninta kaɗan ne. 22 Kada ka ɗaukar wa kanka fansa, ka dogara ga Ubangiji shi zai yi sakamako. 23 Ubangiji yana ƙin waɗanda suke awo da ma'aunin algus. 24 Ubangiji ya ƙayyade hanyoyinmu, ta ƙaƙa wani zai ce ya fahimci rai? 25 Ka yi tunani a hankali kafin ka yi wa'adi za ka miƙa wa Allah wani abu, mai yiwuwa ne ka yi da na sani nan gaba. 26 Sarki mai hikima zai bincika ya gane waɗanda suke aikata mugunta, ya hukunta su ba tausayi. 27 Ubangiji ne ya ba mu hankali da lamiri, ba za mu iya ɓoye masa ba. 28 Sarki zai zauna dafa'an cikin mulkinsa muddin yana mulki da aminci, da adalci, da daidaita. 29 Ƙarfin samari abin darajantawa ne, furfurar tsofaffi abar girmamawa ce. 30 Wani lokaci sai mun sha wuya muke sāke hanyoyinmu.

Karin Magana 21

1 Ubangiji ne yake mallakar tunanin sarki a sawwaƙe kamar yadda yake yi da ruwan rafi. 2 Ko da a ce dukan abin da kake yi daidai ne, ka tuna fa Ubangiji ya san manufarka. 3 Ubangiji ya fi so ka yi abin da yake daidai, mai kyau kuma, fiye da ka miƙa masa hadayu. 4 Girmankai da fāriya suke bi da mugaye, wannan kuwa zunubi ne. 5 Yin shiri a tsanaki zai kai ka ga biyan bukatarka, idan kuwa ka cika gaggawa ba za ka sami abin da zai ishe ka ba. 6 Dukiyar da aka tara ta hanyar rashin gaskiya takan ƙare nan da nan, takan kuma kai ga mutuwa. 7 Mugaye, tasu ta ƙare saboda muguntarsu, gama sun ƙi yin abin da yake daidai. 8 Mutane masu laifi sukan bi ta karkatacciyar hanya, marasa laifi kuwa suna aikata abin da yake daidai. 9 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mace mai mita. 10 Mugaye sun zaƙu su aikata mugunta, ba su yi wa kowa jinƙai. 11 Sa'ad da aka hukunta mai girmankai, ko marar tunani yakan koyi wani abu, mutum mai hikima yakan koyi abin da ake koya masa. 12 Adali ya san tunanin mugaye, yakan kuwa zama sanadin lalacewarsu. 13 Idan ka ƙi jin kukan matalauci, naka kukan da kake yi na neman taimako, ba za a ji ba. 14 Kyauta a asirce takan kwantar da zuciyar wanda yake fushi da kai. 15 Sa'ad da aka yi adalci mutanen kirki sukan yi murna, amma mugaye sukan yi baƙin ciki. 16 Mutuwa tana jiran wanda ya ƙi bin hanyar hankali. 17 Sa kai cikin nishaɗi, wato shan ruwan inabi, da cin abinci mai tsada, ba zai bar ka ka tara dukiya ba. 18 Wahalar da mugaye suke so su jawo wa mutanen kirki, za ta koma kansu. 19 Gara ka zauna a hamada, da ka zauna tare da mace mai mita, mai yawan kai ƙara. 20 Mutane masu hikima suna zaune da wadata da nishaɗi, amma wawaye da zarar sun sami kuɗi sukan kashe su nan da nan. 21 Ka yi alheri ka yi aminci, za ka yi tsawon rai waɗansu kuma za su girmama ka, su yi maka abin da yake daidai. 22 Sarkin yaƙi mai wayo yakan ci birnin da jarumawa suke tsaro, ya rushe garun da suke taƙama da shi. 23 Idan ba ka so ka shiga wahala, ka lura da abin da kake faɗa. 24 Ba kalmar da ta fi “Fāɗin rai” dacewa ga mutum mai girmankai, mai fāriya marar tunani. 25 Malalacin mutumin da ya ƙi yin aiki, kansa yake kashewa. 26 Duk abin da yake tunani dukan yini, shi ne a kan abin da yake so ya samu. Amma adali ko ta ƙaƙa yakan bayar da hannu sake. 27 Ubangiji yana ƙin hadayar da mugaye suka miƙa masa, tun ba wadda suka miƙa ta da mugun nufi ba. 28 Ba a gaskata shaidar maƙaryaci, amma mutumin da yakan yi tunani a kan al'amura, akan karɓi tasa. 29 Adali ya tabbatar da kansa, haka ma mugun mutum yakan yi da'awa, cewa shi ma ya tabbatar da kansa. 30 Hikima, da haziƙanci, da basira, ba kome suke ba gāba da Ubangiji. 31 Kana iya shirya dawakai don zuwa yaƙi, amma nasara ta Ubangiji ce.

Karin Magana 22

1 Idan ya zama dole ne ka zaɓa tsakanin kyakkyawan suna ko dukiya, to, ka zaɓi kyakkyawan suna, tagomashi kuma ya fi azurfa da zinariya. 2 Ba bambanci tsakanin mawadaci da matalauci, gama Ubangiji ne ya halicce su duka. 3 Mutum mai hankali, in ya ga wahala tana zuwa yakan kauce mata, amma shashasha yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani. 4 Kana da tsoron Ubangiji, ka yi tawali'u, za ka arzuta, ka ɗaukaka, ka sami tsawon rai. 5 Idan kana ƙaunar ranka ka nisanci tarkunan da aka kafa a hanya don su kama mugaye. 6 Ka koya wa yaro yadda zai yi zamansa, zai kuwa tuna da ita dukan kwanakinsa. 7 Matalauta su ne bayin attajirai, bawa ne kai ga wanda ka ci bashi a gare shi. 8 In ka shuka rashin gaskiya masifa ce za ta tsiro, wato hukunci mai tsanani wanda zai hallakar da kai. 9 Ka zama mai hannu sake, ka riƙa ba matalauta abincinka, za a sa maka albarka saboda haka. 10 Ka rabu da mutum mai fāriya, mai gardama, mafaɗaci, hatsaniya za ta ƙare. 11 In ka yi ladabi za ka zama aminin sarki, gama yana ƙaunar amintaccen mutum. 12 Ubangiji yana lura ya ga an riƙe gaskiya sosai ta wurin ƙin yarda da maganganun ƙarya. 13 Malalaci yakan yi zamansa a gida, yakan ce, “Zaki zai kama ni in na fita waje.” 14 Zina tarko ce, takan kama waɗannan waɗanda Ubangiji yake fushi da su. 15 Halin yara ne su yi wauta da waɗansu abubuwa na rashin kula, amma tsumagiya za ta koya musu abin da ya fi kyau. 16 Idan attajirai kake yi wa kyauta, kana kuma zaluntar matalauta don ka arzuta, kai kanka za ka talauce.

Umarnai da Dokoki

17 Ka kasa kunne zan koya maka abin da masu hikima suka faɗa, yi nazari a kan koyarwarsu. 18 Za ka yi murna in ka tuna da su, ka iya faɗarsu. 19 Ina so ka dogara ga Ubangiji, don haka zan faɗa maka su yanzu. 20 Na rubuta maka karin magana, suna ƙunshe da ilimi da kyakkyawar shawara. 21 Zan koya maka ainihin gaskiya, domin sa'ad da aka aike ka ka nemo ta, za ka iya kawo amsa daidai. 22 Kada ka ƙwari matalauci don ka fi shi, kada ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari'a. 23 Ubangiji zai yi magana dominsu a kan shari'ar da suke yi, ya nemi ran duk wanda yake neman rayukansu. 24 Kada ka yi abuta da mutane masu zafin fushi, ko masu zafin rai. 25 Mai yiwuwa ne ka koyi irin ɗabi'unsu, har ka kasa sākewa. 26 Kada ka yi alkawarin ɗaukar wa wani lamuni, 27gama idan ka kāsa biya har gadonka ma za su ɗauke. 28 Kada ka kawar da shidar kan iyaka wadda kakanninka suka kafa. 29 Ka nuna mini mutumin da yake aiki mai kyau, ni kuwa in nuna maka mutumin da ya fi duka, wanda ya cancanci ya zauna tare da sarakuna.

Karin Magana 23

1 Sa'ad da ka zauna cin abinci tare da babban mutum, ka tuna da yadda yake. 2 Idan kai mai son ci da yawa ne sai ka kanne. 3 Kada ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da yake gabanku, zai yiwu wayo yake so ya yi maka. 4 Ka zama mai isasshiyar hikima, kada ka gajiyar da kanka garin ƙoƙarin neman dukiya. 5 Kuɗinka sun iya ƙarewa kamar ƙyiftawar ido, kamar suna da fikafikai su tashi kamar gaggafa. 6 Kada ka ci abincin marowaci, ko ka yi haɗamar kyakkyawan abincin da ya sa a gabanka. 7 Zai ce, “Bari a ƙara maka,” amma ba haka yake nufi ba. Kamar gashi yake a cikin maƙogwaronka. 8 Za ka harar da abin da ka ci, dukan daɗin bakinka zai tafi a banza. 9 Kada ka yi wa wawa magana irin ta haziƙai, gama ba zai yaba da maganarka ba. 10 Kada ka kuskura ka kawar da shaidar iyaka, ko ka ƙwace gonar marayu. 11 Ubangiji Mai Iko shi ne kāriyarsu, shi zai yi magana dominsu. 12 Ka mai da hankali ga malaminka, ka koyi dukan abin da kake iyawa. 13 Kada ka bar yaro ba horo, gama ko ka duke shi ba za a kashe shi ba. 14 Lalle ne za ka ceci ransa. 15 Ɗana, idan ka zama mai hikima zan yi murna ƙwarai. 16 Zan yi murna idan na ji kana faɗar magana da hikima. 17 Kada ka yi ƙyashin masu aikata zunubi tsoron Ubangiji kaɗai za ka sa a gaba. 18 Idan haka ta samu za ka yi farin ciki nan gaba. 19 Ka saurara, ya ɗana, ka zama mai hikima. Ka yi tunani mai zurfi a kan hanyarka. 20 Kada ka zauna da mashayan ruwan inabi, ko masu haɗama. 21 Gama bugaggu da ruwan inabi da masu zarin ci za su zama matalauta. Idan iyakar abin da kake yi daga ci sai barci ne, nan da nan za ka ga kana saye da tsummoki. 22 Ka kasa kunne ga mahaifinka, gama da ba dominsa ba, da ba ka, sa'ad da mahaifiyarka ta tsufa ka nuna mata godiyarka. 23 Gaskiya, da hikima, da ilimi, da hankali, sun cancanta a saye su, kome tamaninsu. 24 Mahaifin adali yana da dalilin yin murna. Zai yi fāriya a kan ɗa mai hikima. 25 Ka sa mahaifinka da mahaifiyarka su yi fāriya da kai, ka sa mahaifiyarka farin ciki. 26 Ɗana ka mai da hankali sosai, irin zamana ya zamar maka kyakkyawan misali. 27 Karuwa, da mata mazinata, tarkon mutuwa ne su. 28 Sukan laɓe su jira ka kamar mafasa, suna sa mutane da yawa su zama marasa aminci. 29 Wa ake yi wa kaito? Wa yake da baƙin ciki? Wane ne mafaɗaci? Wa yake yin gunaguni? Wa yake da raunuka ba dalili? Wa yake da jan ido? 30 Sai riƙaƙƙen mashayi wanda yake gaurayar ruwan inabi. 31 Kada ka bar ruwan inabi ya jarabce ka, ko da yake ja wur yake, har kana iya ganin kanka a cikin ƙoƙon, yana kuwa da kyan gani sa'ad da kake motsa shi. 32 Kashegari za ka ji kamar maciji mai dafi ne ya sare ka. 33 Idanunka za su riƙa gane-gane, ba za ka iya tunani ko ka faɗi magana sosai ba. 34 Za ka ji kamar kana can cikin teku, jirin teku na ɗibarka kana lilo a kan rufin jirgin ruwa da yake tangaɗi. 35 Za ka ce, “Lalle an doke ni, sosai an daddoke ni amma ban san lokacin ba, me ya sa ban farka ba? Ina bukatar in ƙara sha.”

Karin Magana 24

1 Kada ka ji ƙyashin mugaye, kada ka yi ƙoƙarin yin abuta da su. 2 Duk tunaninsu na yin mugunta ne, a duk lokacin da suka buɗe bakinsu sai sun cuci wani. 3 An gina gidaje a kan harsashin hikima da fahimi. 4 Ta wurin ilimi a kan ƙawata ɗakuna da kyawawan kayayyaki masu tamani. 5 Mai hikima ƙaƙƙarfa ne, i, mai ilimi yana daɗa ƙarfi. 6 Banda wannan ma, dole ne ka shisshirya a natse kafin ka kama yaƙi. Bisa ga shawarwarin da za ka samu ne za ka yi nasara. 7 Kalmomi masu hikima sun yi wa wawa zurfin ganewa ƙwarai, ba shi da ta cewa sa'ad da ake magana a kan muhimman abubuwa. 8 Idan a koyaushe shirye-shiryen mugunta kake, za ka yi suna a kan kuta tashin hankali. 9 Kowace irin dabarar da wawa yake tunani a kanta zunubi ne. Jama'a suna ƙin mutum mai rainako. 10 Idan ba ka da ƙarfi a lokacin hargitsi, hakika ka tabbata marar ƙarfi. 11 Kada ka ji nauyin ceton wanda ake janye da shi zuwa inda za a kashe shi. 12 Mai yiwuwa ne ka ce kai ba ruwanka, amma Allah ya sani, yana kuwa auna manufofinka. Yana lura da kai, ya kuwa sani. Yakan sāka wa mutane a kan abin da suke aikatawa. 13 Ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau. Kamar yadda kakin zuma yake da zaƙi a harshenka, 14 haka ilimi da hikima suke da amfani ga ranka. Ka same su, a gaba za ka yi farin ciki. 15 Kada ka shirya dabarun yi wa amintacce ƙwace, ko ka ƙwace masa gidansa, wannan mugunta ce. 16 Ko sau nawa amintaccen mutum ya faɗi, ba abin damuwa ba ne, gama a koyaushe zai sāke tashi, amma masifa takan hallaka mugaye. 17 Kada ka yi murna sa'ad da bala'i ya aukar wa maƙiyinka. 18 Ubangiji zai sani in kana murna, ba kuwa zai so haka ba, mai yiwuwa ne ba zai hukunta shi ba. 19 Kada ka damu saboda mugaye, kada ka yi ƙyashin masu aikata abin da ba daidai ba. 20 Gama mugun mutum ba shi da sa zuciya, ba abin da zai sa zuciya a kansa nan gaba. 21 Ɗana, ka yi tsoron Ubangiji, ka kuma ji tsoron sarki, kada ka yi harkar kome da mutanen da suka tayar musu. 22 Irin waɗannan mutane sukan hallaka farat ɗaya. Ka taɓa yin tunani a kan bala'in da Allah ko sarki sukan aukar?

Waɗansu sauran Karin Magana na Hikima

23 Masu hikima kuma sun faɗi waɗannan abu. Kuskure ne alƙali ya yi son zuciya. 24 Idan ya kuɓutar da mugu, kowane mutum da yake a duniya zai la'anta shi ya ƙi shi. 25 Alƙalan da suke hukunta wa mai laifi kuwa, za su arzuta, su ji daɗin kyakkyawan suna. 26 Amsar gaskiya ita ce alamar abuta ta ainihi. 27 Kada ka gina gidanka ka kafa shi, sai ka gyara gonakinka, ka tabbata za ka sami abin zaman gari. 28 Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isasshen dalili ba, ko ka faɗi ƙarya a kansa. 29 Kada ka ce, “Zan yi masa daidai da yadda ya yi mini, zan rama masa!” 30 Na ratsa ta gonakin inabin wani malalaci, dakiki, 31 suna cike da ƙayayuwa, ciyayi sun sha kansu, katangar dutse da take kewaye da su ta faɗi. 32 Da na dubi wannan, na yi tunani a kansa, ya zamar mini ishara. 33 “Yi ta ruruminka, ci gaba da barcinka, rungume hannuwanka don ka shaƙata.” 34 Amma sa'ad da kake ta sharar barci fatara za ta auka maka kamar ƙungiyar 'yan fashi.

Karin Magana 25

Waɗansu sauran Karin Magana na Sulemanu

1 Ga waɗansu sauran karin maganar Sulemanu waɗanda magatakardan Hezekiya Sarkin Yahuza suka juya. 2 Muna girmama Allah saboda abin da ya rufe, muna girmama sarakuna saboda abin da suka ba da bayaninsa. 3 Ba ku taɓa sanin abin da sarki yake tunani ba, gama tunaninsa sun fi ƙarfinmu. Kamar nisan sararin sama suke ko zurfafan teku. 4 Ka tace azurfa, gwani kuwa zai yi wani kyakkyawan abu da ita. 5 A kawar da mugayen mashawarta daga gaban sarki, hukumarsa za ta shahara a kan adalci. 6 Sa'ad da kake tsaye a gaban sarki, kada ka nuna kai wani abu ne, kana kai kanka inda Allah bai kai ka ba. 7 Gara a roƙe ka ka hau zuwa babban matsayi, da a faɗa maka ka ba da wurin da kake ga wanda ya fi ka maƙami. 8 Kada ka yi garajen kai ƙara a majalisa. Idan wani mashaidi ya nuna kai kake da kuskure, me za ka yi? 9 Idan kai da maƙwabcinka kun saɓa, ku daidaita a tsakaninku, kada a tona asiri. 10 Mai yiwuwa ne wani ya ji ya zarge ku, ba za ku taɓa rabuwa da wannan kunya ba. 11 Manufar da aka bayyana sosai kamar zubin zinariya take wanda aka yi a kan azurfa. 12 Faɗakarwar da mutumin da ya gogu da al'amuran duniya ya yi ga wanda yake da niyya ya kasa kunne, tamaninta ya fi na zoben zinariya, ko kayan ado da aka yi da zinariya tsantsa. 13 Amintaccen manzo yakan wartsakar da wanda ya aike shi, kamar ruwan sanyi yake a lokacin zafi. 14 Mutanen da suke yin alkawari, ba su cikawa, kamar holoƙo suke, hadirin kaka. 15 Rinjayen da aka yi cikin haƙuri yakan rushe ƙaƙƙarfar tsayayya, har ma yakan i wa masu ƙarfin gaske. 16 Kada ka kuskura ka sha zuma gaba da kima, in ya yi maka yawa za ka yi hararwa. 17 Kada ka cika ziyartar maƙwabcinka, ko zai gaji da kai har ya ƙi ka. 18 Mutumin da yakan faɗi ƙarairayi a kan maƙwabcinsa, shi kamar kakkaifan takobi ne, ko kulki, ko kibiya mai tsini. 19 Dogara ga marar aminci a lokacin hargitsi, kamar ƙoƙarin yin tauna da ruɓaɓɓun haƙora ne, ko yin tafiya da mai gurguwar ƙafa, 20 ko kuma ka yi ƙoƙarin jin ɗumi ta wurin tuɓe tufafinka a ranar da ake sanyi. Raira waƙa ga mai baƙin ciki kamar marmasa gishiri a kan rauni ne. 21 Idan maƙiyinka yana jin yunwa ka cishe shi, idan yana jin ƙishi ka ba shi abin sha. 22 Za ka sa ya sha kunya, Ubangiji kuma zai sāka maka. 23 Iskar arewa takan kawo ruwan sama, haka kuma jita-jita takan kawo fushi. 24 Gara zama a saƙo da zama a gida ɗaya tare da mata mai mita. 25 Jin labari mai daɗi wanda ba ka zato, yana kamar shan ruwan sanyi ne a sa'ad da ka sha rana kana jin ƙishi. 26 Mutumin kirki wanda yakan yarda da mugun yana tunasshe ka da ƙazantattun maɓuɓɓuga ko rijiya mai dafi. 27 Kamar yadda shan zuma da yawa ba shi da kyau a gare ka, haka kuma ƙoƙarin neman yabo mai yawa yake. 28 Idan ba ka iya danne fushinka ba, ka zama mai kasala kamar birnin da ba shi da garuka, yana buɗe don a faɗa masa.

Karin Magana 26

1 Yabo bai dace da wawa ba, kamar yadda dusar ƙanƙara ba ta dace da lokacin zafi ba, ko ruwan sama a lokacin girbi. 2 La'ana ba za ta kama ka ba, sai dai in ka cancance ta. Tana kamar tsuntsayen da suke firiya da dare ba za su sauka ba. 3 Sai ka fyaɗi doki, ka sa wa jaki linzami, wawa kuma sai ka doke shi. 4 Idan ka amsa tambayar wauta, ka zama wawa daidai da mutumin da ya yi tambayar. 5 Ka amsa wauta ga tambayar wauta, wanda ya yi tambayar zai gane wawancinsa. 6 Mutumin da ya sa wawa ya isar masa da saƙo ya datse ƙafafunsa, yana nemar wa kansa wahala. 7 Wawa yakan yi amfani da karin magana kamar yadda tauyayyen mutum yake amfani da ƙafafunsa. 8 Wanda ya yabi wawa yana kama da wanda ya ɗaura dutse a majajjawa. 9 Karin magana a bakin wawa kamar sukar ƙaya ce a hannun mai maye. 10 Wanda ya ɗauki wawa aiki yana cutar duk wanda aikin ya shafa. 11 Wawan da yake maimaita aikin wautarsa yana kama da kare mai yin amai ya koma ya tanɗe. 12 Gwamma riƙaƙƙen wawa da mutum mai ganin kansa mai hikima ne. 13 Don me malalaci yakan kasa fita daga gida? Zaki yake tsoro? 14 Malalaci yana ta jujjuyawa a gadonsa kamar yadda ƙyauren ƙofa yake juyawa. 15 Malalaci yana sa hannu cikin ƙwaryar abinci, amma ya kāsa kaiwa bakinsa. 16 Malalaci yana ganin kansa mai hikima ne fiye da mutum bakwai waɗanda suke da dalilai a kan ra'ayinsu. 17 Mutumin da ya tsoma baki cikin jayayyar da ba ta shafe shi ba sa'ad da yake wucewa, yana kama da mutum wanda yake kama kare a kunne. 18-19 Mutum wanda yakan ruɗi maƙwabcinsa sa'an nan ya ce, wasa yake yi kawai, yana kama da mahaukaci wanda yake wasa da wuta, da kibau, da mutuwa. 20 Idan ba itace wuta takan mutu, haka kuma idan ba mai gulma ba za a yi jayayya ba. 21 Kamar yadda gawayi yake ga garwashin wuta, itace kuma ga wuta, haka mai gardama yake ga jayayya. 22 Kamar yadda lomar abinci mai daɗi takan gangara can cikin ciki haka maganar mai gulma take. 23 Bakin da ba ya faɗar gaskiya, da zuciya mai ƙiyayya suna kama da kaskon da aka dalaye da azurfar da ba a tace ba. 24 Mai yin ƙiyayya yakan ɓoye ta da maganar bakinsa, yana kuma ƙunshe da munafunci. 25 Sa'ad da yake magana mai kyau kada ka gaskata shi, domin zuciyarsa tana cike da mugunta. 26 Ko da yake kila zai ɓoye ƙiyayyarsa, duk da haka muguntarsa za ta bayyana ga mutane. 27 Wanda ya haƙa ramin mugunta shi zai faɗa ciki, wanda kuma ya mirgino dutse, zai fāɗo a kansa. 28 Maƙaryaci yana ƙin wanda ya yi wa ƙarya, mai daɗin baki kuma yakan aikata ɓarna.

Karin Magana 27

1 Kada ka yi fāriya a kan abin da za ka yi gobe domin ba ka san abin da zai faru daga yanzu zuwa gobe ba. 2 Bari waɗansu su yabe ka ko da baƙi ne, faufau kada ka yabi kanka. 3 Dutse da yashi suna da nauyi ƙwarai, amma nauyin wahalar da wawa zai haddasa ya fi nasu duka. 4 Fushi mugun abu ne mai hallakarwa, amma duk da haka bai kai ga kishi ba. 5 Gara ka tsauta wa mutum a fili da ka bar shi ya zaci ba ka kula da shi ba sam. 6 Aboki aboki ne ko da ya cuce ka, amma maƙiyi ko ya rungume ka kada ka sake! 7 Wanda ya ƙoshi ba zai ko kula da zuma ba, amma wanda yake jin yunwa abinci mai ɗaci zaƙinsa yake ji. 8 Mutumin da ya bar gida yana kama da tsuntsun da ya bar sheƙarsa. 9 Turare da man ƙanshi sukan sa ka ji daɗi, haka abuta ta ainihi takan ƙara maka ƙarfi. 10 Kada ka manta da abokanka, ko abokan mahaifinka. Idan kana shan wahala kada ka nemi taimako wurin ɗan'uwanka. Maƙwabci na kusa yana iya taimakonka fiye da ɗan'uwan da yake nesa. 11 Ɗana, ka zama mai hikima, ni kuwa zan yi farin ciki, zan iya amsa kowace irin s�kar da wani zai yi mini. 12 Mutum mai hankali yakan hango hatsari ya kauce masa, amma mutumin da ba shi da kula, yakan kutsa kai ciki, daga baya ya yi da na sani. 13 Ka karɓe tufar wanda ya zamar wa baƙo lamuni, da kuma wanda ya zama lamunin karuwa. 14 In ka farkar da abokinka da babbar murya tun da sassafe, daidai ne da zaginsa. 15 Mace mai mita kamar ɗiɗɗigar ruwa take ba ƙaƙƙautawa. 16 Kaƙa za ka iya sa ta ta kame bakinta? Ka taɓa ƙoƙarin tsai da iska? Ko kuwa ka taɓa ƙoƙarin dintsi mai a tafin hannunka? 17 Daga wurin mutane mutane suke koyo, kamar yadda a kan wasa ƙarfe da ƙarfe. 18 Ka lura da itacen ɓaure, zai yi 'ya'ya ka ci. Baran da ya lura da maigidansa za a girmama shi. 19 Yadda kake ganin fuskarka a ruwa, haka kake ganin kanka a zuciyarka. 20 Muradin mutum kamar lahira yake, a kullum ba ya ƙoshi. 21 Da wuta ake gwada azurfa da zinariya, amma yabon da ake yi wa mutum shi ne magwajinsa. 22 Ko da za ka doki wawa ka bar shi tsakanin rai da mutuwa, duk da haka yana nan da wautarsa kamar yadda yake. 23 Ka lura da garkunan tumakinka da na shanunka da kyau iyakar iyawarka, 24 domin dukiya ba ta tabbata har abada, al'ummai ma haka ne. 25 Ka yanki ingirici, lokacin da yake toho kana iya yankar ciyawa a gefen tuddai. 26 Kana iya yin tufafi da ulun tumakinka, kana iya sayen gona da kuɗin awakinka. 27 Madarar awakinka za ta zama abincinka kai da iyalinka, da kuma barorinka 'yan mata.

Karin Magana 28

Mugaye da Adalai

1 Mugun mutum yakan gudu, alhali kuwa ba mai korarsa, amma amintaccen mutum kamar zaki yake, ba shi da tsoro. 2 Al'umma za ta ƙarfafa ta jure idan shugabanninta masu basira ne, masu hankali. Amma idan ƙasar mai aikata zunubi ce za ta sami shugabanni da yawa. 3 Mai mulki wanda yake zaluntar talakawa, ya zama kamar ruwa mai lalatar da amfanin gona. 4 Wanda ba ya bin doka tare da mugaye yake, amma idan kana bin doka kai abokin gāban mugaye ne. 5 Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada sun san ta sosai. 6 Gara ka zama matalauci mai aminci da ka zama mawadaci, marar aminci. 7 Saurayi wanda ya kiyaye doka mai basira ne shi, amma wanda yake abuta da 'yan iska zai zama mai jawo wa mahaifinsa kunya. 8 Idan kana tara dukiya ta wurin ba da bashi da ruwa kana kuma ƙwarar jama'a, dukiyarka za ta koma ga wanda yake yi wa talakawa alheri. 9 Idan ka ƙi biyayya ga doka, Allah zai ƙi jin addu'o'inka. 10 Idan ka yaudari mutumin kirki don ya faɗa cikin mugunta, kai kanka ne za ka fāɗa cikin tarkon da ka haƙa. Marar laifi kuwa zai sami babban sakamako. 11 Attajirai, a koyaushe, zato suke su masu hikima ne, amma matalauci mai tunani ya fi sanin abin da yake daidai. 12 Sa'ad da mutanen kirki suke sarauta, kowa da kowa yakan yi biki, amma sa'ad da mugaye suka kama mulki mutane sukan riƙa ɓuya. 13 Ba za ka taɓa cin nasara a zamanka ba muddin kana ɓoye laifofinka. Ka hurta zunubanka ka tuba, sa'an nan Allah zai yi maka jinƙai. 14 Mutumin da yake tsoron Ubangiji koyaushe, zai yi farin ciki, amma idan ya taurare zai lalace. 15 Talakawa ba su da wani taimako sa'ad da suke ƙarƙashin mulkin mugun. Abin tsoro ne shi kamar zaki mai ruri, ko beyar mai sanɗa. 16 Mai mulki wanda ba shi da basira yakan zama mai mugun tsanani. Amma wanda yake ƙin rashin aminci, ko ta ƙaƙa zai daɗe yana mulki. 17 Mutumin da yake da laifin kisankai, yana haƙa wa kansa kabari da gaggawa. Kada ka yi ƙoƙarin hana shi. 18 Ka yi aminci za ka zauna lafiya, idan kuwa ka yi rashin aminci za ka fāɗi. 19 Manomin da yake aiki sosai, zai sami wadataccen abinci, amma mutanen da suke zaman banza koyaushe, za su zama matalauta. 20 Amintaccen mutum zai cika kwanakinsa lafiya, amma idan kana so ka sami dukiya dare ɗaya, za a hukunta ka. 21 Nuna sonkai mugun abu ne, waɗansu alƙalai sukan aikata mugunta saboda 'yar ƙaramar rashawa. 22 Mutum mai haɗama yana gaggawar samun dukiya, bai kuwa sani ba, ashe, fatara ce za ta same shi. 23 Wanda ya tsauta wa mutum zai sami yabo daga baya, fiye da wanda ya yi masa daɗin baki. 24 Wanda yake yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa sata, yana kuwa tsammani ba laifi ba ne, daidai da ɓarawo yake. 25 Mutum mai haɗama yana haddasa tashin hankali, amma wanda ya dogara ga Ubangiji zai sami wadar zuci. 26 Wanda yake dogara ga son zuciyarsa, wawa ne, amma wanda yake tafiya cikin hikima zai kuɓuta. 27 Wanda yake bayarwa ga matalauta, ba zai talauce ba, amma wanda bai kula da su ba, mutane da yawa za su la'ance shi. 28 Mutane sukan ɓuya sa'ad da mugaye suka sami iko, amma sa'ad da iko ya fita daga hannunsu adalai sukan ƙaru.

Karin Magana 29

1 Wanda ake ta tsauta wa a kai a kai, amma ya taurare, ba makawa tasa ta ƙare farat ɗaya. 2 Sa'ad da masu adalci suke mulki, jama'a sukan yi murna, amma sa'ad da mugaye suke mulki, jama'a sukan yi nishi. 3 Wanda yake ƙaunar hikima yana faranta zuciyar mahaifinsa. Amma wanda yake abuta da karuwai zai lalatar da dukiyarsa. 4 Sarkin da yake aikata adalci ƙasarsa za ta yi ƙarƙo, amma wanda yake karɓar rashawa zai lalatar da ƙasar. 5 Mutum wanda yake yi wa maƙwabcinsa daɗin baƙi yana kafa wa kansa tarko. 6 Laifin mugun zai zama tarko a gare shi, amma adali zai raira waƙa, ya yi farin ciki. 7 Adali yana sane da hakkin matalauta, amma mugun bai san wannan ba. 8 Ashararai sukan sa wa birni wuta, amma masu hikima sukan kwantar da hasala. 9 Idan gardama ta shiga tsakanin mai hikima da wawa, sai wawa ya yi ta fushi, ko kuwa ya yi ta dariya, gardamar dai ba za ta ƙare ba. 10 Mutane masu kisankai suna ƙin amintaccen mutum, amma adalai za su kiyaye ransa. 11 Wawa yakan nuna fushinsa koyaushe, amma mutum mai hikima yakan kanne fushinsa. 12 Idan mai mulki yana kasa kunne ga maganganun ƙarya, dukan ma'aikatansa za su zama maƙaryata. 13 Matalauci da azzalumi suna tarayya a abu ɗaya, wato dukansu Ubangiji ne yake ba su ganin gari. 14 Idan sarki yana yi wa talakawa shari'ar gaskiya, zai daɗe yana mulki. 15 Horo da tsautawa suna ba da hikima, amma yaron da aka sangarta zai jawo wa mahaifiyarsa kunya. 16 Sa'ad da mugaye suke mulki, laifofi suka ƙaru, amma adalai za su ga faɗuwar waɗannan mutane. 17 Ka hori ɗanka zai daɗaɗa maka rai, ya kuma faranta maka zuciya. 18 Inda ba a bin faɗar Allah, jama'a za su kangare, amma mai farin ciki ne wanda yake kiyaye dokar Allah. 19 Bara ba ya horuwa ta wurin magana kawai, gama ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba. 20 Ka ga mutum mai garajen yin magana? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi. 21 Baran da aka shagwaɓa tun yana yaro, a ƙarshe zai ɗauki kansa tankar magājin gida. 22 Mutum mai saurin fushi yakan ta da faɗa, mai zafin rai kuma yakan aikata laifi da yawa. 23 Girmankan mutum zai jawo masa ƙasƙanci, amma za a girmama mai tawali'u. 24 Abokin ɓarawo mugun maƙiyin kansa ne, yana jinsa yana ta rantsuwa, amma ba zai ce kome ba. 25 Jin tsoron mutane tarko ne, amma wanda ya dogara ga Ubangiji za a ɗaukaka shi. 26 Mutane da yawa sukan nemi farin jini daga wurin mai mulki, amma Ubangiji ne yake yi wa mutum adalci. 27 Mutum marar gaskiya abin ƙyama ne ga adali, adali kuma abin ƙyama ne ga mugun.

Karin Magana 30

Hikimar Agur

1 Waɗannan su ne maganar Agur ɗan Yake, da ya yi wa Etiyel da Yukal, 2 “Hakika wautata ta sa na zama kamar dabba ba mutum ba, Ba ni kuwa da fahimi irin na mutum. 3 Ban koyi hikima ba, Ban kuwa san kome game da Allah ba. 4 Wa ya taɓa hawa cikin Sama ya sauko? Wa ya taɓa kama iska cikin tafin hannunsa? Wa ya taɓa ƙunshe ruwa cikin rigarsa? Wa kuma ya kafa iyakar duniya? Ina sunansa, ina kuma sunan ɗansa? Hakika ka sani! 5 “Kowace maganar Allah takan tabbata. Shi garkuwa ne ga waɗanda suke fakewa a wurinsa. 6 Kada ka yi ƙari a kan maganarsa, don kada ya tsauta maka, a kuma bayyana kai maƙaryaci ne.”

Waɗansu Karin Magana Kuma

7 Abu biyu na roƙe ka, kada ka hana mini su kafin in mutu. 8 Ka kawar da ƙarya nesa da ni. Kada ka ba ni talauci ko dukiya, sai dai ka ba ni abinci daidai da bukatata, 9 don kada in wadata, har in yi musunka, in ce, “Wane ne Ubangiji?” Kada kuwa in yi talauci har in yi sata in saɓi sunan Allahna. 10 Kada ka kushe bara a wurin maigidansa domin kada ka yi laifin da zai sa a la'ance ka. 11 Akwai waɗansu mutane da sukan zagi iyayensu maza, ba sukan kuma nuna godiya ga iyayensu mata ba. 12 Akwai waɗansu mutane da suke ganin kansu tsarkaka ne, alhali kuwa ƙazamai ne su. 13 Akwai waɗansu mutane da suke yi wa jama'a ƙallon raini suna ɗaurin gira. 14 Akwai waɗansu mutane waɗanda haƙoransu takuba ne, mataunansu kuma wuƙaƙe ne, don su cinye matalauta da masu fatara daga duniya. 15-16 Matsattsaku tana da 'ya'ya mata biyu, ana kiransu, “Ba ni, Ba ni.” Akwai abu uku da ba su ƙoshi, i, har huɗu ma da ba su cewa, “Ya isa,” wato lahira, macen da ba ta haihuwa, ƙasa wadda ba ta ƙoshi da ruwa, wuta wadda ba ta cewa, “Ya isa.” 17 Idan ɗa ya raina mahaifi, ya kuma yi wa mahaifiya ba'a hankakin kwari za su ƙwaƙule masa idanu, 'ya'yan mikiya za su cinye. 18-19 Akwai abu uku, i, har huɗu ma, waɗanda ban iya fahimtar su ba, wato yadda gaggafa take tashi a sararin sama, yadda maciji yake jan ciki a kan dutse, yadda jirgin ruwa yake tafiya a teku, Sha'anin namiji da 'ya mace. 20 Ga yadda al'amarin mazinaciya yake, takan yi sha'aninta sa'an nan ta yi wanka ta ce, “Ban yi laifin kome ba!” 21-23 Akwai abu uku, i, har huɗu ma waɗanda duniya ba ta jurewa da su, wato bara da ya zama sarki, wawa da ya ƙoshi da abinci, mummunar mace da ta sami miji, baiwar da ta gāji uwargijiyarta. 24-28 Akwai ƙananan abubuwa huɗu a duniya, amma suna da hikima ƙwarai, wato tururuwa talikai ne marasa ƙarfi, amma duk da haka sukan tanadi abincinsu da rani, remaye ba ƙarfafa ba ne, duk da haka suna yi wa kansu gidaje a cikin duwatsu, fara ba su da sarki, amma duk da haka suna tafiya sahu-sahu. ƙadangare ma wanda ka iya kama shi a hannu, amma yana zama a cikin fādodin sarakuna. 29-31 Akwai abu uku, i, har huɗu ma da suke da kwarjini da taƙama a tafiyarsu, wato Zaki wanda ya fi dukan dabbobi ƙarfi, ba ya ratse wa kowa daga cikinsu, bunsuru da zakara mai taƙama, sarkin da yake tafiya gaban jama'arsa. 32 Idan ka yi wauta kana ta ɗaukaka kanka, ko kuwa kana shirya mugunta, ka tsaya ka yi tunani! 33 Gama kaɗa madara takan kawo mai, murɗa hanci takan sa a yi haɓo, tsokanar fushi takan kawo jayayya.

Karin Magana 31

Shawara ga Sarki

1 Wannan ita ce maganar sarki Lamuwel wadda uwarsa ta koya masa. 2 “Mene ne, ɗana? Mene ne, ya ɗana ne cikina? Mene ne, ɗana na wa'adi? 3 Kada ka ba da ƙarfinka ga mata, kada kuwa ka mai da hankali gare su, waɗanda suke hallaka sarakuna. 4 Bai dace ba, ya Lamuwel, bai dace ba ko kaɗan, sarakuna su sha ruwan inabi, ko masu mulki su yi marmarin barasa, 5 don kada su sha su manta da doka, su kuma kauce wa gaskiya a shari'ar waɗanda aka zalunta. 6 A ba da barasa ga wanda yake cikin halin ƙaƙa naka yi, ruwan inabi kuma ga waɗanda suke cikin ɓacin rai. 7 Bari ya sha don ya manta da talaucinsa, don kada kuma ya ƙara tunawa da ɓacin ransa. 8 “Ka yi magana domin bebaye, domin kuma hakkin dukan waɗanda ba su da wani mataimaki. 9 Ka yi magana dominsu, ka yi shari'ar adalci, ka kiyaye hakkin matalauta da masu bukata.”

Yabon Macen Kirki

10 Wa yake iya samun cikakkiyar mace? Darajarta ta fi ta lu'ulu'ai. 11 Mijinta yakan amince da ita, ba kuwa zai yi hasara ba. 12 Takan yi masa alheri ba mugunta ba, dukan kwanakinta. 13 Takan samo ulu da lilin, ta yi saƙa da hannuwanta da farin ciki. 14 Takan kawo abincinta daga nesa, kamar fatake. 15 Takan yi asubanci ta shirya wa iyalinta abinci, ta kuma shirya wa 'yan matan gidanta aike-aiken da za su yi. 16 Takan lura da gona sosai kafin ta saya, da ribar da ta ci take dasa gonar inabi. 17 Takan himmantu ta yi aiki tuƙuru. 18 Ta sani akwai riba a cikin kasuwancinta. Fitilarta na ci dare farai. 19 Da hannunta take kaɗi, tana kuma saƙa da hannuwanta. 20 Takan yi wa matalauta da masu fatara karamci. 21 Ba ta jin tsoron lokacin sanyi gama 'ya'yanta duka suna da tufafi masu ƙauri. 22 Takan yi wa gadonta kayan shimfiɗa, tufafinta kuma na lilin ne mai laushi na shunayya. 23 Mijinta sananne ne a dandali, sa'ad da yake zaune tare da dattawan gari. 24 Takan yi riguna na lilin ta sayar, takan kuma sayar wa fatake da abin ɗamara. 25 Wadata da mutunci su ne suturarta. Ba ta jin tsoron tsufa. 26 Tana magana da hikima. Koyarwarta ta alheri ce. 27 Tana lura da al'amuran 'ya'yanta da kyau. Ba ruwanta da ƙyuya. 28 'Ya'yanta sukan tashi su gode mata, mijinta kuma yana yabonta. 29 Ya ce, “Mata da yawa sun yi abin yabo, amma ke kin fi su duka.” 30 Kayan tsari da jamali duk banza ne, amma mace mai tsoron Ubangiji, ita ce abar yabo. 31 A yi mata cikakken yabo saboda ayyukanta, za a yabi ayyukanta a dandali.

Mai Hadishi 1

Kome Banza Ne

1 Maganar Mai Wa'azi ɗan Dawuda, Sarkin Urushalima. 2 Banza a banza ne, in ji Mai Hadishi, Banza a banza ne, dukan kome banza ne. 3 Wace riba ce mutum zai samu daga cikin aikinsa, Da yake yi a duniya? 4 Zamani yakan wuce, wani zamani kuma ya zo, Amma abadan duniya tana nan yadda take. 5 Rana takan fito, takan kuma faɗi, Sa'an nan ta gaggauta zuwa wurin fitowarta. 6 Iska takan hura zuwa kudu, ta kuma hura zuwa arewa, Ta yi ta kewayawa, har ta koma inda ta fito. 7 Kowane kogi yakan gangara zuwa teku, Amma har yanzu teku ba ta cika ba. Ruwan yakan koma mafarin kogin, Ya sāke gangarawa kuma. 8 Kowane abu yana sa gajiya, Gajiyar kuwa ta fi gaban magana. Idanunmu ba sā ƙoshi da gani, Haka kuma kunnuwanmu ba sā ƙoshi da ji. 9 Abin da ya faru a dā, shi zai sāke faruwa, Abin da aka yi a dā, shi za a sāke yi. A duniya duka ba wani abu da yake sabo. 10 Da akwai wani abu da za a ce, “Duba, wannan sabon abu ne?” Abin yana nan tuntuni kafin zamaninmu. 11 Ba wanda yake iya tunawa da abin da ya faru a dā, Da abin da zai faru nan gaba. Ba wanda zai iya tunawa da abin da zai faru A tsakanin wannan lokaci da wancan.

Abin da Mai Hadishi Ya Kware da Shi

12 Ni Mai Hadishi sarki ne, na sarauci Isra'ilawa a Urushalima. 13 Na ɗauri aniya in jarraba, in bincika dukan abubuwan da ake yi a duniyar nan. Allah ya ƙaddara mana abu mai wuya. 14 Na ga dukan abin da ake yi a duniya, duk aikin banza ne da ɓata lokaci kawai. 15 Ba za a iya miƙar da abin da ya tanƙware ba, ba kuma za a iya ƙidaya abin da ba shi ba. 16 Na ce wa kaina, “Na zama babban mutum, na fi duk wanda ya taɓa mulkin Urushalima hikima. Hakika na san hikima da ilimi.” 17 Na ɗaura aniya in san bambancin da yake tsakanin ilimi da wauta, da a tsakanin hikima da gāɓanci. Amma na gane harbin iska nake yi kawai. 18 Gwargwadon hikimarka gwargwadon damuwarka, gwargwadon ƙarin iliminka gwargwadon jin haushinka.

Mai Hadishi 2

1 Na sa rai in ji wa kaina daɗi, in kuma san yadda farin ciki yake. Sai na tarar wannan ma aikin banza ne. 2 Na kuma gane dariya wauta ce, nishaɗi kuma ba shi da wani amfani. 3 Muradina shi ne in san hikima in nemi yadda zan ji wa raina daɗi da ruwan inabi, in sa kaina ga aikata wawanci. Bisa ga tsammanina mai yiwuwa ne wannan shi ne abu mafi kyau da mutane za su yi a duniya, a 'yan kwanakinsu. 4 Na kammala manyan abubuwa. Na gina wa kaina gidaje, na yi gonakin inabi. 5 Na kuma yi wa kaina lambuna da gonakin itatuwa, ba irin itatuwa masu 'ya'ya da ba su a ciki. 6 Na yi tafkuna na yi wa itatuwana banruwa. 7 Na sayo bayi mata da maza, an kuma haifa mini cucanawa a gidana. Ina kuma da manyan garkunan shanu, da na tumaki, da na awaki fiye da dukan wanda ya taɓa zama a Urushalima. 8 Na tara wa kaina azurfa, da zinariya, daga baitulmalin ƙasashen da nake mulki. Mawaƙa mata da maza suna raira mini waƙa, ina da dukan irin matan da kowane namiji zai so. 9 I, na ƙasaita fiye da dukan waɗanda suka riga ni zama a Urushalima. Hikimata kuma ba ta taɓa a rabuwa da ni ba. 10 Duk abin da nake so, na samu, ban taɓa hana wa kaina kowane irin nishaɗin da nake so ba. Ina fāriya da kowane irin abin da na aikata. Wannan shi ne ladana na dukan aikina. 11 Na yi tunani a kan dukan abin da na aikata, da irin wahalar da na sha lokacin da nake yin aikin, sai na gane ba shi da wata ma'ana, na zama kamar mai harbin iska, ba shi da wani amfani. 12 Bayan wannan duka, abin da sarki zai iya yi kaɗai, shi ne abin da sarakunan da suka riga shi suka yi. Sai na fara tunani a kan abin da ake nufi da hikima, ko rashin kula, ko wauta. 13 To, na sani hikima ta fi wauta, kamar yadda haske ya fi duhu. 14 Mai hikima ya san inda ya nufa, amma wawa ba zai iya sani ba. Na kuma sani makomarsu guda ce. 15 A zuciyata na ce, “Abin da yakan sami wawa shi ne kuma zai same ni. To, wace riba na ci ke nan saboda hikimar da nake da ita?” Na kuma ce a zuciyata, “Wannan ma aikin banza ne.” 16 Gama ba za a ƙara tunawa da mai hikima ko wawa ba, nan gaba za a manta da dukansu. Yadda mai hikima yake mutuwa haka ma wawa yake mutuwa. 17 Saboda haka rai ba wani abu ba ne a gare ni, domin dukan abin da yake cikinsa bai kawo mini kome ba sai wahala. Duka banza ne, ba abin da nake yi sai harbin iska kawai. 18 Daga cikin dukan abin da na samu kan aikin da na yi, ba su da wata ma'ana a gare ni, gama na sani zan bar wa magājina ne. 19 Wa ya sani ko shi mai hikima ne, ko kuma wawa ne? Duk da haka shi zai mallaki dukan abin da na sha wahalar tanadinsa. Dukan aikin da na yi na hikima a wannan duniya aikin banza ne. 20 Na yi baƙin ciki a kan dukan wahalar aikin da na yi a duniya. 21 Kai ne ka yi aiki da dukan hikimarka, da iliminka, da gwanintarka, amma kuma tilas ka bar shi duka ga wanda bai yi wahalar kome a ciki ba. Wannan ma bai amfana kome ba, mugun abu ne. 22 Me mutum zai samu daga cikin aikin da ya yi duka, da irin ɗawainiyar da ya sha a kan yin aikin? 23 Dukan abin da yake yi a kwanakinsa, ba abin da ya jawo masa, sai damuwa da ɓacin zuciya. Da dare ma ba ya iya hutawa. Wannan kuma aikin banza ne duka. 24 Ba abin da ya fi wa mutum kyau fiye da ya ci, ya sha, ya saki jiki, ya ci moriyar aikinsa. Na gane wannan ma daga wurin Allah ne. 25 Ƙaƙa za ka sami abin da za ka ci, ko ka ji daɗin zamanka in ba tare da shi ba? 26 Allah ne yake ba da hikima, da ilimi, da farin ciki ga wanda yake ƙauna. Amma yakan sa matalauci, mai zunubi, ya yi ta wahalar nema ya tara dukiya, domin Allah ya bayar ga wanda yake ƙauna. Wannan ma aikin banza ne, harbin iska ne kawai.

Mai Hadishi 3

Kowane Abu da Lokacinsa

1 Dukan abin da yake faruwa a duniyar nan yakan faru ne a cikin lokacin da Allah ya so. 2 Shi yake sa lokacin haihuwa, da lokacin mutuwa, Da lokacin dashe, da lokacin tumɓuke abin da aka dasa, 3 Da lokacin kisa, da lokacin rayarwa, Da lokacin rushewa, da lokacin ginawa. 4 Shi ne kuma yake sa lokacin yin kuka, da lokacin yin dariya, Da lokacin yin makoki, da lokacin yin murna, 5 Da lokacin warwatsa duwatsu, da lokacin tattarawa, Da lokacin rungumewa, da lokacin da ba a yi. 6 Shi ne kuma yake sa lokacin nema, da lokacin rashi, Da lokacin adanawa, da lokacin zubarwa, 7 Da lokacin ketawa, da lokacin gyarawa, Da lokacin yin shiru, da lokacin magana. 8 Shi ne kuma yake sa lokacin ƙauna, da lokacin ƙiyayya, Da lokacin yaƙi, da lokacin salama. 9 Wace riba mutum zai ci a kan dukan aikinsa? 10 Na san hukuncin da Allah ya ɗora mana mu yi ta fama da shi. 11 Shi ya sa wa kowane abu lokacinsa. Shi ne kuma ya sa mana buri mu san abin da yake nan gaba, amma fa bai ba mu cikakken sanin ayyukan da yake yi ba, tun daga farko har zuwa ƙarshe. 12 Na gane iyakar abin da mutum zai yi, shi ne ya yi farin ciki, ya yi abin kirki tun yana da rai. 13 Dukanmu mu ci, mu sha, mu yi murna da abin da muka yi aikinsa, gama wannan kyautar Allah ce. 14 Na sani dukan abin da Allah ya yi zai dawwama, ba abin da za a ƙara, ko a rage. Allah ya yi haka kuwa domin mutane su zama masu tsoronsa. 15 Dukan abin da ya faru, ya riga ya faru a dā. Allah ya sa abin da ya faru ya yi ta faruwa. Allah yana hukunta abin da ya riga ya faru.

Rashin Adalcin da yake a Duniya

16 Banda wannan kuma, na gane a duniyar nan mugunta ta gāje matsayin adalci da na abin da yake daidai. 17 Sai na ce a zuciyata, “Da adali, da mugu, Allah zai shara'anta su, domin an ƙayyade lokaci na yin kowane abu da na yin kowane aiki.” 18 Na dai ce Allah yana jarraba mutum ne domin ya nuna masa bai ɗara dabba ba. 19 Gama makomar 'yan adam da ta dabbobi ɗaya ce, yadda ɗayan yake mutuwa haka ma ɗayan. Dukansu numfashinsu iri ɗaya ne. Mutum bai fi dabba ba, gama rai ba shi da wata ma'ana ga kowannensu. 20 Dukansu wuri ɗaya za su tafi, gama dukansu biyu daga turɓaya suka fito, dukansu biyu kuma za su koma cikinta. 21 Wa zai iya tabbatarwa, cewa ruhun mutum zai tafi sama, ruhun dabba kuwa zai tafi ƙasa? 22 Na gane abin da ya fi wa mutum, shi ne ya more wahalar aikinsa, gama ba wani abu da zai iya yi. Ba wata hanya da zai san abin da zai faru bayan mutuwarsa.

Mai Hadishi 4

1 Sa'an nan na sāke dubawa a kan rashin adalcin da yake ci gaba a duniyar nan. Waɗanda ake zalunta suna kuka, ba kuwa wanda zai taimake su, domin waɗanda suke zaluntarsu suke da iko. 2 Ina ƙyashin waɗanda suka mutu, gama sun fi waɗanda suke da rai yanzu jin daɗi. 3 Amma wanda ya fi su jin daɗi duka, shi ne wanda bai taɓa rayuwa ba, balle ya ga rashin adalcin da yake ta ci gaba a duniyar nan. 4 Na gane dalilin da ya sa mutane suke aiki ƙwarai don su ci nasara, so suke su fi kowa samu. Wannan ma aikin banza ne harbin iska kawai. 5 Za su ce, “Wawa ne zai ƙi yin aiki, ya zauna har yunwa ta kashe shi.” 6 Gara tafin hannu guda cike da kwanciyar rai, da tafin hannu biyu cike da tashin hankali, harbin iska ne kawai. 7 Na kuma ga wani abu a zaman mutum, wanda bai amfana kome ba, 8 mutumin da ba shi da kowa, ba ɗa, ba ɗan'uwa, duk da haka a kullum yana ta fama da aiki. Bai taɓa ƙoshi da wadatar da yake da ita ba. Saboda me yana ta fama da aiki, ya hana wa kansa jin daɗi? Wannan ma aikin banza ne, zaman baƙin cikin ne. 9 Biyu sun fi ɗaya, gama za su fi samun amfanin wahalar aikinsu. 10 Gama idan ɗaya daga cikinsu ya fāɗi, ɗayan zai taimake shi ya tashi, amma idan ya faɗi yana shi kaɗai, to, tir, domin ba wanda zai taimake shi. 11 Idan mutum biyu sun kwanta tare, za su ji ɗumin juna, amma ƙaƙa mutum ɗaya zai ji ɗumi? 12 Mutum biyu za su iya kāre kansu su ci nasara, amma mutum ɗaya ba zai iya kāre kansa ya ci nasara a kan wanda ya kawo masa hari ba. Igiya riɓi uku tana da wuyar tsinkawa. 13-14 Mutum yana iya tashi daga matsayin talauci ya zama sarki a ƙasarsa, ko ya fita daga kurkuku ya hau gadon sarauta. Amma lokacin da sarki ya tsufa, idan wautarsa ta hana shi karɓar shawara, bai fi saurayin ɗin da yake talaka mai basira ba. 15 Na yi tunani a kan dukan mutanen da suke zaune a duniyar nan, sai na gane a cikinsu akwai saurayin da zai maye matsayin sarkin. 16 Mutanen da sarki yake mallaka suna da yawan gaske. Amma bayan ba shi ba wanda zai gode masa saboda ayyukan da ya yi. Hakika wannan ma aikin banza ne, harbin iska kawai.

Mai Hadishi 5

Kada ka yi Gaggawar Yin Wa'adi

1 Ka yi hankali lokacin da kake shiga Haikali. Gara ka tafi can da niyyar koyon wani abu, da ka miƙa hadaya kamar waɗansu wawaye da ba su san halal da haram ba. 2 Yi tunani kafin ka yi magana, kada ka yi wa Allah wa'adi na gaggawa. Allah yana Sama kai kuwa kana duniya. Don haka kada ka faɗa fiye da abin da ya kamata. 3 Yawan damuwarka yana iya sa ka yi mafarkai. Yawan maganarka kuma yana iya sa ka ka yi maganar wauta. 4 Sa'ad da ka yi wa'adi ga Allah, yi hanzari ka cika, gama wawa ba shi da wani amfani a gare shi. Sai ka cika wa'adin da ka yi! 5 Gara kada ka yi wa'adi, da ka yi wa'adi, amma ba ka cika ba. 6 Kada ka bar maganar bakinka ta kai ka ga yin zunubi, har ka ce wa manzon Allah, ba haka kake nufi ba. Don me za ka sa Allah ya yi fushi da kai, har ya hallakar da abin da ka yi wahalarsa? 7 Yawan mafarkanka, da dukan ayyukanka, da yawan maganganunka duk banza ne, duk da haka ya fi maka amfani ka yi tsoron Allah.

Rai Banza Ne

8 Idan ka ga hukuma na zaluntar talakawa, ba ta yi musu adalci, ba ta kiyaye hakkinsu, kada ka yi mamaki. Kowane shugaba yana da shugaban da yake goyon bayansa. Dukansu biyu suna da goyon bayan manyan shugabanni. 9 Abin da ƙasa take bukata, shi ne sarkin da yake kulawa da aikin gona. 10 Idan kana ƙaunar kuɗi, daɗi ba zai ishe ka ba, wanda kuma yake ƙaunar dukiya, ba zai ƙoshi da riba ba, wannan kuma aikin banza ne. 11 Gwargwadon dukiyarka gwargwadon mutanen da za ka ciyar, ribarka kaɗai ita ce sanin kana da dukiya. 12 Ma'aikaci, ko yana da isasshen abinci, ko ba shi da isasshe, duk da haka yakan ji daɗin barcinsa da dare. Amma mawadaci yakan kwana bai rintsa ba, saboda yawan tunani. 13 Wani mugun abu da na gani a duniyar nan, shi ne mutane sun ajiye kuɗi domin lokacin da za su bukace su. 14 Amma sukan lalace saboda muguwar ma'amala, har ba abin da ya ragu da za su bar wa 'ya'yansu gado. 15 Mukan bar duniyar nan kamar yadda muka shigo ta, ba mu da kome. Dukan ayyukanmu, ba abin da za mu ɗauka mu tafi da shi. 16 Wannan mugun abu ne, mukan tafi kamar yadda muka zo. Mukan yi aiki, muna ƙoƙari mu kama iska, me muka samu ke nan? 17 Mun yi zamanmu a duhu, da baƙin ciki, da damuwa, da fushi, da cuta. 18 Ga abin da na gani yana da kyau, ya kuma dace, shi ne kurum mutum ya ci, ya sha, ya ji daɗin aikin da ya yi a 'yan kwanakin rai da Allah ya ba shi, gama wannan shi aka ƙaddara wa mutum. 19 Duk wanda Allah ya ba wadata da dukiya ya kuma bar shi ya ci moriyarsu, sai ya yi godiya ya ci moriyar aikin da ya yi, wannan kyauta ce ta Allah. 20 Tun da yake Allah ya yarje masa, ya zauna da farin ciki, ba ya cika damuwa saboda rashin tsawon kwanaki.

Mai Hadishi 6

Rashin Ma'anar Rai

1 Na kuma lura, a duniyar nan an yi wa ɗan adam rashin adalci ƙwarai. 2 Allah yakan ba wani mutum dukiya, da daraja, da wadata, i, da kowane abu da yake bukata. Amma bai ba shi iko ya more su ba. A maimakonsa wani baƙo ne zai more su. Wannan aikin banza ne ba kuwa daidai ba ne. 3 Mai yiwuwa ne mutum ya haifi 'ya'ya ɗari ya kuma yi tsawon rai, amma kome tsawon ransa ba wani abu ba ne idan ba shi da farin ciki, bai kuma sami kyakkyawar binnewa ba. Sai na ce, gara jaririn da aka haifa matacce da shi. 4 Haihuwar ba ta amfane shi kome ba, gama ya zo daga duhu ya koma duhu inda aka manta da shi. bai taɓa ganin hasken rana ba, bai kuma san abin da ake ce da shi rai ba. Amma duk da haka ya dai huta, fiye da mutumin da bai more wa rai ba, ko da ya shekara dubu biyu. Duk da haka dukansu wuri ɗaya za su tafi. 7 Dukan wahalar da ɗan adam yake yi ta samun abinci ce, amma duk da haka bai taɓa ƙoshi ba. 8 Da me mai hikima ya fi wawa? Wace riba ce kuma matalaucin da ya iya zama da mutane zai samu? 9 Abin da ya zo hannu ya fi dogon buri gama dogon buri aikin banza ne, harbon iska kawai. 10 Kowane abu da ya kasance, an riga an ba shi suna, yadda aka yi mutum haka zai zama. Ba kuwa zai iya gardama da abin da ya fi ƙarfinsa ba. 11 Yawan magana yakan ɓata al'amari. Wane amfani zai yi wa mutum? 12 Wa ya san abin da ya fi dacewa ga mutum a 'yan kwanakinsa marasa amfani? Sukan wuce kamar inuwa. Wa kuma zai iya faɗa wa mutum abin da zai faru a duniya bayan rasuwarsa?

Mai Hadishi 7

Fifikon Hikima

1 Kyakkyawan suna ya fi man ƙanshi tsada, ranar mutuwa kuma ta fi ranar haihuwa. 2 Gara a tafi gidan da ake makoki Da a tafi gidan da ake biki, Gama wannan shi ne ƙarshen dukan mutane Ya kamata duk mai rai ya riƙe wannan a zuciyarsa, Mutuwa tana jiran kowa. 3 Baƙin ciki ya fi dariya, Gama baƙin ciki yakan kawo gyara. 4 Mai hikima yakan yi tunanin mutuwa, Amma wawa yakan yi tunanin shagalin duniya. 5 Gara mutum ya ji tsautawar mai hikima, Da ya ji wawaye suna yabonsa. 6 Dariyar wawa kamar ƙarar ƙayar da take karce gindin tukunya ce. Wannan ma aikin banza ne. 7 Hakika zalunci yakan sa mai hikima ya zama wawa, Karɓar rashawa kuma yakan lalata hali. 8 Gara ƙarshen abu da farkonsa. Mai haƙuri kuma ya fi mai girmankai. 9 Ka kame fushinka, Gama wawa ne yake cike da fushi. 10 Kada ka yi tambaya, cewa me ya sa zamanan dā suka fi na yanzu? Gama wannan tambaya ba ta hikima ba ce. 11 Ya kamata kowane mutum ya zama mai hikima, Gama tana da kyau kamar cin gādo. 12 Hikima mafaka ce, takan kāre mutum kamar yadda kuɗi suke yi. Kiyayewar da hikima takan yi wa mai ita, ita ce amfanin ilimi. 13 Ka yi tunanin aikin Allah, Wa ya isa ya miƙe abin da ya tanƙware? 14 In kana jin daɗi, ka yi murna, In kuma wahala kake sha, ka tuna, Allah ne ya yi duka biyunsa, Don kada mutum ya san abin da zai faru a nan gaba. 15 A kwanakina marasa amfani na ga kowane irin abu. Adali ba safai yakan yi tsawon rai ba, mugu kuwa yakan yi tsawon rai a mugayen ayyukansa. 16 Kada ka cika yin adalci, kada kuma ka cika yin hikima, gama don me za ka kashe kanka? 17 Kada ka cika yin mugunta, kada kuma ka cika yin wauta, gama don me za ka mutu tun kwanakinka ba su cika ba? 18 Idan ka riƙe wannan zai amfane ka. Kada ka bar wancan, gama shi wanda yake tsoron Allah zai yi amfani da su. 19 Abin da hikima take iya yi wa mutum ɗaya ya fi abin da masu mulki goma za su yi wa birni. 20 Ba wani mutum a duniyar nan wanda yake aikata abin da yake daidai dukan lokaci, ba tare da yin kuskure ba. 21 Kada ka kula da kowane abu da mutane suke faɗa, mai yiwuwa ne ka ji baranka yana zaginka. 22 Kai kanka ka sani sau da yawa kakan zagi waɗansu mutane.

Neman Hikima

23 Na yi amfani da hikimata don in jarraba wannan duka, domin na ɗaura aniya in zama mai hikima, amma abin ya fi ƙarfina. 24 Wane ne zai iya sanin gaibi? Abin ya yi mana zurfi ƙwarai, yana da wuyar ganewa. 25 Amma na duƙufa neman ilimi, ina ta yin nazari, ina nema in san hikima da amsoshin tambayoyina, in kuma san mugunta da wautar dakikanci. 26 Sai na iske wani abu da ya fi mutuwa ɗaci, wato mace wadda ƙaunar da take yi maka za ta kama ka kamar tarko, kamar kuma raga. Rungumewar da za ta yi maka za ta ɗaure ka kamar sarƙa. Wanda Allah yake jin daɗinsa zai tsere mata, amma za ta kama mai zunubi. 27 Haka ne, in ji Mai Hadishi, da kaɗan da kaɗan na gane wannan sa'ad da nake neman amsa. 28 Amsar da nake nema ban samu ba. Na sami mutum ɗaya mai hikima, wato a cikin mutum dubu, amma daga cikin mata ban sami ko ɗaya ba. 29 Wannan ne kaɗai abin da na gane, tsaf Allah ya yi mu, amma mu muka rikitar da kanmu.

Mai Hadishi 8

1 Mutum mai hikima ne kaɗai ya san ainihin ma'anar yadda abubuwa suke. Hikima takan sa shi fara'a, da sakin fuska.

Yi wa Sarki Biyayya

2 Ka kiyaye umarnin sarki saboda alkawarin da ka ɗauka. 3 Sarki yana iya yin kowane abu da ya ga dama, don haka ka guje wa wurin da yake, kada ka zauna a wuri mai hatsari haka. 4 Da iko sarki yake aiki, don haka ba mai iya ce masa, “Don me?” 5 Muddin ka kiyaye umarnin sarki gidanka lafiya, mai hikima yakan yi abu, ya kuma san lokacin yi da hanyar da ta dace da yinsa. 6 Akwai lokacin da ya dace, da hanyar da ta dace na yin kowane abu, ko da yake wahalar mutum ta yi masa yawa. 7 Ko ɗaya daga cikinmu ba wanda ya san abin da zai faru, wane ne zai faɗa mana? 8 Ba wanda zai iya hana kansa mutuwa, ko ya dakatar da ranar mutuwarsa. Idan yaƙi ya zo ba makawa, ba yadda za mu yi mu zurare.

Mugun da Adali

9 Na ga wannan duka a sa'ad da nake tunani a kan abubuwan da ake yi a duniyar nan, duniyar da waɗansu sukan sami mulki, waɗansu kuwa su sha wuya a ƙarƙashinsu. 10 Hakika na ga an kai mugaye an binne, amma a birnin nan inda suka aikata wannan mugun abu, mutane suna yabonsu, amma sun kuma manta da su. Wannan kuma aikin banza ne. 11 Don me mutane suke aikata laifofi a natse? Domin ba a hukunta laifofi nan da nan. 12 Ko da yake mugun mutum ya aikata laifofi sau ɗari, amma kuwa ya rayu, duk da haka na sani idan kana tsoron Allah kome zai tafi daidai. 13 Ga mugaye ba zai tafi daidai ba, kamar inuwa ransu yake. Za su yi mutuwar ƙuruciya domin ba su da tsoron Allah. 14 Dubi aikin banza da yake faruwa a duniya. Wani lokaci adalai suke shan hukuncin da za a yi wa mugaye, mugaye kuwa su karɓi sakayyar da za a ba adalai. Na ce wannan ma aikin banza ne. 15 Abin da na ce, shi ne mutum ya ji daɗi, domin iyakar jin daɗinsa a wannan rai, shi ne ya ci, ya sha, ya ji wa kansa daɗi. Aƙalla yana iya yin wannan in ya yi aiki a kwanakinsa wanda Allah ya ba shi a wannan duniya. 16 A duk lokacin da nake ƙoƙari in zama mai hikima, in san abin da yake faruwa a duniya, sai na gane, ko da a ce mutum ba zai yi barci ba dare da rana, 17 sam, ba zai taɓa fahimtar abin da Allah yake yi ba. Iyakar ƙoƙarin da ka yi duk ba za ka iya ganewa ba. Masu hikima suna iya cewa sun sani, amma kuwa ba su sani ba.

Mai Hadishi 9

Rashin Daidaitawa

1 Na daɗe ina tunani ƙwarai a kan wannan abu duka, yadda Allah yake sarrafa ayyukan masu hikima da na adalai, har da ƙaunarsu da ƙiyayyarsu. Ba wanda ya san abin da zai faru nan gaba. 2 Ba wani bambanci. Makoma ɗaya ce, ta adali da ta mugu, da ta mutumin kirki da ta marar kirki, da ta tsattsarka da ta marar tsarki, da ta masu yin sujada da ta marasa yi. Mutumin kirki bai fi mai zunubi ba. Wanda ya yi rantsuwa bai fi wanda bai yi ba. 3 Duk makomarsu ɗaya ce, wannan ita ce ɓarnar da take faruwa a duniya. Muddin mutane suna da rai tunaninsu cike yake da mugunta da rashin hankali. Bayan haka sukan mutu. 4 Amma dukan wanda yake da rai a wannan duniya ta rayayyu, yana sa zuciya, gara rayayyen kare da mataccen zaki. 5 Hakika rayayyu sun san za su mutu, amma matattu ba su san kome ba. Ba su da wani sauran lada nan gaba, an manta da su ke nan sam. 6 Ƙaunarsu, da ƙiyayyarsu, da kishinsu sun mutu tare da su. Ba za su ƙara yin wani abu da ake yi a duniya ba. 7 Yi tafiyarka, ka ci abincinka da farin ciki, ka sha ruwan inabinka da fara'a, gama abin da ka yi duka daidai ne a wurin Allah. 8 Ka yi farin ciki da fara'a kullum. 9 Ka yi nishaɗi da matar da kake ƙauna, dukan kwanakin ranka na banza waɗanda Allah ya ba ka a wannan duniya, ka more kowace rana, wannan ne kaɗai rabonka na wahalar aikinka a duniya. 10 Duk abin da kake iya yi, ka yi shi da iyakar iyawarka, domin ba aiki, ko tunani, ko ilimi, ko hikima a lahira, gama can za ka. 11 Na gane wani abu kuma, ashe, a duniyar nan ba kullum maguji ne yake cin tsere ba, ba kullum jarumi ne yake cin nasara ba. Ba kullum mai hikima ne da abinci ba, ba kullum mai basira ne yake da wadata ba, ba kullum gwani ne yake samun tagomashi ba. Amma sa'a, da tsautsayi, sukan sami kowannensu. 12 Gama mutum bai san lokacinsa ba, kamar kifayen da akan kama da taru, kamar kuma tsuntsayen da akan kama da tarko, hakanan mugun lokaci yakan auko wa 'yan adam farat ɗaya.

Hikima ta Fi Iko

13 A duniyar nan na ga wani babban al'amari game da hikima. 14 Dā akwai wani ɗan ƙaramin gari, mutane kuma suke ciki. Sai wani babban sarki ya kawo masa yaƙi, ya kafa masa babban sansani. 15 Akwai wani matalauci, mai hikima, a garin, sai ya ceci garin ta wurin hikimarsa. Duk da haka ba wanda ya tuna da wannan matalauci. 16 Na ce hikima ta fi ƙarfe ƙarfi, ko da yake an raina hikimar matalauci da maganarsa. 17 Gara a kasa kunne ga tattausar maganar mai hikima, da a kasa kunne ga hargagin mai mulki a tsakanin wawaye. 18 Hikima ta fi makaman yaƙi, amma mai zunubi ɗaya yakan yi ɓarna mai yawa.

Mai Hadishi 10

Sakamakon Wauta

1 Matattun ƙudaje sukan sa man ƙanshi ya yi wari, hakanan wauta kaɗan takan ɓata hikima da daraja. 2 Zuciyar mai hikima takan kai shi ga yin abin da yake daidai, amma zuciyar wawa takan kai shi ga yin mugun abu. 3 Ko lokacin da wawa yake tafiya a hanya, yakan nuna ba shi da hankali, yakan kuma bayyana wa kowa shi wawa ne. 4 Idan mai mulki ya husata da kai, kada ka bar inda kake, gama kwantar da hankali yakan sa a yafe manyan laifofi. 5 Akwai mugunta wadda na gani a duniya, wato kuskuren da masu mulki suke yi. 6 Ana ba wawaye manyan matsayi, attajirai kuwa ana ƙasƙantar da su. 7 Na taɓa ganin bayi a kan dawakai, shugabanni kuwa suna tafiya a ƙasa kamar bayi. 8 Wanda ya haƙa rami shi ne zai fāɗa a ciki. Wanda kuma ya rushe katanga, shi maciji zai sara. 9 Wanda yake farfasa duwatsu shi za su yi wa rauni. Wanda kuma yake faskare itace yana cikin hatsarinsu. 10 Idan gatari ya dakushe ba a wasa shi ba, dole ne a yi amfani da ƙarfi da yawa, amma hikima takan taimake shi ya ci nasara. 11 Idan maciji ya sari mutum kafin a ba shi makarin gardi kuma, ba shi da wani amfani. 12 Maganar mai hikima alheri ce, amma maganganun wawa za su hallaka shi. 13 Farkon maganganunsa wauta ne, ƙarshensu kuma mugunta ne da hauka. 14 Wawa ya cika yawan surutu. Wa ya san abin da zai faru nan gaba? Wa zai iya faɗa masa abin da zai raru bayan rasuwarsa? 15 Wahalar wawa takan gajiyar da shi, har bai san hanyar zuwa gari ba. 16 Kaitonki, ya ƙasa wadda sarkinki yaro ne, shugabanninki kuma suna ta shagalinsu tun da safe. 17 Mai farin ciki ce, ke ƙasar da sarkinki mai dattako ne, shugabanninki kuma suka ci a kan kari don su sami ƙarfi, ba domin su bugu ba. 18 Saboda lalaci ɗaki yakan yi yoyo, sai tsaiko ya lotsa. 19 Akan shirya abinci don jin daɗi, ruwan inabi kuwa don faranta zuciya, amma ba za ka sami ko ɗaya ba, sai idan kana da kuɗi. 20 Kada ka zagi sarki ko a cikin zuciyarka, kada kuma ka zagi mawadaci a cikin ɗakin kwananka, gama tsuntsu zai kai maganarka, wani taliki mai fikafikai zai tone asirinka.

Mai Hadishi 11

Abin da Mai Hikima yakan Yi

1 Ka jefa kyautarka a baya, ka tsince ta a gaba. 2 Ka raba abin da yake hannunka ga mutum bakwai ko takwas, gama ba ka san irin masifar da za ta auka wa duniya ba. 3 Idan gizagizai sun cika da ruwa sukan sheƙar da shi ƙasa. A inda itace ya faɗi, a nan zai kwanta, ko wajen kudu ko arewa. 4 Wanda yake la'akari da iska, ba zai yi shuka ba, wanda kuma yake la'akari da gizagizai, ba zai yi girbi ba. 5 Kamar yadda ba ka san hanyar iska ba, ko yadda ƙasusuwan jariri suke girma a mahaifar uwarsa, hakanan kuma ba ka san aikin Allah ba, wato wanda ya yi abu duka. 6 Ka shuka iri da safe, da yamma kuma kada ka janye hannunka, gama ba ka san wanda zai yi albarka ba, ko wannan ko wancan, ko kuma duka biyunsu su yi albarka. 7 Haske yana da daɗi, abu mai kyau kuma idanu su dubi hasken rana. 8 Idan mutum ya rayu har shekaru da yawa, bari ya yi murna a cikinsu duka. Sai dai kuma ya tuna da kwanakin duhu, gama sun fi yawa. Duk abin da ya faru banza ne.

Shawara ga Matasa

9 Ya saurayi! Ka yi murna a lokacin ƙuruciyarka, ka bar zuciyarka ta yi farin ciki a kwanakin samartakarka. Ka bi nufin zuciyarka da sha'awar idanunka. Amma ka sani fa, a cikin al'amuran nan duka Allah zai shara'anta ka. 10 Kada ka bar kome ya dame ka, ko ya yi maka zafi a rai, gama ƙuruciya da samartaka ba za su dawwama ba.

Mai Hadishi 12

1 Ka tuna da Mahaliccinka a kwanakin samartakarka kafin mugayen kwanaki da shekaru su zo, da za ka ce, “Ba na jin daɗinsu.” 2 Wato lokacin da rana, da haske, da wata, da taurari za su duhunta, gizagizai kuma su tattaru bayan da suka sheƙar da ruwa. 3 A lokacin nan hannuwanka da suke kāre ka, za su yi makyarkyata, ƙafafunka za su rasa ƙarfi. Haƙora kaɗan za su ragu a bakinka. Idanunka za su duhunta. 4 Bakinka a rufe yake, haƙora ba su tauna abinci. Muryar tsuntsu za ta farkar da kai. Ba za ka iya jin muryar mawaƙa ba. 5 Sa'an nan za ka ji tsoron hawan tudu, tafiya kuma za ta yi maka wuya. Gashin kanka zai furfurce. Za ka ja jikinka. Ba sauran sha'awar mace. Daganan sai kabari, masu makoki kuwa su yi ta kai da kawowa a kan tituna. 6 Hakika, ka tuna da Mahaliccinka kafin igiyar azurfa ta katse, ko tasar zinariya ta fashe, ko tulu ya fashe a bakin rijiya, ko igiya ta tsinke a bakin tafki, 7 sa'an nan turɓaya ta koma ƙasa kamar a dā, ruhu kuma ya koma wurin Allah wanda ya ba da shi. 8 Banza a banza, duk banza ne, in ji Mai Hadishi. Duk a banza ne.

Abin da ake Bukata wajen Mutum

9 Saboda hikimar Mai Hadishi ya koya wa mutane ilimi. Ya auna, ya bincika, ya tsara karin magana da lura sosai. 10 Ya nemi kalmomi, ya rubuta su daidai. 11 Kalmomin mutane masu hikima kamar sanduna suke da makiyaya suke amfani da su, su bi da tumaki. 12 Ya ɗana, ka yi hankali, kada ka zarce waɗannan, gama wallafa littattafai ba shi da iyaka, yawan karatu kuma gajiyar da kai ne! 13 Bayan wannan duka, makasudin maganar shi ne, ka yi tsoron Allah, ka kiyaye dokokinsa, gama wannan shi ne wajibi ga mutum. 14 Allah zai shara'anta kowane irin aiki, ko a ɓoye aka yi shi, ko nagari ne, ko mugu.

Waƙar Waƙoƙi 1

1 Ga waƙar Sulemanu mafi daɗi.

WAƘAR ta Fari

2 Leɓunanka sun lulluɓe ni da sumba, Ƙaunarka ta fi ruwan inabi zaƙi. 3 Akwai ƙanshi kuma kewaye da kai, Jin amon sunanka yana tunasar da ni. Ba wata matar da za ta ƙi ƙaunarka. 4 Ka ɗauke ni mana, mu gudu, Ka zama sarkina, ka kai ni ɗakinka. Da yake kana nan za mu yi farin ciki, Za mu sha ruwan inabi, mu yi murna da ƙaunarki. Ya dace a ƙaunace ka! 5 Rana ta sa na zama akawala kyakkyawa. Matan Urushalima, bisa ga launi, ni ƙasa ƙasa ce, Kamar alfarwar hamada, Kamar labulen fādar Sulemanu. 6 Kada ka raina ni saboda launina, Domin rana ta dafe ni. 'Yan'uwana suna fushi da ni, Sun sa ni aiki a gonar inabi. Ba ni da zarafin da zan lura da kaina. 7 Faɗa mini, ƙaunataccena, Ina za ka kai garkenka kiwo? Ina za su huta sa'ad da rana ta take? Ina zan neme ka a cikin garkunan makiyaya? 8 Mafi kyau cikin mata, ashe, ba ki san wurin ba? Tafi, ki bi garken, Ki samar wa awakinki wurin kiwo Kusa da alfarwan makiyaya.

Amarya da Ango

9 Ke ƙaunatacciyata, kina ɗauke hankalina Kamar yadda goɗiya take ɗauke hankalin ingarmun karusan Fir'auna. 10 Kitsonki yana da kyau a kumatunki, Ya sauka a wuyanki kamar lu'ulu'ai. 11 Mu kuma za mu ƙera miki sarƙar zinariya, A yi miki ado da azurfa. 12 A sa'ad da sarki yake kan kujerarsa, Yana jin daɗin ƙanshin turarena ƙwarai. 13 Ƙaunataccena yana da ƙanshin mur Lokacin da yake kwance a ƙirjina. 14 Ƙaunataccena kamar furen jeji yake Wanda yake huda a gonar inabi a En-gedi. 15 Ke kyakkyawa ce ƙwarai, kyakkyawa ce ke, ya ƙaunatacciyata, Idonki suna haskaka da ƙauna. 16 Kai kyakkyawa ne ƙwarai, ya ƙaunataccena, kana da bansha'awa. Koriyar ciyawa ita ce gadonmu. 17 Itatuwan al'ul su ne jigajigan gidanmu, Itatuwan fir su ne rufin gidan

Waƙar Waƙoƙi 2

1 Ni fure ce na Sharon, Furen bi-rana na cikin kwari. 2 Kamar yadda furen bi-rana yake a cikin ƙayayuwa, Haka ƙaunatacciyata take a cikin sauran mata. 3 Kamar yadda itacen gawasa yake a cikin itatuwan jeji, Haka ƙaunataccena yake a cikin sauran maza. Da farin ciki na zauna a inuwarsa, Ina jin daɗin halinsa ƙwarai. 4 Ya kai ni babban ɗakin da ake liyafa, Ƙauna ita ce tutarsa a gare ni. 5 Ka ciyar da ni da wainar zabibi, Ka ba ni 'ya'yan gawasa in sha in wartsake! Gama na cika da sha'awarka. 6 Bari ka ta da kaina da hannun hagunka, Ka rungume ni da hannun damanka. 7 Ku 'yan matan Urushalima, Ku rantse da bareyi, da batsiyoyi, Ba za ku shiga tsakaninmu ba, Ku bar ta kurum.

Waƙa ta Biyu

8 Na ji muryar ƙaunataccena! Ya zo a guje daga kan tuddai, Ya sheƙo daga tuddai zuwa wurina. 9 Ƙaunataccena kamar barewa yake, Kamar sagarin kishimi. Ga shi can, yana tsaye a bayan katangarmu. Yana leƙe ta tagogi, Yana kallona ta cikin asabari. 10 Ƙaunataccena ya yi magana da ni. Tashi mu tafi, ƙaunatacciyata, kyakkyawa. 11 Gama lokacin sanyi ya wuce, Ruwa kuma ya ɗauke. 12 Furanni suna hudowa a itatuwa ko'ina. Lokacin raira WAƘOƘI ya yi, Lokacin da kurciyoyi yake kuka ya yi. 13 'Ya'yan ɓaure sun nuna, Tohon inabi yana ƙanshi. Tashi mu tafi, ƙaunatacciyata, kyakkyawa! 14 Ya kurciyata kina zaune a kogon dutse mai tsayi. Bari in ga fuskarki, in kuma ji muryarki, Gama muryarki tana da daɗin ji, Fuskarki kuma tana da kyan gani. 15 Ku kama mana 'yan ƙananan diloli Waɗanda suke ɓata gonakin inabi, Gama gonakin inabinmu sun yi fure. 16 Ƙaunataccena nawa ne, ni ma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin furannin bi-rana, 17 Har hurowar iskar safiya, Sa'ad da duhu ya kawu. Komo ya ƙaunataccena, yi kamar barewa, Kamar sagarin kishimi a kan duwatsu.

Waƙar Waƙoƙi 3

Tunanin Amarya

1 Ina kwance a gadona dukan dare, Ina mafarki da ƙaunataccena, Na neme shi, amma ban same shi ba. Na kira shi, amma ba amsa. 2 Bari in tashi yanzu in shiga birni, In bi titi-titi, in bi dandali-dandali, In nemi wanda raina yake ƙauna. Na neme shi, amma ban same shi ba. 3 Da matsaran da suke kai da kawowa cikin birni suka gan ni, Sai na tambaye su ko sun ga ƙaunataccena. 4 Rabuwata da matsaran ke nan, Sai na yi kaciɓis da ƙaunataccena. Na riƙe shi, ban sake shi ba, Na kai shi gidanmu, har ɗakin mahaifiyata. 5 Ku 'yan matan Urushalima, Ku rantse da bareyi da batsiyoyi, Ba za ka shiga tsakaninmu ba, Ku bar ta kurum.

Waƙa ta Uku

6 Wane ne wannan da yake fitowa daga cikin jeji, Kamar tunnuƙewar hayaƙi cike da kayan ƙanshi iri iri na fatake? 7 Ai, duba suna ɗauke da karaga wadda aka shirya domin Sulemanu, Dakarai sittin na kewaye da karagar, Zaɓaɓɓun sojoji daga cikin Isra'ila. 8 Dukansu gwanayen yaƙi da takobi ne, gogaggu ne na aikin soja, Kowannensu yana da takobi, Suna tsaro don kada a hume su da dare. 9 Ana ɗauke da sarki Sulemanu a karagar da aka shirya da itace mafi kyau. 10 An dalaye ginshiƙanta da azurfa, An rufe ta da zane da aka yi wa ado da zinariya. An lulluɓe wurin zama da zanen shunayya. Matan Urushalima sun yi mata irin yayin da ake yi na ƙauna. 11 Matan Sihiyona, ku fito ku ga sarki Sulemanu Ya sa kambin sarauta, Wanda uwarsa ta sa masa, a ranar aurensa, A ranarsa ta murna da farin ciki.

Ango ya Yabi Amarya

Waƙar Waƙoƙi 4

1 Kyakkyawa ce ke ƙaunatacciyata. Idonki kamar na kurciya, suna haskakawa daga cikin lulluɓi. Gashinki yana zarya kamar garken awaki Da yake gangarowa daga tuddan Gileyad. 2 Haƙoranki farare fat kamar tunkiyar da aka yi mata sausaya, Aka yi mata wanka nan da nan. Ba giɓi, suna nan shar. An jera su tantsai. 3 Leɓunanki ja wur kamar kin shafa jan-baki. Maganarki tana faranta zuciya. Kumatunki suna haske bayan lulluɓi. 4 Wuyanki kamar hasumiyar Dawuda yake, kewayayye sumul sumul, Inda aka rataye garkuwoyi dubu na jarumawa. 5 Mamanki kamar bareyi biyu ne, Wato tagwayen barewa, suna kiwo cikin furen bi-rana. 6 Har iskar safiya ta huro, Duhu kuma ya kawu, Zan zauna a kan tudun mur, Wato tudun kayan ƙanshi. 7 Ke kyakkyawa ce ƙaunatacciyata, Ba wanda zai kushe ki! 8 Amaryata, ki taho daga Dutsen Lebanon, Taho daga Lebanon. Ki taho daga ƙwanƙolin Dutsen Amana, Da Dutsen Senir da Harmon, Inda zakuna da damisoshi suke zaune. 9 Kallon idonki, budurwata, amaryata, Da duwatsun da suke wuyanki Sun sace zuciyata. 10 Ƙaunarki abar murna ce, ya budurwata, amaryata! Ƙaunarki ta fi ruwan inabi. Ƙanshinki ya fi kowane irin turare ƙanshi. 11 Zaƙin leɓunanki kamar zuma ne, ya budurwata, A gare ni harshenki madara ne da zuma. Tufafinki suna ƙanshi kamar turaren da yake cikin Dutsen Lebanon. 12 Budurwata, amaryata, ke asirtaccen lambu ce, Lambu mai katanga, asirtacciyar maɓuɓɓuga. 13 Shuke-shuke suna girma sosai. Suna girma kamar gonar itatuwan rumman. Suna ba da 'ya'ya mafi kyau Da kayan shafe-shafe kamar su lalle da nardi. 14 Nardi, da asfaran, da kalamus, da kirfa, Da dukan itatuwan da suke ba da kayan ƙanshi, Da mur, da aloyes, da dukan turare mafi ƙanshi. 15 Maɓuɓɓugai suna ba lambun ruwa, ruwan rafuffuka suna gudu, Ƙoramu suna bulbulo ruwa daga Dutsen Lebanon. 16 Farka, ya iskar arewa. Ki hura a kan lambuna, ke iskar kudu. Iska ta cika da ƙanshi. Bari ƙaunataccena ya zo lambunsa, Ya ce 'ya'yan itatuwa mafi kyau.

Waƙar Waƙoƙi 5

1 Na shiga cikin lambuna, budurwata, amaryata, Ina tattara mur da ƙaro. Ina shan zuma da kakinsa. Ina shan ruwan inabi da madara kuma. Ƙaunatattuna, ku ci ku sha, har ku bugu da ƙauna!

Waƙa ta Huɗu Shan Kewa

2 Ina barci, amma zuciyata na a farke, Sai na ji ƙaunataccena yana ƙwanƙwasa ƙofa. Buɗe mini in shigo, ƙaunatacciyata, budurwata, kurciyata, Wadda ba wanda zai kushe ki. Kaina ya jiƙe da raɓa, Gashina ya yi danshi da laimar ƙāsashi. 3 Na riga na tuɓe tufafina, in sāke sa su kuma? Na wanke ƙafafuna, in sāke ɓata su? 4 Ƙaunataccena ya janye hannunsa daga ƙofa, Zuciyata kuwa tana kansa. 5 Sai na tashi don in buɗe wa ƙaunataccena, ya shigo. Hannuna sharkaf da mur, Yatsuna suna ɗiga da mur sa'ad da na kama hannun ƙofar. 6 Na buɗe wa ƙaunataccena ƙofa, amma ya riga ya tafi! Na so in ji muryarsa ƙwarai! Na neme shi, amma ban same shi ba. Na yi kiransa, amma ba amsa. 7 Matsara masu kai da kawowa cikin birni suka same ni, Suka doke ni suka yi mini rauni. Matsaran da suke kan garu suka fige gyalena. 8 Ku yi mini alkawari ku matan Urushalima, Idan kun ga ƙaunataccena, Ku faɗa masa na yi suwu saboda ƙauna. 9 Ke mafi kyau cikin mata, Ki faɗi yadda ƙaunatacce naki yake. Wane abin sha'awa yake gare shi, Har da za mu yi miki alkawari?

Amarya ta Yabi Ango

10 Ƙaunataccena kyakkyawa ne ƙaƙƙarfa kuma, Da ƙyar a sami ɗaya irinsa a cikin dubu goma. 11 Gashin kansa dogaye ne suna zarya, Baƙi wulik kamar jikin shaya. Kansa ya fi zinariya daraja. 12 Idanunsa kamar na kurciyoyi a bakin ƙorama, Waɗanda suka yi wanka da madara suna tsaye a bakin rafi. 13 Kumatunsa kyawawa ne kamar lambu, Wanda yake cike da tsire-tsire da kayan yaji. Leɓunansa kamar furen bi-rana ne, suna bulbulo da mur. 14 Hannuwansa kyawawa ne, Saye da ƙawanen da aka yi musu ado da duwatsu masu daraja. Ƙugu nasa sumul sumul ne kamar hauren giwa da aka manne da yakutu. 15 Cinyoyinsa kamar ginshiƙan da aka yi da dutsen alabasta, Aka kafa su a cikin kwasfar zinariya. Kamanninsa kamar Dutsen Lebanon ne, Da itatuwan al'ul ɗinsa mafi kyau. 16 Bakinsa yana da daɗin sumbata, Kome nasa yana faranta mini rai. Matan Urushalima, yadda ƙaunataccena yake ke nan.

Waƙar Waƙoƙi 6

1 Ke mafi kyau cikin matan, Ina ƙaunatacce naki ya tafi? Wace hanya ƙaunatacce naki ya bi? Za mu taimake ki nemansa. 2 Ƙaunataccena ya tafi lambunsa inda fangulan furanninsa suke. Yana kiwon garkensa a lambun, yana tattara furannin bi-rana. 3 Ƙaunataccena nawa ne, ni kuma tasa ce, Yana kiwon garkensa a cikin bi-rana.

Waƙa ta Biyar Ango ya Yabi Amarya

4 Ƙaunatacciyata, kina kyakkyawa kamar Urushalima, Kyakkyawa kuma kamar birnin Tirza, Kina da shiga rai kamar ɗaya daga cikin biranen nan. 5 Ki daina dubana gama idanunki suna rinjayata, Gashinki yana zarya kamar garken awaki Da yake gangarowa daga tuddan Gileyad. 6 Haƙoranki farare fat kamar tunkiyar da aka yi mata sausaya Aka yi mata wanka nan da nan. Ba giɓi, suna nan shar. An jera su tantsai. 7 Kumatunki suna haske bayan lulluɓi. 8 Ina da matan aure sittin, kowace kuwa sarauniya ce, Da ƙwaraƙwarai tamanin, da 'yan mata kuwa ba a magana! 9 Amma ɗaya kaɗai nake ƙauna, Ita kyakkyawa ce kamar kurciya. Tilo ce ga mahaifiyarta, 'yar lele ce ga mahaifiyarta. Mata duk sukan dube ta, su yaba. Matan sarki da ƙwaraƙwaransa suka raira waƙa suka yabe ta. 10 Wace ce wannan, kamar ketowar alfijir? Ita kyakkyawa ce mai haske, kamar hasken rana, Ko na wata mai kashe ido. 11 Na gangara zuwa cikin itatuwan almond Domin in ga ƙananan itatuwan da suke a kwarin, Domin in ga ganyayen inabi Da furannin itatuwan rumman. 12 Ina karkaɗuwa, don kin sa in ƙosa saboda ƙauna, Kamar mai korar dawakan karusar yaƙi. 13 Komo, ki komo, ke Bashulamiya, Ki komo, ki komo domin mu ƙara dubanki. Me ya sa kuke so ku dubi Bashulamiya, Sa'ad da take taka rawar zamanin dā?

Waƙar Waƙoƙi 7

1 Ƙafafunki suna da kyau da takalmi, Ke mafificiyar budurwa! Tsarin cinyoyinki kamar aikin gwanin sassaƙa ne. 2 Cibinki kamar finjali ne, wanda bai taɓa rasa gaurayayyen ruwan inabi a ciki ba. Kwankwasonki kamar damin alkama ne a tsakiyar bi-rana. 3 Mamanki kamar bareyi biyu ne, wato tagwayen barewa ne. 4 Wuyanki kamar hasumiyar hauren giwa ne. Idonki kamar tafki ne cikin birnin Heshbon, Kusa da ƙofar Bat-rabbim. Hancinki kyakkyawa ne kamar hasumiyar Lebanon ta tsaron Dimashƙu. 5 Kin ɗaga kanki sama kamar Dutsen Karmel. Kitsattsen gashin kanki kamar shunayya mafi kyau ne, Yakan kama hankalin sarki.

Daɗin Soyayyar Amarya da Ango

6 Ke kyakkyawa ce ƙaunatacciyata, Kina sa ni jin daɗi a rai. 7 Kina da kyan gani kamar itacen dabino, Mamanki kamar nonnan dabino. 8 Zan hau itacen dabino in tsinko 'ya'yan. Mamanki kamar nonnan inabi suke a gare ni. Numfashinki kamar ƙanshin gawasa ne. 9 Bakinki kamar ruwan inabi mafi kyau ne. Idan haka ne bari ya bulbulo sosai zuwa ga ƙaunataccena, Ya gangara leɓunan masu barci. 10 Ni ta ƙaunataccena ce, yana bukatata. 11 Zo saurayina, bari mu tafi waje, Mu kwana a karkara. 12 Za mu tashi da sassafe, mu duba kurangun inabi, Mu ga ko sun fara tohowa, Ko furanni sun fara buɗewa. Mu ga ko itatuwan rumman sun yi fure. A can zan bayyana maka ƙaunata. 13 Za ka ji ƙanshin shuke-shuke Da na dukan 'ya'yan itatuwa masu daɗi. Na adana maka jin daɗi na dā da na yanzu, ya ƙaunataccena.

Waƙar Waƙoƙi 8

1 Da ma a ce kai ɗan'uwana ne, wanda mahaifiyata ta goya, Da in na gamu da kai a titi, Sai in sumbace ka, ba wanda zai kula. 2 Sai in kai ka gidan mahaifiyata, In ba ka gaurayayyen ruwan inabina wanda aka yi da rumman, ka sha. 3 In ta da kai da hannun hagunka, Ka rungume ni da hannun damanka. 4 Ku yi mini alkawari, ku matan Urushalima, Ba za ku shiga tsakaninmu ba.

Waƙa ta Shida Ƙauna tana da Iko kamar Mutuwa

5 Wace ce take zuwa daga cikin jeji, Kafaɗa da kafaɗa da ƙaunataccenta? A ƙarƙashin itacen gawasa na farkar da ke, A wurin da aka haife ki, Wurin da mahaifiyarki ta haife ki. 6 Kada ki ƙaunaci kowa sai ni, Kada ki rungume kowa sai ni. Ikon ƙauna kamar na mutuwa ne, Ƙarfin kishin ƙauna kamar na mutuwa ne. Yakan kama kamar wuta, Yakan ci kamar gagarumar wuta. 7 Kome yawan ruwa ba zai iya kashe ta ba. Ba rigyawar da za ta nutsar da ita. Duk wanda ya ce zai iya sayen ƙauna da dukiya, Ba abin da zai same shi sai tashin hankali. 8 Muna da 'yar'uwa ƙunƙuma. Me za mu yi idan wani saurayi ya ce yana sonta? 9 Da a ce ita bango ce, da mun gina mata hasumiyar azurfa. Da a ce ita ƙofa ce, da mun yi mata ƙyaure da itacen al'ul. 10 Ni bango ce, doguwa, mamana tantsai tantsai, Na sami kwarjini wurin ƙaunataccena. 11 Sulemanu yana da gonar inabi A Ba'al-hamon, wato wuri mai yawan albarka. Ya yi ijara da waɗansu zaɓaɓɓun manoma. Kowannensu yana biyansa kuɗi, azurfa dubu. 12 Ni ma ina da gonar inabi ta kaina. Kai Sulemanu zan ba ka kuɗi azurfa dubu, Sauran ma'aikata kuma zan ba kowanne ɗari biyu. 13 Aminaina suna kasa kunne ga ƙaunataccena. Ina so in ji muryarka daga cikin lambun. 14 Ya ƙaunataccena, ka zo wurina da sauri, kamar batsiya, Ko sagarin kishimi a kan duwatsu inda kayan yaji suke tsirowa.

Ishaya 1

1 Abin da yake rubuce a littafin nan, jawabi ne a kan Yahuza da Urushalima, wanda Allah ya bayyana wa Ishaya ɗan Amoz a zamanin da Azariya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, suka yi sarautar Yahuza.

Allah ya Tsauta wa Al'umma Mai Zunubi

2 Ubangiji ya ce, “Duniya da sararin sama, ku kasa kunne ga abin da ni, Ubangiji, nake cewa! 'Ya'yan da na goya sun tayar mini. 3 Shanu sun san ubangijinsu, jakai sun san wurin da ubangijinsu yake ba su abinci. Amma wannan ya fi abin da jama'ata Isra'ila suka sani. Ba su gane ba ko kaɗan.” 4 An hallaka ki, ke al'umma mai zunubi, ku lalatattun mutane! Zunubinku ya ja ku ƙasa! Kun ƙi Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, kun juya masa baya. 5 Me ya sa kuke ta tayarwa? Kuna so a ƙara muku hukunci ne? Ya Isra'ila, kanki duka rauni ne, zuciyarki da kwanyarki suna ciwo. 6 Daga kanki har zuwa ƙafafunki, ba inda yake da lafiya a jikinki. Raunuka da ƙujewa da manyan gyambuna sun rufe jikinki, ba a tsabtace raunukanki an ɗaure ba. Ba a yi musu magani ba. 7 An lalatar da ƙasarku, an ƙone biranenku ƙurmus. Kuna gani, baƙi suka ƙwace ƙasarku, suka mai da ko'ina kufai. 8 Urushalima kaɗai ta ragu, birnin da aka kewaye da yaƙi, ba wata kariya kamar rumfar mai ƙumu a gonar inabi, ko ta mai ƙumu a gonar kankana. 9 Da a ce Ubangiji Mai Runduna bai rage sauran jama'a ba, da an hallakar da Urushalima gaba ɗaya, kamar yadda aka yi wa Saduma da Gwamrata.

An Kira su Tuba

10 Ya Urushalima sarakunanki da jama'arki sun zama kamar Saduma da Gwamrata. Ku kasa kunne ga abin da Ubangiji yake faɗa muku. Ku mai da hankali ga abin da Allahnmu yake koya muku. 11 Ya ce, “Kuna tsammani ina jin daɗin dukan hadayun nan da kuke ta miƙa mini? Tumakin da kuke miƙawa hadaya ta ƙonawa, da kitsen kyawawan dabbobinku ya ishe ni. Na gaji da jinin bijimai, da na tumaki, da na awaki. 12 Wa ya roƙe ku ku kawo mini dukan wannan sa'ad da kuka zo yi mini sujada? Wa kuma ya roƙe ku ku yi ta kai da kawowa a kewaye da Haikalina? 13 Ko kusa ba na bukatar hadayunku marasa amfani. Ina jin ƙyamar ƙanshin turaren da kuke miƙawa. Ba zan jure da bukukuwanku na amaryar wata, da na ranakun Asabar, da taronku na addini ba, duka sun ɓaci saboda zunubanku. 14 Ina ƙin bukukuwanku na amaryar wata, da na tsarkakan ranaku. Sun zama nawaya wadda na gaji da ita. 15 “Sa'ad da kuke ɗaga hannuwanku wajen yin addu'a, ba zan dube ku ba. Kome yawan addu'ar da kuka yi, ba zan kasa kunne ba domin zunubi ya ɓata hannuwanku. 16 Ku yi wanka sarai. Ku daina aikata dukan wannan mugun abu da na ga kuna aikatawa. I, ku daina aikata mugunta. 17 Ku koyi yin abin da yake daidai. Ku ga an aikata adalci, ku taimaki waɗanda ake zalunta, ku ba marayu hakkinsu, ku kāre gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu.” 18 Ubangiji ya ce, “Yanzu fa, bari mu daidaita al'amarinmu. Duk kun yi ja wur da zunubi, amma zan wanke ku, ku yi fari fat kamar auduga. Zai yiwu zunubinku ya sa ku zama ja wur, amma za ku yi fari fat kamar farin ulu. 19 Idan za ku yi mini biyayya kaɗai za ku ci kyawawan abubuwa da ƙasa take bayarwa. 20 Amma idan kuka ƙi, kuka raina ni, mutuwa ce ƙaddararku. Ni Ubangiji na faɗi wannan.”

Hukuncin Urushalima da Tubanta

21 Birnin da yake dā mai aminci ne, yanzu ya zama kamar karuwa! Dā adalai a can suke zaune, amma yanzu sai masu kisankai kaɗai. 22 Ya Urushalima, dā kamar azurfa kike, amma yanzu ba ki da amfani, dā kamar kyakkyawan ruwan inabi kike, amma yanzu baƙin ruwa ne kaɗai. 23 Shugabanninku 'yan tawaye ne, abokan ɓarayi, a koyaushe sai karɓar kyautai suke yi, da rashawa. Amma ba su taɓa kare marayu a ɗakin shari'a, ko su kasa kunne ga ƙarar da gwauraye suka kawo ba, wato matan da mazansu suka mutu. 24 Domin haka fa yanzu, sai ku kasa kunne ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah mai iko na Isra'ila, yake cewa, “Zan ɗauki fansa a kanku ku maƙiyana, ba za ku ƙara wahalshe ni ba. 25 Zan hukunta ku. Zan tace ku kamar yadda ake tace ƙarfe, in kawar da dukan ƙazantarku. 26 Zan ba ku shugabanni da mashawarta kamar waɗanda kuke da su dā can. Sa'an nan za a ce da Urushalima adala, amintaccen birni.” 27 Gama Ubangiji mai adalci ne, zai ceci Urushalima da dukan wanda ya tuba a can. 28 Amma zai ragargaza dukan wanda ya yi zunubi, ya tayar gāba da shi, zai kashe duk wanda ya rabu da shi. 29 Za ku yi da na sani, ku da kuka taɓa yin sujada ga itatuwa da dashe-dashen masujada. 30 Za ku bushe kamar busasshen itacen oak, kamar lambun da ba wanda yake ba shi ruwa. 31 Daidai kamar yadda busasshen itacen da tartsatsin wuta ya fāɗa wa, haka mutane masu iko za su hallaka ta wurin mugayen ayyukansu, ba wanda zai iya hana a hallaka su.

Ishaya 2

Madawwamin Mulkin Salama

1 Ga jawabin da Allah ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz a kan Yahuza da Urushalima. 2 A kwanaki masu zuwa, Dutse inda aka gina Haikali zai zama mafi tsayi duka. Al'ummai da yawa za su zo su yi ta bumbuntowa su zo gare shi. 3 Jama'arsu za su ce, “Bari mu haura zuwa tudun Ubangiji, Zuwa ga Haikalin Allah na Isra'ila. Za mu koyi abin da yake so mu yi, Za mu yi tafiya a hanyar da ya zaɓa. Koyarwar Ubangiji daga Urushalima take zuwa, Daga Sihiyona yake magana da jama'arsa.” 4 Zai sulhunta jayayyar da take tsakanin manyan al'ummai, Za su mai da takubansu garemani, Masunsu kuma su maishe su wuƙaƙen aske itace, Al'ummai ba za su ƙara fita zuwa yaƙi ba, Ba za su ƙara koyon yaƙi ba.

Hukuncin Allah a kan masu Girmankai

5 Yanzu fa, zuriyar Yakubu, bari mu yi tafiya a cikin hasken da Ubangiji ya ba mu! 6 Ya Allah, ka rabu da jama'arka, zuriyar Yakubu. Ƙasa ta cika da ayyukan sihiri da aka kawo daga Gabas, daga kuma ƙasar Filistiya. Jama'a suna bin baƙin al'adu. 7 Ƙasarsu tana cike da azurfa da zinariya, dukiyarsu kuma ba iyaka. Ƙasarsu tana cike da dawakai, karusansu kuma ba iyaka. 8 Ƙasarsu tana cike da gumaka, suna sujada ga abubuwan da suka yi da hannuwansu. 9 Za a ƙasƙantar da kowane mutum, a kunyata shi. Kada ka gafarta musu, ya Ubangiji! 10 Za su ɓuya a cikin kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa! 11 Rana tana zuwa sa'ad da girmankan 'yan adam zai ƙare, zai kuma lalatar da fāriyar 'yan adam. Sa'an nan Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka. 12 A wannan rana, Ubangiji Mai Runduna zai ƙasƙantar da kowane mai iko, da kowane mai girmankai, da kowane mai fāriya. 13 Zai hallaka dogayen itatuwan al'ul na Lebanon, da dukan itatuwan oak na ƙasar Bashan. 14 Zai baje duwatsu da tuddai masu tsayi, 15 da kowace doguwar hasumiya, da ganuwar kowace kagara. 16 Zai nutsar da jiragen ruwa mafi girma mafi kyau. 17 Girmankan ɗan adam zai ƙare, za a hallakar da fāriyar ɗan adam, Ubangiji ne kaɗai za a ɗaukaka sa'ad da wannan rana ta yi, 18 za a shafe gumaka ƙaƙaf. 19 Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya. 20 Sa'ad da wannan rana ta yi za su zubar da gumakan da suka yi na zinariya da azurfa, za su bar wa ɓeraye da jemagu. 21 Sa'ad da Ubangiji ya zo domin ya girgiza duniya, jama'a za su ɓuya a cikin kogwannin tuddai da ramummukan duwatsu, suna ƙoƙari su ɓuya daga fushinsa, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa. 22 Kada ku dogara ga 'yan adam. Wace daraja take gare su?

Ishaya 3

Hukuncin Ubangiji a kan Yahuza da Urushalima

1 Yanzu fa Ubangiji, Ubangiji Mai Runduna, yana gab da ya kwashe kowane abu da kowane mutum da jama'ar Urushalima da na Yahuza suke dogara da su. Zai kwashe abincinsu da ruwan shansu, 2 da jarumawansu, da sojojinsu, da alƙalansu, da annabawansu, da masu yi musu duba, da manyan mutanensu, 3 da shugabannin sojojinsu, da na farar hula, da 'yan siyasarsu, da kowane mai aikin sihiri don ya sarrafa abubuwan da suke faruwa. 4 Ubangiji zai sa yaran da ba su balaga ba su mallaki jama'ar. 5 Za a yi ta cutar juna. Matasa ba za su girmama manyansu ba, talakawa ba za su girmama na gaba da su ba. 6 Lokaci yana zuwa sa'ad da mutanen wani dangi za su zaɓi ɗaya daga cikinsu, su ce, “Kai da kake da ɗan abin sawa za ka zama shugabanmu a wannan lokaci na wahala.” 7 Amma zai amsa, ya ce, “Ba ni ba dai! Ba zan iya taimakonku ba. Ba ni ma da abinci sam, ko tufafi ma. Kada ku naɗa ni shugabanku!” 8 Hakika Urushalima ta shiga uku! Yahuza tana kan fāɗuwa! Duk abin da suke faɗa, da abin da suke yi, na gāba da Ubangiji ne, a fili suke raina Allah, shi kansa. 9 Ayyukansu na son zuciya za su zama shaida gāba da su. Suna ta aikata zunubi a fili, kamar yadda mutanen Saduma suka yi. Sun shiga uku, su ne kuwa suka jawo wa kansu. 10 Adalai za su yi murna, kome zai tafi musu daidai. Za su ji daɗin abin da suka aikata. 11 Amma mugaye sun shiga uku, za a sāka musu bisa ga abin da suka aikata. 12 Masu ba da rance da ruwa suna zaluntar jama'ata, masu ba da bashi kuwa suna cutarsu. Ya jama'ata, shugabanninku a karkace suke bi da ku, saboda haka ba ku san inda za ku nufa ba.

Ubangiji yana Hukunta Jama'arsa

13 Ubangiji a shirye yake ya hurta maganarsa, a shirye yake ya hukunta al'ummai. 14 Ubangiji ya kawo dattawa da shugabannin jama'arsa a gaban shari'a. Ga laifin da ya same su da shi, “Kun washe gonakin inabi, kun cika gidajenku da abin da kuka ƙwato daga matalauta. 15 Ba ku da izinin da za ku ragargaza jama'ata, ku cuci matalauta, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Hukunci a kan Matan Urushalima

16 Ubangiji ya ce, “Duba irin girmankai da matan Urushalima suke da shi! Suna tafe suna hura hanci, a koyaushe suna ta fara'a irin ta yaudara, suna takawa ɗaya ɗaya a hankali da mundaye a ƙafafunsu, suna cas cas. 17 Amma zan hukunta su, in aske kawunansu, in bar su ƙwal.” 18 Rana tana zuwa sa'ad da Ubangiji zai raba matan Urushalima da dukan abin da suke taƙama da shi, da kayan adon da suke sawa a ƙafafunsu, da kawunansu, da wuyansu, 19 da hannuwansu. Zai raba su da lulluɓinsu, 20 da hulunansu. Zai raba su da layun da suke sa wa damatsansu, da kwankwasonsu, 21 da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu. 22 Ubangiji zai raba su da dukan kyawawan rigunansu na ado, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakunkunansu, 23 da rigunansu na yanga, da ƙyallayensu na lilin, da adikai, da gyale masu tsawo waɗanda suke sawa a kawunansu. 24 Maimakon su riƙa ƙanshin turare, za su yi wari, a maimakon abin ɗamara, za su yi ɗamara da igiyoyi masu kaushi, a maimakon su kasance da kyakkyawan gashi, za su zama masu sanƙo, a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki, kyansu zai zama abin kunya! 25 Jama'ar garin, i, har da ƙarfafan mutane, za a kashe su a yaƙi. 26 Ƙofofin birnin za su yi makoki, su yi kuka. Za a kamanta birnin da matar da take zaune a ƙasa tsirara.

Ishaya 4

1 Sa'ad da wannan lokaci ya yi, mata bakwai za su riƙe mutum guda su ce, “Mā iya ciyar da kanmu, mu kuma tufasar da kanmu, amma in ka yarda, bari mu ce kai ne mijinmu, domin kada mu sha kunyar zaman gwagwarci.”

An Ceci Urushalima

2 Lokaci na zuwa sa'ad da Ubangiji zai sa kowane tsiro da kowane itacen da yake a ƙasar su girma su yi kyau. Dukan jama'ar Isra'ila waɗanda suka ragu za su yi fāriya, su yi murna saboda amfanin da ƙasar take bayarwa. 3 Duk wanda aka rage a Urushalima, wanda Ubangiji ya nufa da rayuwa, za a ce da shi mai tsarki. 4 Ta wurin ikonsa Ubangiji zai shara'anta al'ummar, ya kuma tsarkake ta, ya wanke laifin Urushalima, har da na jinin da aka zubar a can. 5 Sa'an nan a kan Dutsen Sihiyona, da a kan dukan waɗanda suka tattaru a can, Ubangiji zai aika da girgije da rana, hayaƙi da hasken harshen wuta kuma da dare. Darajar Ubangiji za ta rufe, ta kuma kiyaye birnin duka. 6 Ɗaukakarsa za ta inuwantar da birnin daga zafin rana, ta sa ya zama lafiyayyen wurin da aka kāre daga ruwan sama da hadiri.

Ishaya 5

Waƙar Gonar Inabi

1 Ku saurara in raira muku wannan waƙa, Waƙar abokina da gonar inabinsa. Abokina yana da gonar inabi A wani tudu mai dausayi. 2 Ya kauce ƙasar ya tsintsince duwatsun, Ya daddasa itatuwan inabi mafi kyau. Ya gina hasumiya don a yi tsaronsu, Ya kuma haƙa rami inda za a matse 'ya'yan inabin. Ya yi ta jira don 'ya'yan inabin su nuna, Amma ko wannensu tsami ke gare shi. 3 Saboda haka, abokina ya ce, “Ku jama'ar da kuke zaune a Urushalima da Yahuza, ku shara'anta tsakanina da gonar inabina. 4 Akwai abin da ban yi mata ba? Me ya sa ta yi 'ya'yan inabi masu tsami, maimakon 'ya'yan inabi masu kyau da nake sa zuciya. 5 “Ga abin da zan yi wa gonar inabina. Zan cire shingen da yake kewaye da ita, in rushe bangon da ya kāre ta, in bar namomin jeji su cinye ta, su tattake ta. 6 Zan bar ciyayi su rufe ta. Ba zan yi wa kurangar inabin aski ba, ko in yi mata noma, amma zan bar sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa su rufe ta. Har ma zan sa gizagizai su hana ta ruwan sama.” 7 Isra'ila ita ce gonar inabin Ubangiji Mai Runduna, Jama'ar Yahuza su ne itatuwan inabin da aka daddasa. Ya sa zuciya za su yi abin da yake mai kyau, Amma a maimakon haka sai suka zama masu kisankai! Ya zaci za su aikata abin da yake daidai, Amma waɗanda suka fāɗa hannunsu kururuwa suke, suna neman adalci!

Mugaye sun Shiga Uku

8 Kun shiga uku! Kuna ƙara wa kanku gidaje da gonaki a kan waɗanda kuke da su a dā. Ba da jimawa ba za a ga ba sauran filin da zai ragu ga kowa, ku kaɗai za ku zauna a ƙasar. 9 Na ji Ubangiji Mai Runduna yana cewa, “Duk waɗannan manya manyan gidaje kyawawa za su zama kangwaye. 10 Kadada biyar na gonar inabi za ta ba da kwalaba shida kaɗai na ruwan inabi. Garwa ashirin na iri za su ba da tsabar hatsi garwa biyu!” 11 Kun shiga uku! Kukan tashi da sassafe ku fara sha, ku yi ta sha har yamma ta yi sosai, ku raba dare kuna buguwa. 12 A cikin bukukuwanku kuna kaɗa garaya, da bandiri, da bushe-bushe, da ruwan inabi. Amma ba ku gane da abin da Ubangiji yake yi ba. 13 Don haka za a kwashe ku, ku zama 'yan sarƙa, a raba ku da ƙasarku. Yunwa za ta kashe shugabanninku, sauran jama'a kuwa ƙishirwa za ta kashe su. 14 Lahira ta ƙosa, ta wage bakinta. Ta lanƙwame manyan mutanen Urushalima da sauran babban taron jama'a masu hayaniya. 15 Za a kunyatar da kowa, dukan masu girmankai za a ƙasƙantar da su. 16 Amma Ubangiji Mai Runduna yana nuna girmansa ta wurin aikata abin da yake daidai, yana kuma bayyana shi Mai Tsarki ne, ta yadda yake shara'anta jama'arsa. 17 A cikin kangwayen birnin, raguna za su ci ciyawa, a nan ne kuma awaki za su sami wurin kiwo. 18 Kun shiga uku! Ba ku iya kuɓuta daga zunubanku ba. 19 Kukan ce, “Bari Ubangiji ya gaggauta ya aikata abin da ya ce zai yi don mu gani. Bari Allah, Mai Tsarki na Isra'ila, ya i da shirye-shiryensa. Bari mu ga abin da yake nufi.” 20 Kun shiga uku! Kun ce mugunta ita ce nagarta, nagarta kuwa mugunta. Kun mai da duhu shi ne haske, haske kuwa duhu. Kun mai da abin da yake mai ɗaci mai zaƙi, mai zaƙi kuwa kun maishe shi mai ɗaci. 21 Kun shiga uku! A tsammaninku ku masu hikima ne, masu wayo ƙwarai. 22 Kun shiga uku! Jarumawan kwalabar ruwan inabi! Masu ƙarfin zuciya marasa tsoro a gauraya shaye-shaye! 23 Amma kukan ƙyale masu laifi waɗanda suka ba ku rashawa, kukan kuwa ƙi yi wa marasa laifi shari'ar gaskiya. 24 Don haka, kamar yadda tattaka da busasshiyar ciyawa sukan yanƙwane su ƙone a wuta, saiwoyinku za su ruɓe, furanninku kuma za su bushe. Iska za ta kwashe su, domin kun ƙi abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya koya muku. 25 Ubangiji yana fushi da jama'arsa, ya miƙa hannunsa domin ya hukunta su. Duwatsu za su jijjigu, gawawwaki kuwa za a bar su a kan tituna kamar shara. Duk da haka Ubangiji ba zai huce daga fushinsa ba, ba kuwa zai janye hannunsa daga yin hukunci ba. 26 Ubangiji ya ba da alama a kirawo al'ummar da take nesa. Ya yi musu f�to su zo daga bangon duniya. Ga shi kuwa sun iso da sauri nan da nan. 27 Ko ɗaya ba wanda ya gaji, ba kuwa wanda ya yi tuntuɓe. Ba su yi gyangyaɗi ko barci ba. Ba abin ɗamarar da ya kwance, ba igiyar takalmin da ta tsinke. 28 Kibansu masu tsini ne, bakunansu kuwa a shirye suke don yin harbi. Kofaton dawakansu suna da ƙarfi kamar dutsen ƙanƙara, ƙafafun karusansu kamar guguwa ne. 29 Sojojinsu na ruri kamar zakunan da suka kashe nama, suna kuwa ɗauke da shi don kada wani ya ƙwace musu. 30 Sa'ad da ranar ta yi, za su yi ruri a kan Isra'ila da ƙarfi kamar rurin teku. Ku duba ƙasan nan! Duhu da damuwa! Duhu ya haɗiye hasken.

Ishaya 6

Allah ya Kira Ishaya ya Zama Annabi

1 A shekarar da sarki Azariya ya rasu na ga Ubangiji. Yana zaune a kursiyinsa a Sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika Haikali. 2 Kewaye da shi sai ga waɗansu talikai masu kama da harshen wuta a tsaye, ko wannensu yana da fikafikai shida. Ko wannensu ya rufe fuskarsa da fiffike biyu, jikinsa kuma da fiffike biyu, sauran fiffike biyu ɗin kuma, da su yake tashi. 3 Suna ta kiran junansu suna cewa, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Mai Runduna Mai Tsarki ne! Ɗaukakarsa ta cika duniya.” 4 Amon muryoyinsu ya sa harsashin ginin Haikali ya girgiɗa, Haikalin kansa kuma ya game da hayaƙi. 5 Sai na ce, “Sa zuciyata ya ƙare! Na shiga uku! Kowace maganar da ta fito bakina zunubi ce, ina zaune a tsakanin mutane waɗanda duk maganarsu zunubi ce, ba ta da tsarki. Amma yanzu da idona na ga Sarki, Ubangiji Mai Runduna!” 6 Sa'an nan ɗaya daga cikin talikan ya tashi ya sauko zuwa gare ni, yana riƙe da garwashin wuta wanda ya ɗauko da arautaki daga bagade. 7 Ya taɓa leɓunana da garwashin wutar ya ce, “Wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.” 8 Sai na ji Ubangiji yana cewa, “Wa zan aika? Wa zai zama manzonmu?” Sai na amsa na ce, “Ga ni! Ka aike ni!” 9 Saboda haka sai ya ce mini in tafi in faɗa wa jama'a wannan jawabi cewa, “Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba. Kome yawan dubawar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.” 10 Sa'an nan ya ce mini, “Ka sa hankalin mutanen nan ya dushe, kunnuwansu su kurunce, idanunsu su makance, har da ba za su iya gani, ko ji, ko fahimta ba. In da za su yi haka mai yiwuwa ne su sāke juyowa gare ni in warkar da su.” 11 Na yi tambaya na ce, “Har yaushe zai ta zama haka, ya Ubangiji?” Sai ya amsa, ya ce, “Har birane suka zama kufai ba kowa ciki. Har gidaje suka zama kangwaye. Har ƙasar kanta ta zama ba kowa, marar amfani. 12 Zan sa jama'a su tafi nesa, in sa ƙasar duka ta zama kango. 13 Ko da mutum ɗaya cikin goma zai ragu a ƙasar, shi ma za a hallaka shi. Zai zama kamar kututturen itacen oak wanda aka sare.” Wato kututturen alama ce ta tohuwar jama'ar Allah zuwa gaba.

Ishaya 7

Jawabi zuwa ga Sarki Ahaz

1 Sa'ad da sarki Ahaz, ɗan Yotam, wato jikan Azariya yake mulkin Yahuza, sai yaƙi ya ɓarke. Rezin, Sarkin Suriya, da Feka ɗan Remaliya, Sarkin Isra'ila, suka fāɗa wa Urushalima da yaƙi, amma ba su iya cinta ba. 2 Labari ya kai gun Sarkin Yahuza, cewa sojojin Suriya sun shiga ƙasar Isra'ila. Sai shi da dukan jama'arsa suka firgita ƙwarai, suna ta kaɗuwa kamar itatuwan da iska take kaɗawa. 3 Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Ka ɗauki ɗanka Sheyar-yashub ka je ka sami sarki Ahaz. Za ka same shi a hanya inda masu wankin tufafi suke aiki, a wajen ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga kududdufin da yake sama da ita. 4 Faɗa masa ya zauna da shiri, ya natsu, kada ya ji tsoro ko ya damu. Fushin sarki Rezin da Suriyawansa da na sarki Feka ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin 'yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba. 5 Suriya tare da Isra'ila da sarkinta sun ƙulla maƙarƙashiya. 6 Nufinsu su kai wa ƙasar Yahuza yaƙi, su tsoratar da jama'a, don su haɗa kai da su, sa'an nan su naɗa ɗan Tabeyel. 7 “Amma ni Ubangiji na hurta, faufau wannan ba zai faru ba. 8 Don me? Saboda Dimashƙu ita ce ƙarfin Suriya, sarki Rezin kuwa shi ne ƙarfin Dimashƙu. Isra'ila kuwa a shekara sittin da biyar masu zuwa za ta karkasu, har ba za ta iya rayuwa ta zama al'umma ba. 9 Samariya ita ce ƙarfin Isra'ila, sarki Feka kuma shi ne ƙarfin Samariya. “Idan bangaskiyarku ba ta da ƙarfi, to, ba za ku dawwama ba.”

Immanuwel

10 Ubangiji ya aika wa Ahaz da wani jawabi, ya ce, 11 “Ka roƙi Ubangiji Allahnka ya ba ka alama. Yana yiwuwa daga can zurfin lahira ne, ko kuma daga can cikin sama ne.” 12 Ahaz ya amsa, ya ce, “Ba zan nemi wata alama ba. Ba zan jarraba Ubangiji ba.” 13 Ga amsar da Ishaya ya ba Ahaz, “Kasa kunne yanzu, kai zuriyar sarki Dawuda. Ba abin kirki kuke yi ba, da kuka ƙure haƙurin jama'a, haƙurin Allah kuma kuke so ku ƙure? 14 Yanzu fa, Ubangiji kansa zai ba ku alama. Wata budurwa wadda take da ciki, za ta haifi ɗa, za a raɗa masa suna Immanuwel. 15 In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa. 16 Kafin lokacin ya yi, ƙasashen sarakunan nan biyu waɗanda suka firgita ku za su zama kango. 17 “Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama'arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Isra'ila daga na Yahuza. Zai kawo Sarkin Assuriya! 18 “A lokacin nan, Ubangiji zai yi feɗuwa ya kirawo Masarawa su zo kamar ƙudaje daga manisantan mazaunan Kogin Nilu, ya kuma kirawo Assuriyawa su zo daga ƙasarsu kamar ƙudajen zuma. 19 Za su zo jingim su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, za su rufe kowane fili mai ƙayayuwa da kowace makiyaya. 20 “A lokacin nan, Ubangiji zai yi ijara da wanzami daga wancan hayi na Yufiretis, wato Sarkin Assuriya! Zai aske gyammanku, da gashin kawunanku, da na jikunanku. 21 “A lokacin nan, ko da karsana ɗaya da awaki biyu kaɗai manomi yake da su, 22 za su ba da isasshiyar madarar da za ta biya dukan bukatarsa. Hakika dukan waɗanda suka ragu a ƙasar za su sami yawan albarka su ƙoshi. 23 “A lokacin nan, waɗannan kyawawan gonakin inabi waɗanda suke da kurangar inabi dubu, kuɗin kowace gonar inabi azurfa dubu guda ne, gonakin za su cika da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya. 24 Ba wanda yake da ƙarfin hali da zai iya tafiya can, sai ko wanda yake da kwari da baka. Hakika ƙasar duka za ta cika da sarƙaƙƙiya da ƙayayuwa. 25 Dukan tuddai inda dā akan shuka amfanin gona, za su cika da ƙayayuwa, har da ba mai iya zuwa wurin. Zai zama wurin kiwon shanu da tumaki.”

Ishaya 8

Sunan Ɗan Annabi

1 Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki allo babba ka rubuta a kansa da manyan harufa, ‘Kwashe ganima nan da nan, washe da hanzari.’ 2 Nemo mutum biyu amintattu, wato Uriya firist, da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama shaidu.” 3 Bayan wannan na yi jima'i da matata annabiya. Ta ɗauki ciki, ta haifi ɗa namiji, Ubangiji ya ce mini, “Ka raɗa masa suna, ‘Kwashe ganima nan da nan, washe da hanzari.’ 4 Kafin yaron ya isa kiran mama ko baba, Sarkin Assuriya zai kwashe dukan dukiyar Dimashƙu da dukan ganimar Samariya.”

Sarkin Assuriya yana Zuwa

5 Ubangiji kuma ya sake yi mini magana. 6 Ya ce, “Saboda wannan jama'a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa, suka yi ta rawar jiki a gaban sarki Rezin da sarki Feka, 7 ni Ubangiji kuwa, zan kawo Sarkin Assuriya da dukan sojojinsa su fāɗa wa Yahuza. Za su tasar musu kamar rigyawar Kogin Yufiretis wadda ta yi ambaliya ta shafe kowace gaɓa. 8 Za su sheƙa cikin ƙasar Yahuza kamar rigyawa wadda ta kai har kafaɗa, ta rufe kome da kome.” Allah yana tare da mu! Fikafikansa a buɗe suke su tsare ƙasar. 9 Ku tattaru a tsorace ya ku sauran al'umma! Ku saurara, ya ku manisantan wurare na duniya. Ku yi shirin faɗa, amma ku ji tsoro! Hakika ku yi shiri, amma ku ji tsoro! 10 Ku yi ta shirye-shiryenku! Amma ko kusa ba za ku yi nasara ba. Ku yi magana a kan dukan abin da kuke so! Amma duk a banza, gama Allah yana tare da mu.

Ubangiji za ku Ji Tsoro

11 Bisa ga ikonsa mai girma Ubangiji ya faɗakar da ni kada in bi hanyar da jama'ar ke bi. Ya ce, 12 “Kada ka haɗa kanka da jama'a cikin ƙulle-ƙullensu, kada kuma ka ji tsoron abubuwan da su suke jin tsoro. 13 Ka tuna fa, ni Ubangiji Mai Runduna, mai tsarki ne. Wajibi ne ni kaɗai za ka ji tsoro. 14 Saboda tsananin tsarkina na zama kamar dutse wanda mutane suke tuntuɓe da shi. Na zama kamar tarko wanda zai kama jama'ar mulkokin Yahuza da Isra'ila da mutanen Urushalima. 15 Da yawa za su yi tuntuɓe su faɗi. Za su faɗi, a kuwa ragargaza su. Za a kama su da tarko.” 16 Almajiraina su ne za su lura, su kuma kiyaye jawabin da Allah ya ba ni. 17 Ubangiji ya ɓoye kansa daga jama'arsa, amma ni na dogara gare shi, na kafa zuciyata a gare shi. 18 Ga ni tare da 'ya'yan da Ubangiji ya ba ni. Ubangiji Mai Runduna, wanda kursiyinsa a kan Dutsen Sihiyona yake, ya maishe mu rayayyen jawabi ga jama'ar Isra'ila. 19 Mutane za su riƙa ce muku ku nemi shawarar 'yan bori da masu sihiri waɗanda suke shaƙe muryar, har ba a jin abin da suke faɗa. Za su ce, “Ai, ma, ya kamata mutane su nemi shawara daga aljannu, su kuma nemi shawarar matattu saboda masu rai.” 20 Ga amsar da za ku ba su, ku ce, “Ku kasa kunne ga koyarwar Ubangiji. Kada ku kasa kunne ga 'yan bori. Gama abin da suka faɗa muku ba zai amfane ku ba.”

Lokacin Wahala

21 Mutane za su yi ta kai da kawowa a ko'ina cikin ƙasar, cikin matsuwa da yunwa. A yunwar da suke sha da haushin da suke ji, za su zagi sarkinsu, su kuma zagi Allahnsu. Har ma zai yiwu su ɗaga ido su dubi sararin sama, 22 ko su zura wa ƙasa ido, amma ba abin da za su gani, sai wahala da duhu mai banrazana, inda za a kora su a ciki.

Ishaya 9

Haihuwar Sarkin Salama

1 Ba sauran baƙin ciki ga wadda take shan azaba. Dā an ƙasƙantar da ƙasar kabilan Zabaluna da na Naftali, amma nan gaba wannan jiha za ta sami daraja, tun daga Bahar Maliya, zuwa gabashin ƙasar a wancan sashe na Urdun, har zuwa Galili kanta, wurin da baƙi suke zaune. 2 Jama'ar da suka yi tafiya cikin duhu, Sun ga babban haske! Suka zauna a inuwar mutuwa, Amma yanzu haske ya haskaka su. 3 Ka ba su babbar murna, ya Ubangiji, Ka sa su yi farin ciki. Suna murna da abin da ka aikata, Kamar yadda mutane suke murna sa'ad da suke girbin hatsi, Ko sa'ad da suke raba ganima. 4 Gama ka karya karkiyar da ta nawaita musu, Da kuma sandan da ake dukan kafaɗunsu da shi. Kai ne, ya Ubangiji, ka kori al'ummar Da ta zalunci jama'arka, ta kuma zambace su, Daidai da yadda dā ka kori rundunar sojojin Madayana tuntuni. 5 Takalman sojojin da suka kawo yaƙi Da dukan tufafinsu da suka birkiɗe da jini, Za a ƙone su da wuta! 6 Ga shi, an haifa mana ɗa! Mun sami yaro! Shi zai zama Mai Mulkinmu. Za a kira shi, “Mashawarci Mai Al'ajabi,” “Allah Maɗaukaki,” “Uba Madawwami,” “Sarkin Salama.” 7 Sarautar ikonsa za ta yi ta ci gaba, Mulkinsa zai kasance da salama kullayaumin, Zai gāji sarki Dawuda, ya yi mulki a matsayinsa, Zai kafa mulkinsa a kan adalci da gaskiya, Tun daga yanzu har zuwa ƙarshen zamani. Ubangiji Mai Runduna ne ya yi niyyar aikata wannan duka.

Ubangiji ya yi Fushi da Isra'ila

8 Ubangiji ya hurta hukunci a kan mulkin Isra'ila, da a kan zuriyar Yakubu. 9 Dukan jama'ar Isra'ila, duk wanda yake zaune a birnin Samariya, zai sani Ubangiji ne ya aikata haka. Yanzu suna da girmankai suna fāriya. Sun ce, 10 “Gine-ginen da aka yi da tubali sun rushe, amma za mu sāke gina su da dutse. An sassare ginshiƙan da aka yi da itacen durumi, amma za mu sāke kakkafa su da kyawawan itatuwan al'ul.” 11 Ubangiji ya kuta maƙiyansu daga Rezin su fāɗa su da yaƙi. 12 Suriya daga gabas, da Filistiya daga yamma, sun wage bakinsu don su haɗiye Isra'ila. Duk da haka fushin Ubangiji bai huce ba, amma har yanzu dantsensa yana a miƙe don ya yi hukunci. 13 Jama'ar Isra'ila ba su tuba ba, ko da yake Ubangiji Mai Runduna ya hukunta su, duk da haka ba su juyo ba. 14 A rana ɗaya Ubangiji zai hukunta shugabannin Isra'ila da jama'arta. Zai hallaka kawunansu da ƙafafunsu, da dabino da iwa, 15 wato tsofaffi da manyan mutane su ne kawunan, ƙafafu kuwa su ne annabawan da suke koyar da ƙarairayi! 16 Su waɗanda suke bi da jama'an nan, sun bashe su, sun ruɗar da su ɗungum. 17 Don haka Ubangiji ba zai bar ko ɗaya daga cikin samarin ya tsira ba, ba zai nuna jinƙai ga gwauraye ba, wato matan da mazansu suka mutu, ko ga marayu, gama dukan mutane maƙiyan Allah ne, mugaye, duk abin da suke faɗa mugunta ce. Duk da haka fushin Ubangiji ba zai huce ba, amma har yanzu dantsensa yana a miƙe don ya yi hukunci. 18 Muguntar jama'a tana ci kamar wutar da take cinye ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya. Tana ci kamar wutar dawa wadda hayaƙinta yake murtukewa har sama. 19 Saboda Ubangiji Mai Runduna ya yi fushi, hukuncinsa yana ci kamar wuta ko'ina a ƙasar, yana hallakar da jama'a, kowa na ta kansa. 20 A ko'ina a ƙasar jama'a sukan wawashe su ci ɗan abincin da suke iya samu, amma ba su taɓa ƙoshi ba. Har 'ya'yansu ma suke ci! 21 Jama'ar Manassa da jama'ar Ifraimu suna fāɗa wa juna, tare kuma suke fāɗa wa Yahuza. Duk da haka fushin Ubangiji bai huce ba, amma har yanzu dantsensa yana a miƙe don ya yi hukunci.

Ishaya 10

1 Kun shiga uku! Kuna kafa dokokin rashin gaskiya don ku zalunci jama'ata. 2 Ta haka kuke hana wa talakawa hakkinsu, kuna kuma ƙin yi musu shari'ar gaskiya. Ta haka kuke ƙwace dukiyar gwauraye, wato matan da mazansu suka rasu, da ta marayu. 3 Me za ku yi sa'ad Allah zai hukunta ku? Me za ku yi kuma sa'ad da ya kawo muku masifa daga wata ƙasa mai nisa? Ina za ku sheƙa neman taimako? A ina kuma za ku ɓoye dukiyarku? 4 Za a kashe ku a yaƙi, ko a kwashe ku, kamammun yaƙi. Duk da haka fushin Ubangiji ba zai huce ba, amma har yanzu dantsensa yana a miƙe don ya yi hukunci.

Allah zai Sarrafa Sarkin Assuriya

5 Ubangiji ya ce, “Assuriya! Ina yin amfani da Assuriya kamar kulki don in hukunta waɗanda nake fushi da su. 6 Na aiki Assuriya ta faɗa wa al'ummar da ba ta tsoron Allah, da yaƙi, wato jama'ar da ta sa na yi fushi. Na aike su su yi waso su yi sata, su tattake jama'a kamar ƙura a tituna.” 7 Amma Sarkin Assuriya yana da nasa mugayen shirye-shirye da zai yi. Ya yi niyya ya hallaka al'ummai masu yawa. 8 Ya yi kurari, ya ce, “Kowane shugaban mayaƙana sarki ne! 9 Na ci biranen Kalno da na Karkemish. Na ci biranen Hamat da na Arfad. Na kuma ci Samariya da Dimashƙu. 10 Na miƙa hannuna don in hukunta wa waɗannan mulkoki masu bauta wa gumaka, wato gumakan sun yi yawa fiye da na Urushalima, da na Samariya. 11 Na hallaka Samariya da dukan gumakanta, haka ma zan yi wa Urushalima da siffofin da suke yi wa sujada a can.” 12 Ubangiji ya ce, “Sa'ad da na gama abin da nake yi a kan Dutsen Sihiyona da cikin Urushalima, zan hukunta Sarkin Assuriya saboda dukan kurarinsa da girmankansa.” 13 Sarkin Assuriya ya yi kurari ya ce, “Dukan waɗannan ni da kaina na yi su. Ni ƙaƙƙarfa ne, mai hikima, mai wayo. Na kawar da kan iyakokin da suke tsakanin ƙasashen sauran al'umma, na kwashe dukan abin da suka tattara suka adana. Kamar bijimi, haka na tattake mutanen da suke zaune a can. 14 Al'umman duniya kamar sheƙar tsuntsaye suke. Na tattara dukiyarsu, a sawwaƙe kamar yadda ake tattara ƙwai, ba tsuntsun da ya buɗe baki don ya yi mini kuka!” 15 Amma Ubangiji ya ce, “Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma? Ko zarto ya fi wanda yake amfani da shi muhimmanci? Ba kulki yake riƙe da mutum ba, amma mutum yake riƙe da kulki.” 16 Ubangiji Mai Runduna zai aukar da cuta don ya hukunta waɗanda suke ƙosassu yanzu. Za su ji jikinsu na ta ƙuna kamar wuta. 17 Allah da yake hasken Isra'ila, zai zama wuta. Allah, Mai Tsarki na Isra'ila, zai zama harshen wuta, wanda zai ƙone kowane abu rana ɗaya, har da ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya. 18 Jeji mai dausayi da ƙasar noma za a lalatar da su ƙaƙaf, kamar yadda ciwon ajali yake hallaka mutum. 19 Sai 'yan itatuwa kaɗan za su ragu, ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.

Mutanen Isra'ila kima ne za su Komo

20 Lokaci zai yi sa'ad da jama'ar Isra'ila da suka ragu ba za su ƙara dogara ga al'ummar da ta kusa hallaka su ba. Hakika za su dogara ga Ubangiji Allah, Mai Tsarki na Isra'ila. 21 Kaɗan daga cikin jama'ar Isra'ila za su koma wurin Allahnsu Mai Iko Dukka. 22 Ko da yake yanzu akwai jama'ar Isra'ila da yawa, yawansu kuwa kamar yashin teku, duk da haka, sai kaɗan ne za su komo. An tanada wa jama'a hallaka, sun kuwa cancanci hallakar. 23 Hakika a ƙasar duka, Ubangiji Allah Mai Runduna zai kawo hallaka kamar yadda ya ce zai yi.

Ubangiji zai Hukunta Assuriya

24 Ubangiji Mai Runduna ya ce wa jama'arsa da suke Sihiyona, “Kada ku ji tsoron Assuriyawa, ko da yake suna wahalshe ku kamar yadda Masarawa suka yi. 25 Saura kaɗan in gama hukuncin da nake yi muku, sa'an nan in hallaka su. 26 Ni, Ubangiji Mai Runduna, zan bulale su da bulalata, kamar yadda na bugi mutanen Madayana a dutsen Oreb. Zan sa Assuriyawa su sha wahala kamar yadda Masarawa suka sha. 27 A lokacin nan zan 'yantar da ku daga mulkin Assuriya, karkiyarsu ba za ta ƙara zama kaya mai nauyi a wuyanku ba.”

Mahara sun Faɗa musu da Yaƙi

28 Magabta suna cikin Ayiyat! Sun bi ta Migron! Sun bar kayayyakinsu a Mikmash! 29 Sun ƙetare hanya suka kwana a Geba! Mutanen Rama suka firgita. Mutanen da suke cikin Gibeya, garin sarki Saul, sun gudu. 30 Ku yi ihu, ku mutanen Gallim! Ku kasa kunne, ku mutanen Layish! Ku amsa, ku mutanen Anatot! 31 Jama'ar Madmena da na Gebim suna gudu su tsira da rayukansu. 32 Yau abokan gāba suna cikin Nob, daga can suke nuna wa Dutsen Sihiyona yatsa, wato wanda yake cikin Urushalima. 33 Ubangiji Mai Runduna zai sa su ragargaje har ƙasa, kamar rassan da aka sassare daga itace. Masu girmankai da manyansu za a datse su ƙasa, a ƙasƙantar da su. 34 Ubangiji zai sassare su har ƙasa kamar yadda ake sassare itatuwa da gatari a tsakiyar kurmi, kamar yadda itatuwa mafi kyau na Lebanon za su fāɗi.

Ishaya 11

Mulkin Adalci na Ɗan Yesse

1 Gidan sarautar Dawuda kamar itacen da aka sare ne, amma kamar yadda rassa sukan toho daga cikin kututture, hakanan za a sami sabon sarki daga zuriyar Dawuda. 2 Ikon Ubangiji zai ba shi hikima, Da sani, da gwaninta yadda zai mallaki mutanensa. Zai kuwa san nufin Ubangiji, ya kuma yi tsoronsa, 3 Zai ji daɗin yin hidimarsa. Ba zai yi shari'ar ganin ido ko ta waiwai ba. 4 Zai yi wa matalauta shari'a daidai. Zai kuma kāre hakkin masu tawali'u. Bisa ga umarninsa za a hukunta ƙasar, Mugaye za su mutu. 5 Zai yi mulkin mutanensa da adalci da mutunci. 6 Kyarketai da tumaki za su zauna tare lafiya. Damisoshi za su kwanta tare da 'yan awaki. 'Yan maruƙa da kwiyakwiyan zaki za su yi kiwo tare, Ƙananan yara ne za su lura da su. 7 Shanu da beyar za su yi kiwo tare, 'Yan maruƙansu da kwiyakwiyansu za su kwanta lafiya. Zaki zai ci ciyawa kamar sā. 8 Jariri zai yi wasa kusa da maciji mai mugun dafi Amma ba zai cuta ba. 9 A kan Sihiyona, dutse tsattsarka, Ba wani macuci ko mugu. Ƙasar za ta cika da sanin Ubangiji Kamar yadda tekuna suke cike da ruwa.

Masu Zaman Dole sun Komo da Nasara

10 Rana tana zuwa sa'ad da sabon sarki zai fito daga cikin gidan sarautar Dawuda, zai zama alama ga sauran al'umma. Za su tattaru a birnin sarautarsa su girmama shi. 11 A wannan rana Ubangiji zai sāke zuwa, ya nuna ikonsa. Zai komo da mutanensa gida waɗanda suka ragu a Assuriya, da Masar, da ƙasashen Fatros, da Habasha, da Elam, da Babila, da Hamat, da kuma ƙasashen bakin gāɓa da na tsibiran teku. 12 Ubangiji zai ɗaga tuta, alama ce ta nuna wa sauran al'umma, ya sāke tattara jama'ar Isra'ila da ta Yahuza waɗanda aka warwatsa, ya sāke komo da su daga kusurwoyi huɗu na duniya. 13 Masarautar Isra'ila ba za ta ƙara jin kishin Yahuza ba, Yahuza kuma ba za ta zama abokiyar gābar Isra'ila ba. 14 Tare za su fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi daga yamma, su washe mutanen da suke wajen gabas. Za su ci nasara a kan mutanen Edom da na Mowab, jama'ar Ammon kuwa za su yi musu biyayya. 15 Ubangiji zai kawo iska mai zafi wadda za ta busar da Kogin Nilu, da na Yufiretis. Zai bar ƙananan rafuffuka bakwai ne kaɗai, don kowa da kowa ya taka ya haye. 16 Za a yi babbar karauka daga Assuriya domin sauran mutanen Isra'ila da suka ragu a can, kamar yadda aka yi wa kakanninsu sa'ad da suka bar Masar.

Ishaya 12

Waƙar Godiya

1 Rana tana zuwa sa'ad da jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ina yabonka ya Ubangiji! A dā ka yi fushi da ni, Amma yanzu kana yi mini ta'aziyya, ba za ka ƙara yin fushi da ni ba. 2 Allah ne Mai Cetona, Zan dogara gare shi, ba zan ji tsoro ba. Ubangiji ne yake ba ni iko da ƙarfi, Shi ne Mai Cetona.” 3 Kamar yadda ruwan daɗi yake sa mai jin ƙishirwa farin ciki, Hakanan jama'ar Allah suke farin ciki sa'ad da ya cece su. 4 A wannan rana jama'a za su raira waƙa, su ce, “Ku yi wa Ubangiji godiya! Ku nemi taimako a gare shi! Ku faɗa wa dukan sauran al'umma abin da ya aikata! Ku faɗa musu irin girman da yake da shi! 5 Ku raira waƙa ga Ubangiji, saboda manyan ayyuka da ya aikata. Bari dukan duniya ta ji labarin. 6 Bari dukan waɗanda suke zaune a Sihiyona su yi sowa su raira waƙa! Gama Mai Tsarki, Allah na Isra'ila, mai girma ne, Yana zaune tare da mutanensa.”

Ishaya 13

Annabci a kan Babila

1 Wannan shi ne saƙo a kan Babila, wanda Ishaya ɗan Amoz ya karɓa daga wurin Allah. 2 A kan tudun da yake faƙo ka kafa tutar yaƙi, ka ta da murya ka ba mayaƙa umarni, ka ɗaga hannu, ka ba su alamar kama yaƙi a ƙofofin birni mai alfarma. 3 Ubangiji ya kira mayaƙansa masu jin kansu, masu ƙarfin zuciya, domin su yi jahadi, su hukunta wa waɗanda suke fushi da su. 4 Ji hayaniyar da ake yi a duwatsu da amon babban taron jama'a. Amon al'ummai da mulkoki suna tattaruwa. Ubangiji Mai Runduna yana shirya mayaƙansa domin yaƙi. 5 Suna zuwa daga manisantan ƙasashe, daga kan iyakokin duniya. Ubangiji yana zuwa da fushinsa, ya lalatar da dukan ƙasar. 6 Ku yi ihu saboda shan azaba, ranar Ubangiji ta yi kusa. Ranar da Mai Iko Dukka zai kawo hallaka. 7 Hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa. 8 Dukansu za su firgita, azaba za ta ci ƙarfinsu kamar mace wadda take shan azabar naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu za su cika da kunya. 9 Ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana ce ta zafin fushinsa. Za a mai da duniya jeji, a hallaka kowane mai zunubi. 10 Kowane tauraro, da kowace ƙungiyar taurari za su daina ba da haske. Rana za ta yi duhu lokacin da ta fito, wata kuwa ba zai ba da haske ba. 11 Ubangiji ya ce, “Zan kawo masifa a duniya. Zan hukunta dukan mugaye saboda zunubansu. Zan ƙasƙantar da kowane mai girmankai. Zan hukunta kowane mai izgili da mai mugunta. 12 Sauran da suka ragu za su fi zinariya wuyar samuwa. 13 Zan sa sammai su yi rawar jiki, duniya kuwa za a girgiza ta a inda take, a wannan rana sa'ad da ni, Ubangiji Mai Runduna, na nuna fushina. 14 “Baƙin da suke zaune a Babila za su gudu zuwa ƙasashensu, suna a warwatse kamar bareyin da suke tsere wa maharbansu, kamar tumakin da ba su da makiyayi. 15 Duk wanda aka kama za a soke shi ya mutu. 16 Sa'ad da suke cikin halin ƙaƙa naka yi, za a fyaɗa 'ya'yansu ƙasa, su mutu. Za a washe gidajensu, a yi wa matansu faɗe.” 17 Ubangiji ya ce “Ina zuga mutanen Mediya, don su faɗa wa Babila da yaƙi. Ba su kula da azurfa ba, ba kuwa za a jarabce su da zinariya ba. 18 Da bakkuna da kibansu, za su karkashe samari. Ba za su nuna jinƙai ga jarirai ba, ba kuwa za su ji tausayin 'yan yara ba. 19 Daular Babila ita ce mafi kyau duka, abin fāriya ce ga jama'arta. Amma ni Ubangiji, zan kaɓantar da ita kamar yadda na yi da Saduma da Gwamrata! 20 Ba wanda zai ƙara zama a cikinta. Ba wani Balaraben da yake yawo da zai kafa alfarwarsa a can. Ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can. 21 Za ta zama wurin zaman namomin jejin hamada, inda mujiyoyi za su yi sheƙarsu. Jiminai za su zauna a can, awakin jeji za su yi ta warnuwa a cikin kufanta. 22 A hasumiyarta da fādodinta za a ji amsar ihun koke-koken kuraye da na diloli. Lokacin Babila ya yi! Kwanakinta sun kusa ƙarewa!”

Ishaya 14

Takama Gāba da Sarkin Babila

1 Ubangiji zai sāke yi wa jama'arsa Isra'ila jinƙai, ya zaɓe su su zama nasa. Zai sāke sa su zauna a ƙasarsu, baƙi ma za su zo su zauna tare da su. 2 Al'ummai da yawa za su taimaki jama'ar Isra'ila su koma ƙasarsu wadda Ubangiji ya ba su. A can sauran al'umma za su yi wa Isra'ila hidima kamar bayi. Waɗanda suka kama Isra'ilawa a dā yanzu Isra'ilawa za su kama su. Jama'ar Isra'ila za ta mallaki waɗanda suka taɓa zaluntarsu. 3 Ubangiji Allah kuwa zai sawwaƙe wa jama'ar Isra'ila azaba da wahala da suke sha, daga kuma aikin da aka tilasta su su yi. 4 Sa'ad da ya aikata wannan za su yi wa Sarkin Babila ba'a. Za su ce, “Mugun sarkin ya fāɗi, ba zai ƙara zaluntar kowa ba! 5 Ubangiji ya ƙare mulkin mugun, 6 wanda yake zaluntar jama'a a husace, bai taɓa daina tsananta wa al'ummai ba, wanda ya ci da yaƙi. 7 Yanzu magana ta ƙare, duniya duka tana jin daɗin hutawa da salama. Kowa na ta raira waƙar murna. 8 Itatuwan fir da itatuwan al'ul na Lebanon suna murna da faɗuwar sarkin! Ba wanda zai tasar musu da sara! 9 “Lahira tana shirye-shiryen yi wa Sarkin Babila maraba. Fatalwan waɗanda suka yi iko a duniya suna kaiwa suna komowa a hargitse. Fatalwan sarakuna suna tashi daga gadajen sarautarsu. 10 Dukansu suka yi kira gare shi, suka ce, ‘Ashe, kai ma rarrauna ne kamarmu! Ka zama ɗaya daga cikinmu. 11 Dā ana ɗaukaka ka da kaɗe-kaɗen garaya, amma yanzu ga ka a lahira! Kana kwance a kan tsutsotsi. Kana rufe da tsutsotsi!’ ” 12 Ya Sarkin Babila, kai da kake tauraron asubahi mai haske, ka fāɗo daga sama. A dā ka ci al'ummai da yaƙi amma yanzu an fyaɗa ka ƙasa. 13 Ka yi niyyar hawan sama, ka sa gadon sarautarka a kan taurari mafi nisa. Ka zaci za ka zauna kamar sarki a kan dutsen nan na arewa, inda alloli suke tattare. 14 Kai ka ce za ka hau can bisa kan taurari, ka zama kamar Mai Iko Dukka. 15 Amma a maimakon haka an saukar da kai a sashe mafi zurfi a lahira. 16 Matattu za su zura maka ido su yi mamaki. Za su yi tambaya su ce, “Ashe, ba wannan mutum ba ne ya girgiza duniya, ya sa mulkoki suka jijjigu? 17 Wannan shi ne wanda ya hallaka birane, ya mai da duniya hamada, wanda bai taɓa sakin ɗaurarru ko ya bar su su koma gida ba?” 18 Dukan sarakunan duniya suna kwance a cikin manya manyan kaburburansu, 19 amma kai ba ka sami kabari ba, jefar da gawarka aka yi don ta ruɓe. Aka hautsuna gawarka da gawawwakin mayaƙan da aka kashe cikin yaƙi. Tare da su aka jefa ka gangaren dutse, aka tattake. 20 Ba za a binne ka kamar sauran sarakuna ba, saboda ka lalata da ƙasarka, ka karkashe mutanenka. Daga cikin mugayen iyalinka ba wanda zai ragu. 21 A fara yanyanka su! 'Ya'ya maza na sarkin nan za su mutu saboda zunuban kakanninsu. Daga cikinsu ba wanda zai taɓa mallakar duniya, ko ya cika ta da birane.

Allah zai Hallaka Babila

22 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan fāɗa wa Babila da yaƙi, in lalata ta, ba abin da zan bari, ko yara, ba wanda zai ragu. Ni, Ubangiji, na faɗi wannan. 23 Zan su Babila ta zama fadama, mujiyoyi za su zauna a can. Zan kuwa share Babila da tsintsiyar da za ta share kome. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”

Allah Zai Hallaka Assuriya

24 Ubangiji Mai Runduna ya rantse, ya ce, “Abin da na riga na shirya, haka zai faru. Abin da na yi niyyar yi, za a yi. 25 Zan hallaka Assuriyawa a ƙasata ta Isra'ila, in tattake su a kan duwatsuna. Zan 'yantar da jama'ata daga karkiyar Assuriyawa, daga nauyin da suka tilasta musu su ɗauka. 26 Abin da na shirya zan yi wa duniya, shi ne in miƙa hannuna domin in hukunta wa al'ummai.” 27 Ubangiji Mai Runduna ne ya ƙudura ya yi wannan, ya miƙa dantsensa don ya yi hukunci, ba kuwa mai iya hana shi.

Annabci a kan Filistiya

28 Wannan shi ne jawabin da aka yi shelarsa a shekarar da sarki Ahaz ya rasu. 29 Ku mutanen Filistiya, sandan da ake d�kanku da shi ya karye, amma kada wannan ya zamar muku dalilin murna. Gama idan wani maciji ya mutu, wani mafi mugunta zai maye gurbinsa. Ƙwan maciji yake ƙyanƙyashe maciji mai tashi sama! 30 Ubangiji zai zama makiyayin jama'arsa wadda take talauce, zai kuma sa su zauna lafiya. Amma ku Filistiyawa, zai aukar muku da matsananciyar yunwa, wadda ba za ta bar ko ɗayanku da rai ba. 31 Ku yi kururuwa, ku yi kuka na neman taimako, dukanku biranen Filistiya! Ku razana dukanku! Ƙurar da ta murtuke tana zuwa daga arewa, mayaƙa ne, ba kuwa matsorata a cikinsu. 32 Ƙaƙa za mu amsa wa manzannin da suka zo gare mu daga Filistiya? Za mu faɗa musu, cewa Ubangiji ya tabbatar da Sihiyona, jama'arsa da take shan wahala kuwa za su sami zaman lafiya a can.

Ishaya 15

Annabci a kan Mowab

1 Wannan shi ne jawabi a kan Mowab. Biranen Ar da Kir, an hallaka su dare ɗaya, ƙasar ta yi tsit, ba kowa. 2 Mutanen Dibon sun hau kan tuddai don su yi kuka a matsafarsu. Mutanen Mowab suna kuka da baƙin ciki saboda biranen Nebo da Medeba, sun aske kawunansu da gyammansu saboda baƙin ciki. 3 Mutane a tituna sun sa tsummoki a jikinsu, suka taru a filayen taruwa na birni da a kan rufin ɗakuna, sai makoki suke suna ta kuka. 4 Mutanen Heshbon da na Eleyale suka yi kuka da ƙarfi, har ana iya jin kukansu daga Yahaza. Har mayaƙa ma sun yi rawar jiki, zuciyarsu ta karai. 5 Zuciyata ta yi kuka ainun saboda Mowab! Mutane sun gudu zuwa cikin garin Zowar. Waɗansu sun haura zuwa Luhit, suna tafe suna kuka, waɗansu sun tsere zuwa Horonayim, suna hargowa saboda baƙin ciki. 6 Rafin Nimra ya ƙafe, ciyawar da take gefensa ta bushe, ba sauran wani ɗanyen abu. 7 Mutane sun haye kwarin Larabawa, suna ƙoƙari su tsere da dukan abin da suka mallaka. 8 A ko'ina a kan iyakokin Mowab, sai ƙugin kukansu ake ji. Ana kuwa ji daga garuruwan Eglayim da Biyer-elim. 9 A garin Dibon, kogin ya yi ja wur da jini, Allah kuwa ya tanada wa mutanen wurin abin da ya fi wannan muni. Hakika za a yi wa duk wanda ya ragu a Mowab mummunan kisa.

Ishaya 16

1 Daga birnin Sela a hamada, mutanen Mowab za su aiko da kaiwar rago ga mai mulki a Urushalima. 2 Za su dakata a gaɓar kogin Arnon, za su yi ta kai da kawowa kamar tsuntsayen da aka kora daga sheƙunansu. 3 Suna ce wa mutanen Yahuza, “Ku faɗa mana abin da za mu yi. Ku kāre mu, ku bar mu mu huta a inuwarku mai sanyi kamar inuwar itace da tsakar rana. Mu 'yan gudun hijira ne, ku ɓoye mu inda ba wanda zai gan mu. 4 Ku bar mu mu zauna ƙasarku. Ku kāre mu daga masu neman hallaka mu.” Zalunci da hallakarwa za su ƙare, masu lalatar da ƙasar za su ƙare. 5 Sa'an nan wani daga cikin zuriyar Dawuda zai zama sarki. Zai mallaki jama'a da aminci da ƙauna. Zai aikata abin da yake daidai da hanzari, zai sa a aikata adalci. 6 Mutanen Yahuza sun ce, “Mun ji irin fāriyar da mutanen Mowab suke yi. Mun sani su masu girmankai ne, masu ruba, amma fankamarsu ta banza ce.” 7 Mutanen Mowab za su yi kuka saboda wahalar da suke sha. Dukansu za su yi kuka sa'ad da suka tuna da kyakkyawan abincin da suka riƙa ci a birnin Kir-hareset. Za a kore su har su fid da zuciya. 8 Gonakin da suke kusa da Heshbon, da gonakin inabin da suke Sibma an lalatar da su, gonakin inabin nan waɗanda ruwan inabinsu yake sa masu mulkin al'ummai su bugu. Da kurangunsu sun taɓa yaɗuwa zuwa gabas har suka kai birnin Yazar da cikin hamada, wajen yamma kuma sai da suka dangana da gefen Tekun Gishiri. 9 Yanzu ina kuka saboda gonakin inabin Sibma kamar yadda na yi wa na Yazar. Na zub da hawayena saboda Heshbon da Eleyale, domin ba a sami kaka mai albarka ba, wadda za ta sa mutane yin murna. 10 Ba wanda yake farin ciki a cikin sauruka masu dausayi. Ba wanda yake sowa ko waƙa a cikin gonakin inabi. Ba mai matse ruwan inabi, sowar murna ta ƙare. 11 Na yi nishi da ɓacin zuciya a kan Mowab, na yi nishi da baƙin ciki saboda Kir-heres. 12 Mutanen Mowab sun gajiyar da kansu da zuwa wurin matsafarsu na kan dutse da masujadarsu, suna addu'a, amma ba zai amfana musu kome ba. 13 Wannan shi ne jawabin da Ubangiji ya riga ya yi a kan Mowab. 14 Yanzu Ubangiji ya ce, “A shekara uku daidai, dukiyar Mowab mai yawan nan za ta ƙare. Daga cikin ɗumbun mutanenta 'yan kaɗan ne kaɗai zai su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”

Ishaya 17

Annabci a kan Dimashƙu

1 Wannan shi ne jawabi a kan Dimashƙu. Ubangiji ye ce, “Dimashƙu ba za ta ƙara zama birni ba, za ta zama tsibin kufai ne kawai. 2 Za a watse a bar biranen Suriya har abada. Za su zama makiyayar tumaki da shanu. Ba wanda zai tsoratar da su. 3 Ba za a kāre Isra'ila ba, Dimashƙu kuma za ta rasa 'yancinta. Suriyawan da suka ragu za su sha wulakanci kamar mutanen Isra'ila. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗa.”

Hukunci a kan Isra'ila

4 Ubangiji ya ce, “Rana taba zuwa, ran da girman Isra'ila zai ƙāre, fatara za ta gāje gurbin dukiyarsu. 5 Isra'ila za ta zama kamar gonar da aka girbe, aka yanke amfaninta, ta zama marar kome kamar gona a kwarin Refayawa sa'ad da aka ɗebe amfaninta. Mutane kima ne kurum za su ragu. 6 Isra'ila kuma za ta zama kamar itacen zaitun wanda aka karkaɗe 'ya'yansa, aka bar biyu ko uku kawai a ƙwanƙolin itacen, ko kuma aka bar huɗu ko biyar a rassansa. Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na faɗa.” 7 A wannan rana, mutane za su juyo neman taimako ga Mahaliccinsu, Allah Mai Tsarki na Isra'ila. 8 Ba za su ƙara dogara ga bagaden da suka yi da hannuwansu ba, ko kuwa su dogara ga ayyukan hannuwansu, ko keɓaɓɓun wuraren da suke wa gumaka sujada, ko bagadai don ƙona turare. 9 A wannan rana, za a watse a bar birane masu ƙaƙƙarfar kagara su zama kufai a jeji kuwa kamar rassan da aka watsar a gaban jama'ar Isra'ila. 10 Isra'ila, kin manta da Allah wanda ya kuɓutar da ke, wanda ya kāre ki kamar babban dutse. Kin dasa wa kanki lambuna masu ni'ima don ki yi wa gumaka sujada. 11 Amma ko da za su toho su yi fure a safiyar da kuka dasa su, duk da haka ba za a girbe kome ba. Wahala ce kaɗai da azabar da ba ta warkuwa.

An Ci Al'ummai, Abokan Gāba

12 Al'ummai masu iko sun hargitse suna ta rugugi kamar rurin teku, kamar karon manyan raƙuman ruwa. 13 Al'ummai sun ci gaba kamar sukuwar raƙuman ruwa, amma Allah ya tsauta musu suka kuwa janye, aka kora su kamar ƙura a gefen dutse, kamar kuma tattaka a cikin guguwa. 14 Da maraice sukan ba da tsoro, amma da safe ba su! Wannan ita ce ƙaddarar duk wanda ya washe ƙasarmu!

Ishaya 18

Annabci a kan Habasha

1 A hayin kogunan Habasha akwai wata ƙasa inda ake jin amon fikafikai. 2 Daga waccan ƙasar wakilai sukan gangaro daga Kogin Nilu a cikin jiragen ruwa da aka yi da iwa. Ku koma gida, ku manzanni masu gaggawa! Ku kai saƙo ƙasarku, can a mafarin Kogin Nilu, zuwa ga al'ummarku mai ƙarfi mai iko, zuwa ga dogayen mutanenku masu sulɓin jiki, waɗanda ake jin tsoronsu ko'ina a duniya. 3 Kowane mutum da yake a duniya ya kasa kunne, ko wanne da yake zaune a duniya, ya duba tutar, alama da za a ɗaga sama a ƙwanƙolin duwatsu, ya kasa kunne ga busar ƙaho! 4 Ubangiji ya ce mini “Zan duba daga samaniya a hankali kamar yadda raɓa take saukowa a natse da gumin dare a lokacin girbi, hasken rana kuma a yini. 5 Kafin a tattara 'ya'yan inabi, sa'ad da furanni duka suka karkaɗe, 'ya'yan inabi suna ta nuna, haka magabta za su hallaka Habasha a sawwaƙe kamar yadda ake faffalle rassan kurangar inabi da wuƙa. 6 Za a bar gawawwakin sojojinsu a fili domin tsuntsaye da namomin jeji su zama abincin tsuntsaye de bazara, abincin namomin jeji kuma a lokacin sanyi.” 7 A wannan lokaci Ubangiji Mai Runduna zai karɓi hadayu daga wannan ƙasa, a mafarin Kogin Nilu, wato wannan ƙaƙƙarfar al'umma mai iko, waɗannan dogayen mutane masu sulɓin jiki, waɗanda ake jin tsoronsu ko'ina a duniya. Za su zo Dutsen Sihiyona, inda ake yi wa Ubangiji Mai Runduna sujada.

Ishaya 19

Annabci a kan Masar

1 Wannan shi ne jawabi a kan Masar. Ubangiji yana zuwa Masar a kan girjije a sukwane. Gumakan Masarawa za su yi rawar jiki a gabansa, zuciyar Masarawa za ta karai. 2 Ubangiji ya ce, “Zan ta da hargitsi a yi yaƙin basasa a Masar, ɗan'uwa ya yi gāba da ɗan'uwa, maƙwabci kuma gaba da maƙwabci. Biranen da suke hamayya za su yi faɗa da juna, sarakunan da suke hamayya kuma za su yi faɗa saboda neman iko. 3 Zan warware shirye-shiryen Masarawa in sa ku karai. Za su roƙi taimako ga gumakansu, za su je kuma su yi shawara da mabiyansu, su kuma nemi shawarar kurwar matattu. 4 Zan ba da Masarawa a hannun azzalumi a hannun mugun sarki kuma da zai mallake su. Ni, Ubangiji Mai Runduna, na faɗi wannan.” 5 Ruwan Kogin Nilu zai ƙafe, a hankali kogin zai bushe. 6 Mazaunan kogin za su ji wari sa'ad da yake ƙafewa a hankali. Iwa da jema za su bushe. 7 Dukan amfanin gonakin da aka shuka a gaɓar Kogin Nilu za su bushe, iska ta fyauce su. 8 Duk wanda sana'arsa ta kama kifi ce a Kogin Nilu zai yi ƙugi ya yi kuka, gama ƙugiyoyinsa da tarunansa za su zama marasa amfani. 9 Waɗanda suke yin tufafin lilin za su fid da zuciya, 10 shugabanni da ma'aikata za su karai su kuma damu. 11 Shugabannin birnin Zowan wawaye ne! Mutanen Masar mafi hikima za su ba da gurguwar shawara! Ta ƙaƙa za su iya dosar sarki su faɗa masa, cewa su ne suka gāji masana da sarakuna na dā can? 12 Sarkin Masar, ina mashawartan nan naka masu hikima? Watakila za su iya faɗa maka shirye-shiryen da Ubangiji Mai Runduna ya yi domin Masar. 13 Shugabannin Zowan da na Memfis wawaye ne. Su ake zaton za su bi da al'ummar, amma sai suka bi da su a karkace. 14 Ubangiji ne ya sa su ba da gurguwar shawara. Sakamakon haka sai Masar ta yi ta aikata dukan abu a hugunce, tana tangaɗi kamar bugagge wanda santsi na kwasarsa cikin aman da ya yi. 15 A Masar duka, attajiri da matalauci, ƙarami ko babba, ba wanda zai iya yin wani taimako. 16 Lokaci zai yi in da zuciyar mutanen Masar za ta narke kamar mata. Za su yi rawar jiki da razana lokacin da suka ga Ubangiji Mai Runduna ya miƙa hannunsa don ya hukunta su. 17 Mutanen Masar za su firgita saboda Yahuza, kowane lokaci za su tuna da ƙaddarar da Ubangiji Mai Runduna ya shirya dominsu. 18 A wannan rana, za a yi amfani da harshen Ibrananci a birane biyar na Masar. Mutanen da suke can za su riƙa yin rantsuwarsu da sunan Ubangiji Mai Runduna. Za a sa wa ɗaya daga cikin biranen nan suna, “Birnin Hallaka.” 19 A wannan rana, za a gina wa Ubangiji bagade a ƙasar Masar, za a keɓe masa ginshiƙi na dutse a kan iyakar Masar. 20 Za su zama alamu na kasancewar Ubangiji Mai Runduna a Masar. Sa'ad da aka zalunci mutanen da suke can, za su yi kira ga Ubangiji su nemi taimako, zai aika musu wanda zai kuɓutar da su. 21 Ubangiji zai bayyana kansa ga mutanen Masar, sa'ad da ya yi haka kuwa, za su karɓe shi, su yi masa sujada, su kuma kawo masa hadayu da sadakoki. Za su yi masa alkawarai ƙwarara, su kuwa cika abin da suka alkawarta. 22 Ubangiji zai hukunta Masarawa, amma zai warkar da su. Za su juyo gare shi, shi kuma zai ji addu'o'insu ya warkar da su. 23 A wannan rana, za a yi wata babbar hanya tsakanin Masar da Assuriya. Mutanen ƙasashen nan biyu za su yi ta kai da kawowa tsakaninsu, al'ummai biyu za su yi sujada tare. 24 A wannan rana, za a lasafta Isra'ila tare da Masar da Assuriya, waɗannan al'ummai uku za su zama albarka ga dukan duniya. 25 Ubangiji Mai Runduna zai sa musu albarka, ya ce, “Zan sa muku albarka, ke Masar, jama'ata, da take Assuriya wadda na halitta, da ke kuma Isra'ila zaɓaɓɓiyar jama'ata.”

Ishaya 20

Assuriya za ta Ci Masar da Habasha

1 Bisa ga umarnin Sargon, Sarkin Assuriya, sai sarkin yaƙin Assuriya ya fāɗa wa Ashdod, birnin Filistiyawa, da yaƙi. 2 A wannan lokaci Ubangiji ya riga ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz, cewa ya tuɓe tsummokin da yake saye da su, ya kuma tuɓe takalmansa. Shi kuwa ya yi biyayya ya yi ta yawo tsirara, ba kuma takalmi a ƙafarsa. 3 Sa'ad da aka ci Ashdod, sai Ubangiji ya ce, “Bawana Ishaya ya yi ta yawo tsira, ba kuma takalmi a ƙafarsa har shekara uku. Wannan ita ce alamar abin da zai faru a ƙasa Masar da Habasha. 4 Sarkin Assuriya zai kwashe kamammun yaƙi waɗanda ya kama a ƙasashen nan biyu, ya tafi da su tsirara. Matasa da manya kuma ba takalmi a ƙafafunsu, asirinsu a tsiraice, don a kunyata Masar. 5 Waɗanda suke dogara ga Habasha, suna kuwa fāriya da Masar, za su ruɗe, sa zuciyarsu zai wargaje. 6 A wannan rana mutanen da suke zaune a gaɓar Filistiyawa za su ce, ‘Dubi abin da ya faru ga jama'ar da muka dogara da su don su tsare mu daga Sarkin Assuriya! Ƙaƙa za mu yi mu tsira?’ ”

Ishaya 21

Annabci a kan Babila

1 Wannan shi ne jawabi a kan Babila. Kamar yadda guguwa take tasowa daga hamada, haka masifa za ta auko daga wata ƙasa mai razanarwa. 2 Na ga wahayi na waɗansu mugayen abubuwa, wato na cin amana da hallakarwa. Rundunar sojojin Elam, ku kama yaƙi! Rundunar sojojin Mediya ku kewaye birane da yaƙi. Allah zai kawar da wahalar da Babila ta haddasa. 3 Abin da na gani, da abin da na ji a wahayin, ya razanar da ni, ya sa ni cikin azaba kamar ta mace mai naƙuda. 4 Kaina ya yi yum, ina ta rawar jiki saboda tsoro. Ina ta marmarin maraice ya yi, amma bai kawo mini kome ba, sai razana. 5 A wahayin na ga an shirya biki, an shisshimfiɗa darduma inda waɗanda aka gayyata za su zauna. Suna ci suna sha. Farat ɗaya sai aka ji umarni cewa, “Jarumawa! Ku shirya garkuwoyinku.” 6 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Tafi ka sa mai tsaro, ka faɗa masa ya riƙa ba da labarin abin da ya gani. 7 Idan ya ga mutane biyu biyu suna zuwa a kan dawakai, waɗansu kuma a kan raƙuma da jakuna, ka faɗa masa ya lura da su sosai.” 8 Mai tsaro ya ce, “Ya mai girma, ina ta tsaro dare da rana a wurin da aka sa ni.” 9 Farat ɗaya sai ga su sun zo! Suna tafe a kan dawakai biyu biyu. Sai mai tsaro ya ba da labari cewa, “Babila ta fāɗi! Dukan gumakan da suke yi wa sujada an ragargaza su har ƙasa.” 10 Ya jama'ata, an buga ku kamar yadda ake bugun alkama a masussuka. Amma yanzu na kawo muku albishir wanda na ji daga wurin Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila.

Annabci a kan Edom

11 Wannan shi ne jawabi a kan Edom. Wani daga Edom ya kira ni ya ce, “Ya mai tsaro, gari ya kusa wayewa? Ka gaya mini har sai yaushe zai waye?” 12 Sai na amsa na ce, “Gari zai waye, amma za a sāke yin dare! Idan kana so ka sāke yin dare! Idan kana so ka sāke yin tambaya, sai ka sāke zuwa, ka tambaya.”

Annabci a kan Arabiya

13 Wannan shi ne jawabi a kan Arabiya. Ya ku jama'ar Dedan, waɗanda ayarorinku suka yi zango a ƙasar Arabiya wadda take faƙo, 14 ku ba jama'a waɗanda suka zo gare ku masu jin ƙishi ruwa su sha. Ya ku jama'ar ƙasar Tema, ku ba 'yan gudun hijira abinci. 15 Mutane suna gudu don su tsere wa takuban da za su kashe su, da bakkunan da za su harbe su, su kuma tsere wa dukan hatsarorin yaƙi. 16 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Saura shekara ɗaya tak girman kabilar Kedar zai ƙare. 17 Jarumawan Kedar su ne maharba, amma sai kaɗan za su ragu daga cikinsu, ni, Ubangiji Allah na Isra'ila, na faɗa.”

Ishaya 22

Annabci a kan Kwarin Wahayi

1 Wannan shi ne jawabi a kan kwarin wahayi. Me yake faruwa? Me ya sa jama'ar birni duka suke biki a kan rufin gidaje? 2 Birnin duka ya ruguntsume, cike da hayaniya da tashin hankali. Mutanenku da suka mutu ba su mutu suna yaƙi ba. 3 Dukan shugabanninku sun gudu, an kuwa kama su tun kafin su harba ko kibiya ɗaya. Dukanku da aka iske tare, aka kama ku, ko da yake kuka gudu da nisa. 4 Ni dai ƙyale ni kurum, in yi ta kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta'azantar da ni, saboda yawancin mutanena sun mutu. 5 Wannan shi ne lokacin gigicewa, da shan ɗibga, da ruɗewa a cikin kwarin wahayi, Ubangiji Allah Mai Runduna shi ya aukar mana da shi. An ragargaza garukan birninmu har ƙasa, ana jin amsar kuwwar koke-kokenmu na neman taimako a cikin tsaunuka. 6 Sojojin ƙasar Elam sun zo kan dawakai suna rataye da kwari da baka. Sojojin ƙasar Kir sun shirya garkuwoyinsu. 7 Kwarurukansu masu dausayi na ƙasar Yahuza suna cike da karusai, sojoji kuma a kan dawakai suna tsattsaye a ƙofofin Urushalima. 8 Dukan kagaran Yahuza sun rushe. Sa'ad da wannan ya faru kun kwaso makamai daga cikin taskar makamai. ga wuraren da suke bukatar gyara a garukan Urushalima. Ku ƙidaye dukan gidaje da suke cikin Urushalima, kuka rushe waɗansu gidaje don ku sami duwatsun da za ku gyara garukan Urushalima. Don ku tanada ruwa a cikin birnin, 11 kun gina matarar ruwa a jikin garuka don ta tare ruwan da yake gangarowa daga tsohon tafki. Amma ba ku kula da Allah ba, wanda ya shirya wannan tuntuni, wanda kuma ya sa wannan ya kasance. 12 Ubangiji Mai Runduna yana kiranku ku yi kuka, ku yi makoki, ku aske kawunanku, ku sa tsummoki. 13 A maimakon haka sai kuka yi dariya, kuka yi biki. Kuka yanka tumaki da shanu don ku ci, kuka sha ruwan inabi. Kuka ce, “Gara mu ci mu sha! Gobe za mu mutu.” 14 Ubangiji Mai Runduna ya ce mini, “Ko kusa ba za a gafarta musu wannan mugunta ba muddin ransu. Ni, Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Eliyakim zai Gāji Shebna

15 Ubangiji Mai Runduna ya faɗa mini in tafi wurin Shebna, mai hidimar iyalin gidan sarki, in ce masa, 16 “Kana tsammani kai wane ne? Wa ya ba ka 'yancin sassaƙa wa kanka kabari a jikin duwatsu? 17 Yana yiwuwa kai wani abu ne, amma Ubangiji zai ɗauke ka, ya jefar. 18 Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasar da ta fi girma. A can za ka mutu a kusa da karusan da kake fāriya da su. Abin kunya kake a gidan maigidanka! 19 Ubangiji zai fisshe ka daga maƙaminka, ya ƙasƙantar da kai daga babban matsayinka!” 20 Ubangiji ya ce wa Shebna, “Idan haka ya faru zan aika wa bawana Eliyakim ɗan Hilkiya. 21 Zan sa masa tufafin sarautarka, in ɗaura masa ɗamara, in kuma ba shi dukan ikon da kake da shi. Zai zama kamar uba ga jama'ar Urushalima da na Yahuza. 22 Zan sa shi ya zama sarki mai cikakken iko, na zuriyar Dawuda. Mabuɗan fāda suna hannunsa, abin da ya buɗe, ba mai ikon rufewa. Abin da ya rufe kuwa ba mai ikon buɗewa. 23 Zan kafa shi da ƙarfi a wurin kamar turke, zai kuwa zama sanadin daraja ga dukan iyalinsa. 24 “Amma dukan 'yan'uwansa da masu dogara gare shi za su zama nawaya a gare shi. Za su rataya gare shi kamar tukwane da ƙoren da aka sa a ragaya! 25 Sa'ad da wannan ya faru ragayar da aka ɗaura tam za ta tsinke ta fāɗo. Wannan shi ne ƙarshen kowane abin da aka sa a cikin ragayar ke nan. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Ishaya 23

Annabci a kan Taya da Sidon

1 Wannan shi ne jawabi a kan Taya. Ku yi hargowa ta baƙin ciki, ku matuƙan jiragen ruwan teku! An lalatar da tashar jiragen ruwan garinku na Taya. Gidajenta da gaɓarta sun rurrushe. Sa'ad da jiragen ruwanku suka komo daga Kubrus za ku ji labarin. 2 Ku yi kuka ku fataken Sidon! Kun aika da mutane 3 a hayin teku don su yi muku saye da sayarwa na hatsin da ake nomawa a Masar, su yi hulɗa da dukan sauran al'umma. 4 Birnin Sidon, ke abar kunya ce! Teku da manyan zurfafan ruwaye sun yanke hulɗa da ke, sun ce, “Ban taɓa haihuwar 'ya'ya ba, ban taɓa goyon 'ya'ya mata ko maza ba.” 5 Har Masarawa ma za su firgita su razana, sa'ad da suka ji, cewa an hallakar da Taya. 6 Ku yi ruri da baƙin ciki, ku jama'ar bakin teku, ku yi ƙoƙari ku tsere zuwa Tarshish! 7 Ya yiwu kuwa a ce wannan Taya ce birnin farin ciki, wadda aka kafa ta tuntuni? Wannan kuwa ita ce birnin da ke aikawa da mutane hayin teku su kafa nahiyoyi? 8 Wane ne wannan wanda ya shirya ya aukar wa Taya da wannan duka, wannan muhimmiyar alkarya, wadda fatakenta hakimai ne, waɗanda ake ɗaukaka su fiye da sauran mutane a duniya? 9 Ubangiji Mai Runduna ne ya shirya wannan! Ya shirya haka ne don ya kawo ƙarshen girmankanta saboda abin da suka aikata, don ya ƙasƙantar da manyan mutanenta. 10 Ku je ku nomi ƙasarku jama'ar nahiyoyin Tarshish! Ba wanda zai ƙara kiyaye ku. 11 Ubangiji ya miƙa dantsensa a kan tekun, ya hamɓarar da mulkoki. Ya umarta a lalatar da manyan biranen ciniki na Taya. 12 Birnin Sidon, farin cikinki ya ƙare. Ana zaluntar jama'arki, ko da za su tsere zuwa Kubrus duk da haka ba za su zauna lafiya ba. 13 (Mutanen Babila ne, ba na Assuriya ba, waɗanda suka bar namomin jeji su murƙushe Taya. Mutanen Babila ne suka gina hasumiya, suka ragargaza kagarar Taya suka bar birnin kango.) 14 Ku yi hargowar baƙin ciki ku matuƙan jiragen teku! An hallaka birnin da kuke dogara gare shi. 15 Lokaci yana zuwa da za a manta da Taya har shekara saba'in, gwargwadon kwanakin sarki. Bayan waɗannan shekaru kuma, Taya za ta yi waƙa irin ta karuwa, cewa 16 “Ɗauki garayarki, kewaya cikin gari, Ayya, an manta da karuwa! Yi kiɗa, sāke raira waƙoƙinki, Don ki komo da masoyanki.” 17 Bayan shekara saba'in ɗin, Ubangiji zai bar Taya ta koma a kan cinikinta na dā, za ta ba da kanta ijara ga dukan mulkokin duniya. 18 Kuɗin da ta samu ta kasuwanci za a keɓe wa Ubangiji. Ba za ta tara wa kanta ba, amma waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada su za su yi amfani da kuɗinta don su saya wa kansu abinci da sutura da suke bukata.

Ishaya 24

Ubangiji zai Hukunta Duniya

1 Ubangiji zai hallaka duniya ya bar ta kufai. Zai kaɓantar da duniya ya watsar da jama'ar da take cikinta. 2 Bala'i ɗaya ne zai sami kowa da kowa, firistoci da sauran jama'a, bayi da iyayengijinsu, masu saye da masu sayarwa, masu ba da rance da masu karɓa, attajirai da matalauta. 3 Duniya za ta ragargaje ta zama kufai. Ubangiji ne ya faɗa, haka kuwa za a yi. 4 Duniya za ta bushe ta ƙeƙashe, duniya duka za ta raunana, duniya da sararin sama za su ruɓe. 5 Jama'ar sun ƙazantar da duniya da suka keta dokokin Allah, suka ta da alkawarin da ya yi don ya dawwama. 6 Saboda haka Allah ya aiko da la'ana ta hallaka duniya. Jama'arta suna karɓar sakayyar abin da suka aikata. 'Yan kalilan ne suka ragu da rai. 7 Kurangun inabi sun bushe, ruwan inabi ya yi kaɗan. Dukan wanda yake farin ciki a dā, yanzu sai baƙin ciki yake yi, 8 kaɗe-kaɗen garayunsu da gangunansu na farin ciki sun ƙare. 9 Babu sauran waƙar farin ciki ga mashayan ruwan inabi, ba kuma wanda zai ƙara jin daɗin ɗanɗanar ruwan inabi. 10 A cikin birni kome ya birkice, an kulle kowane gida don a hana mutane shiga. 11 Mutane za su tsaya a tituna, suna ihu, suna neman ruwan inabi. Farin ciki ya ƙare har abada, ya ƙare a ƙasar. 12 Birnin ya zama kango, an farfashe ƙofofinsa. 13 Wannan shi ne abin da zai sami kowace al'umma ko'ina a duniya. Zai zama kamar ƙarshen kaka sa'ad da aka karkaɗe zaitun daga kowane itace, aka kuma gama tsinke 'ya'yan inabi daga kurangar inabi. 14 Waɗanda suka tsira za su raira waƙa don farin ciki. Waɗanda suke wajen yamma za su ba da labarin girman Allah, 15 waɗanda suke wajen gabas kuma za su yabe shi. Jama'ar da take zaune a gefen teku za su yabi Ubangiji, Allah na Isra'ila. 16 Daga manisantan wurare na duniya za mu ji waƙoƙin yabon Isra'ila, al'umma adala. Amma ba ni da sauran sa zuciya! Lalacewa nake yi! Maciya amana suna ta cin amana, cin amanarsu sai gaba gaba yake yi. 17 Ya jama'ar duniya, razana, da wushefe, da tarkuna suna jiranku. 18 Duk wanda ya yi ƙoƙarin tserewa daga razana zai fāɗa cikin wushefe, wanda kuma ya tsere daga wushefe za a kama shi a tarko. Za a kwararo ruwa daga sama kamar da bakin ƙwarya, harsashin ginin duniya zai jijjigu. 19 Duniya za ta tsage, ta farfashe ta wage. 20 Duniya kanta za ta yi tangaɗi kamar mashayi, ta yi ta yin lau kamar rumfa a lokacin hadiri. Nauyin zunuban duniya ya rinjaye ta har ƙasa, za ta fāɗi, ba za ta ƙara tashi ba. 21 A wannan rana Ubangiji zai hukunta wa ikoki na sama, da sarakunan da suke a duniya. 22 Allah zai tattara sarakuna wuri ɗaya kamar ɗaurarru a rami, zai kulle su a kurkuku kafin lokacin da zai hukunta su ya yi. 23 Wata zai duhunta, rana ba za ta ƙara haskakawa ba, domin Ubangiji Mai Runduna yake sarauta. Zai yi mulki a Urushalima a kan Dutsen Sihiyona, shugabannin jama'a za su dubi ɗaukakarsa.

Ishaya 25

Waƙar Yabo saboda Alherin Ubangiji

1 Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka. Ka aikata al'amura masu banmamaki, Ka tafiyar da su da aminci, Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni. 2 Ka mai da birane kufai Ka lalatar da kagaransu, Wuraren da maƙiya suka gina kuwa, An shafe su har abada. 3 Jama'ar al'ummai masu iko za su yabe ka, Za a ji tsoronka a biranen mugayen al'ummai. 4 Matalauta da 'yan ƙaƙa naka yi sun sheƙa zuwa wurinka, Sun sami zaman lafiya a lokatan wahala. Ka ba su mafaka daga hadura, Ka inuwantar da su daga matsanancin zafi. Mugaye sukan tasar musu kamar hadirin ƙanƙara, 5 Kamar fari a ƙeƙasasshiyar ƙasa. Amma kai, ya Ubangiji, ka rufe bakin abokan gābanmu, Ka sa hayaniyar mugaye ta yi tsit, Kamar yadda girgije yake sanyaya zafin rana.

Allah ya Shirya Biki

6 A kan Dutsen Sihiyona Ubangiji Mai Runduna zai shirya wa dukan sauran al'umman duniya biki da abinci irin na adaras da ruwan inabi mafi kyau. 7 A can ne zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan sauran al'umma. 8 Ubangiji zai hallaka mutuwa har abada! Zai share hawaye daga idanun kowane mutum, ya kawar da kunyar da jama'arsa suke sha a duniya duka. Ubangiji ne da kansa ya faɗa! 9 Sa'ad da wannan ya faru, kowa zai ce, “Shi Allahnmu ne! Mun dogara gare shi, ya kuwa cece mu. Shi ne Ubangiji. Mun dogara gare shi, yanzu kuwa muna da farin ciki domin ya cece mu!” 10 Ubangiji zai kiyaye Dutsen Sihiyona, amma za a tattake jama'ar Mowab a ƙasa, kamar yadda ake tattake tattaka cikin taki. 11 Za su miƙa hannuwansu kamar suna ƙoƙarin yin ninƙaya, amma girmankansu zai jā hannuwansu ƙasa a duk sa'ad da suka ɗaga. 12 Allah zai lalatar da kagaran Mowab da dogayen garukansu, ya rushe su ƙasa su zama ƙura.

Ishaya 26

Waƙar Dogara ga Kiyayewar Ubangiji

1 Rana tana zuwa da jama'a za su raira wannan waƙa a ƙasar Yahuza. Birni ƙaƙƙarfa ne, Allah kansa yake tsare garukansa! 2 A buɗe ƙofofin birnin, A bar amintacciyar al'umma ta shiga, Al'ummar da jama'arta take aikata abin da yake daidai. 3 Kai kake ba da cikakkiyar salama, ya Ubangiji, Ga waɗanda suke riƙe da manufarsu da ƙarfi, Waɗanda suke dogara gare ka. 4 Ku dogara ga Ubangiji har abada. Zai kiyaye mu kullayaumin. 5 Ya ƙasƙantar da masu girmankai, Ya hallaka ƙaƙƙarfan birnin da suke zaune ciki, Ya rusa garunsa ƙasa. 6 Waɗanda aka zalunta, a kansa suke tafiya yanzu, Suna tattaka shi da ƙafafunsu. 7 Ka sa hanyar mutanen kirki ta yi sumul, Hanyar da suke bi ta yi bai ɗaya, 8 Muna bin nufinka, muna sa zuciya gare ka. Kai kaɗai ne bukatarmu. 9 Da dare ina zuba ido gare ka da zuciya ɗaya. Sa'ad da kake yi wa duniya da jama'arta shari'a Dukansu za su san yadda adalci yake. 10 Ko da yake kana yi wa mugaye alheri, Duk da haka ba su taɓa koyon abin da yake na kirki ba. Har a nan ma, a ƙasar adalai, Suna ta aikata kuskure, Sun ƙi ganin girmanka. 11 Maƙiyanka ba su san za ka hukunta su ba. Ya Ubangiji, ka kunyatar da su, ka sa su sha wahala, Wato su sha wahalar hukuncin da ka shirya. Ka nuna musu yawan ƙaunar da kake yi wa jama'arka. 12 Kai za ka wadata mu, ya Ubangiji, Duk abin da muka iya yi daga gare ka ne. 13 Ya Ubangiji Allahnmu, waɗansu sun mallake mu, Amma kai kaɗai ne Ubangijinmu. 14 Yanzu kuwa sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba, Kurwarsu ba za ta tashi ba, Domin ka hukunta su, ka hallaka su. Ba wanda zai ƙara tunawa da su. 15 Ya Ubangiji, ka sa al'ummarmu ta yi ƙarfi, Ka faɗaɗa karkararta a kowane gefe, Wannan kuwa ya sa ana girmama ka. 16 Ka hukunta jama'arka, ya Ubangiji, A cikin azaba sun yi addu'a gare ka. 17 Kai ne, ya Ubangiji, ka sa muka yi kuka, Kamar macen da take naƙuda tana kuka da azaba. 18 Muna shan azaba da wahala, Amma ba abin da muka haifa. Ba mu ciwo wa ƙasarmu nasara ba, Ba abin da muka kammala! 19 Mutanenmu da suka mutu za su sāke rayuwa! Jikunansu za su sāke rayuwa! Dukan waɗanda suke kwance cikin kaburburansu Za su farka, su yi waƙa don farin ciki! Kamar laimar raɓa wanda yake wartsakar da duniya, Haka Ubangiji zai rayar da waɗanda suka daɗe da mutuwa. 20 Jama'ata, ku shiga gidajenku, ku kukkulle ƙofofi, ku ɓoye kanku ɗan lokaci, kafin Allah ya huce daga fushinsa. 21 Ubangiji yana zuwa ya hukunta jama'arsa a duniya saboda zunubansu. Kashe-kashen da aka yi a duniya a ɓoye, za a bayyana su, ƙasa ba za ta ƙara ɓoye waɗanda aka kashe ba.

Ishaya 27

Ceton Isra'ila da Tarawarta

1 A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da takobinsa mai ƙarfi, mai muguwar ɓarna, don ya hukunta dodon ruwan nan mai kanannaɗewa, mai murɗewa, ya kashe dodon da yake cikin teku. 2 A wannan rana Ubangiji zai yi magana a kan kyakkyawar gonar inabinsa, 3 ya ce, “Ina tsaronta ina yi mata banruwa kowane lokaci, ina tsaronta dare da rana, don kada a yi mata ɓarna. 4 Ba zan ƙara yin fushi da gonar inabin ba. Da ma a ce akwai ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya in yi faɗa da su, da na ƙone su ƙurmus. 5 Amma idan maƙiyan jama'ata suna so in cece su, sai su yi sulhu da ni, i, bari su yi sulhu da ni.” 6 A wannan rana jama'ar Isra'ila, zuriyar Yakubu, za su yi saiwa kamar itace, za su yi toho, su yi fure. 'Ya'yan da suka yi za su cika duniya. 7 Ubangiji bai hukunta Isra'ila da tsanani kamar yadda ya yi wa maƙiyanta ba, ba za su yi hasarar mutane da yawa ba. 8 Ubangiji ya hukunta jama'arsa da ya sa aka kai su baƙuwar ƙasa. Ya sa iskar gabas mai ƙarfin gaske ta tafi da su. 9 Ba za a gafarta zunuban Isra'ila ba, sai an niƙe duwatsun bagadan arna su zama kamar alli, har kuma ba sauran keɓaɓɓun ginshiƙai ko bagadan ƙona turare. 10 Birni mai garu ya zama kufai. An bar shi kamar jejin da ba kowa ciki. Ya zama wurin kiwon shanu, inda za su huta su yi kiwo. 11 Rassan itatuwa sun bushe sun kakkarye, mata kuwa sun tattara, don su riƙa hura wuta da su. Da yake jama'a ba su gane kome ba, Allah Mahaliccinsu ba zai ji tausayinsu ba, ba zai nuna musu jinƙai ba. 12 A wannan rana Ubangiji kansa zai hukunta jama'arsa, Isra'ila, daga wannan iyakar ƙasa zuwa waccan, tun daga Yufiretis har zuwa iyakar Masar. Zai raba tsakanin nagari da mugu. 13 A wannan rana za a busa ƙaho don a kirawo Isra'ilawan da suke zaman baƙunci a Assuriya da Masar. Za su zo su yi wa Ubangiji sujada a Urushalima a tsattsarkan dutsensa.

Ishaya 28

Faɗakarwa game da Ifraimu

1 Mulkin Isra'ila ya ƙare, darajarsa tana dushewa kamar rawanin furanni a kan shugabanninsa da suka bugu da giya. Sun bulbula turare a kawunansu na girmankai, amma ga su nan a kwance bugaggu. 2 Ubangiji yana da wani ƙaƙƙarfa mai iko a shirye don ya fāɗa musu da yaƙi. Zai zo kamar hadirin ƙanƙara, kamar kwararowar ruwan sama, kamar kuma rigyawa mai kirmewa wadda ta shafe ƙasa. 3 Za a tattake girmankan bugaggun shugabannin nan. 4 Darajan nan mai dushewa ta shugabanni masu girmankai za ta shuɗe kamar 'ya'yan ɓaure, nunan fari, da aka tsinke aka cinye nan da nan da nunarsu. 5 Rana tana zuwa da Ubangiji Mai Runduna zai zama kamar rawanin furanni mai daraja ga jama'arsa da suka ragu. 6 Zai ba da ruhun adalci ga waɗanda suke alƙalai, ƙarfin hali kuma ga waɗanda suka kori abokan gāban da suka fāɗa musu da yaƙi a ƙofofin birni.

Faɗaka da Alkawari ga Urushalima

7 Har da annabawa da firistoci, tangaɗi suke yi, mashaya ne. Sun sha ruwan inabi da barasa da yawa, suna ta tuntuɓe barkatai. Annabawan sun bugu ƙwarai, har ba su iya fahimtar wahayin da Allah ya aiko musu ba, firistoci su ma sun bugu, har sun kāsa yanke shari'un da aka kawo musu. 8 Duk sun cika teburorin da suke zaune da amai, ba inda ba su amaye ba. 9 Suna gunaguni a kaina suna cewa, “Su wa wannan mutum yake tsammani yana koya musu? Wa yake bukatar jawabinsa? Sai ga 'yan yaran da aka yaye kaɗai yake da amfani! 10 Yana ƙoƙari ya koya mana baƙaƙe baƙaƙe, da shaɗara shaɗara, da babi babi.” 11 Idan ba za ku saurare ni ba, to, Allah zai yi amfani da baƙi masu magana da harshen da ba ku sani ba, su koya muku darasi. 12 Ya miƙa muku hutawa da wartsakewa, amma kun ƙi saurarawa gare shi. 13 Saboda haka ne Ubangiji zai koya muku baƙaƙe baƙaƙe, da shaɗara shaɗara, da babi babi. Sa'an nan kowane ɗaga ƙafar da kuka yi, za ku yi tuntuɓe, za a yi muku rauni, a kama ku a tarko, a kai ku kurkuku. 14 Yanzu fa ku mutane masu girmankai, da kuke mulki a nan a Urushalima a kan wannan jama'a, ku saurara ga abin da Ubangiji yake faɗa. 15 Kuna fāriya a kan alkawarin da kuka yi da mutuwa, kun ƙulla yarjejeniya da lahira. Kun tabbata masifa za ta ƙetare ku sa'ad da ta zo, domin kun dogara ga ƙarairayi da ruɗi don su kiyaye ku. 16 Yanzu fa ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan kafa ƙaƙƙarfan harsashin gini a Sihiyona. A kansa zan sa ƙaƙƙarfan dutsen kusurwa. A kansa an rubuta wannan magana, ‘Amincin da yake kafaffe mai haƙuri ne kuma.’ 17 Adalci ne zai zama igiyar gwajin tushen ginin, aminci kuma zai zama shacin dirin ginin.” Hadirin ƙanƙara zai share dukan ƙarairayin da kuke dogara gare su, rigyawa za ta hallakar da zaman lafiyarku. 18 Alkawarin da kuka ƙulla da mutuwa ya tashi, yarjejeniyar da kuka yi da lahira, an soke ta. Sa'ad da masifa ta auko za a hallaka ku. 19 Za ta yi ta auko muku a kai a kai kowace safiya. Tilas ku sha ta dare da rana. Kowane sabon jawabin da zai zo muku daga wurin Allah, zai kawo muku sabuwar razana! 20 Za ku zama kamar mutumin da ya zama abin karin magana, wanda ya yi ƙoƙari ya kwanta a gajeren gado, ya kuma rufa da ɗan siririn bargo. 21 Ubangiji zai yi yaƙi kamar yadda ya yi a Dutsen Ferazim da a Kwarin Gibeyon domin ya aikata abin da ya yi nufin yi, ko da yake ayyukansa suna da ban al'ajabi. Zai gama aikinsa, wannan aiki kuwa mai ban al'ajabi ne. 22 Kada ku yi dariya saboda faɗakarwar da nake yi muku! Idan kuwa kun yi, zai ƙara yi muku wuya ku tsira. Na ji niyyar da Ubangiji Mai Runduna ya yi, ta ya hallaka dukan ƙasar.

Hikimar Allah

23 Ku kasa kunne ga abin da nake cewa, ku mai da hankali ga abin da nake faɗa muku. 24 Manomi ba zai dinga huɗar gonakinsa har abada ba, ya yi ta shirya su domin shuka. 25 Da zarar ya shirya ƙasar yakan shusshuka ganyayen ci, kamar su kanumfari da ɗaɗɗoya, yakan kuma dasa kunyoyin alkama da na sha'ir, a gyaffan gonakin kuwa yakan shuka hatsi. 26 Ya san yadda zai yi aikinsa, gama Allah ya koya masa. 27 Ba ya bugun kanumfari da ɗaɗɗoya da ƙaton kulki, a maimakon haka yakan yi da 'yan sanduna sirara. 28 Ba zai yi ta bugun alkama, har ya ɓata tsabar ba, ya san yadda zai sussuke alkamarsa, ba tare da ya ɓata tsabarta ba. 29 Dukan wannan hikima daga wurin Ubangiji Mai Runduna ne. Shirye-shiryen da Allah ya yi na hikima ne kullum kuwa sukan yi nasara!

Ishaya 29

Urushalima da Maƙiyanta

1 Bagaden Allah, Urushalima kanta, ƙaddara ta auko mata! Birnin da Dawuda ya kafa zango, ƙaddara ta auko mata! Bari shekara ɗaya ko biyu su zo su wuce suna shagulgulansu, suna bukukuwansu, 2 sa'an nan Allah zai kawo wa birnin wanda ake ce da shi, “Bagaden Allah,” masifa. Za a yi kuka a yi kururuwa, birnin kansa za a maishe shi bagade inda za a ƙona hadayun ƙonawa! 3 Allah zai tasar wa birnin, ya kewaye shi da yaƙi. 4 Urushalima za ta zama kamar fatalwar da take ƙoƙarin yin magana daga ƙarƙashin ƙasa, guni yana fitowa daga turɓaya. 5 Ya Urushalima, dukan baƙin da suka auka miki da yaƙi za a hure su kamar yadda iska take hure ƙura, sojojinsu kuma masu firgitarwa za a hure su kamar yadda iska take hure tattaka. Farat ɗaya ba zato ba tsammani, 6 Ubangiji Mai Runduna zai cece ki da tsawar hadiri da girgizar ƙasa. Zai aiko da hadirin iska da gagarumar wuta. 7 Sa'an nan dukan sojojin sauran al'umma da suka fāɗa wa birni inda bagaden Allah yake da yaƙi, da dukan makamansu, da kayayyakin yaƙinsu, kome da kome za su shuɗe kamar mafarki, kamar tunanin dare. 8 Dukan al'ummai da suka tattaru don su yaƙi Urushalima, za su zama kamar mutum mayunwaci da ya yi mafarki yana cin abinci, ya farka yana a mayunwacinsa, kamar wanda yake mutuwa da ƙishi ya yi mafarki yana kwankwaɗar ruwa, ya farka da busasshen maƙogwaro.

Makantar Isra'ilawa da Riyarsu

9 Ku ci gaba da aikin wautarku! Ku ci gaba da makancewarku, ku yi ta zama a makance. Ku bugu ba tare da kun sha ruwan inabi ba! Ku yi ta tangaɗi, ba don kun sha ko ɗigon ruwan inabi ba! 10 Ubangiji ya sa ku ku yi gyangyaɗi ku yi barci mai nauyi. Annabawa ne ya kamata su zama idon jama'a, amma Allah ya rufe idanunsu. 11 Za a ɓoye muku ma'anar kowane annabci na cikin wahayi. Zai zama kamar naɗaɗɗen littafin da aka liƙe. Ko kun kai wa wanda ya iya karatu, don ya karanta muku, zai ce ba zai iya ba saboda a liƙe yake. 12 In kuwa kun ba wanda bai iya karatu ba, kuka roƙe shi ya karanta muku, zai ce bai iya karatu ba. 13 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun ce suna mini sujada, amma kalmominsu ba su da ma'ana, zukatansu kuma suna wani wuri dabam. Addininsu ba wani abu ba ne, sai dai dokoki ne da ka'idodin mutane da suka haddace. 14 Don haka zan firgita su ba zato ba tsammani, da d�ka a kai a kai. Waɗanda suke da hikima za su zama wawaye, dukan wayon nan nasu kuwa ba zai amfana musu kome ba.”

Maƙaryatan Mashawarta

15 Waɗanda suke ƙoƙarin ɓoye wa Ubangiji shirye-shiryensu sun shiga uku! Suna gudanar da dabarunsu a ɓoye, suna tsammani ba wanda zai gan su ko ya san abin da suke yi. 16 Sun birkitar da kome! Wane ne ya fi muhimmanci, mai ginin tukwane ko yumɓun? Abin da mutum ya yi da hannunsa ya iya ce wa mutumin, “Ba kai ka yi ni ba?” Ko kuma zai iya ce masa, “Ai, ba ka san abin da kake yi ba?”

Fansar Isra'ila

17 Kamar yadda karin maganar ta ce, kafin a jima kurmi zai zama gona, gona kuma za ta zama kurmi. 18 A wannan rana, kurame za su ji sa'ad da aka karanta littafi da murya, makafi kuwa waɗanda suke zaune cikin duhu za su buɗe idanunsu su gani. 19 Matalauta da masu tawali'u za su sāke samun farin ciki wanda Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya bayar. 20 Zai zama ƙarshen waɗanda suke zaluntar waɗansu, suna raina Allah. Za a hallakar da kowane mai zunubi. 21 Allah zai hallakar da waɗanda suke zambatar waɗansu, da waɗanda sukan hana a hukunta wa masu mugun laifi, da waɗanda sukan yanka ƙarya don a hana wa amintattu samun shari'ar adalci. 22 Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda ya fanshi Ibrahim daga wahala, ya ce, “Jama'ata, ba za a ƙara kunyatar da ku ba, fuskokinku ba za su ƙara yanƙwanewa don kunya ba. 23 Za ku ga 'ya'yan da zan ba ku, sa'an nan ne za ku tabbatar, cewa ni ne Allah Mai Tsarki na Isra'ila. Za ku girmama ni, ku yi tsorona. 24 Wawaye za su koya su gane, waɗanda a kullum sai gunaguni suke yi, za su yi murna su koya.”

Ishaya 30

Rashin Amfanin Dogara ga Masar

1 Ubangiji ya yi magana, ya ce, “Waɗanda suke mulkin Yahuza sun shiga uku, domin sun tayar mini. Suna aiki da shirye-shiryen da ba ni ne na yi ba, suka sa hannu a kan yarjejeniya gāba da nufina. Suna ta aikata zunubi a kan zunubi. 2 Suna tafiya Masar neman taimako, ba su shawarce ni ba. Suna so Masar ta kāre su, saboda haka suka sa dogararsu ga Sarkin Masar. 3 Amma sarkin zai rasa ikon taimakonsu, kāriyar da Masar za ta yi musu ƙarshenta masifa. 4 Ko da yake jakadunsu sun riga sun isa Zowan da Hanes, biranen Masar, 5 duk da haka jama'ar Yahuza za su yi da na sani, da suka dogara ga al'ummar da ba abar dogara ba ce, al'ummar da ba ta daɗa musu kome a lokacin da suke sa zuciya ga taimako ba.” 6 Wannan shi ne jawabin da Allah ya yi a kan dabbobin da suke kudancin hamada, “Jakadu sun yi tafiya a ƙasa mai hatsari, inda zakoki suke, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke. Suna labta wa jakunansu da raƙumansu kayayyaki masu tsada da za su kai gaisuwa ga al'ummar da ba za ta taimake su da kome ba. 7 Taimakon da Masar za ta yi marar amfani ne. Don haka na yi mata laƙabi, ‘Macijin da ba ya yin kome.’ ”

Jama'a Marar Biyayya

8 Allah ya faɗa mini in rubuta a littafi yadda mutane suke, saboda ya zama tabbatacciyar shaida a kansu. 9 A kullum suna tayar wa Allah, a kullum ƙarya suke yi, a kullum suna ƙin kasa kunne ga koyarwar Allah. 10 Sukan faɗa wa annabawa su yi shiru. Sukan ce, “Kada ku yi mana magana a kan abin da yake daidai. Ku faɗa mana abin da muke so mu ji ne kawai. Bari mu ci gaba da ruɗewarmu. 11 Tashi daga nan, kada ku toshe mana hanya. Ba ma so mu ji kome game da Allah Mai Tsarki na Isra'ila.” 12 Amma wannan shi ne abin da Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya ce, “Kun yi banza da abin da nake faɗa muku, kuna dogara ga aikin kamakarya da yin zamba. 13 Kun yi laifi. Kuna kamar bango wanda ya tsage daga bisa har ƙasa. Za ku fāɗi ba zato ba tsammani. 14 Za a ragargaza ku kamar tukunyar yumɓu, da mummunar ragargazawa har da ba za a sami 'yar katangar da za a ɗauki garwashin wuta ba, ko a ɗebo ruwa daga randa.” 15 Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya ce wa jama'a, “Ku komo gare ni a natse, ku dogara gare ni. Sa'an nan za ku zama ƙarfafa ku zauna lafiya.” Amma ba ku yarda ba! 16 A maimakon haka sai kuka shirya ku tsere wa maƙiyanku a kan dawakai masu gudu. Daidai ne, tilas ku tsere! Tsammani kuke saurin gudun dawakanku ya isa, amma waɗanda za su fafare ku sun fi ku gudu! 17 Dubunku za su gudu da ganin abokin gābanku ɗaya, abokan gāba biyar sun isa su sa dukanku ku gudu. Ba abin da zai ragu daga cikin rundunar sojojinku, sai sandan tutarku kaɗai da yake kan tudu. 18 Duk da haka dai, Ubangiji yana jira ya yi muku alheri. A shirye yake ya yi muku jinƙai, domin a kullum yana aikata abin da yake daidai. Ta wurin dogara ga Ubangiji ake samun farin ciki.

Ubangiji zai sa wa Jama'arsa Albarka

19 Ku jama'ar da kuke zaune a Urushalima ba za ku ƙara yin kuka ba. Ubangiji mai juyayi ne, sa'ad da kuka yi kuka gare shi neman taimako, zai amsa muku. 20 Ubangiji zai sa ku ku sha wahala, amma shi kansa zai kasance tare da ku, ya koya muku, ba za ku ƙara wahalar nemansa ba. 21 Idan kuka kauce daga hanya zuwa dama ko hagu, za ku ji muryarsa a bayanku yana cewa, “Ga hanyan nan, ku bi ta.” 22 Za ku kwashe gumakanku waɗanda aka dalaye da azurfa, da waɗanda aka rufe da zinariya, ku jefar da su kamar abin ƙyama, kuna ihu, kuna cewa, “Ku ɓace mana da gani!” 23 Duk lokacin da kuka shuka amfanin gonakinku, Ubangiji zai aiko da ruwan sama ya sa su girma, zai ba ku kaka mai albarka, shanunku kuma za su sami makiyaya wadatacciya. 24 Takarkaranku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau duka. 25 A wannan rana sa'ad da aka kame kagaran abokan gābanku, aka kashe jama'arsu, rafuffukan ruwa za su malalo daga kowane tsauni da kowane tudu. 26 Wata zai yi haske kamar rana, hasken rana zai riɓanya har sau bakwai kamar a tattara hasken rana na kwana bakwai a maishe shi ɗaya! Dukan wannan zai faru sa'ad da Ubangiji zai ɗaure raunukan da ya yi musu, ya warkar da su.

Allah zai Hukunta Assuriya

27 Ana iya ganin ikon Allah da ɗaukakarsa daga nesa! Wuta da hayaƙi suna nuna fushinsa. Ya yi magana, maganarsa tana ƙuna kamar wuta. 28 Ya aika da iska a gabansa kamar rigyawa wadda take kwashe kome, ta tafi da shi. Yakan gwada al'ummai ya kai su hallaka, yakan sa dukan shirye-shiryensu na mugunta su ƙare. 29 Amma ku, jama'ar Allah, za ku yi farin ciki, ku raira waƙa kamar yadda kukan yi a daren tsattsarkan idi. Za ku yi murna kamar waɗanda suke tafiya suna bushe-bushe a hanyarsu ta zuwa Haikalin Ubangiji Mai Tsarki, Mai Ceton Isra'ila. 30 Ubangiji zai bar kowane mutum ya ji maɗaukakiyar muryarsa, ya kuma ji ƙarfin fushinsa. Za a ga harsunan wuta, gizagizai za su ɓarke, za a yi ƙanƙara, da ruwan sama kamar da bakin ƙwarya. 31 Assuriyawa za su firgita sa'ad da suka ji muryar Allah, suka kuma ji irin zafin hukuncinsa. 32 Sa'ad da Ubangiji ya miƙa sandan hukuncinsa ya yi ta bugun Assuriyawa, jama'arsa kuwa za su yi ta kaɗa ganguna da garayu, su yi murna! 33 An riga an shirya wurin ƙonawa don Sarkin Assuriya. An tsiba itace cike da wurin. Kamar kibritu, numfashin Ubangiji zai cinna masa wuta.

Ishaya 31

Masarawa Mutane ne, ba Allah Ba

1 Waɗanda suka tafi Masar neman taimako, sun shiga uku! Suna dogara ga ƙarfin tulin dawakan Masar na yaƙi, da karusansu, da sojojinsu. Amma ba su dogara ga Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila ba, ba su ko roƙe shi taimako ba. 2 Ya san abin da yake yi! Zai aika da bala'i. Zai ci gaba da niyyarsa ta hukunta wa mugaye duk da masu kiyaye su. 3 Masarawa su ba Allah ba ne, mutane ne kurum! Dawakansu ba su wuce ikon ɗan adam ba! Sa'ad da Ubangiji zai matsa, ƙaƙƙarfar al'umma za ta marmashe, al'ummar da aka yi wa taimako kuma za ta fāɗi. Dukansu za su hallaka. 4 Ubangiji ya ce mini, “Kamar dai makiyaya ba za su iya tsoratar da zakin da ya kashe dabba ba, kome irin tsawa da ihun da suka yi, haka ni ma, ba abin da zai iya hana ni, ni Ubangiji Mai Runduna, in kiyaye Dutsen Sihiyona. 5 Kamar yadda tsuntsu yake shawagi a kan sheƙarsa don ya kiyaye 'ya'yansa, haka ni, Ubangiji Mai Runduna, zan kiyaye Urushalima in kāre ta kuma.” 6 Allah ya ce, “Jama'ar Isra'ila, kun yi mini zunubi, kuna kuwa yin gāba da ni. Amma yanzu ku komo wurina! 7 Lokaci zai yi da dukanku za ku watsar da gumakan da kuka yi na azurfa da na zinariya. 8 Assuriya za ta hallaka cikin yaƙi, amma ba ta wurin ikon mutum ba. Assuriyawa za su gudu daga bakin dāga, za a mai da majiya ƙarfinsu bayi. 9 Sarkinsu zai tsere saboda razana, shugabannin sojojinsu kuwa za su firgita, har su watsar da tutocinsu na yaƙi.” Ubangiji ne ya faɗa, Ubangiji da ake yi wa sujada a Urushalima, wanda kuma wutarsa tana ci a can domin hadayu.

Ishaya 32

Sarki Mai Adalci

1 Wata rana za a yi wani sarki mai adalci, da kuma shugabannin ƙasa waɗanda za su yi mulki da gaskiya. 2 Ko wannensu zai zama kamar wurin fakewa daga iska da kuma wurin ɓuya saboda hadiri, za su zama kamar rafuffukan da suke gudu cikin hamada, kamar inuwar babban dutse a ƙeƙasasshiyar ƙasa. 3 Idanunsu da kunnuwansu za su kasance a buɗe domin sauraron jama'a. 4 Za su zama masu haƙuri sosai, za su yi kome da haziƙanci, za su kuma faɗi abin da suke nufi. 5 Ba wanda zai girmama wawayen mutane, ko kuma ya ce da mazambata suna da aminci. 6 Dakiki yakan yi maganar wauta ya kuma yi tunanin mugayen ayyukan da zai aikata. Abin da dakiki yakan aikata da abin da yakan faɗa, duk ɓatanci ne ga Allah, bai kuwa taɓa ciyar da masu jin yunwa ba, ko ya ba masu jin ƙishi ruwa su sha. 7 Mugu ne shi, yana kuwa yin mugayen abubuwa, yakan yi shiri don ya lalatar da matalauta da ƙarya, ya kuma hana su samun hakkinsu. 8 Amma mutum mai aminci yakan yi aikin aminci ya kuwa tsaya da ƙarfi a kan abin da yake daidai.

An Yi wa Matan Urushalima Faɗaka

9 Ku matan da kuke zaman jin daɗi, ba ku da damuwar kome, ku kasa kunne ga abin da nake faɗa. 10 Zai yiwu ku wadatu yanzu, amma baɗi war haka za ku fid da zuciya, gama ba inabin da za ku tattara. 11 Kuna ta zaman jin daɗi, ba abin da yake damunku, amma yanzu ku yi rawar jiki don tsoro! Ku tuɓe tufafinku ku ɗaura tsummoki a kwankwasonku. 12 Ku bugi ƙirjinku don baƙin ciki, gama an lalatar da gonaki masu dausayi da kuma gonakin inabi, 13 ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya ne suke girma a ƙasar jama'ata. Ku yi kuka domin dukan gidajen da mutane suke murna a cikinsu dā, domin kuma birnin da yake cike da jin daɗi a dā. 14 Har ma za a bar fādar, babban birnin sarauta kuma za a gudu a bar shi gaba ɗaya. Gidaje kuma da kagaran da suke tsaronsu za su zama rusassu har abada. A can jakunan jeji za su yi ta zarya, tumaki kuma za su sami wurin kiwo. 15 Amma Allah zai ƙara aiko mana da Ruhunsa. Ƙasar da ta zama marar amfani za ta komo mai dausayi, gonaki kuma za su ba da amfani mai yawa. 16 A ko'ina a ƙasar za a aikata adalci da gaskiya. 17 Gama kowa zai yi abin da yake daidai, za a sami salama da zaman lafiya har abada. 18 Gidajen jama'ar Allah za su zama da salama da zaman lafiya, ba abin da zai dame su. 19 (Amma ƙanƙara za ta faɗo a jeji, za a kuma rurrushe birni.) 20 Kowa zai yi murna da ruwan sama mai yawa domin amfanin gona, da kuma lafiyayyiyar makiyaya domin jakuna da shanu.

Ishaya 33

Ubangiji zai Kawo Ceto

1 Magabtanmu sun shiga uku! Sun yi fashi sun ci amana, ko da yake ba wanda ya yi musu fashi ko cin amana. Amma lokacinsu na fashi da na cin amana zai ƙare, su ne kuma za a yi wa fashi da cin amana. 2 Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai. Muna sa zuciyarmu gare ka. Ka dinga kiyaye mu yau da gobe, ka kuma cece mu a lokatan wahala. 3 Lokacin da kake yaƙi dominmu, al'ummai sukan gudu daga bakin dāga. 4 Akan tsirga a bisa abubuwan da suke da su, a kwashe su ganima. 5 Ubangiji da girma yake! Yana mulki a kan kome. Zai cika Urushalima da adalci da mutunci, 6 zai kuma sa aminci cikin al'ummar. A koyaushe yakan kiyaye jama'arsa ya kuma ba su hikima da sani. Dukiyarsu mafi girma ita ce tsoron Ubangiji. 7 Mutane masu jaruntaka suna kira don a taimake su! Jakadu waɗanda suke ƙoƙarin kawo salama suna kuka mai zafi. 8 Manyan karauku suna da hatsari har ba mai iya binsu. Aka keta yarjejeniya, aka ta da sharuɗa. Ba a kuma ganin girman kowa. 9 Ƙasar na zaman banza, an gudu an bar ta. Jejin Lebanon ya bushe, kwarin Sharon mai dausayi ya zama kamar hamada, a Bashan kuma da a kan Dutsen Karmel sai ganyaye suke karkaɗewa daga itatuwa. 10 Ubangiji ya ce wa al'ummai, “Yanzu zan tashi! Zan nuna irin ikon da nake da shi. 11 Kuka yi shirye-shiryen banza, kowane abu da kuke yi kuma ba shi da amfani. Kuna hallakar da kanku! 12 Za ku marmashe kamar duwatsun da aka ƙona don a yi farar ƙasa, kamar ƙayayuwan da aka ƙone suka zama toka. 13 Bari kowa da yake kusa da na nesa ya ji abin da na yi, ya kuma san ikona.” 14 Jama'ar Sihiyona cike da zunubi suke, suna ta rawar jiki don tsoro. Suka ce, “Hukuncin Allah kamar wuta ce mai ci har abada. Akwai wani daga cikinmu da zai iya tsira daga irin wannan wuta?” 15 Kuna iya tsira idan kuna faɗar gaskiya kuna kuma yin abin da yake daidai. Kada ku gwada ikonku don ku cuci talakawa, kada kuwa ku karɓi rashawa. Kada ku haɗa kai da masu shiri su yi kisankai, ko su aikata waɗansu mugayen abubuwa. 16 Sa'an nan za ku yi nasara, ku kuma zauna lafiya kamar kuna cikin kagara mai ƙarfi. Za ku sami abincin da za ku ci da ruwan da za ku sha.

Gaba Mai Daraja

17 Wata rana za ku ga sarki mai ɗaukaka yana mulki a dukan ƙasar da take shimfiɗe zuwa kowace kusurwa. 18 Tsoronku na dā game da baƙi masu tara haraji, magewaya, zai ƙare. 19 Ba za ku ƙara ganin baƙin nan masu girmankai, masu magana da harshen da ba ku fahimta ba! 20 Ku duba Sihiyona, birni inda muke idodinmu. Ku duba Urushalima! Za ta zama wurin zama mai lafiya! Za ta zama kamar alfarwar da ba ta taɓa gusawa ba, wadda ba a taɓa tumɓuke turakunta ba, igiyoyinta kuma ba su taɓa tsinkewa ba. 21 Ubangiji zai nuna mana ɗaukakarsa. Za mu zauna a gefen koguna da rafuffuka masu faɗi, amma ba kuwa jirgin ruwan abokan gāba da zai bi ta cikinsu. kayayyakin waɗannan jiragen ruwa ba su da amfani, tafiyarsu ba za ta yi nisa ba! Za a kwashe dukan dukiyar sojojin abokan gāba. Za ta yi yawa har sauran jama'a za su sami rabonsu. Ubangiji kansa shi zai zama sarkinmu, zai mallake mu, ya kiyaye mu. 24 Ba wanda zai zauna a ƙasarmu har ya ƙara yin kukan yana ciwo, za a kuma gafarta dukan zunubai.

Ishaya 34

Ubangiji zai Hukunta Edom

1 Ku zo, ku jama'ar dukan al'ummai! Ku tattaru ku kasa kunne. Bari dukan duniya, da kowane mai zama cikinta, ya zo nan ya kasa kunne. 2 Ubangiji yana fushi da al'ummai duka, da kuma dukan sojojinsu. Ya zartar musu da hukuncin hallaka. 3 Ba za a binne gawawwakinsu ba, amma za a bar su can, su ruɓe, su yi ɗoyi, duwatsu kuma za su yi ja wur da jini. 4 Za a murtsuke rana, da wata, da taurari su zama ƙura. Sararin sama zai shuɗe kamar yadda ake naɗe littafi, taurari kuma su faɗo kamar yadda ganyaye suke karkaɗewa daga itacen inabi ko na ɓaure. 5 Ubangiji ya shirya takobinsa a can Sama, yanzu kuwa zai buga Edom, wato mutanen can da ya zartar musu da hukuncin hallaka. 6 Jininsu da kitsensu za su rufe takobinsa, kamar jini da kitsen raguna, da na awaki, da aka miƙa hadaya. Ubangiji zai yi wannan hadaya a birnin Bozara, zai sa wannan ya zama babban kisa a ƙasar Edom. 7 Mutane za su fāɗi kamar bijiman jeji da 'yan bijimai, ƙasar za ta yi ja wur da jini, kitse kuma zai rufe ta. 8 Wannan shi ne lokacin da Ubangiji zai kuɓutar da Sihiyona, ya kuma ɗauki fansa a kan abokan gābanta. 9 Kogunan Edom za su zama kalo, wato kwalta, ƙasar za ta zama kibritu, wato farar wuta. Dukan ƙasar za ta ƙone kamar kalo. 10 Za ta yi ta ci dare da rana, hayaƙi zai yi ta tashi sama har abada. Ƙasar za ta zama marar amfani shekara da shekaru, ba wanda zai iya ƙara bi ta cikinta. 11 Mujiyoyi da hankaki su ne za su gāji ƙasar. Ubangiji zai maishe ta marar amfani, kamar yadda take tun kafin halitta. 12 Ba sarkin da zai yi mulkin ƙasar, dukan shugabanni kuma za su ƙare. 13 Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su tsiro su yi girma a cikin dukan fādodi da garuruwa masu garuka, diloli da mujiyoyi za su zauna a cikinsu. 14 Namomin jeji za su yi ta kaiwa da komowa a can suna kiran juna. Mugun naman jeji zai je can ya nemi wurin hutawa. 15 Mujiyoyi za su yi sheƙarsu a can, su nasa ƙwayaye, su ƙyanƙyashe 'ya'yansu, su kuma lura da su a can. Ungulai za su tattaru a can a kai a kai. 16 Bincika cikin Littafin Ubangiji ka karanta abin da yake faɗa. Ba ko ɗaya cikin halittattun nan da zai ɓata ba, ba kuwa wanda zai rasa ɗan'uwansa. Ubangiji ne ya umarta ya zama haka, shi kansa zai kawo su tare. 17 Ubangiji ne zai rarraba musu ƙasar, ya kuma ba ko wannensu nasa rabo. Za su zauna a ƙasar shekara da shekaru, za ta kuwa zama tasu har abada.

Mayarwar Mutanen Allah

Ishaya 35

1 Hamada za ta yi farin ciki. Furanni za su hudo a ƙasa da ba ta da amfani. 2 Hamada za ta raira waƙa da sowa don murna, Za ta zama kyakkyawa kamar Dutsen Lebanon, Da dausayi kamar filayen Karmel da Sharon. Kowa zai ga mafificiyar ɗaukakar Allah, Ya ga girmansa da ikonsa. 3 Ku ƙarfafa hannuwan da suka gaji, Da gwiwoyin da suke fama da rashin ƙarfi. 4 Ku faɗa wa dukan wanda ya karai, ku ce, “Ka ƙarfafa, kada kuwa ka ji tsoro! Allah yana zuwa domin ya kuɓutar da kai, Yana zuwa domin ya ɗauki fansa a kan abokan gābanka.” 5 Makaho zai iya ganin gari, Kurma kuma zai iya ji. 6 Gurgu zai yi tsalle ya yi rawa, Waɗanda ba su iya magana za su yi sowa don murna. Rafuffukan ruwa za su yi gudu a cikin hamada, 7 Yashi mai ƙuna kuma zai zama tafki, Ƙeƙasasshiyar ƙasa kuma za ta cika da maɓuɓɓugai. Inda diloli suka yi zama, Ciyawar fadama da iwa za su tsiro. 8 Za a yi babbar karauka a can, Za a kira ta, “Hanyar Tsarki.” Ba mai zunubi da zai taɓa bi ta wannan hanya, Ba wawayen da za su ruɗar da waɗanda suke tafiya can. 9 Ba za a sami zakoki a can ba, Mugayen namomin jeji ba za su bi ta can ba. Waɗancan da Ubangiji ya fansar Su za su zo gida ta wannan hanya. 10 Za su kai Urushalima da murna, Suna raira waƙa suna sowa don murna. Za su yi farin ciki har abada, Ba damuwa da ɓacin rai har abada.

Ishaya 36

Assuriyawa sun Kai Hari a Urushalima

1 A shekara ta goma sha huɗu da Hezekiya yake sarautar Yahuza, sai Sennakerib Sarkin Assuriya ya tasar wa birane masu kagara na Yahuza, ya kame su. 2 Sa'an nan ya umarci babban shugaban yaƙinsa ya tashi daga Lakish ya tafi Urushalima tare da babbar rundunar mayaƙa don su sa sarki Hezekiya ya ba da kai. Sai shugaban ya mamaye hanya inda masu wankin tufafi suke aiki, a daidai magudanar da take kawo ruwa daga kududdufin da yake daga can bisa. 3 Mutanen Yahuza su uku suka fito don su tarye shi, shugaba mai lura da fāda, wato Eliyakim ɗan Hilkiya, da marubucin ɗakin shari'a, wato Shebna, da shugaban da yake kula da tarihin da aka rubuta, wato Yowa ɗan Asaf. 4 Sai shugaban Assuriyawa ya faɗa musu, cewa babban sarki yana so ya san ko me ya sa sarki Hezekiya yake dogara ga kansa. 5 Ya ce, “Kana tsammani magana da baki kawai ta isa ta yi aiki da gwanayen sojoji, da kuma masu ƙarfi? Wa kake tsammani zai taimake ka, har da za ka yi mini tawaye? 6 Kana sa zuciya Masar za ta taimake ka, to, wannan ya zama kamar ka ɗauki kyauro ya zama sandan dogarawa, zai karye, ya yi wa hannunka sartse. Haka Sarkin Masar yake ga duk wanda ya dogara gare shi.” 7 Ya ci gaba ya ce, “Ko za ka ce mini kana dogara ga Ubangiji Allahnka? Shi ne wannan da Hezekiya ya lalatar masa da wuraren sujada da bagadai, sa'an nan ya faɗa wa jama'ar Yahuza da na Urushalima su yi sujada ga bagade ɗaya kurum. 8 Zan yi ciniki da kai da sunan babban sarki, wato Sennakerib. Zan ba ka dawakai dubu biyu idan za ka iya samun yawan mutanen da za su hau su! 9 Ba ka yi daidai da ka ƙi ko wani marar maƙami a shugabannin Assuriya ba, duk da haka kana sa rai ga Masarawa su aiko maka da karusai, da mahayan dawakai! 10 Kana tsammani na tasar wa ƙasarka na kuma lalatar da ita ba tare da taimakon Ubangiji ba? Ubangiji da kansa ne ya faɗa mini in tasar wa ƙasarka in lalatar da ita.” 11 Sa'an nan sai Eliyakim, da Shebna, da Yowa suka ce wa shugaba na Assuriya, “Ka yi mana magana da harshen Aramiyanci, muna jinsa. Kada ka yi da Ibrananci, dukan jama'ar da take a kan garu suna saurare.” 12 Ya amsa ya ce, “Kuna tsammani babban sarki ya aiko ni don in daɗa wa ku da sarki kurum dukan magana? Sam, ina magana ne da jama'ar da take a kan garu, waɗanda za su ci kāshinsu su kuma sha fitsarinsu, kamar yadda ku kanku za ku yi.” 13 Sa'an nan ya tsaya ya ta da murya da harshen Ibrananci, ya ce, “Ku saurara ga abin da Sarkin Assuriya yake faɗa muku. 14 Yana muku kashedi, cewa kada ku yarda Hezekiya ya ruɗe ku, Hezekiya ba zai iya cetonku ba. 15 Kada kuma ku bari ya rinjaye ku ku dogara ga Ubangiji, har ku sa tsammani Ubangiji zai cece ku, ya hana sojojinmu na Assuriya su cinye birninku. 16 Kada ku kasa kunne ga Hezekiya. Sarkin Assuriya yana umartarku ku fito daga cikin birni ku sallama. Za a yardar muku duka ku ci 'ya'yan inabi daga gonakinku, da 'ya'yan ɓaure na itatuwan ɓaurenku, ku kuma sha ruwa daga rijiyoyinku na kanku, 17 har babban sarki ya sāke zaunar da ku a wata ƙasa mai kama da taku, inda akwai gonakin inabi da za su ba da ruwan inabi, da hatsi don yin gurasa. 18 Kada ku bar Hezekiya ya ruɗe ku, da cewa Ubangiji zai kuɓutar da ku. Ko gumakan waɗansu al'ummai sun ceci ƙasashensu daga Sarkin Assuriya? 19 Ina suke yanzu, wato gumakan Hamat da na Arfad? Ina gumakan Sefarwayim? Ba ko ɗaya da ya ceci Samariya, ko ba haka ba? 20 A yaushe ko gunki ɗaya na dukan waɗannan ƙasashe ya taɓa ceton ƙasarsa daga babban sarkinmu? To, yanzu me ya sa kuke tsammani Ubangiji zai ceci Urushalima?” 21 Jama'a suka yi tsit, kamar dai yadda sarki Hezekiya ya faɗa musu, ba su amsa da kome ba. 22 Sa'an nan Eliyakim, da Shebna, da Yowa suka kyakkece tufafinsu don baƙin ciki, suka tafi, suka faɗa wa sarki abin da shugaban mayaƙan Assuriya ya yi ta farfaɗa.

Ishaya 37

An Ceci Yahuza daga Sennakerib

1 Da sai sarki Hezekiya ya ji abin da suka faɗa, sai ya kyakkece tufafinsa don baƙin ciki, ya sa tsummoki a jiki, ya shiga Haikalin Ubangiji. 2 Ya aiki Eliyakim mai kula da fāda, da Shebna marubucin ɗakin shari'a, da manyan firistoci zuwa wurin annabi Ishaya ɗan Amoz. Su kuma suna saye da tsummoki. 3 Ga saƙon da ya aike su su faɗa wa Ishaya, “Yau rana ce ta wahala, muna shan hukunci da wulakanci. Mun zama daidai da mace wadda take naƙuda, amma ba ta da ƙarfin da za ta haihu. 4 Sarkin Assuriya ya aiko babban shugaban mayaƙansa don ya zagi Allah mai rai. Da ma Ubangiji Allahnka ya ji waɗannan zage-zage ya kuma hukunta waɗanda suka yi su. Don haka sai ka yi addu'a ga Allah saboda mutanenmu waɗanda suka ragu.” 5 Sa'ad da Ishaya ya karɓi saƙon sarki Hezekiya, 6 sai ya aika masa da amsa cewa, “Ubangiji ya ce kada ka damu da irin zargin da Assuriyawa suke ta yi a kansa. 7 Ubangiji zai sa Sarkin Assuriya ya ji jita-jitar da za ta sa ya koma ƙasarsa, Ubangiji kuwa zai kashe shi a can.” 8 Shugaban mayaƙan Assuriya ya ji labari sarkin ya bar Lakish, yana can yana yaƙi da birnin Libna sai ya janye. 9 Sai Assuriyawa suka ji, cewa mayaƙan Masarawa, waɗanda sarki Tirhaka na Habasha yake yi wa jagora, suna zuwa su far musu da yaƙi. Sa'ad da sarkin ya ji haka sai ya aika wa sarki Hezekiya da wasiƙa, 10 ya ce masa, “Allahn da kake dogara gare shi ya faɗa maka, ba za ka faɗa a hannuna ba, amma kada ka yarda wannan ya ruɗe ka. 11 Ka dai ji abin da Sarkin Assuriya ya yi wa duk ƙasar da ya yi niyyar hallakarwa. Kana tsammani za ka kuɓuta? 12 Kakannina sun hallakar da biranen Gozan, da Haran, da Rezef, suka kuma kashe mutanen Eden, mazaunan Telassar, ba ko ɗaya daga cikin gumakansu da ya iya cetonsu. 13 Ina sarakunan biranen Hamat da Arfad, da Sefarwayim, da Hena, da Iwwa?” 14 Sarki Hezekiya ya karɓi wasiƙar daga hannun manzannin, ya karanta ta. Sa'an nan ya shiga Haikali, ya ajiye wasiƙar a gaban Ubangiji, 15 ya yi addu'a, 16 ya ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, kana kan kursiyinka, kai kaɗai ne Allah, kana mulkin dukan mulkokin duniya. Ka halicci duniya da sararin sama. 17 Yanzu, ya Ubangiji, ka ji mu, ka kuma dube mu. Ka kasa kunne ga dukan abubuwan da Sennakerib yake ta faɗa, yana zaginka, ya Allah mai rai. 18 Dukanmu mun sani, ya Ubangiji, yadda sarakunan Assuriya suka hallakar da al'ummai masu yawa, suka mai da ƙasashensu kufai, marasa amfani, 19 suka ƙaƙƙone gumakansu waɗanda ba Allah ba ne ko kaɗan, siffofi ne kurum na itace da na dutse, da mutane suka yi da hannuwansu. 20 Yanzu dai, ya Ubangiji Allahnmu, ka cece mu daga Assuriyawa domin dukan al'umman duniya su sani kai ne Allah kai kaɗai.” 21 Sa'an nan Ishaya ya aiki manzo zuwa wurin sarki Hezekiya, ya faɗa masa amsar Ubangiji a kan addu'ar sarki. 22 Ubangiji ya ce, “Birnin Urushalima yana yi maka dariya, kai Sennakerib, yana kuma yi maka ba'a. 23 Wa kake tsammani kana raina, kana yi masa ba'a? Ba ka ba ni girma ba, ni Allah mai tsarki na Isra'ila. 24 Ka aike da barorinka don su yi mini fāriya, da cewa ka ci nasara da duwatsu mafi tsayi da karusanka, har da ƙwanƙolin Dutsen Lebanon. Kana fāriya da cewa a can ka sare dogayen itatuwan al'ul da na fir, ka kuma kai wuri mafi nisa na jeji. 25 Ka kuma yi fāriya da cewa ka haƙa rijiyoyi a baƙuwar ƙasa, ka kuma sha ruwansu, sojojinka kuma sun tattake Kogin Nilu da ƙafafunsu, har ya ƙafe. 26 “Ba ka taɓa sani, na riga na shirya a yi haka tuntuni ba? Yanzu ne kuwa na cika wannan. Ni na ba ka iko ka ragargaza birane masu kagarai su zama tsibin ɓuraguzai. 27 Mutanen da suke zaune a can marasa ƙarfi ne. Sun firgita, sun suma. Sun zama kamar ciyawa a saura, ko hakukuwan da suka tsiro a kan rufi, waɗanda zafin iskar gabas ta buga su. 28 “Amma na san kome game da kai, abin da kake yi da inda kake tafiya. Na san yadda ka harzuƙa gāba da ni. 29 Na sami labarin irin harzuƙarka da girmankanka, yanzu kuwa zan sa ƙugiya a hancinka, linzami kuma a bakinka, in komar da kai.” 30 Sa'an nan Ishaya ya ce wa sarki Hezekiya, “Ga alama a kan abin da zai faru. Da bana da baɗi sai gyauro za ku ci, amma a shekara ta biye za ku iya shuka hatsi ku kuma girbe shi, ku dasa kurangar inabi ku ci 'ya'yan. 31 Su da suka tsira daga al'ummar Yahuza za su yi lafiya kamar dashe-dashen da saiwoyinsu suka shiga da zurfi cikin ƙasa, suka kuma ba da amfani. 32 Mutanen da za su tsira su ne na cikin Urushalima da na kan Dutsen Sihiyona, gama Ubangiji Mai Runduna ne ya yi niyya ya sa haka ya faru. 33 “Wannan shi ne abin da Ubangiji ya ce a kan Sarkin Assuriya, ‘Ba zai shiga wannan birni ba, ko kuwa ya harba ko da kibiya ɗaya a cikinsa. Sojoji masu garkuwoyi ba za su zo ko kusa da birnin ba, ba kuma za su yi mahaurai kewaye da birnin ba. 34 Zai koma ta kan hanyar da ya zo, ba kuwa zai taɓa shiga wannan birni ba. Ni, Ubangiji, ni na faɗa. 35 Zan kāre wannan birni in kiyaye shi, saboda girmana, domin kuma alkawarin da na yi wa bawana Dawuda.’ ” 36 Mala'ikan Ubangiji kuwa ya shiga sansanin Assuriyawa ya kashe sojoji dubu ɗari da dubu tamanin da dubu biyar (185,000 ). Da asuba ta yi, sai ga su can kwankwance, duk sun mutu! 37 Sa'an nan sai Sarkin Assuriya, wato Sennakerib, ya janye ya koma Nineba. 38 Wata rana ya je yana sujada a gidan gunkinsa Nisrok, sai biyu daga cikin 'ya'yansa, Adrammelek da Sharezer, suka kashe shi da takubansu, sa'an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Wani daga cikin sauran 'ya'yansa, wato Esar-haddon, ya gāje shi ya zama sarki.

Ishaya 38

Ciwon Sarki Hezekiya da Warkewarsa

1 A lokacin nan sai sarki Hezekiya ya kamu da rashin lafiya, har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya, ɗan Amoz, ya je wurinsa domin ya gaishe shi, ya ce masa, “Ubangiji ya ce ka kintsa kome daidai, gama ba za ka warke ba. Ka yi shirin mutuwa.” 2 Hezekiya kuwa ya juya wajen bango ya yi addu'a, ya ce, 3 “Ya Ubangiji, ka tuna, na bauta maka da aminci da biyayya, na kuma yi ƙoƙarin aikata abin da kake so in yi.” Sai ya fara kuka mai zafi. 4 Sa'an nan Ubangiji ya umarci Ishaya, 5 cewa ya koma wurin Hezekiya ya faɗa masa, “Ni, Ubangiji Allah na kakanka Dawuda, na ji addu'arka, na kuma ga hawayenka, zan bar ka ka ƙara shekara goma sha biyar nan gaba. 6 Zan cece ka, da wannan birni na Urushalima, daga Sarkin Assuriya, zan ci gaba da kiyaye birnin.” 7 Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ubangiji zai nuna maka alama da za ta tabbatar maka zai cika alkawarinsa. 8 Ubangiji zai komar da inuwa baya da taki goma, bisa ga ma'aunin rana na sarki Ahaz.” Inuwa kuwa ta koma da baya daga fuskar rana har mataki goma. 9 Bayan da Hezekiya ya warke daga rashin lafiyarsa, sai ya rubuta wannan waƙar yabo. 10 Na zaci a gaɓar ƙarfina Zan tafi lahira, Ba zan ƙara rayuwa ba. 11 Na zaci ba zan ƙara ganin Ubangiji ba A wannan duniya ta masu rai, Ko kuwa in ga wani mutum mai rai. 12 An datse raina, ya ƙare, Kamar alfarwar da aka kwance, Kamar saƙar da aka yanke, Na zaci Allah zai kashe ni. 13 Dare farai na yi ta kuka saboda azaba, Sai ka ce zaki yake kakkarya ƙasusuwana. Na zaci Allah zai kashe ni. 14 Muryata ƙarama ce, ba kuma ƙarfi, Na kuwa yi kuka kamar kurciya, Idanuna sun gaji saboda duban sama. Ya Ubangiji, ka cece ni daga dukan wannan wahala. 15 Me zan iya faɗa? Ubangiji ne ya yi wannan. Ina da ɓacin zuciya, ba na iya barci. 16 Ya Ubangiji, zan bi ka, kai kaɗai. Ka warkar da ni, ka bar ni da rai. 17 Ɓacin zuciyata zai juya ya zama salama. Ka ceci raina daga dukan hatsari, Ka gafarta dukan zunubaina. 18 Ba wanda yake yabonka a lahira, Matattu ba za su iya dogara ga amincinka ba. 19 Masu rai ne suke yabonka, Kamar yadda nake yabonka yanzu. Iyaye za su faɗa wa 'ya'yansu irin amincinka. 20 Ya Ubangiji, ka riga ka warkar da ni! Za mu kaɗa garayu mu kuma raira waƙar yabo, Za mu raira yabo cikin Haikalinka muddin ranmu. 21 Haka ya faru bayan da Ishaya ya faɗa wa sarki ya sa curin da aka yi da 'ya'yan ɓaure a kan marurun, ya kuwa warke. 22 Sarki Hezekiya ya riga ya yi tambaya ya ce, “Me zai zama alama ta cewa zan iya zuwa Haikali?”

Ishaya 39

Manzanni daga Ƙasar Babila

1 A wannan lokaci sai Sarkin Babila, wato Merodak Baladan, ɗan Baladan, ya ji labarin sarki Hezekiya ya yi rashin lafiya, saboda haka sai ya aika masa da wasiƙa da kuma kyautai. 2 Hezekiya kuwa ya marabci manzannin, ya kuma nunnuna musu dukiyarsa, wato azurfa da zinariya, da kayan yaji da na ƙanshi, da dukan kayayyakinsa na yaƙi. Ba abin da bai nuna musu ba a ɗakunan ajiya, da ko'ina a mulkinsa. 3 Sa'an nan annabi Ishaya ya je wurin sarki Hezekiya, ya tambaye shi ya ce, “Daga ina waɗannan mutane suka zo? Me kuma suka faɗa maka?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Daga ƙasa mai nisa suka zo, wato daga ƙasar Babila.” 4 Ishaya ya ce, “Me suka gani a fāda?” Hezekiya ya amsa ya ce, “Suka ga kome da kome. Ba abin da ban nuna musu ba a ɗakunan ajiya.” 5 Sa'an nan Ishaya ya faɗa wa sarki ya ce, “Ubangiji Mai Runduna ya faɗi haka, 6 ‘Lokaci yana zuwa da za a kwashe dukan abin da yake a fādarka, da dukan abin da kakanninka suka tara har ya zuwa yau, zuwa ƙasar Babila. Ba abin da za a rage. 7 Waɗansu daga cikin zuriyarka ta kanka, za a tafi da su a maishe su babani domin su yi hidima a fādar Sarkin Babila.’ ” 8 Da sarki Hezekiya ya gane, wannan zai faru ne a bayansa, wato a zamaninsa ba kome sai lafiya, sai ya amsa ya ce, “Jawabin da ka kawo mini daga wurin Ubangiji yana da kyau.”

Ishaya 40

Jawabin Ubangiji na Ta'aziyya ga Isra'ila

1 Ubangiji ya ce, “Ka ta'azantar da jama'ata. Ka ta'azantar da su! 2 Ka ƙarfafa jama'ar Urushalima. Ka faɗa musu sun sha wahala, ta isa, Yanzu kuwa an gafarta musu zunubansu. Na yi musu cikakken hukunci saboda dukan zunubansu.” 3 Murya tana kira tana cewa, “Ka shirya hanya a jeji domin Ubangiji! Ka share hanya a hamada domin Allahnmu! 4 Za a cike kowane kwari, Za a baje kowane dutse. Tuddai za su zama fili, Ƙasa mai kururrumai za ta zama sumul. 5 Sa'an nan za a bayyana ɗaukakar Ubangiji, Dukan 'yan adam kuwa za su gan ta. Ubangiji ne kansa ya yi wannan alkawari.” 6 Murya ta yi kira ta ce, “Ka yi shela!” Na yi tambaya na ce, “Shelar me zan yi?” “Ka yi shela, cewa dukan 'yan adam kamar ciyawa suke, Ba su fi furannin jeji tsawon rai ba. 7 Ciyawa takan bushe, furanni kuma sukan yi yaushi Sa'ad da Ubangiji ya aiko da iska ta hura ta kansu. Mutane kuwa ba su fi ciyawa ƙarfi ba! 8 Hakika ciyawa takan bushe, furanni kuwa su yi yaushi, Amma maganar Allah ba za ta taɓa faɗuwa ba!” 9 Ki haura a kan dutse mai tsayi, ke Urushalima, Ki faɗi albishir! Ki yi kira da babbar murya, ya Sihiyona, Ki faɗi albishir! Yi magana da ƙarfi, kada kuwa ki ji tsoro. Ki faɗa wa garuruwan Yahuza, Cewa Allahnsu yana zuwa! 10 Ubangiji yana zuwa ya yi mulki da iko, Zai taho tare da mutanen da ya cece su. Ga shi, zai kawo lada Zai kuma yi wa mutane sakamako. 11 Zai lura da garkensa kama yadda makiyayi yake yi, Zai tattara 'yan raguna wuri ɗaya, Zai ɗauke su ya rungume su, A hankali zai bi da iyayensu.

Allah na Isra'ila, Gagara Misali

12 Akwai wanda zai iya auna teku da tafin hannu, Ko sararin sama da tafin hannunsa? Akwai wanda zai iya tallabe turɓayar duniya a cikin finjali, Ko ya iya auna duwatsu da tuddai a ma'auni? 13 Akwai wanda zai iya umartar Ubangiji ya yi abu? Wa zai iya koya wa Ubangiji, ko ya yi masa shawara? 14 Da wa Allah yake yin shawara Domin ya sani, ya kuma fahimta, Ya kuma koyi yadda za a yi abubuwa? 15 Al'ummai ba kome ba ne a wurin Ubangiji, Ba su fi ɗigon ruwa ba, Manisantan tsibirai ba su fi ƙura nauyi ba. 16 Dukan dabbobin da suke a jejin Lebanon Ba su isa hadaya guda ga Allahnmu ba, Itatuwan jejin kuma ba su isa a hura wuta da su ba. 17 Al'ummai ba kome ba ne ko kaɗan a gare shi. 18 Da wa za a iya kwatanta Allah? Wa zai iya faɗar yadda yake? 19 Shi ba kamar gunki yake ba, wanda mutane suka yi, Maƙera kuma suka dalaye da zinariya, Suka sa shi cikin abin da suka yi da azurfa. 20 Mutum wanda bai isa samun azurfa ko zinariya ba, Yakan zaɓi itacen da ba zai ruɓe ba. Yana neman gwanin sassaƙa Domin ya yi masa siffa wadda ba za ta fāɗi ba. 21 Ashe, ba ka sani ba? Ashe, ba ka ji ba? Ashe, ba a faɗa maka ba tuntuni? Ashe, ba ka ji yadda aka fara duniya ba? 22 Wanda yake zaune a kursiyi ne ya yi ta, Can ƙwanƙolin duniya, gaba kuma da sararin sama, Yana ganin mutane a ƙarƙas kamar 'yan ƙananan ƙwari. Ya miƙa sararin sama kamar labule, Kamar kuma alfarwa domin mutane su zauna ciki. 23 Yakan kawo masu mulki masu iko ƙwarai, Ya kuwa mai da su ba kome ba ne, 24 Suna kama da ƙaramin dashe Wanda bai daɗe ba, Bai yi ko saiwar kirki ba. Sa'ad da Ubangiji ya aiko da iska, Sai su bushe, iskar ta hure su kamar ƙaiƙayi. 25 Da wane ne za a kwatanta Allah Mai Tsarki? Ko akwai wani mai kama da shi? 26 Ka dubi sararin sama a bisa! Wane ne ya halicci taurarin da kake gani? Shi wanda yake musu jagora kamar sojoji, Ya sani ko su guda nawa ne, Yana kiran dukansu, ko wanne da sunansa! Ikonsa da girma yake, Ba a taɓa rasa ko ɗayansu ba! 27 Isra'ila, me ya sa kake gunaguni, Cewa Ubangiji bai san wahalarka ba, Ko ya kula ya daidaita abubuwa dominka? 28 Ashe, ba ka sani ba? Ashe, ba ka ji ba? Ubangiji Madawwamin Allah ne? Ya halicci dukkan duniya. Bai taɓa jin gajiya ko kasala ba. Ba wanda ya taɓa fahimtar tunaninsa. 29 Yakan ƙarfafa masu kasala da masu jin gajiya. 30 Har da waɗanda suke yara ma, sukan ji kasala, Samari sukan siƙe su fāɗi, 31 Amma waɗanda suke dogara ga Ubangiji domin taimako Za su ji an sabunta ƙarfinsu. Za su tashi da fikafikai kamar gaggafa, Sa'ad da suke gudu, ba za su ji gajiya ba, Sa'ad da suke tafiya, ba za su ji kasala ba.

Ishaya 41

Alkawarin Allah ga Isra'ila

1 Allah ya ce, “Ku yi shiru ku kasa kunne gare ni, ku manisantan ƙasashe! Ku yi shiri ku gabatar da ƙararku a ɗakin shari'a. Za ku sami zarafi ku yi magana. Bari mu taru mu ga wanda yake da gaskiya. 2 “Wane ne wannan da ya kawo mai yin nasara daga gabas, Ya kuma sa ya ci nasara a dukan inda ya tafi? Wa ya ba shi nasara a kan sarakuna da al'ummai? Takobinsa ya sassare su sun zama kamar ƙura! Kibansa sun warwatsar da su kamar ƙaiƙayi a gaban iska! 3 Yana biye da kora, yana kuma tafiya lafiya, Da sauri ƙwarai, da ƙyar yake taɓa ƙasa! 4 Wane ne ya sa wannan ya faru? Wane ne ya ƙudurta labarun tarihi? Ni Ubangiji, ina can tun da farko, Ni kuma Ubangiji Allah, Zan kasance a can har ƙarshe. 5 “Mutanen manisantan ƙasashe suka ga abin da na yi, Suka tsorata, suka yi rawar jiki saboda tsoro. Saboda haka duka suka tattaru wuri guda. 6 Masu aikin hannu suka taimaka suka ƙarfafa juna. 7 Masassaƙi yakan ce wa maƙerin zinariya, ‘A gaishe ka!’ Wanda yake gyara gumaka ya yi sumul Yana ƙarfafa wanda yake harhaɗa su. Wani yakan ce, ‘Haɗin ya yi kyau,’ Sukan kuma manne gumakan da ƙusoshi. 8 “Amma kai, Isra'ila bawana, Kai ne jama'ar da na zaɓa, Zuriyar Ibrahim, abokina, 9 Na kawo ka daga maƙurar duniya, Na kira ka daga kusurwoyi mafi nisa. Na ce maka, ‘Kai ne bawana.’ Ban ƙi ka ba, amma maimakon haka na zaɓe ka. 10 Kada ka ji tsoro, ina tare da kai, Ni ne Allahnka, kada ka bar kome ya firgita ka. Zan sa ka yi ƙarfi, in kuma taimake ka, Zan kiyaye ka, in cece ka. 11 “Su waɗanda suke fushi da ku, ku jama'ata, Za a ƙasƙantar da su su ji kunya. Waɗanda suke faɗa da ku kuwa za su mutu. 12 Za ku neme su, amma ba za ku same su ba, Wato waɗanda suke gāba da ku. Waɗanda suka kama yaƙi da ku, Za su shuɗe daga duniya. 13 Ni ne Ubangiji Allahnku, Na ƙarfafa ku, na kuwa faɗa muku, ‘Kada ku ji tsoro, ni zan taimake ku.’ ” 14 Ubangiji ya ce, “Isra'ila, ku kima ne marasa ƙarfi kuma, Kada ku ji tsoro, zan taimake ku. Ni Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ni ne mai fansarku. 15 Zan sa ku zama kamar abin sussuka, Wanda yake sabo, mai kaushi, mai tsini. Za ku sussuke duwatsu ku lalatar da su, Za a marmashe tuddai kamar ƙura. 16 Za ku watsa su sama cikin iska, Iska za ta hure su, ta tafi da su, Hadiri kuma zai warwatsar da su. Amma za ku yi murna, gama ni ne Allahnku, Za ku yabe ni, Allah Mai Tsarki na Isra'ila. 17 “Sa'ad da jama'ata ta bukaci ruwa, Sa'ad da maƙogwaronsu ya bushe da ƙishi, Sa'an nan ni Ubangiji, zan amsa addu'arsu, Ni Allah na Isra'ila, ba zan taɓa yashe su ba. 18 Zan sa kogunan ruwa su yi gudu daga ƙeƙasassun tuddai, Maɓuɓɓugan ruwa su yi gudu a kwaruruka. Zan sa hamada ta zama kududdufan ruwa, Busasshiyar ƙasa kuma ta zama maɓuɓɓugan ruwa. 19 Zan sa itatuwan al'ul su tsiro a hamada, Da itacen ƙirya, da itacen ci-zaki, da zaitun. Ƙeƙasasshiyar ƙasa za ta zama kurmi, Jejin itatuwan fir. 20 Mutane za su ga wannan, su sani, Ni Ubangiji, na yi shi. Za su fahimta, Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya sa abin ya faru.”

Allah ya Ce wa Allolin Ƙarya, Ƙalubalanku

21 Ubangiji, Sarki na Isra'ila, ya faɗi wannan, “Ku allolin al'ummai ku gabatar da matsalarku. Ku kawo dukan gardandamin da kuke da su! 22 Ku zo nan ku faɗi abin da zai faru nan gaba, Ku bayyana wa ɗakin shari'a abubuwan da suka riga sun faru, Ku faɗa mana yadda zai zama duka, Domin lokacin da ya faru mu mu sani. 23 Ku faɗa mana abin da gaba ta ƙunsa. Sa'an nan za mu sani, ku alloli ne! Ku aikata wani abu mai kyau, ko ku kawo wani bala'i, Ku cika mu da jin tsoro da fargaba! 24 Ku da dukan abin da kuke yi ba kome ba ne, Waɗanda suke yi muku sujada kuwa, Abin ƙyama ne su! 25 “Na zaɓi mutum wanda yake zaune a gabas, Zan kawo shi don ya kawo hari daga arewa. Zai tattake masu mulki su zama kamar lāka, Kamar yadda magini yake tattake yumɓu. 26 Wane ne a cikinku ya faɗa mana tun da wuri, Ko ya yi annabci, cewa wannan zai faru, Har da za mu ce kun yi daidai? Ba ko ɗayanku da ya ce tak a kan wannan, Ba kuwa wanda ya ji kuna faɗar wani abu! 27 Ni Ubangiji, ni ne na farko da na faɗa wa Sihiyona albishir, Na aiki manzo zuwa Urushalima don ya ce, ‘Jama'arki suna zuwa! Suna zuwa gida.’ 28 Sa'ad da na duba alloli, Ba wanda yake da abin da zai faɗa, Ko ɗaya, ba wanda ya iya amsa tambayar da na yi. 29 Dukan waɗannan alloli ba su da amfani, Ba su iya kome ba, ko kaɗan, Gumakansu ba su da ƙarfi, ba su kuma da iko!”

Ishaya 42

1 Ubangiji ya ce, “Ga bawana, wanda na ƙarfafa, Wanda na zaɓa, wanda nake jin daɗinsa. Na cika shi da ikona, Zai kuwa kawo shari'ar gaskiya ga dukan al'ummai. 2 Ba zai yi tsawa ko ya ta da muryarsa ba, Ko ya yi jawabi da babbar murya a tituna. 3 Zai lallaɓi marasa ƙarfi, Ya nuna alheri ga tafkakku. Zai kawo madawwamiyar gaskiya ga duka. 4 Ba zai fid da zuciya ko ya karai ba, Zai kuma kafa gaskiya a duniya, Manisantan ƙasashe sun zaƙu, suna jiran koyarwarsa.” 5 Allah ya halicci sammai ya kuma shimfiɗa su, Ya yi duniya, da dukan masu rai nata, Ya ba da rai da numfashi ga dukan mutanenta. Yanzu kuwa Ubangiji Allah ya ce wa bawansa, 6 “Ni Ubangiji, na kira ka, na kuma ba ka iko Domin ka ga ana aikata gaskiya a duniya. Ta wurinka zan yi wa dukan mutane alkawari, Ta wurinka zan kawo haske ga al'ummai. 7 Za ka buɗe idanun makafi, Ka kuma kwance waɗanda suke ɗaure a kurkuku masu duhu. 8 “Ni kaɗai ne Ubangiji Allahnka. Ba wani allahn da zai sami ɗaukakata, Ba zan bar gumaka su sami yabona ba. 9 Abubuwan da na faɗa yanzu sun cika. Yanzu zan faɗa muku sababbin abubuwa, Tun kafin ma su soma faruwa.”

Yabo ga Ubangiji domin Cetonsa

10 Ku raira sabuwar waƙa ga Ubangiji, Ku raira yabo ku dukan duniya! Ku yabe shi, ku da kuke tafiya ta teku, Ku yabe shi, ku dukan halitta a teku! Ku raira, ku manisantan ƙasashe, da dukan waɗanda suke a can! 11 Bari hamada da garuruwanta su yabi Allah, Bari mutanen Kedar su yabe shi! Bari su da suke zaune a birnin Sela Su yi sowa don murna daga ƙwanƙolin duwatsu! 12 Bari waɗanda suke a manisantan ƙasashe su yi yabo, Su kuma girmama Ubangiji! 13 Ubangiji ya fita domin ya yi yaƙi kamar jarumi, Ya shirya, ya kuma ƙosa domin yaƙi. Ya yi gunzar yaƙi da tsawar yaƙi, Ya nuna ikonsa a kan abokan gābansa.

Allah ya yi wa Mutanensa Alkawarin Taimako

14 Allah ya ce, “Na daɗe na yi shiru, Ban amsa wa jama'ata ba. Amma yanzu lokaci ya yi da zan yi wani abu, Na yi ƙara kamar matar da take fama da zafin naƙuda. 15 Zan lalatar da tuddai da duwatsu, In kuma busar da ciyawa da itatuwa, Zan mai da kwaruruka inda akwai rafi hamada, In kuma busar da kududdufan ruwa. 16 “Zan yi wa mutanena makafi jagora A hanyar da ba su taɓa bi ba. Zan sa duhunsu ya zama haske, In kuma sa ƙasa mai kururrumai ta zama sumul a gabansu. Ba zan kasa yin waɗannan abu ba. 17 Dukan waɗanda suke dogara ga gumaka, Masu kiran siffofi allolinsu, Za a ƙasƙantar da su, su kuma sha kunya.”

Isra'ila suka Kāsa Koyo

18 Ubangiji ya ce, “Ku kasa kunne, ya ku kurame! Ku duba da kyau sosai, ku makafi! 19 Akwai sauran wanda ya fi bawana makanta, Ko wanda ya fi manzona kurunta, wato wanda na aiko? 20 Isra'ila, kun ga abu da yawa, Amma bai zama da ma'ana a gare ku ba ko kaɗan. Kuna da kunnuwan da za ku ji, Amma a ainihi me kuka ji?” 21 Ubangiji shi Allah ne da ya ƙosa ya yi ceto saboda gaskiyarsa, Saboda haka yana so a girmama koyarwarsa, 22 Amma yanzu an washe mutanensa, Aka kukkulle su a kurkuku, Aka ɓoye su a rami. Aka yi musu fashi, aka washe su, Ba wanda ya zo domin ya kuɓutar da su. 23 Ko akwai wanda zai kasa kunne ga wannan? Ko za ku kasa kunne ku yi lura daga yanzu? 24 Wane ne ya ba da Isra'ila ga masu waso? Ubangiji ne kansa, shi wanda muka yi wa zunubi! Ba mu iya zama kamar yadda yake so mu yi ba, Ko mu yi biyayya da koyarwarsa da ya ba mu. 25 Domin haka ya sa mu ji zafin fushinsa, Mu kuma sha wahalar da yaƙi ya kawo. Fushinsa ya yi ƙuna cikin dukan Isra'ila kamar wuta, Amma ba mu taɓa sanin abin da yake faruwa ba, Ba mu koyi kome daga wannan ba ko kaɗan.

Ishaya 43

Ubangiji kaɗai ne Mai Fansa

1 Ya Isra'ila, Ubangiji wanda ya halicce ku ya ce, “Kada ku ji tsoro, na fanshe ku. Na kira ku da sunanku, ku nawa ne. 2 Sa'ad da kuke bi ta cikin ruwa mai zurfi, Zan kasance tare da ku, Wahala ba za ta fi ƙarfinku ba. Sa'ad da kuke bi ta cikin wuta, ba za ku ƙuna ba, Wuyar da ta same ku ba za ta cuce ku ba. 3 Gama ni ne Ubangiji Allahnku, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, wanda ya cece ku. Zan ba da Masar, da Habasha, da Seba Ga Sairus domin fansarku. 4 Zan ba da dukan al'ummai don in ceci ranku, Gama kuna da daraja a gare ni, Gama na ba ku girma, ina kuma ƙaunarku. 5 Kada ku ji tsoro, ina tare da ku! “Daga gabas mafi nisa, da kuma yamma mafi nisa, Zan kawo jama'arku zuwa gida. 6 Zan faɗa wa kudu su bar su su tafi, Arewa kuma kada su riƙe su a can. Bari mutanena su komo daga manisantan ƙasashe, Daga kowane sashi na duniya. 7 Su mutanena ne, na kaina, Na kuwa halicce su don su girmama ni.” 8 Allah ya ce, “Kirawo mutanena a ɗakin shari'a. Suna da idanu, amma makafi ne, Suna da kunnuwa, amma kurame ne! 9 Kirawo sauran al'umma, su zo ga shari'a. A cikin allolinsu wane zai iya faɗar abin da yake a gaba? A cikinsu wa ya yi hurci a kan abin da yake faruwa yanzu? Bari waɗannan alloli su kawo shaidunsu Don su tabbatar daidai suke, Su shaida gaskiyar maganganunsu. 10 “Ya jama'ar Isra'ila, ku ne shaiduna, Na zaɓe ku al'umma, baiwata, Domin ku san ni, ku gaskata ni, Ku kuma fahimta, ni kaɗai ne Allah. In banda ni ba wani Allah, Ba a taɓa yin wani ba, Ba kuwa za a yi ba. 11 “Ni kaɗai ne Ubangiji, Ni kaɗai ne wanda yake da ikon yin ceto. 12 Na faɗi abin da zai faru Sa'an nan na zo domin taimakonku. Ba wani gunkin da ya taɓa yin haka, Ku ne shaiduna. 13 Ni ne Allah, haka kuwa nake tutur, Ba wanda zai iya tserewa daga ikona, Ba mai iya sāke abin da na riga na yi.”

Za a Hallaka Babila

14 Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji wanda ya fanshe ku ya ce, “Domin in cece ku zan aiko sojoji gāba da Babila, Zan rushe ƙofofin birni, Sowar mutanen birnin za ta zama kuka. 15 Ni ne Ubangiji, Allahnku Mai Tsarki na Isra'ila, Ni na halicce ku, ni ne kuma sarkinku.” 16 Tuntuni Ubangiji ya shirya hanya ta cikin teku, Da turba kuma a cikin ruwa. 17 Ya bi da manyan sojoji zuwa hallaka, Sojojin karusai da na dawakai. Sun faɗi warwar, ba za su ƙara tashi ba, An hure su kamar 'yar wutar fitila! 18 Amma Ubangiji ya ce, “Kada ku maƙale wa abubuwan da suka wuce, Ko ku riƙa tunanin abin da ya faru tuntuni. 19 Ku duba abin da nake shirin yi. Yana ta faruwa ma, kuna iya ganinsa yanzu! Zan yi hanya a cikin jeji, In kuma ba ku rafuffukan ruwa a can. 20 Har da namomin jeji za su girmama ni, Diloli da jiminai za su yi yabona Sa'ad da na sa kogunan ruwa su yi gudu a hamada, Domin su ba da ruwa ga zaɓaɓɓun mutanena. 21 Su ne mutanen da na yi domin kaina, Za su raira yabbaina!” 22 Ubangiji ya ce, “Amma ba ni kuka yi wa sujada ba, Kun gaji da ni, ya Isra'ila. 23 Ba ku kawo mini hadayun ƙonawa na tumaki ba, Ba ni kuke girmamawa da hadayunku ba. Ban nawaita muku da neman hadayu ba, Ko in gajiyar da ku da roƙon turare. 24 Ba ku sayi turare domina ba, Ko ku gamshe ni da kitsen dabbobinku. Maimakon haka, sai kuka nawaita mini da zunubanku, Kuka gajiyar da ni da abubuwan da kuke aikatawa da ba daidai ba. 25 Duk da haka, ni ne Allah wanda ya shafe zunubanku, Na kuwa yi haka saboda yadda nake. Ba zan ƙara tunawa da zunubanku kuma ba. 26 “Bari mu tafi ɗakin shari'a, ku kawo ƙararrakinku. Ku gabatar da matsalarku don a tabbatar kuna da gaskiya! 27 Kakanninku na farko sun yi zunubi, Manyanku sun yi mini laifi. 28 Zan musunci masu mulkin tsattsarkan masujadai, Saboda haka zan jawo wa Isra'ila hallaka, Zan bari a la'anta mutanena su sha zagi!”

Ishaya 44

Ubangiji shi kaɗai ne Allah

1 Ubangiji ya ce, “Ka saurara yanzu, ya Isra'ila, bawana, Zaɓaɓɓun mutanena, zuriyar Yakubu, 2 Ni ne Ubangiji wanda ya halicce ku, Tun farko, na taimake ku. Kada ku ji tsoro, ku bayina ne, Zaɓaɓɓun mutanena waɗanda nake ƙaunarsu. 3 “Zan ba da ruwa ga ƙasa mai ƙishi, In kuma sa rafuffuka su yi gudu a hamada. Zan kwararo da albarka a kan 'ya'yanku, In sa albarkata kuma a kan zuriyarku. 4 Za su yi kumari kamar ciyawar da ta sami ruwa sosai, Kamar itatuwan wardi a gefen rafuffukan ruwa mai gudu. 5 “Da ɗaya ɗaya da ɗaya ɗaya mutane za su ce, ‘Ni na Ubangiji ne!’ Za su zo su haɗa kai da jama'ar Isra'ila. Ko wanne zai ɗaura sunan Ubangiji a dantsensa, Ya ce da kansa ɗaya daga cikin mutanen Allah.” 6 Ubangiji, wanda yake mulkin Isra'ila, ya kuma fanshe su, Ubangiji Mai Runduna, yake faɗar wannan, “Ni ne farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici, Ba wani Allah sai ni. 7 Ko akwai wanda zai iya yin abin da na yi, Ya kuma fito fili ya faɗi abin da zai faru Tun daga farko, har zuwa ƙarshe? 8 Ya jama'ata, kada ku ji tsoro! Kun sani tun daga zamanin dā can, har zuwa yanzu, Na faɗa tun da wuri abin da zai faru. Ku ne kuwa shaiduna! Ko akwai wani Allah? Ko akwai wani Allah mai iko da ban taɓa jin labarinsa ba?”

Wautar Bautar Gumaka

9 Dukan waɗanda suke ƙera gumaka mutanen banza ne, gumakan da suke sa wa kuɗi da tsada kuma aikin banza ne. Waɗanda suke yi wa gumaka sujada kuwa makafi ne su, jahilai, za su sha kunya. 10 Wannan aikin banza ne, mutum ya yi siffa da ƙarfe don ya yi mata sujada! 11 Dukan wanda ya yi mata sujada za a ƙasƙantar da shi. Mutanen da suka ƙera gumakan, 'yan adam ne, ba wani abu ba. Bari su zo su tsaya gaban shari'a, za su razana, su kuma sha kunya. 12 Maƙeri yakan ɗauki guntun ƙarfe ya sa shi a wuta ya yi aiki. Da hannunsa mai ƙarfi yana ɗaukar guduma yana bugun ƙarfen, yana mai da shi siffa. Yakan ji yunwa, da ƙishi, yakan kuma ji gajiya. 13 Masassaƙi yakan auna itace. Ya zana siffa da alli, sa'an nan ya sassaƙe shi da kayan aikinsa. Ya yi shi da siffar mutum kyakkyawa, domin a ajiye shi a masujadarsu. 14 Zai yiwu ya sare itacen al'ul ya yi da shi, ko kuwa ya zaɓi itacen oak, ko na kasharina daga jeji. Ko kuwa ya dasa wani itace, ya jira ruwan sama don ya sa itacen ya yi girma. 15 Mutum yakan yi abin wuta da wani sashi na itacen, wani sashi kuma ya yi gunki da shi. Yakan hura wuta da wani sashi don ya ji ɗumi, yakan kuma toya gurasa. Yakan yi gunki da wani sashi, ya riƙa yi masa sujada! 16 Yakan hura wuta da wani sashi domin ya gasa nama, ya ci, ya ƙoshi. Ya ji ɗumi ya ce, “Kai, ɗumi da daɗi, wutar tana da kyau!” 17 Sauran itacen ya mai da shi gunki. Yana rusunawa ya yi masa sujada. Yana addu'a gare shi yana cewa, “Kai ne Allahna, ka cece ni!” 18 Irin waɗannan mutane dakikai ne, har ba su san abin da suke yi ba. Sun rufe idanunsu da tunaninsu ga gaskiya. 19 Masu ƙera gumaka ba su da ko tunanin da za su ce, “Na ƙone wani sashi na itacen nan. Na toya gurasa a garwashin, na kuma gasa nama, na ci shi, na kuwa ce sauran itacen zan sassaƙa gunki da shi. Ga ni yanzu, ina ta rusunawa gaban guntun itace!” 20 Ya zama daidai kamar mutum ya ci toka. Manufarsa ta wauta ta ɓatar da shi, har ba yadda za a iya taimakonsa. Ba zai iya ganewa ba, gunkin da ya riƙe a hannunsa ba allah ba ne ko kaɗan.

Ubangiji Mai Fansar Isra'ila

21 Ubangiji ya ce, “Ka tuna da waɗannan abu, ya Isra'ila, Ka tuna kai bawana ne. Na halicce ka domin ka zama bawana, Ba zan taɓa mantawa da kai ba. 22 Na shafe zunubanka kamar baƙin girgije, Da girgije kuma zan rufe laifofinka Ka komo wurina, ni ne na fanshe ka.” 23 Ku yi sowa ta farin ciki ya ku sammai! Ku yi sowa ku zurfafan wurare na duniya! Ku yi sowa ta murna, ku duwatsu, da kowane itace na jeji! Ubangiji ya fanshi mutanensa, Isra'ila, Saboda haka ya nuna girmansa. 24 “Ni ne Ubangiji, Mahaliccinku, Mai Fansarku. Ni ne Ubangiji, Mahaliccin dukkan abu. Ni kaɗai na shimfiɗa sammai, Ba wanda ya taimake ni sa'ad da na yi duniya. 25 Na sa masu duba su zama wawaye, Na sassāke annabce-annabcen masanan taurari. Na bayyana kuskuren maganar masu hikima, Na kuma nuna masu hikimarsu wauta ce. 26 Amma sa'ad da bawana ya yi annabci, Sa'ad da na aika da manzona domin ya bayyana shirye-shiryena, Na sa waɗannan shirye-shirye da annabce-annabce su cika. Ina faɗa wa Urushalima, cewa mutane za su sāke zauna a can, Za a kuma sāke gina biranen Yahuza. Waɗannan birane za su daina zama kufai. 27 Na yi umarni na sa teku ta ƙafe. 28 Na ce wa Sairus, ‘Kai ne wanda za ka yi mulki domina, Za ka yi abin da nake so ka yi, Za ka ba da umarni, cewa a sāke gina Urushalima, A kuma kafa harsashin ginin Haikali.’ ”

Ishaya 45

Ubangiji ya Mori Sairus

1 Sairus shi ne zaɓaɓɓen sarki na Ubangiji! Ubangiji ya sa shi ya ci al'ummai, Ya aike shi ya tuɓe ikon sarakuna, Ubangiji zai buɗe masa ƙofofin birni. Ubangiji ya ce wa Sairus, 2 “Ni kaina zan shirya hanya dominka, Ina baji duwatsu da tuddai. Zan kakkarye ƙyamaren tagulla, In kuma daddatse gagara badau na baƙin ƙarfe. 3 Zan ba ka dukiya daga cikin duhu, a asirtattun wurare, Sa'an nan za ka sani ni ne Ubangiji, Allah na Isra'ila kuma, shi ne ya zaɓe ka. 4 Na sa ka domin ka taimaki bawana Isra'ila, Jama'ar da ni na zaɓa. Na ba ka girma mai yawa, Ko da yake kai ba ka san ni ba. 5 “Ni ne Ubangiji, ba wani Allah sai ni. Zan ba ka irin ƙarfin da kake bukata, Ko da yake kai ba ka san ni ba. 6 Na yi wannan domin dukan waɗanda suke daga wannan bangon duniya zuwa wancan Su sani ni ne Ubangiji, Ba kuwa wani Allah sai ni. 7 Ni na halicci haske duk da duhu, Ni ne na kawo albarka duk da la'ana. Ni Ubangiji, na yi dukkan waɗannan abu. 8 Zan aiko da nasara daga sararin sama kamar ruwan sama. Ƙasa za ta buɗe ta karɓe ta, Za ta kuwa hudo da 'yanci da gaskiya. Ni Ubangiji, ni zan sa haka ya faru.”

Ubangiji Mahalicci Ne

9 Ko tukunyar yumɓu tana iya gardama da magininta, Tukunyar da take daidai da sauran tukwane? Ko yumɓu ya iya tambayar abin da maginin yake yi? Ko tukunya tana iya gunaguni a kan magininta? 10 Ko akwai wanda zai iya ce wa iyayensa, “Don me kuka haife ni kamar haka?” 11 Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Shi wanda ya halicce su, ya ce, “Ba ka da iko ka yi mini tambaya game da 'ya'yana, Ko ka faɗa mini abin da ya kamata in yi! 12 Ni ne wanda ya halicci duniya, Na kuma halicci mutum don ya zauna cikinta. Da ikona na shimfiɗa sammai, Ina kuwa mallakar rana, da wata, da taurari. 13 Ni kaina na iza Sairus ya yi wani abu, Don ya cika nufina ya daidaita al'amura. Zan miƙar da kowace hanyar da zai yi tafiya a kai. Zai sāke gina birnina, wato Urushalima, Ya kuma 'yantar da mutanena da suke bautar talala. Ba wanda ya yi ijara da shi, ko ya ba shi rashawa don ya yi wannan.” Ubangiji Mai Runduna ne ya faɗi wannan. 14 Ubangiji ya ce wa Isra'ila, “Dukiyar Masar da ta Habasha za ta zama taku, Dogayen mutanen Seba kuma za su zama bayinku, Za su bi ku suna a ɗaure da sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su tuba, su ce, ‘Allah yana tare da ku, shi kaɗai ne Allah.’ ” 15 Allah na Isra'ila, wanda ya ceci mutanensa, Shi ne yakan ɓoye kansa. 16 Su waɗanda suka yi gumaka, dukansu za su sha kunya, Dukansu za su zama abin kunya. 17 Amma Ubangiji ya ceci Isra'ila, Nasararsa kuwa za ta tabbata har abada, Mutanensa ba za su taɓa shan kunya ba. 18 Ubangiji ne ya halicci sammai, Shi ne wanda yake Allah! Shi ne ya shata duniya ya kuma yi ta, Ya kafa ta, ta kahu da ƙarfi, za ta yi ƙarƙo! Bai halicce ta hamada da ba kome a ciki ba, Amma wurin zaman mutane. Shi ne wanda ya ce, “Ni ne Ubangiji, Ba kuwa wani Allah, sai ni. 19 Ba a ɓoye na yi magana ba, Ban kuwa ɓoye nufina ba. Ban ce jama'ar Isra'ila Su neme ni a kowace hanyar ruɗami ba. Ni ne Ubangiji, gaskiya kuwa nake faɗa, Ina sanar da abin da yake daidai.”

Ubangiji da Gumakan Babila

20 Ubangiji ya ce, “Ku taru wuri ɗaya ku jama'ar al'ummai, Dukanku da kuka tsira daga faɗuwar mulki, Ku gabatar da kanku domin shari'a! Waɗancan da suka ɗauka gumakansu na itace, Suna kuma addu'a ga allolin da ba su iya cetonsu, Waɗannan mutane ba su san kome ba ko kaɗan! 21 Ku zo ku gabatar da matsalarku a ɗakin shari'a, Bari waɗanda aka kai ƙara su yi shawara da juna. Wane ne ya faɗi abin da zai faru, Ya kuma yi annabci tuntuni? Ashe, ba ni ba ne, Ubangiji, Allah wanda ya ceci mutanensa? Ba wani Allah sai ni. 22 “Ku juyo wurina a cece ku, Ku mutane ko'ina a duniya! Ni kaɗai ne Allah da yake akwai. 23 Abin da na faɗa gaskiya ne, Ba kuwa zai sāke ba. Ni, a dukkan yadda nake, na yi alkawari mai ƙarfi, Kowa da kowa zai zo ya durƙusa a gabana, Ya yi wa'adin zama mai biyayya a gare ni. 24 “Za su ce ta wurina kaɗai Za a iya samun nasara da ƙarfi, Amma dukan waɗanda suka raina ni za su sha kunya. 25 Ni Ubangiji, zan kuɓutar da dukan zuriyar Yakubu, Za su kuwa yi yabona.”

Ishaya 46

1 “Wannan ne ƙarshen allolin Babila! Dā ana yi wa Bel da Nebo sujada, Amma yanzu ana labtunsu a kan jakuna, Sun zama nawaya a kan dabbobin da suka gaji! 2 Wannan ne ƙarshen waɗannan alloli, Gumaka ba su iya ceton kansu, Aka kame su aka tafi da su. 3 “Ku kasa kunne gare ni ku zuriyar Yakubu, Dukanku, mutanena da kuka ragu. Ina ta lura da ku tun daga lokacin da aka haife ku. 4 Ni ne Allahnku, zan kuwa lura da ku, Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura. Ni na halice ku zan kuwa lura da ku, Zan yi muku taimako in kuwa kuɓutar da ku.” 5 Ubangiji ya ce, “Da wane ne za ku kwatanta ni? Akwai wani mai kama da ni? 6 Mutane suka buɗe alabensu suna zazzage zinariya, Suna auna azurfa a kan ma'auni. Suka yi jingar maƙerin zinariya don ya yi musu gunki, Sa'an nan suka rusuna suka yi masa sujada! 7 Suka ɗauke shi a kafaɗunsu su tafi da shi, Suna ajiyewa a wani wuri, ya yi ta tsayawa a can, Ba ya iya motsawa daga inda yake. Idan wani ya yi addu'a gare shi, ba zai iya amsawa ba, Ko ya cece shi daga bala'i. 8 “Ku tuna da wannan, ku masu zunubi, Ku dubi irin abin da na yi. 9 Ku tuna da abin da ya faru tuntuni, Ku sani, ni kaɗai ne Allah, Ba kuwa wani mai kama da ni. 10 Tun da farko na faɗa muku yadda abin zai zama, Tuntuni na yi faɗi a kan abin da zai faru. Na kuwa ce shirye-shiryena ba za su taɓa fāɗuwa ba, Zan aikata dukan abin da na yi niyyar yi. 11 Ina kiran wani mutum ya zo daga gabas, Zai kawo sura kamar shaho, Zai kammala abin da na shirya. Na yi faɗi, zai kuwa cika. 12 “Ku kasa kunne gare ni, ku mutane masu taurinkai, Ku da kuke tsammani nasara tana can da nisa. 13 Ina kawo ranar nasara kusa, Ba ta da nisa ko kaɗan. Nasarata ba za ta yi jinkiri ba. Zan ceci Urushalima, Zan kuma kawo ɗaukaka ga Isra'ila a can.”

Ishaya 47

Hukunci a kan Babila

1 Ubangiji ya ce, “Babila, ki sauko daga kan gadon sarautarki, Ki zauna a ƙasa cikin ƙura. Dā ke budurwa ce, birnin da ba a yi nasara da shi ba! Amma ba sauran taushi da kuma rashin ƙarfi! Ke baiwa ce yanzu! 2 Ki juya dutsen niƙa, ki niƙa gari! Ki kware lulluɓi! Ki tuɓe kyawawan tufafinki! 3 Mutane za su gan ki a ƙasƙance, a kunyace kuma, A tuɓe ki tsirara kamar yarinyar da take baiwa. Zan ɗauki fansa, ba kuwa wanda zai hana ni.” 4 Allah Mai Tsarki na Isra'ila ya fanshe mu, Sunansa Ubangiji Mai Runduna ne! 5 Ubangiji ya ce wa Babila, “Ki zauna shiru a cikin duhu, Ba za su ƙara kiranki sarauniyar al'ummai ba! 6 Na yi fushi da mutanena, Na maishe su kamar su ba nawa ba ne. Na sa su a ƙarƙashin ikonki, Ba ki kuwa yi musu jinƙai ba, Har da tsofaffi ma kin ba su wuya. 7 Kina tsammani za ki yi ta zama sarauniya kullayaumin, Ba ki ɗauki waɗannan al'amura a zuci ba, Ko ki yi tunanin yadda za su ƙare. 8 “Ki kasa kunne, ke mai ƙaunar nishaɗi, Ke da kike tsammani kina zaune lami lafiya. Kin ɗauka kina da girma kamar Allah, Har kina ganin ba wani kamarki. Kina tsammani ba za ki taɓa zama gwauruwa ba, Ko ki sha hasarar 'ya'yanki. 9 Amma ba da jimawa ba, a rana ɗaya Dukan waɗannan al'amura za su faru. Kome sihirin da za ki yi, Za ki rasa 'ya'yanki, ki kuwa zama gwauruwa. 10 “Kin amince da kanki cikin muguntarki, Kina tsammani ba wanda yake ganinki. Hikimarki da saninki suka sa kika ɓata, Kika kuwa ce da kanki, ‘Ni ce Allah, Ba mai kama da ni!’ 11 Duk da haka bala'i zai auko miki, Ba ɗaya daga cikin sihirinki da zai tsai da shi ba, Lalacewa za ta auko a kanki farat ɗaya, Lalacewar da ba ki taɓa ko mafarkinta ba! 12 Ki riƙe dukan sihirinki, da makarunki, da layunki, Kina amfani da su tun kina ƙarama. Watakila za su yi miki wani taimako, Watakila kya iya tsoratar da abokan gāba. 13 Kome shawarar da kika samu ba ki da ƙarfi. Bari mashawartanki su fito su cece ki, Waɗancan mutane masu binciken taurari Waɗanda suka zana taswirar sammai, Su kuma faɗa miki Dukan abin da zai faru da ke wata wata. 14 “Za su zama kamar budu, Wuta kuwa za ta ƙone su ƙurmus! Ba ma za su ko iya ceton kansu ba. Harshen wuta zai fi ƙarfinsu, Ba wutar da za su zauna, su ji ɗumi! 15 Nan ne inda shawararsu za ta kai ki, Waɗannan masanan taurari da kika yi ta neman shawararsu dukan kwanakin ranki. Dukansu za su bar ki, kowa ya tafi inda ya nufa, Ba wanda zai ragu da zai cece ki.”

Ishaya 48

Annabci a kan Sababbin Abubuwa

1 Ku kasa kunne, ya jama'ar Isra'ila, Ku da kuke zuriyar Yahuza. Kuna rantsuwa da sunan Ubangiji, Kuna nuna kamar kuna sujada ga Allah na Isra'ila, Amma abin da kuke faɗa ba haka kuke nufi ba. 2 Amma duk da haka kuna fāriya, da cewa Ku ne mazaunan birni mai tsarki, Kuna kuma dogara ga Allah na Isra'ila, Wanda sunansa Ubangiji, Mai Runduna. 3 Ubangiji ya ce wa Isra'ila, “Tuntuni na yi faɗi a kan abin da zai faru, Sa'an nan na sa ya faru ba labari! 4 Na sani kuna nuna ku masu taurinkai ne, Kuna ƙage kamar ƙarfe, kun taurare kamar tagulla. 5 Tuntuni na yi faɗi a kan makomarku, Na hurta abubuwa tun kafin su faru, Domin kada ku ɗauka cewa gumakanku ne suka yi su, Siffofinku ne kuma suka sa abin ya zama haka. 6 “Dukan abin da na faɗa yana cika yanzu, Sai ku yarda, faɗata gaskiya ce. Yanzu zan faɗa muku sababbin abubuwan da za su zo, Abubuwan da ban bayyana su a dā ba. 7 Yanzu ne kaɗai nake sawa su faru, Ba wani abu makamancin wannan da ya faru a baya. Da ya faru, da za ku ɗauka cewa kun san kome a kansa. 8 “Na sani ba za a iya gaskata ku ba, Tun daga haihuwarku kuma an san ku da tayarwa. Shi ya sa ba ku taɓa jin wannan ba ko kaɗan, Ko kalma ɗaya ba ta taɓa shiga kunnenku ba. 9 “Saboda mutane su yi yabon sunana Shi ya sa nake danne fushina, Ina kuma ɓoye shi, kada in hallaka ku. 10 Na gwada ku da wutar wahala, Kamar yadda ake tace azurfa a tanda, Amma na tarar ba ku da amfani. 11 Abin da na yi, na yi shi don kaina ne, Ba zan bari a rasa girmama sunana ba, Ko kuwa wani dabam ya sami ɗaukaka Wadda take tawa ce, ni kaɗai.”

Ubangiji zai Fanshi Isra'ila

12 “Ku kasa kunne gare ni, ya Isra'ila, jama'ar da na kira! Ni ne Allah, farko, da ƙarshe, Allah Makaɗaici! 13 Dantsena ne ya kafa harsashin ginin duniya, Ya kuma shimfiɗa sammai. Lokacin da na kira duniya da sararin sama, Sukan zo nan da nan, su gabatar da kansu! 14 “Ku tattaru, ku duka, ku kasa kunne! Ba ko ɗaya cikin alloli da zai iya yin annabci ba, Cewa mutumin da na zaɓa, shi zai iya fāɗa wa Babila, Zai yi abin da na umarce shi. 15 Ni ne na yi magana, na kuwa kira shi, Na yi masa jagora na kuwa ba shi nasara. 16 “Yanzu fa, sai ku matso kusa da ni, Ku ji abin da nake faɗa. Tun da farko na yi magana da ku a fili, A koyaushe nakan cika maganata.” (Yanzu Ubangiji Allah ya ba ni iko, ya kuwa aike ni.) 17 Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Ubangiji, wanda ya fanshe ku, ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, Wanda yake so ya koya muku domin amfanin kanku, Ya kuwa nuna muku hanyar da za ku bi. 18 “Da ma kun kasa kunne ga umarnina kurum! Da sai albarka ta yi ta kwararowa dominku Kamar ƙoramar da ba ta taɓa ƙafewa ba! Da kuma nasara ta samu a gare ku kamar raƙuman ruwa Da suke bugowa zuwa gāɓa. 19 Zuriyarku za su yi yawa kamar tsabar yashi, Zan kuma tabbatar, cewa ba za a hallaka su ba.” 20 Ku fita daga Babila, ku tafi a sake! Ku yi sowar albishir da farin ciki, ku sa a sani a ko'ina, “Ubangiji ya fanshi bawansa Isra'ila!” 21 Lokacin da Ubangiji ya bi da mutanensa ta cikin busasshiyar hamada, mai zafi, Ba su sha wahalar ƙishi ba. Ya sa ruwa ya gudano daga cikin dutse dominsu, Ya tsage dutse, ruwa ya kwararo. 22 Ubangiji ya ce, “Ba mafaka domin masu zunubi.”

Ishaya 49

Bawan Ubangiji zai zama Haske ga Al'ummai

1 Ku kasa kunne gare ni, ku al'ummai manisanta, Ku mutanen da kuke zaune a can nesa! Ubangiji ya zaɓe ni, tun kafin a haife ni, Ya kuwa sa ni in zama bawansa. 2 Ya sa maganata ta yi kaifi kamar takobi, Ya kiyaye ni da ikonsa. Ya sa na zama kamar kibiya Mai tsini shirayayyiya domin harbi. 3 Ya ce mini, “Isra'ila, kai bawana ne. Mutane za su yabe ni saboda kai.” 4 Na ce, “Na yi aiki, amma a banza ne. Na mori ƙarfina, amma ban ƙulla kome ba.” Duk da haka na dogara ga Ubangiji, ya daidaita al'amura, Shi zai sāka mini abin da na yi. 5 Ubangiji ya zaɓe ni tun kafin a haife ni. Ya maishe ni bawansa domin in komo da mutanensa, In komo da jama'ar Isra'ila da aka warwatsar. Ubangiji ya ba ni daraja, Shi ne tushen ƙarfina. 6 Ubangiji ya ce mini, “Bawana, ina da aiki mai girma dominka, Ba komo da girman jama'ar Isra'ila da suka ragu kaɗai ba, Amma zan sa ka zama haske ga al'ummai, Domin dukan duniya ta tsira.” 7 Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Mai Fansa, Ya ce wa wanda aka raina ƙwarai, Al'ummai suka ƙi shi, Bawa na masu mulki kuma, “Sarakuna za su gan ka a sake, Su kuma miƙe tsaye su ba ka girma, Shugabanni su kuma za su gani, Su rusuna har ƙasa su ba ka girma.” Wannan kuwa zai faru saboda Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, ya zaɓi bawansa, Ya kuwa cika alkawaransa.

Alkawarin Maido Urushalima

8 Ubangiji ya ce wa jama'arsa, “Idan lokacin da zan cece ku ya yi, zan nuna muku alheri. Zan ji kukanku in taimake ku. Zan tsare ku in kiyaye ku, Zan kuwa yi wa dukan mutane alkawari ta wurinku. Zan bar ku ku sāke zama a ƙasarku wadda take kufai a yanzu. 9 Zan ce wa 'yan kurkuku, ‘Ku tafi na sake ku!’ Waɗanda suke cikin duhu kuwa, in ce musu, ‘Ku fito zuwa wurin haske!’ Za su zama kamar tumakin da suke kiwo a tuddai, 10 Ba za su taɓa jin yunwa ko ƙishi ba. Ba za su sha zafin rana da na hamada ba, Gama wanda yake ƙaunarsu ne zai bi da su. Zai bi da su zuwa maɓuɓɓugan ruwa. 11 “Zan yi babbar hanya ta kan duwatsu, In kuma shirya hanya domin mutanena su bi. 12 Mutanena za su zo daga can nesa, Daga Birnin Sin a kudu, Daga yamma, da arewa.” 13 Ku raira, ku sammai! Ki yi sowar murna, ke duniya! Bari duwatsu su ɓarke da waƙa! Ubangiji zai ta'azantar da mutanensa, Zai ji juyayin mutanensa da suke shan wahala. 14 Amma mutanen Urushalima suka ce, “Ubangiji ya yashe mu! Ya manta da mu.” 15 Saboda haka Ubangiji ya amsa ya ce, “Mace za ta iya mantawa da jaririnta, Ta kuma ƙi ƙaunar ɗan da ta haifa? Ya yiwu mace ta manta da ɗanta, To, ni ba zan taɓa mantawa da ku ba. 16 Ya Urushalima, ba zan taɓa mantawa da ke ba, Na rubuta sunanki a gabana. 17 “Su waɗanda za su sāke gina ki suna tafe yanzu, Waɗanda suka lalatar da ke kuwa za su tashi. 18 Ki dudduba, ki ɗaga idonki, ki ga abin da yake faruwa! Mutanenki suna tattaruwa suna komowa gida! Hakika, da yake ni ne Allah Mai Rai, Za ki yi fāriya da mutanenki, Kamar yadda amarya take fāriya da kayan adonta! 19 “Aka lalatar da ƙasar, ta zama kufai, Amma yanzu za ta yi wa waɗanda suke komowa domin su zauna cikinta kaɗan. Waɗanda suka lalatar da ke kuwa, Za a kawar da su daga gare ki. 20 Mutanenki da aka haifa a lokacin zaman talala, Wata rana za su ce miki, ‘Wannan ƙasa ta yi kaɗan ƙwarai, Muna bukatar ƙarin wurin zama!’ 21 Sa'an nan za ki ce wa kanki, ‘Wa ya haifa mini waɗannan 'ya'ya? Na rasa 'ya'yana, ba kuwa zan iya haifar waɗansu ba. Aka kore ni, aka yi mini ɗaurin talala, Wane ne ya haifi waɗannan 'ya'ya? Aka bar ni, ni kaɗai, Daga ina waɗannan 'ya'ya suka fito?’ ” 22 Ubangiji Allah ya ce wa jama'arsa, “Zan nuna alama ga al'ummai, Za su kuwa kawo 'ya'yanku gida. 23 Sarakuna za su zama kamar iyaye a gare ku, Sarauniyoyi za su yi renonku kamar uwaye. Za su rusuna har ƙasa su ba ku girma, Da tawali'u za su nuna muku bangirma. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji, Dukan mai jiran taimakon Ubangiji, ransa ba zai ɓaci ba.” 24 Kuna iya ku ƙwace wa sojoji wason da suka yi? Kuna iya kuɓutar da 'yan kurkuku daga ɗaurin masu baƙin mulki? 25 Ubangiji ya amsa ya ce, “Wannan shi ne ainihin abin da zai faru. Za a ƙwace kamammun yaƙi, Za a kuma ƙwace wason da masu baƙin mulki ya yi. Zan yi yaƙi da dukan wanda yake yaƙi da ku, Zan kuwa kuɓutar da 'ya'yanku. 26 Zan sa masu zaluntarku su karkashe juna, Za su yi māye, da kisankai, da fushi. Sa'an nan dukan 'yan adam za su sani, ni ne Ubangiji, Wanda ya cece ku, ya fanshe ku. Za su sani ni ne Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila.”

Ishaya 50

1 Ubangiji ya ce, “Kuna tsammani na kori mutanena Kamar yadda mutum yakan saki mata tasa? To, in haka ne ina takardar kisan auren? Kuna tsammani na sayar da ku cikin bauta Kamar mutumin da ya sayar da 'ya'yansa? A'a, kun tafi bauta ne saboda da zunubanku, Aka tafi da ku saboda da laifofinku. 2 “Don me mutanena ba su amsa ba Sa'ad da na je wurinsu domin in cece su? Don me ba su amsa ba sa'ad da na yi kiransu? Ba ni da isasshen ƙarfin da zan fanshe su ne? Ina da iko in sa teku ya ƙafe ta wurin umarnina, Ina kuma da iko in sa rafuffukan ruwa su zama hamada, Kifayen da suke ciki su mutu saboda rashin ruwa. 3 Ina da iko in sa sararin sama ya yi duhu, In sa ya zama makoki domin matattu.”

Biyayyar Bawan Ubangiji

4 Ubangiji ya koya mini abin da zan faɗa, Domin in iya ƙarfafa marar ƙarfi. A kowace safiya yakan sa in yi marmarin jin abin da zai koya mini. 5 Ubangiji ya ba ni fahimi, Ban kuwa yi masa tayarwa ba Ko in juya in rabu da shi. 6 Na tsiraita ga masu d�kana. Ban hana su sa'ad da suke zagina ba, Suna tsittsige gemuna, Suna tofa yau a fuskata. 7 Amma zaginsu ba zai yi mini ƙari ba, Gama Ubangiji Allah yana taimakona. Na ƙarfafa kaina domin in jure da su. Na sani ba zan kunyata ba, 8 Gama Allah yana kusa, Zai tabbatar da ni, marar laifi ne, Ko akwai wanda zai iya kawo ƙararraki game da ni? Bari mu je ɗakin shari'a tare! Bari ya kawo ƙararrakinsa! 9 Ubangiji kansa zai kāre ni, Wa zai iya tabbatar da ni mai laifi ne? Dukan waɗanda suke sarana za su shuɗe, Za su shuɗe kamar tufar da asu ya cinye! 10 Ku duka da kuke tsoron Ubangiji, Kuna kuma biyayya da kalmomin bawansa, Zai yiwu hanyar da kuke bi ta yi duhu ƙwarai, Amma ku dogara ga Ubangiji, ku jingina ga Allahnku. 11 Dukanku da kuke ƙulle-ƙullen hallaka juna Ƙulle-ƙullenku za su hallaka ku! Ubangiji kansa zai sa wannan ya faru, Za ku gamu da mummunar ƙaddara.

Ishaya 51

Maganar Ta'aziyya ga Sihiyona

1 Ubangiji ya ce, “Ku kasa kunne gare ni, ku da kuke so a cece ku, Ku da kuka zo gare ni neman taimako. Ku yi tunanin dutse inda kuka fito, Da mahaƙar duwatsu inda kuka fito. 2 Ku yi tunani a kan kakanku Ibrahim, Da Saratu, wadda kuke zuriyarta. Sa'ad da na kira Ibrahim ba shi da ɗa, Amma na sa masa albarka, na ba shi 'ya'ya, Na sa zuriyarsa suka yi yawa. 3 “Zan ji juyayi a kan Sihiyona, Da dukan masu zama a kufanta. Ko da yake ƙasarta hamada ce, zan sa ta zama lambu, Kamar lambun da na dasa a Aidan. Murna da farin ciki za su kasance a can, Da waƙoƙi na yabo da godiya zuwa gare ni. 4 “Ku kasa kunne gare ni, ku mutanena, Ku saurara ga abin da nake faɗa, Na ba da koyarwata ga al'ummai, Dokokina za su kawo musu haske. 5 Zan zo da sauri in cece su, Lokacina na nasara ya yi kusa. Ni kaina zan yi mulki a kan al'ummai. Manisantan ƙasashe za su jira ni in zo, Za su jira da sa zuciya, ni in cece su. 6 Ku duba sammai, ku duba duniya! Sammai za su shuɗe kamar hayaƙi, Duniya kuwa za ta yage kamar tsohuwar tufa, Dukan mutanenta kuma za su mutu. Amma ceton da zan kawo zai dawwama har abada, Nasarata, ita ce za ta zama ta har abada. 7 “Ku kasa kunne gare ni, ku da kuka san abin da yake daidai, Ku da kuke riƙe da koyarwata a zuciyarku. Kada ku ji tsoro sa'ad da mutane suke yi muku ba'a da zagi. 8 Irin waɗannan mutane za su shuɗe kamar tufar da asu ya cinye! Amma ceton da zan kawo zai dawwama har abada, Nasarata za ta kasance har abada abadin.” 9 Ya Ubangiji, ka tashi, ka taimake mu! Ka nuna ikonka, ka cece mu, Ka nuna ikonka kamar yadda ka yi a dā. Kai ne ka daddatse dodon ruwa, wato Rahab. 10 Kai ne ka sa teku ta ƙafe, Ka kuma shirya hanya ta ruwa, Domin waɗanda kake cetonsu su haye. 11 Su waɗanda ka fansa Za su kai Urushalima da farin ciki, Da waƙa, da sowa ta murna. Za su yi ta murna har abada, Ba sauran baƙin ciki ko ɓacin zuciya har abada. 12 Ubangiji ya ce, “Ni ne wanda yake ƙarfafa ku. Don me za ku ji tsoron mutum mai mutuwa, Wanda bai fi ciyawa tsawon rai ba? 13 Kuna mantawa da Ubangiji wanda ya halicce ku, Wanda ya shimfiɗa sammai, Ya kuma kafa harsashin ginin duniya? Don me za ku yi ta jin tsoron fushin waɗanda suke zaluntarku, Da waɗanda suke shiri su hallaka ku? Fushinsu ba zai taɓa yi muku kome ba! 14 'Yan sarƙa za su fita ba da jimawa ba Za su yi tsawon rai, Su kuma sami dukan abincin da suke bukata. 15 “Ni ne Ubangiji Allahnku, Na dama teku Na sa raƙumanta suka yi ruri. Sunana Ubangiji Mai Iko Dukka! 16 Na shimfiɗa sammai, Na kafa harsashin ginin duniya, Na ce wa Sihiyona, ‘Ku jama'ata ne! Na ba ku koyarwata, Na kuwa kiyaye ku da ikona.’ ”

Ƙarshen Wahalar Urushalima

17 Ya Urushalima, ki farka! Ki tashi da kanki, ki miƙe! Kika sha ƙoƙon hukunci wanda Ubangiji cikin fushinsa, ya ba ki ki sha, Kika shanye shi, ya kuwa sa ki yi tangaɗi! 18 Ba wanda zai yi miki jagora, Ba wani daga cikin mutanenki Da zai kama hannunki. 19 Masifa riɓi biyu ta auko miki, Yaƙi ya lalatar da ƙasarki, Mutanenki suka tagayyara da yunwa. 20 A kan kusurwar kowane titi Mutanenki sun rafke saboda rashin ƙarfi, Sun zama kamar barewa da tarkon maharbi ya kama. Suka ji ƙarfin fushin Allah. 21 Ku mutanen Urushalima, masu shan wahala, Ku da kuke tangaɗi kamar waɗanda suka bugu, 22 Ubangiji Allahnku ya kāre ku ya ce, “Ina ɗauke ƙoƙon da na ba ku cikin fushina. Ba za ku ƙara shan ruwan inabin da zai sa ku yi tangaɗi ba. 23 Zan ba da shi ga waɗanda suke zaluntarku, Su waɗanda suka sa kuka kwanta a tituna Suka tattake ku, sai ka ce kun zama ƙura.”

Ishaya 52

Allah zai Ceci Urushalima

1 Urushalima, ki ƙarfafa, ki yi girma kuma! Birni mai tsarki na Allah, Ki yafa wa kanki jamali! Arna ba za su ƙara shiga ta ƙofofinki ba. 2 Ki kakkaɓe kanki, ya Urushalima! Ki tashi daga cikin ƙura, Ki hau gadon sarautarki. Ki ɓaɓɓale sarƙoƙin da suke ɗaure da ke, Ke kamammiyar jama'ar Sihiyona! 3 Ubangiji ya ce wa jama'arsa, “Ba a biya kuɗi domin a saye ku ba, Amma ga shi, kuka zama bayi. Ba za a biya kuɗin fansa domin a 'yantar da ku ba, Amma, ga shi, za a 'yantar da ku. 4 Kuka taɓa zaman baƙuntaka a Masar, Daga baya Assuriyawa suka zalunce ku ba gaira ba dalili. 5 Yanzu kuma, ga shi, yana faruwa a Babila, Kuka zama kamammu a can, ba gaira ba dalili. Su da suke mulkinku suna girmankai, suna fāriya, Suna ta nuna mini raini. 6 Amma zuwa gaba za ku sani Ni ne Allah, wanda na yi magana da ku.” 7 Me ya fi wannan kyau? A ga manzo yana zuwa ta kan duwatsu, Ɗauke da albishir mai daɗi, labarin salama. Ya yi shelar nasara, ya ce wa Sihiyona, “Allahnki sarki ne!” 8 Waɗanda suke tsaron birni suna sowa, Suna sowa tare saboda murna! Za su ga komowar Ubangiji a Sihiyona da idanunsu! 9 Ku ɓarke da sowar murna, Ku kufan Urushalima! Ubangiji ya ta'azantar da jama'arsa, Ya fanshi birninsa. 10 Ubangiji ya nuna ikonsa mai tsarki, Ya ceci jama'arsa, Dukan duniya kuwa ta gani. 11 Ku fita, ku bar Babila Ku dukanku da kuke ɗauke da keɓaɓɓen kayan Ubangiji! Kada ku taɓa abin da aka hana, Ku kiyaye kanku da tsarki, Ku fita ku bar birnin. 12 A wannan lokaci ba za ku bukaci ku fita da garaje ba, Ba za ku yi ƙoƙari ku tsere ba! Ubangiji Allah ne zai bishe ku, Ya kuma kiyaye ku ta kowane gefe.

Bawan Ubangiji Mai Shan Wuya

13 Ubangiji ya ce, “Bawana zai yi nasara a aikinsa, Zai zama babba, a kuwa girmama shi ƙwarai. 14 Mutane da yawa suka gigice sa'ad da suka gan shi, Ya munana har ya fita kamannin mutum. 15 Amma yanzu al'ummai da yawa za su yi mamaki a kansa, Sarakuna kuwa za su riƙe baki saboda mamaki. Za su gani su kuma fahimci abin da ba su taɓa sani ba.”

Ishaya 53

1 Wane ne zai gaskata abin da muka ji yanzu? Wane ne zai iya ganin ikon Ubangiji cikin wannan? 2 Nufin Ubangiji ne bawansa ya yi girma Kamar dashe wanda yake kafa saiwarsa a ƙeƙasasshiyar ƙasa. Ba shi da wani maƙami ko kyan ganin Da zai sa mu kula da shi. Ba wani abin da zai sa mu so shi, Ba kuwa abin da zai ja mu zuwa gare shi. 3 Muka raina shi, muka ƙi shi, Ya daure da wahala da raɗaɗi. Ba wanda ya ko dube shi. Muka yi banza da shi kamar shi ba kome ba ne. 4 Amma ya daure da wahala wadda a ainihi tamu ce, Raɗaɗin da ya kamata mu ne za mu sha shi. Mu kuwa muna tsammani wahalarsa Hukunci ne Allah yake yi masa. 5 Amma aka yi masa rauni saboda zunubanmu, Aka daddoke shi saboda muguntar da muka aikata. Hukuncin da ya sha ya 'yantar da mu, D�kan da aka yi ta yi masa, ya sa muka warke. 6 Dukanmu muna kama da tumakin da suka ɓata, Ko wannenmu ya kama hanyarsa. Sai Ubangiji ya sa hukunci ya auko a kansa, Hukuncin da ya wajaba a kanmu. 7 Aka ƙware shi ba tausayi, Amma ya karɓa da tawali'u, Bai ko ce uffan ba. Kamar ɗan rago wanda ake shirin yankawa, Kamar tunkiya wadda ake shirin yi wa sausaya, Bai ko ce uffan ba. 8 Aka kama shi, aka yanke masa shari'a, Aka tafi da shi domin a kashe shi, Ba wanda ya kula da ƙaddararsa. Aka kashe shi saboda zunubin mutanenmu. 9 Aka yi jana'izarsa tare da maguye. Aka binne shi tare da masu arziki Ko da yake bai taɓa yin laifin kome, ko ƙarya ba. 10 Ubangiji ya ce, “Nufina ne ya sha wahala, Mutuwar kuwa hadaya ce domin ta kawo gafara, Saboda haka zai ga zuriyarsa, Zai yi tsawon rai, Ta wurinsa nufina zai cika. 11 Bayan shan wahalarsa, zai sāke yin murna, Zai fahimta wahalar da ya sha ba ta banza ba ce, Shi ne bawana, adali, Zai ɗauki hukuncin mutane masu yawa, Ya sa su zama mutanena amintattu. 12 Saboda haka zan ba shi matsayi mai girma, Matsayi a cikin manyan mutane masu iko. Da yardarsa ya ba da ransa Ya ɗauki rabon masu laifi. Ya maye gurbin masu zunubi da yawa, Ya kuwa sha hukuncin da ya cancanci masu zunubi. Ya yi roƙo dominsu.”

Ishaya 54

Ƙaunar Ubangiji ga Isra'ila

1 Urushalima, kika zama kamar matar da ba ta da ɗa. Amma yanzu kina iya rairawa, ki yi sowa saboda murna. Yanzu za ki ƙara samun 'ya'ya fiye da na Matar da mijinta bai taɓa rabuwa da ita ba! 2 Ki fāɗaɗa alfarwar da kike zama ciki! Ki ƙara tsawon igiyoyinta, ki kuma ƙara ƙarfin turakunta! 3 Za ki faɗaɗa kan iyakar ƙasarki a kowane gefe, Jama'arki za su karɓi ƙasarsu Wadda al'ummai suke mallaka yanzu, Biranen da aka bari ba kowa, za su cika da mutane. 4 Kada ki ji tsoro, ba za a ƙara kunyatar da ke ba, Ba kuwa za a ƙasƙantar da ke ba. Za ki manta da rashin amincinki irin na matar ƙuruciya, Za ki manta da matsanancin kaɗaicinki, Mai kama da na gwauruwa. 5 Mahaliccinki zai zama kamar miji a gare ki, Sunansa Ubangiji Mai Runduna! Allah Mai Tsarki na Isra'ila mai fansarki ne, Shi ne mai mulkin dukan duniya! 6 Kina kama da amarya Wadda mijinta ya rabu da ita, tana baƙin ciki ƙwarai. Amma Ubangiji yana kiranki zuwa gare shi, ya ce, 7 “A ɗan ƙanƙanen lokaci na rabu da ke, Amma da ƙauna mai zurfi zan sāke karɓarki. 8 Na juya, na rabu da ke da fushi da ɗan lokaci, Amma zan nuna miki ƙaunata har abada.” Haka Ubangiji mai fansarki ya faɗa, shi wanda ya cece ki. 9 “Na yi alkawari a zamanin Nuhu, Cewa ba zan ƙara rufe duniya da Ruwan Tsufana ba. Yanzu kuwa ina miki alkawari, Cewa ba zan ƙara yin fushi da ke ba, Ba zan ƙara tsawata miki, ko in hukunta ki ba. 10 Duwatsu da tuddai za su ragargaje, Amma ƙaunar da nake yi miki ba za ta ƙare ba sam. Zan cika alkawarina na salama har abada.” Haka Ubangiji ya faɗa, shi wanda yake ƙaunarki. 11 Ubangiji ya ce, “Ya Urushalima, mai shan wahala, birnin da yake cikin halin ƙaƙa naka yi, Ba ki da wanda zai ta'azantar da ke. Zan sake gina harsashinki da duwatsu masu daraja. 12 Zan gina hasumiyarki da jan yakutu, Da ƙofofinki kuma da duwatsu masu haske kamar hasken wuta, Da garun da ya kewaye ki kuwa zan gina ta da lu'ulu'ai. 13 “Ni kaina zan koya wa mutanenki, Zan kuwa ba su wadata da salama. 14 Adalci da gaskiya za su ƙarfafa ki. Za ki tsira daga shan zalunci da razana. Gama ba za su kusace ki ba. 15 Idan wani ya far miki, Ya yi ne ba da yardata ba, Dukan wanda ya hau ki da yaƙi zai fāɗi! 16 “Ni ne na halicci maƙeri Wanda ya zuga wuta ya kuwa ƙera makamai. Ni ne kuma na halicci mayaƙi Wanda yakan mori makamai domin kisa. 17 Amma ba makamin da aka ƙera da ya isa ya cuce ki, Za ki iya amsa wa dukan waɗanda za su yi ƙararki. Zan kāre bayina, In kuwa ba su nasara.” Ubangiji ne ya faɗa.

Ishaya 55

Allah ya Nuna Jinƙai ga Kowa

1 Ubangiji ya ce, “Duk mai jin ƙishi ya zo, Ga ruwa a nan! Ku da ba ku da kuɗi ku zo, Ku sayi hatsi ku ci! Ku zo ku sayi ruwan inabi da madara, Ba za ku biya kome ba! 2 Don me za ku kashe kuɗi a kan abin da ba abinci ba? Don me za ku ɓad da albashinku, amma kuna ta shan yunwa? Ku kasa kunne gare ni, ku yi abin da na faɗa, Za ku sha daɗin abinci mafi kyau duka. 3 “Ku mutanena, ku kasa kunne yanzu, ku zo gare ni, Ku zo gare ni, za ku kuwa sami rai! Zan yi tabbataccen alkawari da ku, Zan sa muku albarkun da na alkawarta wa Dawuda. 4 Na sa ya zama shugaba, da shugaban yaƙi na al'ummai, Ta wurinsa kuwa na nuna musu girmana. 5 Yanzu kuwa za ku kira al'ummai, baƙi, Dā ba su kuwa san ku ba, ko da rana ɗaya, Amma yanzu za su sheƙo a guje domin su haɗa kai da ku! Ni, Ubangiji Allahnku, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Zan sa dukan wannan ya faru, Zan ba ku girma da daraja.” 6 Ku juyo wurin Ubangiji, ku yi addu'a gare shi, Yanzu da yake kusa. 7 Bari mugaye su bar irin al'amuransu, Su sāke irin tunaninsu. Bari su juyo wurin Ubangiji, Allahnmu, Shi mai jinƙai ne, mai saurin gafartawa. 8 Ubangiji ya ce, “Tunanina ba kamar irin naku ba ne, Al'amurana kuma dabam suke da naku. 9 Kamar yadda sammai suke can nesa da ƙasa, Haka al'amurana da tunanina suke nesa da naku. 10 “Maganata kamar dusar ƙanƙara take, Kamar kuma ruwan sama da yake saukowa domin ya jiƙe duniya. Ba za su kasa sa amfanin gona ya yi girma ba, Sukan ba da iri domin shukawa, da abinci kuma domin a ci. 11 To, haka maganar da na faɗa take, Ba ta kāsa cika abin da na shirya mata, Za ta yi kowane abin da na aike ta ta yi. 12 “Za ku fita daga cikin Babila da murna, Za a bi da ku, ku fita daga birnin da salama. Duwatsu da tuddai za su ɓarke da waƙa, Itatuwa za su yi ta sowa don murna! 13 Itacen fir zai tsiro a wurin da sarƙaƙƙiya take yanzu, Itacen ci-zaƙi zai tsiro a maimakon ƙayayuwa. Wannan zai zama alamar da za ta kasance har abada, Matuni ne na abin da ni, Ubangiji, na yi.”

Ishaya 56

Sakamakon Cikar Alkawarin Ubangiji

1 Ga jawabin da Ubangiji ya yi, “Ku kiyaye gaskiya ku yi adalci, gama cetona yana zuwa nan da nan, za a kuwa bayyana adalcina. 2 Mai albarka ne mutumin da yake aikata wannan, da ɗan adam da yake riƙe da shi kam, wanda yake kiyaye ranar Asabar, bai kuwa ƙazantar da ita ba, wanda kuma ya tsame hannunsa daga aikata kowace irin mugunta.” 3 Kada baƙon da ya hada kansa da mutanen Ubangiji ya ce, hakika Ubangiji zai ware shi daga jama'arsa. Kada kuma baban ya ce shi busasshen itace ne. 4 Ga abin da Ubangiji ya ce, wa mutanen nan, “Ku babani waɗanda kuka kiyaye Asabar ɗina, ku da kuka zaɓi abubuwan da suka gamshe ni, kuka kuwa cika alkawarina da aminci, 5 zan ba ku matuni da suna a Haikalina da cikin garukana, da sun fi na 'ya'ya mata da maza. Zan ba ku tabbataccen suna wanda ba za a raba ku da shi ba.” 6 Ubangiji ya ce wa baƙin da suka bi shi, don su yi masa hidima, suna ƙaunar sunansa, sun kuma zama bayinsa, dukan wanda yake kiyaye ranar Asabar, bai kuwa ɓata ta ba, ya kuma cika alkawarinsa da aminci, 7 “Zan kai ku tsattsarkan dutsena, in sa ku yi murna a masujadata. Hadayunku na ƙonawa da sadakokinku za su zama abin karɓa a bagadena. Za a kira Haikalina wurin yin addu'a na dukan jama'a.” 8 Haka Ubangiji Allah, shi wanda ya tattara Isra'ilawa korarru, ya faɗa, ya ce, “Zan ƙara tattaro waɗansu, bayan waɗanda na riga na tattara.”

Kā da Tsafin Isra'ila

9 Dukanku namomin jeji ku zo ku ci, dukanku namomin jeji. 10 Matsaransa makafi ne, dukansu marasa ilimi ne. Dukansu kamar karnuka ne bebaye, ba su iya haushi ba, suna kwance suna ta mafarki, suna jin daɗin rurumi! 11 Suna kama da karnuka masu zarin ci, ba su taɓa samun abin da ya ishe su ba. Makiyayan nan kuma ba haziƙai ba ne, dukansu, kowa ya nufi inda ya ga dama. Kowa yana ta nemar wa kansa riba. 12 Sukan ce, “Zo mu samo ruwan inabi, bari mu cika cikinmu da barasa. Gobe ma kamar yau za ta zama, har ma fiye da haka.”

Ishaya 57

1 Adalin mutum yakan mutu, amma ba wanda ya kula. An kwashe mutanen kirki ba kuwa wanda ya kula, an tsame adali daga cikin bala'i. 2 Ya shiga da salama yana hutawa a kabarinsa, shi wanda ya yi tafiya da adalci. 3 Amma ku ku matso nan kusa, ku 'ya'ya maza na masu sihiri, ku zuriyar mazinaci da karuwa. 4 Wa kuke yi wa ba'a? Ga wa kuke wage baki, kuna zaro harshe? Ashe, ku ba 'ya'yan masu laifi ba ne, zuriyar marikita, 5 ku da muguwar sha'awa take ƙonawa a tsakanin itatuwan oak, da ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa. Ku da kuka karkashe 'ya'yanku a cikin kwaruruka, da a ƙarƙashin duwatsu masu tsayi? 6 Rabonku yana cikin duwatsu masu sulɓi na cikin kwari. A gare su kuka kwarara hadaya ta sha, kuka kawo hadaya ta gari. Kuna tsammani zan ji daɗin waɗannan al'amura? 7 A kan dogayen duwatsu masu tsayi kuka sa gadonku. A can kuka haura don ku miƙa hadaya. 8 A bayan ƙofa da madogaran ƙofa kuka kafa gumakanku. Kun rabu da ni, kun kware gadonku, kuna hau kun fāɗaɗa shi, kuka ƙulla yarjejeniya tsakaninku da su. Kuna ƙaunar gadonsu, kun dubi tsiraici. 9 Kun tafi wurin Molek da mai, da turare iri iri da kuka riɓaɓɓanya. Kun aika jakadunku can nesa, kun aike su su gangara, har zuwa lahira. 10 Kun damu saboda nisan hanyarku, amma ba ku ce, “Ba shi da wani amfani ba.” Ƙarfinku ya sake sabunta ranku, don haka ba ku suma ba. 11 Ubangiji ya ce, “Wa ya sa ku fargaba, kuke jin tsoronsa, har kuka yi ƙarya? Ba ku tuna da ni, ko ku kula da ni ba? Ashe, ban yi haƙuri tun da daɗewan nan ba, duk da haka kuwa ba ku ji tsorona ba? 12 Zan ba da labarin adalcinku da ayyukanku, amma ba za su taimake ku ba. 13 Sa'ad da kuka ta da murya kuka yi kuka, to, bari tattaruwar gumakanku su cece ku! Iska za ta fauce su, numfashi zai kawar da su. Amma wanda ya fake gare ni zai mallaki ƙasar. Zai kuma yi sujada a Haikalina.”

Taimakon Allah da Warkarwa

14 Ubangiji ya ce, “Ku gina, ku shirya hanya. Ku kawar da kowane abin sa tuntuɓe daga kan hanyar jama'ata!” 15 Gama haka wanda yake can Sama, Maɗaukaki, wanda ake kira Mai Tsarki ya ce, “Ina zaune a can Sama a tsattsarkan wuri, tare kuma da wanda yake da halin tuba mai tawali'u, don in farfaɗo da ruhun masu tawali'u, in kuma farfaɗo da zukatan masu tuba. 16 Ba zan yi ta gāba da ku, ko in yi ta fushi da ku har abada ba. Gama ruhu zai yi suma a gabana, da numfashin su waɗanda na halitta. 17 Na yi fushi da su saboda muguntar kwaɗayinsu, don haka na buge su. Na ɓoye fuskata, na yi fushi. Amma sun yi taurinkai, sun yi ta komawa da baya, sun bi son zuciyarsu. 18 “Na ga al'amuransu, amma zan warkar da su, zan bi da su, in ta'azantar da su tare da masu makoki. 19 Salama, salama,” in ji Ubangiji, “Ga wanda yake nesa da wanda yake kusa. Zan warkar da su. 20 Amma mugaye suna kama da tumbatsar teku, gama ba ta iya natsuwa. Ruwanta kuma yana tumbatsa, ya gurɓace, ya ƙazantu.” 21 Allah ya ce, “Ba salama ga mugaye.”

Ishaya 58

Kiyaye Azumi yadda ya Kamata

1 Ubangiji ya ce, “Ku yi kuka da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa! Ku ta da muryoyinku kamar busar ƙaho. Ku shaida wa jama'ata laifinsu, ku shaida wa zuriyar Yakubu zunubansu. 2 Duk da haka suna ta nemana kowace rana, suna murna su san al'amurana, sai ka ce su al'umma ce wadda take aikata adalci, wadda kuma ba ta rabu da dokokin Allahnta ba. Suna roƙona in yi musu shari'ar adalci, suna murna su zo kusa da Allah.” 3 Mutane sukan ce, “Me ya sa muka yi azumi, Ubangiji bai gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, Ubangiji kuwa bai kula ba?” Ubangiji ya ce musu, “Duba, a ranar da kuke azumi, nishaɗin kanku kuke nema, kuna zaluntar dukan ma'aikatanku. 4 Duba, kuna azumi don ku yi jayayya ne, ku yi ta faɗa, ku yi ta naushin juna. Irin wannan azumi naku a wannan rana, ba zai sa a ji muryarku a can Sama ba. 5 Irin azumin da nake so ke nan ne? Wato ranar da mutum zai ƙasƙantar da kansa kawai. Wato ku sunkuyar da kanku ne kamar jema, ku kuma shimfiɗa tsumma, ku barbaɗa toka a inda kuke zama. Kun iya ce da wannan azumi, karɓaɓɓiyar rana ga Ubangiji? 6 “To, ba irin wannan azumi ne na zaɓa ba? Wato ku kwance sarƙoƙin mugunta, ku kwance masu karkiya, ku 'yantar da waɗanda ake zalunta, ku kakkarye kowace karkiya. 7 Ku ci abincinku tare da mayunwata, ku kuma shigo da matalauta, marasa mahalli a cikin gidajenku. Idan kuma kun ga wanda yake tsirara, ku sa masa sutura, kada kuma ku ɓoye fuskokinku ga 'yan'uwanku. 8 “Sa'an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, za ku warke nan da nan. Adalcinku zai yi muku jagora, zatina zai rufa muku baya. 9 Sa'an nan za ku yi kira, ni kuwa zan amsa, za ku yi kuka, ni kuwa zan ce muku, ‘Ga ni.’ “Idan kuka kawar da karkiya daga cikinku, kuka daina nuna wa juna yatsa, da faɗar mugayen maganganu, 10 idan kuka ƙosar da mayunwata, kuka biya bukatar waɗanda suke shan tsanani, sa'an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu, duhunku kuma zai zama kamar hasken tsakar rana. 11 Zan bi da ku kullayaumin, zan biya bukatarku da abubuwa masu kyau, in sa ƙasusuwanku su yi ƙarfi, ku zama kamar lambun da ake masa banruwa, za ku zama kamar maɓuɓɓugar ruwa da ba ta ƙonewa. 12 Za ku sāke gina tsofaffin kufanku na dā can, za ku sāke kafa tushen zuriya da yawa. Za a kira ku, ‘Masu gyaran abin da ya lalace, masu sāke gyaran gidaje.’ ” 13 Ubangiji ya ce, “Idan kun juyo kuna kiyaye ranar Asabar, kuka daina annashuwarku a tsattsarkar ranata, kuka kuma kira Asabar ranar murna, tsattsarkar rana ta Ubangiji, mai daraja, idan kun girmama ta, har kuka daina bin son zuciyarku, ba ku kuma bar shagulgula su ɗauke hankalinku ba, ko ku hurta maganganun banza, 14 sa'an nan ne za ku yi murna cikin Ubangiji, zan sa ku a kan maɗaukakan wurare na duniya. Zan kuma ciyar da ku da gādon mahaifinku Yakubu, ni Ubangiji na faɗa.”

Ishaya 59

Faɗar Muguntar Al'ummar

1 Duba, ikon Ubangiji bai kasa ba, har da ba zai yi ceto ba. Shi ba kurma ba, har da ba zai ji ba. 2 Amma laifofinku suka raba tsakaninku da Allahnku. Zunubanku ne kuma suka sa ya juya daga gare ku don kada ya ji ku. 3 Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma sun ƙazantu da mugunta, leɓunanku kuma suna faɗar ƙarairayi, harsunanku kuwa suna raɗar mugunta. 4 Ba wanda yake kai ƙara ta gaskiya, ba wanda yake yanke shari'a da adalci. Kuna dogara ga shaidar ƙarya, kuna faɗar ƙarya, kuna ɗaukar ciki na ɓarna, ku haifi mugunta. 5 Kuna ƙyanƙyashe ƙwan kāsa, kuna saƙa da saƙar gizogizo. Duk wanda ya ci ƙwayayenku zai mutu, ƙwan da ya fashe zai ƙyanƙyashe kububuwa. 6 Saƙarku ba za ta yi amfani kamar tufa ba, ba za ku yi sutura da abin da kuka yi ba. Ayyukanku ayyukan mugunta ne, kuna aikata ayyukan kama-karya. 7 Kukan sheƙa a guje don ku aikata mugunta, kuna gaggawar zub da jinin marasa laifi. Tunaninku tunanin mugunta ne, lalatarwa da hallakarwa suna a manyan karaukunku. 8 Hanyar salama ba ku san ta ba. Ba adalci a hanyoyinku, kukan karkatar da hanyoyinku, ba wanda zai yi tafiya lafiya a cikinku. 9 Mutane suna cewa, “Don haka ne, yin gaskiya ya yi nisa da mu, adalci kuwa bai iske mu ba. Muna ta neman haske, sai ga duhu, muna neman haske, sai muka yi tafiya cikin duhu. 10 Muna ta lalubar bango kamar makafi, muna ta lalubawa kamar marasa idanu. Da tsakar rana muke ta tuntuɓe, sai ka ce da almuru. A tsakanin waɗanda suke da cikakken ƙarfi, kamar matattu muke. 11 Dukanmu muna gurnani kamar beyar, muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci, amma ina. Muna ta neman ceto, amma ya yi nisa da mu. 12 “Gama laifofinmu sun yi yawa a gabanka, zunubanmu kuwa suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu suna tare da mu, muna kuwa sane da laifofinmu, 13 wato musun Ubangiji, da ƙin bin Allah, da maganar zalunci, da ta tayarwa, da shirya ƙarairayi a zuciya, da kuma hurta su. 14 Aikata gaskiya ya kawu, adalci ya tsaya daga can nesa, gama gaskiya ta fāɗi a dandali, sahihanci ba zai shiga ba. 15 Gaskiya ba ta, wanda ba ya aikata mugunta ya zama ganima.” Ubangiji ya gani, bai kuwa ji daɗi ba, da yake gaskiya ba ta. 16 Ya ga ba wani mutum, ba kuwa wanda zai taimaki waɗanda ake zalunta. Sa'an nan da ikon kansa ya yi nasara, adalcinsa ya goyi bayansa. 17 Ya rufe ƙirjinsa da sulken adalci, da kwalkwalin ceto a kansa. Ya sa rigar ɗaukar fansa, ya yafa alkyabbar ikonsa. 18 Bisa ga ayyukansu, haka zai sāka musu hasala, a kan maƙiyansa kuwa ramawa, a kan abokan gābansa, zai rama, da kuma a kan ƙasashen da suke a bakin gāɓa. 19 Saboda haka waɗanda suke yamma za su ji tsoron sunan Ubangiji, waɗanda suke wajen gabas kuma za su ji tsoron ɗaukakarsa, gama zai zo kamar rafi mai tsananin gudu, wanda iskar Ubangiji take korawa. 20 Zai zo Sihiyona ya zama mai fansa ga waɗanda suke na Yakubu, su da suka juya suka bar mugunta. 21 Ubangiji ya ce, “Amma ni, wannan shi ne alkawarina da su, Ruhuna da yake tare da ku, da kalmomina da na sa a bakunanku, ba za su rabu da bakunanku ba, ko daga bakunan 'ya'yanku, ko na jikokinku, tun daga wannan lokaci har abada.”

Ishaya 60

Darajar Urushalima a Gaba

1 Ki tashi, ya Urushalima, ki haskaka kamar rana, Daukakar Ubangiji tana haskakawa a kanki kamar rana! 2 Duhu zai rufe sauran al'umma, Amma hasken Ubangiji zai haskaka a kanki, Daukakarsa za ta kasance tare da ke! 3 Za a jawo al'ummai zuwa ga haskenki, Sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki. 4 Ki duba kewaye da ke, ki ga abin da yake faruwa, Mutanenki suna ta tattaruwa domin su komo gida! 'Ya'yanki maza za su taho daga nesa, Za a ɗauki 'ya'yanki mata kamar yara. 5 Za ki ga wannan, ki cika da farin ciki, Za ki yi rawar jiki saboda jin daɗi. Za a kawo miki dukiyar al'ummai, Wato waɗanda suke a ƙasashen hayi. 6 Babban ayarin raƙuma zai zo daga Madayana da Efa. Za su zo daga Sheba, su kawo zinariya da kayan ƙanshi. Mutane za su ba da labari mai daɗi a kan abin da Allah ya yi! 7 Dukan tumaki na Kedar da Nebayot, Za a kawo miki su hadaya, A kuwa miƙa su a kan bagade domin Ubangiji ya ji daɗi. Ubangiji zai darajanta Haikalinsa fiye da dā. 8 Waɗannan jiragen ruwa fa? Suna tafe kamar gizagizai, Kamar kurciyoyi suna komowa gida. 9 Jiragen ruwa ne suke zuwa daga manisantan ƙasashe, Suna kawo mutanen Allah gida. Suna tafe da azurfa da zinariya, Domin su girmama sunan Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila, Wanda ya sa dukan al'ummai su girmama mutanensa. 10 Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Baƙi ne za su sāke gina garukanki, Sarakunansu kuma za su bauta miki. Na hukunta ki da fushina, Amma yanzu zan nuna miki alheri da jinƙai. 11 Ƙofofinki za su kasance a buɗe dare da rana, Domin sarakunan al'ummai su kawo miki dukiyarsu. 12 Amma al'umman da ba su bauta miki ba, Za a hallakar da su. 13 “Itatuwan fir da irinsu Mafi kyau daga jejin Lebanon, Za a kawo su domin a sāke gina ki, ke Urushalima, Domin a ƙawata Haikalina, A darajanta birnina. 14 'Ya'ya maza na waɗanda suka zalunce ki za su zo, Su rusuna, su nuna bangirma. Dukan waɗanda suka raina ki za su yi sujada a ƙafafunki. Za su ce da ke, ‘Birnin Ubangiji,’ ‘Sihiyona, Birni na Allah Mai Tsarki na Isra'ila.’ 15 “Ba za a ƙara ƙinki, a yashe ki ba, Ki zama birnin da aka fita aka bari ba kowa ciki. Zan sa ki zama babba, mai ƙayatarwa kuma, Wurin yin farin ciki har abada abadin. 16 Al'ummai da sarakuna za su lura da ke Kamar yadda uwa take lura da ɗanta. Za ki sani, ni Ubangiji, na cece ki, Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila ya fanshe ki. 17 “Zan kawo miki zinariya maimakon tagulla, Azurfa maimakon baƙin ƙarfe, Tagulla kuma maimakon itace. Za ki sami baƙin ƙarfe maimakon dutse. Masu mulkinki ba za ƙara zaluntarki ba, Zan sa su yi mulki da gaskiya da salama. 18 Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali ba, Ba za a ƙara aukar wa ƙasar da ɓarna ba. Zan kiyaye ki, in kāre ki kamar garu, Za ki yi yabona domin na cece ki. 19 “Rana ba za ta ƙara zama haskenki da rana ba, Ko wata ya zama haskenki da dare. Ni, Ubangiji, zan zama madawwamin haskenki, Hasken ɗaukakata zai haskaka a kanki. 20 Kwanakin baƙin cikinki za su ƙare. Ni, Ubangiji, zan zama madawwamin haskenki, Mai daɗewa fiye da na rana da na wata. 21 Dukan mutanenki za su yi abin da yake daidai, Za su kuwa mallaki ƙasar har abada. Ni na dasa su, ni na yi su Domin su bayyana girmana ga duka. 22 Har ma da iyalin da suka fi ƙanƙanta da ƙasƙanci, Za su zama babbar al'umma, Kamar al'umma mai iko. Zan sa wannan ya faru nan da nan Sa'ad da lokacin da ya dace ya yi. Ni ne Ubangiji!”

Ishaya 61

Albishirin Ceto ga Sihiyona

1 Ubangiji ya saukar mini da ikonsa. Ya zaɓe ni, ya aike ni Domin in kawo albishir mai daɗi ga talakawa, In warkar da waɗanda suka karai a zuci, In yi shelar kwance ɗaurarru, Da kuma 'yanci ga waɗanda suke cikin kurkuku. 2 Ya aike ni in yi shela, Cewa lokaci ya yi Da Ubangiji zai ceci mutanensa, Ya kuma ci nasara a kan abokan gābansu. Ya aike ni domin in ta'azantar da masu makoki, 3 Domin in kawo wa masu makoki a Sihiyona Farin ciki da murna maimakon baƙin ciki, Waƙar yabo maimakon ɓacin rai. Ubangiji kansa zai lura da su, Za su ji daɗi kamar itace mai duhuwa. Kowa da kowa zai aikata abin da yake daidai, Za a yi yabon Allah saboda abin da ya yi. 4 Za su sāke gina biranen da suke a rurrushe tun da daɗewa. 5 Ya Urushalima, baƙi za su bauta miki, Za su lura da garkunanki, Za su nome gonakinki, su gyara gonakinki na inabi. 6 Amma za a sani, ku firistoci ne na Ubangiji, Za ku mori dukiyar al'ummai, Za ku yi fāriya da cewa, taku ce. 7 Kunyarku da shan wulakancinku za su ƙare. Za ku zauna a ƙasarku, Za a riɓanya dukiyarku, Za ku yi ta farin ciki har abada. 8 Ubangiji ya ce, “Ina ƙaunar aikin gaskiya, Amma ina ƙin zalunci da aikata laifi. Da aminci zan ba mutanena lada, In yi madawwamin alkawari, da su. 9 Za su yi suna a cikin al'ummai, Dukan wanda ya gan su zai sani, Su ne mutanen da na sa wa albarka.” 10 Urushalima tana murna saboda abin da Ubangiji ya yi. Tana kama da amaryar da ta sha ado a ranar aurenta. Allah ya suturce ta da ceto da nasara. 11 Ba shakka, Ubangiji zai ceci jama'arsa, Kamar yadda iri yakan tsiro ya yi girma. Dukan al'ummai kuwa za su yi yabonsa.

Ishaya 62

1 Zan yi magana domin in ƙarfafa Urushalima, Ba zan yi shiru ba, Sai na ga adalcinta ya bayyana kamar haske, Cetonta kuma ya haskaka kamar fitila da dare. 2 Ya Urushalima, al'ummai za su ganki mai gaskiya! Dukan sarakunansu za su ga darajarki. Za a kira ki da sabon suna, Sunan da Ubangiji ya bayar da kansa. 3 Za ki zama kamar kyakkyawan rawani ga Ubangiji, Wato kambin sarauta mai daraja gare shi. 4 Ba za a ƙara ce da ke, “Yasasshiya” ba, Ko a ce da ƙasarki, “Mata wadda Mijinta ya Rabu da Ita.” Sabon sunanki yanzu shi ne, “Wadda Allah ya Yarda da Ita.” Ƙasarki kuwa za a ce da ita, “Ta yi Aure da Farin Ciki,” Domin Ubangiji ya ji daɗinki, Zai kuwa zama kamar miji ga ƙasarki. 5 Ubangiji zai ɗauke ki amaryarsa, Za ku yi murna tare, Kamar murnar amarya da ango. 6 Ya Urushalima, na sa matsara a garukanki Ba za su taɓa yin shiru ba, dare da rana. Za su tuna wa Ubangiji da alkawaransa, Ba kuwa za su bari ya manta ba! 7 Ba za su bari ya huta ba, sai ya ceci Urushalima tukuna, Ya sa ta zama birnin da dukan duniya za ta yaba wa. 8 Ubangiji ya yi alkawari mai ƙarfi, Ta wurin ikonsa kuwa zai cika shi. “Hatsinku ba zai ƙara zama abincin abokan gābanku ba, Baƙi ba za su ƙara shanye ruwan inabinku ba. 9 Amma ku da kuka shuka hatsin kuka kuma girbe shi, Za ku ci abinci, ku yi yabon Ubangiji! Ku da kuka lura da itatuwan inabi kuka tara su, Za ku sha ruwan inabi a filayen Haikalina.” 10 Ku mutanen Urushalima, ku fita daga cikin birni, Ku gyara hanyoyi domin jama'arku da suke komowa! Ku shirya babbar hanya, Ku kawar da duwatsu daga hanyar! Ku sa alama domin al'ummai su sani, 11 Ubangiji yana sanarwa ga dukan duniya, Cewa, “Ku ce wa jama'ar Urushalima, Ubangiji Mai Cetonku yana zuwa, Yana kawo mutanen da ya cece su.” 12 Za a ce da ku, “Tsattsarkar Jama'ar Allah,” “Jama'ar da Ubangiji ya Fansa!” Za a kira Urushalima, “Birnin da Allah yake Ƙauna,” “Birnin da Allah bai Yashe shi Ba.”

Ishaya 63

Ranar Ramawa ta Ubangiji

1 Wane ne wannan da yake zuwa daga Bozara cikin Edom? Wane ne wannan da ya sha ado da jajayen kaya, yana tafe, ga shi kuwa ƙaƙƙarfa? Ubangiji ne, mai ikon yin ceto, yana zuwa ya yi sanarwar nasara. 2 Me ya sa tufafinsa suke da ja haka, kamar na mutumin da ya tattake 'ya'yan inabi domin ya sami ruwan inabi? 3 Ubangiji ya amsa ya ce, “Na tattake al'ummai kamar 'ya'yan inabi, ba kuwa wanda ya taimake ni. Na tattake su cikin fushina, jininsu kuwa ya fantsamar wa dukan tufafina. 4 Na ga lokacin da zan fanshi mutanena ya yi, lokaci ne da zan hukunta wa abokan gābansu. 5 Na yi mamaki sa'ad da na duba, sai na ga ba wanda zai taimake ni. Amma fushina ya sa na sami ƙarfi, har ni kaina na ci nasara. 6 Da fushina na tattake dukan sauran al'umma, na farfashe su. Na kwararar da jinin ransu a ƙasa.”

Alherin Ubangiji ga Isra'ila

7 Zan faɗi ƙaunar Ubangiji marar ƙarewa, Zan yabe shi saboda dukan abin da ya yi mana. Ya sa wa jama'ar Isra'ila albarka mai yawa, Saboda jinƙansa da ƙaunarsa marar matuƙa. 8 Ubangiji ya ce, “Su mutanena ne, ba za su ruɗe ni ba.” Saboda haka kuwa ya cece su 9 daga dukan wahalar da suke sha. Ba mala'ika ne ya cece su ba, amma Ubangiji ne. Da ƙaunarsa da juyayinsa ya fanshe su. A koyaushe yake lura da su a dā, 10 amma suka i masa tayarwa, suka cika shi da ɓacin rai. Saboda haka Ubangiji ya yi gāba da su, ya kuwa yi yaƙi da su. 11 Amma suka tuna da zamanin dā, zamanin Musa bawan Ubangiji, suka yi tambaya suka ce, “Yanzu fa, ina Ubangiji yake wanda ya ceci shugabannin jama'arsa daga teku? Ina Ubangiji yake, wanda ya ba Musa iko musamman? 12 Ina Ubangiji yake wanda ya yi manyan al'amura da ikonsa ta wurin Musa, ya raba ruwan teku a gaban jama'arsa, domin ya yi wa kansa madawwamin suna?” 13 Sa'ad da Ubangiji ya bi da su ta ruwa mai zurfi, suka taka kamar ingarmun dawakai, ba su ko yi tuntuɓe ba. 14 Kamar yadda ake bi da shanu cikin kwari mai dausayi, haka Ubangiji ya ba mutanensa hutawa. Haka kuma Ubangiji ya bi da mutanensa, ya kuwa kawo ɗaukaka ga sunansa.

Addu'ar Neman Jinƙai da Taimako

15 Ya Ubangiji, ka dube mu daga Sama, wurin da kake cike da tsarki da ɗaukaka. Ina kulawan nan da kake yi mana? Ina ikon nan naka? Ina ƙaunan nan taka da juyayin nan naka? Kada ka watsar da mu. 16 Kai ne Ubanmu. Ko kakanninmu, wato su Ibrahim da Yakubu, ba za su iya taimakonmu ba, amma kai, ya Ubangiji, kai ne Ubanmu. Kai ne Mai Fansarmu a koyaushe. 17 Don me ka bari muka ɓata daga al'amuranka? Don me ka bari muka taurare, har muka bar binka? Ka komo, domin darajar waɗanda suke bauta maka, domin kuma mutanen da suke naka ne a koyaushe. 18 Abokan gabanmu sun kusa su kori mutanenka gaba ɗaya sun kuma tattake Haikalinka. 19 Mun zama kamar ba ka taɓa zama mai mulkinmu ba, kamar mu kuma ba mu taɓa zama mutanenka ba.

Ishaya 64

1 Don me ba za ka kware sararin sama, ka sauko ba? Duwatsu za su gan ka, su girgiza saboda tsoro! 2 Za su karkaɗu kamar ruwan da yake tafasa a wuta. Ka zo ka bayyana ikonka a kan abokan gābanka, ka sa al'ummai su yi rawar jiki a gabanka. 3 Ka taɓa zuwa ka yi abubuwan banrazana waɗanda ba mu sa tsammani ba, duwatsu suka ganka suka kaɗu domin tsoro. 4 Ba wanda ya taɓa gani ko jin labarin wani Allah kamarka, wanda ya yi waɗannan ayyuka ga waɗanda suka sa zuciyarsu gare shi. 5 Ka amince da waɗanda suke murna su aikata abin yake daidai, su waɗanda suka tuna da yadda kake so su yi zamansu. Ka yi fushi da mu, amma muka ci gaba da yin zunubi, har da fushin da ka yi ƙwarai, muka ci gaba da aikata abin da ba daidai ba, tun daga zamanan dā. 6 Dukanmu muka cika da zunubi har ayyukanmu mafi kyau ƙazamai ne duka. Saboda zunubanmu, muka zama kamar busassun ganyaye waɗanda iska take faucewa ta tafi da su. 7 Ba wanda ya juyo gare ka ya yi addu'a, ba wanda ya je gare ka neman taimako. Ka ɓuya mana, ka kuwa yashe mu saboda zunubanmu. 8 Amma kai ne Ubanmu, ya Ubangiji. Mu kamar yumɓu ne, kai kuwa kamar maginin tukwane. Kai ka halicce mu, 9 saboda haka kada ka yi fushi da mu ainun, ko ka riƙe da zunubanmu har abada, mu dai mutanenka ne, ka yi mana jinƙai. 10 Keɓaɓɓun biranenka suna kama da hamada, aka kuma ƙaurace wa kufan Urushalima. 11 Haikalinmu, kyakkyawan keɓaɓɓen wuri inda kakanninmu suka yi yabonka, aka lalatar da shi da wuta, dukan wuraren da muka ƙauna aka lalatar da su. 12 Ya Ubangiji, dukan wannan bai sa ka yi wani abu ba? Ba za ka yi kome ba, kana kuwa sa mu yi ta shan wuya, har fiye da yadda muke iya daurewa?

Ishaya 65

Hukuncin Allah a kan Masu Tawaye

1 Ubangiji ya ce, “Na shirya in amsa addu'o'in mutanena, amma ba su yi addu'a ba. Na yi shiri domin su same ni, amma ba su ko yi ƙoƙarin nemana ba. Al'ummar ba ta yi addu'a a gare ni ba, ko da yake a koyaushe ina a shirye domin in amsa cewa, ‘Ga ni nan, zan taimake ku.’ 2 Kullum ina a shirye domin in marabci waɗannan mutane, waɗanda saboda taurinkansu suka yi ta aikata abin da ba daidai ba, suka bi hanyoyin kansu. 3 Suka yi ta ƙara sa ni fushi ta wurin rashin kunyarsu. Suka miƙa hadayu irin na arna a ɗakunan tsafi da suke a lambu, suka kuma ƙona turare a kan bagadan arna. 4 Da dare sukan tafi cikin kogwanni da kaburbura, suna neman shawarar kurwar matattu. Waɗannan mutane sukan ci naman alade, su kuma sha romon naman da aka miƙa hadaya irin ta arna. 5 Sa'an nan su riƙa ce wa sauran mutane, ‘Ku yi nesa da mu gama muna da tsarki da yawa, har da ba za mu taɓa ku ba.’ Ba zan daure da irin waɗannan mutane ba, fushina a kansu kamar wuta ce wadda ba za ta taɓa mutuwa ba. 6 “Na riga na ƙudura hukuncinsu, shari'ar da aka yanke kuwa an rubuta ta. Ba zan ƙyale abin da suka aikata ba, amma zan sāka musu 7 saboda zunubansu da zunuban kakanninsu. Gama suka ƙona turare a ɗakunan tsafin arna na kan tuddai, suka kuwa faɗi mugun abu a kaina. Saboda haka zan hukunta su yadda ya cancance su.” 8 Ubangiji ya ce, “Ba wanda ya lalatar da 'ya'yan inabi, maimakon haka sai suka yi ruwan inabi da su. Ni kuwa ba zan hallakar da dukan mutanena ba, zan ceci waɗanda suke bauta mini. 9 Zan sa wa Isra'ilawa waɗanda suke na kabilar Yahuza albarka, zuriyarsu kuma za su mallaki ƙasata da duwatsuna. Zaɓaɓɓun mutanena waɗanda suke bauta mini za su zauna a can. 10 Za su yi mini sujada, za su kai tumakinsu da shanunsu wurin kiwo a kwarin Sharon a wajen yamma, da kuma a kwarin Akor a wajen gabas. 11 “Amma ba haka zai zama ba, ga ku da kuka rabu da ni, ku waɗanda kuka yi watsi da Sihiyona, tsattsarkan dutsena, kuka yi sujada ga Gad da Meni, wato allolin sa'a da na ƙaddara. 12 Mutuwa ta ƙarfi da yaji za ku yi, gama sa'ad da na yi kiranku ba ku amsa ba, ba ku kasa kunne ba kuwa sa'ad da nake magana da ku. Kuka zaɓa ku yi mini rashin biyayya, ku kuma aikata mugunta. 13 Saboda haka ina faɗa muku, cewa su waɗanda suke yin sujada gare ni suna kuwa yi mini biyayya, za su sami wadataccen abinci da abin sha, amma ku za ku sha yunwa da ƙishi. Su za su yi murna, amma ku za ku sha kunya. 14 Za su raira waƙa don farin ciki, amma ku za ku yi kuka da karayar zuci. 15 Zaɓaɓɓun mutane ne za su mori sunayenku wajen la'antarwa. Ni, Ubangiji, zan kashe ku. Amma zan ba da sabon suna ga waɗanda suke yi mini biyayya. 16 Dukan wanda yake so ya roƙi albarka, sai ya roƙi Allah ya sa masa albarka, Allah da yake mai aminci ne. Dukan wanda zai sha rantsuwa, sai ya rantse da sunan Allah, Allah da yake mai aminci ne. Wahalan dā za su ƙare, za a kuwa manta da su.”

Sabuwar Sama da Sabuwar Duniya

17 Ubangiji ya ce, “Ina yin sabuwar duniya da sabon sararin sama. Abubuwa na dā za a manta da su ɗungum. 18 Ku yi murna da farin ciki a kan abin da na halitta. Sabuwar Urushalima da nake halittawa za ta cika da murna, jama'arta kuma za su yi farin ciki. 19 Ni kaina kuma zan cika da murna saboda Urushalima da jama'arta. Ba kuka a can, ba bukatar neman taimako. 20 Jarirai ba za su mutu tun suna jarirai ba, ko wanne zai cika yawan kwanakinsa kafin ya mutu. Waɗanda suke masu shekara ɗari da haihuwa su ne samari. Waɗanda suka mutu kafin wannan lokaci, to, alama ce, ta cewa na hukunta su. za su gina gidaje su kuwa zauna a cikinsu, ba waɗansu dabam za su mori gidajen ba. Za su dasa gonakin inabi su kuwa ji daɗin ruwan inabi, ba waɗansu dabam za su sha shi ba. Mutanena za su yi tsawon rai kamar itatuwa. Za su ci cikakkiyar moriyar abubuwan da suka yi aikinsu. 23 Aikin da suka yi zai yi nasara, 'ya'yansu ba za su gamu da bala'i ba, zan sa musu albarka duk da zuriyarsu har dukan zamanai. 24 Zan amsa addu'o'insu tun ma kafin su gama yin addu'a gare ni. 25 Kyarketai da 'yan raguna za su ci abinci tare, zaki kuma zai ci budu kamar yadda shanu suke yi. Maciji ba zai ƙara zama abu mai hatsari ba. A kan Sihiyona tsattsarkan dutsena, ba za a sami wani abu da zai cutar ba, ko wani mugun abu.”

Ishaya 66

Hukuncin Ubangiji da Wadatar Sihiyona

1 Ubangiji ya ce, “Sama kursiyina ce, duniya kuwa matashin sawuna ce. Daganan wane irin gida za ku iya ginawa domina, wane irin wuri ne kuma zan zauna? 2 Ni kaina na halicci dukan kome ka kome! Ina jin daɗin waɗanda suke da tawali'u, da kuma masu tuba, waɗanda suke tsorona suna kuwa biyayya gare ni. 3 “Mutane suna yin abin da suka ga dama. Suna kashe bijimi domin hadaya, ko su yi hadaya da mutum. Sukan yi hadaya da ɗan rago, ko kuwa su karye wuyan kare. Sukan miƙa hadaya ta hatsi, ko kuwa su miƙa jinin alade. Suna miƙa turare, ko kuwa su yi addu'a ga gumaka. Suna jin daɗin al'amuran banƙyama a lokacin yin sujada. 4 Saboda haka zan aukar musu da masifa, ainihin abin da suke jin tsoro, gama ba wanda ya amsa sa'ad da na yi kira, ko ya kasa kunne sa'ad da na yi magana. Suka zaɓa su yi mini rashin biyayya, su kuma aikata mugunta.” 5 Ku kasa kunne ga abin da Ubangiji yake faɗa, ku da kuke tsoronsa gama ya ce, “Domin kuna da aminci gare ni, waɗansu daga 'yan'uwanku suka ƙi ku, har ba su da hulɗar kome da ku. Suna yi muku ba'a suna cewa, ‘Muna so mu ga kuna murna, saboda haka bari a ɗaukaka Ubangiji.’ Amma su za su sha kunya! 6 Ku kasa kunne! Waccan babbar hayaniya cikin birni, wancan amo a Haikali, amon Ubangiji ne da yake hukunta abokan gābansa! 7 “Tsattsarkan birnina yana kama da uwa wadda ta haifi ɗa, ba tare da naƙuda ba. 8 Ko akwai wanda ya taɓa gani ko ya ji labari irin wannan abu? Ko an taɓa haihuwar al'umma rana ɗaya? Sihiyona ba za ta sha wahala ba kafin a haifi al'umma. 9 Kada ku zaci zan kawo jama'ata a wurin haihuwa in kuma hana ta haihuwa.” Ubangiji ne ya faɗa. 10 Ku yi murna tare da Urushalima Ku yi farin ciki tare da ita, Dukanku da kuke ƙaunar birnin nan! Ku yi murna tare da ita yanzu, Dukanku da kuka yi makoki dominta! 11 Za ku ji daɗin wadatarta, Kamar yaro a ƙirjin mamarsa. 12 Ubangiji ya ce, “Zan kawo muku wadata madawwamiya, dukiyar al'ummai za ta malalo zuwa gare ku kamar kogi wanda ba ya ƙafewa. Za ku zama kamar yaro wanda mahaifiyarsa take renonsa, tana rungume da shi da ƙauna. 13 Zan ta'azantar da ku a Urushalima, kamar yadda uwa take ta'azantar da ɗanta. 14 Sa'ad da kuka ga wannan ya faru, za ku yi murna, wannan zai ba ku ƙarfi da lafiya. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji, mai taimakon masu biyayya gare ni, ina kuwa nuna fushina a kan abokan gābana.” 15 Ubangiji zai zo da wuta. Zai hau a kan fikafikan hadiri, domin ya hukunta waɗanda yake fushi da su. 16 Zai hukunta dukan mutanen duniya da wuta da takobi, waɗanda ya same su da laifi, za su kuwa mutu. 17 Ubangiji ya ce, “Ƙarshe ya kusa ga waɗanda suka tsabtace kansu domin sujadar arna, suka kuma yi jerin gwano zuwa ɗakin tsafi a lambu, inda suka ci naman alade da na ɓera, da waɗansu abinci masu banƙyama. 18 Na san tunaninsu da ayyukansu. Ina zuwa domin in tattara jama'ar dukan al'ummai. Sa'ad da suka tattaru, za su ga abin da ikona zai yi, 19 su kuwa sani ni ne wanda yake hukunta musu. “Amma zan bar waɗansu, in aika da su ga al'ummai da manisantan ƙasashe inda ba a ji labarin sunan da na yi ba, ba a kuwa ga girmana da ikona ba, wato zuwa Tarshish, da Libiya, da Lidiya, duk da gwanayen maharbanta, Rosh da Tubal, da kuma Helas. Za su ba da labarin girmana ga waɗannan al'ummai. 20 Za su taho da 'yan ƙasarku daga al'ummai, su kawo mini su kyauta. Za su zo da su a tsattsarkan dutsena, wato Urushalima, za su kawo su a kan dawakai, da alfadarai, da raƙuma, da cikin karusai, kamar dai yadda Isra'ilawa suke kawo hadaya ta hatsi a Haikali cikin tsabtatattun ƙore. 21 Zan sa waɗansu su zama firistoci da Lawiyawa.” 22 Ubangiji ya ce, “Kamar yadda sabuwar duniya da sabon sararin sama za su tabbata ta wurin ikona, haka zuriyarku da sunanku za su tabbata. 23 A kowane bikin amaryar wata, da kowace ranar Asabar, jama'ar kowace al'umma za su zo su yi mini sujada a nan cikin Urushalima. 24 Sa'ad da suke tafiya, za su ga gawawwakin mutanen da suka yi mini tayarwa. Tsutsotsin da suke cinsu ba za su taɓa mutuwa ba, wutar da take ƙona su kuma ba za ta taɓa mutuwa ba. Dukan mutane za su ji ƙyamarsu.”

Irmiya 1

Kiran Irmiya da Keɓewarsa

1 Maganar Irmiya ɗan Hilkiya ke nan, na cikin firistocin da suke a Anatot, a yankin ƙasar Biliyaminu, 2 wanda Ubangiji ya yi masa magana a zamanin Yosiya ɗan Amon, Sarkin Yahuza, a shekara ta goma sha uku ta mulkinsa, 3 da a zamanin Yehoyakim ɗan Yosiya Sarkin Yahuza kuma, har ƙarshen shekara ta goma sha ɗaya ta Zadakiya ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, har zuwa lokacin da aka kai mazaunan Urushalima zaman talala a wata na biyar. 4 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 5 “Na san ka tun kafin a yi cikinka, Na keɓe ka tun kafin a haife ka, Na sa ka ka zama annabi ga al'ummai.” 6 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah! Ban san abin da zan faɗa ba, Gama ni yaro ne.” 7 Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce kai yaro ne, Kai dai ka tafi wurin mutanen da zan aike ka, 8 Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai, Zan kiyaye ka. Ni Ubangiji na faɗa.” 9 Sa'an nan Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina, ya ce mini, “Ga shi, na sa maganata a bakinka. 10 Ga shi, a wannan rana na ba ka iko a kan al'ummai da mulkoki, Don ka tumɓuke, ka rusar, Ka hallakar, ka kaɓantar, Ka gina, ka dasa.” 11 Sai Ubangiji ya tambaye ni, ya ce, “Irmiya, me ka gani?” Na amsa, na ce, “Sandan itacen almond.” 12 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Ka gani sosai, gama zan lura da maganata don in cika ta.” 13 Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce, “Me kuma ka gani?” Na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, daga wajen arewa kamar za ta jirkice wajen kudu.” 14 Sai Ubangiji ya ce mini, “Daga wajen arewa masifa za ta fito ta auka wa dukan mazaunan ƙasar. 15 Ga shi kuwa, ina kiran dukan kabilan mulkokin arewa, za su kuwa zo su kafa gadajen sarautarsu a ƙofofin Urushalima, su kewaye dukan garukanta da dukan sauran biranen Yahuza. 16 Zan hurta hukuncin da zan yi musu saboda dukan muguntarsu, da suka bar bina, suka ƙona turare ga gumaka, suka kuma bauta wa gumakan da suka yi. 17 Amma kai, ka tashi ka sha ɗamara, ka faɗa musu dukan abin da na umarce ka. Kada ka ji tsoronsu domin kada in tsoratar da kai a gabansu. 18 Ni kuwa, ga shi, yau na maishe ka birni mai kagara, da ginshiƙin ƙarfe, da bangon tagulla ga dukan ƙasar, da sarakunan Yahuza, da shugabanninta, da firistocinta, da mutanen ƙasar. 19 Za su yi gāba da kai, amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, ni Ubangiji na faɗa.”

Irmiya 2

Ubangiji ya Ji da Isra'ila da Masu Ridda

1 Ubangiji ya ce mini, 2 in tafi in yi shelar abin da Ubangiji ya ce a kunnen Urushalima, in ce, “Na tuna da amincinki a lokacin ƙuruciyarki, Da ƙaunarki kamar ta amarya da ango. Yadda kika bi ni a cikin jeji, da a ƙasar da ba a shuka ba. 3 Isra'ila tsattsarka ce ta Ubangiji, Nunar fari ta girbina. Dukan waɗanda suka ci daga cikinki sun yi laifi, Masifa za ta auko miki. Ni Ubangiji, na faɗa.” 4 Ku ji jawabin Ubangiji, ku zuriyar Yakubu, ku dukan kabilan Isra'ila. 5 Ubangiji ya ce, “Wane laifi ne na yi wa kakanninku, Da suka bar bina? Suka bauta wa gumaka marasa amfani, Su kuma suka zama marasa amfani. 6 Ba su kula da ni ba, Ko da yake na cece su daga ƙasar Masar. Na bi da su a cikin hamada, A ƙasa mai tuddai da kwazazzabai, Busasshiya mai yawan hatsari, Ba a bi ta cikinta, Ba wanda yake zama cikinta kuma. 7 Na kawo su zuwa ƙasa mai dausayi, Don su more ta su ci amfaninta, Amma da suka shiga, sun ƙazantar mini da ita, Suka sa ƙasar da na gādar musu ta zama abar ƙyama. 8 Firistoci kuma ba su ce, ‘Ina Ubangiji Yake ba?’ Masanan shari'a ba su san ni ba. Masu mulki sun yi mini laifi, Annabawa sun yi annabci da sunan Ba'al, Sun bi waɗansu abubuwa marasa amfani.”

Shari'ar da Ubangiji yake Yi wa Mutanensa

9 “Domin haka, ni Ubangiji zan gabatar da ku gaban shari'a, Ku da 'ya'yanku, da 'ya'yan 'ya'yanku, wato jikokinku. 10 Ku haye zuwa tsibirin Kittim wajen yamma, ku gani, Ku aika zuwa Kedar wajen gabas, ku duba da kyau, A dā an taɓa yin wani abu haka? 11 Akwai wata al'umma da ta taɓa sāke gumakanta Ko da yake su ba kome ba ne? Amma mutanena sun sauya darajarsu da abin da ba shi da rai. 12 Sammai, ku girgiza saboda wannan, ku razana, Ku yi shiru, ni Ubangiji na faɗa. 13 Mutanena sun yi zunubi iri biyu, Sun rabu da ni, ni da nake maɓuɓɓugar ruwan rai, Sun haƙa wa kansu tafkunan ruwa, hudaddu, Waɗanda ba za su iya ajiye ruwa ba. 14 “Isra'ila ba bawa ba ne, ba a kuma haife shi bawa ba, Amma me ya sa ya zama ganima? 15 Zakuna suna ruri a kansa, Suna ruri da babbar murya. Sun lalatar da ƙasarsa, Garuruwansa sun lalace, Ba wanda yake zaune cikinsu. 16 Mutanen Memfis kuma da na Tafanes sun fasa ƙoƙwan kansa. 17 Ya Isra'ila, kai ne ka jawo wa kanka wannan, Da ka rabu da Ubangiji Allahnka, Sa'ad da ya bishe ka a hanya. 18 Wace riba ka samu, har da ka tafi Masar, Don ka sha ruwan Kogin Nilu? Wace riba ka samu, har da ka tafi Assuriya, Don ka sha ruwan Kogin Yufiretis? 19 Muguntarka za ta hore ka, Riddarka kuma za ta hukunta ka. Sa'an nan za ka sani, ka kuma gane, Ashe, mugun abu ne, mai ɗaci, a gare ka Ka rabu da Ubangiji Allahnka, Ba ka tsorona a zuciyarka. Ni Ubangiji, Allah Mai Runduna na faɗa.”

Isra'ila ya Ƙi yi wa Ubangiji Biyayya

20 “Ya Isra'ila, tun da daɗewa, ka ƙi yarda Ubangiji ya mallake ka, Ka ƙi yin biyayya da ni, Ka kuwa ce, ‘Ba zan yi bauta ba.’ Amma ka yi karuwanci a kan kowane tudu, Da kowane ɗanyen itace. 21 Na dasa ka kamar zaɓaɓɓiyar kurangar inabi, zaɓaɓɓen iri mafi kyau. Ta yaya ka lalace haka ka zama rassan kurangar inabi ta jeji, Waɗanda ba zan yarda da su ba? 22 Ko da za ka yi wanka da sabulun salo, Ka yi amfani da sabulu mai yawa, Duk da haka zan ga tabban zunubanka. Ni Ubangiji Allah na faɗa. 23 Ƙaƙa za ka ce ba ka ƙazantar da kanka ba, Ba ka taɓa bin gunkin nan Ba'al ba? Ka duba hanyarka ta zuwa cikin kwari, ka san abin da ka yi. Kana kama da taguwa, mai yawon neman barbara. 24 Kamar jakar jeji kake, wadda take son barbara, Wadda take busar iska, Sa'ad da take son barbara, wa zai iya hana ta? Jakin da yake sonta, ba ya bukatar wahalar da kansa Gama a watan barbararta za a same ta. 25 Kai Isra'ila, kada ka bar ƙafafunka ba takalma, Kada kuma ka bar maƙogwaronka ya bushe. Amma ka ce, ‘Wannan ba amfani, Gama na ƙaunaci baƙi, su kuwa zan bi.’ 26 “Kamar yadda ɓarawo yakan sha kunya sa'ad da aka kama shi, Hakanan mutanen Isra'ila za su sha kunya, Da su, da sarakunansu, da shugabanninsu, Da firistocinsu, da annabawansu. 27 Waɗanda suka ce wa itace, ‘Kai ne mahaifinmu.’ Suna kuma ce wa dutse, ‘Kai, ka haife mu.’ Gama sun ba ni baya, ba su fuskance ni ba. Amma sa'ad da suke shan wahala, sukan ce, ‘Ka zo ka taimake mu.’ 28 Ina gumakan da kuka yi wa kanku? Bari su tashi in sun iya cetonku lokacin wahalarku. Yahuza, yawan gumakanku sun kai Yawan garuruwanku. 29 Ni Ubangiji, ina tambayarku, ‘Wace ƙara kuke da ita game da ni?’ Kun yi mini tawaye dukanku. 30 Na hori 'ya'yanku, amma a banza, ba su horu ba, Kun kashe annabawanku da takobi kamar mayunwacin zaki. 31 Ya ku mutanen zamanin nan, ku saurari maganata. Na zamar wa Isra'ila jeji? Ko ƙasar da take da kurama? Don me fa mutanena suke cewa, ‘Mu 'yantattu ne, Ba za mu ƙara zuwa wurinka ba?’ 32 Budurwa ta manta da kayan kwalliyarta? Ko kuwa amarya ta manta da kayan adonta? Amma mutanena sun manta da ni kwanaki ba iyaka. 33 Kun sani sarai yadda za ku yi ku farauci masoya, Har mugayen mata ma, kun koya musu hanyoyinku. 34 Tufafinku sun ƙasantu da jinin marasa laifi, Waɗanda ba ku same su suna fasa gidajenku ba. Amma duk da haka kuna cewa, 35 ‘Ba mu da laifi, hakika kuwa, Ubangiji bai yi fushi da mu ba.’ Amma ni Ubangiji zan hukunta ku, Domin kun ce ba ku yi zunubi ba. 36 Me ya sa ba ku da tsayayyiyar zuciya, Sai ku yi nan ku yi can? Masar za ta kunyata ku kamar yadda Assuriya ta yi. 37 Da hannuwanku a kā za ku komo daga Masar don kunya. Gama waɗanda kuke dogara gare su, ni Ubangiji, na ƙi su, Ba za ku yi arziki tare da su ba.”

Irmiya 3

1 Ubangiji ya ce, “Idan mutum ya saki matarsa, Ta kuwa rabu da shi, har ta auri wani, Ya iya ya komo da ita? Ashe, yin haka ba zai ƙazantar da ƙasar ba? Ya Isra'ila, kin yi karuwanci, Abokan sha'anin karuwancinki, suna da yawa. Za ki sāke komowa wurina? Ni, Ubangiji, na faɗa. 2 Ki ta da idonki, ki duba filayen tuddai ki gani, Akwai wurin da ba ki laɓe kin yi karuwanci ba? Kin yi ta jiran abokan sha'anin karuwancinki a kan hanya, Kamar Balaraben da ke fako a hamada. Kin ƙazantar da ƙasar da mugun karuwancinki. 3 Saboda haka aka ƙi yin ruwa, Ruwan bazara bai samu ba. Goshinki irin na karuwa ne, ba ki jin kunya. 4 “Yanzu kin ce, ‘Kai ne mahaifina, Ka ƙaunace ni tun ina cikin ƙuruciyata. 5 Za ka dinga yin fushi da ni? Za ka husata da ni har abada?’ Ga shi, ke kika faɗa, amma ga shi, kin aikata dukan muguntar da kika iya yi.”

Dole Isra'ila da Yahuza su Tuba

6 A zamanin sarki Yosiya, Ubangiji ya ce mini, “Ka ga abin da ta yi, ita marar amincin nan, wato Isra'ila? Yadda a kowane tudu mai tsayi, da a gindin kowane itace mai duhuwa, a wurare ne ta yi karuwancinta. 7 Na yi zaton bayan da ta aikata wannan duka, za ta komo wurina. Amma ba ta komo ba, maƙaryaciyar 'yar'uwarta, wato Yahuza, ta gani. 8 Yahuza kuwa ta ga dukan karuwancin da marar amincin nan, Isra'ila ta yi, na sake ta, na ba ta takardar sarki. Amma duk da haka maƙaryaciyar 'yar'uwan nan tata, Yahuza, ba ta ji tsoro ba, amma ita ma ta tafi ta yi karuwanci. 9 Domin karuwanci a wurinta abu ne mai sauƙi, ta ƙazantar da ƙasar. Ta yi karuwanci da duwatsu, da itatuwa. 10 Duk da haka maƙaryaciyar 'yar'uwan nan tata, Yahuza ba ta juyo wurina da zuciya ɗaya ba, sai a munafunce, ni Ubangiji na faɗa.” 11 Ubangiji kuma ya faɗa mini, ko da ya ke Isra'ila ta bar binsa, duk da haka ta nuna laifinta bai kai na Yahuza marar aminci ba. 12 Ya ce mini in tafi wajen arewa in yi shela in ce, “Ki komo ya Isra'ila, marar aminci, Ni Ubangiji, na faɗa. Domin ni mai jinƙai ne, Ba zan yi fushi da ke ba. Ba zan yi fushi da ke har abada ba, Ni, Ubangiji na faɗa. 13 Ke dai ki yarda da laifinki, Da kika yi wa Ubangiji Allahnki, Kin kuma watsar da mutuncinki a wurin baƙi A gindin kowane itace mai duhuwa. Kika ƙi yin biyayya da maganata, Ni, Ubangiji, na faɗa. 14 “Ku komo, ya ku mutane marasa aminci, Gama ni ne Ubangijinku. Zan ɗauki mutum guda daga kowane gari, In ɗauki mutum biyu daga kowane iyali, Zan komo da su zuwa Dutsen Sihiyona. 15 Zan ba ku sarakuna waɗanda suke yi mini biyayya da hikima da fahimi. 16 Sa'ad da kuka yawaita a ƙasar, mutane ba za su ƙara yin magana a kan akwatin alkawari na Ubangiji ba. Ba za su ƙara yin tunaninsa ko su tuna da shi, ko su bukace shi, ko kuwa su yi wani irinsa ba. 17 In lokacin nan ya yi, za a kira Urushalima gadon sarautar Ubangiji, dukan sauran a'umma za su taru a Urushalima da sunana. Ba za su ƙara bin tattaurar zuciyarsu mai mugunta ba. 18 A waɗannan kwanaki mutanen Yahuza za su haɗu da mutanen Isra'ila. Tare za su zo daga ƙasar arewa zuwa cikin ƙasar da na ba kakanninku gādo. 19 “Isra'ila, na yi niyya in karɓe ku kamar ɗana, In gādar muku da kyakkyawar ƙasa Mafi kyau a dukan duniya. Na zaci za ku ce ni ne mahaifinku, Ba za ku ƙara rabuwa da bina ba. 20 Hakika kamar yadda mace marar aminci takan bar mijinta, Haka kun zama marar aminci a gare ni, ya jama'ar Isra'ila. Ni Ubangiji, na faɗa.” 21 An ji murya a kan filayen tuddai, K�ka da roƙo ne na 'ya'yan Isra'ila maza, Domin sun rabu da hanyarsu, Sun manta da Ubangiji Allahnsu. 22 “Ku juyo ku marasa aminci, Zan warkar da rashin amincinku.” “To, ga shi, mun zo gare ka, Gama kai ne Ubangiji Allahnmu, 23 Daga kan tuddai ba mu da wani taimako, Ko daga hayaniyar da ake yi a kan duwatsu, Daga wurin Ubangiji Allahnmu ne kaɗai taimakon Isra'ila yake fitowa. 24 “Amma yin sujada ga gunkin nan Ba'al ya cinye mana amfanin wahalar da kakanninmu suka sha tun muna yara, wato na garkunan tumakinsu, da na awakinsu, da na shanunsu, da 'ya'yansu mata da maza. 25 Bari mu kwanta mu sha kunyarmu, bari kuma rashin kirkinmu ya rufe mu. Gama mun yi wa Ubangiji Allahnmu zunubi mu da kakanninmu, tun daga ƙuruciyarmu har zuwa yau, ba mu yi biyayya ga maganar Ubangiji Allahnmu ba.”

Irmiya 4

1 Ubangiji ya ce, “Ya mutanen Isra'ila, idan za ku juyo ku komo wurina, Idan kuka kawar da abubuwan banƙyama daga gabana, Kuka kuma bar yin shakka, 2 Idan kun yi rantsuwa kuka ce, ‘Har da ran Ubangiji kuwa,’ Da gaskiya, da aminci, da adalci, Sa'an nan sauran al'umma za su so in sa musu albarka, Za su kuma yabe ni.” 3 Ubangiji ya ce wa mutanen Yahuza da na Urushalima, “Ku kafce saurukanku, Kada ku yi shuka cikin ƙayayuwa. 4 Ya ku mutanen Yahuza da na Urushalima, Ku yi wa kanku kaciya domin Ubangiji, Ku kawar da loɓar zukatanku Don kada fushina ya fito kamar wuta, Ya cinye, ba mai iya kashewa, Saboda mugayen ayyukan da kuka aikata.”

Yahuza tana cikin Barazanar Yaƙi

5 “Ku yi shela a cikin Yahuza, Ku ta da murya a Urushalima, ku ce, ‘Ku busa ƙaho a dukan ƙasar!’ Ku ta da murya da ƙarfi, ku ce, ‘Ku tattaru, mu shiga birane masu garu.’ 6 Ku ta da tuta wajen Sihiyona! Ku sheƙa a guje neman mafaka, kada ku tsaya! Gama zan kawo masifa da babbar halaka daga arewa. 7 Zaki ya hauro daga cikin ruƙuƙinsa, Mai hallaka al'ummai ya kama hanya, Ya fito daga wurin zamansa don ya mai da ƙasarku kufai, Ya lalatar da biranenku, su zama kango, ba kowa. 8 Domin haka sai ku sa tufafin makoki, Ku yi makoki ku yi kuka, Gama fushin Ubangiji bai rabu da mu ba.” 9 Ubangiji ya ce, “A ranan nan, sarki da sarakuna, za su rasa ƙarfin hali, firistoci za su firgita, annabawa kuwa za su yi mamaki.” 10 Sai na ce, “Kaito, kaito, ya Ubangiji Allah, ka ruɗi jama'an nan da Urushalima, da ka ce musu, ‘Za ku zauna lafiya,’ amma ga shi, takobi zai sassare su.” 11 Lokaci yana zuwa da za a faɗa wa mutanen Urushalima cewa, “Iska mai zafi za ta huro daga tuddan hamada zuwa wajen jama'ata, ba domin a sheƙe ta ko a rairaye ta ba! 12 Wannan iska da za ta zo daga wurin Ubangiji, tana da mafificin ƙarfi. Yanzu fa zan yanke hukunci a kansu.”

Abokan Gāba sun Kewaye Yahuza da Yaƙi

13 Duba, ga abokin gāba yana zuwa kamar gizagizai, Karusan yaƙinsa suna kama da guguwa, Dawakansa sun fi gaggafa sauri. Kaitonmu, mun shiga uku! 14 Ya Urushalima, ki wanke mugunta daga zuciyarki, Domin a cece ki, Har yaushe mugayen tunaninki za su yi ta zama a cikinki? 15 Gama wata murya daga Dan ta faɗa, Ta kuma yi shelar masifar da za ta fito daga duwatsun Ifraimu. 16 “A faɗakar da al'ummai, yana zuwa, A faɗa wa Urushalima cewa, ‘Masu kawo mata yaƙi suna zuwa daga ƙasa mai nisa, Suna yi wa biranen Yahuza ihu. 17 Za su kewaye Yahuza kamar masu tsaron saura, Saboda ta tayar wa Ubangiji.’ Ni Ubangiji na faɗa. 18 “Al'amuranki da ayyukanki suka jawo miki wannan halaka, Tana da ɗaci kuwa, Ta soki har can cikin zuciyarki.”

Irmiya ya yi Baƙin Ciki don Mutanensa

19 Azaba! Ba zan iya daurewa da azaba ba! Zuciyata! Gabana yana faɗuwa da ƙarfi, Ba zan iya yin shiru ba, Gama na ji amon ƙaho da hargowar yaƙi. 20 Bala'i a kan bala'i, Ƙasa duka ta zama kufai, An lalatar da alfarwaina, ba zato ba tsammani, Labulena kuwa farat ɗaya. 21 Har yaushe zan yi ta ganin tuta, In yi ta jin amon ƙaho? 22 Ubangiji ya ce, “Mutanena wawaye ne, Ba su san ni ba, Yara ne dakikai, Ba su da ganewa. Suna gwanance da aikin mugunta, Amma ba su san yadda za su yi nagarta ba.” 23 Da na duba duniya sai na ga kufai ce kawai ba kome, Na kuma dubi sammai sai na ga ba haske. 24 Da na duba duwatsu, sai na ga suna makyarkyata, Dukan tuddai kuma suna rawar jiki, su yi gaba su yi baya. 25 Na duba sai na ga ba ko mutum ɗaya, Dukan tsuntsaye kuma sun tsere. 26 Na duba, sai na ga ƙasa mai dausayi ta zama hamada, An mai da dukan biranenta kangwaye A gaban Ubangiji saboda zafin fushinsa. 27 Gama Ubangiji ya ce, “Ƙasar duka za ta zama kufai, amma duk da haka, ba wannan ne zai zama ƙarshenta na har abada ba. 28 Duniya za ta yi makoki saboda wannan, Sammai za su duhunta, Gama ni na faɗa, haka kuwa na nufa in yi, Ba zan ji tausayi ba, Ba zan kuwa fāsa ba.” 29 Da jin motsin mahayan dawakai da na maharba Kowane gari zai fashe. Waɗansu za su shiga kurama, Waɗansu kuma su hau kan duwatsu. Dukan birane za su fashe tas, Ba wanda zai zauna a cikinsu. 30 Ya ke da kike kufai marar kowa, Me kike nufi da kika ci ado da mulufi, Kike caɓa ado da kayan zinariya, Kika sa wa idanunki tozali ram? Kin yi kwalliyarki a banza, Abokan sha'anin karuwancinki sun raina ki, Ranki suke nema. 31 Na ji kuka kamar na mace wadda ke naƙuda, Na ji nishi kamar na mace a lokacin haihuwarta ta fari, Na ji kukan 'yar Sihiyona tana kyakyari, Tana miƙa hannuwanta tana cewa, “Wayyo ni kaina, gama ina suma a gaban masu kisankai!”

Irmiya 5

Zunubin Urushalima da Yahuza

1 “Ku bi titunan Urushalima ko'ina! Ku dudduba ku lura! Ku bincika kowane dandali, ku gani, Ko za ku iya samun ko mutum ɗaya Mai aikata adalci, mai son gaskiya, Sai in gafarta mata. 2 Ko da ya ke suna cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji,’ Duk da haka rantsuwar ƙarya suke yi.” 3 Ya Ubangiji, ashe, ba masu gaskiya kake so ba? Ka buge su, amma ba su yi nishi ba, Ka hore su, amma sun ƙi horuwa, Fuskarsu ta ƙeƙashe fiye da dutse, Sun ƙi tuba. 4 Sai na ce, “Waɗannan mutane ba su da kirki, Ba su da hankali, Ba su san hanyar Ubangiji, Ko shari'ar Allahnsu ba. 5 Zan tafi wurin manyan mutane, in yi musu magana, Gama sun san nufin Ubangiji, da shari'ar Allahnsu.” Amma dukansu sun ƙi yarda Ubangiji ya mallake su, Suka ƙi yi masa biyayya. 6 Domin haka zaki daga kurmi zai kashe su, Kyarkeci kuma daga hamada zai hallaka su. Damisa tana yi wa biranensu kwanto, Duk wanda ya fita daga cikinsu sai a yayyage shi, Domin laifofinsu sun yi yawa, Karkacewarsu babba ce. 7 “Don me zan gafarce ki? 'Ya'yanki sun rabu da ni, Sun yi rantsuwa da gumaka, Na ciyar da su har sun ƙoshi sosai, Suka yi karuwanci, suka ɗunguma zuwa gidajen karuwai, 8 Kamar ƙosassun ingarmu suke, masu jaraba, Kowa yana haniniya, yana neman matar maƙwabcinsa. 9 Ba zan hore su saboda waɗannan abubuwa ba? Ni Ubangiji na ce, ba zan ɗauka wa kaina fansa a kan wannan al'umma ba? 10 Ku haura, ku lalatar da gonar kurangar inabinta, Amma kada ku yi mata ƙarƙaf, Ku sassare rassanta, Gama su ba na Ubangiji ba ne. 11 Gama mutanen Isra'ila da mutanen Yahuza Sun zama marasa aminci a gare ni. Ni Ubangiji na faɗa.” 12 Sun yi ƙarya a kan Ubangiji, Suka ce, “Ba abin da zai yi, Ba wata masifa da za ta same mu. Ba kuwa za mu ga takobi ko yunwa ba. 13 Annabawa holoƙo ne kawai, Maganar ba ta cikinsu. Haka za a yi da su!”

Urushalima tana gab da Faɗuwa

14 Saboda haka Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Domin sun hurta wannan magana, Ga shi, zan sa maganata a bakinka ta zama wuta, Waɗannan mutane kuwa su zama itace, Wutar za ta cinye su. 15 “Ya ku mutanen Isra'ila, ga shi, ina kawo muku Wata al'umma daga nesa,” in ji Ubangiji, “Al'umma ce mai ƙarfin hali ta tun zamanin dā. Al'umma wadda ba ku san harshenta ba, Ba za ku fahimci abin da suke faɗa ba. 16 Kwarinsu kamar buɗaɗɗen kabari ne, Dukansu jarumawa ne. 17 Za su cinye amfanin gonakinku da abincinku. Za su ƙare 'ya'yanku mata da maza. Za su cinye garkunanku na tumaki, da na awaki, da na shanu, Za su kuma cinye 'ya'yan inabinku da na ɓaurenku. Za su hallaka biranenku masu kagara da takobi, waɗanda kuke fariya da su. 18 “Amma ko a cikin waɗancan kwanaki ba zan yi muku ƙaƙaf ba,” in ji Ubangiji. 19 “Sa'ad da mutanenki suka ce, ‘Me ya sa Ubangiji Allahnmu ya yi mana waɗannan abubuwa duka?’ Sai ki ce musu, ‘Kamar yadda kuka rabu da ni kuka bauta wa gumaka a ƙasarku, haka kuma za ku bauta wa baƙi a ƙasar da ba taku ba.’ ” 20 “Ka sanar wa zuriyar Yakubu da wannan, Ka kuma yi shelarsa a Yahuza, ka ce, 21 ‘Ku ji wannan, ya ku wawaye, marasa hankali, Kuna da idanu, amma ba ku gani, Kuna da kunnuwa, amma ba ku ji.’ ” 22 Ubangiji ya ce, “Ba za ku ji tsorona ba? Ba za ku yi rawar jiki a gabana ba? Ni ne na sa yashi ya zama iyakar teku, Tabbatacciyar iyaka, wadda ba ta hayuwa, Ko da ya ke raƙuman ruwa za su yi hauka, ba za su iya haye ta ba, Ko da suna ruri, ba za su iya wuce ta ba. 23 Amma mutanen nan suna da taurin zuciya, masu halin tayarwa ne, Sun rabu da ni, sun yi tafiyarsu. 24 A zuciya ba su cewa, ‘Bari mu ji tsoron Ubangiji Allahnmu Wanda yake ba mu ruwan sama a kan kari, Na kaka da na bazara, Wanda yake ba mu lokacin girbi.’ 25 Laifofinku sun raba ku da waɗannan abubuwa. Zunubanku kuma sun hana ku samun alheri. 26 “Gama an sami mugaye, a cikin jama'ata, Suna kwanto kamar masu kafa ashibta. Sun ɗana tarko su kama mutane. 27 Kamar kwando cike da tsuntsaye, Hakanan gidajensu ke cike da cin amana, Don haka suka zama manya, suka sami dukiya. 28 Sun yi ƙiba, sun yi bul-bul, Ba su da haram a kan aikata mugunta, Ba su yi wa marayu shari'ar adalci, don kada su taimake su. A wajen shari'a ba su bin hakkin matalauta. 29 “Ba zan hukunta su saboda waɗannan abubuwa ba? Ba zan ɗaukar wa kaina fansa a kan al'umma irin wannan ba? 30 “Abin banmamaki da bantsoro Ya faru a ƙasar. 31 Annabawa sun yi annabcin ƙarya, Firistoci kuma sun yi mulki da ikon kansu, Mutanena kuwa suna so haka! Amma sa'ad da ƙarshe ya zo, me za ku yi?”

Irmiya 6

Ajalin Urushalima da Yahuza

1 “Ya ku mutanen Biliyaminu, ku gudu neman mafaka, Daga cikin Urushalima! Ku busa ƙaho a Tekowa, Ku ba da alama a Bet-akkerem, Gama masifa da babbar halaka sun fito daga arewa. 2 Ya Sihiyona, ke kyakkyawar makiyaya ce, zan hallaka abin da kika hahhaifa. 3 Makiyaya da garkunansu za su zo wurinki, Za su kafa alfarwansu kewaye da ke, Kowa zai yi kiwo a makiyayarki. 4 Za su ce, ‘Mu yi shiri mu fāɗa mata da yaƙi! Ku tashi, mu fāɗa musu da tsakar rana!’ Sai kuma suka ce, ‘Kaitonmu, ga rana tana faɗuwa, ta yi ruɗa-kuyangi. 5 Mu tashi mu fāɗa mata da dare, Mu lalatar da fādodinta.’ ” 6 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ku sassare itatuwanta, Ku tula ƙasa kewaye da Urushalima, Dole in hukunta wannan birni saboda ba kome cikinsa sai zalunci, 7 Kamar yadda rijiya take da ruwa garau, Haka Urushalima take da muguntarta, Ana jin labarin kama-karya da na hallakarwa a cikinta, Kullum akwai cuce-cuce, da raunuka a gabana, 8 Ku ji faɗaka, ya ku mutanen Urushalima, Don kada a raba ni da ku, Don kada in maishe ku kufai, Ƙasar da ba mazauna ciki.” 9 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Za a kalace ringin Isra'ila sarai, kamar yadda ake wa inabi, Ka miƙa hannunka a kan rassanta kamar mai tsinkar 'ya'yan inabi.” 10 Da wa zan yi magana don in faɗakar da shi, don su ji? Ga shi, kunnuwansu a toshe suke, su ji, Ga shi, maganar Ubangiji kuwa ta zama abin ba'a a gare su, Ba su marmarinta. 11-12 Don haka ina cike da fushin Ubangiji Na gaji da kannewa. Ubangiji ya ce, “Zan kwararo fushi kan yara da ke a titi. Da kuma kan tattaruwar samari. Za a ɗauke mata da miji duka biyu, Da tsofaffi, da waɗanda suka tsufa tukub-tukub. Za a ba waɗansu gidajensu, da gonakinsu, da matansu, Gama zan nuna ikona in hukunta mazaunan ƙasar. 13 Gama daga ƙaraminsu zuwa babba, Kowannensu yana haɗama ya ci ƙazamar riba, Har annabawa da firistoci, Kowannensu ya shiga aikata rashin gaskiya. 14 Sun warkar da raunin mutanena sama sama, Suna cewa, ‘Lafiya, Lafiya,’ alhali kuwa ba lafiya. 15 Sun ji kunya sa'ad da suka aikata abubuwan banƙyama? Ba su ji kunya ba ko kaɗan. Ko gezau ba su yi ba, Don haka za su fāɗi tare da fāɗaɗɗu, Sa'ad da na hukunta su, za a hamɓarar da su. Ni Ubangiji na faɗa.” 16 Haka Ubangiji ya ce, “Ku tsaya kan hanyoyi, ku duba, Ku nemi hanyoyin dā, inda hanya mai kyau take, Ku bi ta, don ku hutar da rayukanku. Amma suka ce, ‘Ai, ba za mu bi ta ba.’ 17 Na sa muku matsara cewa, in kun ji an busa ƙaho ku kula! Amma suka ce, ‘Ba za mu kula ba.’ 18 “Don haka, ku ji, ya ku al'ummai, Ku sani, ku taron jama'a, Don ku san abin da zai same ku. 19 Ki ji, ya ke duniya, Ga shi, ina kawo masifa a kan wannan jama'a, Sakayyar ƙulle-ƙullensu, Don ba su kula da maganata ba, Sun ƙi dokokina. 20 Da wane nufi kuke kawo mini turare daga Sheba, Ko raken da kuke kawowa daga ƙasa mai nisa? Ba zan karɓi hadayunku na ƙonawa ba, Ba kuwa zan ji daɗin sadakokinku ba. 21 Don haka, ni Ubangiji na ce, Zan sa abin tuntuɓe a gaban wannan jama'a, Za su kuwa yi tuntuɓe, su fāɗi. Iyaye tare da 'ya'yansu, da maƙwabci, Do abokansu za su lalace.” 22 Haka Ubangiji ya ce, “Ga shi, jama'a tana fitowa daga ƙasar arewa. Babbar al'umma ce, Ta yunƙuro tun daga manisantan wurare na duniya. 23 Suna riƙe da baka da māshi, Mugaye ne marasa tausayi, Motsinsu kamar ƙugin teku ne. Suna haye a kan dawakai, A jere kamar wanda ya yi shirin yaƙi Gāba da ke, ya 'yar Sihiyona.” 24 Mutanen Urushalima sun ce, “Mun ji labarin yaƙin, Hannuwanmu suka yi rauni. Azaba ta kama mu, Ciwo irin na mai naƙuda. 25 Kada ku fita zuwa gona, Kada kuma ku yi yawo a kan hanya, Gama abokin gāba yana da takobi, Razana a kowane sashi.” 26 “Ya mutanena, ku sa tufafin makoki, Ku yi birgima cikin toka, Ku yi makoki mai zafi irin wanda akan yi wa ɗa tilo, Gama mai hallakarwa zai auko mana nan da nan.” 27 Ubangiji ya ce wa Irmiya, “Na maishe ka mai aunawa da mai jarraba mutanena Domin ka sani, ka auna al'amuransu, 28 Su duka masu taurinkai ne, 'yan tawaye, Suna yawo suna baza jita-jita. Su tagulla ne da baƙin ƙarfe, Dukansu lalatattu ne. 29 Ana zuga da ƙarfi, Dalma ta ƙone, Tacewar aikin banza ne, Gama ba a fitar da mugaye ba. 30 Ana ce da su ƙwan maƙerar azurfa ne, Gama ni na ƙi su.”

Irmiya 7

Ku Gyara Hanyoyinku da Ayyukanku

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce, 2 “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Haikalin Ubangiji, ka yi shelar wannan magana, ka ce, su kasa kunne ga maganar Ubangiji, dukansu mutanen Yahuza, su da suke shiga ta ƙofofin nan don su yi wa Ubangiji sujada! 3 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, ni kuwa zan ƙyale ku, ku zauna a wannan wuri. 4 Kada ku amince da maganganun nan na ruɗarwa, cewa wannan shi ne Haikalin Ubangiji. Wannan shi ne Haikalin Ubangiji, wannan shi ne Haikalin Ubangiji! 5 “ ‘Idan dai kun gyara hanyoyinku, da ayyukanku bisa kan gaskiya, idan da gaskiya kuke aikata adalci ga junanku, 6 idan ba ku tsananta wa baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, idan ba ku zubar da jinin marar laifi a wannan wuri ba, idan kuma ba ku bi abin da zai cuce ku ba, wato gumaka, 7 sa'an nan zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasa wadda tuni na ba kakanninku har abada. 8 “ ‘Ga shi, kun amince da maganganu na ruɗami, marasa amfani. 9 Za ku yi ta yin sata, da kisankai, da zina, da rantsuwar ƙarya, da ƙona wa Ba'al turare, da bin waɗansu gumakan da ba ku sani ba? 10 Sa'an nan za ku zo ku tsaya a gabana a wannan Haikali, wanda ake kira da sunana, ku ce, “An cece mu,” don kawai ku ci gaba da yin dukan waɗannan abubuwan banƙyama? 11 Wannan Haikali wanda ake kira da sunana ya zama kogon mafasa a idanunku. Ga shi, ni da kaina na gani,’ ” in ji Ubangiji. 12 “ ‘Ku tafi Shilo wurin da na fara zaunar da sunana, ku ga abin da na yi mata saboda muguntar mutanena Isra'ila. 13 Yanzu kuwa saboda kun aikata waɗannan al'amura, sa'ad da na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne ba, sa'ad da na kira ku, ba ku amsa ba, 14 domin haka zan yi wa Haikali wanda ake kira da sunana, wanda kuma kuka amince da shi, da kuma wurin da na ba ku, ku da kakanninku, kamar yadda na yi wa Shilo. 15 Zan kore ku daga gabana kamar yadda na yi wa dukan 'yan'uwanku, dukan zuriyar Ifraimu.’ ”

Fushin Allah a kan Bin Gumaka

16 “Kai kuwa, Irmiya kada ka yi wa mutanen nan addu'a. Kada ka yi kuka ko addu'a dominsu, kada ka roƙe ni, gama ba zan ji ka ba. 17 Ba ka ga abin da suke yi a biranen Yahuza da titunan Urushalima ba? 18 Yara sukan tara itace, iyaye maza sukan haɗa wuta, iyaye mata sukan kwaɓa ƙullu don su yi wa gunkin nan wadda ake kira sarauniyar sama, waina. Sukan kuma miƙa wa gumaka hadayu na sha domin su tsokane ni.” 19 In ji Ubangiji, “Ni suke tsokana? Ashe, ba kansu ba ne don su ruɗar da kansu?” 20 Saboda haka ga abin da Ubangiji Allah ya ce, “Duba, zan kwarara fushina da hasalata a kan wannan wuri, a kan mutum duk da dabba, da akan itatuwan saura da amfanin gona. Zai yi ta cin wuta, ba kuwa za a kashe ba.”

Horon Yahuza saboda Tayarwa

21 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Ku ba da hadayunku na ƙonawa da na sadakarku, ku ci naman. 22 A ranar da na fito da kakanninku daga ƙasar Masar, ban yi magana da su, ko na umarce su, a kan hadayun ƙonawa da na sadaka ba. 23 Amma na umarce su su yi biyayya da maganata, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena, su bi dukan al'amuran da na umarce su, domin lafiyarsu, don su zama lafiya. 24 Amma ba su yi biyayya ba, ba su kuma kula ba. Sai suka bi shawarar kansu da ta tattaurar muguwar zuciyarsu. Suka koma baya maimakon su yi gaba. 25 Tun daga ran da kakanninku suka fito ƙasar Masar, har zuwa yau na yi ta aika musu da dukan bayina annabawa kowace rana. 26 Duk da haka ba su saurare ni ba, ba su kula su ji ba, sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu. 27 “Saboda haka za ka faɗa musu waɗannan abubuwa duka, amma ba za su ji ka ba. Za ka kira su, amma ba za su amsa ba. 28 Za ka faɗa musu ka ce, wannan ita ce al'ummar da ba ta yi biyayya da maganar Ubangiji Allahnta ba, ba ta karɓi horo ba. Gaskiya kuma ta ƙare sam, ba ta a bakinsu. 29 “Ku aske gashin kanku, ku zubar da shi. Ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi 'yan zamanin nan, ya rabu da su saboda fushinsa. 30 Ni Ubangiji, na faɗa, cewa mutanen Yahuza sun yi mugun abu a gabana. Suna ajiye gumakansu a Haikalina, sun ƙazantar da shi. 31 A cikin kwarin ɗan Hinnon sun gina bagade, mai suna Tofet, don su miƙa 'ya'yansu mata da maza hadayar ƙonawa. Ni ban umarce su su yi haka ba, irin wannan abu ba shi a zuciyata. 32 Domin haka, ni Ubangiji na ce, kwanaki suna zuwa lokacin da ba za a ƙara faɗar Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a kira shi Kwarin Kisa, gama za a binne mutane a Tofet domin ba sauran wuri a ko'ina. 33 Gawawwakin mutanen nan za su zama abincin tsuntsaye da na namomin jeji, ba wanda zai kore su. 34 Zan sa muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya su ƙare a biranen Yahuza da titunan Urushalima, gama ƙasar za ta zama kufai.”

Irmiya 8

1 “Ni Ubangiji na faɗa, cewa a wancan lokaci, za a fitar da ƙasusuwa daga kaburburan sarakunan Yahuza, da na sarakansu, da na firistoci, da na annabawa, da na mazaunan Urushalima. 2 Za a shimfiɗa su a rana, da a farin wata, da a gaban dukan rundunan sama, waɗanda suka ƙaunata, suka bauta wa, waɗanda suka nemi shawararsu, suka yi musu sujada. Ba za a tattara su a binne ba, amma za su zama juji a bisa ƙasa. 3 Sauran mutanen muguwar tsaran nan waɗanda ke a wuraren da na warwatsa su, za su fi son mutuwa fiye da rayuwa. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Zunubi da Hukunci

4 “Ka faɗa musu, ka ce, ni Ubangiji na ce, ‘Wanda ya fāɗi ba zai sāke tashi ba? Idan wani ya kauce ba zai komo kan hanya ba? 5 Me ya sa, mutanen nan na Urushalima suke ratsewa, suke komawa baya kullayaumin? Sun riƙe ƙarya kan-kan Sun ƙi komowa. 6 Na kula sosai, na saurara, Amma ba wanda ya faɗi wata maganar kirki, Ba wanda ya taɓa barin muguntarsa, Kowa cewa yake, “Me na yi?” Kamar dokin da ya kutsa kai cikin fagen fama. 7 Ko shamuwa ta sararin sama ma, ta san lokatanta, Tattabara da tsattsewa, da gauraka suna kiyaye lokacin komowarsu. Amma mutanena ba su san dokokina ba. 8 “ ‘Ƙaƙa za ku ce, “Muna da hikima, Dokar Ubangiji tana tare da mu?” Ga shi kuwa, alkalamin ƙarya na magatakarda, ya yi ƙarya. 9 Za a kunyatar da masu hikima. Za su tsorata, za a kuma tafi da su. Ga shi, sun ƙi maganar Ubangiji. Wace hikima suke da ita? 10 Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu, Gonakinsu kuma ga waɗanda suke cinsu da yaƙi, Saboda tun daga ƙarami har zuwa babba Kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba, Tun daga annabawa zuwa firistoci Kowannensu aikata ha'inci yake yi. 11 Sun warkar da raunin mutanena sama sama, Suna cewa, “Lafiya, lafiya,” alhali kuwa ba lafiya. 12 Ko sun ji kunya Sa'ad da suka aikata ayyuka masu banƙyama? A'a, ba su ji kunya ba ko kaɗan, Fuskarsu ko gezau ba ta yi ba. Domin haka za su faɗi tare da fāɗaɗɗu, Sa'ad da na hukunta su, za a ci su da yaƙi. Ni Ubangiji na faɗa.’ 13 “Ni Ubangiji na ce, ‘Sa'ad da zan tattara su kamar amfanin gona, Sai na tarar ba 'ya'ya a kurangar inabi, Ba 'ya'ya kuma a itacen ɓaure, Har ganyayen ma sun bushe. Abin da na ba su kuma ya kuɓuce musu. Ni Ubangiji na faɗa.’ ” 14 Mutanen Urushalima sun ce, “Don me muke zaune kawai? Bari mu tattaru, mu tafi cikin garuruwa masu garu, Mu mutu a can, Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa, Ya ba mu ruwan dafi, Domin mun yi masa laifi. 15 Mun sa zuciya ga salama, amma ba lafiya, Mun sa zuciya ga lokacin samun warkewa, Amma sai ga razana! 16 Daga Dan, an ji firjin dawakai. Dakan ƙasar ta girgiza saboda haniniyar ingarmunsu. Sun zo su cinye ƙasar duk da abin da ke cikinta, Wato da birnin da mazauna cikinsa.” 17 “Ni Ubangiji na ce, ‘Zan aiko muku da macizai, da kāsā, Waɗanda ba su da makari, Za su sassare ku.’ ” 18 Baƙin cikina ya fi ƙarfin warkewa, Zuciyata ta ɓaci ƙwarai! 19 Ku ji kukan jama'ata ko'ina a ƙasar, “Ubangiji, ba shi a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya a cikinta ne?” Ubangiji ya ce, “Me ya sa suka tsokane ni da sassaƙaƙƙun gumakansu, Da baƙin gumakansu?” 20 Mutane suna ta cewa, “Damuna ta ƙare, kaka kuma ta wuce, Amma ba a cece mu ba.” 21 Raunin da aka yi wa jama'ata, Ya yi wa zuciyata rauni. Ina makoki, tsoro kuma ya kama ni ƙwarai. 22 Ba abin sanyayawa a Gileyad ne? Ba mai magani a can ne? Me ya sa ba a warkar da jama'ata ba?

Irmiya 9

1 Da ma kaina ruwa ne kundum, Idanuna kuma maɓuɓɓuga ne, Da sai in yi ta kuka dare da rana, Saboda an kashe jama'ata! 2 Da ma ina da wurin da zan fake a hamada, Da sai in rabu da mutanena, in tafi can! Gama dukansu mazinata ne, Ƙungiyar mutane maciya amana. 3 Ubangiji ya ce, “Sun tanƙwasa harshensu kamar baka, Ƙarya ce take rinjayar gaskiya a ƙasar. Suna ta cin gaba da aikata mugunta, Ba su kuwa san ni ba. 4 “Bari kowane mutum ya yi hankali da maƙwabcinsa, Kada kuma ya amince da kowane irin ɗan'uwa, Gama kowane ɗan'uwa munafuki ne, Kowane maƙwabci kuma mai kushe ne. 5 Kowane mutum yana ruɗin maƙwabcinsa da abokinsa, Ba mai faɗar gaskiya, Sun koya wa harshensu faɗar ƙarya. Suna aikata laifi, Sun rafke, sun kasa tuba. 6 Suna ƙara zalunci a kan zalunci, Yaudara a kan yaudara, Sun ƙi sanina,” in ji Ubangiji. 7 Saboda haka, Ubangiji Mai Runduna, ya faɗa cewa, “Zan tsabtace su, in gwada su, Gama me zan yi kuma saboda jama'ata? 8 Harshensu kibiya ce mai dafi, yana faɗar ƙarya, Kowa yana maganar alheri da maƙwabcinsa Amma a zuciyarsa yana shirya masa maƙarƙashiya. 9 Ba zan hukunta su saboda waɗannan al'amura ba? Ba zan sāka wa al'umma irin wannan ba?” 10 Zan yi kuka in yi kururuwa saboda tsaunuka, Zan yi kuka saboda wuraren kiwo, Domin sun bushe sun zama marasa amfani. Ba wanda yake bi ta cikinsu. Ba a kuma jin kukan shanu, Tsuntsaye da namomin jeji, sun gudu sun tafi. 11 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da Urushalima tsibin kufai, Wurin zaman diloli, Zan kuma mai da biranen Yahuza kufai, inda ba kowa.”

Za a Rushe Birni a Kai su Zaman Talala

12 Wa ke da isasshiyar hikimar da zai fahimci wannan? Wa Ubangiji ya faɗa masa don ya sanar? Me ya sa ƙasar ta lalace ta zama kufai, har ba wanda ke iya ratsa ta, kamar hamada? 13 Sai Ubangiji ya ce, “Saboda sun bar dokata wadda na sa a gabansu, ba su yi biyayya da maganata ko su yi aiki da ita ba. 14 Amma suka taurare, suka biye wa zuciyarsu, suka bi Ba'al, kamar yadda kakanninsu suka koya musu. 15 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, zan ciyar da mutanen nan da abinci mai ɗaci, in shayar da su da ruwan dafi. 16 Zan watsa su cikin sauran al'umma waɗanda su da kakanninsu ba su san su ba, zan sa takobi ya bi su don in hallaka su. 17 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna na ce, Ku yi tunani, ku kirawo mata masu makoki su zo, Ku aika wa gwanaye fa.” 18 Jama'a suka ce, “Su gaggauta, su ta da murya, Su yi mana kuka da ƙarfi, Har idanunmu su cika da hawaye, Giranmu kuma su jiƙe sharaf. 19 “Gama ana jin muryar kuka daga Sihiyona cewa, ‘Ga yadda muka lalace! Aka kunyatar da mu ɗungum! Don mun bar ƙasar, domin sun rurrushe wuraren zamanmu.’ ” 20 Irmiya ya ce, “Ya ku mata, ku ji maganar Ubangiji, Ku kasa kunne ga maganar da ya faɗa, Ku koya wa 'ya'yanku mata kukan makoki, Kowacce ta koya wa maƙwabciyarta waƙar makoki, 21 Gama mutuwa ta shiga tagoginmu, Ta shiga cikin fādodinmu, Ta karkashe yara a tituna, Ta kuma karkashe samari a dandali. 22 Ubangiji ya ce mini, ‘Ka yi magana, cewa gawawwakin mutane za su fāɗi tuli Kamar juji a saura, Kamar dammunan da masu girbi suka ɗaura, Ba wanda zai tattara su.’ ” 23 Ubangiji ya ce, “Kada mai hikima ya yi fariya da hikimarsa, kada mai ƙarfi ya yi fariya da ƙarfinsa, kada kuma mawadaci ya yi fariya da wadatarsa. 24 Amma bari wanda zai yi fariya, ya yi fariya a kan cewa ya fahimce ni, ya kuma san ni. Ni ne Ubangiji mai yin alheri, da gaskiya, da adalci a duniya, gama ina murna da waɗannan abubuwa, ni Ubangiji na faɗa.” 25 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa sa'ad da zan hukunta dukan waɗanda aka yi musu kaciya, 26 da Masar, da Yahuza, da Edom, da 'ya'yan Ammon, maza, da na Mowab, da dukan waɗanda ke zaune a hamada, da waɗanda ke yi wa kansu sanƙo, gama dukan al'umman nan marasa kaciya ne, dukan jama'ar Isra'ila kuma marasa kaciya ne a zuci.”

Irmiya 10

Gumaka da Allah na Gaskiya

1 Ya jama'ar Isra'ila, ku ji jawabin da Ubangiji yake yi muku. 2 Ubangiji ya ce, “Kada ku koyi abubuwan da al'ummai suke yi, Kada ku ji tsoron alamun da ke a sama, Ko da ya ke al'ummai suna jin tsoronsu. 3 Gama al'adun mutane na ƙarya ne, Daga cikin jeji aka sare wani itace, Gwanin sassaƙa ya sassaƙa shi da gizago. 4 Mutane sukan yi masa ado na azurfa da zinariya, Sukan ɗauki guduma su kafa shi da ƙusoshi, Don kada ya motsa. 5 Gumakansu dodon gona suke, a cikin gonar kabewa, Ba su iya yin magana, Ɗaukarsu ake yi domin ba su iya tafiya! Kada ku ji tsoronsu. Gama ba su da ikon aikata mugunta ko alheri.” 6 Ya Ubangiji, ba wani kamarka, Kai mai girma ne, Sunanka kuma yana da girma da iko. 7 Wanene ba zai ji tsoronka ba, ya Sarkin dukan al'ummai? Ka isa a ji tsoronka, Gama babu kamarka a cikin dukan masu hikima na al'ummai, Da kuma cikin dukan mulkokinsu, Ba wani kamarka. 8 Dukansu dakikai ne wawaye, Koyarwar gumaka ba wani abu ba ne, itace ne kawai! 9 An kawo fallayen azurfa daga Tarshish, Da zinariya kuma daga Ufaz, Aikin gwanaye da maƙeran zinariya. Tufafinsu na mulufi ne da shunayya, duka aikin gwanaye. 10 Amma Ubangiji shi ne Allah na gaskiya, Shi Allah mai rai ne, Shi Sarki ne madawwami. Saboda hasalarsa duniya ta girgiza, Al'ummai ba za su iya jurewa da fushinsa ba. 11 Haka za ku faɗa musu, “Gumakan da ba su yi sammai da duniya ba, za su lalace a duniya da a ƙarƙashin sammai.” 12 Shi ne, ta wurin ikonsa ya yi duniya, Ta wurin hikimarsa ya kafa ta, Ta wurin basirarsa kumaya ya shimfiɗa sammai. 13 Sa'ad da ya yi murya akan ji ƙugin ruwa a cikin sammai Yakan kawo ƙasashi daga ƙurewar duniya, Yakan yi walƙiyoyi saboda ruwan sama, Daga cikin taskokinsa yakan kawo iska. 14 Kowane mutum dakiki ne, marar ilimi, Kowane maƙerin zinariya zai sha kunya saboda gumakansa, Gama siffofinsa ƙarya ne, Ba numfashi a cikinsu. 15 Su ba kome ba ne, aikin ruɗami ne, A lokacin da za a hukunta su za su lalace. 16 Gama shi ba kamar waɗannan yake ba, Shi na Yakubu ne. Shi ne ya yi dukan kome, Kabilan Isra'ilawa gādonsa, Sunansa Ubangiji Mai Runduna.

Risɓewar Yahuza

17 Ku tattara kayayyakinku, Ku mazaunan wurin da aka kewaye da yaƙi. 18 Gama haka Ubangiji ya ce, “Ga shi, ina jefar da mazaunan ƙasar daga ƙasarsu a wannan lokaci, Zan kawo musu wahala, za su kuwa ji jiki.” 19 Tawa ta ƙare, saboda raunin da aka yi mini. Raunina mai tsanani ne, Amma na ce, lalle wannan azaba ce, Tilas in daure da ita. 20 An lalatar da alfarwata, Dukan igiyoyi sun tsintsinke, 'Ya'yana maza sun bar ni, ba su nan. Ba wanda zai kafa mini alfarwata Ya kuma rataya labulena. 21 Makiyayan dakikai ne, Ba su roƙi Ubangiji ba, Don haka ba su sami wadata ba, An watsa dukan garkensu. 22 Ku ji fa, an ji ƙishin-ƙishin! Ga shi kuma, yana tafe. Akwai babban hargitsin da ya fito daga arewa, Don a mai da biranen Yahuza kufai, wurin zaman diloli. 23 “Ya Ubangiji, na sani al'amuran mutum ba a hannunsa suke ba, Ba mutum ne ke kiyaye takawarsa ba 24 Ka tsauta mini, ya Ubangiji, amma da adalcinka, Ba da fushinka ba, don kada ka wofinta ni. 25 Ka kwarara hasalarka a kan sauran al'umma da ba su san ka ba, Da a kan jama'ar da ba su kiran sunanka, Gama sun cinye Yakubu, Sun cinye shi, sun haɗiye shi, Sun kuma mai da wurin zamansa kufai.”

Irmiya 11

An Ta da Alkawari

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya cewa, 2 “Ka ji maganar wannan alkawari, sa'an nan ka faɗa wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima. 3 Ka faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Allah na Isra'ila, la'ananne ne wanda bai kula da maganar alkawarin nan ba. 4 Wato alkawarin da na yi da kakanninku a lokacin da na fito da su daga ƙasar Masar, daga cikin tanderun ƙarfe. Na faɗa musu su yi biyayya da maganata, su aikata dukan abin da na umarce su. Ta haka za su zama mutanena, ni kuma in zama Allahnsu. 5 Sa'an nan zan cika maganar rantsuwa da na rantse wa kakanninku, da na ce zan ba su ƙasa wadda ke cike da albarka kamar yadda yake a yau.’ ” Irmiya ya ce, “Amin, amin, ya Ubangiji.” 6 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka yi shelar dukan maganan nan a biranen Yahuza da titunan Urushalima duka, cewa su ji maganar alkawarin nan, su aikata. 7 Lokacin da na fito da kakanninsu daga ƙasar Masar na faɗakar da su musamman, na yi ta faɗakar da su har wannan rana, ina cewa, ‘Ku yi biyayya da maganata.’ 8 Amma duk da haka ba su yi biyayya ba, ba su kuma kasa kunne ba. Kowa ya bi tattaurar zuciyarsa mai mugunta. Domin haka na kawo musu dukan maganar alkawarin nan wanda na umarce su su yi, amma ba su yi ba.” 9 Ubangiji ya kuma ce mini, “Akwai tawaye a cikin mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima. 10 Sun koma a kan laifofin kakanninsu, waɗanda suka ƙi jin maganata, suka bi gumakansu don su bauta musu, jama'ar Isra'ila da na Yahuza sun ta da alkawarina wanda na yi da kakanninsu. 11 Saboda haka ni Ubangiji na ce, ‘Ga shi, ina kawo musu masifa wadda ba za su iya tsere mata ba, ko da za su yi kuka gare ni ba zan ji su ba. 12 Sa'an nan biranen Yahuza da mazaunan Urushalima za su tafi, su yi kuka ga gumaka waɗanda suka ƙona musu turare, amma ba za su iya cetonsu a lokacin wahalarsu ba. 13 Gama yawan gumakansu sun kai yawan biranensu. Yawan bagadan da suke da su kuma sun kai yawan titunan Urushalima, abin kunya, bagadan ƙona wa Ba'al turare ne.’ 14 Don haka kada ka yi wa waɗannan mutane addu'a. Kada ka yi kuka ko addu'a dominsu, gama ba zan kasa kunne gare su ba, ko da sun yi kirana a lokacin wahalarsu.” 15 Ubangiji ya ce, “Wane iko ƙaunatacciyata take da shi cikin Haikalina, da ya ke ta aikata mugayen ayyuka? Ko alkawarai da naman hadayu za su iya kawar miki da ƙaddararki, har da za ki yi taƙama? 16 Dā na kira ki itacen zaitun mai duhuwa, kyakkyawa, mai kyawawan 'ya'ya, amma da ƙugin babbar iska za a cinna miki wuta, za ta kuwa cinye rassanki.” 17 Ubangiji Mai Runduna, wanda ya dasa ku, ya hurta masifar da za ta same ku saboda muguntar da mutanen Isra'ila da na Yahuza suka yi, suka tsokane ni in yi fushi saboda suna ƙona wa Ba'al turare.

An Shirya Maƙarƙashiya don a Kashe Irmiya

18 Ubangiji ya sanasshe ni, Na kuwa sani, Sa'an nan ya nuna mini mugayen ayyukansu. 19 Amma ina kama da lafiyayyen ɗan rago, Wanda aka ja zuwa mayanka, Ashe, ni suke ƙulla wa munafuncin! Ni kuwa ban sani ba, da suke cewa, “Bari mu lalatar da itacen duk da 'ya'yansa. Bari mu datse shi daga ƙasar masu rai, Har da ba za a ƙara tunawa da sunansa ba.” 20 Amma ya Ubangiji Mai Runduna, mai shari'ar adalci, Kakan gwada zuciya da tunani, Ka yarda mini in ga sakayyar da za ka yi mini a kansu, Gama a gare ka na danƙa maganata. 21 Saboda haka ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mutanen Anatot, waɗanda suke neman ranka, da suka ce, “Kada ka yi annabci da sunan Ubangiji, in ba haka ba, da hannunmu za mu kashe ka.” 22 Domin haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ga shi kuwa, zan hukunta su, za a kashe samarinsu da takobi, 'ya'yansu mata da maza, yunwa za ta kashe su. 23 Ba wanda zai ragu daga cikin mutanen Anatot, gama zan kawo wa mutanen Anatot masifa, a shekarar hukuncinsu.”

Irmiya 12

Fatawar Irmiya da Amsar Ubangiji

1 Ya Ubangiji, kai adali ne sa'ad da na kawo ƙara a gare ka. Duk da haka zan bayyana ƙarata a gabanka, Me ya sa mugaye ke arziki cikin harkarsu? Me ya sa dukan maciya amana suke zaman lafiya, Suna kuwa ci gaba? 2 Kai ka dasa su, sun kuwa yi saiwa, Suna girma, suna kuma ba da 'ya'ya, Sunanka na a cikin bakinsu, amma kana nesa da zuciyarsu. 3 Amma kai, ya Ubangiji, kana sane da ni, kana ganina, Kai kanka kake gwada tunanina. Ka jawo su kamar tumaki zuwa mayanka, Ka ware su domin ranar yanka. 4 Sai yaushe ƙasar za ta daina makoki, Ciyawar kowace saura kuma ta daina yin yaushi? Saboda muguntar mazaunan ƙasar ne dabbobi da tsuntsaye suka ƙare, Domin mutanen suna cewa, “Ba zai ga ƙarshenmu ba.” 5 Ubangiji ya ce, “Idan kai da mutane kun yi tseren ƙafa sun gajiyar da kai, Yaya za ka iya gāsa da dawakai? Idan ka fāɗi a lafiyayyiyar ƙasa, Ƙaƙa za ka yi a kurmin Urdun? 6 Gama har da 'yan'uwanka da gidan mahaifinka, Sun ci amanarka, Suna binka da kuka, Kada ka gaskata su, Ko da ya ke suna faɗa maka maganganu masu daɗi.” 7 Ubangiji ya ce, “Na bar jama'ata. Na rabu da gādona, Na ba da wanda raina ke ƙauna a hannun maƙiyansa. 8 Abin gādona ya zama mini kamar zaki a cikin kurmi, Ya ta da murya gāba da ni, Domin haka na ƙi shi. 9 Ashe, abin gadon nan nawa ya zama dabbare-dabbaren tsuntsun nan ne mai cin nama? Tsuntsaye masu cin nama sun kewaye shi? Tafi, ka tattaro namomin jeji, Ka kawo su su ci. 10 Makiyaya da yawa sun lalatar da gonar inabina. Sun tattake nawa rabo, Sun mai da nawa kyakkyawan rabo kufai da hamada. 11 Sun maishe shi kufai, ba kowa, Yana makoki a gare ni, Ƙasar duka an maishe ta kufai, Amma ba wanda zuciyarsa ta damu a kan wannan. 12 A kan dukan tsaunukan nan na hamada Masu hallakarwa sun zo, Gama takobin Ubangiji yana ta kisa Daga wannan iyakar ƙasa zuwa waccan, Ba mahalukin da yake da salama. 13 Sun shuka alkama, sun girbe ƙayayuwa, Sun gajiyar da kansu, amma ba su amfana da kome ba. Za su sha kunya saboda abin da suke girbe, Saboda zafin fushin Ubangiji.” 14 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan mugayen maƙwabtan Isra'ila waɗanda suka taɓa gādon da ya ba jama'arsa Isra'ila su gada. “Saboda haka zan tumɓuke su daga cikin ƙasarsu. Zan kuma tumɓuke mutanen Yahuza daga cikinsu. 15 Bayan na tumɓuke su kuma, zan sāke yi musu jinƙai, in komar da su, kowanne zuwa gādonsa. 16 Zai zama kuwa, idan za su himmantu su koyi al'amuran jama'ata, su yi rantsuwa da sunana, su ce, ‘Da zatin Ubangiji,’ kamar yadda suka koya wa jama'ata yin rantsuwa da Ba'al, sa'an nan za a gina su a tsakiyar jama'ata. 17 Amma idan wata al'umma za ta ƙi kasa kunne, to, sai in tumɓuke ta ɗungum, in hallaka ta, in ji Ubangiji.”

Irmiya 13

Misali da Abin Ɗamara

1 Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, ya ce, “Tafi ka sayo lilin na yin ɗamara, ka sha ɗamara da shi kada kuwa ka tsoma shi a ruwa.” 2 Sai na sayo abin ɗamara kamar yadda Ubangiji ya ce, na sha ɗamara da shi. 3 Ubangiji kuma ya sāke yin magana da ni sau na biyu, 4 ya ce, “Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi Kogin Yufiretis, ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.” 5 Sai na tafi, na ɓoye shi a Yufiretis kamar yadda Ubangiji ya umarce ni. 6 Bayan an ɗan daɗe, sai Ubangiji ya ce mini, “Tashi, ka tafi Yufiretis, ka ɗauko abin ɗamara wanda na umarce ka ka ɓoye a can.” 7 Sai na tafi Yufiretis, na haƙa na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi. Amma abin ɗamara ya lalace, ba shi da sauran amfani. 8 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 9 “Haka zan lalatar da alfarmar Yahuza da yawan alfarmar Urushalima. 10 Wannan muguwar jama'a, wadda ta ƙi jin maganata, wadda ta taurare, ta bi son zuciyarta, ta kuma bi gumaka ta bauta musu, ta yi musu sujada, za ta zama kamar abin ɗamaran nan, wanda ba shi da sauran amfani. 11 Gama kamar yadda abin ɗamara yakan kame tam a gindin mutum, haka na sa dukan mutanen Isra'ila da dukan mutanen Yahuza su manne mini domin su zama jama'a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.”

Misali da Tulun Ruwan Inabi

12 “Sai ka faɗa musu wannan magana cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce, a cika kowane tulu da ruwan inabi.’ Su kuwa za su ce maka, sun sani sarai za a cika kowane tulu da ruwan inabi. 13 Sa'an nan za ka faɗa musu, Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan sa dukan mazaunan ƙasar su bugu da ruwan inabi, wato sarakunan da suka hau gadon sarautar Dawuda, da firistoci, da annabawa, da dukan mazaunan Urushalima. 14 Zan sa su kara da junansu, iyaye maza da 'ya'yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi, ko juyayi, ko jinƙai ba za su sa in fasa hallaka su duka ba.’ ”

Yahuza bai Tuba ba, za a Kai shi Zaman Talala

15 Ku kasa kunne, ku ji, Kada ku yi girmankai, gama Ubangiji ya yi magana. 16 Ku girmama Ubangiji Allahnku, Kafin ya kawo duhu, Kafin kuma ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan dutse, da duhu duhu, Sa'ad da kuke neman haske, sai ya maishe shi duhu, Ya maishe shi duhu baƙi ƙirin. 17 Amma idan ba za ku ji ba, Raina zai yi kuka a ɓoye saboda girmankanku, Idanuna za su yi kuka ƙwarai, za su zub da hawaye, Domin an kai garken Ubangiji zuwa bauta. 18 Ubangiji ya ce wa Irmiya, “Ka faɗa wa sarki da sarauniya, uwarsa, su sauka daga gadon sarautarsu, Domin an tuɓe kyakkyawan rawanin sarautarsu daga kansu. 19 An kulle biranen Negeb, Ba wanda zai buɗe su, Yahuza duka an kai ta zaman dole, Dukanta an kai ta zaman dole. 20 “Ku ta da idanunku, ku ga waɗanda ke zuwa daga arewa! Ina kyakkyawan garken nan da aka ba ku? 21 Me za ku ce sa'ad da aka naɗa muku shugabanni, Waɗanda ku da kanku kuka koya musu, suka zama abokanku? Ashe, azabai ba za su auko muku ba Kamar yadda sukan auko wa mace mai naƙuda? 22 Idan kun ce a zuciyarku, ‘Me ya sa waɗannan abubuwa suka same mu?’ Saboda yawan zunubanku ne, Shi ya sa an tone tsiraicinku, Aka wahalshe ku. 23 Mutumin Habasha zai iya sāke launin fatar jikinsa? Ko kuwa damisa za ta iya sāke dabbare-dabbarenta? Idan haka ne, ku kuma za ku iya yin nagarta, Ku da kuka saba da yin mugunta. 24 Zan warwatsar da ku Kamar yadda iskar hamada ke watsar da ƙaiƙayi.” 25 Ubangiji ya ce, “Wannan shi ne rabonku, Rabon da na auna muku, ni Ubangiji na faɗa. Domin kun manta da ni, kun dogara ga ƙarairayi, 26 Ni kaina kuma zan kware muku suturarku ta rufe fuskarku Don a ga tsiraicinku. 27 Na ga abubuwanku masu banƙyama, Wato zinace-zinacenku, da haniniya kamar dawakai, Da muguwar sha'awarku ta karuwanci a kan tuddai da filaye, Ya Urushalima, taki ta ƙare! Har yaushe za a tsarkake ki?”

Irmiya 14

Babban Fari

1 Maganar da Ubangiji ya yi wa Irmiya a kan fari ke nan, 2 “Yahuza tana makoki, Ƙofofin biranenta suna lalacewa, Mutanenta suna kwance a ƙasa, suna makoki, Urushalima tana kuka da babbar murya. 3 Manyan mutanenta sun aiki barorinsu su ɗebo ruwa. Da suka je maɓuɓɓuga, sai suka tarar ba ruwa. Sai suka koma da tulunansu hakanan, An kunyatar da su, an ƙasƙantar da su, Suka lulluɓe kansu don kunya. 4 Saboda ƙasar ta bushe, Tun da ba a yi ruwa a kanta ba, Manoma sun sha kunya, Suka lulluɓe kansu don kunya. 5 Barewa ma a saura takan gudu, Ta bar ɗanta sabon haihuwa, Domin ba ciyawa. 6 Jakunan jeji suna tsaye a kan tuddan da ba ciyawa, Suna haki kamar diloli, Idanunsu ba su gani Domin ba abinci.” 7 Irmiya ya ce, “Ko da ya ke zunubanmu su ne shaidunmu, Ya Ubangiji, ka yi taimako saboda sunanka! Gama kāsawarmu ta yi yawa, Domin mun yi maka zunubi. 8 Ya kai, wanda kake begen Isra'ila, Mai Cetonta a lokacin wahala, Ƙaƙa ka zama kamar baƙo a ƙasar? Kamar matafiyi wanda ya kafa alfarwarsa a gefen hanya don ya kwana, ya wuce? 9 Ƙaƙa ka zama kamar wanda bai san abin da zai yi ba, Kamar jarumin da ya kasa yin ceto? Duk da haka, ya Ubangiji, kana nan a tsakiyarmu. Da sunanka ake kiranmu, Kada ka bar mu!” 10 Haka Ubangiji ya ce a kan waɗannan mutane, “Sun cika son yawaceyawace, ba su iya zama wuri ɗaya, don haka ni Ubangiji, ban yarda da su ba, zan tuna da laifofinsu in hukunta zunubansu.” 11 Sai Ubangiji ya ce mini, “Kada ka yi addu'a domin lafiyar jama'an nan. 12 Ko da sun yi azumi, ba zan ji kukansu ba, ko da sun miƙa hadaya ta ƙonawa da hadaya ta sha, ba zan karɓe su ba. Amma zan hallaka su da takobi, da yunwa, da annoba.” 13 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, ga shi, annabawa sun faɗa musu, sun ce, ‘Ba za ku ga takobi ko yunwa ba, amma zan ba ku dawwamammiyar salama a wannan wuri.’ ” 14 Ubangiji kuwa ya ce mini, “Annabawa, annabcin ƙarya suka yi da sunana. Ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba, ban kuma yi magana da su ba. Annabcin da suke yi muku na wahayin ƙarya ne, dubar da suke yi marar amfani ce, tunaninsu ne kawai. 15 Domin haka ga abin da ni Ubangiji na ce a kan annabawan da ke yin annabci da sunana, ko da ya ke ban aike su ba, waɗanda suke cewa, ‘Takobi da yunwa ba za su shigo ƙasan nan ba.’ Za a hallaka su da takobi da yunwa. 16 Mutanen da suka yi wa annabci, za a jefar da su waje a kan titunan Urushalima, a karkashe su da yunwa da takobi, ba wanda zai binne su, da su, da matansu, da 'ya'yansu mata da maza. Zan sa muguntarsu ta koma kansu. 17 “Irmiya, ka faɗa wa mutanen baƙin ciki da ya same ka, Ka ce, ‘Bari idanuna su yi ta zub da hawaye dare da rana, Kada su daina, saboda an buge budurwa, 'yar jama'ata, An yi mata babban rauni da d�ka mai tsanani. 18 Idan na tafi cikin saura, Sai in ga waɗanda aka kashe da takobi! Idan kuma na shiga birni, Sai in ga waɗanda ke ta fama da yunwa! Gama annabi da firist, sai harkarsu suke ta yi a ƙasar, Amma ba su san abin da suke yi ba.’ ”

Mutane Sun Roƙi Ubangiji

19 “Ka ƙi Yahuza ke nan ɗungum? Ranka kuma yana jin ƙyamar Sihiyona ne? Me ya sa ka buge mu, har da ba za mu iya warkewa ba? Mun zuba ido ga samun salama, amma ba wani abin alheri da ya zo. Mun kuma sa zuciya ga warkewa, amma sai ga razana. 20 Mun san muguntar da muka yi, ya Ubangiji, Da wadda kakanninmu suka yi, Gama mun yi maka zunubi. 21 Saboda darajar sunanka, kada ka wulakanta mu, Kada kuma ka ƙasƙantar da darajar kursiyinka, Ka tuna da alkawarin da ka yi mana, Kada ka ta da shi. 22 A cikin gumakan al'ummai akwai mai iya sa a yi ruwa? Sammai kuma su yi yayyafi? Ashe, ba kai ne ba, ya Ubangiji Allahnmu? Domin haka a gare ka muke sa zuciya, Gama kai ne mai yin waɗannan abubuwa duka.”

Irmiya 15

Fushin Ubangiji da Yahuza bai Huce Ba

1 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ko da a ce Musa da Sama'ila za su tsaya a gabana, duk da haka zuciyata ba za ta komo wurin mutanen nan ba. Ka kore su daga gabana su yi tafiyarsu! 2 Sa'ad da suka tambaye ka, ‘Ina za mu tafi?’ Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce, ‘Waɗanda suke na annoba, su tafi ga annoba! Waɗanda suke na takobi, su tafi ga takobi! Waɗanda suke na yunwa, su tafi ga yunwa! Waɗanda suke na bauta, su tafi ga bauta!’ 3 Zan sa musu masu hallakarwa huɗu,” in ji Ubangiji, “Da takobi don kisa, da karnuka don yayyagawa, da tsuntsayen sararin sama, da dabbobin duniya don su cinye, su hallakar. 4 Zan kuma sa su zama abin banƙyama ga dukan mulkokin duniya saboda abin da Manassa ɗan Hezekiya, Sarkin Yahuza ya aikata a Urushalima. 5 “Wa zai ji tausayinki, ya Urushalima? Wa zai yi baƙin ciki dominki? Wa kuma zai ratso wurinki don ya tambayi lafiyarki? 6 Ni Ubangiji na ce, kun ƙi ni, kuna ta komawa da baya, Don haka na nuna ikona gāba da ku, na hallaka ku, Na gaji da jin tausayinku! 7 Na sheƙe su da abin sheƙewa a ƙofofin garuruwan ƙasar. Na sa 'ya'yansu su mutu, na hallaka mutanena, Ba su daina yin mugayen ayyukansu ba. 8 Na yawaita gwauraye, wato mata da mazansu suka mutu, Fiye da yashin teku. Na kawo wa uwayen samari mai hallakarwa da tsakar rana. Na sa azaba da razana su auka musu farat ɗaya. 9 Ita wadda ta haifi 'ya'ya bakwai ta yi yaushi ta suma, Ranarta ta faɗi tun lokaci bai yi ba, An kunyatar da ita, an wulakantar da ita. Waɗanda suka ragu daga cikinsu Zan bashe su ga takobi gaban abokan gābansu. Ni Ubangiji na faɗa.” 10 Kaitona, ya mahaifiyata, da kika haife ni, mai jayayya mai gardama da kowa cikin dukan ƙasar! Ban ba da rance ba, ba kuma wanda ya ba ni rance, duk da haka dukansu suna zagina. 11 Ubangiji ya ce mini, “Zan keɓe ka domin alheri, hakika zan sa abokan gaba su yi roƙo gare ka a lokacin bala'i da kuma lokacin damuwa. 12 Wa zai iya karya ƙarfe ko tagulla daga arewa?” 13 Ubangiji ya ce mini, “Zan ba da wadatarku da dukiyarku ganima kyauta, saboda dukan zunubanku a dukan ƙasar. 14 Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama fushina ya kama kamar wuta, zai yi ta ci har abada.” 15 Sa'an nan Irmiya ya ce, “Ya Ubangiji, ka sani. Kai ne, ka ziyarce ni, Ka kuma sāka wa waɗanda ke tsananta mini. Ka sani saboda kai nake shan zargi. 16 Maganarka da na samu na ci. Maganarka kuwa ta zama abar murna a gare ni, Ta faranta mini zuciya. Gama ana kirana da sunanka, Ya Ubangiji Allah Mai Runduna. 17 Ban zauna cikin ƙungiyar masu annashuwa ba. Ban kuwa yi murna ba, Na zauna ni kaɗai saboda kana tare da ni, Gama ka sa na cika da haushi. 18 Me ya sa azabata ta ƙi ƙarewa, Raunukana kuma ba su warkuwa, Sun kuwa ƙi warkewa? Za ka yaudare ni kamar rafi, Ko kamar ruwa mai ƙafewa?” 19 “Domin haka ga abin da ni, Ubangiji na ce, Idan ka komo sa'an nan zan kawo ka. Za ka tsaya a gabana. Idan ka hurta abin da yake gaskiya ba na ƙarya ba, Za ka zama kakakina. Za su komo gare ka, Amma kai ba za ka koma wurinsu ba. 20 Zan maishe ka garun tagulla saboda waɗannan mutane, Za su yi yaƙi da kai, amma ba za su yi nasara a kanka ba, Gama ina tare da kai don in cece ka, in kuɓutar da kai. 21 Zan kuɓutar da kai daga hannun mugaye, Zan ɓamɓare ka daga hannun marasa tausayi.”

Irmiya 16

Umarnin Ubangiji zuwa ga Irmiya

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ba za ka yi aure ka haifi 'ya'ya mata da maza a wannan wuri ba. 3 Ga abin da ni Ubangiji na faɗa a kan 'ya'ya mata da maza da aka haifa a wannan wuri, da kuma a kan iyayensu mata da maza da suka haife su a wannan ƙasa, 4 za su mutu da muguwar cuta. Ba za a yi makoki dominsu ba, ba kuwa za a binne su ba. Za su zama juji. Takobi da yunwa za su kashe su, gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji.” 5 Ubangiji kuma ya ce, “Kada ka shiga gidan da ake makoki, ko ka tafi inda ake baƙin ciki, kada ka yi baƙin ciki saboda su, gama na ɗauke salamata, da ƙaunata, da jinƙaina daga wurin jama'an nan. 6 Yaro da babba za su mutu a wannan ƙasa, ba za a binne su ba, ba kuwa za a yi baƙin ciki dominsu ba. Ba kuwa wanda zai tsaga jikinsa ko ya aske kansa ƙwal dominsu. 7 Ba wanda zai ba mai makoki abinci don ya ta'azantar da shi saboda mamacin, ba kuma wanda zai ba shi abin sha don ya ta'azantar da shi saboda mahaifinsa ko mahaifiyarsa. 8 “Kada kuma ka shiga gidan da ake biki, ka zauna ka ci ka sha tare da su. 9 Gama ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, zan sa muryar murna, da ta farin ciki, da ta ango, da ta amarya, su ƙare a wurin nan a idonka da zamaninka. 10 “Sa'ad da ka faɗa wa mutanen nan wannan magana duka, za su kuwa ce maka, ‘Me ya sa Ubangiji ya hurta wannan babbar masifa a kanmu? Menene laifinmu? Wane irin zunubi muka yi wa Ubangiji Allahnmu?’ 11 Sai ka faɗa musu cewa, Ubangiji ya ce, ‘Domin kakanninku sun rabu da ni, sun bi gumaka, sun bauta musu, sun yi musu sujada. Sun rabu da ni, sun ƙi kiyaye dokokina. 12 Ku kuma kun yi laifi fiye da na kakanninku. Kowannenku kuwa ya bi tattauran mugun nufin zuciyarsa, yana ƙin kasa kunne gare ni. 13 Don haka zan fitar da ku daga wannan ƙasa zuwa wata ƙasa wadda ku ko kakanninku ba ku sani ba. A can za ku bauta wa gumaka dare da rana, gama ba zan nuna muku ƙauna ba.’ 14 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “Da ba za a ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama'ar Isra'ila daga ƙasar Masar ba.’ 15 Amma za a ce, ‘Na rantse da Ubangiji wanda ya fito da jama'ar Isra'ila daga ƙasar arewa, da kuma daga dukan ƙasashe da ya kora su,’ gama zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu. 16 “Ga shi, ina aiko da masunta da yawa,” in ji Ubangiji, “Za su kuwa kama su, daga baya kuma zan aika da mafarauta da yawa, za su farauce su daga kowane tsauni, da tudu, da kogwannin duwatsu. 17 Gama ina ganin dukan ayyukansu, ba a ɓoye suke a gare ni ba, muguntarsu kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. 18 Zan riɓaɓɓanya sakayyar da zan yi musu saboda muguntarsu da zunubinsu, domin sun ƙazantar da ƙasata da ƙazantattun gumakansu marasa rai, abin gādona kuma sun cika shi da abubuwansu na banƙyama.”

Addu'ar Irmiya ta Dogara ga Allah

19 “Ya Ubangiji, ƙarfina da kagarata, Mafakata a ranar wahala, A gare ka al'ummai za su zo, Daga ƙurewar duniya, su ce, ‘Kakanninmu ba su gāji kome ba, sai ƙarya, Da abubuwan banza marasa amfani.’ 20 Mutum zai iya yi wa kansa alloli? Ai, waɗannan ba alloli ba ne!” 21 Ubangiji ya ce, “Saboda haka, ga shi, zan sa su sani, Sau ɗayan nan kaɗai zan sa su su san ikona da ƙarfina, Za su kuma sani sunana Ubangiji ne.”

Irmiya 17

Zunubin Yahuza ya yi Kanta

1 Ubangiji ya ce, “An rubuta zunubin mutanen Yahuza da alƙalamin ƙarfe, mai bakin yakutu. An zana shi a allon zuciyarsu da a zankayen bagadansu. 2 Idan sun tuna da 'ya'yansu haka sun tuna da bagadansu da Ashtarot ɗinsu a gindin itatuwa masu duhuwa da kan tuddai masu tsayi. 3 Ku mazauna a tsaunuka da cikin saura, zan ba da dukiyarku da wadatarku ganima saboda dukan zunuban da kuka yi a dukan ƙasar. 4 Za ku rasa abin da ke hannunku daga cikin gādon da na ba ku. Zan sa ku bauta wa abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, gama da fushina wuta ta kama wadda za ta yi ta ci har abada.” 5 Ubangiji ya ce, “La'ananne ne mutumin da ke dogara ga mutum, Wanda jiki ne makaminsa, Wanda ya juya wa Ubangiji baya, 6 Gama yana kama da sagagi a hamada, Ba zai ga wani abu mai kyau yana zuwa ba. Zai zauna a busassun wuraren hamada, A ƙasar gishiri, inda ba kowa. 7 “Mai albarka ne mutumin da ke dogara ga Ubangiji, Wanda Ubangiji ne madogararsa. 8 Shi kamar itace ne wanda ake dasa a bakin rafi Wanda ke miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafin, Ba zai ji tsoron rani ba, Kullum ganyensa kore ne, Ba zai damu a lokacin fari ba, Ba zai ko fasa yin 'ya'ya ba. 9 “Zuciya ta fi kome rikici, Cuta gare ta matuƙa, Wa zai san kanta? 10 Ni Ubangiji nakan bincike tunani, In gwada zuciya, Domin in sāka wa kowane mutum gwargwadon al'amuransa, Da kuma gwargwadon ayyukansa. 11 “Kamar makwarwar da ta kwanta kan ƙwan da ba ita ta nasa ba, Haka yake ga wanda ya sami dukiyar haram, Yana gaɓar ƙarfinsa, za ta rabu da shi, A ƙarshe zai zama wawa.” 12 Kursiyi mai daraja, Da aka sa a bisa tun daga farko, Wurin ke nan inda Haikalinmu yake. 13 Ya Ubangiji, begen Isra'ila, Duk waɗanda suka rabu da kai, za su sha kunya. Waɗanda suka ba ka baya a duniya za a rubuta su Domin sun rabu da Ubangiji, maɓuɓɓugar ruwan rai.

Irmiya ya Roƙi Ubangiji ya Kiyaye Shi

14 Ubangiji, ka warkar da ni, zan kuwa warke, Ka cece ni, zan kuwa cetu, Gama kai ne abin yabona. 15 Ga shi, suna ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Ta zo mana!” 16 Amma ni ban yi gudun zaman makiyayi a gabanka ba, Ban kuma so zuwan ranar bala'i ba, Ka kuwa sani. Abin da ya fito daga bakina kuwa, A bayyane yake gare ka. 17 Kada ka zamar mini abin razana, Kai ne mafakata cikin ranar masifa, 18 Bari waɗanda suka tsananta mini su sha kunya, Amma kada ka bar ni in kunyata. Bari su tsorata, Amma kada ka bar ni in tsorata. Ka aukar musu da ranar masifa, Ka hallaka su riɓi biyu!

A kan Kiyaye Ranar Asabar

19 Haka Ubangiji ya ce mini, “Ka tafi ka tsaya a ƙofar Biliyaminu, wadda sarakunan Yahuza ke shiga da fita ta cikinta, ka kuma tafi dukan ƙofofin Urushalima. 20 Ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuza, da dukan Yahuza, da dukan mazaunan Urushalima, waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi. 21 Haka Ubangiji ya ce, ku yi hankali saboda rayukanku, kada ku ɗauki kaya a ranar Asabar, ko ku shigar da kowane abu ta ƙofofin Urushalima. 22 Kada ku ɗauki kaya, ku fita da shi daga gidajenku a ranar, ko ku yi kowane irin aiki, amma ku kiyaye ranar Asabar da tsarki, kamar yadda na umarci kakanninku.’ 23 Amma duk da haka ba su kasa kunne, ko su mai da hankali ba. Amma suka taurare don kada su ji, su karɓi koyarwa. 24 “ ‘Amma idan kun kasa kunne gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofin wannan birni a ranar Asabar ba, amma kuka kiyaye ranar Asabar da tsarki, ba ku yi aiki a cikinta ba, 25 sa'an nan ne sarakuna waɗanda za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda, za su shiga ta ƙofofin wannan birni, suna hawan karusai, da dawakai, su da sarakunansu, da jama'ar Yahuza da mazaunan Urushalima. Za a zauna a wannan birni har abada. 26 Mutane za su zo daga biranen Yahuza da wuraren da ke kewaye da Urushalima, daga ƙasar Biliyaminu, da ta Shefela, da ta ƙasar tuddai, da kuma ta Negeb, suna kawo hadayu na ƙonawa da sadakoki, da hadayu na sha, da na turare, za su kuma kawo hadayu na godiya a Haikalin Ubangiji. 27 Amma idan ba ku kasa kunne gare ni ba, ba ku kuwa kiyaye ranar Asabar da tsarki ba, kun kuma ɗauki kaya kun shiga ta ƙofofin Urushalima a ranar Asabar, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wuta. Za ta kuwa cinye fādodin Urushalima, ba kuwa za ta kasu ba.’ ”

Irmiya 18

Irmiya a Gidan Maginin Tukwane

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce, 2 “Ka tashi, ka gangara zuwa gidan maginin tukwane, a can zan yi maka magana.” 3 Sai na gangara zuwa gidan maginin tukwanen, na iske shi yana ginin tukwane a kan na'urar ginin tukwanen. 4 Abin da yake ginawa ya lalace a hannunsa, sai ya sāke gina wani abu dabam da yumɓu ɗin, yadda ya ga dama. 5 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, 6 “Ya jama'ar Isra'ila, ashe, ba zan yi da ku kamar yadda maginin tukwanen nan ya yi ba? Duba, kamar yadda yumɓu yake a hannun maginin tukwane, haka kuke a hannuna, ya ku jama'ar Isra'ila. 7 A duk lokacin da na ce zan tumɓuke, in kakkarya in hallaka wata al'umma, ko wani mulki, 8 idan wannan al'umma da na yi magana a kanta, ta juyo, ta tuba daga mugayen ayyukanta, zan janye masifar da na yi niyyar aukar mata. 9 A duk kuma lokacin da na ce zan gina, in kafa wata al'umma, ko wani mulki, 10 amma idan al'ummar ta aikata mugunta a gabana, ta ƙi saurarawa ga maganar, zan janye alherin da na yi niyyar yi mata. 11 Saboda haka yanzu, sai ka faɗa wa jama'ar Yahuza da mazaunan Urushalima, ka ce, haka Ubangiji ya faɗa, ‘Ga shi, na shirya muku masifa, ina tsara wahalar da za ta same ku. Bari kowannenku ya koma ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara al'amuransa da ayyukansa.’ 12 Amma za su ce, ‘Wannan ba abin da za mu kula da shi ba ne, mu ra'ayinmu za mu bi, kowannenmu kuwa zai yi bisa ga nufin tattaurar muguwar zuciyarsa.’ 13 “Domin haka ni Ubangiji na ce, ‘Ka tambayi sauran al'umma. Wa ya taɓa jin irin wannan? Budurwa Isra'ila, ta yi mugun abu ƙwarai! 14 Dusar ƙanƙara mai danshi ta taɓa rabuwa da tsaunukan Lebanon? Ko ruwan rafuffuka mai sanyi na kan dutse ya taɓa ƙonawa? 15 Amma mutanena sun manta da ni, Sun ƙona wa gumaka turare. Sun yi tuntuɓe a cikin al'amuransu, a hanyoyin dā, Sun bi ɓarayin hanyoyi, ba su bi karauka ba. 16 Sun mai da ƙasarsu abar banƙyama, Abin raini har abada. Duk wanda ya wuce ta wurin zai razana ya kaɗa kansa. 17 Haka zan warwatsa su Kamar yadda iskar gabas ke yi, a gaban abokan gābansu, Zan juya musu baya, ba za su ga fuskata ba, A ranar masifarsu.’ ”

Maƙarƙashiyar Mutane da Addu'ar Irmiya

18 Sa'an nan suka ce, “Zo mu shirya wa Irmiya maƙarƙashiya, gama firist ba zai bar bin shari'a ba. Hakanan ma masu hikima ba za su bar yin shawara ba, hakanan kuma annabi ba zai bar yin magana ba! Ku zo mu kai ƙararsa, kada mu kula da abin da zai faɗa.” 19 Irmiya kuwa ya yi addu'a ya ce, “Ya Ubangiji, ka kasa kunne gare ni, ka ji ƙarar maƙiyana! 20 Daidai ne a rama alheri da mugunta? Duk da haka sun kafa wa raina tarko. Ka tuna yadda na tsaya a gabanka, Na yi maganar alheri a kansu, Domin ka janye fushinka daga gare su. 21 Saboda haka ka kawo wa 'ya'yansu yunwa, Ka bashe su ga takobi, Bari matansu su rasa 'ya'ya, mazansu su mutu, Ka sa annoba ta kashe mazansu, A kashe samarinsu da takobi a yaƙi. 22 Bari a ji kururuwa daga gidajensu, Saboda maharan da ka aika musu farat ɗaya, Gama sun haƙa rami don in fāɗa, Sun kafa wa ƙafafuna tarkuna. 23 Amma ya Ubangiji, Ka san dukan maƙarƙashiyarsu, su kashe ni, Kada ka gafarta musu muguntarsu, kada kuma ka shafe zunubinsu daga gabanka. Ka sa a jefar da su daga gabanka, Ka yi da su sa'ad da kake fushi!”

Irmiya 19

Fasasshen Tulu

1 Ubangiji ya ce mini, “Tafi ka sayo tulu a wurin maginin tukwane. Sa'an nan kuma ka ɗauki waɗansu daga cikin dattawan jama'a, da waɗansu manyan firistoci, 2 ku tafi kwarin ɗan Hinnom na mashigin Ƙofar Kasko, ka yi shelar maganar da zan faɗa maka a can. 3 Za ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ya ku sarakunan Yahuza da mazaunan Urushalima, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, zan kawo wata irin masifa a wannan wuri, wanda duk ya ji, kunnuwansa za su kaɗa. 4 Ga shi, mutanen nan sun rabu da ni, sun ƙazantar da wannan wuri sun ƙona wa gumaka turare, waɗanda su, ko kakanninsu, ko sarakunan Yahuza, ba su san su ba. Sun cika wannan wuri da jinin marasa laifi. 5 Sun gina wa Ba'al masujadai don su miƙa masa 'ya'yansu maza hadayar ƙonawa, abin da ban umarta ba, ban kuma ba da izni ba, ban ma yi tunanin haka ba. 6 Saboda haka rana tana zuwa da ba za a ƙara ce da wannan wuri Tofet, ko kwarin ɗan Hinnom ba, amma za a ce da shi Kwarin Kisa. 7 A wannan wuri zan wofinta dabarun Yahuza da na Urushalima, zan sa a kashe jama'arsu da takobi, a gaban abokan gābansu, ta hannun waɗanda ke neman ransu. Zan ba da gawawwakinsu su zama abincin tsuntsayen sararin sama da na namomin jeji. 8 Zan mai da wannan birni abin ƙyama, abin raini, dukan wanda ya wuce wurin zai yi mamaki, ya yi tsaki saboda dukan masifun da suka auka wa birnin. 9 Zan sa su ci naman 'ya'yansu mata da maza. Kowa zai ci naman maƙwabcinsa cikin damuwa a lokacin da za a kewaye su da yaƙi, zai sha wahala daga wurin abokan gābansa da waɗanda ke neman ransa.’ 10 “Sa'an nan sai ka fasa tulun a gaban mutanen da suka tafi tare da kai, 11 ka kuwa ce musu, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, haka zai farfasa jama'a, da wannan birni kamar yadda aka fashe tulun maginin tukwanen, ba kuwa zai gyaru ba. Za a binne mutane a Tofet domin za a rasa makabartar da za a binne su. 12 Haka zai yi wa wurin nan da mazauna cikinsa, ya mai da birnin nan kamar Tofet. 13 Gidajen Urushalima da gidajen sarakunan Yahuza da dukan gidaje waɗanda a kan rufinsu aka ƙona wa rundunar sararin sama turare, aka zuba wa gumaka hadayu na sha, za su ƙazantu kamar Tofet.’ ” 14 Sa'an nan Irmiya ya komo daga Tofet, inda Ubangiji ya aike shi don ya yi annabci, sai ya tsaya a fili na Haikalin Ubangiji, ya ce wa dukan jama'a, 15 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Ga shi, ina aukar wa wannan birni da dukan garuruwansa dukan masifu da na ambata a kansa, domin sun taurare zukatansu, sun ƙi jin maganata.’ ”

Irmiya 20

Saɓani Tsakanin Irmiya da Fashur Firist

1 Sa'ad da Fashur, firist, ɗan Immer, shugaban Haikalin Ubangiji ya ji Irmiya yana annabci a kan waɗannan abubuwa, 2 sai ya sa aka yi wa Irmiya d�ka, aka kuma sa shi cikin turu a ƙofar Biliyaminu, a Haikalin Ubangiji. 3 Kashegari sa'ad da Fashur ya fitar da Irmiya daga turu, sai Irmiya ya ce masa, “Ubangiji ba zai kira ka Fashur ba, amma ya ba ka suna Magormissabib, wato razana ta kowace fuska. 4 Haka Ubangiji ya ce, ‘Ga shi, zan maishe ka abin tsoro ga kai kanka, da dukan abokanka. Abokan gābansu za su kashe su da takobi a kan idonka. Zan ba da dukan Yahuza a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai kwashe waɗansu ya kai bautar talala a Babila, ya kuma kashe waɗansu da takobi. 5 Banda haka kuma zan ba da dukan dukiyar wannan birni, da dukan ribarsa, da dukan abubuwa masu tamani, da dukan dukiyar sarakunan Yahuza, ga abokan gābansu, waɗanda za su washe su, su kama su, su kai Babila. 6 Kai kuma, Fashur, da dukan waɗanda ke a gidanka, za ku tafi bauta a Babila, za ku shiga Babila, a can za ku mutu, a can za a binne ku, kai da abokanka waɗanda ka yi wa annabcin ƙarya.’ ”

Kukan Irmiya

7 “Ya Ubangiji ka ruɗe ni, na kuwa ruɗu, Ka fi ni ƙarfi, ka kuwa rinjaye ni. Na zama abin dariya dukan yini, Kowa yana ta yi mini ba'a. 8 Duk lokacin da zan yi magana, Nakan ta da murya in yi magana da ƙarfi cewa, ‘Hargitsi da hallakarwa!’ Gama saboda maganar Ubangiji na zama abin zargi, Da abin ba'a dukan yini. 9 Idan na ce, ‘Ba zan ambaci Ubangiji ba, Ban zan ƙara yin magana da sunansa ba,’ Sai in ji damuwa a zuciyata, An kulle ta a ƙasusuwana, Na gaji da danne ta a cikina, Ba zan iya jurewa ba. 10 Na ji mutane da yawa suna sa mini laƙabi cewa, ‘Razana ta kowace fuska,’ Suna cewa, ‘Mu la'anta shi! Mu la'anta shi!’ Har ma da abokaina shaƙiƙai Suna jira su ga fāɗuwata. Suka ce, ‘Watakila a ruɗe shi, Sa'an nan ma iya rinjayarsa Mu ɗauki fansa a kansa.’ 11 Amma Ubangiji kana tare da ni Kamar jarumi mai bantsoro, Don haka masu tsananta mini za su yi tuntuɓe, Ba za su rinjaye ni ba. Za su sha kunya ƙwarai, Gama ba za su yi nasara ba. Ba za a manta da su ba. 12 Ya Ubangiji Mai Runduna, mai gwada adali, Mai ganin zuciya duk da tunani, Ka sa in ga sakayyar da za ka yi musu, Gama a gare ka nake kawo ƙarata.” 13 Ku raira waƙa ga Ubangiji! Ku yabi Ubangiji! Gama ya kuɓutar da ran mabukaci daga hannun mugaye. 14 La'ananniya ce ranar da aka haife ni, Kada ranar da uwata ta haife ni ta yi albarka! 15 La'ananne ne mutum da ya kai wa mahaifina labari Cewa, “An haifa maka ɗa,” don ya sa shi farin ciki. 16 Bari wannan mutum ya zama kamar biranen da Ubangiji ya kaɓantar ba tausayi. Bari ya ji kuka da safe, Da rana kuma ya ji gangamin yaƙi, 17 Domin bai kashe ni tun ina ciki ba. Da ma cikin uwata ya zama mini kabari, In yi ta kwanciya a ciki har abada. 18 Me ya sa na fito daga cikin mahaifa, Don in ga wahala da baƙin ciki, Don kwanakin raina su ƙare da kunya?

Irmiya 21

An yi Faɗi a kan Faɗuwar Urushalima

1 Wannan ita ce maganar Ubangiji wadda ya faɗa wa Irmiya sa'ad da sarki Zadakiya ya aiki Fashur ɗan Malkiya, da Zafaniya firist, ɗan Ma'aseya, wurin Irmiya cewa, 2 “Ka tambayar mana Ubangiji, gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kawo mana yaƙi. Ko Ubangiji zai yi mana al'amuran nan nasa masu ban al'ajabi kamar yadda ya saba, ya sa Sarkin Babila ya janye, ya rabu da mu?” 3 Sai Irmiya ya ce musu, 4 “Ku faɗa wa Zadakiya, Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce, ‘Ga shi, zan juyo kayan yaƙin da ke hannunka waɗanda kake yaƙi da su gāba da Sarkin Babila, da sojojinsa, waɗanda suka kewaye garun birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan. 5 Ni kaina zan yi yaƙi da kai da dukan ƙarfina, da hasalata, da dukan zafin fushina. 6 Zan kuwa kashe mazaunan birnin nan, mutum da dabba, da babbar annoba. 7 Bayan wannan zan ceci Zadakiya Sarkin Yahuza, shi da bayinsa, da mutanen birnin nan waɗanda suka tsira daga annoba, da takobi, da yunwa, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, da hannun abokan gābansu, da waɗanda suke neman rayukansu. Zai kashe su da takobi, ba zai ji tausayinsu, ko ya rage waɗansunsu, ko ya ji juyayinsu ba.’ 8 “Sai ka faɗa wa wannan jama'a, ka ce, ‘Ni Ubangiji na ce, ga shi, na sa tafarkin rai da na mutuwa a gabanku. 9 Shi wanda ya zauna a birnin nan zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma shi wanda ya fita ya ba da kansa ga Kaldiyawa waɗanda suke kewaye da ku zai rayu ya tserar da ransa. 10 Gama na ƙudura zan kawo wa wannan birni masifa, ba alheri ba. Zan bashe shi a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai ƙone shi da wuta.’ ”

Annabci a kan Sarakunan Yahuza

11 “Sai ka faɗa wa gidan sarautar Yahuza cewa, ‘Ku ji maganar Ubangiji, 12 Ya gidan Dawuda, ni Ubangiji na ce, Ku aikata adalci kowace safiya. Ku ceci wanda aka yi masa ƙwace daga hannun mai matsa masa, Don kada hasalata ta tashi kamar wuta, Ta yi ƙuna, har ba mai iya kashe ta, Saboda mugayen ayyukanku. 13 Ga shi, ina gāba da ku, ya ku mazaunan kwarin, Ya dutsen da ke a fili,’ in ji Ubangiji. ‘Ku da kuke cewa, wa zai iya gangarowa wurinku, Ko kuwa wa zai shiga wurin zamanku? 14 Zan hukunta ku bisa ga ayyukanku,’ in ji Ubangiji, ‘Zan sa wa jejin ƙasar wuta. Za ta cinye duk abin da ke kewaye da ita.’ ”

Irmiya 22

1 Haka Ubangiji ya faɗa, “Ka tafi ka gangara zuwa gidan Sarkin Yahuza, ka faɗi wannan magana a can, 2 ka ce, ‘Ka ji maganar Ubangiji, ya Sarkin Yahuza, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda kai da barorinka, da mutanenka waɗanda ke shiga ta ƙofofin nan. 3 Haka Ubangiji ya ce, ka yi gaskiya da adalci, ka ceci wanda ake masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka cuci baƙo, ko maraya, ko gwauruwa, wato matar da mijinta ya rasu, kada kuma ka zubar da jinin marasa laifi a wannan wuri. 4 Hakika idan ka kiyaye wannan magana, sa'an nan sarakunan da za su zauna a kan gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan gida da karusai da dawakai, su da barorinsu da jama'arsu. 5 Amma idan ba ka kula da waɗannan zantuttuka ba, na rantse da zatina,’ in ji Ubangiji, ‘wannan fāda ta zama kufai.’ ” 6 Abin da Ubangiji ya ce ke nan a kan fādar Sarkin Yahuza, “Kyanta kamar Gileyad take a gare ni, Kamar kuma ƙwanƙolin Lebanon. Duk da haka zan maishe ta hamada, Birnin da ba kowa ciki. 7 Zan shirya waɗanda za su hallaka ta. Kowannensu da makamansa, Za su sassare zaɓaɓɓun itatuwan al'ul ɗinta, a jefa su a wuta. 8 “Al'ummai masu yawa za su wuce ta gefen wannan birni, kowane mutum zai ce wa maƙwabcinsa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’ 9 Za su amsa, su ce, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada ga gumaka, suka bauta musu.’ ” 10 Ku mutanen Yahuza, kada ku yi kuka saboda sarki Yosiya, Kada ku yi makokin rasuwarsa, Amma ku yi kuka ƙwarai saboda ɗansa Yehowahaz. Sun ɗauke shi, sun tafi da shi, ba zai ƙara komowa ba, Ba kuma zai ƙara ganin ƙasar da aka haife shi ba. 11 Gama haka Ubangiji ya ce a kan Yahowahaz, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, wanda ya gāji sarautar ubansa, Yosiya, wanda ya tafi ya bar wurin nan. Ba zai ƙara komowa nan ba. 12 Amma a wurin da suka kai shi zaman talala, a can zai mutu, ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba. 13 Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, Benayensa kuma ta hanyar rashin gaskiya. Wanda ya sa maƙwabcinsa ya yi masa aiki a banza, Bai ba shi hakkinsa ba. 14 Kaiton wanda ya ce, “Zan gina wa kaina babban gida Da waɗansu irin benaye musamman.” Ya yi masa tagogi, Ya manna masa itacen al'ul, Sa'an nan ya yi masa jan shafe. 15 Kana tsammani kai sarki ne, Da ya ke ƙasarka ta itacen al'ul ce? Amma ubanka ya ci, ya sha, Ya yi gaskiya, ya aikata adalci, Ya kuwa zauna lafiya. 16 Ya biya wa matalauta da masu bukata hakkinsu, Ya kuwa yi kyau. Abin da ake nufi da sanina ke nan, In ji Ubangiji. 17 Amma ka sa idonka da zuciyarka ga ƙazamar riba, Da zubar da jinin marar laifi, Da yin zalunci da danniya. 18 Domin haka ga abin da Ubangiji ya ce a kan Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, “Ba za su yi makoki dominsa ba, ko su ce, ‘Wayyo ɗan'uwanmu!’ ko, ‘Wayyo 'yar'uwarmu!’ Ba za su yi makoki dominsa ba, su ce, ‘Wayyo ubangidanmu!’ ko ‘Wayyo mai martaba!’ 19 Za a binne shi kamar jaki, Za a ja shi a yar a bayan ƙofofin Urushalima.” 20 Ku haura zuwa Lebanon, ku yi kuka, Ku ta da muryarku cikin Bashan, Ku yi kuka daga Abarim, Gama an hallakar da dukan ƙaunatattunku. 21 Ubangiji ya yi muku magana a lokacin wadatarku. Amma kun ce, “Ba za mu kasa kunne ba!” Wannan shi ne halinku tun kuna samari, Don ba ku yi biyayya da murya Ubangiji ba. 22 Iska za ta kwashe shugabanninku, Za a kai ƙaunatattunku cikin bauta, Sa'an nan za ku sha kunya ku ruɗe, Saboda dukan muguntarku. 23 Ya ku mazaunan Lebanon, Waɗanda ke zaune cikin itatuwan al'ul, Irin nishin da za ku yi sa'ad da azaba ta same ku, Azaba ce irin ta mace mai naƙuda! 24 “Ni Ubangiji na rantse da raina, ko da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, zoben hatimi ne a yatsan hannun damana, duk da haka zan kwaɓe shi, 25 in bashe shi a hannun waɗanda suke neman ransa, da a hannun wanda yake jin tsoronsa, wato Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da Kaldiyawa. 26 Zan jefar da shi da uwarsa a wata ƙasa inda ba a haife shi ba, a can zai mutu. 27 Amma ƙasan nan da suke marmarin komowa cikinta, ba za su koma cikinta ba.” 28 Ashe, Yekoniya kamar fasasshen tulu yake, Wanda ba wanda ya kula da shi? Me ya sa aka watsar da shi da 'ya'yansa, A ƙasar da ba su sani ba? 29 Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa! Ki ji maganar Ubangiji! 30 Haka Ubangiji ya ce, “Rubuta wannan mutum, marar 'ya'ya. Mutumin da ba zai yi albarka a duk kwanakinsa ba. Gama ba wani daga zuriyarsa Da zai gāji gadon sarautar Dawuda, Ko ya yi mulki kuma a Yahuza.”

Irmiya 23

Komowar waɗanda suka Ragu

1 “Taku ta ƙare! Makiyayan da suka lalatar, suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji. 2 Haka Ubangiji Allah na Isra'ila ya faɗa a kan makiyayan jama'arsa. “Kun warwatsar da garkena kun kore su, ba ku lura da su ba. Ni ma haka zan yi da ku saboda muguntarku, ni Ubangiji na faɗa. 3 Sa'an nan zan tattaro sauran garkena daga wuraren da aka warwatsa su, zan komo da su cikin garkensu, zan sa su hayayyafa su riɓaɓɓanya. 4 Zan sa makiyayan da za su lura da su. Ba kuwa za su ƙara jin tsoro, ko razana ba, ba kuma wanda zai ɓace, ni Ubangiji na faɗa. 5 “Ga shi, ni Ubangiji na ce, kwanaki suna zuwa, Sa'ad da zan tsiro da wani mai adalci daga zuriyar Dawuda Wanda zai ci sarauta. Zai yi sarauta da hikima, Zai aikata abin da ke daidai a ƙasar. 6 A zamaninsa za a ceci Yahuza, Isra'ila kuwa za ta zauna lafiya. Sunan da za a kira shi da shi ke nan, ‘Ubangiji Adalcinmu.’ 7 “Saboda haka, ga shi, kwanaki suna zuwa, ni Ubangiji na faɗa, sa'ad da mutane ba za su ƙara cewa, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da jama'ar Isra'ila daga cikin ƙasar Masar ba,’ 8 amma za su ce, ‘Na rantse da ran Ubangiji wanda ya fito da zuriyar Isra'ila daga ƙasar arewa, daga kuma dukan ƙasashen da ya warwatsa su!’ Sa'an nan za su zauna a ƙasarsu ta kansu.”

Jawabi a kan Annabawan Ƙarya

9 A kan annabawa kuwa, zuciyata ta karai, Dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa, Saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki. Na zama kamar mashayi, wanda ya bugu da ruwan inabi, 10 Gama ƙasar cike take da mazinata, Saboda la'ana, ƙasar za ta yi makoki, Wuraren kiwo na jeji sun bushe, Manufarsu mugunta ce, Ba su mori ƙarfinsu a inda ya kamata ba. 11 “Annabi da firist, dukansu biyu marasa tsoron Allah ne, Har a cikin Haikalina na tarar da muguntarsu.” Ubangiji ya faɗa. 12 “Saboda haka hanyarsu za ta zama da santsi da duhu, Inda za a runtume su, su fāɗi. Gama zai kawo musu masifa a shekarar da za su sha hukuncinsu.” Ubangiji ya faɗa. 13 “A cikin annabawan Samariya, Na ga abu marar kyan gani. Da sunan Ba'al suke yin annabci, Suna ɓad da jama'ata Isra'ila 14 Amma cikin annabawa na Urushalima, Na ga abin banƙyama. Suna yin zina, suna ƙarya, Suna ƙarfafa hannuwan masu aikata mugunta, Saboda haka ba wanda ya juya ga barin muguntarsa, Dukansu suna kama da Saduma, Mazaunanta kuwa kamar Gwamrata.” 15 Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce a kan annabawa, “Ga shi, zan ciyar da su da abinci mai ɗaci, In shayar da su da ruwan dafi. Daga wurin annabawan Urushalima Rashin tsoron Allah ya fito ya mamaye dukan ƙasar.” 16 Ubangiji Mai Runduna ya ce wa mazaunan Urushalima, “Kada ku kasa kunne ga maganar annabawa, Gama sukan cika kunnuwanku da ƙarairayi. Suna faɗar ganin damarsu, Ba faɗar Ubangiji ba. 17 Suna ta faɗa wa waɗanda ke raina maganar Ubangiji cewa, ‘Za ku zauna lafiya!’ Ga kowane mai bin nufin tattaurar zuciyarsa, ‘Ba masifar da za ta same ka.’ ” 18 Irmiya ya ce, “Gama wanene a cikin annabawan nan ya taɓa neman shawarar Ubangiji don ya fahimci maganarsa, ko kuwa wanene ya taɓa kasa kunne don ya ji maganarsa? 19 Ga shi, hadirin hasalar Ubangiji ya taso, Kamar iskar guguwa, Zai tashi a bisa kan mugaye. 20 Ubangiji ba zai huce ba, Sai ya aikata nufin zuciyarsa. Amma sai daga baya za ku gane sarai.” 21 Ubangiji ya ce, “Ni ban aiki waɗannan annabawa ba, Duk da haka sun tafi, Ban kuwa yi musu magana ba, Amma sun yi annabci. 22 Amma da a ce sun tsaya cikin shawarata, Da sun yi shelar maganata, ga jama'ata, Da sun juyar da su daga muguwar hanyarsu, Da mugayen ayyukansu. 23 “Ni Allah na kusa ne kaɗai, Banda na nesa?” In ji Ubangiji. 24 “Mutum ya iya ɓoye kansa a wani lungu Inda ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji. “Ashe, ban cika sammai da duniya ba? 25 Na ji abin da annabawan nan suka ce, su da ke annabcin ƙarya da sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki!’ 26 Har yaushe ƙarya za ta fita daga zuciyar annabawan nan masu annabcin ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗin da ke a zuciyarsu? 27 Suna zaton za su sa mutanena su manta da sunana ta wurin mafarkansu da suke faɗa wa junansu, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana saboda Ba'al. 28 Bari annabin da ke da mafarki ya faɗi mafarkinsa, amma wanda ke da maganata ya faɗe ta da aminci. Me ya haɗa ciyawa da alkama? Ni Ubangiji na faɗa. 29 Maganata kamar wuta ce, kamar guduma mai farfashe dutse. Ni Ubangiji na faɗa. 30 Domin haka, ga shi, ina gāba da annabawan da ke satar maganata daga wurin junansu. Ni Ubangiji na faɗa. 31 Ina kuma gāba da annabawan da ke faɗar ra'ayin kansu, sa'an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya faɗa.’ 32 Ina kuma gāba da annabawan da ke annabcin mafarkansu na ƙarya, suna kuwa faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu, saboda rashin hankalinsu. Ni ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan jama'a ba ko kaɗan, ni Ubangiji na faɗa.” 33 “Kai Irmiya, sa'ad da wani mutum daga cikin mutanen nan, ko annabi, ko firist ya tambaye ka cewa, ‘Mecece nawayar Ubangiji?’ Sai ka ce masa, ‘Ku ne nawayar, zan kuwa rabu da ku,’ ni Ubangiji na faɗa. 34 Idan annabi ko firist, ko wani daga cikin jama'a, ya ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ zan hukunta shi duk da iyalin gidansa. 35 Haka kowannenku zai ce wa maƙwabcinsa da ɗan'uwansa, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’ 36 Amma ba za ku ƙara ambatar nawayar Ubangiji ba, gama maganar kowane mutum za ta zama nawaya, ga shi, kun ɓata maganar Allah mai rai, Ubangiji Mai Runduna, Allahnmu. 37 Haka za ka faɗa wa annabi, ‘Wace amsa Ubangiji ya bayar? Me Ubangiji ya faɗa?’ 38 Amma idan kun ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ ga abin da ni Ubangiji na ce, tun da ya ke kun faɗi wannan magana, wato ‘Nawayar Ubangiji,’ alhali kuwa na aika muku cewa, kada ku ce, ‘Nawayar Ubangiji,’ 39 saboda haka, hakika zan ɗaga in jefar da ku daga gabana, da ku da birni wanda na ba ku, ku da kakanninku. 40 Zan sa ku zama abin zargi da abin kunya har abada, ba kuwa za a manta da wannan ba.”

Irmiya 24

Kwando Biyu na 'Ya'yan Ɓaure

1 Bayan da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya kama Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, daga Urushalima, ya kai shi bautar talala a Babila, tare da sarakunan Yahuza, da gwanayen sana'a, da maƙera, dukansu, ya kawo su Babila. Sai Ubangiji ya nuna mini wannan wahayi. Na ga kwando biyu na ɓaure, an ajiye su a gaban Haikalin Ubangiji. 2 A ɗaya kwandon akwai ɓaure masu kyau, kamar nunan fari. A ɗayan kuwa marasa kyau ne, ba mai iya cinsu. 3 Sai Ubangiji ya ce mini, “Irmiya, me ka gani?” Sai na ce, “'Ya'yan ɓaure, akwai masu kyau ƙwarai, akwai kuma marasa kyau ƙwarai, har da ba za su ciwu ba.” 4 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, 5 “Haka ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce, kamar kyawawan ɓauren nan, haka nake ganin mutanen Yahuza waɗanda aka kai su bautar talala a ƙasar Kaldiyawa. 6 Zan lura da su da kyau, in kuma komo da su a wannan ƙasa. Zan gina su, ba zan rushe su ba. Zan kafa su, ba zan tumɓuke su ba. 7 Zan ba su zuciyar da za su sani ni ne Ubangiji. Za su kuwa zama jama'ata, ni kuwa zan zama Allahnsu, gama za su komo wurina da zuciya ɗaya. 8 “Ni Ubangiji na ce, zan mai da Zadakiya Sarkin Yahuza, da sarakunansa, da sauran mutanen Urushalima da suka ragu a ƙasar, da mutanen da suka tafi Masar, kamar ruɓaɓɓen ɓauren nan da suka lalace har ba su ciwuwa. 9 Zan maishe su abin ƙyama da masifa ga mulkokin duniya duka. Za su zama abin zargi, da karin magana, da ba'a, da la'ana a dukan wuraren da zan warwatsa su. 10 Zan aika musu da takobi, da yunwa, da annoba har an hallaka su sarai daga cikin ƙasar da na ba su, su da kakanninsu.”

Irmiya 25

Za a Zama Kufai har Shekara Saba'in

1 A shekara ta huɗu ta mulkin Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana a kan dukan mutanen Yahuza. A shekarar da Nebukadnezzar ya ci sarautar Babila, 2 a shekarar ce, annabi Irmiya ya yi wa dukan mutanen Yahuza da dukan mazaunan Urushalima magana cewa, 3 “Shekaru ashirin da uku ke nan tun daga shekara ta goma sha uku ta mulkin Yosiya, ɗan Amon, Sarkin Yahuza, har zuwa yau, Ubangiji ya yi mini magana, ni kuwa na yi ta faɗa muku, amma ba ku ji ba. 4 Ba ku saurara ba, ba ku kasa kunne don ku ji ba, ko da ya ke Ubangiji ya yi ta aiko muku da dukan bayinsa annabawa, 5 yana cewa, ‘Sai kowane ɗayanku ya juyo daga mugun halinsa da mugayen ayyukansa don ya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku, ku da kakanninku tun daga zamanin dā har abada. 6 Kada ku bi gumaka, ku bauta musu, ku yi musu sujada, ko ku tsokane ni da ayyukan hannuwanku, sa'an nan ba zan hore ku ba.’ 7 Duk da haka ba ku kasa kunne gare shi ba, shi Ubangiji ya faɗa, sai kuka tsokane shi da ayyukan hannuwanku. Wannan kuwa zai cuce ku. 8 “Domin haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Tun da ya ke kun ƙi yin biyayya da maganata, 9 zan aiko kabilai daga arewa da bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Zan kawo su, su yi yaƙi da ƙasan nan da mazaunanta, da dukan al'umman da ke kewaya da ita. Zan hallaka su sarai, in sa su zama abin ƙyama, da abin raini, da abin zargi har abada. 10 Banda haka zan kawar da muryar sowa da ta farin ciki, da ta ango da ta amarya, da amon dutsen niƙa daga gare su. Zan kashe hasken fitilunsu. 11 Ƙasar duka za ta zama kufai marar amfani, waɗannan al'ummai za su bauta wa Sarkin Babila har shekara saba'in. 12 Sa'an nan bayan cikar shekara saba'in ɗin, zan hukunta Sarkin Babila da ƙasarsa, wato ƙasar Kaldiyawa. Zan maishe ta kango har abada, saboda zunubinsa. 13 Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abin da na faɗa gāba da ita. Dukan abin da aka rubuta a wannan littafi, wato dukan abin da Irmiya ya yi annabcinsa gāba da dukan al'umman nan. 14 Al'ummai da yawa da manyan sarakuna za su bautar da su, ni kuwa zan yi musu sakayya bisa ga ayyukan hannuwansu.’ ”

Hukuncin da Allah zai yi wa Al'ummai

15 Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce mini, “Ka karɓi ƙoƙon ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al'umman da na aike ka gare su, su sha. 16 Za su sha, su yi tangaɗi su yi hauka saboda takobin da zan aiko a cikinsu.” 17 Sai na karɓi ƙoƙon daga wurin Ubangiji, na sa dukan al'umman da Ubangiji ya aike ni gare su, su sha daga cikinsa. 18 Urushalima, da biranen Yahuza, da sarakunanta, da shugabanninta, za su zama kango da abin ƙyama da abin raini, da abin la'ana. Haka yake a yau. 19-26 Ga lissafin sauran da za su sha ƙoƙon. Fir'auna Sarkin Masar da kuma barorinsa, da sarakunansa, Dukan jama'arsa, da dukan baƙin da ke tare da su, dukan sarakunan ƙasar Uz, dukan sarakunan ƙasar Filistiyawa, wato Ashkelon, da Gaza, da Ekron, da saura na Ashdod, Edom da Mowab, da 'ya'yan Ammon maza, dukan sarakunan Taya, da dukan sarakunan Sidon, dukan sarakunan da ke gaɓar Bahar Rum da waɗanda ke a tsibiran tekun, Dedan, da Tema, da Buz, da dukan waɗanda suke yi wa kansu sanƙo, dukan sarakunan Arabiya, dukan sarakunan tattarmukan mutane da ke zaune a hamada, dukan sarakunan Zimri, da dukan sarakunan Elam, da dukan sarakunan Mediya, dukan sarakunan arewa, na nesa da na kusa bi da bi. Dukan mulkokin da ke fuskar duniya za su sha daga ciki. Daganan sai Sarkin Babila a bayansu duka, zai sha nasa. 27 “Za ka kuma faɗa musu cewa, ‘In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ku sha, ku bugu, ku yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku tashi saboda takobin da zan aiko muku.’ 28 Idan kuwa sun ƙi su karɓi ƙoƙon daga hannunka su sha sai ka faɗa musu cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, dole ne ku sha! 29 Gama ga shi, na fara sa masifa ta yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana. To, kuna tsammani ba za a hukunta ku ba? Sai an hukunta ku, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.’ 30 “Kai Irmiya kuma sai ka yi annabcin dukan waɗannan magana gāba da su, ka faɗa musu cewa, ‘Ubangiji zai yi ruri daga Sama, Zai yi magana daga wurin zamansa mai tsarki, Zai yi wa garkensa ruri da ƙarfi ƙwarai, Zai yi ihu kamar masu matse 'ya'yan inabi, Zai yi gāba da dukan mazaunan duniya. 31 Za a ji hayaniya har iyakar duniya, Gama Ubangiji yana da ƙara game da al'ummai, Zai shiga hukunta wa dukan 'yan adam, Zai kashe mugaye da takobi, Ubangiji ya faɗa.’ ” 32 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ga masifa tana tahowa daga al'umma zuwa al'umma, Hadiri kuma yana tasowa daga dukan manisantan wurare na duniya. 33 Waɗanda Ubangiji ya kashe a wannan rana, Za su zama daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi makoki dominsu ba, Ba kuwa za a tattara gawawwakinsu a binne ba. Za su zama taki ga ƙasa. 34 “Ku yi makoki, ku yi kuka, ku makiyaya, Ku yi ta birgima a cikin toka ku iyayengijin garke, Gama ranar da za a yanka ku da ranar da za a warwatsa ku ta zo, Za ku fāɗi kamar zaɓaɓɓen kasko. 35 Ba mafakar da ta ragu domin makiyaya, Iyayengijin garken ba za su tsira ba. 36 Ji kukan makiyayan, Da kukan iyayengijin garken, Gama Ubangiji yana lalatar da wurin kiwonsu. 37 Garkunan da ke zaune lafiya kuwa, an yi kaca-kaca da su Saboda zafin fushin Ubangiji. 38 Ya rabu da wurin ɓuyarsa kamar zaki, Gama ƙasarsu ta zama marar amfani, Saboda takobin Ubangiji, da kuma zafin fushinsa.”

Irmiya 26

Maƙarƙashiya a Kashe Irmiya

1 A farkon sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce, 2 “Ka tsaya a filin Haikalin Ubangiji, ka yi wa dukan biranen Yahuza magana, su waɗanda suka zo Haikalin Ubangiji domin su yi sujada. Ka faɗa musu dukan maganar da na umarce ka, kada ka rage ko ɗaya. 3 Mai yiwuwa ne su ji, har kowa ya juyo ya bar muguwar hanyarsa. Ni ma sai in janye masifar da na yi niyyar aukar musu da ita, saboda mugayen ayyukansu.” 4 Ubangiji ya faɗa wa Irmiya ya ce wa jama'a, “Haka Ubangiji ya ce, idan ba za ku kasa kunne gare ni ba, ku yi tafiya a dokata wadda na sa a gabanku ba, 5 ku kuma kula da zantuttukan bayina, annabawa, waɗanda na yi ta aiko muku, to, amma ba ku kula ba. 6 Saboda haka zan mai da wannan Haikali kamar Shilo, in mai da wannan birni ya zama abin la'ana ga dukan al'umman duniya.” 7 Firistoci, da annabawa, da dukan jama'a sun ji dukan maganan nan da Irmiya ya faɗa a cikin Haikalin Ubangiji. 8 Sa'ad da Irmiya ya gama faɗar dukan abin da Ubangiji ya umarce shi ya faɗa wa dukan jama'a, sai firistoci, da annabawa, da dukan jama'a suka kama shi, suna cewa, “Mutuwa za ka yi! 9 Don me ka yi annabci da sunan Ubangiji, ka ce wannan Haikali zai zama kamar Shilo, wannan birni kuma zai zama kufai, ba mazauna a ciki?” Sai jama'a duk suka taru, suka kewaye Irmiya cikin Haikalin Ubangiji. 10 Sa'ad da sarakunan Yahuza suka ji waɗannan al'amura, sai suka fito daga gidan sarki zuwa Haikalin Ubangiji, suka zauna a bakin Sabuwar Ƙofa ta Haikalin Ubangiji. 11 Sai firistoci da annabawa suka faɗa wa sarakunan nan da jama'a duka, suka ce, “Mutumin nan ya cancanci hukuncin kisa, gama ya yi annabci gāba da wannan birni kamar yadda kuka ji da kunnuwanku.” 12 Sa'an nan sai Irmiya ya yi magana da dukan sarakuna da dukan jama'a, ya ce, “Ubangiji ne ya aiko ni in yi annabci gāba da wannan Haikali da wannan birni, da irin maganar da kuka ji. 13 Saboda haka yanzu sai ku gyara al'amuranku da ayyukanku, ku yi biyayya kuma da muryar Ubangiji Allahnku. Ubangiji kuwa zai janye masifar da ya hurta gāba da ku. 14 Amma ni kaina kuwa a hannunku nake, sai ku yi mini yadda kuka ga ya yi kyau, ya kuma dace a gare ku. 15 Ku tabbata dai, idan kuka kashe ni, za ku jawo hakkin jinin marar laifi a kanku da a kan wannan birni da mazauna a cikinsa, gama a gaskiya Ubangiji ne ya aiko ni wurinku domin in faɗa muku dukan maganan nan a kunnuwanku.” 16 Sarakuna kuwa da dukan jama'a suka ce wa firistoci da annabawa, “Wannan mutum bai yi abin da ya isa hukuncin kisa ba, gama ya yi magana da sunan Ubangiji Allahnmu.” 17 Sai waɗansu daga cikin dattawan ƙasar suka miƙe tsaye, suka ce wa dukan taron jama'a, 18 “Mika kuwa, mutumin Moreshet, ya yi annabci a kwanakin Hezekiya, Sarkin Yahuza, ya faɗa wa dukan mutanen Yahuza cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya ce, Za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za ta zama tsibin juji, Ƙwanƙolin dutsen Haikalin zai zama kurmi.’ 19 Ashe, Hezekiya Sarkin Yahuza da dukan Yahuza sun kashe shi ne? Ashe, Hezekiya bai ji tsoron Ubangiji, ya roƙi alherinsa ba? Ashe, Ubangiji bai janye masifar da ya hurta a kansu ba? Yanzu fa gab muke da mu jawo wa kanmu babbar masifa.” 20 Akwai wani mutum kuma wanda ya yi annabci da sunan Ubangiji. Sunansa Uriya ɗan Shemaiya mutumin Kiriyat-yeyarim. Ya yi annabci gāba da birnin nan da ƙasan nan da magana irin ta Irmiya. 21 Sa'ad da sarki Yehoyakim, da dukan jarumawansa, da dukan sarakunansa suka ji maganarsa, sai sarki yana so ya kashe shi, amma sa'ad da Uriya ya ji, sai ya ji tsoro, ya gudu ya tsere zuwa Masar. 22 Sa'an nan sai sarki Yehoyakim ya aiki waɗansu mutane zuwa Masar, wato Elnatan ɗan Akbor da waɗansu tare da shi. 23 Suka kamo Uriya daga Masar suka kawo shi wurin sarki Yehoyakim, sai ya sa aka kashe shi da takobi, aka binne gawarsa a makabartar talakawa. 24 Amma Ahikam ɗan Shafan yana tare da Irmiya, saboda haka ba a bashe shi ga mutane don su kashe shi ba.

Irmiya 27

Irmiya ya Ɗaura Karkiyar Shanu a Wuyansa

1 A farkon sarautar Zadakiya ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Ubangiji ya yi wa Irmiya magana. 2 Ya ce ya yi wa kansa karkiyar itace da maɗaurai na fata ya ɗaura su a wuyansa, 3 ya aika da magana zuwa ga Sarkin Edom, da Sarkin Mowab, da Sarkin Ammon, da Sarkin Taya, da Sarkin Sidon ta hannun manzannin da suka zo Urushalima wurin Zadakiya Sarkin Yahuza. 4 Ubangiji ya ce wa Irmiya ya umarce su, su tafi, su faɗa wa iyayengijinsu cewa, “In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ga abin da za ku faɗa wa iyayengijinku, 5 ‘Ni ne da ikona da ƙarfina na yi duniya, da mutane, da dabbobi waɗanda ke cikinta. Nakan ba da ita ga wanda na ga dama. 6 Yanzu fa na ba bawana Nebukadnezzar, Sarkin Babila, dukan ƙasashen nan, na kuma ba shi namomin jeji su bauta masa. 7 Dukan ƙasashe za su bauta masa, da shi da ɗansa, da jikansa, har lokacin da na sa ƙasar ta fāɗi, sa'an nan al'ummai masu yawa da manyan sarakuna za su bautar da shi. 8 “ ‘Amma idan wata al'umma ko wani mulki bai yarda ya bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila ba, bai kuma ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyansa ba, zan hukunta wa wannan al'umma da takobi, da yunwa, da annoba, har in hallaka ta, ta hannun Nebukadnezzar, ni Ubangiji na faɗa. 9 Saboda haka kada ku saurari annabawanku, da masu duba, da masu mafarkai, da matsubbata, ko masu sihiri waɗanda suka ce muku ba za ku bauta wa Sarkin Babila ba. 10 Suna yi muku annabcin ƙarya ne, za su kuwa sa a kai ku wata ƙasa nesa da ƙasarku. Zan kore ku, za ku kuwa lalace. 11 Amma duk al'ummar da za ta ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyanta, ta kuma bauta masa, zan bar ta a ƙasarta, ta yi noman ƙasarta, ta zauna a ciki, ni Ubangiji na faɗa.’ ” 12 Sai na faɗa wa Zadakiya Sarkin Yahuza wannan magana cewa, “Ka ɗaura karkiyar Sarkin Babila a wuyanka, ka bauta masa, shi da mutanensa, don ka rayu! 13 Don me kai da mutanenka za ku mutu ta takobi, da yunwa, da annoba, kamar yadda Ubangiji ya yi magana a kan kowace al'umma da ta ƙi ta bauta wa Sarkin Babila? 14 Kada ka kasa kunne ga maganar annabawan da suke ce maka, ‘Ba za ku bauta wa Sarkin Babila ba.’ Annabcin ƙarya suke yi muku. 15 Gama Ubangiji ya ce shi bai aike su ba, annabcin ƙarya suke yi muku da sunansa, don ya kore ku, ku halaka, ku da annabawan da suke yi muku annabci.” 16 Sa'an nan na faɗa wa firistoci da jama'a cewa, “In ji Ubangiji, kada ku kasa kunne ga abin da annabawanku suke muku annabci cewa, ‘Ba da daɗewa ba za a komo da kayan Haikalin Ubangiji daga Babila.’ Ƙarya ce suke yi muku. 17 Kada ku ji su, amma ku bauta wa Sarkin Babila don ku rayu! Don me birnin nan zai zama kufai? 18 Idan su annabawa ne, idan kuwa Ubangiji yana magana da su, to, bari su roƙi Ubangiji Mai Runduna kada a tafi Babila da kayayyakin da suka ragu a Haikalin Ubangiji, da a fādar Sarkin Yahuza, da a Urushalima. 19 Gama Ubangiji Mai Runduna ya faɗi zancen ginshiƙai, da babbar kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan, 20 wato waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila bai kwashe ba a lokacin da ya tafi da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, da dukan dattawan Yahuza da na Urushalima zuwa bauta a Babila. 21 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa a kan kayayyakin da suka ragu a Haikalin Ubangiji, da a fādar Sarkin Yahuza, da a Urushalima, 22 ‘Za a kwashe su a kai Babila, a can za su kasance har lokacin da zan sāke kulawa da su. Sa'an nan ne zan komo da su, in maishe su a wannan wuri.’ ”

Irmiya 28

Annabcin Ƙarya na Hananiya

1 Ya zama fa a wannan shekara, a watan biyar, a shekara ta huɗu ta sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza, sai annabi Hananiya ɗan Azzur mutumin Gibeyon, ya yi magana da ni a Haikalin Ubangiji, a gaban firistoci da dukan jama'a, ya ce, 2 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa, ‘Na karya karkiyar Sarkin Babila. 3 Bayan shekara biyu zan komo da kayayyakin Haikalin Ubangiji zuwa wurin nan. Kayayyakin da Nebukadnezzar, Sarkin Babila ya kwashe daga wannan wuri, ya kai Babila. 4 Zan kuma komo da Yekoniya ɗan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, da dukan waɗanda aka kai su zaman talala daga Yahuza, gama zan karya karkiyar Sarkin Babila.’ ” 5 Sa'an nan annabi Irmiya ya yi magana da annabi Hananiya a gaban firistoci da dukan jama'ar da ke tsaye a Haikalin Ubangiji, ya ce, 6 “Amin, amin, Ubangiji ya sa ya zama haka, Ubangiji ya sa annabcin da ka yi ya zama gaskiya, Ubangiji ya komo da kayayyakin Haikalinsa da dukan waɗanda aka kai su zaman talala a Babila. 7 Amma yanzu sai ka ji maganan nan da zan faɗa maka, kai da dukan jama'an nan. 8 Annabawan da suka riga mu, ni da kai a zamanin dā, sun yi wa ƙasashe masu yawa da manyan mulkoki annabcin yaƙi da yunwa, da annoba. 9 Idan maganar wannan annabi kuwa da ya yi annabcin salama ta cika, sa'an nan ne za a sani gaskiya Ubangiji ne ya aiko shi.” 10 Sai annabi Hananiya ya cire karkiyar daga wuyan annabi Irmiya ya karya ta. 11 Sa'an nan Hananiya ya yi magana a gaban dukan jama'a, ya ce, “In ji Ubangiji, haka zan karya karkiyar Nebukadnezzar, Sarkin Babila, daga wuyan dukan al'ummai kafin shekara biyu.” Sai annabi Irmiya ya yi tafiyarsa. 12 Da ɗan daɗewa bayan da annabi Hananiya ya karya karkiyar da ke a wuyan annabi Irmiya, sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce 13 ya tafi ya faɗa wa Hananiya, ya ce, “Haka Ubangiji ya ce, ‘Ka karya karkiya ta itace, amma zan yi karkiya ta ƙarfe a maimakonta. 14 Gama haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na faɗa. Na sa wa wuyan dukan waɗannan al'ummai karkiya ta ƙarfe, don su bauta wa Nebukadnezzar, Sarkin Babila, za su kuwa bauta masa, gama na ba shi su, har da namomin jeji.’ ” 15 Sai annabi Irmiya ya ce wa annabi Hananiya, “Ka ji, ya Hananiya, Ubangiji bai aike ka ba, kana sa mutanen nan su dogara ga ƙarya. 16 Saboda haka, in ji Ubangiji, ‘Zan kawar da kai daga duniya. Za ka mutu a wannan shekara domin ka kuta tayarwa ga Ubangiji.’ ” 17 A wannan shekara kuwa, a watan bakwai, sai annabi Hananiya ya mutu.

Irmiya 29

Wasiƙar Irmiya Zuwa ga Yahudawan da ke Babila

1 Ga maganar wasiƙar da annabi Irmiya ya aika daga Urushalima zuwa ga dattawa, da firistoci, da annabawa, da dukan mutanen da Nebukadnezzar ya kwaso daga Urushalima zuwa Babila. 2 (Ya rubuta wannan bayan tashin sarki Yekoniya, da uwa tasa, da bābāni, da sarakunan Yahuza, da na Urushalima, da gwanayen aikin hannu, da maƙera daga Urushalima.) 3 Ya aika da wasiƙar ta hannun Elasa ɗan Shafan, da Gemariya ɗan Hilkiya waɗanda Zadakiya Sarkin Yahuza ya aika zuwa Babila, wurin Nebukadnezzar, Sarkin Babila. Ga abin da wasiƙar ta ce. 4 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce wa dukan waɗanda aka kai bauta, wato waɗanda ya aika da su bauta daga Urushalima zuwa Babila. 5 ‘Ku gina gidaje, ku zauna a ciki, ku dasa gonaki, ku ci amfaninsu. 6 Ku auri mata, ku haifi 'ya'ya mata da maza. Ku auro wa 'ya'yanku mata, ku aurar da 'ya'yanku mata, domin su haifi 'ya'ya mata da maza, ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu. 7 Amma ku nemi zaman lafiyar birni inda na sa aka kai ku zaman talala, ku yi addu'a ga Ubangiji saboda birnin, gama zaman lafiyar birnin shi ne naku zaman lafiyar.’ 8 Gama haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya faɗa. ‘Kada ku yarda annabawanku da malamanku na duba waɗanda ke tare da ku su ruɗe ku, kada ku kasa kunne ga mafarkansu. 9 Gama annabcin da suke yi muku da sunana, ƙarya ne, ni ban aike su ba.’ 10 “Ubangiji ya ce, ‘Sa'ad da kuka cika shekara saba'in a Babila, zan ziyarce ku, zan kuwa cika muku alkawarina. Zan komo da ku zuwa wannan wuri. 11 Gama na san irin shirin da na yi muku, ni Ubangiji na faɗa. Shirin alheri, ba na mugunta ba. Zan ba ku gabata da sa zuciya. 12 Sa'an nan za ku yi kira a gare ni, ku yi addu'a a wurina, zan kuwa ji ku. 13 Za ku neme ni ku same ni, idan kun neme ni da zuciya ɗaya. 14 Za ku same ni, ni Ubangiji na faɗa, zan mayar muku da arzikinku, in tattaro ku daga cikin dukan al'ummai da dukan wurare inda na kora ku, ni Ubangiji na faɗa, zan komo da ku a wurin da na sa a kwashe ku a kai ku zaman talala.’ 15 “Domin kun ce, Ubangiji ya ba ku annabawa a Babila, 16 ku ji abin da Ubangiji ya faɗa a kan sarkin da ya hau gadon sarautar Dawuda, da a kan dukan jama'ar da ke zaune a wannan birni, wato a kan danginku waɗanda ba a kwashe su zuwa zaman talala ba. 17 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Ga shi, zan aiko musu da takobi, da yunwa, da masifa, zan maishe su kamar ruɓaɓɓen ɓaure waɗanda suka lalace ƙwarai, har ba su ciwuwa. 18 Zan fafare su da takobi, da yunwa, da masifa. Zan maishe su abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya. Za su zama abin la'ana, da abin razana, da abin raini, da abin zargi, ga dukan al'ummai, inda na kora su. 19 Domin ba su ji maganata wadda ni Ubangiji na faɗa ba, na yi ta aika muku da ita ta wurin bayina annabawa, amma kuka ƙi, ni Ubangiji na faɗa. 20 Ku ji maganar Ubangiji, dukanku da aka kai ku zaman talala waɗanda na kora daga cikin Urushalima zuwa Babila.’ 21 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce a kan Ahab ɗan Kolaya, da Zadakiya ɗan Ma'aseya, waɗanda ke yi muku annabcin ƙarya da sunana. Ga shi, zan bashe su a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, zai kashe su a kan idonku. 22 Saboda su duka waɗanda aka kai bautar talala daga Yahuza zuwa Babila, za su mori kalman nan suna yin la'ana cewa, ‘Ubangiji ya maishe ka kamar Zadakiya da Ahab, waɗanda Sarkin Babila ya gasa da wuta!’ 23 Gama sun yi wauta a Isra'ila, sun yi zina da matan maƙwabtansu, sun yi ƙarya da sunana, ni kuwa ban umarce su ba. Ni na sani, ni ne kuma shaida, ni Ubangiji na faɗa.

Saƙo ga Shemaiya

24 “Zancen Shemaiya mutumin Nehelam, 25 haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya faɗa. Ga shi, ka aika da wasiƙu da sunanka zuwa ga dukan jama'ar da ke a Urushalima, da zuwa ga Zafaniya ɗan Ma'aseya, firist, da kuma ga dukan firistoci, cewa 26 Ubangiji ya naɗa ka firist a madadin Yehoyada firist, ka lura da Haikalin Ubangiji, ka sa kowane mahaukacin da zai yi annabci a turu, ka sa masa ƙangi. 27 To, me ya sa ba ka tsauta wa Irmiya, mutumin Anatot, wanda yake yin maka annabci ba? 28 Gama ya aiko mana a Babila, cewa za mu daɗe a zaman talala, mu gina wa kanmu gidaje, mu zauna a ciki, mu dasa gonaki mu ci amfaninsu.” 29 Sai Zafaniya firist, ya karanta wasiƙan nan a gaban annabi Irmiya. 30 Ubangiji kuwa ya yi magana da Irmiya, ya ce, 31 ya aika wa dukan waɗanda ke zaman talala ya ce, “Haka Ubangiji ya ce a kan Shemaiya mutumin Nehelam, ‘Saboda Shemaiya ya yi muku annabci, alhali ni ban aike shi ba, ya sa ku dogara ga ƙarya,’ 32 saboda haka Ubangiji ya ce, ‘ga shi, zan hukunta Shemaiya, mutumin Nehelam, shi da zuriyarsa ba za a bar masa mai rai ko ɗaya a wannan jama'a ba, wanda zai ga irin alherin da zan yi wa jama'ata, gama ya kuta tayarwa ga Ubangiji,’ ” in ji Ubangiji.

Irmiya 30

Tabbatarwar Komowa daga Zaman Talala

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce, 2 “Ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce, ‘Ka rubuta dukan maganar da na faɗa maka a littafi. 3 Gama kwanaki suna zuwa sa'ad da zan komo da mutanena, wato Isra'ila da Yahuza. Zan komo da su zuwa ƙasar da na ba kakanninsu, za su kuwa mallake ta,’ ni Ubangiji na faɗa.” 4 Waɗannan ne maganar da Ubangiji ya faɗa a kan Isra'ila da Yahuza. 5 “Ni Ubangiji na ce, Mun ji kukan gigitacce, Kukan firgita ba kuma salama. 6 Yanzu ku tambaya, ku ji, Namiji ya taɓa haihuwa? To, me ya sa nake ganin kowane namiji yana riƙe da kwankwaso, Kamar mace mai naƙuda, Fuskar kowa kuma ta yi yaushi? 7 Kaito, gama wannan babbar rana ce, Ba kuma kamarta, Lokaci ne na wahala ga Yakubu, Duk da haka za a cece shi daga cikinta.” 8 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “A wannan rana zan karya karkiya da ke a wuyansu, in cire musu ƙangi, ba kuma za su ƙara zama bayin baƙi ba. 9 Amma za su bauta mini, ni Ubangiji Allahnsu, da Dawuda sarkinsu, wanda zan tayar musu da shi.” 10 Ubangiji ya ce, “Kada ka ji tsoro, ya barana Yakubu, Kada kuma ka yi fargaba, ya Isra'ila, Gama zan cece ka daga ƙasa mai nisa, Zan kuma ceci zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yakubu zai komo, ya yi zamansa rai a kwance, Ba kuwa za a tsoratar da shi ba. 11 Gama ina tare da kai don in cece ka, Zan hallaka dukan al'ummai sarai, Inda na warwatsa ku. Amma ku ba zan hallaka ku ba, Zan hore ku da adalci, Ba yadda za a yi in ƙyale ku ba hukunci, Ni Ubangiji na faɗa.” 12 Ubangiji ya ce, “Rauninku ba ya warkuwa, Mikinku kuwa mai tsanani ne ƙwarai. 13 Ba wanda zai kula da maganarku, Ba magani domin mikinku, Ba za ku warke ba. 14 Dukan masu ƙaunarku sun manta da ku, Ba su ƙara kulawa da ku, Domin na yi muku bugu irin na maƙiyi. Na yi muku horo irin na maƙiyi marar tausayi, Domin laifofinku masu girma ne, Domin zunubanku da yawa suke. 15 Don me kuke kuka a kan rauninku? Ciwonku ba zai warke ba. Saboda laifofinku masu girma ne, Domin zunubanku da yawa suke, Shi ya sa na yi muku waɗannan abubuwa. 16 Domin haka dukan waɗanda suka cinye ku, za a cinye su, Dukan maƙiyanku, kowane ɗayansu zai tafi bauta, Waɗanda suka washe ku, za a washe su. Dukan waɗanda suka kwashe ku ganima, su ma za a kwashe su ganima. 17 Zan mayar muku da lafiyarku, Zan kuma warkar da raunukanku, Ko da ya ke maƙiyanku suna kiranku yasassu, Suna cewa, ‘Ai, Sihiyona ce, ba wanda ya kula da ita.’ Ni Ubangiji na faɗa.” 18 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan komar wa alfarwar Yakubu arzikinta, Zan kuma nuna wa wuraren zamansa jinƙai, Za a sāke gina birnin a kufansa, Fādar kuma za ta kasance a inda take a dā. 19 Daga cikinsu za a ji waƙoƙin godiya. Da muryoyin masu murna. Zai riɓaɓɓanya su, ba za su zama kaɗan ba, Zan kuwa ɗaukaka su, ba za a ƙasƙantar da su ba. 20 'Ya'yansu za su zama kamar dā, Jama'arsu kuma za su kahu a gabana, Zan hukunta dukan waɗanda suka zalunce su. 21 Sarkinsu zai zama ɗaya daga cikinsu, Mai mulkinsu kuma zai fito daga cikinsu. Zan kawo shi kusa, zai kuwa kusace ni, Gama wanene zai yi ƙarfin hali ya kusace ni? Ni Ubangiji na faɗa. 22 Za ku zama mutanena, Ni kuwa zan zama Allahnku.” 23 Ga hadirin hasalar Ubangiji ya taso, wato iskar guguwa, Zai huce a kan mugaye. 24 Zafin fushin Ubangiji ba zai huce ba, Sai ya aikata, ya kammala abubuwan da ya yi niyya a tunaninsa. A nan gaba mutanensa za su fahimci wannan.

Irmiya 31

1 Ubangiji ya ce, “Lokaci yana zuwa da zan zama Allah na dukan iyalan Isra'ila, za su kuwa zama jama'ata.” 2 Haka Ubangiji ya ce, “Jama'ar da suka tsere wa takobi, Sun sami alheri a cikin jeji, A sa'ad da Isra'ila suka nemi hutawa.” 3-4 Ubangiji ya bayyana gare ni tun daga nesa cewa, “Ya Isra'ila, budurwa! Na kusace ki da madawwamiyar ƙaunata, Ba zan fasa amintacciyar ƙaunata a gare ki ba. Zan sāke gina ki, Za ki kuwa ginu, Za ki ɗauki kayan kaɗe-kaɗe, Za ki shiga rawar masu murna. 5 Za ki sāke dasa gonar inabi A kan duwatsun Samariya, Masu dashe za su dasa, Za su mori 'ya'yan. 6 Gama rana tana zuwa sa'ad da mai tsaro zai yi kira A ƙasar tudu ta Ifraimu, ya ce, ‘Ku tashi mu haura zuwa Sihiyona Zuwa wurin Ubangiji Allahnmu.’ ” 7 Ga abin da Ubangiji ya ce, “Raira wa Yakubu waƙar farin ciki da ƙarfi, Ku ta da murya saboda shugaban al'ummai, Ku yi shela, ku yi yabo, ku ce, ‘Ya Ubangiji ka ceci jama'arka, Wato ringin mutanen Isra'ila,’ 8 Ga shi, zan fito da su daga ƙasar arewa, Zan tattaro su daga manisantan wurare na duniya, Tare da su makafi da guragu, Da mace mai goyo da mai naƙuda, Za su komo nan a babbar ƙungiya. 9 Da kuka za su komo. Da ta'aziyya zan bishe su, in komar da su, Zan sa su yi tafiya a gefen rafuffukan ruwa, A kan miƙaƙƙiyar hanya, inda ba za su yi tuntuɓe ba. Gama ni uba ne ga Isra'ila, Ifraimu kuwa ɗan farina ne.” 10 “Ku ji maganar Ubangiji, Ya ku al'ummai, Ku yi shelarsa har a ƙasashen da ke nesa, na gāɓar teku. Ku ce, ‘Shi wanda ya warwatsa Isra'ila zai tattaro ta, Zai kiyaye ta kamar yadda makiyayi yakan kiyaye garkensa.’ 11 Gama Ubangiji ya fanshi Yakubu. Ya fanshe shi daga hannuwan waɗanda suka fi ƙarfinsa. 12 Za su zo su raira waƙa da ƙarfi, A bisa ƙwanƙolin Sihiyona, Za su yi annuri saboda alherin Ubangiji, Saboda hatsi, da ruwan inabi, da mai, Saboda 'ya'yan tumaki da na shanu. Rayuwarsu za ta zama kamar lambu, Ba za su ƙara yin yaushi ba. 13 Sa'an nan 'yan mata za su yi rawa da farin ciki, Samari da tsofaffi za su yi murna. Zan mai da makokinsu ya zama murna, Zan ta'azantar da su, in ba su farin ciki maimakon baƙin ciki. 14 Zan yi wa ran firistoci biki da wadata, Jama'ata za su ƙoshi da alherina, Ni Ubangiji na faɗa.” 15 Ga abin da Ubangiji ya ce, “An ji murya daga Rama, Muryar baƙin ciki da kuka mai zafi, Rahila tana kuka saboda 'ya'yanta, ba su. 16 Ki yi shiru, ki daina kuka, Ki shafe hawaye daga idanunki. Za a sāka miki wahalarki, Za su komo daga ƙasar abokin gāba, Ni Ubangiji na faɗa. 17 Akwai sa zuciya dominki a nan gaba, Ni Ubangiji na faɗa. 'Ya'yanki za su komo ƙasarsu. 18 “Na ji Ifraimu yana baƙin ciki, yana cewa, ‘Ka hore ni, na kuwa horu, Kamar ɗan maraƙin da ba shi da horo, Ka komo da ni don in zama kamar yadda nake a dā, Gama kai ne Ubangiji Allahna. 19 Gama na tuba saboda na rabu da kai, Bayan da aka ganar da ni, sai na sunkuyar da kai, Kunya ta kama ni, na gigice, Domin ina ɗauke da wulakancin ƙuruciyata.’ 20 Ashe, Ifraimu ba ƙaunataccen ɗana ba ne? Ashe, shi ba ɗan gaban goshina ba ne? A duk lokacin da na ambace shi a kan muguntarsa Nakan tuna da shi da ƙauna. Saboda na ƙwallafa zuciyata a kansa, Hakika zan yi masa jinƙai, ni Ubangiji na faɗa. 21 “Ki kafa wa kanki alamun hanya, Ki kafa wa kanki shaidu, Ki lura da gwadabe da kyau, Hanyar da kin bi, kin tafi. Ya budurwa Isra'ila, ki komo, Komo zuwa biranen nan naki. 22 Har yaushe za ki yi ta shakka, Ya ke 'yar marar bangaskiya? Gama Ubangiji ya halitta sabon abu a duniya, Mace ce za ta kāre namiji.” 23 Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Nan gaba za su sāke yin magana a ƙasar Yahuza da biranenta a sa'ad da na mayar musu da dukiyarsu. ‘Ubangiji ya sa maka albarka, Ya wurin zaman adalci, Ya tsattsarkan tudu!’ 24 Yahuza kuwa da dukan biranenta za su zauna tare a can, da manoma, da makiyaya, da garkunansu. 25 Gama zan biya bukatar waɗanda suka gaji, in wartsakar da waɗanda ransu ya yi yaushi.” 26 Irmiya ya farka, ya ce, “Ina kuwa cikin barcina mai daɗi sai na farka na duba.”

Sabon Alkawari

27 “Ni Ubangiji na ce, ga shi, zan sa mutane da dabbobi su cika ƙasashen Isra'ila da na Yahuza. 28 Zai zama kamar yadda na lura da su don a tumɓuke su, a rushe su, a lalatar da su, a kawo musu masifa, haka kuma zan lura da su, a kuma dasa su, ni Ubangiji na faɗa. 29 A waɗannan kwanaki ba za su ƙara cewa, ‘Ubanni suka ci 'ya'yan inabi masu tsami, Haƙoran 'ya'ya suka mutu’ ba. 30 Amma kowa zai mutu saboda zunubin kansa, Wanda ya ci inabi masu tsami, Shi ne haƙoransa za su mutu.” 31 Ubangiji ya ce, “Ga shi, kwanaki suna zuwa da zan yi sabon alkawari da mutanen Isra'ila da na Yahuza. 32 Ba irin wanda na yi da kakanninsu ba, sa'ad da na fito da su daga ƙasar Masar, alkawarin da suka karya, ko da ya ke ni Ubangijinsu ne, ni Ubangiji na faɗa. 33 Amma wannan shi ne alkawarin da zan yi da mutanen Isra'ila bayan waɗancan kwanaki, ni Ubangiji na faɗa. Zan sa dokokina a cikinsu, zan rubuta su a zukatansu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama jama'ata. 34 Mutum ba zai ƙara koya wa maƙwabcinsa, ko ɗan'uwansa cewa, ‘Ka san Ubangiji’ ba, gama su duka za su san ni, tun daga ƙarami har zuwa babba. Zan gafarta musu laifofinsu, ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.” 35 Haka Ubangiji ya ce, Shi wanda ya ba da rana ta haskaka yini, Ya sa wata da taurari su ba da haske da dare, Shi ne yakan dama teku, ya sa raƙumanta su yi ruri, Sunansa Ubangiji Mai Runduna. 36 “Idan dai wannan kafaffiyar ka'ida ta daina aiki a gabana, Ni Ubangiji na faɗa, To, ashe, zuriyar Isra'ila za ta daina zama al'umma a gabana ke nan har abada. 37 Idan a iya auna sammai a kuma iya bincike tushen duniya a ƙarƙas, To, ashe, zan watsar da dukan zuriyar Isra'ila ke nan saboda dukan abin da suka yi, Ni Ubangiji na faɗa. 38 “Ga shi, kwanaki suna zuwa da za a sāke gina birnin domin Ubangiji, ni Ubangiji na faɗa, tun daga hasumiyar Hananel zuwa yamma, har zuwa Ƙofar Kan Kusurwa. 39 Sa'an nan ma'aunin zai daɗa gaba, har ya kai tudun Gareb, sa'an nan ya nausa zuwa Gowa. 40 Dukan filin kwarin gawawwaki da toka, da dukan filaye har zuwa rafin Kidron zuwa kan kusurwar Ƙofar Doki wajen gabas, za su zama mai tsarki ga Ubangiji. Ba za a ƙara tumɓuke shi ko a rushe shi ba har abada.”

Irmiya 32

Irmiya ya Sayi Saura a Anatot

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a shekara ta goma ta mulkin Zadakiya, Sarkin Yahuza. A lokacin kuwa Nebukadnezzar yana da shekara goma sha takwas da sarauta a Babila. 2 A lokacin nan kuwa sojojin Sarkin Babila sun kewaye Urushalima da yaƙi, annabi Irmiya kuwa yana a tsare a gidan waƙafi, a fādar Sarkin Yahuza. 3 Zadakiya Sarkin Yahuza, ya sa shi a kurkuku, gama ya ce, “Don me kake yin annabci? Ka ce, Ubangiji ya ce, ga shi, zai ba da wannan birni a hannun Sarkin Babila, zai kuwa cinye shi da yaƙi. 4 Zadakiya Sarkin Yahuza kuwa, ba zai tsere wa Kaldiyawa ba, amma za a ba da shi a hannun Sarkin Babila. Zai yi magana da shi fuska da fuska, ya kuma gan shi ido da ido. 5 Sarkin Babila kuwa zai tafi da Zadakiya zuwa Babila. Zai zauna can sai lokacin da na ziyarce shi. Ko da ya yi yaƙi da Kaldiyawa ba zai yi nasara ba.” 6 Irmiya ya ce, “Ubangiji ya yi magana da ni, cewa 7 ga shi, Hanamel, ɗan Shallum kawuna, zai zo wurina ya ce mini, ‘Ka sayi gonata wadda ke a Anatot, gama kai ne ka cancanci ka fanshe ta, sai ka saye ta.’ ” 8 Sai Hanamel ɗan kawuna ya zo wurina a gidan waƙafi, bisa ga faɗar Ubangiji, ya ce mini, “Ka sayi gonata wadda ke a Anatot a ƙasar Biliyaminu, gama kai ne ka cancanta ka mallake ta, kai ne za ka fanshe ta, sai ka saye ta.” Sa'an nan na sani wannan maganar Ubangiji ce. 9 Sai na sayi gonar a Anatot daga hannun Hanamel ɗan kawuna, na biya shi shekel goma sha bakwai na azurfa. 10 Na sa hannu a takarda, na buga hatimi na liƙe, na sami shaidu na kuwa auna kuɗin da ma'auni. 11 Na ɗauki takardun ciniki waɗanda aka rubuta sharuɗan a ciki da wadda aka liƙe da wadda ba a liƙe ba, 12 na ba Baruk, ɗan Neriya, ɗan Ma'aseya, a gaban Hanamel, ɗan kawuna, da gaban shaidun da suka sa hannun a takardar shaidar sayen, da gaban dukan Yahudawa waɗanda ke zaune a gidan waƙafi. 13 Sai na umarci Baruk a gabansu cewa, 14 “Haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, ‘Ka ɗauki waɗannan takardun shaida, wadda aka liƙe da wadda ba a liƙe ba, ka sa su a cikin tukunyar ƙasa domin kada su lalace.’ 15 Gama haka Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya faɗa, ‘Gidaje, da gonaki, da gonakin inabi, za a sāke sayensu a ƙasan nan.’ ”

Addu'ar Irmiya

16 Bayan da na ba Baruk, ɗan Neriya, takardar sharuɗan ciniki, sai na yi addu'a ga Ubangiji, na ce, 17 “Ya Ubangiji Allah, kai ne ka yi sammai da duniya ta wurin ikonka da ƙarfinka, ba abin da ya fi ƙarfinka. 18 Kakan nuna madawwamiyar ƙauna ga dubbai, amma kakan hukunta wa 'ya'ya saboda laifin ubanninsu. Ya maigirma Maɗaukaki, Allah, sunanka kuwa Ubangiji Mai Runduna. 19 Kai babban mashawarci ne, mai aikata manyan ayyukanka. Kana ganin dukan ayyukan 'yan adam. Kakan sāka wa kowa bisa ga halinsa da ayyukansa. 20 Ka aikata alamu da al'ajabai a ƙasar Masar. Har wa yau kuma kana aikata su a Isra'ila da kuma cikin dukan al'ummai, ka yi wa kanka suna kamar yadda yake a yau. 21 Ta wurin alamu da al'ajabai, da iko, da ƙarfi, da banrazana, ka fito da jama'arka Isra'ila daga ƙasar Masar. 22 Ka kuwa ba su wannan ƙasa wadda ka rantse za ka ba kakanninsu. Ƙasar da ke cike da yalwar albarka. 23 Amma sa'ad da suka shiga cikinta suka mallake ta, ba su yi biyayya da muryarka ba, ba su kiyaye dokokinka ba, ba su aikata dukan abin da ka umarce su ba, saboda haka ka sa wannan masifa ta auko musu. 24 “Ga shi, Kaldiyawa sun gina mahaurai kewaye da birnin da suka kewaye shi da yaƙi. Saboda takobi, da yunwa, da annoba aka ba da birnin a hannun Kaldiyawa, waɗanda suke yaƙi da birnin. Abin da ka faɗa ya tabbata, ka kuwa gani. 25 Duk da haka ya Ubangiji Allah, ka ce mini, ‘Sayi gonar da kuɗi, a gaban shaidu, ko da ya ke an ba da birnin a hannun Kaldiyawa.’ ” 26 Ubangiji kuwa ya ce wa Irmiya, 27 “Ni ne Ubangiji Allah na dukan 'yan adam, ba abin da ya fi ƙarfina. 28 Saboda haka, ni Ubangiji, na ce zan ba da wannan birni a hannun Kaldiyawa da hannun Nebukadnezzar Sarkin Babila, za su ci birnin. 29 Kaldiyawa da ke yaƙi da wannan birni za su zo, za su ƙone wannan birni da wuta ƙurmus, da gidaje waɗanda aka ƙona turare ga Ba'al a kan rufinsu. Aka kuma miƙa hadayu na sha ga gumaka, don su tsokane ni in yi fushi. 30 Gama jama'ar Isra'ila da ta Yahuza, tun daga ƙuruciyarsu, ba su aikata kome a gabana ba sai mugunta, ba abin da jama'ar Isra'ila suka yi, sai tsokanata da gumaka don in yi fushi da ayyukan hannuwansu, ni Ubangiji na faɗa. 31 Wannan birni ya tsokane ni ƙwarai tun lokacin da aka gina shi har zuwa yau, domin haka zan kawar da shi daga gabana. 32 Wannan kuwa saboda muguntar jama'ar Isra'ila ce da ta Yahuza, wadda suka yi don su tsokane ni in yi fushi, su da sarakunansu, da shugabanninsu, da firistocinsu, da annabawansu, da mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima. 33 Sun juya mini baya, ba su fuskance ni ba, ko da ya ke na yi ta koya musu, amma ba su saurara ga koyarwata ba. 34 Sun kafa gumakansu na banƙyama a cikin Haikalina wanda ake kira da sunana, sun kuwa ƙazantar da shi. 35 Sun gina wa Ba'al masujadai a kwarin ɗan Hinnom don su miƙa 'ya'yansu mata da maza hadaya ga Molek, ni kuwa ban umarce su ba, ba shi kuwa a tunanina. Ga shi, sun aikata wannan abin banƙyama, don su sa Yahuza ta yi zunubi.”

Alkawari na Sa Zuciya

36 “Domin haka ga abin da ni Ubangiji Allah na Isra'ila na ce a kan wannan birni wanda ka ce, ‘An ba da shi ga Sarkin Babila, da takobi, da yunwa, da annoba.’ 37 Ga shi, zan tattaro su daga dukan ƙasashe inda na kora su, da fushina, da hasalata, da haushina. Zan komo da su a wannan wuri, zan sa su su zauna lafiya. 38 Za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu. 39 Zan ba su zuciya ɗaya, da tafarki ɗaya domin su yi tsorona har abada, domin amfanin kansu da na 'ya'yansu a bayansu. 40 Zan yi madawwamin alkawari da su, ba zan fasa nuna musu alheri ba, zan kuwa sa tsorona a zukatansu domin kada su bar bina. 41 Zan ji daɗin yi musu alheri. Zan dasa su a wannan ƙasa da aminci da zuciya ɗaya.” 42 Gama haka Ubangiji ya faɗa, “Daidai kamar yadda na kawo wannan babbar masifa a kan jama'an nan, haka kuma zan kawo musu dukan waɗannan alherai da na alkawarta musu. 43 Za a sayi gonaki a wannan ƙasa wadda kake cewa ta zama kufai, ba mutum, ba dabba a ciki, wadda aka ba da ita ga Kaldiyawa. 44 Za a sayi gonaki da kuɗi, a sa hannu a kan sharuɗa, a hatimce su a gaban shaidu, a ƙasar Biliyaminu da wuraren da ke kewaye da Urushalima, da cikin garuruwan Yahuza, da na garuruwan ƙasar tudu, da a garuruwan kwaruruka, da a garuruwan Negeb, gama zan komar wa mutane da wadatarsu a ƙasarsu, ni Ubangiji na faɗa.”

Irmiya 33

Komo da Harka a Urushalima

1 Ubangiji ya sāke yin magana da Irmiya sa'ad da yake a kulle a gidan waƙafi. 2 Ubangiji wanda ya halitta duniya, ya siffata ta, ya kafa ta, sunansa Ubangiji, ya ce, 3 “Ka kira ni, ni kuwa zan amsa maka, zan kuwa nuna maka manyan al'amura masu girma da banmamaki, waɗanda ba ka sani ba.” 4 Gama haka Ubangiji, Allah na Isra'ila, ya ce, a kan gidajen da ke a wannan birni, da gidajen sarakunan Yahuza, waɗanda aka rurrushe domin a yi wa garukan jigo saboda mahaurai da suka kewaye birni, da kuma saboda yaƙi. 5 “Sa'ad da ake zuwa yaƙi da Kaldiyawa gidaje za su cika da gawawwakin mutane waɗanda na kashe da fushina da hasalata, gama na ɓoye wa wannan birni zatina saboda dukan muguntarsu. 6 Ga shi, zan kawo wa birnin lafiya, gama zan warkar da su, in wadata su da salama da gaskiya. 7 Zan kuma mayar wa mutanen Yahuza da mutanen Isra'ila da arzikinsu, in sāke kafa su kamar yadda suke a dā. 8 Zan shafe dukan laifin da suka yi mini, in kuma gafarta musu dukan zunubansu da tayarwar da suka yi mini. 9 Sunan wannan birni zai zama mini abin murna, da abin yabo, da darajantawa ga dukan al'umman duniya waɗanda za su ji dukan alherin da na yi dominsu, za su ji tsoro su yi rawar jiki saboda dukan alheri da dukan wadata da na tanada musu.” 10 Haka Ubangiji ya faɗa, “A wannan wuri da ka ce ya zama kufai, ba mutum ko dabba, wato a biranen Yahuza da titunan Urushalima, inda ba kowa, ba mutum ko dabba a ciki, 11 za a sāke jin muryar murna da ta farin ciki, da muryar ango da ta amarya, da muryoyin mawaƙa, sa'ad da suke kawo hadayun godiya a cikin Haikalin Ubangiji, suna cewa, ‘Ku yi godiya ga Ubangiji Mai Runduna, Gama Ubangiji nagari ne, Gama madawwamiyar ƙaunarsa tabbatacciya ce.’ Gama zan mayar da arzikin ƙasar kamar yadda yake a dā, ni Ubangiji na faɗa.” 12 Haka Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Wannan wuri wanda yake kufai, inda ba mutum ko dabba, da cikin dukan biranensa, zai sāke zama makiyaya, inda masu kiwo za su zauna da garkunansu. 13 A garuruwan ƙasar tuddai, da na kwaruruka, da na Negeb, da na ƙasar Biliyaminu, da na wuraren da ke kewaye da Urushalima, da na Yahuza, garkuna za su sāke bi ta ƙarƙashin hannun mai ƙidayawa,” in ji Ubangiji. 14 “Ga shi, kwanaki suna zuwa sa'ad da zan cika alkawarin da na yi wa mutanen Isra'ila da na Yahuza. 15 A waɗannan kwanaki da a lokacin nan, zan sa wani reshe mai adalci ya fito daga zuriyar Dawuda, zai aikata gaskiya da adalci a ƙasar. 16 A waɗannan kwanaki za a ceci mutanen Yahuza, mutanen Urushalima kuwa za su zauna lafiya. Sunan da za su sa wa Urushalima birninsu, shi ne, ‘Adalcinmu Ubangiji ne.’ 17 Gama ni Ubangiji na ce Dawuda ba zai taɓa rasa mutumin da zai zauna a gadon sarautar Isra'ila ba. 18 Lawiyawa kuma ba za su rasa firistocin da za su tsaya a gabana, suna miƙa hadayun ƙonawa ba, da hadayu na gari na ƙonawa, su kuma miƙa sadaka har abada.” 19 Ubangiji kuma ya yi magana da Irmiya ya ce, “Haka Ubangiji ya faɗa, 20 idan ka iya hana dare da yini su bayyana a ƙayyadaddun lokatansu, 21 to, ashe, alkawarin da na yi wa bawana Dawuda zai tashi ke nan, har ya rasa ɗan da zai yi mulki a gadon sarautarsa, alkawarin kuma da na yi wa firistoci masu yi mini hidima, da ma'aikatana, zai tashi. 22 Kamar yadda ba a iya ƙidaya rundunan sammai ba, ba a iya kuma auna yashin teku ba, hakanan zan yawaita zuriyar bawana Dawuda da Lawiyawa, firistoci, masu yi mini hidima.” 23 Ubangiji kuma ya ce wa Irmiya, 24 “Ba ka ji abin da mutanen nan suke cewa ba? Wai, ‘Ubangiji ya ƙi iyalin nan biyu da ya zaɓa!’ Suka raina jama'ata, ba su kuma maishe ta al'umma ba. 25 Amma ni Ubangiji na ce, idan ban kafa alkawarina game da yini, da kuma game da dare, da ka'idodin da ke mulkin sammai da duniya ba, 26 sa'an nan zan ƙi zuriyar Yakubu da bawana Dawuda. Ba kuma zan zaɓi wani daga cikin zuriyarsa ya yi mulkin zuriyar Ibrahim, da ta Ishaku, da ta Yakubu ba. Amma zan mayar musu da arzikinsu, in nuna jinƙai a kansu.”

Irmiya 34

Faɗaka ga Zadakiya

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya sa'ad da Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da dukan sojojinsa, da dukan sojojin mulkokin al'umman da ke a ƙarƙashinsa, da dukan mutane suke yaƙi da Urushalima da dukan biranenta. 2 Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce wa Irmiya ya tafi, ya faɗa wa Zadakiya Sarkin Yahuza cewa, “Ni Ubangiji, zan ba da wannan birni a hannun Sarkin Babila, zai kuwa ƙone shi da wuta. 3 Ba za ka tsere masa ba, amma lalle za a kama ka, a ba da kai a hannunsa. Za ka ga Sarkin Babila ido da ido, ka kuma yi magana da shi fuska da fuska. Za ka tafi Babila. 4 Ya Zadakiya, Sarkin Yahuza, ka ji maganar da ni Ubangiji na faɗa a kanka, ba za ka mutu ta wurin takobi ba. 5 Za ka mutu da salama. Kamar yadda aka ƙona wa sarakuna marigayanka turare, haka kai ma mutane za su ƙona maka turare, za su yi makoki dominka suna cewa, ‘Kaito, sarki ya rasu.’ Ni Ubangiji na faɗa.” 6 Sai annabi Irmiya ya faɗa wa Zadakiya, Sarkin Yahuza, dukan maganan nan a Urushalima, 7 sa'ad da sojojin Sarkin Babila suke yaƙi da Urushalima da kuma dukan biranen da suka ragu na Yahuza, wato Lakish da Azeka. Waɗannan su kaɗai ne biranen Yahuza masu garu da suka ragu.

Ta da Alkawari game da Bayi, Ibraniyawa

8 Ubangiji kuma ya yi magana da Irmiya bayan da Zadakiya ya yi alkawari da dukan mutanen Urushalima don a yi musu shelar ba da 'yanci, 9 cewa kowa ya saki bayinsa, mata da maza, waɗanda ke Yahudawa. Kada kowa ya riƙe bawa wanda yake Bayahude, ɗan'uwansa. 10 Sai suka yi biyayya. Dukan sarakuna da dukan jama'a waɗanda suka yi alkawarin, cewa kowa zai 'yantar da bawansa ko baiwarsa, ba za su ƙara bautar da su ba, suka yi biyayya, suka 'yantar da su. 11 Daga baya kuwa suka sāke komo da waɗannan bayi, mata da maza waɗanda suka 'yantar, suka kuma mai da su bayi. 12 Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce, 13 “Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na yi alkawari da kakanninku lokacin da na fito da su daga ƙasar Masar daga bauta, na ce, 14 ‘A shekara ta bakwai, dole ne ku 'yantar da 'yan'uwanku, Ibraniyawa, waɗanda aka sayar muku, suka kuwa bauta muku shekara shida. Dole ne ku 'yantar da su daga bautarku.’ Amma kakanninku ba su kasa kunne gare ni ba. 15 A 'yan kwanakin da suka wuce kuka yi abu mai kyau a gabana da kuka tuba, har kuka yi wa juna shelar 'yanci. Kuka yi alkawari a gabana a Haikalin da ake kira da sunana. 16 Amma sai kuka sāke tunaninku, kuka ɓata sunana sa'ad da kowannenku ya komo da bayinsa, mata da maza, waɗanda kuka 'yantar, don su zauna yadda suke so. Ga shi kuma, kun komo da su su zama bayinku. 17 Domin haka ni Ubangiji na ce, ba biyayya kuka yi mini ba, da irin shelar 'yancin da kowannenku ya yi wa ɗan'uwansa da maƙwabcinsa, saboda haka ni zan yi muku shelar 'yanci zuwa mutuwa ta takobi, da annoba, da yunwa. Zan sa ku zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya. 18 Mutanen da suka keta alkawarina, ba su kuma kiyaye maganar alkawarin da suka yi a gabana ba, sa'ad da suka raba ɗan maraƙi kashi biyu, suka bi ta tsakiyarsa, 19 wato manyan fādawan Yahuza, da na Urushalima, da 'yan majalisa, da firistoci da dukan jama'ar ƙasa, waɗanda suka bi ta tsakanin rababben ɗan maraƙin, 20 zan bashe su a hannun abokan gabansu waɗanda suke neman ransu. Gawawwakinsu za su zama abincin tsuntsaye da namomin jeji. 21 Zadakiya, Sarkin Yahuza kuwa, da sarakunansa, zan bashe su a hannun abokan gābansu waɗanda suke neman ransu, wato sojojin Sarkin Babila, waɗanda suka tashi suka bar ku. 22 Ni Ubangiji zan umarce su su komo zuwa wannan birni don su yi yaƙi da shi, su ci shi, su ƙone shi da wuta. Zan sa biranen Yahuza su zama kufai, ba masu zama a ciki.”

Irmiya 35

Biyayyar Rekabawa

1 A lokacin da Yehoyakim, ɗan Yosiya ke mulkin Yahuza, sai Ubangiji ya ce wa Irmiya, 2 “Ka tafi gidan Rekabawa, ka yi magana da su, ka kawo su a Haikalin Ubangiji, cikin ɗayan ɗakunan, sa'an nan ka ba su ruwan inabi su sha.” 3 Sai na ɗauki Yazaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da 'yan'uwansa, da dukan 'ya'yansa maza da dukan iyalin gidan Rekabawa. 4 Na kawo su cikin Haikalin Ubangiji, a ɗakin 'ya'yan Hanan da Igdaliya, mutumin Allah. Ɗakin yana kusa da na shugabanni, a kan ɗakin Ma'aseya ɗan Shallum mai tsaron bakin ƙofa. 5 Sa'an nan na sa tuluna cike da ruwan inabi, da ƙoƙuna a gaban Rekabawa, sai na ce musu, “Ku sha ruwan inabi!” 6 Sai suka amsa, suka ce, “Ba za mu sha ruwan inabi ba, gama Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko 'ya'yanku, ba za ku sha ruwan inabi ba har abada, 7 ba kuma za ku gina ɗaki ba, ba kuwa za ku yi shuka ba, ba za ku yi dashe ba, ba za ku yi gonar inabi ba. Za ku zaune cikin alfarwai dukan kwanakin ranku, domin ku yi tsawon rai a ƙasar baƙuncinku.’ 8 Mu kuma muka yi biyayya da umarnin da Yonadab ɗan Rekab, kakanmu, ya yi mana, cewa kada mu sha ruwan inabi, mu da matanmu, da 'ya'yanmu mata da maza, 9 kada kuma mu gina wa kanmu gidajen zama. Ba mu da gonar inabi, ko gona ko iri. 10 Amma a alfarwai muke zamanmu. Mun yi biyayya da dukan abin da Yonadab kakanmu ya umarce mu. 11 Amma sa'ad da Nebukadnezzar Sarkin Babila ya kawo yaƙi a ƙasar, sai muka ce, ‘Bari mu tafi Urushalima domin muna jin tsoron sojojin Kaldiyawa da Suriyawa.’ Shi ya sa muke zaune a Urushalima.” 12 Sa'an nan Ubangiji ya yi magana da Irmiya ya ce, 13 “Haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na faɗa, ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima cewa, ‘Ba za ku karɓi umarnina, ku kasa kunne ga maganata ba?’ 14 Umarnin da Yonadab ɗan Rekab ya yi wa 'ya'yansa, kada su sha ruwan inabi, sun kuwa kiyaye shi. Ba su taɓa shan ruwan inabi ba har wa yau, domin suna biyayya da umarnin kakansu. Ni kuwa na yi ta yi muku magana, amma ba ku kasa kunne gare ni ba. 15 Na yi ta aiko muku da bayina annabawa, ina cewa, kowa ya bar muguwar hanyarsa, ya gyara ayyukansa, kada ya bauta wa gumaka. Ta haka za ku zauna a ƙasa wadda na ba ku, ku da kakanninku, amma ba ku kasa kunne, ku ji ni ba. 16 'Ya'yan Yonadab ɗan Rekab sun kiyaye umarnin da kakansu ya yi musu. Amma jama'an nan ba su yi mini biyayya ba. 17 Domin haka, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na ce zan kawo wa mutanen Yahuza da mazaunan Urushalima masifar da na ce zan kawo musu, domin na yi musu magana, ba su ji ba, na kira su, ba su amsa ba.” 18 Sai Irmiya ya ce wa Rekabawa, “Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Tun da ya ke kun kiyaye dukan abin da Yonadab kakanku ya umarce ku, 19 saboda haka Yonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa magaji wanda zai tsaya a gabana ba.’ ”

Irmiya 36

An Ƙone Littafi

1 A sa'ad da Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, yana shekara huɗu da sarauta, sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya, ya ce, 2 “Ka ɗauki takarda, ka rubuta dukan maganar da na yi maka a kan Isra'ila, da Yahuza, da dukan al'ummai, tun daga ran da na fara yi maka magana a zamanin Yosiya har ya zuwa yau. 3 Mai yiwuwa ne idan mutanen Yahuza suka ji dukan masifar da na yi niyya in aukar musu da ita, za su bar mugayen ayyukansu don in gafarta musu muguntarsu da zunubinsu.” 4 Sai Irmiya ya kirawo Baruk ɗan Neriya. Baruk kuwa ya rubuta maganar da Irmiya ya faɗa masa a takarda, wato dukan maganar da Ubangiji ya faɗa wa Irmiya. 5 Sai Irmiya ya umarci Baruk, ya ce, “An hana ni zuwa Haikali, 6 saboda haka kai za ka tafi. A ranar azumi za ka karanta wa mutane maganar Ubangiji, wadda ke a takardar da ka rubuta ta wurin shibtar da na yi maka. Ka karanta ta a cikin Haikali, a gaban mutanen Yahuza waɗanda suka fito daga biranensu. 7 Mai yiwuwa ne za su roƙi Ubangiji, su tuba, su bar mugayen ayyukansu, gama Ubangiji yana fushi ƙwarai, Ubangiji ya hurta hasala a kan wannan jama'a.” 8 Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya umarce shi. Ya karanta takardan nan ta maganar Ubangiji a Haikalin Ubangiji. 9 A watan tara a shekara ta biyar ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, sai dukan jama'ar Urushalima da dukan jama'ar da suka zo Urushalima daga biranen Yahuza suka yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji. 10 Sai Baruk ya karanta maganar Irmiya wadda ke a takardar, kowa yana ji, a cikin Haikali a ɗakin Gemariya ɗan Shafan, magatakarda. Ɗakinsa yana a shirayi na bisa a hanyar shiga Sabuwar Ƙofa ta Haikalin Ubangiji. 11 Sa'ad da Mikaiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji da ke a littafin, 12 sai ya gangara gidan sarki, ya shiga ɗakin magatakarda, inda dukan shugabanni suke zaune, wato Elishama magatakarda, da Delaiya ɗan Shemaiya, da Elnatan ɗan Akbor, da Gemariya ɗan Shafan, da Zadakiya ɗan Hananiya, da dukan sarakuna. 13 Sai Mikaiya ya faɗa musu dukan maganar da ya ji sa'ad da Baruk ya karanta littafin a kunnuwan jama'a. 14 Sai dukan sarakunan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya faɗa wa Baruk ya kawo littafin nan da ya karanta wa jama'a. Sai Baruk ɗan Neriya ya ɗauki littafin ya je wurinsu. 15 Suka ce masa ya zauna, ya karanta musu littafin. Baruk kuwa ya karanta musu. 16 Da suka ji dukan maganar, suka dubi juna a firgice, suka ce wa Baruk, “Ai, sai mu faɗa wa sarki wannan magana.” 17 Suka kuma tambayi Baruk, suka ce, “Ka faɗa mana yadda ka yi ka rubuta wannan magana. Ya yi maka shibta ne?” 18 Sai Baruk ya ce musu, “Ya yi mini shibtar dukan wannan magana ne, na kuwa rubuta su da tawada a takarda.” 19 Sarakunan kuwa suka ce wa Baruk, “Ka tafi, da kai da Irmiya ku ɓuya kada ku bari kowa ya san wurin da kuke.” 20 Suka tafi zauren sarki bayan sun ajiye littafin a ɗakin Elishama, magatakarda, suka sanar da sarki dukan abin da ke cikin littafin. 21 Sarki ya aiki Yehudi ya je ya kawo littafin. Sai ya je ya ɗauko littafin daga ɗakin Elishama magatakarda. Yehudi kuwa ya karanta wa sarki tare da dukan sarakunan da suke tsaye kewaye da sarkin. 22 A watan tara ne, sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, ga wuta tana ci cikin kasko a gabansa. 23 Da Yehudi ya karanta sakin layi uku ko huɗu sai sarki ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da ke ci a kasko, da haka ya ƙone littafin duka. 24 Duk da haka da sarkin da barorinsa suka ji maganar, ba wanda ya ji tsoro, balle su keta rigunansu don baƙin ciki. 25 Ko da ya ke Elnatan, da Delaiya, da Gemariya, sun faɗa wa sarki kada ya ƙone littafin, amma ya yi biris da su. 26 Sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, da Seraiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel, su kamo Baruk magatakarda da annabi Irmiya, amma Ubangiji ya ɓoye su! 27 Bayan da sarki ya ƙone littafin da Baruk ya rubuta ta wurin shibtar da Irmiya ya yi masa, sai Ubangiji ya yi wa Irmiya magana, ya ce, 28 ya ɗauki wata takarda ya rubuta dukan maganar da ke cikin littafin da Yehoyakim Sarkin Yahuza, ya ƙone. 29 Zai kuma ce wa Yehoyakim Sarkin Yahuza, “Haka Ubangiji ya ce maka, ka ƙone littafin, kana cewa, ‘Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle Sarkin Babila zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?’ 30 Saboda haka Ubangiji ya ce Yehoyakim, Sarkin Yahuza, ba zai sami māgaji wanda zai zauna a gadon sarautar Dawuda ba. Za a jefar da gawarsa a waje ta sha zafin rana, da dare kuma za ta sha matsanancin sanyi. 31 Zan hukunta shi, shi da zuriyarsa, da barorinsa saboda muguntarsu. Zan kawo dukan masifar da na hurta a kansu, da a kan mazaunan Urushalima, da a kan mutanen Yahuza, amma sun ƙi ji.” 32 Sai Irmiya ya ɗauko wata takarda ya ba Baruk, magatakarda, ɗan Neriya. Shi kuwa ta wurin shibtar Irmiya, ya rubuta dukan maganar da ke a wancan littafi, wanda Yehoyakim Sarkin Yahuza ya ƙone a wuta. An ƙara magana da yawa kamar ta dā.

Irmiya 37

An Sa Irmiya a Kurkuku

1 Zadakiya ɗan Yosiya, wanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila ya naɗa Sarkin Yahuza, ya yi mulki a maimakon Yekoniya ɗan Yehoyakim. 2 Amma shi da barorinsa, da mutanen ƙasar, ba wanda ya kasa kunne ga maganar Ubangiji wadda ya yi musu ta bakin annabi Irmiya. 3 Sai sarki Zadakiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya, da Zafaniya firist, ɗan Ma'aseya, a wurin annabi Irmiya cewa, “Ka yi addu'a ga Ubangiji Allah dominmu.” 4 A lokacin nan Irmiya yana kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a tsare shi a kurkuku ba tukuna. 5 Rundunar sojojin Fir'auna kuwa ta taho daga Masar, amma da Kaldiyawa waɗanda suka kewaye Urushalima da yaƙi suka ji labari, sai suka janye daga Urushalima. 6 Sai Ubangiji ya yi magana da annabi Irmiya, ya ce, 7 “Ni Ubangiji Allah na Isra'ila, na ce ka faɗa wa Sarkin Yahuza wanda ya aiko ka ka tambaye ni, ka faɗa masa cewa, ‘Rundunar sojojin Fir'auna, wadda ta kawo maka gudunmawa tana gab da juyawa zuwa ƙasarta a Masar. 8 Kaldiyawa kuwa za su komo su yi yaƙi da wannan birni. Za su ci birnin, su ƙone shi da wuta. 9 Ni Ubangiji, na ce kada ku ruɗi kanku da cewa Kaldiyawa ba za su dawo ba, gama ba shakka za su zo. 10 Ko da a ce za ku ci dukan rundunar sojojin Kaldiyawa wadda ke yaƙi da ku, sauran waɗanda kuka yi wa rauni da suke kwance a alfarwai za su tashi su ƙone birnin da wuta.’ ” 11 Da rundunar sojojin Kaldiyawa ta janye daga Urushalima saboda zuwan rundunar sojojin Fir'auna, 12 sai Irmiya ya tashi daga Urushalima zai tafi can ƙasar Biliyaminu, don ya karɓi nasa rabo tare da dangi. 13 A sa'ad da ya isa Ƙofar Biliyaminu, shugaban matsara, Irija ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama annabi Irmiya ya ce, “Kai kana gudu zuwa wurin Kaldiyawa ne.” 14 Sai Irmiya ya ce, “Ƙarya ce, ni ba gudu zuwa wurin Kaldiyawa nake yi ba.” Amma Irija bai yarda ba, sai ya kai shi wurin shugabanni. 15 Shugabanni suka yi fushi da Irmiya, suka yi masa d�ka, suka tsare shi a gidan Jonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku. 16 Irmiya ya yi kwanaki da yawa can cikin kurkukun.

Zadakiya ya Nemi Shawara ga Irmiya

17 Sarki Zadakiya ya aika a kawo masa Irmiya. Sarki kuwa ya shigar da shi gidansa, ya tambaye shi a asirce, ya ce, “Ko akwai wata magana daga wurin Ubangiji?” Sai Irmiya ya ce, “Akwai kuwa!” Ya ci gaba ya ce, “Za a ba da kai a hannun Sarkin Babila.” 18 Sai kuma ya tambayi sarki Zadakiya ya ce, “Wane laifi na yi maka, ko barorinka, ko wannan jama'a da ka sa ni a kurkuku? 19 Ina annabawanku waɗanda suka yi maka annabci cewa, ‘Sarkin Babila ba zai kawo wa ƙasarku yaƙi ba?’ 20 Yanzu ya maigirma sarki, ina roƙonka ka ji wannan roƙo da nake yi maka, kada ka mai da ni a gidan Jonatan magatakarda, domin kada in mutu a can.” 21 Sai sarki Zadakiya ya ba da umarni, suka sa Irmiya a gidan waƙafi. Aka riƙa ba shi malmalar abinci daga unguwar masu tuya kowace rana, har lokacin da abinci ya ƙare duka a birnin. Haka kuwa Irmiya ya zauna a gidan waƙafi.

Irmiya 38

An Fitar da Irmiya daga Rijiya Marar Ruwa

1 Shefatiya ɗan Mattan, da Gedaliya ɗan Fashur, da Yehukal ɗan Shelemiya, da Fashur ɗan Malkiya, suka ji maganar da Irmiya ke faɗa wa dukan mutane cewa, 2 “Ubangiji ya ce wanda ya zauna a wannan birni zai mutu da takobi, da yunwa, da annoba, amma wanda ya fita ya je wurin Kaldiyawa zai rayu, zai sami ransa kamar ganimar yaƙi. 3 Gama Ubangiji ya ce, hakika za a ba da wannan birni a hannun rundunar sojojin Sarkin Babila su ci shi.” 4 Sarakunan suka ce wa sarki, “A kashe mutumin nan, gama yana karya zuciyar sojojin da suka ragu a birnin, da zuciyar sauran jama'a duka ta wurin irin maganganun da yake faɗa musu. Gama wannan mutum ba ya neman jin daɗin zaman wannan jama'a sai dai wahala yake nemar musu.” 5 Sarki Zadakiya ya ce, “Ai, ga shi nan a hannunku, gama sarki ba zai yi abin da ba ku so ba.” 6 Sai suka ɗauki Irmiya suka saka shi a rijiyar Malkiya ɗan sarki, wadda ke gidan waƙafi. Suka zurara Irmiya a ciki da igiya. Ba ruwa a rijiyar, sai dai lāka, Irmiya ya nutse cikin lākar. 7 Ebed-melek, bābā, mutumin Habasha, wanda ke a gidan sarki, ya ji labari sun saka Irmiya a rijiya. A lokacin nan, sarki yana zaune a Ƙofar Biliyaminu. 8 Sai Ebed-melek ya fita, ya tafi gaban sarki, ya ce masa, 9 “Ya maigirma sarki, waɗannan mutane sun yi mugun abu da suka saka annabi Irmiya cikin fijiya, Zai mutu can da yunwa, gama ba sauran abinci a birnin.” 10 Sa'an nan sarki ya umarci Ebedmelek, mutumin Habasha, ya tafi da mutum talatin su tsamo annabi Irmiya daga cikin rijiyar kafin ya mutu. 11 Sai Ebed-melek ya tafi da mutanen, ya kuma tafi gidan sarki, a ɗakin ajiya, ya kwaso tsummoki da tsofaffin tufafi, ya zurara wa Irmiya a rijiyar. 12 Ebedmelek, mutumin Habasha, ya ce wa Irmiya ya sa tsummokin da tsofaffin tufafin a hammatarsa, ya zarga igiya, Irmiya kuwa ya yi yadda aka ce masa. 13 Suka jawo Irmiya da igiyoyi, suka fito da shi daga rijiya. Irmiya kuwa ya zauna a gidan waƙafi.

Zadakiya ya Nemi Shawarar Irmiya

14 Sarki Zadakiya ya aika a kirawo annabi Irmiya. Ya tafi ya sadu da Irmiya a ƙofa ta uku ta Haikalin Ubangiji. Sarki kuwa ya ce wa Irmiya, “Zan yi maka tambaya, kada kuwa ka ɓoye mini kome.” 15 Irmiya kuwa ya ce wa Zadakiya, “Idan na faɗa maka gaskiya za ka kashe ni, idan kuma na ba ka shawara, ba za ka karɓi shawarata ba.” 16 Sarki Zadakiya ya rantse wa Irmiya a ɓoye, ya ce, “Na rantse da Ubangiji, wanda ke ba mu rai, ba zan kashe ka ko in bashe ka a hannun waɗannan mutane da ke neman ranka ba.” 17 Irmiya ya ce wa Zadakiya, “Haka Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, idan ka miƙa wuya ga sarakunan Sarkin Babila, za ka tsira, ba kuwa za a ƙone birnin da wuta ba, kai da gidanka za ku tsira. 18 Amma idan ba ka miƙa wuya ga sarakunan Sarkin Babila ba, to, za a ba da wannan birni a hannun Kaldiyawa, za su ƙone shi da wuta. Kai kuma ba za ka tsira daga hannunsu ba.” 19 Sarki Zadakiya ya ce wa Irmiya, “Ina jin tsoron Yahudawa waɗanda suka gudu zuwa wurin Kaldiyawa. Kila a bashe ni a hannunsu, su ci mutuncina.” 20 Irmiya kuwa ya ce masa, “Ba za a bashe ka gare su ba. Kai dai ka yi biyayya da maganar Ubangiji wadda nake faɗa maka yanzu. Yin haka zai fi maka amfani, za ka tsira. 21 Amma idan ka ƙi miƙa wuya, to, ga abin da Ubangiji ya nuna mini a wahayi. 22 Ga shi, dukan matan da suka ragu a gidan Sarkin Yahuza, za a kai su wurin sarakunan Sarkin Babila, suna cewa, ‘Aminanka sun ruɗe ka, Sun rinjaye ka. Yanzu sun ga ƙafafunka sun nutse cikin laka, Sai suka rabu da kai.’ 23 “Dukan matanka da 'ya'yanka za a kai su wurin Kaldiyawa, kai kanka kuma ba za ka tsere musu ba, amma Sarkin Babila zai kama ka, birnin kuma za a ƙone shi da wuta.” 24 Sai Zadakiya ya ce wa Irmiya, “Kada ka bar wani ya san wannan magana, kai kuwa ba za a kashe ka ba. 25 Idan sarakuna suka ji, wai na yi magana da kai, in suka zo wurinka, suka ce, ‘Ka faɗa mana abin da ka faɗa wa sarki da abin da sarki ya faɗa maka, kada ka ɓoye mana kome mu kuwa ba za mu kashe ka ba.’ 26 Sai ka ce musu, ‘Na roƙi sarki da ladabi don kada ya mai da ni a gidan Jonatan, don kada in mutu a can.’ ” 27 Dukan sarakuna suka tafi wurin Irmiya suka tambaye shi. Shi kuwa ya amsa musu yadda sarki ya umarce shi. Sai suka daina magana da shi, tun da ya ke ba wanda ya ji maganar da ya yi da sarki. 28 Irmiya kuwa ya yi zamansa a gidan waƙafi har ranar da aka ci Urushalima da yaƙi.

Irmiya 39

Faɗuwar Urushalima

1 A watan goma a na shekara ta tara ta sarautar sarki Zadikiya, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar Sarkin Babila, da dukan sojojinsa suka zo, suka kewaye Urushalima da yaƙi. 2 A rana ta tara ga watan huɗu, a shekara ta goma sha ɗaya ta sarautar Zadakiya, sai aka huda garun birnin. 3 Sa'an nan da aka ci Urushalima, sai dukan sarakunan Sarkin Babila suka shiga, suka zauna a Ƙofar Tsakiya. Sarakuna, su ne Nergal-sharezer, da Samgar-nebo, da Sarsekim, wato Rabsaris, da Nergal-sharezer, wato Rabmag, da dukan sauran shugabannin Sarkin Babila. 4 Sa'ad da Zadakiya, Sarkin Yahuza, da dukan sojoji suka gan su, sai suka gudu, suka fita daga birnin da dare, ta hanyar gonar sarki a ƙofar da ke a tsakanin garu biyu. Suka nufi zuwa wajen Araba. 5 Amma sojojin Kaldiyawa suka bi su, suka ci wa Zadakiya a filayen Yariko. Suka kama shi, suka kawo shi gaban Sarkin Babila a Ribla a ƙasar Hamat, a can Nebukadnezzar ya yanka masa hukunci. 6 Sarkin Babila ya kashe 'ya'yan Zadakiya, maza, a Ribla a kan idon Zadakiya. Ya kashe dukan shugabannin Yahuza. 7 Ya kuma ƙwaƙule idanun Zadakiya, ya buga masa ƙuƙumi, ya kai shi Babila. 8 Sai Kaldiyawa suka ƙone gidan sarki, da gidajen jama'a. Suka kuma rushe garun Urushalima. 9 Sa'an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashi sauran mutane da suka ragu a birnin zuwa babila, wato mutanen da suka gudu zuwa wurinsa. 10 Amma ya bar matalauta waɗanda ba su da kome a ƙasar. Ya ba su gonakin inabi da waɗansu gonaki a ran nan.

Nebukadnezzar ya Lura da Irmiya

11 Sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya yi wa Nebuzaradan shugaban matsara umarni a kan Irmiya ya ce, 12 “Ka ɗauke shi ka lura da shi da kyau, kada ka yi masa wani mugun abu, amma ka yi masa dukan abin da yake so.” 13 Sai Nebuzaradan shugaban matsara, da Nebushazban, wato Rabsaris, da Nergal-sharezer, wato Rabmag, da dukan shugabannin Sarkin Babila, 14 suka aika aka kawo Irmiya daga gidan waƙafi, suka ba da Irmiya amana ga Gedaliya, ɗan Ahikam ɗan Shafan, don ya kai shi gida. Da haka Irmiya ya zauna tare da mutane.

Ebed-melek yana Sa Zuciya ga Kuɓuta

15 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a lokacin da aka kulle shi a gidan waƙafi, ya ce, 16 “Ka tafi ka faɗa wa Ebedmelek mutumin Habasha, cewa Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Zan sa masifa, ba alheri ba, ta auko wa wannan birni. Wannan kuwa zai faru a kan idanunka a wannan rana. 17 Amma a ranan nan, ni Ubangiji zan cece ka, ba za a ba da kai a hannun mutanen da kake jin tsoronsu ba. 18 Gama hakika zan cece ka, ba za ka mutu ta takobi ba. Za ka sami ranka kamar ganimar yaƙi, domin ka dogara gare ni, ni Ubangiji na faɗa.’ ”

Irmiya 40

Irmiya da waɗanda suka Ragu sun Zauna tare da Gedaliya

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya bayan da Nebuzaradan shugaban matsara ya sake shi daga Rama, sa'ad da ya yi masa ƙuƙumi tare da waɗanda aka kwaso daga Urushalima da Yahuza, za su Babila. 2 Shugaban matsara ya ware Irmiya, sa'an nan ya ce masa, “Ubangiji Allahnka ne ya hurta wannan masifa a kan wurin nan. 3 Ga shi kuwa, ya yi kamar yadda ya faɗa, domin kun yi wa Ubangiji zunubi, ba ku yi biyayya da muryarsa ba, don haka wannan masifa ta auko muku. 4 Yau na kwance ƙuƙumin da ke a wuyanka, idan ka ga ya fi maka kyau, ka zo mu tafi tare zuwa Babila, to, sai ka zo, zan lura da kai da kyau, amma idan ba ka ga haka ya yi maka daidai ba, to, kada ka bi ni. Ga dukan ƙasa shimfiɗe a gabanka, ka tafi duk inda ka ga ya fi maka kyau.” 5 Amma Irmiya bai tafi ba, sai Nebuzaradan ya ce masa, “Ka koma wurin Gedaliya ɗan Ahikam, jikan Shafan, wanda Sarkin Babila ya sa ya zama mai mulkin garuruwan Yahuza, ka zauna tare da shi da mutanen, ko kuwa ka tafi duk inda ka ga ya fi maka kyau.” Sai ya ba Irmiya abinci da kyauta, sa'an nan ya sallame shi. 6 Irmiya kuwa ya tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam, a Mizfa, ya zauna tare da shi da mutanen da suka ragu a ƙasar. 7 Sa'ad da shugabannin sojoji waɗanda ke a karkarar Yahudiya tare da mutanensu, suka ji labari Sarkin Babila ya sa Gedaliya ɗan Ahikam ya zama mai mulkin ƙasar, a kan matalauta, wato mata da maza, da yara na ƙasar, waɗanda ba a kwashe su zuwa bautar talala a Babila ba, 8 sai shugabannin, wato Isma'ilu ɗan Netaniya, da Yohenan da Jonatan, 'ya'yan Kareya, da Seraiya ɗan Tanhumet, da 'ya'yan Efai, mutumin Netofa, da Yazaniya ɗan mutumin Ma'aka suka tafi tare da mutanensu zuwa wurin Gedaliya a Mizfa. 9 Gedaliya ɗan Ahikam, jikan shafan ya rantse musu da mutanensu, ya ce, “Kada ku ji tsoron bauta wa Kaldiyawa, ku yi zamanku a ƙasar, ku bauta wa Sarkin Babila, za ku kuwa zauna lafiya. 10 Amma ni zan zauna a Mizfa, in zama wakilinku a wurin Kaldiyawa waɗanda za su zo wurinmu. Ku tattara inabi, da 'ya'yan itatuwa na kaka, da man zaitun, ku tanada su a gidajenku, ku zauna a garuruwan da kuka ci.” 11 Haka kuma Yahudawan da ke a Mowab, da Ammon, da Edom, da kuma sauran ƙasashe suka ji, cewa Sarkin Babila ya bar waɗansu mutane a Yahuza, ya kuma shugabantar da Gedaliya ɗan Ahikam, jikan Shafan a kansu, 12 sai dukan Yahudawa suka koma daga inda aka kora su zuwa ƙasar Yahuza. Suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. Suka tattara ruwan inabi da 'ya'yan itatuwa na kaka da yawa.

Maƙarƙashiyar Isma'ilu gāba da Gedaliya

13 Yohenan ɗan Kareya kuwa, tare da dukan shugabannin sojojin da ke cikin sansani a karkara, suka zo wurin Gedaliya a Mizfa. 14 Suka ce masa, “Ko ka sani Ba'alis Sarkin Ammonawa ya aiko Isma'ilu ɗan Netaniya ya kashe ka?” Amma Gedaliya ɗan Ahikam, bai gaskata su ba. 15 Sai Yohenan ɗan Kareya ya yi magana da Gedaliya a Mizfa a asirce ya ce, “Ka bar ni in tafi in kashe Isma'ilu ɗan Netaniya, ba wanda zai sani. Don me shi zai kashe ka, ya watsa dukan Yahudawan da ke tare da kai, har sauran Yahudawan da suka ragu su halaka.” 16 Amma Gedaliya ɗan Ahikam ya ce wa Yohenan ɗan Kareya, “Kada ka kuskura ka yi wannan abu, gama ƙarya ce kake yi wa Isma'ilu.”

Irmiya 41

1 A watan bakwai sai Isma'ilu ɗan Netaniya, ɗan Elishama, na cikin zuriyar sarauta, ɗaya daga cikin ma'aikatan sarki, ya zo a wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa tare da mutum goma. Sa'ad da suke cin abinci tare a Mizfa, 2 Isma'ilu ɗan Netaniya, da mutanen nan goma da ke tare da shi, suka tashi suka sare Gedaliya ɗan Ahikam ɗan shafan, da takobi, suka kashe shi, wato Gedaliya wanda Sarkin Babila ya naɗa ya zama mai mulkin ƙasar. 3 Isma'ilu kuma ya kashe dukan Yahudawa da ke tare da Gedaliya a Mizfa da waɗansu sojojin Kaldiyawa da ke a wurin. 4 Kashegari bayan da an kashe Gedaliya, tun kafin wani ya sani, 5 sai waɗansu mutane, su tamanin, suka zo daga Shekem, da Shilo, da Samariya, da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage. Suka kawo hadaya ta gari da hadayar turare domin su miƙa a Haikalin Ubangiji. 6 Sai Isma'ilu ɗan Netaniya ya fito daga cikin Mizfa yana kuka, don ya tarye su. Da ya sadu da su, sai ya ce musu, “Ku zo mu tafi wurin Gedaliya ɗan Ahikam!” 7 Sa'ad da suka shiga birnin, sai Isma'ila ɗan Nataniya da mutanen da ke tare da shi suka kashe su, suka jefa su a wata rijiya. 8 Amma waɗansu mutum goma daga cikinsu suka ce wa Isma'ila, “Kada ka kashe mu, gama muna da rumbunan alkama, da na sha'ir, da kuma man zaitun da zuma a ɓoye a cikin gonaki.” Sai ya bar su, bai kashe su tare da abokansu ba. 9 Rijiyar da Isma'ilu ya zuba dukan gawawwakin mutanen da ya kashe mai zurfi ce, sarki Asa ne ya haƙa saboda tsoron Ba'asha Sarkin Isra'ila. Isma'ilu ɗan Netaniya kuwa ya cika ta da gawawwakin mutanen da ya kashe. 10 Sai Isma'ilu ya kwashe dukan sauran mutanen da ke Mizfa, gimbiyoyi da dukan jama'ar da aka bari a Mizfa, waɗanda Nebuzaradan, shugaban matsara, ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Isma'ilu ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya haye da su zuwa yankin Ammonawa. 11 Amma sa'ad da Yohenan ɗan Kareya, tare da dukan shugabannin sojoji da ke tare da shi suka ji irin wannan mugun aiki wanda Isma'ilu ɗan Netaniya ya yi, 12 sai suka kwashe mutanensu duka, suka tafi su yi yaƙi da Isma'ilu ɗan Netaniya. Suka iske shi a babban tafkin da ke a Gibeyon. 13 Sa'ad da dukan jama'ar da Isma'ilu ya kwashe suka ga Yohenan ɗan Kareya, da dukan shugabannin sojoji tare da shi, sai suka yi murna. 14 Dukan mutanen nan da Isma'ilu ya kwashe su ganima daga Mizfa, suka juya, suka koma wurin Yohenan ɗan Kareya. 15 Amma Isma'ilu ɗan Netaniya tare da mutum takwas suka tsere suka gudu zuwa wurin Ammonawa. 16 Sai Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji da ke tare da shi, suka kwashe dukan sauran jama'a, waɗanda Isma'ilu ɗan Netaniya ya kamo daga Mizfa bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato sojoji da mata, da yara, da bābāni, su ne Yohenan ya komo da su daga Gibeyon. 17 Suka fa tafi suka zauna a wurin Kimham kusa da Baitalami. Suna nufin su tafi Masar, 18 don gudun Kaldiyawa, gama suna jin tsoronsu, domin Isma'ilu ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam wanda Sarkin Babila ya naɗa shi mai mulkin ƙasa.

Irmiya 42

Jawabin Irmiya ga Yohenan

1 Shugabannin sojoji, da Yohenan ɗan Kareya, da Yazaniya ɗan Hoshaiya, da jama'a duka, daga ƙarami zuwa babba, suka zo, 2 suka ce wa annabi Irmiya, “Muna roƙonka, ka roƙi Ubangiji Allahnka dominmu, dukanmu da muka ragu, gama mu kima muka ragu daga cikin masu yawa, kamar yadda kake ganinmu da idonka. 3 Ka yi mana addu'a domin Ubangiji Allahnka ya nuna mana hanyar da za mu bi, da kuma abin da za mu yi.” 4 Annabi Irmiya kuwa ya ce musu, “Na ji abin da kuka ce. Ga shi kuwa, zan yi addu'a ga Ubangiji Allahnku kamar yadda kuka roƙa. Kowace irin amsa da Ubangiji ya bayar, zan faɗa muku, ba zan ɓoye muku kome ba.” 5 Sa'an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji mai gaskiya, mai aminci ya zama shaida a tsakaninmu, idan ba mu yi duk yadda Ubangiji Allahnka ya aiko ka gare mu ba. 6 Ko magari ne ko mugu ne, za mu yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnmu wanda muka aike ka wurinsa, gama zai zama alheri a gare mu idan mun yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnmu.” 7 Bayan kwana goma sai Ubangiji ya yi magana da Irmiya. 8 Sai Irmiya ya kira Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda ke tare da shi, da dukan jama'a tun daga ƙarami har zuwa babba. 9 Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra'ila, wanda kuka aike ni da koke-kokenku wurinsa ya ce, 10 ‘Idan za ku zauna a ƙasan nan, to, zan gina ku, ba zan rushe ku ba. Zan dasa ku, ba zan tumɓuke ku ba, gama zan janye masifar da na aukar muku. 11 Kada ku ji tsoron Sarkin Babila, shi wanda kuke jin tsoronsa. Kada ku ji tsoronsa,’ in ji Ubangiji, ‘gama ina tare da ku, zan cece ku, in kuɓutar da ku daga hannunsa. 12 Zan yi muku jinƙai in sa sarkin ya ji ƙanku, ya bar ku ku zauna a ƙasarku.’ 13 “Amma idan kuka ce ba za ku zauna a wannan ƙasa ba, kuka ƙi yin biyayya da muryar Ubangiji Allahnku, 14 kuna cewa, ‘Mun ƙi, mu, ƙasar Masar za mu tafi, inda ba za mu ga yaƙi ba, ba za mu ji ƙarar ƙahon yaƙi ba, yunwa kuma ba za ta same mu ba, a can za mu zauna.’ 15 To, sai ku ji maganar Ubangiji, ya ku sauran mutanen Yahuza, Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya ce, ‘Idan zuwa Masar kuka sa gaba don ku tafi ku zauna a can, 16 to, takobin nan da kuke jin tsoro, zai ci muku can a ƙasar Masar, yunwan nan kuma da kuke jin tsoro za ta bi ku zuwa Masar ta tsananta muku, a can za ku mutu. 17 Duk waɗanda suka sa gaba zuwa Masar domin su zauna can, da takobi, da yunwa, da annoba su ne ajalinsu. Ba wanda zai ragu, ba wanda zai tsira daga masifar da zan aukar musu.’ 18 “Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa'ad da kuka tafi Masar. Za ku zama najasa, da abin ƙyama, da la'ana, da abin ba'a. Wannan wuri kuwa ba za ku ƙara ganinsa ba.’ 19 “Ya ku sauran mutanen Yahuza, Ubangiji ya ce, ‘Kada ku tafi Masar.’ Ku tabbata fa na faɗakar da ku yau, 20 cewa in kun ratse, to, a bakin ranku. Gama kun aike ni wurin Ubangiji Allah cewa, ‘Ka roƙar mana Ubangiji Allahnmu. Dukan abin da Ubangiji Allahnmu ya ce ka faɗa mana kuma za mu aikata.’ 21 A wannan rana kuwa na faɗa muku abin da ya ce, amma ba ku yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnku a kan kowane abin da ya aiko ni in faɗa muku ba. 22 Domin haka yanzu fa ku sani takobi, da yunwa, da annoba, su ne ajalinku a wurin can da kuke sha'awar ku zauna.”

Irmiya 43

Tafiya zuwa Masar

1 Sa'ad da Irmiya ya gama faɗa wa dukan jama'a maganar da Ubangiji Allahnsu ya aiko musu da ita, 2 sai Yazaniya ɗan Hoshaiya, da Yohenan ɗan Kareya, da dukan 'yan tsagera, suka ce wa Irmiya, “Ƙarya kake yi, Ubangiji Allahnmu bai aiko ka da cewa kada mu tafi, mu zauna a Masar ba! 3 Amma Baruk ɗan Neriya shi ne ya sa ka faɗi wannan magana gāba da mu, don ka bashe mu a hannun Kaldiyawa domin su kashe mu, ko kuwa su kai mu bauta a Babila.” 4 Yohenan ɗan Kareya, da dukan shugabannin sojoji, da dukan jama'a, ba su yi biyayya da umarnin Ubangiji, su zauna a ƙasar Yahuza ba. 5 Amma Yohenan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji suka kwashe sauran mutanen Yahuza duka waɗanda suka komo suka zauna a ƙasar Yahuza, daga wurin al'ummai, inda aka kora su, 6 mata, da maza, da yara, da gimbiyoyi, da kowane mutum da Nebuzaradan shugaban matsara ya bar wa Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da annabi Irmiya, da Baruk ɗan Neriya. 7 Suka zo ƙasar Masar, gama ba su yi biyayya da muryar Ubangiji ba. Suka sauka a Tafanes. 8 Ubangiji kuwa ya yi magana da Irmiya a Tafanes ya ce, 9 “Kwashi manyan duwatsu da hannunka, ka ɓoye su a ƙofar shiga fādar Fir'auna a Tafanes a idon mutanen Yahuza, 10 ka kuma ce musu, ‘In ji Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ga shi, zan aika wa bawana Nebukadnezzar ya zo ya kafa kursiyin sarautarsa a kan duwatsun nan waɗanda na ɓoye. Zai buɗe babbar alfarwarsa a wurin. 11 Nebukadnezzar zai zo ya buga ƙasar Masar. Zai ba annoba waɗanda aka ƙaddara su ga annoba, waɗanda aka ƙaddara ga bauta, za a kai su bauta. Waɗanda aka ƙaddara ga takobi, za su mutu ta takobi. 12 Zai cinna wa gidajen gumakan Masar wuta, zai ƙone su, ya tafi da waɗansu, zai tsabtace ƙasar Masar kamar yadda makiyayi yakan kakkaɓe ƙwarƙwata daga cikin tufafinsa, zai kuwa tashi daga wurin lafiya. 13 Zai kuma farfashe al'amudan duwatsu na On a ƙasar Masar. Zai ƙone gidajen gumakan Masar da wuta.’ ”

Irmiya 44

Jawabin Ubangiji zuwa ga Yahudawan da ke Masar

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan dukan Yahudawan da ke zaune a ƙasar Masar, a garin Migdol, da Tafanes, da Memfis, da dukan ƙasar Fatros, ya ce, 2 “Ni Ubangiji Mai Runduna Allah na Isra'ila, na ce, ku da kanku kun ga masifar da na aukar wa Urushalima, da dukan garuruwan Yahuza. Yanzu sun zama kufai, ba wanda ke zaune a cikinsu, 3 domin mutanen da ke cikinsu sun aikata mugayen abubuwa da suka tsokane ni. Sun miƙa wa gumaka hadayu, suka kuma bauta musu, ko da ya ke su, ko ku, ko kakanninku, ba ku san su ba. 4 Na yi ta aika muku da dukan bayina annabawa waɗanda suka faɗa muku kada ku aikata wannan mugun abin banƙyama. 5 Amma ba su kasa kunne ba, ba su kuwa ji ba, da za su juyo daga mugayen ayyukansu na miƙa wa gumaka hadayu. 6 Saboda haka fushina ya yi zafi a kan garuruwan Yahuza da titunan Urushalima, don haka a yanzu sun lalace, suka zama kufai. 7 “Yanzu, ni Ubangiji Allah Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ina tambaya, me ya sa kuke jawo wa kanku wannan babbar masifa, kuna so ku hallakar da mata da maza, yara da jarirai daga cikin Yahuza, har a rasa wanda zai wanzu? 8 Me ya sa kuke tsokanata da ayyukan hannuwanku, kuna miƙa wa gumaka hadayu a ƙasar Masar inda kuka zo don ku zauna? Yin haka zai sa a hallaka ku, ku zama abin la'ana da zargi a cikin dukan ƙasashen duniya. 9 Ko kun manta da mugayen ayyukan kakanninku, da na sarakunan Yahuza da na matansu, da naku, da na matanku, waɗanda suka aikata a ƙasar Yahuza da kan titunan Urushalima? 10 Amma har wa yau ba ku ƙasƙantar da kanku ba, ba ku ji tsorona ba, ba ku kuwa kiyaye dokokina da umarnaina ba, waɗanda na ba ku ku da kakanninku. 11 “Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, zan aukar muku da masifa, in hallaka mutanen Yahuza duka. 12 Sauran mutanen Yahuza kuwa waɗanda suka ragu, waɗanda suke niyyar zuwa ƙasar Masar da zama, zan sa dukansu su halaka a can. Takobi da yunwa za su kashe dukansu a Masar, da yaro da babba. Za su zama abin la'antawa, da abin tausayi, da abin zargi, da abin kunya. 13 Zan hukunta dukan waɗanda ke zaune a Masar kamar yadda na hukunta wa Urushalima da takobi, da yunwa, da annoba. 14 Ba waɗansu daga cikin mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, da za su tsere ko su rayu. Ba wani daga cikinsu da zai koma Yahuza inda suke marmarin komawa da zama, ba wanda zai koma, sai dai 'yan gudun hijira.” 15 Sai dukan mazan da suka sani matansu sun miƙa wa gumaka hadayu, da dukan matan da ke tsaye a wurin, da dukan Yahudawan da ke zaune a Fatros, babban taron jama'a, suka ce wa Irmiya, 16 “Ba za mu kasa kunne ga jawabin da kake yi mana da sunan Ubangiji ba! 17 Za mu aikata dukan abin da muka faɗa. Za mu miƙa wa gunkiyan nan, wato sarauniyar sama, hadayu, da hadayu na sha kamar yadda kakanninmu, da shugabanninmu suka yi a garuruwan Yahuza, da kan titunan Urushalima. A lokacin kuwa muna da abinci a wadace, muka arzuta, ba wata wahala. 18 Amma tun da muka daina miƙa wa sarauniyar sama hadayu, da hadayu na sha, ba mu da kome, sai dai takobi da yunwa suke kashe mu.” 19 Mata kuma suka ce, “Sa'ad da muka toya waina ga siffar sarauniyar sama, muka miƙa mata hadayu, da hadayu na sha, ai, mazanmu sun goyi bayan abin da muka yi.” 20 Sa'an nan Irmiya ya ce wa dukan mutane, mata da maza, waɗanda suka ba shi irin amsan nan, ya ce, 21 “A kan turaren da ku da kakanninku, da sarakunanku, da shugabanninku, da mutanen ƙasar, kuka ƙona a garuruwan Yahuza da a titunan Urushalima, kuna tsammani Ubangiji bai san su ba, ko kuna tsammani ya manta? 22 Ubangiji ba zai yarda da mugayen ayyukanku ba, da ƙazantarku da kuka aikata, don haka ƙasarku a yau ta zama kufai ba mai zama a cikinta. Ta zama abin ƙyama da la'ana. 23 Saboda kun ƙona turare, kun yi wa Ubangiji zunubi, ba ku yi biyayya da muryarsa ba, ba ku kiyaye dokokinsa, da umarnansa, da sharuɗansa ba, shi ya sa wannan masifa ta auko muku a yau.” 24 Sai Irmiya ya ce wa dukan mutane duk da mata, “Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuza da ke a Masar. 25 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, ‘Ku da matanku kun faɗa da bakinku, kun kuma aikata da hannuwanku, cewa za ku aikata wa'adodin da kuka yi na ƙona turare, da miƙa hadayu na sha ga sarauniyar sama.’ To, sai ku tabbatar da wa'adodinku, ku cika su! 26 Domin haka ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuza da ke zaune a ƙasar Masar. ‘Ni Ubangiji na rantse da sunana Maɗaukaki, cewa ba zan yarda kuma wani mutumin Yahuza da ke ƙasar Masar ya ambaci sunana da yin rantsuwa, cewa ya rantse da zatin Ubangiji ba.’ 27 Ga shi, ina lura da su, ba domin alheri ba, amma domin in aukar musu da masifa. Takobi da yunwa za su hallaka dukan mutanen Yahuza waɗanda ke a ƙasar Masar. 28 ‘Yan kaɗan ne za su tsere wa takobi, za su kuwa koma daga ƙasar Masar zuwa ƙasar Yahuza. Sauran mutanen Yahuza da suka ragu, waɗanda suka zo Masar da zama, za su sani ko maganar wa za ta cika, tasu ko kuwa tawa. 29 Ni Ubangiji na ce, wannan zai zama muku alama, cewa zan hukunta ku a wannan wuri domin ku sani lalle maganata ta aukar muku da masifa za ta cika. 30 Zan kuma ba da Fir'auna Hofra, Sarkin Masar, a hannun abokan gabansa, da waɗanda suke neman ransa, kamar yadda na ba da Zadakiya, Sarkin Yahuza, a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila wanda ya zama abokin gābansa, ya kuwa nemi ransa.’ ”

Irmiya 45

Jawabin Irmiya ga Baruk

1 A shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim, ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza, Baruk ɗan Neriya ya rubuta abin da Irmiya ya faɗa masa. 2 “Ubangiji Allah na Isra'ila ya ce maka, kai Baruk, 3 kai ka ce, ‘Kaitona, gama Ubangiji ya ƙara baƙin ciki a kan wahalaina, na gaji da nishina, ba ni da hutu!’ 4 “Sai ka faɗa wa Baruk cewa, ‘Ni Ubangiji na ce, ga shi, abin da na gina zan rushe shi, abin da kuma na dasa zan tumɓuke shi, wato ƙasar ɗungum. 5 Kana nemar wa kanka manyan abubuwa? Kada ka neme su, gama zan kawo masifa a kan dukan 'yan adam, amma zan kuɓutar da ranka kamar ganima, a dukan wuraren da za ka tafi.’ ”

Irmiya 46

Annabci a kan Masar

1 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan sauran al'umma. 2 Ya yi magana game da sojojin Fir'auna, Sarkin Masar, waɗanda ke a bakin Kogin Yufiretis a Karkemish, waɗanda Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya ci su da yaƙi a shekara ta huɗu ta sarautar Yehoyakim ɗan Yosiya, Sarkin Yahuza. 3 Masarawa suka yi ihu, suka ce, “Ku shirya kutufani da garkuwa, Ku matso zuwa wurin yaƙi! 4 Ku ɗaura wa dawakanku sirdi, ku hau! Ku tsaya a wurarenku da kwalkwali a ka! Ku wasa māsunku! Ku sa kayan yaƙi!” 5 Ubangiji ya yi tambaya ya ce, “Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, An ci sojojinsu, suna gudu, Ba su waiwayen baya, akwai tsoro a kowane sashi.” 6 Masu saurin gudu ba za su tsere ba, Hakanan kuma jarumi, A arewa a gefen Kogin Yufiretis, Sun yi tuntuɓe, sun fādi. 7 Wanene wannan mai tashi kamar Kogin Nilu, Kamar kogunan da ruwansu ke ambaliya? 8 Masar tana tashi kamar Nilu, Kamar kogunan da ruwansu ke ambaliya. Masar ta ce, “Zan tashi, in rufe duniya, Zan hallaka birane da mazauna cikinsu.” 9 Ku haura, ku dawakai, Ku yi sukuwar hauka, ku karusai! Bari sojoji su fito, Mutanen Habasha da Fut masu riƙon garkuwoyi, Da mutanen Lud, waɗanda suka iya riƙon baka. 10 Wannan rana ta Ubangiji, Allah Mai Runduna ce, Ranar ɗaukar fansa ce don ya rama wa maƙiyansa. Takobi zai ci, ya ƙoshi, Ya kuma sha jininsu, ya ƙoshi, Gama Ubangiji Allah Mai Runduna zai hallaka maƙiyansa, A arewa, a bakin Kogin Yufiretis. 11 Ku mutanen Masar, ku haura zuwa Gileyad Don ku samo ganye! A banza kuke morar magunguna, Ba za ku warke ba. 12 Kunyarku ta kai cikin sauran al'umma, Kukanku kuma ya cika duniya. Soja na faɗuwa bisa kan soja. Dukansu biyu sun faɗi tare. 13 Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan zuwan Nebukadnezzar, Sarkin Babila, don ya yi yaƙi da ƙasar Masar. 14 “Ku yi shelarsa cikin garuruwan Masar, Cikin Migdol, da Memfis, da Tafanes, Ku ce, ‘Ku tsaya, ku yi shiri, Gama takobi yana cin waɗanda ke kewaye da ku!’ 15 Me ya sa gunkinka, Afis, ya fāɗi, Wato bijimi, gunkinka bai tsaya ba? Domin Ubangiji ya tunkuɗe shi ƙasa! 16 Sun yi ta fāɗuwa, Suna faɗuwa a kan juna, Sai suka ce, ‘Mu tashi mu koma wurin mutanenmu, Zuwa ƙasar haihuwarmu, mu gudu daga takobin azzalumi!’ 17 “Ku ba Fir'auna Sarkin Masar sabon suna, ‘Mai yawan surutu, wanda bai rifci zarafi ba!’ 18 Ni wanda sunana Ubangiji Mai Runduna Sarki ne, Na rantse da raina, wani zai ɓullo, Kamar Tabor a cikin tsaunuka, Ko kuwa kamar Karmel a bakin teku. 19 Ya ku mazaunan Masar, Ku shirya kayanku don zuwa bauta, Gama Memfis za ta lalace, ta zama kufai, Ba mai zama a ciki. 20 “Masar kyakkyawar karsana ce, Amma bobuwa daga arewa ta aukar mata! 21 Sojojin ijararta kamar 'yan maruƙa ne, masu yawan kitse, Sun ba da baya, sun gudu, ba su tsaya ba, Domin ranar masifarsu ta zo, Lokacin halakarsu ya yi. 22 Masar tana gudu, tana huci kamar maciji, Gama abokan gābanta suna zuwa da ƙarfi, Za su faɗo mata da gatura kamar masu saran itatuwa. 23 Ni Ubangiji na ce, za su sari kurminta, Ko da ya ke ba su ƙirguwa, Gama suna da yawa kamar fara, Ba su lasaftuwa. 24 Za a kunyatar da mutanen Masar, An bashe su a hannun mutanen arewa.” 25 Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, ya ce, “Ga shi, zan hukunta Amon na No, da Fir'auna, da Masar, tare da allolinta, da sarakunanta, wato Fir'auna, tare da waɗanda ke dogara gare shi. 26 Zan bashe su a hannun waɗanda ke neman ransu, wato a hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, da shugabanninsa. Daga baya kuma mutane za su zauna a Masar kamar dā. Ni Ubangiji na faɗa. 27 “Ya bawana Yakubu, kada ka ji tsoro, Kada ka firgita, ya Isra'ila. Gama zan cece ka daga ƙasa mai nisa, Zan ceci zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yakubu zai komo, ya yi zamansa da rai kwance, Ba wanda zai razanar da shi. 28 Ni Ubangiji na ce, Kada ka ji tsoro, ya bawana Yakubu, Gama ina tare da kai. Zan hallaka dukan sauran al'umma sarai inda na kora ka. Amma ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hukunta ka yadda ya kamata, Ba zan bar ka ba hukunci ba.”

Irmiya 47

Jawabin Ubangiji a kan Filistiyawa

1 Kafin Fir'auna ya ci Gaza da yaƙi Ubangiji ya yi magana da Irmiya a kan Filistiyawa. 2 Ubangiji ya ce, “Ga shi, ruwa yana tasowa daga arewa, Zai zama kogi da ke ambaliya. Zai malala bisa ƙasa da dukan abin da ke cikinta, Da birni da mazauna cikinsa, Maza za su yi kuka, Dukan mazaunan ƙasar za su yi kuka. 3 Da jin takawar kofatan dawakai, Da amon karusai da ƙafafun karusai, Ubanni ba su juya, su dubi 'ya'yansu ba, Domin hannuwansu sun yi laƙwas, 4 Domin lokacin hallaka dukan Filistiyawa ya yi. Za a datse wa Taya da Sidon kowane taimakon da ya ragu, Gama Ubangiji zai hallaka Filistiyawa Waɗanda ke baƙin teku na Kaftor. 5 Baƙin ciki zalla ya sami Gaza, Ashkelon ta lalace. Ya ƙattin mutane, yaushe za ku daina tsattsage kanku? 6 Ya takobin Ubangiji, yaushe za ka huta? Sai ka koma ƙubenka, Ka huta, ka yi shiru! 7 Ƙaƙa zai huta, tun da ni Ubangiji ne na umarce shi? Ni Ubangiji na umarce shi ya yi yaƙi da Ashkelon Da mazauna a bakin teku.”

Irmiya 48

Jawabin Ubangiji a kan Mowab

1 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila ya faɗa a kan Mowab, “Kaiton Nebo, gama ta lalace! An kunyatar da Kiriyatayim, an ci ta da yaƙi, An kunyatar da kagararta, an rushe ta. 2 Darajar Mowab ta ƙare. Ana shirya mata maƙarƙashiya a Heshbon, ‘Bari mu je mu ɓata ta daga zaman al'umma!’ Ke kuma Madmen za ki yi shiru, Takobi zai runtume ki. 3 Muryar kuka daga Horonayim tana cewa, ‘Risɓewa da babbar halaka!’ 4 “An hallakar da Mowab, Ƙanananta suna kuka. 5 Gama a hawan Luhit, za su hau da kuka, Gama a gangaren Horonayim, Suna jin kukan wahalar halaka. 6 Ku gudu don ku tserar da rayukanku, Ku gudu kamar jakin jeji. 7 “Kun dogara ga ƙarfinku da wadatarku, Amma yanzu za a ci ku da yaƙi, Kemosh zai tafi bauta Tare da firistocinsa da shugabanninsa. 8 Mai hallakarwa zai shiga kowane gari, Don haka ba garin da zai tsira. Kwari da tudu za su lalace, Ni Ubangiji na faɗa. 9 Ku ba Mowab fikafikai, Gama za ta tashi ta gudu, Garuruwanta za su zama kango, Ba mazauna cikinsu. 10 “La'ananne ne shi wanda ke yin aikin Ubangiji da ha'inci, La'ananne ne shi kuma wanda ya hana wa takobinsa jini. 11 “Tun daga ƙuruciya Mowab tana zama lami lafiya, Hankali kwance, Ba a jujjuya ta daga tulu zuwa tulu ba, Ba a taɓa kai ta bauta ba, Domin haka daɗin ɗanɗanonta bai rabu da ita ba, Ƙanshinta kuma bai sāke ba.” 12 Ubangiji ya ce, “Domin haka kwanaki suna zuwa, sa'ad da zai aika da mutane su tuntsurar da tuluna, su zubar da ruwan inabi, su farfasa tulunanta. 13 Sa'an nan Kemosh zai kunyatar da Mowab, kamar yadda Betel wadda Isra'ilawa suka dogara gare ta ta kunyatar da su. 14 “Don me kake cewa, ‘Mu jarumawa ne, mayaƙan gaske?’ 15 Mai hallaka Mowab da garuruwanta ya taho, Zaɓaɓɓun majiya ƙarfinta sun gangara mayanka, Ni sarki, mai suna Ubangiji Mai Runduna, na faɗa. 16 Masifar Mowab ta kusato, Halakarta kuma tana gaggabtowa. 17 “Ku yi makoki dominta, ku da ke kewaye da ita, Dukanku da kuka san sunanta, ku ce, ‘Ƙaƙa sandan sarauta mai iko Da sanda mai daraja ya karye?’ 18 Ku da ke zaune a Dibon, Ku sauka daga wurin zamanku mai daraja, Ku zauna a busasshiyar ƙasa, Gama mai hallaka Mowab ya zo ya yi gab da ku. Ya riga ya rushe kagararku. 19 Ku mazaunan Arower, Ku tsaya a kan hanya, ku jira, Ku tambayi wanda yake gudu Da wanda ke tserewa, Abin da ya faru. 20 An kunyatar da Mowab, ta rushe. Ku yi kuka dominta, Ku faɗa a Arnon, cewa Mowab ta halaka. 21 “Hukunci ya auka kan garuruwan da ke a ƙasar fili, wato Holon, da Yahaza, da Mefayat, 22 da Dibon, da Nebo, da Bet-diblatayim, 23 da Kiriyatayim, da Bet-gamal, da Ba'almeyon, 24 da Kiriyot, da Bozara. Hukunci ya zo a kan dukan garuruwan Mowab na nesa da na kusa. 25 An karye ikon Mowab da ƙarfinta, ni Ubangiji na faɗa. 26 “Ku sa Mowab ta yi maye domin ta tayar wa Ubangiji. Za ta yi birgima cikin amanta, mutane kuwa za su yi dariya. 27 Kin yi wa mutanen Isra'ila dariya. A kowane lokacin da kika ambaci sunansu, sai ki taɗa kanki da raini kamar an kama su tare da ɓarayi. 28 “Ku mazaunan Mowab, ku bar garuruwanku, Ku tafi, ku zauna a kogwanni, Ku zama kamar kurciya wadda ke yin sheƙarta a bakin kwazazzabo. 29 Mun ji labarin girmankan Mowab, da ɗaukaka kanta, Da alfarmarta, da izgilinta, Tana da girmankai ƙwarai. 30 Ni Ubangiji na san Mowab tana da girmankai, Alfarmarta ta banza ce, Ayyukanta kuma na banza ne. 31 Don haka zan yi kuka saboda Mowab duka, Zan kuma yi baƙin ciki saboda mutanen Kir-heres. 32 Zan yi kuka saboda kurangar inabin Sibma Fiye da yadda zan yi kuka saboda mutanen Yazar. Rassanku sun haye teku har sun kai Yazar, Amma mai hallakarwa ya faɗo a kan 'ya'yan itatuwanku da damuna Da kan amfanin inabinku. 33 An ɗauke farin ciki da murna daga ƙasa mai albarka ta Mowab, Na hana ruwan inabi malala daga wurin matsewarsa, Ba wanda ke matse shi, yana ihu na murna, Ihun da ake yi ba na murna ba ne. 34 “Mutanen Heshbon da na Eleyale suna kururuwa ana iya jin kururuwansu a Yahaza. Ana iya jinta kuma a Zowar, da Horonayim, da Eglat-shelishiya. Har ma ruwan Nimra ya ƙafe. 35 Zan hana mutanen Mowab miƙa hadayu na ƙonawa a tuddai, da miƙa wa gumakansu sadaka, ni Ubangiji na faɗa. 36 “Zuciyata tana makoki domin Mowab da Kir-heres kamar wanda ke kukan makoki da sarewa saboda wadatarsu ta ƙare. 37 Gama kowa ya aske kansa da gemunsa, sun tsattsage hannuwansu. Kowa kuma ya sa rigar makoki. 38 Ba abin da ake yi a bisa kan soraye da dandali na Mowab sai baƙin ciki, gama na farfashe Mowab kamar tulun da ba a so, ni Ubangiji na faɗa. 39 An farfashe Mowab, ta yi kuka, ta kunyata! Ta zama abin dariya da abin tsoro ga waɗanda ke kewaye da ita. 40 “Ni Ubangiji na ce, Wani zai yi firiya da sauri kamar gaggafa, Zai shimfiɗa fikafikansa a kan Mowab. 41 Za a ci garuruwa da kagarai da yaƙi, A wannan rana zukatan sojojin Mowab Za su zama kamar zuciyar macen da ke naƙuda. 42 Za a hallaka Mowab daga zaman al'umma, Domin ta tayar wa Ubangiji. 43 Tsoro, da rami, da tarko suna jiranku, Ya mazaunan Mowab, Ni Ubangiji na faɗa. 44 Wanda ya guje wa tsoro, Zai fāɗa a rami, Wanda kuma ya fito daga cikin rami, Tarko zai kama shi. Gama na sa wa Mowab lokacin da zan hukunta ta, Ni Ubangiji na faɗa. 45 “A ƙarƙashin inuwar Heshbon 'yan gudun hijira suna tsaye ba ƙarfi. Gama wuta ta ɓullo daga Heshbon, Harshen wuta kuma ya fito daga Sihon, Ta ƙone goshin Mowab da ƙoƙwan kai na 'yan tayarwa. 46 Kaitonku, ya Mowabawa! Mutanen Kemosh sun lalace, An kai 'ya'yanku mata da maza cikin bauta. 47 “Amma zan komar da mutanen Mowab nan gaba, Ni Ubangiji na faɗa.” Wannan shi ne hukuncin Mowab.

Irmiya 49

Jawabin Ubangiji a kan Ammonawa

1 Wannan shi ne abin da Ubangiji ya faɗa akan Ammonawa, “Isra'ila ba shi da 'ya'ya ne? Ko kuwa ba shi da māgada ne? Me ya sa waɗanda ke bautar Milkom suka mallaki inda Gad ke zama, Suka zauna a garuruwanta? 2 Domin haka lokaci yana zuwa, Sa'ad da zan sa mutanen garin Rabba ta Ammon su ji busar yaƙi. Rabba za ta zama kufai, Za a ƙone ƙauyukanta da wuta, Sa'an nan Isra'ila zai mallaki waɗanda suka mallake shi. Ni Ubangiji na faɗa. 3 “Ki yi kuka, ya Heshbon, gama Ai ta zama kufai! Ku yi kuka, ku mutanen Rabba, ku sa tufafin makoki. Ku yi gudu, kuna kai da kawowa a cikin garuka, Gama za a kai Milkom bauta tare da firistocinsa da wakilansa. 4 Me ya sa kuke taƙama da ƙarfinku, Ƙarfinku da ke ƙarewa, ku mutane marasa aminci? Kun dogara ga dukiyarku, Kuna cewa, ‘Wanene zai iya gāba da mu?’ 5 Ga shi, zan kawo muku razana daga waɗanda ke kewaye da ku, Za a kore ku, kowane mutum zai kama gabansa, Ba wanda zai tattara 'yan gudun hijira. Ni Ubangiji Allah Mai Runduna na faɗa. 6 “Amma daga baya zan sa Ammonawa su wadata kuma, Ni Ubangiji na faɗa.”

Jawabin Ubangiji a kan Edom

7 Ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya faɗa a kan Edom, “Ba hikima kuma a cikin Teman? Shawara ta lalace a wurin masu basira? Hikima ta lalace ne? 8 Ku mazaunan Dedan, ku juya, ku gudu, Ku ɓuya cikin zurfafa, Gama zan kawo masifa a kan Isuwa A lokacin da zan hukunta shi, 9 Idan masu tsinkar 'ya'yan inabi sun zo wurinka Ba za su rage abin kala ba? Idan kuma ɓarayi sun zo da dare, Za su ɗauki iyakacin abin da suke so kurum. 10 Amma na tsiraita Isuwa sarai, Na buɗe wuraren ɓuyarsa, Har bai iya ɓoye kansa ba, An hallakar da mutanen Isuwa Tare da 'yan'uwansa da maƙwabtansa, Ba wanda ya ragu. 11 Ka bar marayunka, ni zan rayar da su. Matanka da mazansu sun mutu, Sai su dogara gare ni.” 12 Ubangiji ya ce, “Ga shi, waɗanda ba a shara'anta su ga shan ƙoƙon hukunci ba, za su sha shi, to, kai za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, amma lalle za ka sha shi! 13 Gama ni Ubangiji na rantse da zatina, cewa Bozara za ta zama abar tsoro, da abar dariya, da kufai, da abar la'ana. Dukan garuruwanta za su zama kufai har abada.” 14 Irmiya ya ce, “Na karɓi saƙo daga wurin Ubangiji. An aiki jakada a cikin al'ummai cewa, ‘Ku tattara kanku, ku zo ku yi gāba da ita, Ku tasar mata da yaƙi!’ 15 Gama ga shi, zan maishe ki ƙanƙanuwa cikin al'ummai, Abar raini a wurin mutane. 16 Tsoronki da ake ji da girmankanki sun ruɗe ki, Ke da kike zaune a kogon dutse, a kan tsauni, Ko da ya ke kin yi gidanki can sama kamar gaggafa, Duk da haka zan komar da ke ƙasa, Ni Ubangiji na faɗa.” 17 Ubangiji ya ce, “Edom za ta lalace, duk wanda ya bi ta wurin zai gigice, ya yi tsaki saboda dukan masifunta. 18 Abin da zai faru ga Edom zai zama daidai da abin da ya faru ga Saduma, da Gwamrata, da biranen da ke kusa da su, a lokacin da aka kaɓantar da su. Ba wanda zai zauna cikinta, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a cikinta, ni Ubangiji na faɗa. 19 Kamar yadda zaki yakan fito daga cikin kurmin Urdun, garin ya fāda wa babban garken tumaki, haka zan sa nan da nan su gudu daga gare ta. Zan naɗa wani wanda na zaɓa, gama wa ke kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Ina makiyayin da ya isa ya yi gāba da ni? 20 Domin haka, ku ji shirin da ni Ubangiji na yi wa Edom, da abin da nake nufin yi wa mazaunan Teman. Hakika za a tafi da su, har da ƙanana na garken tumaki, zan kuma sa wurin kiwonsu ya zama ƙeƙuwa saboda su. 21 Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza, za a kuma ji muryar kukansu har a Bahar Maliya. 22 Wani zai tashi da sauri, ya yi sama kamar gaggafa. Zai buɗe fikafikansa a kan Bozara. Zukatan sojojin Edom za su zama kamar zuciyar macen da ke naƙuda.”

Jawabin Ubangiji a kan Dimashƙu

23 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Dimashƙu, “Hamat da Arfad sun gigice, Domin sun ji mugun labari, sun narke saboda yawan damuwa, Ba za su iya natsuwa ba. 24 Dimashƙu ta yi halin ƙaƙa naka yi, Ta juya, ta gudu, Tsoro ya kama ta, Azaba da baƙin ciki sun kama ta kamar na naƙuda. 25 Ƙaƙa aka manta da sanannen birni, Birnin da ke cike da murna? 26 A waccan rana samarinta za su fāɗi a dandalinta. Za a hallaka sojojinta duka, Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 27 Zan kuma sa wuta a garun Dimashƙu, Za ta kuwa cinye fādodin Ben-hadad.”

Jawabin Ubangiji a kan Kedar da Hazor

28 Ga abin da Ubangiji ya faɗa a kan Kedar da sarakunan Hazor, waɗanda sarki Nebukadnezzar ya ci da yaƙi, “Ku tashi zuwa Kedar, Ku hallaka mutanen gabas. 29 Za a kwashe alfarwansu da garkunansu, Da labulan alfarwansu, da dukan kayansu. Za a kuma tafi da raƙumansu, Za a gaya musu cewa, ‘Razana ta kewaye ku!’ 30 “Ku mazaunan Hazor, ku gudu zuwa nesa, Ku ɓuya cikin zurfafa, ni Ubangiji na faɗa, Gama Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya shirya muku maƙarƙashiya, Ya ƙulla mugun nufi game da ku. 31 Ku tashi ku fāɗa wa al'ummar da ke zama lami lafiya, Waɗanda ba su da ƙofofi ko ƙyamare, Suna zama su kaɗai. 32 “Za a washe raƙumansu da garkunan shanunsu ganima, Zan watsar da masu yin kwaskwas ko'ina, Zan kuma kawo musu masifu daga kowace fuska, Ni Ubangiji na faɗa. 33 Hazor za ta zama kufai har abada, wurin zaman diloli, Ba wanda zai zauna a ciki, ba wanda kuma zai yi zaman baƙunci a wurin.”

Jawabin Ubangiji a kan Elam

34 Maganar da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Elam a farkon sarautar Zadakiya Sarkin Yahuza. 35 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan karya bakan Elam, inda ƙarfinta yake. 36 Zan sa iska ta hura a kan Elam daga kusurwoyi huɗu na samaniya. Za ta watsar da mutane ko'ina, Har ba ƙasar da za a rasa mutumin Elam a ciki. 37 Zan sa mutanen Elam su ji tsoron maƙiyansu waɗanda ke neman ransu. Da zafin fushina zan kawo musu masifa, In sa a runtume su da takobi, Har in ƙare su duka, Ni Ubangiji na faɗa. 38 Zan kafa gadon sarautata a Elam, Zan hallaka sarkinta da shugabanninta. 39 Amma daga baya zan sa Elam kuma ta wadata. Ni Ubangiji na faɗa.”

Irmiya 50

Jawabin Ubangiji a kan Babila

1 Jawabin da Ubangiji ya yi wa annabi Irmiya a kan Babila da ƙasar Kaldiyawa ke nan, 2 “Ku ba da labari ga sauran al'umma, ku yi shela, Ku ta da tuta, ku yi shela, Kada ku ɓuya, amma ku ce, ‘An ci Babila da yaƙi, An kunyatar da Bel, An kunyatar da siffofinta, Merodak ya rushe, Gumakanta kuma sun ragargaje!’ 3 “Wata al'umma za ta taso daga arewa gāba da ita, za ta mai da ƙasar abar ƙyama, ba wanda zai zauna ciki. Mutum da dabba duk sun watse, kowa ya bar ta.” 4 Ubangiji ya ce, “Sa'ad da lokacin nan ya yi, mutanen Isra'ila da na Yahuza za su zo tare, suna kuka, suna nemana, ni Ubangiji Allahnsu. 5 Za su tambayi hanyar Sihiyona, sa'an nan su bi ta, suna cewa, ‘Bari mu haɗa kanmu don mu yi madawwamin alkawari da Ubangiji, alkawari wanda ba za a manta da shi ba.’ 6 “Mutanena sun zama kamar ɓatattun tumaki, Waɗanda makiyayansu suka bauɗar da su, Suka ɓata a cikin tsaunuka, Suna kai da kawowa daga wannan dutse zuwa wancan. Sun manta da shingensu. 7 Duk waɗanda suka same su, sun cinye su. Maƙiyansu suka ce, ‘Ba mu yi laifi ba,’ Gama sun yi wa Ubangiji laifi, wanda yake tushen gaskiya, Ubangiji wanda kakanninsu suka dogara gare shi. 8 “Ku gudu daga cikin Babila, Ku fita kuma daga cikin ƙasar Kaldiyawa, Ku zama kamar bunsurai waɗanda ke ja gaban garke. 9 Ga shi, zan kuta manyan ƙasashe daga arewa Su faɗa wa Babila da yaƙi. Za su ja dāgar yaƙi gāba da ita, su cinye ta. Kibansu kamar na gwanayen mayaƙa ne Waɗanda ba su komowa banza. 10 Za a washe Kaldiyawa, Waɗanda suka washe su kuwa za su ƙoshi, Ni Ubangiji na faɗa. 11 “Saboda kuna murna, kuna farin ciki, Ku da kuka washe gādona, Saboda kuma kuna tsalle kamar karsana a cikin ciyawa, Kuna haniniya kamar ingarmu, 12 Domin haka za a kunyatar da Babila sosai, inda kuka fito. Za ta zama ta baya duka a cikin sauran al'umma, Za ta zama hamada, busasshiyar ƙasa. 13 Saboda fushin Ubangiji, ba wanda zai zauna a cikinta, Za ta zama kufai, Duk wanda ya bi ta wajen Babila, zai ji tsoro, Zai kuma yi tsaki saboda lalacewarta. 14 “Dukanku 'yan baka, ku ja dāga, ku kewaye Babila, Ku harbe ta, kada ku rage kibanku, Gama ta yi wa Ubangiji zunubi. 15 Ku kewaye ta da kuwwar yaƙi! Ta ba da gari, Ginshiƙanta sun fāɗi. An rushe garunta, Gama wannan sakayya ce ta Ubangiji. Ku sāka mata, ku yi mata kamar yadda ta yi. 16 Ku datse wa Babila mai shuka, Da mai yanka da lauje a lokacin girbi. Saboda takobin azzalumi, Kowa zai koma wurin mutanensa, Kowa kuma zai gudu zuwa ƙasarsa.” 17 “Isra'ilawa kamar tumaki ne waɗanda zakuna suka bi su suna kora. Da farko dai Sarkin Assuriya ne ya cinye su. Yanzu kuwa Sarkin Babila, wato Nebukadnezzar, shi ne ke gaigayi ƙasusuwansu. 18 Saboda haka ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila na ce, zan yi wa Sarkin Babila da ƙasarsa hukunci, kamar yadda na hukunta Sarkin Assuriya. 19 Zan komar da Isra'ila a makiyayarsa, zai yi kiwo a Karmel da Bashan. Zai sami biyan bukatarsa a tsaunukan Ifraimu da na Gileyad. 20 Ni Ubangiji na ce sa'ad da lokacin nan ya yi za a nemi laifi da zunubi a cikin Isra'ila da Yahuza, amma ba za a samu ba, gama zan gafarta wa sauran da suka ragu. 21 “Ku haura ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da mazaunan Fekod. Ku kashe, ku hallaka su sarai, Ku aikata dukan abin da na umarce ku, Ni Ubangiji na faɗa. 22 Hargowar yaƙi tana cikin ƙasar, Da kuma babbar hallakarwa! 23 Ga yadda aka karya gudumar dukan duniya! Ga yadda Babila ta zama abar ƙyama ga sauran al'umma! 24 Na kafa miki tarko, ya kuwa kama ki, ya Babila, Ke kuwa ba ki sani ba. An same ki, an kama, Domin kin yi gāba da ni.” 25 Ubangiji ya buɗe taskar makamansa, Ya fito da makaman hasalarsa, Gama Ubangiji Allah Mai Runduna yana da aikin da zai yi a ƙasar Kaldiyawa. 26 Ku zo, ku fāɗa mata daga kowane sashi. Ku buɗe rumbunanta, Ku tsittsiba ta kamar tsibin hatsi, Ku hallakar da ita ɗungum, Kada wani abu nata ya ragu. 27 Ku kashe dukan bijimanta, a kai su mayanka! Kaitonsu, gama kwanansu ya ƙare, Lokacin hukuncinsu ya yi. 28 Ku ji, sun gudu sun tsere daga ƙasar Babila, Don su faɗa cikin Sihiyona, Sakayyar Ubangiji Allahnmu domin Haikalinsa. 29 “Ku kirawo 'yan baka, dukan waɗanda sukan ja baka, su faɗa wa Babila. Ku kafa sansani kewaye da ita, kada ku bar kowa ya tsira. Ku sāka mata bisa ga dukan ayyukanta, gama ta raina Ubangiji Mai Tsarki na Isra'ila. 30 Domin haka samarinta za su fāɗi a tituna. Za a hallaka sojojinta duka a wannan rana, Ni Ubangiji na faɗa. 31 “Ga shi, ina gaba da ke, ke Babila, mai girmankai. Gama ranar da zan hukunta ki, ta zo, Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 32 Mai girmankai za ta yi tuntuɓe ta fāɗi, Ba kuwa wanda zai tashe ta, Zan ƙone garuruwanta da wuta, Zan kuma hallaka dukan abin da ke kewaye da ita. 33 “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, An danne mutanen Isra'ila da na Yahuza, Duk waɗanda suka kama su bayi sun riƙe su da ƙarfi. Sun ƙi su sake su. 34 Mai fansarsu mai ƙarfi ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa. Hakika zai tsaya musu don ya kawo wa duniya salama, Amma zai kawo wa mazaunan Babila fitina. 35 Ni Ubangiji na ce, Akwai takobi a kan Kaldiyawa, Da a kan mazaunan Babila, Da a kan ma'aikatanta da masu hikimarta, 36 Akwai takobi a kan masu sihiri Don su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta Don a hallaka su. 37 Akwai takobi a kan mahayan dawakanta, da a kan karusanta, Da a kan sojojin da ta yi ijara da su Don su zama kamar mata, Akwai takobi a kan dukan dukiyarta domin a washe ta. 38 Fari zai sa ruwanta ya ƙafe, Gama ƙasa tana cike da gumaka waɗanda suka ɗauke hankalin mutane. 39 “Domin haka namomin jeji da diloli za su zauna a Babila, Haka kuma jiminai. Ba za a ƙara samun mazauna a cikinta ba har dukan zamanai. 40 Abin da ya faru da Saduma da Gwamrata, Da biranen da ke kewaye da su, Shi ne zai faru da Babila. Ba mutumin da zai zauna cikinta. 41 “Ga mutane suna zuwa daga arewa, Babbar al'umma da sarakuna Suna tahowa daga wurare masu nisa na duniya. 42 Suna riƙe da baka da māshi, Mugaye ne marasa tausayi. Amonsu yana kama da rurin teku, Suna shirya don yin yaƙi da ke, ya Babila. 43 Sarkin Babila ya ji labarinsu, Hannuwansa suka yi suwu. Wahala da azaba sun kama shi kamar mace mai naƙuda. 44 “Ni Ubangiji ina zuwa kamar zakin da ke fitowa daga kurmin Urdun zuwa makiyaya. Nan da nan zan sa su gudu daga gare ta. Sa'an nan zan naɗa mata wanda na zaɓa. Wa ke kama da ni? Wa zai yi ƙarata? Wane shugaba zai yi gāba da ni? 45 Saboda haka ku ji shirin da Ubangiji ya yi gāba da Babila, da nufin ya yi gaba da ƙasar Kaldiyawa. Hakika za a tafi da ƙananansu, garke zai zama kango. 46 Duniya za ta girgiza sa'ad da ta ji an ci Babila da yaƙi. Za a ji kukanta cikin sauran al'umma.”

Irmiya 51

Hukuncin Ubangiji a kan Babila

1 Ubangiji ya ce, “Ga shi, zan kawo iskar ɓarna a kan Babila Da mazaunan Kaldiya. 2 Zan aika da masu casawa zuwa Babila, za su casa ta, Su bar ƙasarta kango. Za su kewaye ta a kowane sashi A wannan ranar masifa. 3 Kada ku bar maharbi ya yi harbi da bakansa, Kada kuma ya sa kayan yaƙinsa, Kada ku rage samarinta, Ku hallaka dukan sojojinta. 4 Za su fāɗi matattu a ƙasar Kaldiyawa, Za a sassoke su a titunansu.” 5 Allah na Isra'ila da Yahuza, Ubangiji Mai Runduna, bai yashe su ba, Ko da ya ke sun yi wa Mai Tsarki na Isra'ila zunubi. 6 Ku gudu daga cikin Babila, Bari kowa ya ceci ransa, Kada a hallaka ku tare da ita, Gama a wannan lokaci Ubangiji zai sāka mata, Zai sāka mata bisa ga alhakinta. 7 Babila ta zama ƙoƙon zinariya a hannun Ubangiji, Ta sa dukan duniya ta yi maye. Ƙasashen duniya sun sha ruwan inabinta, suka haukace. 8 Farat ɗaya, Babila ta fāɗi, ta kakkarye, Ku yi kuka dominta! Ku samo mata magani domin azabar da take sha, watakila ta warke. 9 Mun ba Babila magani, amma ba ta warke ba. Bari mu ƙyale ta, kowannenmu ya koma garinsu, Gama hukuncinta ya kai sammai, ya yi tsawo har samaniya. 10 Ubangiji ya baratar da mu a fili, Bari mu tafi mu yi shelar aikin Ubangiji Allahnmu a cikin Sihiyona. 11 Ku wasa kibau, ku cika kwaruruwanku! Ubangiji ya ta da ruhun sarakunan Mediyawa, Domin yana niyyar hallaka Babila. Gama Ubangiji zai yi ramuwa saboda Haikalinsa. 12 Ku ta da tuta don a faɗa wa garun Babila, Ku ƙarfafa matsara, Ku sa su su yi tsaro, Ku kuma sa 'yan kwanto! Ga shi, Ubangiji ya yi niyya, ya kuwa aikata Abin da ya faɗa a kan mazaunan Babila. 13 Ƙarshenki ya zo, Ke mai zama kusa da ruwa mai yawa, Mai yawan dukiya. Ajalinki ya auka. 14 Ubangiji Mai Runduna ya rantse da zatinsa, ya ce, “Hakika zan cika Babila da mutane kamar fāra, Za su kuwa raira waƙar nasara a kanta.” 15 Ubangiji ne ya halicci ƙasa da ikonsa, Ya kafa duniya da hikimarsa, Ya kuma shimfiɗa sammai da fahiminsa. 16 Bisa ga umarninsa ruwan da ke samaniya yakan yi ruri, Yakan sa gajimare su tashi daga ƙarshen duniya, Yakan sa walƙiya ta walƙata cikin ruwan sama, Yakan sa iska ta haura daga cikin taskokinsa. 17 Kowane ɗan adam wawa ne, marar ilimi, Kowane maƙerin zinariya kuma zai sha kunya daga wurin gumakansa, Gama siffofinsa na ƙarya ne, ba numfashi a cikinsu. 18 Su marasa amfani ne, aikin ruɗarwa ne kawai, Za su lalace a lokacin da za a hukunta su. 19 Amma wanda ke wajen Yakubu ba haka yake ba, Domin shi ne ya halicci dukan abu, Isra'ila kuwa abin mallakarsa ne, Ubangiji Mai Runduna ne sunansa. 20 Ubangiji ya ce, “Kai ne guduma da kayan yaƙina, Da kai ne na farfasa ƙasashen duniya, Da kai ne na hallaka mulkoki. 21 Da kai ne na karya doki da mahayinsa, 22 Da kai ne na farfasa karusa da mahayinsa. Da kai ne na kakkarya mace da namiji, Da kai ne na kakkarya tsoho da saurayi, Da kai ne na kakkarya saurayi da budurwa, 23 Da kai ne na kakkarya makiyayi da garkensa, Da kai ne na kakkarya manoma da dawakan nomansa, Da kai ne na kakkarya masu mulki da shugabanni.” 24 Ubangiji ya ce, “Zan sāka wa Babila da dukan mazaunan Kaldiya a ganin idanunku saboda dukan muguntar da suka aikata a Sihiyona. 25 Ga shi, ina gaba da kai, ya dutse mai hallakarwa, Wanda ya hallaka duniya duka. Zan miƙa hannuna gāba da kai, Zan mirgino da ƙasa daga ƙwanƙolin dutse, Zan maishe ka ƙonannen dutse. 26 Ba za a sami dutsen yin kusurwa, ko na kafa harsashen gini a cikinka ba, Amma za ka zama marar amfani har abada.” 27 Ku ta da tuta a duniya, Ku busa wa ƙasashen duniya ƙaho, Ku shirya ƙasashe don su yi yaƙi da ita, Ku kirawo mulkokin Ararat, da na Minni, da na Ashkenaz, su yi yaƙi da ita. Ku naɗa sarkin yaƙi wanda zai shugabanci yaƙin da za a yi da ita, Ku kawo dawakai kamar fāra. 28 Ku shirya ƙasashe su yi yaƙi da ita, Sarakunan Mediyawa, da masu mulkinsu, da shugabanninsu, Da kowace ƙasar da ke ƙarƙashin mulkinsu. 29 Duniya ta girgiza, tana makyarkyata saboda azaba, Gama nufin Ubangiji na gāba da Babila ya tabbata, Nufinsa na mai da ƙasar Babila kufai, inda ba kowa. 30 Sojojin Babila sun daina yaƙi, suna zaune a cikin kagaransu. Ƙarfinsu ya ƙare, sun zama mata, An sa wa wuraren zamanta wuta, An karya ƙyamaren ƙofofin garinta. 31 Maguji yana biye da maguji a guje, Jakada yana biye da jakada, Don su faɗa wa Sarkin Babila, cewa an ci birninsa a kowane gefe. 32 An ƙwace mashigai An ƙone fadamu da wuta, Sojoji sun gigice. 33 Ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila na ce, “Mutanen Babila sun zama kamar daɓen masussuka A lokacin da ake sussuka, Ba kuwa da daɗewa ba lokacin girbe ta zai zo.” 34 Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya cinye Urushalima, Ya ragargaza ta, Ya maishe ta kufai, Ya haɗiye ta kamar yadda dodon ruwa yakan yi, Ya cika cikinsa da kayan marmarinta, Ya tatse ta sarai. 35 Bari mutanen Sihiyona su ce, “Allah ya sa muguntar da mutanen Babila suka yi mana ta koma kansu!” Bari kuma mutanen Urushalima su ce, “Allah ya sa hakkin jininmu ya koma kan Kaldiyawa!” 36 Ubangiji ya ce, “Zan tsaya muku, Zan ɗaukar muku fansa, Zan sa tekunsu da maɓuɓɓugarsu su ƙafe. 37 Babila za ta zama tarin juji, wurin zaman diloli, Abar ƙyama da abar ba'a, inda ba kowa. 38 Mutanen Babila za su yi ruri kamar zakuna, Su yi gurnani kamar 'ya'yan zaki. 39 Sa'ad da suke cike da haɗama zan yi musu biki, In sa su sha, su yi maye, su yi murna. Za su shiga barcin da ba za su farka ba. 40 Zan kai su mayanka kamar 'yan raguna, da raguna, da bunsurai. 41 “An ci Babila, Ita wadda duniya duka ke yabo an cinye ta da yaƙi, Ta zama abar ƙyama ga sauran al'umma! 42 Teku ta malalo a kan Babila, Raƙuman ruwa masu hauka sun rufe ta. 43 Garuruwanta sun zama abin ƙyama, Ta zama hamada, inda ba ruwa, Ƙasar da ba mazauna, Ba kuma mutumin da zai ratsa ta cikinta. 44 Zan hukunta Bel, gunkin Babila, Zan sa ya yi aman abin da ya haɗiye, Ƙasashen duniya ba za su ƙara bumbuntowa wurinsa ba. Garun Babila ya rushe!” 45 “Ku fito daga cikinta, ya jama'ata, Kowa ya tsere da ransa daga zafin fushin Ubangiji. 46 Kada zuciyarku ta yi suwu, Kada kuma ku ji tsoro saboda labarin da ake ji a ƙasar, Labari na wannan shekara dabam, na wancan kuma dabam, A kan hargitsin da ke a ƙasar, Mai mulki ya tasar wa mai mulki. 47 Saboda haka kwanaki suna zuwa, Sa'ad da zan hukunta gumakan Babila, Za a kunyatar da dukan ƙasar Babila, Dukan matattunta za su faɗi a tsakiyarta. 48 Sa'an nan sama da duniya, da dukan abin da ke cikinsu, Za su raira waƙar farin ciki, Domin masu hallakarwa daga arewa da za su auko mata, Ni Ubangiji na faɗa.” 49 Babila za ta fāɗi, Saboda mutanen Isra'ila da dukan mutanen duniya waɗanda ta kashe. 50 Ku waɗanda kuka tsere wa takobi! Ku gudu! Kada ku tsaya! Ku tuna da Ubangiji a can nesa inda kuke, Ku kuma yi ta tunawa da Urushalima. 51 Mun sha kunya saboda zargin da ake yi mana, Kunya ta rufe mu, Gama baƙi sun shiga tsarkakan wurare na Haikalin Ubangiji. 52 “Domin haka kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “Sa'ad da zan hukunta gumakan Babila, da dukan ƙasarta, Waɗanda aka yi wa rauni, za su yi nishi. 53 Ko da Babila za ta hau samaniya, Ta gina kagara mai ƙarfi a can, Duk da haka zan aiki masu hallakarwa a kanta, Ni Ubangiji na faɗa.” 54 Ku ji muryar kuka daga Babila, Da hargowar babbar hallakarwa daga ƙasar Kaldiyawa! 55 Gama Ubangiji yana lalatar da Babila, Yana kuma sa ta kame bakinta na alfarma, Sojoji suna kutsawa kamar raƙuman ruwa, Suna ta da muryoyinsu. 56 Gama mai hallakarwa ya auka wa Babila, An kama sojojinta, An kuma kakkarya bakunansu, Gama Ubangiji shi Allah ne, mai sakayya, Zai yi sakayya sosai. 57 “Zan sa mahukuntanta, da masu hikimarta, Da masu mulkinta, da shugabanninta, Da sojojinta su sha su yi maye. Za su dinga yin barcin da ba za su farka ba,” In ji Sarkin, mai suna Ubangiji Mai Runduna. 58 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce, Za a baje garun nan na Babila mai fāɗi Za a kuma ƙone dogayen ƙyamarenta da wuta. Mutane sun wahalar da kansu a banza. Sauran al'umma sun yi wahala kawai domin wutar lalata.” 59 Jawabin da annabi Irmiya ya ba Seraiya, ɗan Neriya, wato jikan Ma'aseya, lokacin da ya tafi tare da Zadakiya, Sarkin Yahuza, zuwa Babila a shekara ta huɗu ta mulkinsa. Seraiya shi ne shugaba mai lura da gidajen saukar baƙi. 60 Irmiya ya rubuta a littafi dukan masifun da za su auko wa Babila, wato dukan wannan magana da aka rubuta a kan Babila. 61 Irmiya kuwa ya ce wa Seraiya, “Lokacin da ka kai Babila, sai ka karanta dukan maganan nan. 62 Ka kuma ce, ‘Ya Ubangiji, kai ne ka yi magana a kan wannan wuri, cewa za ka lalatar da shi, har ba abin da zai zauna a ciki, mutum ko dabba. Wurin zai zama kufai har abada.’ 63 Sa'ad da ka gama karanta wannan littafi, sai ka ɗaura wa littafin dutse, sa'an nan ka jefar da shi tsakiyar Kogin Yufiretis. 64 Sa'an nan ka ce, ‘Haka Babila za ta nutse, ba za ta ƙara tashi ba saboda masifar da Ubangiji zai kawo mata.’ ” Wannan shi ne ƙarshen maganar Irmiya.

Irmiya 52

Mulkin Zadakiya

1 Zadakiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa'ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal, 'yar Irmiya, wanda ke zauna a Libna. 2 Sarki Zadakiya ya aikata abin da ke mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehoyakim ya yi. 3 Al'amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra'ila da Yahuza, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala.

Faɗuwar Urushalima

Zadakiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babila. 4 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zadakiya, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina garu kewaye da ita. 5 An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zadakiya. 6 A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci. 7 Sai aka huda garun birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da ke tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa'ad da Kaldiyawa ke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba. 8 Amma sojojin Kaldiyawa suka runtumi sarki Zadakiya, suka ci masa a filayen Yariko. Dukan sojoji suka yashe shi. 9 Da aka kama Zadakiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babila a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babila ya yanke masa shari'a. 10 Ya kuwa kashe 'ya'yan Zadakiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuza a Ribla. 11 Sa'an nan ya ƙwaƙule idanun Zadakiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babila inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.

Yahuza ya Je Zaman Talala

12 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babila, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima. 13 Sai ya ƙone Haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan manyan gidajen da ke Urushalima. 14 Sojojin Kaldiyawa da ke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan garun Urushalima. 15 Sa'an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babila, da sauran masu sana'a, ya kai su bautar talala a Babila. 16 Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki. 17 Kaldiyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda ke a Haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babila. 18 Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar Haikali. 19 Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da ke na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe. 20 Tagullar da sarki Sulemanu ya yi waɗannan abubuwa da ita, wato ginshiƙai biyu, da kwatarniyar tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda ke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna. 21 Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma taƙi huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki. 22 A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman. 23 Akwai siffofin rumman tasa'in da shida da ake gani a gyaffan. Dukan siffofin rumman da ke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne. 24 Shugaban matsara kuma ya ɗauki Seraiya babban firist, da Zafaniya wanda ke biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar Haikali, ya tafi da su. 25 Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai 'yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su. 26 Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babila a Ribla, 27 Sarkin Babila kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuza bautar talala. 28 Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa dubu uku da ashirin da uku (3,023 ). 29 A shekara ta goma sha takwas ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima ɗari takwas da talatin da biyu. 30 A shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa kuma, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa ɗari bakwai da arba'in da biyar. Jimillarsu duka kuwa dubu huɗu da ɗari shida ne (4,600 ).

An saki Yekoniya an ba shi Girma a Babila

31 A shekarar da Ewil-merodak ya zama Sarkin Babila, sai ya nuna wa Yekoniya Sarkin Yahuza alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yekoniya bauta. 32 Ewil-merodak ya nuna wa Yekoniya alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babila tare da shi. 33 Yekoniya ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa. 34 Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarki, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.

Makoki 1

Baƙin Cikin Sihiyona

1 Urushalima wadda ke cike da mutane a dā, Yanzu tana zaman kaɗaici! Tana zama kamar mace wadda mijinta ya rasu, Ita wadda dā ta zama babba a cikin sauran al'ummai! Ita wadda take a dā sarauniya a cikin larduna, Ta zama mai biyan gandu! 2 Da dare tana kuka mai zafi, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf a kumatunta. Dukan masoyanta ba wanda ke ta'azantar da ita. Dukan abokanta sun ci amanarta, sun zama maƙiyanta. 3 Yahuza ta tafi bauta tana shan azaba, Da bauta mai tsanani. Tana zaune a tsakiyar sauran al'umma, Amma ba ta sami hutawa ba, Gama masu runtumarta sun ci mata, ba hanyar tsira. 4 Hanyoyin Sihiyona suna baƙin ciki Domin ba mai halartar ƙayyadaddun idodi. Dukan ƙofofinta sun zama kufai, Firistocinta suna nishi, Budurwanta kuma suna wahala, Ita kanta ma tana shan wuya ƙwarai. 5 Maƙiyanta sun zama shugabanninta, Abokan gābanta kuma sun zama iyayengijinta. Gama Ubangiji ne ya sa ta sha wahala Saboda yawan zunubanta. 'Ya'yanta sun tafi bauta wurin maƙiyanta. 6 Dukan darajar Sihiyona ta rabu da ita, Shugabanninta sun zama kamar bareyin Da ba su sami wurin kiwo ba, Suna gudu ba ƙarfi a gaban wanda ke korarsu. 7 A kwanakin wahalarta na rashin wurin zama, Urushalima ta tuna da dukan abubuwanta masu daraja a dā. A lokacin da mutanenta suka fāɗa a hannun maƙiyi, Ba wanda ya taimake ta, Maƙiyanta sun gan ta, Sun yi mata ba'a saboda faɗuwarta. 8 Urushalima ta yi zunubi ƙwarai da gaske, Saboda haka ta ƙazantu, Dukan waɗanda suka girmama ta sun raina ta Domin sun ga tsiraicinta, Ita kanta ma tana nishi, ta ba da baya. 9 Ƙazantarta tana cikin tufafinta, Ba ta tuna da ƙarshenta ba, Domin haka faɗuwarta abar tsoro ce, Ba ta da mai yi mata ta'aziyya. “Ya Ubangiji, ka dubi wahalata, Gama maƙiyi ya ɗaukaka kansa!” 10 Maƙiyi ya miƙa hannunsa A kan dukan kayanta masu daraja, Gama ta ga al'ummai sun shiga Haikali, Su waɗanda ka hana su shiga cikin jama'arka. 11 Dukan jama'arta suna nishi don neman abinci, Sun ba da kayansu masu daraja saboda abinci Don su rayu. “Ya Ubangiji ka duba, ka gani, Gama an raina ni.” 12 “Dukanku masu wucewa, ba wani abu ba ne a gare ku? Ku duba, ku gani, ko akwai baƙin ciki irin nawa, Wanda Ubangiji ya ɗora mini, A ranar fushinsa mai zafi. 13 “Daga sama ya aukar da wuta a cikin ƙasusuwana. Ya kuma kafa wa ƙafafuna ashibta, Ya komar da ni baya, Ya bar ni a yashe, sumamme dukan yini. 14 “Ubangiji ya tattara laifofina Ya yi karkiya da su, Ya ɗaura su a wuyana, Ya sa ƙarfina ya kāsa. Ya kuma bashe ni a hannun Waɗanda ban iya kome da su ba. 15 “Ubangiji ya yi watsi da majiya ƙarfina, Ya kirawo taron jama'a a kaina Don su murƙushe samarina. Ya kuma tattake Urushalima, zaɓaɓɓiyarsa, Kamar 'ya'yan inabi a wurin matsewa. 16 “Ina kuka saboda waɗannan abubuwa, Hawaye suna zuba sharaf-sharaf daga idanuna. Gama mai ta'azantar da ni, Wanda zai sa in murmure yana nesa da ni. 'Ya'yana sun lalace, Gama maƙiyi ya yi nasara!” 17 Sihiyona tana miƙa hannuwanta, Amma ba wanda zai ta'azantar da ita. Gama Ubangiji ya umarci maƙwabtan Yakubu su zama maƙiyansa. Urushalima kuma ta zama ƙazantacciya a tsakaninsu. 18 “Abin da Ubangiji ya yi daidai ne, Gama ni na ƙi bin maganarsa, Ku ji, ya ku jama'a duka, Ku dubi wahalata, 'Yan matana da samarina, An kai su bauta! 19 “Na kira masoyana, amma suka yaudare ni, Firistocina da dattawana a cikin birni sun halaka Saboda neman abincin da za su ci su rayu. 20 “Ka duba, ya Ubangiji, ina shan wahala, Raina yana cikin damuwa, Zuciyata tana makyarkyata saboda tayarwata. A titi takobi yana karkashewa, A gida kuma ga mutuwa. 21 “Sun ji yadda nake nishi, Ba mai ta'azantar da ni. Dukan maƙiyana sun ji labarin wahalar da nake ciki, Suna kuwa murna da ka yi haka. Ka kawo ranan nan da ka ambata, Domin su ma su zama kamar yadda nake. 22 “Ka sa mugayen ayyukansu su bayyana a gabanka, Sa'an nan ka hukunta su kamar yadda ka hukunta ni saboda dukan laifofina. Gama nishe-nishena sun yi yawa. Zuciyata kuma ta karai.”

Makoki 2

Hukuncin Ubangiji a kan Urushalima

1 Ubangiji ya duhunta Sihiyona saboda fushinsa! Daga Sama kuma ya jefar da darajar Isra'ila a ƙasa. Bai kuma tuna da matashin sawayensa ba A ranar fushinsa. 2 Dukan wuraren zaman Yakubu, Ubangiji ya hallakar ba tausayi, Da fushinsa kuma ya rurrushe kagaran Sihiyona. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulkin. 3 Da zafin fushinsa, ya karya ƙarfin Isra'ila, Ya kuma bar yi musu taimako A lokacin da abokan gāba suka zo. Kamar harshen wuta, ya ƙone dukan abin da ke na Yakubu. 4 Ya ja bakansa kamar abokan gāba, Ya kuma nuna ikonsa kamar maƙiyi. Ya hallaka dukan abin da ke da bansha'awa. A alfarwar Sihiyona, ya zubo da hasalarsa kamar wuta. 5 Ubangiji ya zama kamar maƙiyi, ya hallaka Isra'ila. Ya hallaka fādodinta duka, Ya mai da kagaranta kango. Ya aukar wa Yahuza da makoki da baƙin ciki mai yawa. 6 Ya rushe Haikalinsa kamar bukka cikin gona, Ya mai da wurin yin ƙayyadaddun idodinsa kufai. Ubangiji ya sa ƙayyadadden idi da kiyaye Asabar Su ƙare a Sihiyona, Da zafin fushinsa kuma ya wofinta sarki da firist. 7 Ubangiji ya wulakanta bagadensa, Ya kuma wofinta tsattsarkan Haikalinsa. Ya ba da garun fādodinta a hannun abokan gāba, Suka yi sowa a Haikalin Ubangiji Kamar a ranar idi. 8 Ubangiji ya yi niyya Ya mai da garun Sihiyona kufai, Ya auna ta da igiyar awo, Bai janye dantsensa daga hallaka ta ba. Ya sa kagara da garu su zozaye, su lalace tare. 9 Ƙofofinta sun nutse ƙasa, Ya lalatar, ya kakkarya ƙyamarenta, An kai sarkinta da mahukuntanta cikin al'ummai, Inda ba a bin dokokin annabawanta, Ba su kuma samun wahayi daga wurin Ubangiji. 10 Dattawan Sihiyona suna zaune a ƙasa shiru, Sun yi hurwa, suna saye da tufafin makoki. 'Yan matan Urushalima kuma sun sunkuyar da kansu ƙasa. 11 Idanuna sun dushe saboda kuka, Raina yana cikin damuwa. Zuciyata ta karai saboda halakar mutanena, Gama 'yan yara da masu shan mama Sun suma a titunan birnin. 12 Suna yi wa uwayensu kuka, suna cewa, “Ina abinci da ruwan inabi?” Suna suma kamar mutanen da aka yi wa rauni A titunan birnin, Suna mutuwa a ƙirjin uwayensu. 13 Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ya Urushalima? Da me zan misalta wahalarki Don in ta'azantar da ke, ya Sihiyona? Masifar da ta same ki tana da fāɗi kamar teku, Wa zai iya warkar da ke? 14 Annabawanki sun gano miki wahayan ƙarya, Ba su tone asirin muguntarki, Har da za a komo da ke daga bauta ba. Amma suka yi miki annabcin ƙarya na banza. 15 Dukan masu wucewa suna yin miki tafin raini. Suna yi wa Urushalima tsāki, Suna kaɗa mata kai, suna cewa, “Ai, Urushalima ke nan, Birnin nan da ake cewa mai cikakken jamali, Wanda ya ƙayatar da dukan duniya?” 16 Maƙiyanki duka sun wage bakinsu gāba da ke, Suna tsāki, suna cizon bakinsu, Suna ihu, suna cewa, “Mun hallaka ta! Ai, wannan ita ce ranar da muke fata! Ga shi kuwa, ta zo, mun gan ta!” 17 Ubangiji ya aikata abin da ya yi niyya, Ya cika maganarsa wadda ya faɗa tun dā, Ya hallakar, ba tausayi, Ya sa maƙiyi ya yi murna a kanki, Ya ƙarfafa ƙarfin maƙiyanki. 18 Ya Sihiyona, ki yi kuka ga Ubangiji, Bari hawayenki su gudana dare da rana kamar ruwan rafi, Kada ki huta, kada kuma idanunki su huta! 19 Ki tashi, ki ya ta kuka dukan dare, Ki bulbule abin da ke cikin zuciyarki Kamar ruwa gaban Ubangiji. Ki miƙa hannuwanki zuwa gare shi, Saboda rayukan 'ya'yanki, Waɗanda ke suma da yunwa A magamin kowane titi! 20 Ya Ubangiji, ka duba, ka gani! Wanene ka yi wa haka? Mata za su cinye 'ya'yansu da suke reno? Ko kuwa za a kashe firist da annabi A cikin Haikalin Ubangiji? 21 Yara da tsofaffi suna kwance cikin ƙurar tituna, An kashe 'ya'yana, 'yan mata da samari, da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka, ba tausayi. 22 Ka gayyato mini tsoro Kamar yadda akan gayyato taro a ranar idi. A ranar fushin Ubangiji Ba wanda ya tsere, ko wanda ya tsira. 'Ya'yan da na yi renonsu, na goye su, Maƙiyina ya hallaka su.

Makoki 3

Sa Zuciya ga Samun Taimako daga wurin Ubangiji

1 Ni ne mutumin da ya sha wuyar horon Ubangiji. 2 Ya kore ni zuwa cikin duhu baƙi ƙirin. 3 Hakika ikonsa ya yi ta gāba da ni dukan yini. 4 Ya sa naman jikina da fatar jikina su lalace, Ya kuma kakkarya ƙasusuwana. 5 Ya kewaye ni da yaƙi, Ya rufe ni da baƙin ciki mai tsanani da wahala. 6 Ya zaunar da ni cikin duhu, Kamar waɗanda suka daɗe da mutuwa. 7 Ya kewaye ni da garu don kada in tsere, Ya ɗaure ni da sarƙa mai nauyi. 8 Ko da ya ke ina kira, ina kukan neman taimako, Ya yi watsi da addu'ata. 9 Ya toshe hanyata da sassaƙaƙƙun duwatsu, Ya karkatar da hanyoyina. 10 Ya zamar mini kamar beyar wanda ke fako, Kamar zaki a ɓoye cikin ruƙuƙi. 11 Ya bauɗar da ni daga hanyata, ya yayyage ni, Ya maishe ni, ba ni a kowa. 12 Ya ja bakansa, ya sa in zama abin baratarsa. 13 Ya harbe zuciyata da kiban kwarinsa. 14 Na zama abin dariya ga dukan mutane, Dukan yini suna yi mini waƙar zambo. 15 Ya shayar da ni da ruwan ɗaci, Ya ƙosar da ni da abinci mai ɗaci. 16 Ya sa in tauna tsakuwa da haƙorana, Ya zaunar da ni cikin ƙura. 17 An raba ni da salama, Na manta da abar da ake ce da ita wadata. 18 Sai na ce, “Darajata ta ƙare, Ba ni kuma da sa zuciya wurin Ubangiji.” 19 Ka tuna da azabata, da galabaitata, Da ɗacin raina, da kumallon da nake fama da shi. 20 Kullum raina yana tunanin azabaina, Raina kuwa ya karai. 21 Da na tuna da wannan, sai na sa zuciya ga gaba. 22 Ƙaunar Ubangiji ba ta ƙarewa, Haka kuma jiyejiyanƙansa ba su ƙarewa. 23 Su sababbi ne kowace safiya, Amincinka kuma mai girma ne. 24 Na ce, “Ubangiji shi ne nawa, Saboda haka zan sa zuciya gare shi.” 25 Ubangiji mai alheri ne ga waɗanda suke sauraronsa, Da wanda ke nemansa kuma. 26 Yana da kyau a jira ceton Ubangiji da natsuwa, 27 Yana da kyau mutum ya hori kansa tun yana yaro. 28 Bari ya zauna a kaɗaice, ya yi shiru Sa'ad da yake da damuwa. 29 Bari ya kwanta cikin ƙura, Watakila akwai sauran sa zuciya. 30 Bari ya yarda a mari kumatunsa, Ya haƙura da cin mutunci. 31 Gama Ubangiji ba zai yashe mu har abada ba. 32 Ko da ya sa ɓacin rai, Zai ji tausayi kuma, Saboda tabbatacciyar ƙaunarsa mai yawa. 33 Gama ba da gangan ba ne yakan wahalar da 'yan adam Ko ya sa su baƙin ciki. 34 Ubangiji bai yarda a danne 'Yan kurkuku na duniya ba. 35 Bai kuma yarda a hana wa mutum hakkinsa A gaban Maɗaukaki ba, 36 Ko kuwa a karkatar wa mutum da shari'arsa. 37 Wa ya umarta, abin kuwa ya faru, In ba Ubangiji ne ya umarta ba? 38 Ba daga bakin Maɗaukaki Alheri da mugunta suke fitowa ne ba? 39 Don me ɗan adam Zai yi gunaguni a kan hukuncin zunubansa? 40 Bari mu jarraba, mu bincika hanyoyinmu, Sa'an nan mu komo wurin Ubangiji. 41 Bari mu roƙi Allah na Sama, Muna miƙa hannuwanmu sama, mu ce, 42 “Mun yi zunubi, mun tayar, Kai kuwa ba ka gafarta ba. 43 “Ka yafa fushi, ka runtume mu, Kana karkashe mu ba tausayi. 44 Ka kuma rufe kanka da gajimare Don kada addu'a ta kai wurinka. 45 Ka maishe mu shara da juji a cikin mutane. 46 “Dukan maƙiyanmu suna yi mana ba'a. 47 Tsoro, da wushefe, Da lalatarwa, da hallakarwa sun auka mana. 48 Hawaye suna gangarawa daga idanuna kamar ruwan koguna, Saboda an hallaka mutanena. 49 “Hawayena suna ta gangarawa, ba tsayawa, ba hutawa, 50 Har lokacin da Ubangiji daga Sama ya duba, ya gani. 51 Ganin azabar 'yan matan birnina Ya sa ni baƙin ciki. 52 “Waɗanda ke maƙiyana ba dalili Sun farauce ni kamar tsuntsu. 53 Sun jefa ni da rai a cikin rami, Suka rufe ni da duwatsu. 54 Ruwa ya sha kaina, Sai na ce, ‘Na halaka.’ 55 “Ya Ubangiji, na yi kira ga sunanka Daga cikin rami mai zurfi. 56 Ka kuwa ji muryata. Kada ka rufe kunnenka ga jin kukana na neman taimako. 57 Sa'ad da na yi kira gare ka, ka zo kusa. Sa'an nan ka ce mini kada in ji tsoro. 58 “Ka karɓi da'awata, ya Ubangiji, Ka kuwa fanshi raina. 59 Ka ga laifin da aka yi mini, Sai ka shara'anta da'awata, ya Ubangiji. 60 Ka ga dukan irin sakayyarsu, Da dukan dabarun da suke yi mini. 61 “Ya Ubangiji, ka ji zargi Da dukan dabarun da suke yi mini. 62 Leɓunan maƙiyana da tunaninsu Suna gāba da ni dukan yini. 63 Suna raira mini waƙar zambo sa'ad da suke zaune, Da lokacin da suka tashi. 64 “Ya Ubangiji, za ka sāka musu bisa ga ayyukansu, 65 Za ka ba su tattaurar zuciya, La'anarka kuwa za ta zauna a kansu! 66 Da fushi za ka runtume su Har ka hallaka su a duniya, ya Ubangiji!”

Makoki 4

Bayan Faɗuwar Urushalima

1 Ƙaƙa zinariya ta zama duhu! Ƙaƙa zinariya tsantsa ta sāke! Tsarkakakkun duwatsu kuma suna zube A kowane magamin titi. 2 Darajar samarin Sihiyona Ta kai tamanin zinariya tsantsa. To, ƙaƙa ake lissafinsu kamar tukwanen ƙasa, Aikin hannun maginin tukwane? 3 Ko diloli ma sukan ba 'ya'yansu mama, Su shayar da su. Amma mutanena sun zama kamar jiminai cikin jeji. 4 Harshen jinjiri ya liƙe a dasashinsa saboda ƙishi, 'Yan yara suna roƙon abinci, Amma ba wanda ya ba su. 5 Su waɗanda suka ci abubuwa masu daɗi, Sun halaka a titi. Su waɗanda aka goye su da alharini, Yanzu suna kwance a kan tsibin toka. 6 Gama zunubin mutanena Ya fi zunubin Saduma, Wadda Ubangiji ya hallakar da ita nan da nan. 7 Keɓaɓɓunta sun fi dusar ƙanƙara tsabta, Sun kuma fi madara fari. Jikunansu sun fi murjani ja. Kyan tsarinsu yana kama da shuɗin yakutu. 8 Yanzu fuskokinsu sun fi kukunniya baƙi, Ba a iya fisshe su a titi ba, Fatar jikinsu ta liƙe wa ƙasusuwansu, Sun bushe kamar itace. 9 Gara ma waɗanda takobi ya kashe Da waɗanda yunwa ta kashe, Gama sun rame sarai saboda rashin abinci. 10 Mata masu juyayi, da hannuwansu Suka ɗauki 'ya'yansu, suka dafa, Suka zama musu abinci a lokacin halakar mutanena. 11 Ubangiji ya saki fushinsa, Ya zuba fushinsa mai zafi. Ya kunna wa Sihiyona wuta Wadda ta cinye harsashin gininta. 12 Sarakunan duniya da mazaunanta ba su gaskata, Cewa abokan gaba ko maƙiya Za su iya shiga ƙofofin Urushalima ba. 13 Dalili kuwa saboda zunuban annabawa ne, Da muguntar firistoci, Waɗanda suka kashe adalai. 14 Sun yi ta kai da kawowa a titi kamar makafi, Sun ƙazantu da jini Har ba wanda zai taɓa rigunansu. 15 Mutane suka yi ta yi musu ihu, Suna cewa, “Ku tafi, ku ƙazamai, Ku tafi, ku tafi, kada ku taɓa mu!” Don haka suka zama korarru, masu kai da kawowa. A cikin sauran al'umma mutane suna cewa, “Ba za su ƙara zama tare da mu ba.” 16 Ubangiji kansa ya watsar da su, Ba zai ƙara kulawa da su ba. Ba su darajanta firistoci ba, Ba su kuma kula da dattawa ba. 17 Idanunmu sun gaji Da zuba ido a banza don samun taimako, Mun zuba ido Ga al'ummar da ba za ta iya cetonmu ba. 18 Ana bin sawayenmu, Don haka ba mu iya tafiya a titunanmu ba. Ƙarshenmu ya yi kusa, Kwanakinmu sun ƙare, Gama ƙarshenmu ya zo. 19 Masu runtumarmu sun fi gaggafar da ke tashi sama sauri. Sun fafare mu a kan duwatsu, Suna fakonmu a cikin jeji. 20 Shi wanda muke dogara gare shi, Wato zaɓaɓɓe na Ubangiji, ya auka cikin raminsu, Shi wanda muka ce, “A ƙarƙashin inuwarsa ne za mu zauna a cikin sauran al'umma.” 21 Ki yi farin ciki, ki yi murna, ke Edom, Wadda kike zaune cikin ƙasar Uz. Amma fa za a ba ki ƙoƙo ki sha, Ki bugu har ki yi tsiraici. 22 Ya Sihiyona, hukunci a kan muguntarki ya ƙare, Ba zai ƙara barinki a ƙasar bauta ba. Amma zai hukunta ki saboda muguntarki, ya Edom, Zai tone zunubanki.

Makoki 5

Addu'ar Neman Jinƙai

1 Ya Ubangiji, ka tuna da abin da ya same mu. Ka duba, ka ga yadda muka zama abin kunya! 2 An ba baƙi gādonmu, Gidajenmu kuwa an ba bare. 3 Mun zama marayu, marasa ubanni, Uwayenmu sun zama kamar matan da mazajensu sun mutu. 4 Dole ne mu biya ruwan da za mu sha, Dole ne kuma mu sayi itace. 5 Masu binmu a ƙyeyarmu suke, suna korarmu da zafi, Mun gaji, ba a yarda mu huta. 6 Mun miƙa hannu ga Masar da Assuriya Don mu sami abinci. 7 Ubanninmu sun yi zunubi, ga shi kuwa, ba su, Mu kuwa muna ɗaukar alhakin muguntarsu. 8 Bayi suke mulkinmu, Ba kuwa wanda zai cece mu daga hannunsu. 9 Sai mun yi kasai da ranmu kafin mu sami abinci, Domin akwai masu kisa a jeji. 10 Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, Saboda tsananin yunwa. 11 An yi wa mata faɗe a cikin Sihiyona, Haka kuma aka yi wa budurwai a garuruwan Yahuza. 12 An rataye shugabanni da hannuwansu, Ba a kuma girmama dattawa ba. 13 An tilasta wa samari su yi niƙa, Yara kuma suna tagataga da kayan itace. 14 Tsofaffi sun daina zama a dandalin ƙofar birni, Samari kuma sun daina bushe-bushe. 15 Farin cikinmu ya ƙare, Raye-rayenmu sun zama makoki. 16 Rawani ya fāɗi daga kanmu, Tamu tu ƙare, gama mun yi zunubi! 17 Saboda wannan zuciyarmu ta ɓaci, Idanunmu kuma suka duhunta. 18 Gama Dutsen Sihiyona ya zama kufai, Wurin yawon diloli. 19 Amma ya Ubangiji, kai ne kake mulki har abada, Kursiyinka ya dawwama har dukan zamanai. 20 Don me ka manta da mu har abada? Don me ka yashe mu da daɗewa haka? 21 Ya Ubangiji, ka komo da mu zuwa gare ka! Mu kuwa za mu koma. Ka sabunta kwanakinmu su zama kamar na dā. 22 Ko ka ƙi mu ne, sam sam? Ko kuwa ka husata da mu?

Ezekiyel 1

Ezekiyel ya Ga Wahayi na Ɗaukakar Ubangiji

1 A ranar biyar ga watan huɗu, a shekara ta talatin, ina cikin waɗanda aka kai su bautar talala, muna kusa da kobin Kebar, sai aka buɗe mini sammai, na kuwa ga wahayi na ɗaukakar Allah. 2 A kan rana ta biyar ga watan, a shekara ta biyar da aka kai sarki Yekoniya bautar talala, 3 Ubangiji ya yi magana da Ezekiyel, firist, ɗan Buzi, a ƙasar Kaldiyawa, kusa da kogin Kebar. Ikon Ubangiji yana bisa kansa. 4 Da na duba, sai ga hadiri mai iska ya taso daga wajen arewa, da wani babban girgije da haske kewaye da shi, da wuta tana ta ci falfal. A tsakiyar wutar wani abu yana walƙiya kamar tagulla. 5 Daga tsakiya wutar, sai ga kamannin waɗansu talikai su huɗu. Ga irin kamanninsu, suna kama da mutane. 6 Amma kowannensu yana da fuskoki huɗu, da fikafikai huɗu. 7 Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne, tafin sawayensu yana kama da na maraƙi, suna walƙiya kamar gogaggiyar tagulla. 8 Suna kuma da hannuwa kamar na mutane a ƙarƙarshin fikafikansu huɗu. Ga yadda fuskoki da fikafikan talikai huɗu ɗin suke. 9 Fikafikansu suna taɓa juna, kowannensu ya miƙe gaba, ba su juyawa sa'ad da suke tafiya. 10 Kamannin fuskokinsu, su huɗu ɗin, kowannensu yana da fuska irin ta mutum a gaba, da fuska irin ta zaki a dama, da fuska irin ta bijimi a hagu, da fuska irin ta gaggafa a baya. 11 Suka kuma buɗe fikafikansu sama. Kowane taliki yana taɓa fiffiken ɗan'uwansa da fikafikansa biyu, da kuma fikafikansa biyu yake rufe jikinsa. 12 Kowannensu kuwa ya miƙe gaba sosai, zuwa inda ruhu ya bishe shi. Sun tafi ba waiwaye. 13 A tsakiyar talikan akwai wani abu mai kama da garwashin wuta, kamar jiniyoyi kima suna kai da kawowa a tsakanin talikan, wutar kuwa tana haskakawa. Daga cikin wutar kuma, sai ga walƙiya tana fitowa. 14 Talikan kuma suka yi ta giftawa suna kai da kawowa kamar walƙiya. 15 Da na dubi talikan, sai na ga ƙafafu huɗu kamar na keke a ƙasa kusa da talikan. Ɗaya domin kowane taliki. 16 Ga kamannin ƙafafun da yadda aka yi su. Suna ƙyalƙyali kamar duwatsu masu daraja. Dukansu huɗu fasalinsu ɗaya ne. An yi su kamar wata ƙafa tana cikin wata ƙafa. 17 Sa'ad da suke tafiya, suna tafiya a kowane waje, ba sai sun juya ba. 18 Akwai waɗansu ƙarafa kamar zobe, da idanu kuma tantsai kewaye da ƙafafun. 19 Duk sa'ad da talikan suka motsa, sai kuma ƙafafun su motsa tare da su. Idan kuma talikan suka ɗaga sama, sai ƙafafun su ɗaga tare da su. 20 Duk inda ruhu ya nufa, sai talikan su bi, sai kuma ƙafafun su tafi tare da su, gama ruhun talikan yana cikin ƙafafun. 21 Idan talikan sun motsa, sai ƙafafun kuma su motsa. Idan sun tsaya cik, sai su ma su tsaya. Idan kuma talikan sun ɗaga sama, sai ƙafafun su ɗaga sama tare da su, gama ruhun talikan yana cikin ƙafafun. 22 Sama da talikan akwai kamannin al'arshi mai walƙiya kamar madubi. 23 A ƙarƙashin al'arshin fikafikansu sun miƙe kyam daura da juna. Kowane taliki yana da fikafikai biyu da su yake rufe jikinsa. 24 Sa'ad da suke tafiya, sai na ji motsin fikafikansu kamar amon ruwa, kamar kuma muryar tsawar Maɗaukaki, kamar hayaniyar runduna. Idan sun tsaya cik, sai su saukar da fikafikansu. 25 Sai aka ji murya ta fito daga saman al'arshi ɗin. 26 A saman al'arshin akwai wani abu mai kamar kursiyin sarauta da aka yi da yakutu. Akwai wani kamar mutum yana zaune a kan abin nan mai kama da kursiyin sarauta. 27 Daga kwankwasonsa zuwa sama yana walƙiya kamar tagullar da aka kewaye ta da wuta. Daga kwankwasonsa zuwa ƙasa yana haskakawa kamar wuta. 28 Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, hakanan kamannin hasken da ke kewaye da shi yake. Wannan shi ne kamannin kwatancin ɗaukakar Ubangiji. Sa'ad da na gani, sai na faɗi rubda ciki, na ji muryar wani tana magana.

Ezekiyel 2

Kiran Ezekiyel

1 Sai ya ce mini, “Dan mutum, ka tashi tsaye, zan yi magana da kai.” 2 Da ya yi magana da ni, sai Ruhu ya sauko a kaina, ya ta da ni tsaye, sa'an nan na ji yana magana da ni. 3 Ya ce mini, “Ɗan mutum na aike ka zuwa wurin jama'ar Isra'ila, al'umma mai tayarwa, waɗanda suka tayar mini. Su da ubanninsu suna yi ta yi mini laifi har yau. 4 Su mutane ne marasa kunya, masu taurinkai. Ga shi kuwa, na aike ka gare su, ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya faɗa.’ 5 Ko su ji, ko kada su ji, gama su masu tayarwa ne, amma za su sani akwai annabi a cikinsu. 6 “Kai ɗan mutum, kada ka ji tsoronsu, kada kuma ka ji tsoron maganganunsu, ko da ya ke ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya sun kewaye ka, kana kuma zaune tare da kunamai. Kada ka ji tsoron maganganunsu ko ka karai saboda irin kallon da za su yi maka, gama su 'yan tawaye ne. 7 Za ka faɗa musu maganata, ko su ji, ko kada su ji, gama su 'yan tawaye ne. 8 “Amma kai, ya ɗan mutum, ka ji abin da zan faɗa maka, kada ka zama mai tayarwa kamar 'yan tawayen nan. Sai ka buɗe bakinka, ka ci abin da zan ba ka.” 9 Da na duba, sai ga hannu yana miƙo mini littafi. 10 Ya buɗe littafin a gabana, akwai rubutu ciki da baya. Ba abin da aka rubuta sai maganganun baƙin ciki, da makoki, da kaito.

Ezekiyel 3

1 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum ka ci abin da aka ba ka. Ka ci wannan littafi, sa'an nan ka tafi ka yi wa mutanen Isra'ila magana.” 2 Sai na buɗe bakina, sa'an nan ya ba ni littafin in ci. 3 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci littafin nan da na ba ka, ka cika tumbinka da shi.” Sai na ci littafin, na ji shi a bakina da zaƙi kamar zuma. 4 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum ka tafi wurin mutanen Isra'ila ka faɗa musu maganata. 5 Gama ba a aike ka a wurin mutane waɗanda ke da baƙon harshe wanda ba ka sani ba, amma zuwa mutanen Isra'ila, 6 ba wurin waɗansu mutane dabam waɗanda ke da baƙon harshe mai wuya ba, wato harshen da ba ka sani ba. Da na aike ka wurin irin mutanen nan da za su ji. 7 Amma mutanen Isra'ila ba za su ji ka ba, ba su kuwa da nufi su ji ni, gama suna da taurinkai da taurin zuciya. 8 Ga shi, na sa fuskarka da goshinka su zama da tauri kamar nasu. 9 Kamar yadda lu'ulu'u ya fi ƙanƙarar dutse ƙarfi, hakanan na sa goshinka ya zama. Kada ka ji tsoronsu, ko kuwa ka karai saboda irin kallon da za su yi maka, gama su 'yan tawaye ne.” 10 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, sai ka ji, ka karɓi dukan maganata da zan faɗa maka. 11 Sa'an nan ka tafi wurin mutanenka waɗanda suke cikin bautar talala, ka faɗa musu, ko su ji, ko kada su ji.” 12 Sa'an nan Ruhu ya ɗaga ni, sai na ji murya a bayana, kamar babban motsi, tana cewa, “Yabo ga ɗaukakar Ubangiji a kursiyinsa.” 13 Na kuma ji amon fikafikan talikan ne sa'ad da suka taɓa junansu, da kuma amon ƙafafun da ke kusa da talikan, da amon babban motsi. 14 Sai Ruhu ya ɗaga ni, ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da baƙin ciki, ina jin zafi a ruhuna. Ikon Ubangiji yana tare da ni da ƙarfi. 15 Na zo wurin 'yan bautar talala a Telabib, waɗanda ke bakin kogin Kebar. Na zauna tare da su kwana bakwai, ina ta mamaki.

Ezekiyel ya Zama Mai Tsaron Isra'ila

16 A ƙarshen kwana bakwai ɗin, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 17 “Ɗan mutum, na maishe ka mai tsaron gidan Isra'ila. Sa'ad da ka ji magana daga bakina, sai ka faɗakar da su a madadina. 18 Idan na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ kai kuwa ba ka faɗakar da shi a kan mugayen ayyukansa don ka ceci ransa ba, wannan mugun mutum zai mutu cikin zunubinsa, amma zan nemi hakkin jininsa a hannunka. 19 Amma idan ka faɗakar da mugu, ya kuwa ƙi barin muguntarsa, zai mutu cikin zunubinsa, kai kam ka kuɓuta. 20 “Idan kuma adali ya bar adalci sa'an nan ya aikata zunubi, ni kuwa na sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Zai mutu saboda zunubinsa domin ba ka faɗakar da shi ba. Ba za a tuna da ayyukansa na adalci waɗanda ya yi ba, amma zan nemi hakkin jininsa a hannunka. 21 Amma idan ka faɗakar da adali, kada ya aikata zunubi, shi kuwa bai aikata zunubi ba, hakika zai rayu domin ya ji faɗakar, kai kuma ka kuɓuta.”

Annabi ya Zama Bebe

22 Ikon Ubangiji yana tare da ni, Ubangiji kuwa ya ce mini, “Tashi, ka tafi ka tsaya a fili, a can zan yi magana da kai.” 23 Sai na tashi na tafi na tsaya a fili, sai ga ɗaukakar Ubangiji a wurin, a tsaye kamar ɗaukakar da na gani a bakin kogin Kebar. Sai na fāɗi rubda ciki. 24 Ruhu kuwa ya sauko a kaina, ya ta da ni tsaye. Sai ya yi magana da ni, ya ce, “Ka tafi, ka kulle kanka cikin gida. 25 Ya ɗan mutum, za a ɗaure ka da igiyoyi don kada ka tafi cikin jama'a. 26 Ni kuwa zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka zama bebe, ka kasa tsauta musu, gama su 'yan tawaye ne. 27 Amma sa'ad da na yi magana da kai, zan buɗe bakinka, kai kuwa za ka yi ji musu magana, ka ce, ‘Ubangiji ya ce, wanda zai ji, to, ya ji, wanda kuma zai ƙi ji, ya ƙi ji,’ gama su 'yan tawaye ne.”

Ezekiyel 4

Ezekiyel ya Misalta yadda za a Kewaye Urushalima da Yaƙi

1 “Ya kai ɗan mutum, sai ka ɗauki tubali, ka ajiye a gabanka, sa'an nan kaz 2 Sa'an nan ka gina mata kagara, da garu da ɗan tudu. Ka kuma kafa mata sansani ka kewaye ta da dundurusai. 3 Ka ɗauki kwano, ka shirya shi kamar garun ƙarfe tsakaninka da birnin, sa'an nan ka zuba ido. Birnin zai zama kamar an kewaye shi da yaƙi, kai kuwa ka kewaye shi da yaƙi. Wannan kuma zai zama alama ga Isra'ilawa. 4 “Sai kuma ka kwanta a hagunka, ni kuwa zan ɗora maka muguntar Isra'ilawa. Za ka ɗauki muguntarsu bisa ga yawan kwanakin da za ka kwanta a hagunka. 5 Gama na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun muguntarsu, wato kwana ɗari uku da tasa'in da za ka kwanta. Ta haka za ka ɗauki alhakin muguntar mutanen Isra'ila. 6 Sa'ad da ka cika waɗannan kwanaki, sai ka sāke kwantawa, kwanciya ta biyu, a damanka kwana arba'in don ka ɗauki alhakin muguntar mutanen Yahuza. Kwana ɗaya a bakin shekara guda. 7 “Za ka fuskanci Urushalima wadda aka kewaye ta da yaƙi da hannunka a zāge, sa'an nan ka yi annabci a kanta. 8 Ga shi, zan ɗaure ka da igiyoyi don kada ka juya har ka gama misalin adadin kwanakin da za a kewaye Urushalima da yaƙi. 9 “Ka kuma ɗauki alkama, da sha'ir, da wake, da waken soya, da gero, da acca, ka haɗa su a kasko ɗaya, ka yi abinci da su. Shi ne za ka ci a kwanakin na ɗari uku da tasa'in da za ka kwanta. 10 Za a auna maka abincin da za ka ci, kamar nauyin shekel ashirin ne a yini. Za ko ci shi a ƙayyadadden lokaci kowace rana. 11 Za a kuma auna maka ruwan da za ka sha, misalin kwalaba biyu ga yini. Za ka sha ruwan a ƙayyadadden lokaci kowace rana. 12 Za ka yi waina kamar ta sha'ir, ka ci. Za ka toya ta da najasa a idon jama'a.” 13 Ubangiji ya ce, “Haka jama'ar Isra'ila za su ci ƙazantaccen abincinsu a cikin sauran al'umma inda za a kai su bautar talala.” 14 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Tun daga ƙuruciyata har zuwa yau, ban taɓa cin mushe ba, ko abin da namomin jeji suka kashe. Ƙazantaccen nama bai taɓa shiga bakina ba.” 15 Sa'an nan ya ce mini, “To, zan bar ka ka mori taroson shanu maimakon najasa, don ka dafa abincinka.” 16 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ga shi, zan datse abinci a Urushalima. Za su auna abincin da za su ci da tsoro, su kuma auna ruwan da za su sha da damuwa. 17 Haka abinci da ruwa za su kāsa, za su kuwa dubi juna da damuwa. Za su lalace saboda zunubansu.”

Ezekiyel 5

Ezekiyel ya Aske Kansa

1 Ubangiji ya ce, “Ya kai ɗan mutum, sai ka ɗauki takobi mai kaifi, ka more shi kamar askar wanzami, ka aske kanka da gemunka. Ka auna gashin da ma'auni, don ka raba shi kashi uku. 2 Sai ka ƙone kashi ɗaya da wuta a tsakiyar birnin sa'ad da kwanakin kewaye birnin da yaƙi suka cika. Ka kuma ɗauki sulusi ɗaya ka yanyanka da takobi kewaye da birnin. Sulusi ɗayan kuwa za ka watsar ya bi iska. Ni kuwa zan zare takobi a kansu. 3 Za ka ɗibi gashi kaɗan ka ɗaure a shafin rigarka. 4 Daga cikin gashi kaɗan ɗin nan kuma, sai ka ɗibi waɗansu ka sa a wuta. Daganan ne wuta za ta tashi a Isra'ila duka.” 5 Ubangiji Allah ya ce, “Wannan ita ce Urushalima. Na kafa ta a tsakiyar al'ummai da ƙasashe kewaye da ita. 6 Ga shi, ta tayar wa ka'idodina da muguwar tayarwa fiye da la'ummai, ta kuma tayar wa dokokina fiye da sauran ƙasashen da ke kewaye da ita. Ta ƙi bin ka'idodina, ta kuma ƙi ta yi tafiya bisa ga dokokina. 7 Domin haka ni na ce, ‘Da ya ke kin cika rikici fiye da sauran ƙasashen da ke kewaye da ke, kin ƙi yin tafiya cikin dokokina, ba ki kiyaye ka'idodin ba, amma kin bi ka'ikodin al'umman da ke kewaye da ke, 8 to, ina gāba da ke, zan hukunta ki a idanun al'ummai. 9 Saboda yawan abubuwa masu banƙyama da kika aikata, zan yi miki abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan sāke yin irinsa ba. 10 Ubanni za su cinye 'ya'yansu, 'ya'ya kuma za su cinye ubanninsu. Zan hukunta ki, waɗanda kuma suka tsira zan watsar da su ko'ina. 11 “ ‘Tun da ya ke kin ƙazantar da Haikalina mai tsarki da gumakanki da abubuwanki masu banƙyama, hakika, ni Ubangiji Allah, zan kawar da ke, ba zan ji tausayinki ba, ba kuwa zan haƙura ba. 12 Sulusinki zai mutu da annoba da yunwa. Takobi kuma zai kashe sulusinki, sa'an nan zan watsar da sulusinki ko'ina, zan kuma zare takobi a kansu. 13 “ ‘Ta haka zan sa fushina ya huce, hasalata kuma a kansu ta lafa, ni kuma in wartsake. Sa'an nan za su sani ni Ubangiji na yi magana da zafin kishi sa'ad da na iyar da fushina a kansu. 14 Zan kuma maishe ki kufai da abin zargi ga al'ummai da ke kewaye da ke, da kuma a idanun dukan masu wucewa. 15 “ ‘Za ki zama abin zargi, da abin ba'a, da abin faɗaka, da abin tsoro ga al'ummai da ke kewaye da ke sa'ad da na hukunta ki da zarin fushina, ni Ubangiji na faɗa. 16 Gama zan aiko miki da masifu na yunwa domin hallakarwa. Zan aiko miki da su don su hallaka ki. Zan kawo miki yunwa mai tsanani, in sa abincinki ya ƙare. 17 Zan aiko miki da yunwa da namomin jeji, za su washe 'ya'yanki. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki. Zan kuma kawo takobi a kanki, ni Ubangiji na faɗa.’ ”

Ezekiyel 6

Annabci gāba da Duwatsun Isra'ila

1 Ubangiji ya yi magana da ni ya ce, 2 “Ya ɗan mutum, ka zuba ido wajen duwatsun Isra'ila, sa'an nan ka yi annabci a kansu. 3 Ka ce musu, ‘Ya ku duwatsun Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji Allah! Haka Ubangiji Allah ya ce a kan duwatsu, da tuddai, da kwazazzabai, da kwaruruka. Ga shi, ni kaina, zan kawo takobi a kanku, zan hallaka wuraren tsafinku. 4 Bagadanku za su zama kango, za a farfasa bagadanku na ƙona turare, zan sa kisassunku su faɗi a gaban gumakansu, 5 zan sa gawawwakin Isra'ilawa a gaban gumakansu, zan warwatsa ƙasusuwanku kewaye da bagadanku. 6 A duk inda kuke zaune, biranenku za su zama kango, wuraren tsafinku da bagadanku za su lalace, gumakanku da bagadanku na ƙona turare za a farfashe su. Za a shafe dukan abin da kuka yi. 7 Za a kashe waɗansu daga cikinku sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji. 8 “ ‘Duk da haka zan bar waɗansunku da rai, gama waɗansu daga cikinku za su tsere wa takobi, amma zan watsa su cikin sauran al'umma. 9 Waɗansunku da suka tsere za su tuna da ni cikin al'ummai inda aka kai su bautar talala yadda raina ya ɓaci saboda zuciyarsu ta rashin imani wadda ta rabu da ni, da idanunsu masu zina da suke bin gumaka. Za su kuwa ji ƙyamar kansu saboda mugayen abubuwa da suka aikata. 10 Za su kuma sani, ni Ubangiji, ba a banza na ce zan kawo musu wannan masifa ba.’ ” 11 Ubangiji Allah ya ce, “Ka tafa hannunka, ka ɗage ƙafarka, sa'an nan ka ce, ‘Kaito, kaito, saboda dukan mugayen abubuwan ƙyama da mutanen Isra'ila suka yi, gama takobi, da yunwa, da annoba za su kashe su. 12 Annoba za ta kashe wanda ke nesa, wanda ke kusa kuwa takobi zai kashe shi. Yunwa kuma za ta kashe wanda yaƙi ya kewaye shi. Ta haka zan aukar da fushina a kansu. 13 Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji, sa'ad da gawawwakinsu sun kwanta tare da gumakansu kewaye da bagadansu a kan kowane tudu, da kan tsaunuka, da ƙarƙashin kowane itace mai duhuwa, da ƙarƙashin itacen oak mai ganye, duk inda suka miƙa turare mai ƙanshi ga dukan gumakansu. 14 Zan nuna ikona a dukan ƙasar, in mai da ita da wuraren zamansu duka hamada. Ƙasarsu za ta zama hamada har zuwa Dibla. Kowa zai sani ni ne Ubangiji.’ ”

Ezekiyel 7

Matuƙa ta Yi

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ya kai, ɗan mutum, ni Ubangiji Allah, na ce wa ƙasar Isra'ila, matuƙa ta yi a kan kusurwa huɗu na ƙasar! 3 “Yanzu matuƙarki ta yi. Zan fashe fushina a kanki, zan kuma shara'anta ki bisa ga ayyukanki, in hukunta ki saboda dukan ƙazantarki. 4 Ba zan yafe miki ba, ba kuwa zan ji tausayinki ba, amma zan hukunta ki saboda ayyukanki sa'ad da kike tsakiyar aikata ƙazantarki. Sa'an nan za ki sani ni ne Ubangiji.” 5 Ubangiji Allah ya ce, “Masifa a kan masifa, ga shi, tana zuwa! 6 Matuƙa ta yi, ta farka a kanki, ga shi, ta yi! 7 Ƙaddararku ta auko muku, ya ku mazaunan ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato, ranar tunzuri, ba ta murna da ta sowa a kan duwatsu ba. 8 “Yanzu, ba da jimawa ba, zan fashe hasalata a kanku, in aukar da fushina a kanku, in hukunta ku bisa ga ayyukanku. Zan hukunta ku saboda dukan ƙazantarku. 9 Ba zan yafe ba, ba kuwa zan ji tausayi ba, amma zan hukunta ku bisa ga ayyukanku sa'ad da kuke tsakiyar aikata ƙazantarku, sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji wanda ke hukunta ku. 10 “Ga rana ta zo. Ƙaddararku ta zo, rashin gaskiya ta yi fure, girmankai kuma ya yi toho. 11 Hargitsi ya habaka, ya zama sandan mugunta. Ba wanda zai ragu cikinsu, ko yawaitarsu, ko dukiyarsu, ko wani muhimmi a cikinsu. 12 “Lokaci ya yi, ranar ta gabato, kada mai saye ya yi farin ciki, kada kuma mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama fushina yana kan taron jama'a duka. 13 Mai sayarwa ba zai ta da ciniki ba sa'ad da suke da rai, gama fushina yana bisa kan dukan taron jama'arsu, ba zai fasa ba. Ba wanda ke zamansa cikin zunubi da zai iya shiryar da kansa.”

Hukunci a kan Zunuban Isra'ila

14 “Sun busa ƙaho, sun gama shiri duka, amma ba wanda ya tafi yaƙi, gama fushina yana kan dukan taron jama'a. 15 Takobi9 yana zare a waje, annoba da yunwa suna ciki. Wanda ke waje takobi zai kashe shi, wanda kuma yake ciki annoba da yunwa za su kashe shi. 16 Idan akwai waɗanda suka tsere, za a same su a kan duwatsu kamar kurciyoyin kwaruruka, suna baƙin ciki dukansu, kowa yana baƙin ciki saboda laifinsa. 17 Dukan hannuwa sun raunana, dukan gwiyoyi kuma sun zama marasa ƙarfi kamar ruwa. 18 Sun sa tufafin makoki, razana ta kama su, fuskokinsu kuma suna cike da kunya, akwai sanƙo a kawunansu. 19 Sun watsar da azurfarsu a titi, zinariyarsu kuma ta zama kamar ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba, a ranar fushin Ubangiji. Ba za su iya ƙosar da su ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu. 20 Suna fariyar banza da kyawawan kayan adonsu, na zinariya da azurfa. Da su suka yi siffofi masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa. Domin haka zan maishe su ƙazantattun abubuwa a gare su. 21 “Zan ba da su ganima ga baƙi, da kwaso ga mugayen mutanen ƙasar. Za su lalatar da su. 22 Zan kuwa juya daga gare su. Zan bar su su ƙazantar da Haikalina. Mafasa za su shiga su ƙazantar da shi. 23 “Sai ka ƙera surƙa, gama ƙasar tana cike da alhakin jini, birnin kuma yana cike da hargitsi. 24 Zan kawo al'ummai masu muguntar gaske su mallaki gidajensu. Zan sa fariyar masu ƙarfi ta ƙare. Za a ƙazantar da masujadansu. 25 Sa'ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba. 26 Masifa a kan masifa, jita-jita a kan jita-jita. Suna neman wahayi daga wurin annabi, amma doka ta lalace a wurin firist, shawara kuma ta lalace a wurin dattawa. 27 Sarki yana makoki, yarima kuma zai fid da zuciya. Hannuwan mutanen ƙasar sun shanye saboda razana. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su kamar yadda suka hukunta waɗansu. Za su kuwa sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 8

Wahayin Abubuwan Banƙyama da ake Yi a Urushalima

1 A kan rana ta biyar ga wata na shida a shekara ta shida ta zaman talala, sa'ad da nake zaune a gidana, dattawan Yahuza kuma suna zaune a gabana, sai ikon Ubangiji Allah ya sauka akaina. 2 Da na duba, sai ga siffa wadda ke da kamannin mutum. Daga kwankwason siffar zuwa ƙasa yana da kamannin wuta, daga kwankwason kuma zuwa sama yana da haske kamar na tagulla. 3 Sai ya miƙa hannu, ya kama zankon kaina. Ruhu kuma ya ɗaga ni bisa tsakanin sama da ƙasa, ya kai ni Urushalima cikin wahayi zuwa ƙofar farfajiya ta ciki, wadda ke fuskantar arewa, inda mazaunin siffa ta tsokano kishi yake. 4 Sai ga ɗaukakar Allah na Isra'ila a wurin, kamar wahayin da na gani a fili. 5 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ɗaga idanunka, ka duba wajen arewa.” Na kuwa ɗaga idanuna wajen arewa, na kuma ga siffa ta tsokano kishi a mashigin ƙofar bagade na wajen arewa. 6 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwa masu banƙyama da mutanen Isra'ila suke yi a nan don su kore ni nesa da Haikalina? Ai, za ka ga abubuwa masu banƙyama da suka fi haka.” 7 Ya kuma kai ni ƙofar shirayi. Sa'ad da na duba, sai ga wani rami a bangon. 8 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka haƙa bangon.” Da na haƙa bangon, sai ga ƙofa. 9 Ya ce, mini, “Ka shiga ka ga abubuwan banƙyama da suke aikatawa a nan.” 10 Da na shiga, sai na ga zānen siffofin kowane irin abu mai rarrafe, da haramtattun dabbobi, da dukan gumakan mutanen Isra'ila kewaye da bangon. 11 Dattawan Isra'ila saba'in suna tsaye a gabansu. Yazaniya ɗan Shafan yana tsaye tare da su. Kowa yana riƙe da farantin ƙona turare. Hayaƙin turaren ya tunnuƙe zuwa sama. 12 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum ko ka ga abin da dattawan Isra'ilawa suke yi a cikin duhu? Kowa yana cikin ɗakin zānannun siffofin gumaka, sukan ce, ‘Allah ba ya ganinmu. Ubangiji ya rabu da ƙasan nan.’ ” 13 Ya kuma ce mini, “Har yanzu dai za ka ga abubuwa masu banƙyama da suka fi haka waɗanda suke aikatawa.” 14 Sai ya kai ni a bakin ƙofar arewa ta Haikalin Ubangiji, ga kuwa mata a zaune suna kuka domin gunkin nan, Tammuz. 15 Sa'an nan ya ce mini, “Ya ɗan mutum, ka ga wannan? Har yanzu ma za ka ga abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.” 16 Ya kuma kai ni farfajiya ta can cikin Haikalin Ubangiji. Na ga mutum wajen ashirin da biyar a ƙofar Haikalin Ubangiji a tsakanin shirayi da bagade, suka juya wa Haikalin Ubangiji baya, suka fuskanci wajen gabas, suna yi wa rana sujada. 17 Ya kuma ce mini, “Ya ɗan mutum, ka ga wannan? Wato mutanen Yahuza ba su mai da aikata abubuwa masu banƙyama nan wani abu ba. Sun cika ƙasar da hargitsi, suna ta tsokanar fushina. Ga shi, suna hura hanci a gabana. 18 Zan yi hukunci mai zafi, ba zan yafe ba, ba kuma zan ji tausayi ba, ko da ya ke suna kuka da babbar murya a kunnuwana ba zan ji su ba.”

Ezekiyel 9

An Kashe Masu Laifi

1 Sai na ji Allah ya yi kira da babbar murya, ya ce, “Ku matso kusa, ku masu hukunta wa birnin, kowa ya zo da makaminsa na hallakarwa a hannu.” 2 Sai ga mutum shida sun taho daga wajen ƙofa wadda take daga bisa wadda ta fuskanci arewa. Kowa yana da makaminsa na kisa a hannu. Tare da su kuma akwai wani mutum saye da rigar lilin, yana kuma rataye da gafaka. Sai suka tafi suka tsaya a gefen bagaden tagulla. 3 Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tashi daga kan siffar kerubobi inda take zaune zuwa bakin ƙofar Haikalin. Sai Ubangiji ya kira mutumin da ke saye da rigar lilin, wanda ke rataye da gafaka. 4 Ya ce masa, “Ka ratsa cikin birni, wato Urushalima, ka sa shaida a goshin mutanen da ke ajiyar zuciya, suna damuwa saboda dukan abubuwa masu banƙyama waɗanda ake aikatawa a birnin.” 5 Na kuma ji ya ce wa sauran, “Ku bi shi, ku ratsa cikin birnin, ku kashe, kada ku yafe, kada kuwa ku ji tausayi. 6 Ku kashe tsofaffi, da samari, da 'yan mata, da ƙananan yara, da mata, amma kada ku taɓa wanda ke da shaida. Sai ku fara Haikalina.” Suka kuwa fara da dattawan da ke a gaban Haikalin. 7 Ya kuma ce musu, “Ku ƙazantar da Haikalin, ku cika farfajiya da kisassu, sa'an nan ku tafi!” Sai suka tafi, suka yi ta kashe mutanen da ke cikin birnin. 8 Sa'ad da suke karkashewar, aka bar ni, ni kaɗai, sai na faɗi rubda ciki, na yi kuka, na ce, “Ya Ubangiji Allah za ka hallaka dukan sauran Isra'ilawa saboda zafin fushinka a kan Urushalima?” 9 Sa'an nan ya ce mini, “Zunubin mutanen Isra'ila da Yahuza ya kasaita ƙwarai. Ƙasar tana cike da jini, birnin kuma yana cike da rashin imani, gama sun ce, ‘Ubangiji ya rabu da ƙasar, ba ya ganinmu.’ 10 Ni kam, idona ba zai yafe ba, ba kuwa zan ji tausayi ba, amma zan sāka musu bisa ga ayyukansu.” 11 Sai ga mutumin da yake saye da rigar lilin, wanda kuma yake rataye da gafaka, ya komo da jawabi cewa, “Na aikata yadda ka umarci ni.”

Ezekiyel 10

Ɗaukakar Ubangiji ta Rabu da Haikali

1 Da na duba sararin sama da ke bisa kawunan kerubobi, sai na ga wani abu ya bayyana kamar yakutu. Fasalinsa kamar na kursiyi. 2 Sai Ubangiji ya ce wa mutumin da ke saye da rigar lilin. “Ka shiga ƙarƙashin ƙafafun kerubobin, ka cika tafin hannunka da garwashin wuta wanda ke tsakanin kerubobin, ka watsa bisa kan birnin.” Na kuwa ga ya tafi. 3 Kerubobin kuwa suna tsaye a gefen kudu na Haikalin a sa'ad da mutumin ya shiga, girgije kuma ya cika farfajiyar da ke can ciki. 4 Ɗaukakar Ubangiji ta tashi daga kan kerubobin zuwa ƙofar Haikalin. Girgije kuwa ya cika Haikalin, hasken zatin Ubangiji ya cika farfajiyar. 5 Sai aka ji amon fikafikan kerubobin a filin da ke can waje, kamar muryar Allah Maɗaukaki sa'ad da yake magana. 6 Ya kuwa umarci wanda yake saye da lilin ɗin, ya ce, “Ka ɗibi wuta daga ƙarƙashin ƙafafun da ke tsakanin kerubobin.” Sai ya tafi ya tsaya a gefen ƙafar. 7 Kerub kuwa ya miƙa hannunsa daga tsakanin kerubobi zuwa wurin wutar da ke tsakanin kerubobin, ya ɗebo wutar, ya zuba a ahnnun mutumin da ke saye da rigar lilin. Shi kuwa ya karba, ya fita. 8 Kerubobin suna da hannuwa kamar na 'yan adam a ƙarƙashin fikafikansu. 9 Da na duba, sai na ga ƙafa guda huɗu kusa da kerubobin. Kowane kerub yana da ƙafa ɗaya kusa da shi. Ƙafafun suna ƙyalli kamar wani dutse mai daraja. 10 Dukansu kuwa kamanninsu ɗaya, kamar ƙafa a cikin ƙafa. 11 Sa'ad da suke tafiya, sukan tafi kowane waje, ba sai sun juya ba. Duk wajen da ƙafar gaba ta nufa, nan sauran za su bi, ba sai sun juya ba. 12 Suna da idanu a jikunansu ko'ina, a bayansu, da hannuwansu, da fikafikansu da kuma ƙafafunsu. 13 Na ji ana kiran ƙafafun, ƙafafun guguwa. 14 Kowane kerbu yana da fuska huɗu. Fuska ta fari ta kerub ce, fuska ta biyu ta mutum ce, fuska ta uku ta zaki ce, fuska ta huɗu kuwa ta gaggafa ce. 15 Kerubobin kuwa suka tashi sama. Waɗannan su ne talikai huɗu waɗanda na gani a bakin kogin Kebar. 16 Sa'ad da kerubobin suka tafi, ƙafafun kuma sukan tafi tare da su. Sa'ad da suka ɗaga fikafikansu don su tashi daga ƙasa zuwa sama, ƙafafun kuma ba su barinsu. 17 Sa'ad da suka tsaya cik, sai ƙafafun su ma su tsaya cik, sa'ad da suka tashi sama, sai su kuma su tashi tare da su, gama ruhun talikan yana cikinsu. 18 Sai ɗaukakar Ubangiji ta tashi daga bakin ƙofar Haikalin, ta tsaya bisa kerubobin. 19 Kerubobin kuwa suka ɗaga fikafikansu, suka tashi daga ƙasa, suka yi sama a kan idona, suka tafi da ƙafafun gab da su. Suka tsaya a ƙofar gabas ta Haikalin Ubangiji. Ɗaukakar Allah na Isra'ila kuwa tana bisa kansu. 20 Waɗannan su ne talikan da na gani a ƙarƙarshin kursiyin Allah na Isra'ila a bakin kogin Kebar, na kuwa sani su kerubobi ne. 21 Kowannensu yana da fuska huɗu, da fiffike huɗu. A ƙarƙashin fikafikansu suna da hannuwa irin na 'yan adam. 22 Kamannin fuskokinsu kuma daidai yake da kamannin fuskokin da na gani a bakin kogin Kebar. Sai suka tafi, kowa ya nufi gabansa sosai.

Ezekiyel 11

An Tsauta wa Mugayen Shugabanni

1 Sai Ruhu ya ɗaga ni sama, ya kai ni ƙofar gabas ta Haikalin Ubangiji wadda ke fuskantar gabas. Sai ga mutum ashirin da biyar a bakin ƙofar. A cikinsu na ga Yazaniya ɗan Azzur, da Felatiya ɗan Benaiya, shugabannin jama'a. 2 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da ke ƙulla mugunta, waɗanda ke ba da muguwar shawara a cikin birnin. 3 Waɗanda ke cewa, ‘Lokacin gina gidaje bai yi kusa ba. Wannan birni tukunya ce mai ɓararraka, mu ne kuwa naman.’ 4 Saboda haka ka yi musu annabci marar kyau, ka yi annabci, ya ɗan mutum!” 5 Sa'an nan Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya ce mini, “Ka ce, ‘In ji Ubangiji, haka kuke tunani, ku mutanen Isra'ila, gama na san abin da ke cikin zuciyarku. 6 Kun kashe mutane da yawa a wannan birni, har kun cika titunansa da gawawwaki.’ 7 “Domin haka Ubangiji Allah ya ce, ‘Gawawwakin da kuka shimfiɗa a cikin birnin su ne naman, birnin kuwa shi ne tukunya mai ɓararraka, amma za a fitar da ku daga cikinsa. 8 Kun tsorata saboda takobi, ni kuwa zan kawo muku takobi,’ in ji Ubangiji Allah. 9 ‘Zan fitar da ku daga cikin birnin, in bashe ku a hannun baƙi, zan hukunta ku. 10 Za a kashe ku da takobi. Zan hukunta ku duk inda kuke a Isra'ila, sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji. 11 Birnin ba ai zama muku tukunya mai ɓararraka ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinsa ba. Zan hukunta ku duk inda kuke a Isra'ila. 12 Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji, gama ba ku kiyaye dokokina da ka'idodina ba, amma kuka kiyaye ka'idodin sauran al'umma waɗanda suke kewaye da ku.’ ” 13 Sa'ad da nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benaiya, ya rasu. Sai na faɗi rubda ciki na fashe da kuka, na ce, “Ya Ubangiji Allah, za ka ƙare sauran mutanen Isra'ila ƙaƙaf ne?”

Allah ya Yi wa Waɗanda aka Kai Bautar Talala Alkawari

14 Ubangiji kuwa ya yi magana da ni, ya ce, 15 “Ɗan mutum, 'yan'uwanka, da danginka, da mutanenka da ke cikin bautar talala tare da kai, da dukan mutanen Isra'ila, su ne waɗanda mazaunan Urushalima ke ce musu, ‘Ku yi nisa da Ubangiji, mu aka mallakar wa wannan ƙasa.’ 16 “Domin haka, ka ce, ‘Ni Ubangiji Allah na ce, ko da ya ke na kai su nesa tsakanin al'ummai, na warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama Haikali a gare su a ɗan lokaci, a ƙasashen da suka tafi.’ 17 “Saboda haka ka ce, ‘Ni Ubangiji na ce, zan tattaro ku daga cikin al'ummai, da ƙasashen da aka warwatsa ku, ni kuwa zan ba ku ƙasar Isra'ila.’ 18 Sa'ad da suka koma a ƙasar za su kawar da dukan abin da ya ƙazantar da ita, da dukan irin abar ƙyama da ke cikinta. 19 Zan ba su zuciya ɗaya, in kuma sa sabon ruhu a cikinsu. Zan kawar musu da zuciya ta dutse, in ba su zuciya mai taushi, 20 domin su kiyaye dokokina, da ka'idodina, su aikata su. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu. 21 Amma waɗanda zuciyarsu ta karkata zuwa ga bin ƙazantattun abubuwa masu banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, ni Ubangiji na faɗa.”

Ɗaukakar Ubangiji ta Rabu da Urushalima

22 Sa'an nan kerubobin suka ɗaga fikafikansu tare da ƙafafunsu. Ɗaukakar Ubangiji kuwa tana bisa kansu. 23 Sai ɗaukakar Ubangiji ta bar tsakiyar birni, ta tsaya a bisa kan dutse wanda ke wajen gabas da birnin. 24 Ruhu kuwa ya ɗauke ni a cikin wahayi, ya kai ni Kaldiya wurin 'yan zaman talala. Sa'an nan wahayin da na gani ya rabu da ni. 25 Sai na faɗa wa 'yan zaman talala dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.

Ezekiyel 12

Kwatancin Kwashewarsu zuwa Bautar Talala

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, kana zaune a tsakiyar gidan 'yan tawaye da suke da idanun gani, amma ba sa gani, suna da kunnuwa na ji, amma ba sa ji, gama su 'yan tawaye ne. 3 Domin haka, ɗan mutum sai ka shirya kaya don zuwa zaman talala, sa'an nan ka tashi da rana a kan idonsu. Za ka ƙaura daga wurinka zuwa wani wuri a kan idonsu, watakila za su gane, cewa su 'yan tawaye ne. 4 Za ka fitar da kayanka da rana a kan idonsu, kamar kayan mai tafiyar zaman talala. Kai kuma da kanka za ka tafi da maraice a kan idonsu, kamar yadda mutane masu tafiyar zaman talala sukan yi. 5 Ka huda katanga a kan idonsu, sa'an nan ka fita daga ciki. 6 A gabansu za ka ɗauki kayan, ka saɓa shi a kafaɗarka, ka tafi da shi da dare. Za ka rufe fuskarka don kada ka ga ƙasar, gama na maishe ka alama ga jama'ar Isra'ila.” 7 Na kuwa yi kamar yadda aka umarce ni. Na fitar da kayana da rana, kamar kayan mai tafiyar zaman talala. Da maraice na huda katanga da hannuwana, sa'an nan na fita da duhu, ina ɗauke da kayana a kafaɗa, a kan idonsu. 8 Da safe kuwa Ubangiji ya yi mini magana, ya ce, 9 “Ɗan mutum, ashe, mutanen Isra'ila, 'yan tawayen nan, ko suka ce maka, ‘Me kake yi?’ 10 Ka ce musu, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Wannan jawabi ya shafi shugabannin Urushalima da dukan mutanen Isra'ila, waɗanda ke cikinta.’ 11 Ka ce musu, ‘Ni alama ne a gare ku, kamar yadda na yi, haka za a yi da ku, za a kai ku bauta.’ 12 Sarkin da ke cikinsu zai ɗauki kayansa ya saɓa a kafaɗarsa, ya fita da duhu. Zai huda katanga ya fita. Zai rufe fuskarsa don kada ya ga ƙasar da idanunsa. 13 Zan yarɓa masa ragata in kama shi. Zan kai shi Babila, wato ƙasar Kaldiyawa, duk da haka ba zai gan ta ba, ko da ya ke zai rasu a can. 14 Zan warwatsa dukan waɗanda ke kewaye da shi, masu taimakonsa da sojojinsa ko'ina. Zan zare takobi in runtume su. 15 “Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na watsa su cikin sauran al'umma da cikin ƙasashe. 16 Amma zan bar kaɗan daga cikinsu su tsere wa takobi, da yunwa, da annoba, don su tuba, su hurta dukan ayyukansu na banƙyama a cikin al'ummai inda suka tafi. Za su sani ni ne Ubangiji.”

Kwatancin Annabin da ke Rawar Jiki

17 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 18 “Ɗan mutum, ka ci abincinka da rawar jiki, ka sha ruwanka da makyarkyata da damuwa. 19 Ka faɗa wa mutanen ƙasar, cewa ni Ubangiji Allah na ce mutanen Urushalima da ke a ƙasar Isra'ila za su ci abincinsu da razana, su sha ruwansu da tsoro, gama za a washe dukan abin da ke ƙasarsu saboda hargitsin dukan waɗanda ke zaune cikinta. 20 Biranen da ake zaune a cikinsu za su zama kufai, ƙasar kuma za ta zama kango, za su kuwa sani ni ne Ubangiji.”

Sanannen Karin Magana da Jawabi Marar Daɗi

21 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 22 “Ɗan mutum, menene wannan karin magana da ake faɗa a ƙasar Isra'ila cewa, ‘Kwanaki suna ta wucewa, wahayi bai gudana ba?’ 23 Ka faɗa musu, ka ce ni Ubangiji Allah na ce zan kawo ƙarshen wannan karin magana, ba za su ƙara faɗar wannan karin magana a Isra'ila ba. Amma ka faɗa musu, cewa kwanaki sun gabato da za a tabbatar da kowane wahayi. 24 “Wahayin ƙarya da d�bā na kiran kasuwa za su ƙare a Isra'ila. 25 Gama ni Ubangiji zan yi magana, maganata kuwa za ta tabbata, ba za ta yi jinkiri ba, amma za ta tabbata a kwanakinku, ku 'yan tawaye. Zan yi magana, za ta kuwa tabbata, ni Ubangiji Allah, na faɗa.” 26 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 27 “Ɗan mutum, ga shi, mutanen Isra'ila suna cewa, ‘Wahayin da ya gani na wani lokaci ne can gaba, yana annabci a kan wani zamani ne na can.’ 28 Domin haka ka faɗa musu, cewa ni Ubangiji na ce maganata ba za ta yi jinkiri ba, amma maganar da na faɗa za ta tabbata, ni Ubangiji Allah, na faɗa.”

Ezekiyel 13

An La'anci Maƙaryatan Annabawa

1 Sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ya ɗan mutum, ka yi annabci a kan annabawan Isra'ila. Ka yi annabci a kan waɗanda suke annabci bisa ga ra'ayin kansu, ka ce, ‘Ku ji maganar Ubangiji!’ 3 “Ubangiji Allah ya ce kaito ga wawayen annabawa waɗanda suke bin ra'ayin zuciyarsu, ba su kuwa ga wani wahayi ba. 4 Ya Isra'ila, annabawanki suna kamar diloli a kufai. 5 Ba ku ƙaura zuwa inda garu ya tsage ba, ba ku gina wa mutanen Isra'ila garu don su kāre kansu a lokacin yaƙi, a ranar Ubangiji ba. 6 Suna faɗar ƙarya, suna kuma yin duban ƙarya, suna cewa, ‘Ubangiji ya ce,’ alhali kuwa Ubangiji bai aike su ba, duk da haka sun sa zuciya ga cikawar maganarsu. 7 Wahayin ƙarya ne kuka gani, kuna yin duban ƙarya, sa'ad da kuke cewa, ‘Ubangiji ya faɗa,’ ko da ya ke ni Ubangiji ban faɗa ba. 8 “Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce, da ya ke kun yi maganar wofi, kun ga wahayin ƙarya, ina gāba da ku. 9 Ikona zai yi gāba da annabawan da ke ganin wahayin ƙarya, waɗanda suke kuma yin duban ƙarya. Ba za su kasance cikin taron mutanena ba, ba kuwa za a rubuta su a littafin mutanen Isra'ila ba, ba za su shiga ƙasar Isra'ila ba. Za ku kuwa sani, ni ne Ubangiji Allah. 10 “Domin sun ɓad da mutanena suna cewa, ‘Salama,’ sa'ad da ba salama, sa'ad da kuma mutanen ke gina garu marar aminci, sai annabawan nan su shafe shi da farar ƙasa, 11 ka faɗa wa waɗanda suka shafe garun da farar ƙasa, cewa zai faɗi. Za a yi rigyawa da ƙanƙara, da babban hadiri mai iska. 12 Sa'ad da garun ya faɗi, ashe, ba za a tambaye ku ba cewa, ‘Ina shafen farar ƙasar da kuka yi masa?’ 13 “Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce da hasalata zan sa babban hadiri mai iska, da rigyawa, da manyan ƙanƙara su hallaka shi. 14 Zan rushe garun da kuka shafe da farar ƙasa. Za a baje shi, a bar tushen a fili. Za ku halaka a tsakiyarsa sa'ad da ya fāɗi, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji. 15 “Ta haka zan aukar da hasalata a kan garun, da a kan waɗanda suka shafe shi da farar ƙasa. Sa'an nan zan faɗa muku, cewa garun ya faɗi tare da waɗanda suka shafe shi da farar ƙasa. 16 Wato annabawan Isra'ila waɗanda suka yi annabci a kan Urushalima, suka ga wahayin salama dominta, ga shi kuwa, ba salama, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

An La'anci Mata Masu Annabcin Ƙarya

17 “Kai kuwa ɗan mutum, sai ka ɗaure wa matan mutanenka fuska, waɗanda ke annabci bisa ga son zuciyarsu. Ka yi annabci a kansu, 18 ka ce, ‘Ubangiji Allah ya ce, kaiton matan da ke ɗinka wa mutane kambuna, suna yi wa mutane rawunan dabo bisa ga zacinsu don su farauci rayukan mutane. Za ku farauci rayukan mutanena, sa'an nan ku bar rayukan waɗansu don ribar kanku? 19 Kun saɓi sunana a cikin mutanena don a tafa muku sha'ir, a ba ku ɗan abinci. Kuna kashe mutane waɗanda bai kamata su mutu ba, kuna barin waɗanda bai kamata su rayu ba ta wurin ƙaryace-karyacen da kuke yi wa mutanena waɗanda ke kasa kunne ga ƙaryace-ƙaryacen.’ 20 “Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce, ina gāba da kambunanku da kuke farautar rayuka da su. Zan tsintsinke su daga damatsanku, in saki rayuka waɗanda kuka farauto kamar tsuntsaye. 21 Zan kuma kyakketa rawunanku na dabo, in ceci mutanena daga hannunku, ba za su ƙara zama ganima a hannunku ba, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji. 22 “Kun karya zuciyar adali ta wurin ƙaryarku, ko da ya ke ni ban karya zuciyarsa ba. Kun ƙarfafa wa mugu gwiwa, don kada ya bar hanyarsa ta mugunta, ya tsira. 23 Domin haka ba za ku ƙara ganin wahayin ƙarya ba, ko ku yi d�ba. Zan ceci mutanena daga hannunku. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 14

An La'anci Bautar Gumaka

1 Waɗansu dattawa na Isra'ila suka zo wurina, suka zauna a gabana. 2 Sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 3 “Ɗan mutum, waɗannan mutane sun sa zukatansu ga bin gumaka, sun sa abin tuntuɓe a gabansu, zan fa yarda su yi tambaya a wurina? 4 “Sai ka faɗa musu, cewa Ubangiji Allah ya ce duk mutumin Isra'ila, wanda ya manne wa gumaka, ya sa abin tuntuɓe a gabansa sa'an nan kuma ya zo wurin annabi, ni Ubangiji zan sāka masa gwargwadon yawan gumakansa, 5 domin in kama zukatan mutanen Isra'ila waɗanda suka zama baƙi a gare ni, saboda gumakansu. 6 “Domin haka ka ce wa mutanen Isra'ila, ‘Ubangiji ya ce ku tuba, ku rabu da gumakanku, da abubuwanku na banƙyama. 7 “ ‘Gama duk wanda ke na Isra'ila da dukan baƙin da ke baƙunta cikin Isra'ila, wanda ya rabu da ni, ya manne wa gumakansa, ya sa abin tuntuɓe a gabansa, sa'an nan ya zo yana roƙona a wurin annabi, ni Ubangiji zan sāka masa. 8 Zan yi gāba da mutumin nan, zan sa ya zama abin nuni, da abin karin magana, in datse shi daga cikin mutanena, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji. 9 “ ‘Idan aka ruɗi annabin har ya yi magana, ni Ubangiji, ni ne na rinjaye shi, zan miƙa hannuna gāba da shi, zan hallaka shi daga cikin mutanena, Isra'ila. 10 Za su ɗauki alhakin hukuncinsu, wato hukuncin annabin, da hukuncin mai yin roƙonsa duk ɗaya ne, 11 don kada mutanen Isra'ila su ƙara rabuwa da ni, ko kuma su ƙara ƙazantar da kansu ta wurin laifofinsu, amma za su zama mutanena, ni kuwa in zama Allahnsu,’ ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Hukuncin Allah a kan Urushalima

12 Ubangiji ya yi magana da ni ya ce, 13 “Ɗan mutum, sa'ad da wata ƙasa ta yi mini laifi na rashin aminci, ni kuwa na miƙa hannuna gāba da ita, na toshe hanyar abincinta, na aika mata da yunwa, na kashe mata mutum duk da dabba, 14 ko da Nuhu, da Daniyel, da Ayuba suna cikinta, rayukansu ne kaɗai za su ceta saboda adalcinsu, ni Ubangiji na faɗa. 15 “Idan na sa namomin jeji su ratsa cikin ƙasar, su lalatar da ita har ta zama kufai yadda mutum ba zai iya ratsawa ta cikinta ba saboda namomin jejin, 16 ko da mutum uku ɗin nan suna cikinta, ni Ubangiji Allah na rantse da zatina, ba za su ceci 'ya'ya mata ko 'ya'ya maza ba, su ne kaɗai za su tsira, amma ƙasa za ta zama kufai. 17 “Idan kuwa na jawo wa ƙasar takobi, na ce bari takobi ya ratse ƙasar, har na kashe mata mutum duk da dabba, 18 ko da mutum uku ɗin nan suna cikinta, ni Ubangiji Allah na rantse da zatina, ba za su ceci 'ya'ya mata ko 'ya'ya maza ba, su kaɗai za su tsira. 19 Ko kuma na aika da annoba a ƙasar, na kashe mutum duk da dabba da fushina, 20 ko da Nuhu, da Daniyel, da Ayuba suna cikinta, ni Ubangiji Allah na rantse da zatina, ba za su ceci 'ya'ya mata ko 'ya'ya maza ba, rayukansu ne kaɗai za su ceta saboda adalcinsu. 21 “Ni Ubangiji Allah na ce, ‘Balle fa sa'ad da na aika wa Urushalima da hukuntaina guda huɗu masu zafi, wato takobi, da yunwa, da mugayen namomin jeji, da annoba, don in kashe mutum duk da dabba! 22 Idan kuwa waɗansu sun wanzu daga cikinta suka fita da 'ya'yansu mata da maza zuwa wurinta, za ka ga halinsu da ayyukansu, za ka tabbata, masifar da na aukar wa Urushalima, ba kawai ba ne. 23 Bisa ga halinsu da ayyukansu za ka gane abin da na yi musu ba kawai ba ne,’ ni Ubangiji na faɗa.”

Ezekiyel 15

Misali a kan Kurangar Inabi

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum da me itacen kurangar inabi ya fi wani itace? Da me reshen kurangar inabi ya fi wani reshen itacen da ke a kurmi? 3 Za a sami itace a cikin kuranga a yi aiki da shi? Ko kuwa mutane za su iya samun maratayi a cikinta don su rataye kaya? 4 Ga shi, akan sa ta a wuta. Sa'ad da wutar ta cinye kanta da gindinta tsakiyarta kuma ta babbake, tana da amfani don yin wani aiki kuma? 5 Ga shi ma, lokacin da take cikakkiya, ba ta da wani amfani, balle bayan da wuta ta babbake ta, za a iya yin amfani da ita? 6 “Domin haka, ni Ubangiji Allah na ce, kamar itacen kurangar inabi a cikin itatuwan kurmi, wanda na sa ya zama itacen wuta, haka zan sa mazaunan Urushalima su zama. 7 Zan yi gāba da su, ko da ya ke sun tsere wa wuta, duk da haka wuta za ta cinye su. Za ku sani ni ne Ubangiji sa'ad da na tashi yin gāba da su. 8 Zan sa ƙasar ta zama kufai domin sun yi rashin aminci, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 16

Rashin Amincin Urushalima da Samariya

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka sa Urushalima ta san ayyukanta na banƙyama. 3 Ka faɗa wa Urushalima abin da ni Ubangiji Allah na ce mata.” Ubangiji ya ce, “Asalinki da haihuwarki daga ƙasar Kan'ana ne. Mahaifinki Ba'amore ne, mahaifiyarki kuwa Bahittiya ce. 4 Game da haihuwarki kuwa, ran da aka haife ki, ba a yanke cibiyarki ba, ba a kuma yi miki wanka da ruwa don a tsabtace ki ba, ba a kuma goge ki da gishiri ba, ba a naɗe ki cikin tsummoki ba. 5 Ba wanda ya ji tausayinki da zai yi miki waɗannan abubuwa na jinƙai, amma aka jefar da ke a waje, gama kin zama abin ƙyama a ranar da aka haife ki. 6 “Sa'ad da na wuce kusa da ke, na gan ki kina birgima cikin jinin haihuwarki, sai na ce miki lokacin da kike cikin jinin, ‘Ki rayu!’ Ji, na ce miki lokacin da kike cikin jinin, ‘Ki rayu!’ 7 Na sa kin girma kamar tsiro a cikin saura. Kika yi girma, kika yi tsayi, kika zama cikakkiyar budurwa, kika yi mama, gashin kanki kuwa ya yi tsawo, amma duk da haka tsirara kike tik a lokacin. 8 “Sa'ad da na sāke wucewa kusa da ke, na dube ki, ga shi, kin kai lokacin da za a kaunace ki, sai na yafe miki tufata, na rufe tsiraincinki, na rantse miki, na ƙulla alkawari da ke, kin kuwa zama tawa, ni Ubangiji Allah na faɗa. 9 “Sa'an nan na yi miki wanka da ruwa, na wanke jinin haihuwarki na shafe ki da mai. 10 Na sa miki rigar da aka yi wa ado, na kuma sa miki takalmin fata, na yi miki ɗamara da lilin mai kyau, na yi miki lulluɓi da siliki. 11 Na kuwa caɓa miki ado, na sa mundaye a hannuwanki, da abin wuya a wuyanki. 12 Na kuma sa ƙawanya a hancinki, da 'yan kunne a kunnenki, da kyakkyawan kambi bisa kanki. 13 Haka kuwa aka caɓa miki zinariya da azurfa. Tufafinki kuwa na lilin mai kyau ne, da siliki waɗanda aka yi musu ado. Kin ci lallausan gāri, da zuma, da mai. Kin yi kyau ƙwarai har kin zama sarauniya. 14 Kin shahara a cikin sauran al'umma saboda kyanki, gama kyanki ya zama cikakke saboda ƙawata ki da na yi, ni Ubangiji Allah na faɗa. 15 “Amma kin dogara ga kyanki, kika yi karuwanci saboda shahararki. Kin yi ta karuwancinki da kowane mai wucewa. 16 Kin ɗauki waɗansu rigunanki, kika yi wa kanki masujadai masu ado, sa'an nan kika yi karuwanci a cikinsu, irin abin da ba a taɓa yi ba, ba kuwa za a yi ba nan gaba. 17 Kin kuma ɗauki kayan adonki na zinariyata da azurfata waɗanda na ba ki, kin yi wa kanki siffofin mutane don ki yi karuwanci da su. 18 Kin ɗauki tufafinki da aka yi musu ado, kika lulluɓe su, sa'an nan kika ajiye maina da turarena a gabansu. 19 Abincina da na ba ki kuma, wato lallausan gāri, da mai, da zuma, waɗanda na ciyar da ke da su, kin ajiye a gabansu don ƙanshi mai daɗi, ni Ubangiji Allah na faɗa. 20 “Kin kuma kwashe 'ya'yana mata da maza waɗanda kika haifa mini kin miƙa su hadaya ga gumaka. Karuwancinki, ba ƙanƙanen abu ba ne. 21 Kin karkashe 'ya'yana, kin sa su ratsa cikin wuta. 22 A cikin aikata dukan abubuwanki na banƙyama kuma, da karuwancinki, ba ki tuna da kwanakin kuruciyarki ba, lokacin da kike tsirara tik, kina birgima cikin jinin haihuwarki. 23 “Bayan dukan muguntarki Kaito, kaitonki! Ni Ubangiji Allah na faɗa, 24 sai kika gina wa kanki ɗakunan tsafi a kowane fili. 25 Kika kuma gina ɗakin tsafi a kowane titi. Kin waƙala darajarki, kin ba da kanki ga kowane mai wucewa, ta haka kika yawaita karuwancinki. 26 Kin yi karuwanci da Masarawa, maƙwabtanki masu kwaɗayi. Kin yawaita karuwancinki don ki tsokani fushina. 27 “Domin haka na miƙa hannuna gāba da ke, na rage rabonki, na ba da ke ga abokin gābanki masu haɗama, 'yan matan Filistiyawa waɗanda suka ji kunya saboda halinki na lalata. 28 “Kin kuma yi karuwanci da Assuriyawa domin ba ki ƙoshi ba. Kin yi karuwanci da su duk da haka ba ki ƙoshi ba. 29 Kin yawaita karuwancinki da Kaldiya, ƙasar ciniki, duk da haka ba ki ƙoshi ba. 30 “Kin cika uzuri,” in ji Ubangiji Allah. “Duba, kin aikata waɗannan abubuwa duka, ayyuka na karuwa marar kunya. 31 Kin gina ɗakunan tsafi a kowane titi da kowane fili. Amma ke ba kamar karuwa ba ce, da ya ke ba ki karɓar kuɗi. 32 Ke mazinaciyar mace, mai kwana da kwartaye maimakon mijinki! 33 Maza sukan ba dukan karuwai kuɗi, amma ke ce mai ba kwartayenki kuɗi, kina ba su kuɗi don su zo wurinki don kwartanci daga ko'ina. 34 Kin yi dabam da sauran mata a cikin karuwancinki, da ya ke ba wanda ya bi ki don yin karuwanci, ba a ba ki kuɗi, ke ce kike ba da kuɗi, domin haka kin sha bamban.” 35 Domin haka, ya ke karuwa, ki ji maganar Ubangiji. 36 “Ubangiji Allah ya ce, da ya ke kunyarki ta bayyana, an buɗe tsiraicinki cikin karuwancinki, saboda kuma gumakanki, da jinin 'ya'yanki da kika miƙa wa gumakanki, 37 domin haka zan tattara miki daga kowane waje dukan kwartayenki, waɗanda kika yi nishaɗi da su, wato dukan waɗanda kika ƙaunace su, da waɗanda kika ƙi. Zan sa su yi gāba da ke. Zan buɗe musu tsiraicinki don su gani. 38 Zan hukunta ki kamar yadda akan hukunta mata waɗanda suka ci amanar aure, suka zub da jini. Zan hallaka ki cikin zafin fushina da kishina. 39 Zan bashe ki a hannun kwartayenki, za su kuwa rushe ɗakunan tsafinki, su tuɓe tufafinki, su kwashe murjaninki, su bar ki tsirara tik. 40 “Za su kuta taron mutane a kanki, za su jajjefe ki da duwatsu, su yayanka ki gunduwa gunduwa da takubansu. 41 Za su kuma ƙone gidajenki, su hukunta ki a gaban mata da yawa. Ni kuwa zan sa ki bar karuwanci, ba za ki ƙara ba da kuɗi ga kwartayenki ba. 42 Sa'an nan fushina a kanki zai huce, kishina a kanki zai ƙare. Zan huce, ba zan yi fushi ba kuma. 43 Da ya ke ba ki tuna da kwanakin kuruciyarki ba, amma kika husatar da ni da waɗannan abubuwa, domin haka zan sāka miki alhakin ayyukanki. Kin yi lalata, banda ayyukanki na banƙyama kuma, ni Ubangiji na faɗa.” 44 Ubangiji ya ce, “Ga shi, duk mai yin amfani da karin magana, zai faɗi wannan karin magana a kanki. ‘Kamar yadda mahaifiya take haka 'yar take.’ 45 Ke 'yar mahaifiyarki ce wadda ta ƙi mijinta da 'ya'yanta. Ke kuma 'yar'uwar 'yar'uwanki mata ce waɗanda suka ƙi mazansu da 'ya'yansu. Mahaifiyarki Bahittiya ce, mahaifinki kuwa Ba'amore ne. 46 “'Yarki ita ce Samariya wadda ke zaune da 'ya'yanta mata wajen arewa da ke. Ƙanwarki ita ce Saduma wadda ke zaune kudu da ke tare da 'ya'yanta mata. 47 Ba ki bi hanyoyinsu da abubuwansu na banƙyama kaɗai ba, sai ka ce wannan ya yi miki kaɗan, amma kin lalace fiye da su. 48 “Hakika ni Ubangiji Allah na ce Saduma ƙanwarki da 'ya'yanta mata ba su yi kamar yadda ke da 'ya'yanki mata kuka yi ba. 49 Wannan shi ne laifin Saduma, ƙanwarki, ita da 'ya'yanta mata, suna da girmankai domin suna da abinci a wadace, suna zama a sangarce, amma ba su taimaki matalauta da masu bukata ba. 50 Su masu alfarma ne, sun aikata abubuwa masu banƙyama a gabana, saboda haka na kawar da su sa'ad da na gani. 51 “Samariya ba ta aikata rabin zunubin da kika aikata ba. Abubuwan banƙyama da kika aikata sun sa 'yan'uwanki sun zama kamar adalai. 52 Ke kuma sai ki sha kunyarki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su sami rangwamin shari'a saboda zunubanki da kika aikata fiye da nasu, gama gwamma su da ke. Sai ki ji kunya, ki sha ƙasƙancinki, gama kin sa 'yan'uwanki mata su zama kamar adalai.” 53 Ubangiji ya ce wa Urushalima, “Zan komo da Saduma da Samariya da 'ya'yansu mata daga bauta. Sa'an nan zan komo da ke daga bauta tare da su, 54 don ki sha ƙasƙanci saboda abin kunyar da kika aikata. Ƙasƙancinki zai ta'azantar da 'yan'uwanki mata. 55 'Yan'uwanki mata, wato Saduma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā, Samariya kuma da 'ya'yanta mata za su koma kamar yadda suke a dā. Ke kuma da 'ya'yanki mata za ku koma kamar yadda kuke a dā. 56 Ashe, ba ƙanwarki, Saduma, ta zama abar karin magana a bakinki a kwanakin fariyarki, 57 kafin asirin muguntarki ya tonu ba? Amma yanzu kin zama abin zargi ga 'ya'yan Edom mata, da waɗanda ke kewaye da ita, da 'ya'yan Filistiyawa mata waɗanda ke kewaye, waɗanda suke raina ki. 58 Kina ɗauke da hukuncin lalatarki da na abubuwanki masu banƙyama, ni Ubangiji na faɗa.”

Alkawarin da zai Dawwama

59 “Ni Ubangiji Allah na ce, zan yi miki yadda kika yi, ke da kika yi rantsuwar kafara, kika ta da alkawari. 60 Duk da haka zan tuna da alkawarin da na yi da ke a kwanakin kuruciyarki. Zan ƙulla madawwamin alkawari da ke. 61 Sa'an nan za ki tuna da ayyukanki, ki ji kunya, sa'ad da na ɗauki yarki da ƙanwarki, na ba ki su, su zama 'ya'yanki mata, amma ba a kan alkawarin da na yi da ke ba. 62 Zan ƙulla alkawarina da ke, za ki sani ni ne Ubangiji, 63 domin ki tuna, ki gigice, ki kāsa buɗe bakinki saboda kunya, sa'ad da na gafarta miki dukan abin da kika aikata, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 17

Misalin Gaggafa da Kurangar Inabi

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka faɗa wa mutanen Isra'ila ka-cici-ka-cici, da kuma misali. 3 Ka ce, Ubangiji Allah ya ce, ‘Wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai, da dogayen gasusuwan fikafika da gasusuwa da yawa masu launi iri iri, ta zo Lebanon ta ciri kan itacen al'ul. 4 Ta karya kan tohonsa mafi tsawo, ta kai shi a ƙasar ciniki, ta dasa shi a birnin 'yan kasuwa. 5 Sai kuma ta ɗauki irin na ƙasar, ta dasa shi a wuri mai dausayi kusa da ruwa mai yawa. Ta dasa shi kamar itacen wardi. 6 Ya yi toho, ya zama kuranga mai yaɗuwa. Rassanta suka tanƙwasa wajenta. Saiwoyinta suka kama ƙasa sosai. Haka ta zama kuranga, ta yi rassa da ganyaye. 7 “ ‘Akwai kuma wata babbar gaggafa mai manyan fikafikai da gashi mai yawa. Sai wannan kuranga ta tanƙwasa saiwoyinta zuwa wajenta, ta kuma miƙe rassanta zuwa wajenta tun daga inda aka dasa ta, don gaggafar ta yi mata banruwa. 8 An dasa ta a wuri mai dausayi inda akwai ruwa da yawa don ta yi ganyaye, ta kuma ba da 'ya'ya, ta zama kurangar inabi ta ƙwarai.’ 9 Ka ce, Ubangiji Allah ya ce, ‘Ko wannan kurangar inabi za ta ci gaba? Ashe, gaggafa ta farko ba za ta tumɓuke saiwoyinta, ta sassare rassanta, don ganyayenta da ke tohuwa su bushe ba? Ba sai da hannu mai ƙarfi, ko kuwa da yawan mutane za a tumɓuke ta daga saiwoyinta ba. 10 Idan aka sāke dasa ta kuma za ta yi amfani? Ba za ta bushe sarai sa'ad da iskar gabas ta hura ba? Lalle za ta bushe tun daga inda aka dasa ta ta yi girma.’ ”

Fassarar Misalin

11 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 12 “Ka tambayi mutanen Isra'ila, 'yan tawayen nan cewa, ‘Ba ku san ma'anar waɗannan abubuwa ba?’ Ka faɗa musu, cewa Sarkin Babila ya zo Urushalima, ya tafi da sarkinta da shugabanninta zuwa Babila. 13 Sai ya dauƙi wani daga zuriyar sarauta, ya yi alkawari da shi, ya kuma rantsar da shi. Ya kwashe mutanen ƙasa masu maƙami, 14 don sarautar ƙasar ta raunana, ta kāsa ɗaga kanta, amma ta tsaya dai ta wurin cika alkawarinsa. 15 Amma Sarkin Yahuza ya tayar masa, da ya aiki wakilai zuwa Masar don a ba shi dawakai da sojoji masu yawa. To, zai yi nasara? Wanda ya yi irin wannan abu zai tsira? Zai iya ta da alkawari sa'an nan ya tsere? 16 “Ni Ubangiji Allah, na ce, hakika wannan sarki zai mutu a Babila, domin bai cika rantsuwarsa da alkawarin da ya yi wa Sarkin Babila, wanda ya naɗa shi ba. 17 Fir'auna da yawan sojojinsa masu ƙarfi, ba za su taimake shi da yaƙin ba, sa'ad da Babilawa suka gina mahaurai da kagarai don su kashe mutane da yawa. 18 Bai kuwa cika rantsuwarsa da alkawarinsa ba. Ya ƙulla alkawari, amma ga shi, ya aikata dukan waɗannan abubuwa, ba zai kuɓuta ba. 19 “Domin haka ni Ubangiji Allah, na ce, hakika zan nemi hakkin rantsuwar da ya yi mini, da alkawarin da ya yi mini, waɗanda bai cika ba. 20 Zan kafa masa tarko in kama shi, sa'an nan in kai shi Babila inda zan yi masa shari'a saboda ya tayar mini. 21 Dukan sojojinsa zaɓaɓɓu za a kashe su da takobi, za a watsar da waɗanda suka ragu ko'ina. Za ku sani ni Ubangiji ne na faɗa.”

Alkawarin Sa Zuciya

22 Ga abin da Ubangiji Allah ya ce, “Ni kaina zan cire toho a kan itacen al'ul mai tsawo. Daga cikin sababbin rassansa zan karya lingaɓu, In dasa shi a tsauni mai tsayi. 23 A ƙwanƙolin tsaunin Isra'ila zan dasa shi Don ya fito da rassa, ya ba da 'ya'ya, Ya zama itacen al'ul na gaske. Tsuntsaye iri iri za su zauna a ƙarƙashinsa, Za su yi sheƙuna a cikin inuwar rassansa. 24 Dukan itatuwan jeji za su sani, Ni Ubangiji nakan sa manyan itatuwa su zama ƙanana, In sa ƙanana kuma su zama manya, In sa ɗanyen itace ya bushe, In sa busasshen itace kuma ya zama ɗanye, Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.”

Ezekiyel 18

Hakkin Kowa

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Me kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra'ila cewa, ‘Ubanni sun ci 'ya'yan inabi masu tsami, Hakoran 'ya'ya kuwa sun mutu?’ 3 “Ni Ubangiji Allah na ce, hakika, ba za a ƙara faɗar wannan karin magana a Isra'ila ba. 4 Ga shi, dukan rayuka nawa ne, da ran uban da na ɗan, duka nawa ne. Wanda ya yi zunubi shi zai mutu. 5 “Ga irin mutumin da zai rayu, mutumin da yake adali, yana bin shari'a, yana kuma aikata abin da ke daidai, 6 idan ba ya cin abinci a ɗakin tsafi, bai bauta wa gumakan mutanen Isra'ila ba, bai kwana da matar maƙwabcinsa ba, ba yakan kwana da mace a lokacin hailarta ba, 7 wanda ba ya cin zalin kowa, wanda yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa, wanda ba ya ƙwace, amma yakan ba mayunwanci abinci, wanda yakan ba huntu tufa, 8 wanda ba ya ba da bashi da ruwa, ko tare da wani ƙari, wanda yake hana hannunsa yin mugunta, amma yana goyon bayan gaskiya tsakanin masu gardama, 9 wanda ke bin dokokina, yana kuma kiyaye ka'idodina da aminci, shi adali ne. Hakika zai rayu, ni Ubangiji na faɗa. 10 “Amma idan ya haifi ɗa wanda ya zama ɗan fashi, mai kisankai, yana yi wa ɗan'uwansa ɗaya daga cikin abubuwan nan, (ko shi kansa, 11 bai yi irin waɗannan abubuwa ba), wato yana cin abinci a ɗakin tsafi, yana kwana da matar maƙwabcinsa, 12 yana kuma cin zalin matalauta masu fatara, yana yin ƙwace, ba ya mayar da abin da aka jinginar masa, yana bauta wa gumaka, yana kuma aikata abubuwa masu banƙyama, 13 yana ba da bashi da ruwa da ƙari, wannan ba zai rayu ba, gama ya aikata dukan abubuwan nan masu banƙyama. Zai mutu lalle, alhakin jininsa kuwa yana a kansa. 14 “Amma idan wannan mutum ya haifi ɗa wanda ya ga dukan laifofin da mahaifinsa ya yi, sa'an nan ya ji tsoro, bai kuwa yi haka ba, 15 bai ci abinci a ɗakin tsafi ba, bai bauta wa gumakan mutanen gidan Isra'ila ba, bai kwana da matar maƙwabcinsa ba, 16 bai ci zalin kowa ba, bai karɓi jingina ba, bai yi ƙwace ba, amma yana ba mayunwaci abinci, yana ba huntu tufa, 17 yana hana hannunsa aikata mugunta, bai ba da bashi da ruwa ko wani ƙari ba, yana kiyaye ka'idodina, yana kuma bin dokokina, ba zai mutu saboda laifin mahaifinsa ba, amma zai rayu. 18 Amma mahaifinsa, da ya ke ya yi zalunci, ya yi wa ɗan'uwansa ƙwace ya aikata mugun abu a cikin mutanensa, zai mutu saboda muguntarsa. 19 “Za ku yi tambaya cewa, ‘Me ya sa ɗa ba zai ɗauki hakkin laifin mahaifinsa ba?’ Sa'ad da ɗan ya bi shari'a, ya yi abin da ke daidai, ya kiyaye dokokina sosai, lalle zai rayu. 20 Wanda ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai ɗauki hakkin laifin mahaifinsa ba, mahaifi kuma ba zai ɗauki hakkin laifin ɗansa ba. Adalcin adali nasa ne, muguntar mugu kuma tasa ce.

Ayyukan Allah daidai Ne

21 “Amma idan mugu ya bar dukan muguntarsa da ya aikata, ya kiyaye dokokina, ya bi shari'a, ya yi abin da ke daidai, zai rayu, ba zai mutu ba. 22 Ba za a bi hakkin laifin da ya aikata ba. Zai rayu saboda adalcin da ya yi. 23 Ni Ubangiji Allah, na ce, ina jin daɗin mutuwar mugu ne? Ban fi so ya bar mugun halinsa ya rayu ba? 24 “Amma idan adali ya bar yin adalci, ya aikata mugunta, ya yi abubuwa masu banƙyama waɗanda mugu ke aikatawa, zai rayu? Ayyukansa na adalci waɗanda ya aikata, ba za a tuna da su ba, faufau. Zai mutu saboda rashin amincin da ya yi da laifin da ya aikata. 25 “Amma kum ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ku ji ya ku mutanen Isra'ila, hanyata ba daidai ba ce? Ashe, ba hanyarku ce ba daidai ba? 26 Sa'ad da adali ya bar adalcinsa, ya kuwa aikata mugunta zai mutu saboda muguntarsa. 27 Idan kuma mugu ya bar muguntarsa da yake yi, ya kuwa bi shari'a, ya yi abin da ke daidai, zai rayu. 28 Domin ya yi tunani, ya bar laifofin da ya aikata, zai rayu, ba zai mutu ba. 29 Amma mutanen Isra'ila suna cewa hanyar Ubangiji ba daidai ba ce. Ya mutanen Isra'ila, hanyata ba daidai ba ce? Ashe, ba hanyarku ce ba daidai ba? 30 “Domin haka ni Ubangiji Allah zan hukunta ku, ku mutanen Isra'ila, kowa gwargwadon ayyukansa. Ku tuba, ku bar laifofinku domin kada su zama muku dalilin halaka. 31 Ku rabu da laifofin da kuka yi mini, sa'an nan ku samo wa kanku sabuwar zuciya da sabon hali. Don me za ku mutu, ya ku jama'ar Isra'ila? 32 Ni Ubangiji Allah na ce ba na murna da mutuwar kowa, saboda haka sai ku tuba domin ku rayu.”

Ezekiyel 19

Makoki a kan Hakiman Isra'ila

1 “Sai ka yi makoki domin hakiman Isra'ila, 2 Ka ce, ‘Mahaifiyarka zakanya ce a cikin zakoki, Ta yi zamanta tare da 'yan zakoki, Ta yi renon kwiyakwiyanta. 3 Ta goyi ɗaya daga cikin kwiyakwiyanta, Ya zama sagari, Sai ya koyi kamun nama, ya cinye mutane. 4 Da al'ummai suka ji labarinsa, Sai suka kama shi cikin wushefensu, Suka ja shi da ƙugiyoyi zuwa Masar. 5 Sa'ad da ta ga wanda ta sa zuciya a kansa ya tafi, Sai ta ɗauki ɗaya kuma daga cikin kwiyakwiyanta, Ta goye shi ya zama sagari. 6 Sai ya yi ta kai da kawowa a cikin zakoki, Ya zama sagari, Ya koyi kamun nama, ya cinye mutane. 7 Ya lalatar da kagaransu, Ya mai da biranensu kufai, Ƙasar da waɗanda ke cikinta suka tsorata da jin rurinsa. 8 Sai al'ummai suka kafa masa tarko a kowane waje, Sun kafa masa tarko, Suka kama shi cikin wushefensu. 9 Suka sa masa ƙugiyoyi, sa'an nan suka sa shi cikin suru, Suka kai shi wurin Sarkin Babila. Suka sa shi a kurkuku don kada a ƙara jin rurinsa a kan duwatsun Isra'ila.’ ”

Busasshiyar Kurangar Inabi

10 “ ‘Mahaifiyarka tana kama da kurangar inabi, Wadda aka dasa kusa da ruwa, Ta ba da 'ya'ya da rassa da yawa, saboda isasshen ruwa. 11 Rassanta masu ƙarfi sun zama sandunan masu mulki, Ta yi tsayi zuwa sama duk da rassan, Ana hangenta daga nesa. 12 Amma aka tumɓuke kurangar inabin da fushi, Aka jefar da ita ƙasa. Iskar gabas ta busar da ita, 'Ya'yanta suka kakkaɓe, Rassanta masu ƙarfi sun bushe, wuta kuwa ta cinye su. 13 Yanzu na dasa ta a jeji, cikin busasshiyar ƙasa, 14 Wuta ta fito daga jikinta Ta cinye rassanta da 'ya'yanta, Don haka ba wani reshe mai ƙarfi da ya ragu, wanda zai zama sandan mulki. Wannan makoki ne, ya kuwa tabbata makoki.’ ”

Ezekiyel 20

Yadda Ubangiji ya Bi da Isra'ila

1 A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta bakwai, sai waɗansu dattawan Isra'ila suka zo don su yi roƙo a wurin Ubangiji. Suka zauna a gabana. 2 Ubangiji kuwa ya yi magana da ni ya ce, 3 “Ɗan mutum, ka faɗa wa dattawan Isra'ila cewa, ‘Ni Ubangiji Allah na ce kun zo ku yi roƙo a wurina, amma hakika, ba na roƙuwa a gare ku.’ 4 “Za ka shara'anta su? Ɗan mutum, shara'anta su. To, sai ka sanar da su abubuwa masu banƙyama waɗanda kakanninsu suka yi. 5 Ka ce musu, ni Ubangiji Allah, na ce a ranar da na zaɓi Isra'ila na ta da hannuna, na rantse wa zuriyar Yakubu, na kuma bayyana kaina a gare su a ƙasar Masar, cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, 6 a ran nan na rantse musu, cewa zan fito da su daga ƙasar Masar, zuwa wata ƙasa wadda na samo musu, ƙasar da ke da yalwar albarka, wato ƙasa mai albarka duka. 7 Sai na ce musu, ‘Bari kowane ɗayanku ya yi watsi da abubuwan banƙyama da kuke jin daɗinsu, kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masarawa, gama ni ne Ubangiji Allahnku.’ 8 Amma suka tayar mini, ba su ji ni ba, ba su yi watsi da abubuwan banƙyama da suke jin daɗinsu ba, ba su rabu da gumakan Masarawa ba. Sai na ce zan zubo musu da hasalata, in aukar musu da fushina a ƙasar Masar. 9 Amma saboda sunana ban yi wannan ba, domin kada a saɓi mutanen Isra'ila suke zaune, gama na sanar da kaina ga mutanen Isra'ila, a gaban sauran al'umma kuma, sa'ad da na fito da mutanen Isra'ila, daga ƙasar Masar. 10 “Sai na fisshe su daga ƙasar Masar, na kawo su cikin jeji. 11 Na ba su dokokina da ka'idodina, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu. 12 Na kuma ba su ranar Asabar don ta zama alama tsakanina da su, don kuma su sani ni ne Ubangiji wanda ke tsarkake su. 13 Amma mutanen Isra'ila suka tayar mini a cikin jeji, ba su bi dokokina da ka'idodina ba, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu. Suka ɓata ranar Asabar ƙwarai. Sai na ce zan zubo musu da hasalata, in aukar da fushina a kansu. 14 Amma saboda sunana ban yi wannan ba, domin kada a saɓi sunana a cikin sauran al'umma waɗanda a kan idonsu na fisshe su. 15 Na kuma rantse musu a cikin jeji, cewa ba zan kai su ƙasar da na ba su ba, ƙasar da ke cike da yalwar albarka, wato ƙasar da take mafi albarka duka, 16 domin sun ƙi su bi ka'idodina da dokokina. Suka ɓata ranar Asabar ɗina, gama zuciyarsu ta fi so ta bauta wa gumaka. 17 “Duk da haka na yafe musu, ban hallaka su ba, ban kuma shafe su a jeji ba. 18 Sai na ce wa 'ya'yansu a jeji, ‘Kada ku bi dokokin ubanninku, ko kuwa ku kiyaye ka'idodinsu, kada kuma ku ɓata kanku da gumakansu. 19 Ni ne Ubangiji Allahnku, ku kiyaye dokokina da ka'idodina sosai. 20 Ku kiyaye ranar Asabar ɗina domin ta zama alama tsakanina da ku, domin kuma ku sani ni ne Ubangiji Allahnku.’ 21 “Amma 'ya'yansu suka tayar mini, ba su kiyaye dokokina da ka'idodina ba, waɗanda idan mutum ya kiyaye su, zai rayu. Suka kuma ɓata ranar Asabar ɗina. Sai na yi tunani zan zubo musu da hasalata, in aukar da fushina a kansu a jeji. 22 Amma na yi haƙuri saboda sunana, domin kada a saɓi sunana a gaban sauran al'umma waɗanda suka gani na fito da mutanen Isra'ila daga ƙasar Masar. 23 Na rantse musu a jeji, cewa zan warwatsar da su cikin sauran al'umma, da sauran ƙasashe 24 domin ba su kiyaye ka'idodina da dokokina ba, suka ɓata ranar Asabar ɗina, suka bauta wa gumakan kakanninsu. 25 Sai kuma na ba su dokoki da ka'idodi marasa amfani, waɗanda ba za su rayu ta wurinsu ba. 26 Na kuma bari su ƙazantar da kansu ta wurin hadayunsu, su kuma sa 'ya'yan farinsu su ratsa wuta. Na yi haka don in sa su zama abin ƙyama, don kuma su sani ni ne Ubangiji. 27 “Domin haka, ya ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra'ila ka ce, ‘Ni Ubangiji Allah, na ce kakanninku sun saɓe ni da ba su amince da ni ba. 28 Gama sa'ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su, sa'ad da suka ga kowane tudu da kowane itace mai ganye, sai suka miƙa hadayunsu a wuraren nan suka tsokane ni da hadayunsu. A wuraren ne suka miƙa hadayunsu na turare mai ƙanshi da hadayu na sha.’ 29 Sai na ce, ‘Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’ Domin haka aka kira sunan wurin Bama, wato tudu. 30 Domin haka ka ce wa mutanen Isra'ila, ‘Ni Ubangiji Allah na ce za ku ƙazantar da kanku kamar yadda kakanninku suka yi? Za ku bi abubuwan da suka yi na banƙyama? 31 Sa'ad da kuke miƙa hadaya, kuna miƙa 'ya'yanku hadaya ta ƙonawa, kuna ƙazantar da kanku ta wurin gumakanku har wa yau, to, za ku iya tambayata, ya ku mutanen Isra'ila? Ni Ubangiji Allah ba na tambayuwa gare ku. 32 Tunanin nan da kuke yi a zuciyarku, cewa kuna so ku zama kamar sauran al'umma da kabilan ƙasashe, ku bauta wa itace da dutse, ba zai taɓa faruwa ba.’ 33 “Hakika, ni Ubangiji Allah na ce, zan sarauce ku ƙarfi da yaji, da fushi, 34 da ƙarfi da yaji da fushi kuma, zan fito da ku daga cikin mutane, in tattaro ku daga sauran ƙasashe inda aka warwatsa ku. 35 Zan kawo ku cikin ruƙuƙin jama'a, in yi muku shari'a fuska da fuska. 36 Kamar yadda na yi wa kakanninku shari'a a jejin ƙasar Masar, haka kuma zan yi muku shari'a, ni Ubangiji Allah na faɗa. 37 “Zan sa ku wuce ta ƙarƙashin sanda, in ƙulla alkawarina da ku. 38 Zan fitar da 'yan tawaye a cikinku, da waɗanda suke yin mini laifi. Zan fito da su daga ƙasar da suke zaune, amma ba za su shiga ƙasar Isra'ila ba. Za ku kuwa sani ni ne Ubangiji Allah. 39 “Ya ku, mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah, na ce, bari kowa ya tafi ya bauta wa gunkinsa daga yanzu zuwa gaba, tun da ya ke ba za ku kasa kunne gare ni ba, amma kada ku ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku. 40 “Gama a kan dutsena ne mai tsarki, wato a bisa ƙwanƙolin dutsen Isra'ila, dukan mutanen Isra'ila za su bauta mini a ƙasar, a nan ne zan karɓe su. A nan kuma zan nemi sadake-sada-kenku, da hadayunku mafi kyau. 41 Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa'ad da na fisshe ku daga cikin sauran mutane, na tattaro ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku. Zan nuna tsarkina a cikinku a idon sauran al'umma. 42 Za ku sani ni ne Ubangiji sa'ad da na kawo ku ƙasar Isra'ila, ƙasar da na rantse zan ba kakanninku. 43 A nan za ku tuna da ayyukanku da dukan abubuwa da kuka ɓata kanku da su. Za ku ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwa da kuka aikata. 44 Za ku sani ni ne Ubangiji sa'ad da na yi muku haka saboda sunana, ba saboda mugayen ayyukanku ba, ya ku mutanen Isra'ila. Ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Annabci a kan Kudu

45 Ubangiji ya yi magana da ni ya ce, 46 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen kudu ka ja kunnen mutanen kudu, ka kuma yi annabci gāba da kurmin ƙasar Negeb. 47 Ka ce wa kurmin Negeb, ‘Ka ji maganar Ubangiji, gama Ubangiji Allah ya ce zai kunna wuta a cikinka, za ta kuwa cinye kowane ɗanyen itace, da kowane busasshen itacen da ke cikinka. Ba za a kashe harshen wutar ba. Harshen wutar zai babbake kowace fuska daga kudu zuwa arewa. 48 Dukan masu rai za su sani ni Ubangiji ne na kunna wutar, ba wanda zai kashe ta.’ ” 49 Sai na ce, “Ya Ubangiji Allah, suna cewa misalai kawai, nake yi.”

Ezekiyel 21

Takobin Ubangiji

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ya ɗan mutum, ka fuskanci Urushalima, ka yi magana gāba da masujadanta, ka kuma yi annabci a kan ƙasar Isra'ila. 3 Ka faɗa wa ƙasar Isra'ila, ka ce, ni Ubangiji na ce ina gāba da ita. Zan zare takobina daga cikin kubensa, in karkashe adalai da mugaye daga cikinta. 4 Da ya ke zan karkashe adalai da mugaye daga cikinta, domin haka takobina zai fito daga cikin kubensa, ya karkashe dukan mutane daga Negeb wajen kudu, har zuwa arewa. 5 Dukan mutane kuwa za su sani, ni Ubangiji, na zare takobina daga cikin kubensa, ba kuwa zan sāke mayar da shi a kubensa ba. 6 “Domin haka, ya kai ɗan mutum, sai ka yi nishi, da ajiyar zuciya, da baƙin ciki mai zafi a gabansu. 7 Idan sun tambaye ka, ‘Me ya sa kake nishi?’ Sai ka ce musu, ‘Saboda labarin abin da ke zuwa. Sa'ad da ya zo, kowace zuciya za ta narke, hannuwa duka za su yi suwu, kowane ruhu kuma zai suma, gwiwoyi duka kuwa za su rasa ƙarfi kamar ruwa. Ga shi, abin yana zuwa, zai tabbata,’ ni Ubangiji Allah na faɗa.” 8 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 9 “Ya ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce ni Ubangiji na ce, ‘Takobi, takobi wasasshe, Kuma gogagge! 10 An wasa shi domin kisa, An goge shi don ya yi walwal kamar walƙiya!’ Ba wanda zai iya tsai da shi, domin kun ƙi karɓar shawara. 11 An ba da takobin a goge shi domin a riƙe. An wasa shi, an kuma goge shi domin a ba mai kashewa. 12 Ka yi kuka, ka yi ihu, ya ɗan mutum, gama takobin yana gāba da jama'ata da dukan shugabannin Isra'ila. An ba da shugabanni da jama'ata ga takobi, sai ka buga ƙirjinka da baƙin ciki. 13 Gama ba don jarraba shi ba ne, sai me kuma idan ka raina sandan? Ni Ubangiji na faɗa. 14 “Domin haka, ya kai ɗan mutum, ka yi annabci, ka tafa hannuwanka, ka kaɗa takobi sau biyu, har sau uku. Takobin zai kashe waɗanda za a kashe. Takobi ne na yin kashe-kashe mai yawa. Zai kewaye su. 15 Zai sa zukatansu su narke, da yawa kuma su fāɗi a ƙofofinsu. Na ba da takobi mai walƙiya. An yi shi kamar walƙiya, an wasa shi don kashe-kashe. 16 Ka yi sara dama da hagu, duk inda ka juya. 17 Ni kuma zan tafa hannuwana, zan aukar da fushina, ni Ubangiji na faɗa.”

Takobin Sarkin Babila

18 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 19 “Ya ɗan mutum, ka nuna hanya biyu inda takobin Sarkin Babila zai bi. Dukansu biyu za su fito daga ƙasa ɗaya. Ka kafa shaidar hanya a kan magamin hanya zuwa birni. 20 Ka nuna wa takobin hanya zuwa Rabba ta Ammonawa, da hanya zuwa Yahuza, da Urushalima, birni mai garu. 21 Gama Sarkin Babila yana tsaye a mararrabar hanya, inda hanyar ta rabu biyu, yana yin d�bā, yana girgiza kibau, yana neman shawara wurin kan gida, yana d�bān hanta. 22 A hannun damansa, d�bā yana nuna abin da zai sami Urushalima. Zai kafa mata dundurusai, a yi kururuwar yaƙi, a rurrushe ƙofofinta da dundurusai, a gina mahaurai, a kuma gina hasumiyar yaƙi. 23 Amma a gare su d�bān nan ba gaskiya ba ce, gama sun riga sun yi rantsuwa mai nauyi, amma zai tuna musu da laifinsu, don a kama su. 24 Domin haka ni Ubangiji Allah na ce, tun da ya ke kun sa a tuna da laifofinku, an kuma tone su, laifofinku kuma sun bayyana cikin ayyukanku, kun tonu, to, za a kama ku a cikinsu. 25 “Kai kuma ƙazantaccen mugu, yariman Isra'ila, ranarka ta zo, lokacin hukuncinka ya yi. 26 Ni Ubangiji Allah na ce, ka cire rawaninka, ka ɗauke kambinka. Abubuwa ba za su kasance kamar yadda suke a dā ba. Za a ɗaukaka ƙasƙantacce, amma a ƙasƙantar da maigirma. 27 Halaka, halaka, zan hallakar, ba za a bar ko alama ba, sai mai shi ya zo, shi ne zan ba shi.”

Hukunci a kan Ammonawa

28 “Kai ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce, ga abin da Ubangiji Allah ya ce a kan Ammonawa, da a kan zarginsu. ‘An zare takobi don kashe-kashe, An goge shi don ya yi sheƙi kamar walƙiya! 29 Ka faɗa wa Ammonawa, cewa wahayin da suke gani ƙarya ne annabcin da suke yi kuma ƙarya ne. Su mugaye ne, ranar hukuncinsu tana zuwa. Za a sare wuyansu da takobi. 30 “ ‘Ka mai da takobinka cikin kubensa. Zan hukunta ka a ƙasarka inda aka haife ka. 31 Zan zubo maka da fushina, in hura maka wutar fushina. Zan bashe ka a hannun mugaye, gwanayen hallakarwa. 32 Za ka zama itacen wuta, za a zubar da jininka a tsakiyar ƙasar. Ba za a ƙara tunawa da kai ba, ni Ubangiji na faɗa.’ ”

Ezekiyel 22

Laifofin Urushalima

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Kai ɗan mutum, za ka shara'anta? Za ka shara'anta birni mai kisankai? To, sai ka faɗa masa dukan ayyukansa na banƙyama. 3 Sai ka ce masa, ‘Ni Ubangiji Allah na ce, birnin da ke kisankai, yana kuma bauta wa gumaka don ya ƙazantar da kansa, lokacinsa zai yi! 4 Ka yi laifi saboda ka zubar da jini, ka ƙazantar da kanka da gumakan da ka yi. Saboda haka ka matso da lokacinka kusa, ƙayyadaddun shekarunka sun cika. Domin haka na maishe ka abin zargi ga sauran al'umma, da abin ba'a ga dukan ƙasashe. 5 Waɗanda ke kusa, da waɗanda ke nesa za su yi maka ba'a, gama kai shahararren mugu ne, cike da hargitsi. 6 Ga shi, kowane shugaban Isra'ila da ke cikinka ya himmantu ga zub da jini bisa ga ikonsa. 7 A cikinka ana raina mahaifi da mahaifiya, ana kuma tsananta wa baƙo, ana cin zalin marayu, da gwauruwa, wato wadda mijinta ya mutu. 8 Ka raina tsarkakan abubuwa, ka kuma ɓata ranar Asabar ɗina. 9 Akwai mutane a cikinka waɗanda ke haddasa rikici don su zubar da jini, akwai kuma mutanen da ke cin abinci a matsafai, akwai mutanen da ke aikata lalata. 10 A cikinka, mutane suna kwana da matan mahaifansu, waɗansu suna kwana da mata a lokacin hailarsu. 11 Wani yakan yi lalata da matar maƙwabcinsa, wani kuma ya kwana da matar ɗansa, wani ya kwana da 'yar'uwarsa, wato 'yar mahaifinsa. 12 A cikinka mutane suka karɓi toshi don su zub da jini. Kana ba da rance da ruwa da ƙari, kana kuma cin riba a kan maƙwabcinka saboda cutar da kake yi masa, ka kuwa manta da ni, ni Ubangiji na faɗa. 13 “ ‘Ga shi, na tafa hannuna saboda ƙazamar riba da ka ci, da jinin da ka zubar. 14 Zuciyarka za ta iya ɗaurewa, hannuwanka kuma za su ƙarfafa a ranar da zan gamu da kai? Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata. 15 Zan watsar da kai cikin al'ummai, in warwatsa ka cikin ƙasashe, zan kawo ƙarshen mugayen ayyukanka. 16 Za a ƙasƙantar da kai a gaban sauran al'umma, sa'an nan za ka sani ni ne Ubangiji.’ ”

Tanderun Tsarkakewa

17 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 18 “Ɗan mutum, mutanen Isra'ila sun zama kamar ƙwan maƙera a gare ni. Dukansu sun zama kamar tagulla, da kuza, da baƙin ƙarfe, da darma, a tanderu, sun zama ƙwan maƙera na azurfa. 19 Saboda haka ni Ubangiji Allah na ce da ya ke dukanku kun zama ƙwan maƙera zan tattara dukanku a Urushalima. 20 Kamar yadda mutane sukan tattara azurfa, da tagulla, da baƙin ƙarfe, da darma, da kuza a cikin tanderu, su hura wuta a kansu, don su narkar da su, haka zan tattara ku da zafin fushina in narkar da ku. 21 Zan tattaro ku, in hura muku wutar hasalata, za ku narke a cikinta. 22 Kamar yadda azurfa takan narke a cikin tanderu, haka kuma za ku narke, za ku sani ni, Ubangiji ne, na zubo muku da zafin fushina.”

Laifofin Shugabannin Isra'ila

23 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 24 “Ɗan mutum, ka ce mata, ‘Ke ƙasa ce marar tsarki, wadda ba a yi ruwan sama a kanki ba a lokacin da na yi fushi.’ 25 Annabawanta suna kama da zakoki masu ruri waɗanda suke yayyage ganimar da suka samu. Sun kashe mutane, sun ƙwace dukiya da abubuwa masu daraja. Sun sa mata da yawa sun rasa mazansu. 26 Firistocinta sun karya dokokina, sun ƙazantar da tsarkakan abubuwana. Ba su bambanta tsakanin abin da ke mai tsarki da marar tsarki ba, ba su kuma koyar da bambancin da ke tsakanin halal da haram ba. Ba su kiyaye ranar Asabar ɗina ba, da haka suke saɓon sunana. 27 Shugabanninta sun zama kamar kyarketai masu yayyage ganima. Suna yin kisankai don su sami ƙazamar riba. 28 Annabawanta sun yi musu shafe da farar ƙasa, wato wahayan da suke gani, da duban da suke yi musu ƙarya ne. Suna cewa Ubangiji ne ya faɗa, alhali kuwa ni Ubangiji ban faɗa musu kome ba. 29 Mutanen ƙasar sun yi zalunci, sun yi fashi, sun zalunci matalauta da masu fatara. Ba su yi wa baƙo adalci ba, sai cuta. 30 Sai na nemi mutum a cikinsu wanda zai gina garun ya tsaya a hauren garun a gabana, domin kada in hallaka ƙasar, amma ban sami kowa ba. 31 Saboda haka na kwarara musu fushina, na ƙone su da wutar hasalata, na ɗora alhakin ayyukansu a bisa kawunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 23

'Yan Mata Biyu

1 Sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, akwai waɗansu mata biyu, uwarsu ɗaya. 3 Sun yi karuwanci a Masar, a lokacin 'yan matancinsu, aka rungumi mamansu da ƙirjinsu. 4 Sunan babbar Ohola, sunan ƙanwar kuwa Oholiba. Sun zama nawa, sun haifi 'ya'ya mata da maza. A kan sunayensu kuwa Ohola ita ce Samariya, Oholiba kuwa ita ce Urushalima. 5 Ohola ta yi karuwanci sa'ad da take zamana. Ta yi ta kai da kawowa a tsakanin kwartayenta, Assuriyawa, 6 waɗanda suke saye da shunayya, su masu mulki da manyan sojoji, dukansu samari ne masu bansha'awa, suna bisa kan dawakansu. 7 Ta yi karuwanci da su, dukan waɗanda suke ƙusoshin Assuriya, ta kuma ƙazantar da kanta tsakanin gumakan da ta yi ta kai da kawowa a cikinsu. 8 Ba ta bar karuwancinta ba, wanda ta yi tun tana a Masar, gama a lokacin 'yan matancinta mutane sun kwana da ita, sun rungumi ƙirjinta, suka biya kwaɗayinsu a kanta. 9 Domin haka na bashe ta a hannun kwartayenta, Assuriyawa, waɗanda ta yi ta kai da kawowa a cikinsu. 10 Waɗannan suka tsiraita ta, suka kama 'ya'yanta mata da maza, suka kashe ta da takobi. Sai ta zama abin karin magana a wurin mata sa'ad da aka hukunta ta. 11 “Ƙanwarta kuwa ta ga wannan, amma duk da haka ta fi ta lalacewa saboda kai da kawowa na karuwanci, wanda ya fi na 'yar uwarta muni. 12 Ta yi ta kai da kawowa cikin Assuriyawa, a wurin masu mulki da manyan sojoji waɗanda ke saye da kayan yaƙi, suna bisa kan dawakai, dukansu samari ne masu bansha'awa. 13 Na ga ta ƙazantu. Dukansu biyu suka bi hanya ɗaya. 14 “Amma karuwancinta ya zarce. Ta ga an zāna mutane a jikin bango, siffofin Kaldiyawa ne aka zāna da jan launi! 15 Sun sha ɗamara a gindinsu, da rawuna a kansu suna kaɗawa filfil. Dukansu suna kama da jarumawa. Su siffofi suna kama da mutanen Babila na ƙasar Kaldiya. 16 Sa'ad da ta gan su, sai ta yi ta kai da kawowa a cikinsu. Ta aiki jakadu a wurinsu, wato a Kaldiya. 17 Sai Babilawa suka zo wurinta, a gadonta na nishaɗi, suka ƙazantar da ita ta wurin kwana da ita. Bayan da sun ƙazantar da ita, sai ta ji ƙyamarsu, ta rabu da su. 18 Ta yi ta karuwancinta a fili, ta bayyana tsiraicinta. Sai na ji ƙyamarta, na rabu da ita kamar yadda na rabu da 'yar'uwarta. 19 Duk da haka ta yi ta ƙara karuwancinta, tana tunawa da kwanakin 'yan matancinta, a lokacin da ta yi karuwancinta a ƙasar Masar. 20 Ta yi ta kai da kawowa tsakanin kwartayenta waɗanda al'auransu kamar na jakai ne, maniyyinsu kuwa kamar na dawakai ne. 21 Haka kika yi ƙawar zucin lalatar da kika yi a lokacin 'yan matancinki, sa'ad da Masarawa suka rungumi mamanki na ƙuruciya.”

Hukuncin Allah a kan 'Yan Matan nan Biyu

22 “Domin haka, ya Oholiba, ni, Ubangiji Allah na ce zan kuta kwartayenki su yi gāba da ke, waɗanda kika ji ƙyamarsu, kika rabu da su. Daga kowane sashi zan sa su zo su yi gāba da ke. 23 Babilawa da dukan Kaldiyawa, da Fekod, da Showa, da Kowa, da dukan Assuriyawa tare da su, wato samari masu bansha'awa. Dukansu masu mulki ne, da shugabanni, da jarumawa, da shahararru, dukansu suna kan dawakai. 24 Za su zo daga arewa su yi yaƙi da ke da karusai, da kekunan dawakai, da rundunar mutane. Za su kafa miki sansani a kowace sashi su yi yaƙi da ke da sulke, da garkuwa, da kwalkwali. Zan danƙa shari'a a hannunsu, za su kuwa shara'anta ki da irin shari'arsu. 25 Zan yi fushi da ke don su wulakanta ki. Za su datse hancinki da kunnuwanki. Waɗanda suka rage miki za a kashe su da takobi. Za su kama 'ya'yanki mata da maza, waɗanda suka rage miki kuwa, za a ƙone su da wuta. 26 Za su tsiraita ki, su kuma kwashe lu'ulu'anki. 27 Zan ƙarasa lalatarki da karuwancinki da kika kawo daga ƙasar Masar, don kada ki ƙara ɗaga idonki ki dubi Masarawa, ko ki ƙara tunawa da su. 28 “Gama ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ga shi, zan danƙa ki a hannun waɗanda kike ƙinsu, waɗanda kika ƙi su, kika kuwa rabu da su. 29 Za su nuna miki ƙiyayya, za su ƙwace dukiyarki su bar ki tsirara tik, za su kuma buɗe tsiraicin karuwancinki. 30 Lalatarki da karuwancinki su suka jawo miki wannan, gama kin yi karuwanci da sauran al'umma kika ƙazantar da kanki da gumakansu. 31 Kin bi halin 'yar'uwarki, domin haka zan hukunta ki kamar yadda na hukunta ta.’ ” 32 Ubangiji Allah ya ce, “Za ki sha babban hukuncin da 'yar'uwarki ta sha, Za a yi miki dariya da ba'a, Gama hukuncin yana da tsanani. 33 Za ki sha wahala da baƙin ciki, Hukunci na bantsoro da lalacewa, Shi ne irin hukuncin da aka yi wa 'yarki Samariya. 34 Ƙoƙon da kika sha hukunci daga ciki, za ki lashe shi, Ki tattaune sakainunsa, Ki tsattsage nononki, Ni Ubangiji Allah na faɗa.” 35 Ubangiji ya ce, “Da ya ke kin manta da ni, kin ba ni baya. Don haka ki ɗauki hakkin lalatarki da karuwancinki.” 36 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ko ka shara'anta wa Ohola da Oholiba? To, sai ka faɗa musu mugayen ayyukansu. 37 Gama sun yi zina da kisankai, sun bauta wa gumakansu, har ma sun miƙa musu 'ya'yansu maza da suka haifa mini, su zama abincinsu. 38 Ga kuma abin da suka yi mini, sun ƙazantar da Haikalina a ranar, sun kuma ɓata ranar Asabar ɗina. 39 Gama a ranar da suka kashe 'ya'yansu, suka miƙa su hadaya ga gumakansu, sai suka shiga Haikalina suka ƙazantar da shi. Abin da suka yi ke nan cikin Haidalina. 40 “Kun aiki manzo wurin mutanen da ke nesa su kuwa suka zo. Saboda su kun yi wanka, kun sa kwalli, kun ci ado. 41 Kun zauna a gado mai daraja, da tebur a shirye a gabansa. A kansa kuka ajiye turarena da maina. 42 A wurinta akwai hayaniyar taron mutane marasa kula, sai kuma aka kawo mutane irinsu, mashaya daga jeji. Suka sa mundaye a hannuwan matan, suka kuma sa kambi masu kyau a kawunansu. 43 Sai na yi magana a kanta, ita wadda ta ƙare ƙarfinta da yin zina, yanzu za su yi zina da ita da ta zama haka? 44 Suka shiga wurinta kamar yadda akan shiga wurin karuwa. Haka kuwa suka shiga wurin Ohola da Oholiba don su yi zina da su. 45 Amma adalai za su yanka musu hukunci irin wanda akan yi wa mata mazinata, da mata masu kisankai, gama su mazinata ne masu kisankai. 46 “Gama ni Ubangiji Allah na ce, a kawo rundunar soja ta yi yaƙi da su, don su firgita su, su washe su. 47 Rundunar za ta jajjefe su da duwatsu, ta sassare su da takuba. Za ta kuma kashe 'ya'yansu mata da maza, ta ƙone gidajensu. 48 Ta haka zan kawo ƙarshen lalata a cikin ƙasar domin dukan mata su sami faɗaka, kada su yi lalata kamar yadda kuka yi. 49 Za a hukunta ku saboda lalatarku, za ku sha hukunci saboda zunubin bautar gumaka, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji Allah.”

Ezekiyel 24

Misali a kan Tukunyar da ke Tafasa

1 A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka rubuta sunan wannan rana. Ranar ke nan da Sarkin Babila ya kewaye Urushalima da yaƙi. 3 Ka yi wa 'yan tawayen nan magana da misali, ka faɗa musu cewa, ni Ubangiji na ce, ‘Ka ɗora tukunya, ka ɗora ta a wuta, Ka cika ta da ruwa. 4 Ka zuba gunduwoyin nama a ciki, Dukan gunduwoyi masu kyau, wato cinya da kafaɗa, Ka cika ta da tantakwashi. 5 Ka kama mafi kyau daga cikin garken, Ka sa sauran ƙasusuwa a ƙarƙashinsa, Ka tafasa gunduwoyin, Ka kuma tafasa tantakwashin.’ 6 “Ni Ubangiji Allah na ce, ‘Domin haka kaiton birnin nan mai zubar da jini, Da tukunya wadda ke da tsatsa, Wadda tsatsarta ba ta fita cikinta ba! Ka sa sauran ƙasusuwa a ƙarƙashinsa, Kada ka yi zaɓe. 7 Gama jinin da ta zubar yana tsakiyarta, Ta zubar da shi a kan dutse, Ba ta zubar da shi a ƙasa inda za ta rufe shi da ƙura ba. 8 Don a tsokani fushina har in yi sakayya, Na zuba jinin da ta zubar a kan dutse, Don kada a rufe shi.’ 9 “Saboda haka, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Kaitonka, ya birni, mai zubar da jini! Ni kuma zan tsiba itace da yawa. 10 Ka tula gumagumai, ka kunna wuta, Ka tafasa naman sosai, Ka zuba kayan yaji a ciki, Ka bar ƙasusuwan su ƙone. 11 Ka ɗora tukunyar da ba kome cikinta a bisa garwashi Domin ta yi zafi, tagullarta ta yi ja wur, Domin dauɗarta ta narke a ciki, Tsatsarta kuma ta ƙone. 12 Ta gajiyar da ni a banza, Wutar ba ta fitar da yawan tsatsarta ba. 13 Ya Urushalima, tsatsarki ita ce ƙazantar lalatarki. Da ya ke na tsabtace ki, ba ki tsabtatu ba, To, ba za ki ƙara yin tsabta ba, Har lokacin da na fashe fushina a kanki.’ 14 Ni, Ubangiji na faɗa, zai tabbata gama zan aikata, ba zan fasa ba, ba kuwa zan ƙyale ba, ba kuma zan bari ba. Zan hukunta ki saboda hanyoyinki da ayyukanki, ni Ubangiji Allah na faɗa”

Rasuwar Matar Ezekiyel

15 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 16 “Ya ɗan mutum, ga shi, ina gab da ɗauke maka ƙaunatacciyarka farat ɗaya, amma fa, kada ka yi makoki, ko kuka, ko ka zubar da hawaye. 17 Ka yi ajiyar zuciya a hankali, kada ka yi makoki saboda matacciyar. Ka naɗa rawaninka, ka sa takalmanka, kada ka ja amawali, kada kuma ka ci abincin masu makoki.” 18 Sai na yi magana da mutane da safe, da maraice kuwa matata ta rasu. Kashegari da safe, sai na yi kamar yadda aka umarce ni. 19 Mutane kuwa suka tambaye ni dalilin da ya sa nake yin haka. 20 Sai na ce musu, “Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 21 in faɗa wa mutanen Isra'ila, cewa Ubangiji Allah ya ce, ‘Zan ƙazantar da Haikalina, abin fariyarku, da abin da idanunku suke jin daɗin ganinsa, da abin faranta zuciyarku. 'Ya'yanku maza waɗanda kuka bari a baya, za a kashe su da takobi. 22 Za ku kuwa yi kamar yadda na yi, wato ba za ku ja amawali ba, ba kuwa za ku ci abincin masu makoki ba. 23 Za ku naɗa rawunanku, ku sa takalmanku, ba za ku kuma yi makoki ko kuka ba, amma za ku lalace cikin zunubanku. Za ku yi ta nishi. 24 Da haka Ezekiyel zai zama muku alama. Za ku yi kamar yadda ya yi duka. Sa'ad da wannan ya faru, za ku sani nine Ubangiji Allah.’ 25 “Kai ɗan mutum, a ranar da zan ɗauke musu madogararsu, da murnarsu, da darajarsu, da abin da idanunsu suka ji daɗin gani, da abin da ke faranta zuciyarsu, da 'ya'yansu mata da maza, 26 a wannan rana wanda ya tsere zai kawo maka labarin. 27 A ranar bakinka zai buɗe, za ka yi magana da wanda ya tsere, ba kuma za ka zama bebe ba. Da haka za ka zama alama gare su, za su kuwa sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 25

Annabci a kan Ammonawa

1 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka fuskanci wajen Ammonawa, ka yi annabci a kansu. 3 Ka faɗa musu su ji maganar Ubangiji Allah.” Ubangiji Allah ya ce, “Da ya ke kun ce, ‘Madalla,’ a lokacin da aka ƙazantar da Haikalina, da lokacin da ƙasar Isra'ila ta zama kufai, da lokacin da aka kai mutanen Yahuza bautar talala, 4 domin haka zan bashe ku abin mallaka ga mutanen gabas. Za su kafa alfarwansu a cikinku, su zauna tare da ku. Za su ci amfanin gonakinku, su sha madararku. 5 Zan mai da Rabba makiyayar raƙuma, in mai da biranen Ammonawa garken awaki da tumaki. Sa'an nan ku sani ni ne Ubangiji Allah.” 6 Gama Ubangiji Allah ya ce, “Da ya ke kun tafa hannuwanku, kun buga ƙafafunku, kuka yi murna don nuna dukan ƙiyayyarku da ƙasar Isra'ila, 7 domin haka zan miƙa hannuna gāba da ku, zan bashe ku, ku lalace a ƙasashe, zan hallaka ku. Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji.”

Annabci a kan Mowab

8 Ubangiji Allah ya ce, “Da ya ke Mowab da Seyir sun ce mutanen Yahuza sun zama kamar al'ummai, 9 saboda haka zan buɗe ƙofar shiga Mowab daga garuruwan da ke kan iyaka, waɗanda su ne darajarta, wato Bet-yeshimot, da Ba'al-meyon, da Kiriyatayim. 10 Zan bashe ta duk da Ammonawa su zama abin mallakar mutanen gabas, don kada um'ƙara tunawa da su a cikin al'ummai. 11 Zan hukunta Mowab, sa'an nan za ta sani ni ne Ubangiji.”

Annabci a kan Edom

12 Ubangiji Allah ya ce, “Da ya ke Edom ta ɗaukar wa kanta fansa a kan mutanen Yahuza, ta yi babban laifi da ta ɗaukar wa kanta fansa, 13 domin haka ni Ubangiji Allah zan hukunta Edom. Zan kashe mutanenta da dabbobinta, zan maishe ta kufai. Za a kashe su da takobi, tun daga Teman har zuwa Dedan. 14 Mutanen Isra'la za su ɗaukar mini fansa a kan Edom. Za su aukar da fushina da hasalata a kan Edom, sa'an nan Edom za ta san sakayyata, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Annabci a kan Filistiyawa

15 Ubangiji Allah ya ce, “Tun da ya ke Filistiyawa sun yi sakayya, sun ɗauki fansa da muguwar zuciya da ƙiyayya marar ƙarewa, don su hallakar, 16 domin haka ni Ubangiji Allah zan hukunta Filistiyawa. Zan kashe Keretiyawa, in hallaka sauran mazaunan gāɓar teku. 17 Zan yi musu babbar sakayya da hukunci mai tsanani. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na ɗauki fansa a kansu.”

Ezekiyel 26

Annabci a kan Taya

1 A rana ta fari ga watan, a shekara ta goma sha ɗaya, sai kuma Ubangiji ya yi magana da ni ya ce, 2 “Ɗan mutum, da ya ke Taya ta yi magana a kan Urushalima ta ce, ‘Madalla, Urushalima ta rushe, ƙofa ta buɗu, yanzu zan wadata da yake ta zama kufai,’ 3 domin haka ni, Ubangiji Allah na ce, ‘Ina gāba da ke, ke Taya, zan kawo al'ummai da yawa su yi gāba da ke, kamar yadda teku takan kawo raƙuman ruwa. 4 Za su hallaka garun Taya, su rurrushe hasumiyarta. Zan ƙan'kare ƙasarta, in maishe ta fā. 5 Za ta zama wurin shanya taruna a tsakiyar teku. Za ta kuma zama ganima ga sauran al'umma. Ni Ubangiji na faɗa. 6 Ya'yanta mata waɗanda ke zaune a filin kasar za a kashe su da takobi, sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.’ ” 7 Gama Ubangiji Allah ya ce, “Zan kawo wa Taya Nebukadnezzar, Sarkin Babila, sarkin sarakuna, daga arewa. Zai zo da dawakai da karusai, da sojojin dawakai, da babbar rundunar sojoji. 8 Zai kashe ya'yanki mata waɗanda ke a filin ƙasar da takobi. Zai kuma kewaye ki da garun yaƙi, ya gina miki mahaurai, sa'an nan zai rufe ki da garkuwoyi. 9 Zai rushe garunki da dundurusai, ya rushe hasumiyarki da gatura. 10 Saboda yawan dawakansa, ƙurar da za su tayar za ta rufe ki. Garunki kuma zai girgiza saboda motsin sojojin doki, da na ƙafafu kamar na keke, da na karusai sa'ad da ya shiga ƙofofinki, kamar yadda akan shiga birnin da garunsa ya rushe. 11 Kofatan dawakansa za su tattake dukan titunanki, zai kashe mutanenki da takobi. Manyan ginshiƙanki za su rushe. 12 Za su washe dukiyarki da kayan cinikinki. Za su kuma rurrushe garunki da kyawawan gidajenki. Za su kwashe duwatsu, da katakai, da tarkace, su zubar a cikin teku. 13 Zan sa a daina raira waƙoƙi da kaɗa garayu. 14 Zan maishe ki fā, wato wurin shanya taruna. Ba za a sāke gina ki ba, ni Ubangiji Allah na faɗa.” 15 Ubangiji Allah ya ce wa Taya, “Sa'ad da kika fāɗi, ƙasashen da ke a gāɓar teku za su girgiza saboda amon fāɗuwarki, da nishin waɗanda ake yi wa rauni, da kashe-kashen da aka yi a cikinki. 16 Sa'an nan sarakunan bakin teku za su sauka daga gadajen sarautarsu, su tuɓe rigunansu, da rigunansu waɗanda aka yi wa ado. Za su zauna a ƙasa suna rawar jiki a kowane lokaci. Za su razana saboda abin da ya same ki. 17 Za su yi makoki saboda ke, su ce, ‘Ke wadda ake zaune cikinki, kin bace daga tekuna, Ya shahararren birni, wanda yake babba a bakin teku, Ke da mazaunan da ke cikinki, kun sa mazaunan gāɓar teku su ji tsoro! 18 Yanzu tsibiran za su yi rawar jiki a ranar faɗuwarki. Ji, tsibiran teku za su gigice saboda shuɗewarki.’ ” 19 Gama Ubangiji Allah ya ce, “Sa'ad da na maishe ki kufai kamar biranen da ba a zauna cikinsu ba, sa'ad da kuma na dulmuye ki cikin zurfin teku, 20 sa'an nan zan tura ki tare da waɗanda ke gangarawa zuwa lahira, zuwa wurin mutanen dā. Zan sa ki zauna a ƙarƙashin ƙasa inda ya zama kufai, tare da waɗanda ke gangarawa zuwa lahira, don kada a zauna a cikinki, amma zan ƙawata ƙasar masu rai. 21 Zan sa ki yi mummunan ƙarshe, ba za ki ƙara kasancewa ba. Za a neme ki, amma ba za a same ki ba, ni Ubangiji Allah na faɗa!”

Ezekiyel 27

Makoki a kan Taya

1 Sai kuma Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ya kai ɗan mutum, ka yi makoki domin Taya. 3 Ka ce mata, ita wadda ke zaune a mashigin teku, wadda take kuma kasuwar mutanen da ke bakin teku, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ke Taya, kin ce ke kyakkyawa ce cikakkiya! 4 Teku ta kewaye kan iyakarki, Maginanki sun ƙawata ki. 5 Sun yi katakanki da itacen fir na Senir, Sun sari itacen al'ul daga Lebanon don su yi miki jigon jirgin ruwa. 6 Sun yi matuƙan jirgin ruwanki da katakon itacen oak na Bashan. Sun daɓe jirgin ruwanki da itacen kasharina na bakin tekun Kittim, Sa'an nan sun manne masa hauren giwa. 7 An yi filafilan jirgin ruwanki da lilin mai kyau, mai ado daga Masar, Don ya zama alama. An yi tutar jirgin ruwanki da shuɗi da shunayya na gaɓar tekun Elisha. 8 Mazaunan Sidon da Arwad su ne matuƙa, Masu hikima, waɗanda ke cikinki, su ne jagora. 9 Dattawan Gebal da masu hikimarta suna tare da ke, Suna tattoshe mahaɗan katakon jirginki, Dukan matuƙan jiragen ruwa sun zo wurinki don kasuwanci. 10 “ ‘Mutanen Farisa, da na Lud, da na Fut suna cikin sojojinki don su yi miki yaƙi. Sun rataya garkuwoyi, da kwalkwali a cikinki. Sun samo miki daraja. 11 Mutanen Arward sun kewaye kan garunki. Mutanen Gamad kuma suna tsaron hasumiyarki. Sun rataya garkuwoyinsu a jikin garunki. Sun ƙawata ki ƙwarai. 12 “ ‘Tarshish abokiyar cinikinki ce, saboda yawan dukiyarki ta sayi kayan cinikinki da azurfa, da baƙin ƙarfe, da kuza, da darma. 13 Mutanen Yawan, da na Tubal, da na Meshek, abokan kasuwancinki, sun sayi kayan cinikinki da mutane da tasoshin tagulla. 14 Mutanen Togarma kuma sun sayi kayan cinikinki da dawakai da dawakan yaƙi, da alfadarai. 15 Mutane Dedan abokan cinikinki ne. Kasashe da yawa kuma na gaɓar teku sun zama kasuwarki. Sun biya ki da hauren giwa da katakon kanya. 16 Suriya kuma abokiyar cinikinki ce saboda yawan kayan cinikinki. Sun sayi kayan cinikinki, da zumurrudu, da shunayya, da kayan ado, da lilin mai taushi, da murjani, da yakutu. 17 Mutanen Yahuza da na ƙasar Isra'ila abokan cinikinki ne. Sun sayi kayan cinikinki da alkama, da zaitun, da 'ya'yan ɓaure, da zuma, da mai, da ganyaye masu ƙanshi. 18 Dimashƙu kuma ta zama abokiyar cinikinki saboda yawan kayan cinikinki da yawan dukiyarki. Ta sayi kayanki da ruwan inabin Helbon, da farin ulu. 19 Mutanen Dan, da Yawan, da ulu suka sayi kayanki, wato gyararren ƙarfe da kayan yaji. 20 Dedan ta sayi kayanki da kayan dawakai. 21 Mutanen Arabiya da shugabannin Kedar sun sayi kayanki da 'yan raguna, da raguna, da awaki. 22 'Yan kasuwar Sheba da Ra'ama sun sayi kayanki da kayan yaji mafi kyau iri iri, da duwatsu masu daraja iri iri, da zinariya. 23 Garuruwan Haran, da Kanne, da Aidan, da fataken Sheba, da Asshur, da Kilmad sun yi ciniki da ke. 24 Sun sayar miki da tufafi masu tsada, da na shuɗi, da masu ado, da darduma masu ƙyalƙyali da kirtani, da igiyoyi waɗanda aka tufka da kyau. 25 Jiragen ruwan Tarshish suna jigilar kayan cinikinki. Don haka kin bunƙasa, Kin ɗaukaka a tsakiyar tekuna. 26 “ ‘Matuƙanki sun kai ki cikin babbar teku, Iskar gabas ta farfasa ki a tsakiyar teku. 27 Dukiyarki, da kayan cinikinki, da hajarki, Da ma'aikatanki da masu ja miki gora, Da masu tattoshe mahaɗan katakanki, Da abokan cinikinki, da dukan sojojinki, Da dukan taron jama'ar da ke tare da ke, Sun dulmuya cikin tsakiyar teku a ranar halakarki. 28 Saboda kukan masu ja miki gora, ƙasa ta girgiza. 29 “ ‘Daga cikin jiragen ruwansu dukan waɗanda suke riƙe da matuƙi za su zo. Matuƙan jiragen ruwa da masu jagora za su tsaya a gaɓar teku. 30 Za su yi kuka mai zafi dominki. Za su yi hurwa, su yi birgima cikin toka. 31 Za su aske kansu saboda ke, su sa tufafin makoki. Za su yi kuka mai zafi dominki. 32 A cikin makokinsu dominki, suna kuka, suna cewa, Wa ke kama da Taya, Ita wadda ke shiru a tsakiyar teku? 33 Sa'ad da kayan cinikinki suka tafi ƙasashen hayi, Kin wadatar da al'ummai, Kin arzuta sarakunan duniya da yawan dukiyarki da hajarki. 34 Yanzu teku ta farfashe ki cikin zurfafa, Hajarki da dukan ma'aikatan jirgin ruwanki sun nutse tare da ke. 35 Dukan mazaunan ƙasashen gāɓar teku Sun gigice saboda masifar da ta auko miki. Dukan sarakunansu sun tsorata ƙwarai, Fuskokinsu sun yamutse. 36 'Yan kasuwa a cikin al'ummai suna yi miki ba'a, Saboda kin zama musu barazana. Ba za ki ƙara kasancewa ba har abada.’ ”

Ezekiyel 28

Annabci a kan Sarkin Taya

1 Ubangiji ya yi magana da ni ya ce, 2 “Dan mutum, ka faɗa wa Sarkin Taya, cewa Ubangiji Allah ya ce, ‘Da ya ke zuciyarka ta cika da alfarma, Har ka ce kai allah ne, Kana zaune a mazaunin allah, kana zaune a tsakiyar tekuna, To, kai mutum ne kawai, ba allah ba, Ko da ya ke ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah. 3 Lalle ka fi Daniyel hikima, Ba asirin da ke ɓoye a gare ka. 4 Ta wurin hikimarka da ganewarka ka samo wa kanka dukiya, Ka tattara zinariya da azurfa a baitulmalinka. 5 Saboda yawan hikimarka na yin kasuwanci, ka ƙara dukiyarka, Sai dukiyarka ta sa zuciyarka ta cika da alfarma.’ 6 “Saboda haka Ubangiji Allah ya ce, ‘Da ya ke ka aza kanka mai hikima ne kamar Allah, 7 Don haka zan tura baƙi a kanka, Waɗanda suka fi mugunta cikin sauran al'umma. Za su zare takubansu a kan kyakkyawar hikimarka, Za su ɓara darajarka. 8 Za su jefar da kai cikin rami, Za ka mutu kamar waɗanda suka mutu a tsakiyar teku. 9 Har yanzu za ka ce kai allah ne a gaban waɗanda suke ji maka rauni, Ko da ya ke kai mutum ne kawai, ba Allah ba? 10 Za ka yi mutuwa irin ta kare ta hannun baƙi, Gama ni Ubangiji Allah na faɗa.’ ”

Makoki a kan Sarkin Taya

11 Ubangiji kuma ya yi magana da ni ya ce, 12 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Sarkin Taya, ka ce Ubangiji Allah ya ce, ‘Kai cikakke ne, cike da hikima da jamali! 13 Kana cikin Aidan, gonar Allah. An yi maka sutura da kowane irin dutse mai daraja, Tare da zinariya. Kana da molo da abin busa. A ranar da aka halicce ka Suna nan cikakku. 14 Na keɓe ka ka zama mala'ika mai tsaro, Kana bisa tsattsarkan dutsen Allah, Ka yi tafiya a tsakiyar duwatsu na wuta. 15 Daga ranar da aka halicce ka ba ka da laifi cikin al'amuranka, Sai ran da aka iske mugunta a cikinka. 16 A wurin yawan kasuwancinka, Ka yi rikici da yawa har ka yi zunubi. Don haka na jefar da kai daga dutsen Allah Kamar ƙazantaccen abu. Na hallaka ka daga tsakiyar duwatsu na wuta, Kai mala'ikan tsaro. 17 Zuciyarka ta yi alfarma saboda kyanka, Ka lalatar da hikimarka ta wurin nuna darajar kanka. Na jefar da kai zuwa ƙasa, Na tone asirinka a gaban sarakuna don su kallace ka. 18 Saboda yawan muguntarka da rashin gaskiyarka cikin kasuwanci, Ka ƙazantar da tsarkakakkun wurarenka. Don haka na sa wuta ta fito daga cikinka, ta cinye ka, Na maishe ka toka a bisa ƙasa a kan idon dukan waɗanda suka kallace ka. 19 Dukan waɗanda suka san ka a cikin al'ummai Za su gigice saboda masifar da ta auko maka, Za ka zama barazana ga al'ummai, Ba za ka ƙara kasancewa ba har abada.’ ”

Annabci a kan Sidon

20 Ubangiji ya yi magana da ni kuma, ya ce, 21 “Ɗan mutum, ka fuskanci Sidon, ka yi annabci a kanta. 22 Ka ce, Ubangiji Allah ya ce, ‘Duba, ina gāba da ke, ya Sidon, Zan bayyana ikona a cikinki, Za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na hukunta ta, Na bayyana tsarkina a cikinta. 23 Zan aukar mata da annoba da jini a titunanta. Waɗanda za a ji musu rauni da takobi Za su fāɗi matattu a tsakiyarta. Za a tasar mata a kowane waje. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.’ ”

Isra'ila za ta Sami Albarka

24 “ ‘A kan mutanen Isra'ila kuwa, al'ummai da ke kewaye da su, waɗanda suka raina su, ba za su ƙara zamar musu kamar sarƙaƙƙiya da ƙaya ba. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allah.’ 25 “Ubangiji Allah ya ce, ‘Sa'ad da na tattara mutanen Isra'ila daga cikin sauran al'umma, inda na watsar da su, na kuma bayyana tsarkina a cikinsu a kan idon al'ummai, sa'an nan za su zauna a ƙarsarsu wadda na ba bawana Yakubu. 26 Za su zauna lafiya a cikinta, za su gina gidaje, su yi gonakin inabi. Za su zauna gonakin inabi. Za su zauna lafiya sa'ad da na hukunta maƙwabtansu waɗanda suka wulakanta su. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu.’ ”

Ezekiyel 29

Annabci a kan Masar

1 A kan rana ta goma sha biyu ga watan goma a shekara ta goma, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Fir'auna Sarkin Masar, ka yi annabci gāba da shi da dukan Masar. 3 Ka yi magana, ka ce, Ubangiji Allah ya ce, ‘Ga shi, ina gāba da kai, kai Fir'auna Sarkin Masar, Babban mugun dabba wanda ke kwance a tsakiyar koguna, Wanda ke cewa, Kogin Nilu naka ne, kai ka yi shi. 4 Zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka, In kuma sa kifayen kogunanka su manne a ƙamborinka, Zan jawo ka daga cikin tsakiyar kogunanka, Da dukan kifayen kogunanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka, 5 Zan yashe ka, kai da dukan kifayen kogunanka cikin jeji. Za ka fāɗi a fili, ba kuwa wanda zai ɗauke ka, ya binne ka. Zan sa ka zama abincin namomin jeji da tsuntsayen sararin sama. 6 A sa'an nan mazaunan Masar za su sani ni ne Ubangiji, Domin sun zama wa mutanen Isra'ila kamar sandan iwa. 7 Sa'ad da suka riƙe ka, Sai ka karye ka tsattsaga hannuwansu. Sa'ad da suka jingina da kai, Sai ka karye, har ka sa kwankwasonsu ya firgiza. 8 Saboda haka, ni Ubangiji Allah na ce zan jawo takobi a kanka, in kashe mutanenka, duk da dabbobi. 9 Ƙasar Masar za ta zama kufai, marar amfani. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji. “ ‘Domin ka ce, “Kogin Nilu nawa ne, ni na yi shi,” 10 ina gāba da kai da kogunanka. Zan mai da ƙasar Masar kufai sosai, marar amfani, tun daga Migdol zuwa Sewene har zuwa iyakar Habasha. 11 Mutum ko dabba ba zai ratsa ta cikinta ba. Za ta zama kufai har shekara arba'in. 12 Zan mai da ƙasar Masar kufai fiye da sauran ƙasashe. Biranenta za su zama kufai marar amfani, fiye da sauran birane har shekara arba'in. Zan kuma warwatsar da Masarawa a cikin sauran al'umma.’ ” 13 Ubangiji Allah ya ce, “Bayan shekara arba'in zan tattaro Masarawa daga cikin sauran al'umma inda aka warwatsar da su. 14 Zan komo da Masarawa, in maido su a ƙasar Fatros, ƙasarsu ta ainihi. Za su zama mulki marar ƙarfi. 15 Za su zama rarraunan mulki a cikin mulkoki. Ba za su ƙara ɗagawa sauran al'umma kai ba. Zan sa su zama kaɗan, har da ba za su ƙara mallakar waɗansu al'ummai ba. 16 Ba za su ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra'ila ba, gama Isra'ilawa za su tuna da laifin suka yi, suka nemi taimakon Masarawa. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allah.” 17 A kan rana ta fari ga watan fari a shekara ta ashirin da bakwai, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 18 “Ɗan mutum, Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya sa sojojinsa su matsa wa Taya. Kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta yi kanta, amma duk da haka shi, tare da sojojinsa, bai sami hakkin wahalar da ya sha a Taya ba.” 19 Domin haka Ubangiji Allah ya ce, “Zan ba Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ƙasar Masar, zai kwashe dukiyarta, ya lalatar da ita, ya washe ta ganima. Za ta zama abin biyan sojojinsa. 20 Na ba shi ƙasar Masar saboda wahalar da ya sha, gama ni suka yi wa aiki. Ni Ubangiji Allah na faɗa. 21 “A ranan nan zan naɗa ɗaya daga cikin zuriyar Dawuda ya zama babban sarki, zan kuma buɗe bakinka a tsakiyarsu. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 30

Lalacewar Masar

1 Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka yi annabci, ka ce Ubangiji Allah ya ce maka ka yi kuka, kana cewa, ‘Kaito, kaito saboda wannan rana!’ 3 Gama ranar ta gabato, Ranar Ubangiji ta yi kusa, Rana ce ta gizagizai, Ranar halakar al'ummai. 4 Takobi zai fāɗa a kan Masar, Azaba kuma za ta sami Habasha. Za a kashe mutane a Masar, Za a kwashe dukiyarta, A rushe harsashin gininta. 5 “Yaƙi zai ci Habasha, da Fut, da Lud, da dukan Arabiya, da Libya, da mutanen ƙasar da suka haɗa kai da su.” 6 Ubangiji ya ce, “Waɗanda ke goyon bayan Masar za su fāɗi. Ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare. Za a kashe su da takobi tun daga Migdol zuwa Sewene. 7 Za ta zama kufai fiye da sauran ƙasashe, Biranenta kuma za su zama kufai, marar amfani, fiye da sauran birane. 8 Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, Sa'ad da na kunna wuta cikin Masar, Na kuma kakkarya dukan masu taimakonta. 9 “A ranan nan manzanni masu sauri za su fito daga wurina a jiragen ruwa, su tsoratar da Habashawa, ba zato. Azaba za ta auko a kansu a ranar hallakar Masar. Ga ta nan, ta zo.” 10 Ubangiji Allah ya ce, “Zan sa dukiyar Masar ta ƙare Ta hannun Nebukadnezzar, Sarkin Babila, 11 Shi da mutanensa, Mutane mafi bantsoro a cikin sauran al'umma, Za a kawo su don su hallakar da ƙasar. Za su zare takubansu a kan Masar, Su cika ƙasar da gawawwaki. 12 Zan busar da Kogin Nilu, Zan kuma sayar da ƙasar ga mugaye. Zan sa ƙasar ta lalace Da dukan abin da ke cikinta, Ta hannun baƙi, Ni Ubangiji, na faɗa.” 13 Ubangiji Allah ya ce, “Zan hallakar da gumaka Da siffofi a Memfis. Ba za a ƙara samun hakimi a ƙasar Masar ba, Saboda haka zan aukar da tsoro a ƙasar Masar. 14 Zan sa Fatros ta zama kufai, Zan kunna wa Zowan wuta, Zan kuma shara'anta No. 15 Zan kwarara hasalata a kan Felusiyum, Wato kagarar Masar, Zan datse jama'ar No. 16 Zan kunna wa Masar wuta. Felusiyum za ta sha azaba mai tsanani, No kuwa za a tayar mata da hankali, Za a rurrushe garukanta. Za a tasar wa Memfis dukan yini. 17 Samarin Awen da na Fi-beset Za a kashe su da takobi, Matan kuma za su tafi bauta. 18 A Tafanes rana za ta yi duhu, Sa'ad da na karya mulkin ƙasar Masar, Ƙarfinta da take fariya da shi zai ƙare, Za a rufe ta da gizagizai. 'Ya'yanta mata kuwa za a kai su bauta. 19 Ta haka zan hukunta Masar, Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.” 20 A kan rana ta bakwai ga watan fari, a shekara ta goma sha ɗaya, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 21 “Ɗan mutum, na karya hannun Fir'auna, Sarkin Masar, ga shi, ba za a ɗora hannun ba, don kada ya warke ya zama da ƙarfi yadda zai iya riƙon takobi.” 22 Ubangiji Allah kuma ya ce, “Ina gāba da Fir'auna, Sarkin Masar, zan karya hannuwansa duka biyu, da lafiyayyen da kuma wanda na riga na karya. Zan sa takobinsa ya faɗi daga hannunsa. 23 Zan watsar da Masarawa a cikin sauran al'umma, in kuma warwatsa su a ƙasashen duniya. 24 Zan ƙarfafa hannun Sarkin Babila, in sa takobina a hannunsa, amma zan karya hannuwan Fir'auna, zai yi nishi a gaban Sarkin Babila, kamar mutumin da aka yi wa raunin ajali. 25 Zan ƙarfafa hannuwan Sarkin Babila, amma hannuwan Fir'auna za su shanye. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na sa takobina a hannun Sarkin Babila, shi kuwa zai miƙe shi a kan ƙasar Masar. 26 Zan watsar da Masarawa a cikin sauran al'umma, in warwatsa su a ƙasashen duniya. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 31

Ƙaddarar da za ta Sami Fir'auna da Jama'arsa

1 A kan rana ta fari ga watan uku a shekara ta goma sha ɗaya, Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka ce wa Fir'auna, Sarkin Masar, da jama'arsa. ‘Da wa za a kamanta girmanka? 3 Kana kama da Assuriya mai kama da itacen al'ul a Lebanon, Mai rassa masu kyau da inuwar kurmi, Mai tsayi ainun, kansa ya kai cikin gizagizai. 4 Ruwa ya sa ya yi girma, Danshi ya sa ya yi tsayi. Koguna sun gudu kewaye da wurin da aka shuka shi. Yana aikar da rafuffukansa zuwa dukan itatuwan kurmi. 5 Sai ya yi tsayi fiye da dukan itatuwan da ke a kurmi, Rassansa suka yi kauri, suka kuma yi tsayi, Saboda isasshen ruwa a lokacin tohonsa. 6 Dukan tsuntsayen sararin sama sun yi sheƙunansu a rassansa, Namomin jeji kuma suka haifi 'ya'yansu ƙarƙashin rassansa. Dukan al'ummai suka zauna ƙarƙashin inuwarsa. 7 Girmansa yana da kyau, haka kuma dogayen rassansa, Gama saiwoyinsa sun nutse can ƙasa har cikin ruwa. 8 Ko itatuwan al'ul da ke cikin gonar Allah, ba su kai kyansa ba. Itatuwan kasharina kuma ba du kai rassansa ba. Itatuwan durumi kuma ba su kai rassansa ba. Ba wani itace a gonar Allah wanda ya kai kyansa. 9 Na sa shi ya yi kyau, ga kuma rassansa da yawa. Dukan itatuwan Aidan, waɗanda ke cikin gonar Allah sun yi ta jin ƙyashinsa.’ ” 10 Domin haka Ubangiji Allah ya ce, “Saboda ya yi tsayi, kansa kuma ya kai cikin gizagizai, zuciyarsa kuwa ta yi fariya saboda tsayinsa, 11 zan bashe shi a hannun mai ƙarfi, a cikin al'ummai. Zai sāka masa gwargwadon muguntarsa. Na fitar da shi. 12 Baƙi mafi bantsoro daga cikin al'ummai sun sare shi, sun bar shi. Rassansa sun faɗi a kan duwatsun da ke cikin dukan kwaruruka, rassansa kuma sun kakkarye, sun faɗi a cikin dukan magudanan ruwa na ƙasa. Dukan mutanen duniya sun tashi daga inuwarsa, sun bar shi. 13 Dukan tsuntsayen sararin sama za su zauna a gorarsa. Namomin jeji kuma za su yi ta yawo a cikin rassansa. 14 An yi wannan domin kada itatuwan da ke bakin ruwa su yi girma, su yi tsayi da yawa har kawunansu su kai cikin gizagizai, domin kuma kada itacen da ke shan ruwa ya yi tsayi kamarsa, gama an bashe su ga mutuwa zuwa lahira, tare da 'yan adam masu gangarawa zuwa cikin kabari.” 15 Ubangiji Allah ya ce, “A ranar da ya gangara zuwa lahira, na sa zurfi ya rufe shi, ya yi makoki dominsa. Na tsai da kogunansa, yawan ruwansa ya ƙafe. Na sa Lebanon ta yi duhu saboda shi. Dukan itatuwan jeji kuwa sun yi yaushi saboda shi. 16 Al'ummai suka yi rawar jiki saboda amon faɗuwarsa, sa'ad da na jefar da shi cikin lahira tare da waɗanda suke gangarawa zuwa cikin kabari. Dukan itatuwan Aidan da itatuwa mafi kyau na Lebanon waɗanda suka ƙoshi da ruwa, sun ta'azantu a lahira. 17 Su kuma suka gangara tare da shi zuwa lahira, suka tarar da waɗanda aka kashe da takobi, wato waɗanda daga cikin al'ummai suka yi zama a inuwarsa. 18 “A cikin itatuwan Aidan, da wa za a kamanta darajarka da girmanka? Duk da haka za a kai ka lahira tare da itatuwan Aidan. Za ka zauna tare da marasa kaciya, da waɗanda aka kashe da takobi. Wannan Fir'auna ke nan, da dukan jama'arsa, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 32

Makoki saboda Fir'auna

1 A kan rana ta fari, ga watan goma sha biyu, a shekara ta goma sha biyu, sai Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka yi makoki a kan Fir'auna, Sarkin Masar, ka ce, ‘Ka aza kanka kamar zaki a cikin al'ummai, Amma kai kada ne a cikin ruwa. Ka ɓullo cikin kogunanka, Ka gurɓata ruwa da ƙafafunka, Ka ƙazantar da kogunansu.’ 3 Ubangiji Allah ya ce, ‘Zan jefa taruna a kanka, a babban taron mutane, Zan jawo ka cikin taruna. 4 Zan jefar da kai a tudu, A fili zan jefa ka. Zan sa tsuntsayen sararin sama su ɗira a kanka, Zan ƙosar da namomin jeji na dukan duniya da namanka. 5 Zan watsa namanka a kan duwatsu, In cika kwaruruka da gawarka. 6 Zan watsar da jininka a ƙasa da tuddai, Magudanan ruwa za su cika da jininka. 7 Sa'ad da na shafe ka, zan rufe sammai, In sa taurarinsu su duhunta, Zan sa girgije ya rufe rana, Wata kuma ba zai haskaka ba. 8 Dukan haskokin sama zan sa su zama duhu a gare ka, In sa ƙasarka ta duhunta, ni Ubangiji Allah na faɗa.’ 9 “Zukatan al'ummai da yawa za su ɓaci, sa'ad da na baza labarin halakarka a ƙasashen da ba ka sani ba. 10 Al'ummai da yawa za su gigice saboda abin da zai same ka, sarakunansu kuma za su yi rawar jiki saboda kai sa'ad da na kaɗa takobi a gabansu. A ranar faɗuwarka za su yi rawar jiki a kowane lokaci, kowa saboda ransa.” 11 Ubangiji Allah ya ce, “Takobin Sarkin Babila zai auko maka. 12 Zan sa ƙarfafan mutane masu bantsoro daga cikin al'ummai su kashe jama'arka da takuba. Za su wofinta girmankan Masar, Su kuma hallaka jama'arta. 13 Zan hallaka dukan dabbobinta da ke bakin ruwa, Ba ƙafar mutum ko ta dabba da za ta ƙara gurɓata ruwa. 14 Zan sa ruwansu ya yi garau, In sa kogunansu su malala kamar mai, Ni Ubangiji Allah na faɗa. 15 Sa'ad da na mai da ƙasar Masar kufai, In raba ƙasar da abin da take cike da shi, Sa'ad da na bugi dukan waɗanda ke cikinta, Daganan za su sani ni ne Ubangiji. 16 Wannan ita ce waƙar makokin. 'Yan matan al'ummai za su raira wa Masar da jama'arta duka, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Lahira

17 A rana ta goma sha biyar ga wata na fari, a shekara ta goma sha biyu, Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 18 “Ɗan mutum, ka yi kuka saboda jama'ar Masar. Ka tura su tare da sauran al'umma zuwa lahira wurin waɗanda suka gangara zuwa cikin kabari. 19 Ka ce, ‘Su wa kika fi kyau? Ki gangara, ki kwanta tare da marasa imani.’ 20 “An zare takobi don a kashe jama'ar Masar. Za su fāɗi a tsakiyar waɗanda aka kashe da takobi. 21 Manyan jarumawa daga lahira za su yi magana a kansu da mataimakansu, su ce, ‘Marasa imani waɗanda aka kashe da takobi, sun gangaro, ga su nan kwance shiru!’ 22 “Assuriya tana can da dukan taron jama'arta. Kaburburansu suna kewaye da ita. An kashe dukansu da takobi. 23 An binne su a can ƙurewar lahira. Taron jama'arta suna kewaye da kabarinta. An kashe dukansu da takobi. Su ne suka haddasa tsoro a cikin ƙasar. 24 “Elam tana can da dukan jama'arta kewaye da kabarinta. An kashe dukansu da takobi. Sun gangara da rashin imaninsu zuwa lahira. Su ne suka haddasa tsoro a duniya. Sun sha kunyarsu tare da waɗanda suka gangara zuwa kabari. 25 An shirya mata gado tare da matattu. Kaburburan dukan sojojinta suna kewaye. Dukansu marasa imani ne, waɗanda aka kashe da takobi, amma a dā sun yaɗa tsoro a duniya. Yanzu kuwa suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa kabari. An tara su tare da waɗanda aka kashe. 26 “Meshek da Tubal suna can da dukan sojojinsu. Kaburburan sojojinsu suna kewaye. Dukansu marasa imani ne, waɗanda aka kashe da takobi, gama sun yaɗa tsoro a duniya. 27 Ba su kwanta kusa da manyan jarumawan da aka kashe ba, waɗanda suka tafi lahira da makamansu, aka yi musu matasan kai da takubansu, aka rufe ƙasusuwansu da garkuwoyinsu, gama manyan jarumawan nan sun baza tsoro a duniya. 28 Amma za a karya ku, ku kwanta tare da marasa imani, tare da waɗanda aka kashe da takobi. 29 “Edom kuma tana can tare da sarakunanta da dukan shugabanninta masu iko, Suna kwance tare da waɗanda aka kashe da takobi, marasa imani, masu gangarawa zuwa cikin kabari. 30 “Dukan shugabannin arewa suna can, da dukan Sidoniyawa. Da kunya, suna gangarawa tare da waɗanda aka kashe, ko da ya ke a dā sun haddasa tsoro saboda ikonsu. Yanzu suna kwance tare da marasa imani waɗanda aka kashe da takobi. Suna shan kunya tare da waɗanda suka gangara zuwa cikin kabari. 31 “Sa'ad da Fir'auna zai gan su, zai ta'azantu a kan rundunarsa da aka kashe da takobi. Lalle Fir'auna da dukan rundunarsa za su ta'azantu. Ni Ubangiji Allah na faɗa. 32 “Ko da ya ke na sa Fir'auna ya haddasa tsoro a duniya, duk da haka zan sa a kashe shi tare da rundunarsa. Za su kwanta tare da marasa imani waɗanda aka kashe da takobi. Ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 33

Wajibin Mai Tsaro

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka yi magana da mutanenka, ka faɗa musu cewa, ‘Idan na zare takobi a kan wata ƙasa, idan mutanen ƙasar suka ɗauki wani mutum daga cikinsu, suka sa shi ya zama ɗan tsaronsu, 3 idan ya ga an taso wa ƙasar da takobi, sai ya busa ƙaho don ya faɗakar da jama'ar. 4 Idan wani ya ji amon ƙahon, amma bai kula ba, har takobin ya zo ya kashe shi, hakkin jininsa yana bisa kansa. 5 Gama ya ji amon ƙahon, bai kuwa kula ba, hakkin jininsa zai zauna a bisa kansa. Amma idan ya kula da faɗakar, zai tsira da ransa. 6 Idan kuwa ɗan tsaron ya ga takobi yana zuwa, amma bai busa ƙahon don ya faɗakar da mutanen ba, takobin kuwa ya zo, ya kashe wani daga cikinsu, shi wanda aka kashe ya mutu saboda laifinsa, amma zan nemi hakkin jininsa daga hannun ɗan tsaron.’ 7 “Yanzu fa, kai ɗan mutum, na sa ka zama ɗan tsaro a al'ummar Isra'ila. Duk lokacin da ka ji magana daga bakina, sai ka faɗakar da su. 8 Idan na hurta, cewa hakika mugu zai mutu, amma ba ka faɗakar da shi don ya juyo, ya bar muguwar hanyarsa ba, wannan mugun zai mutu saboda laifinsa, amma zan nemi hakkin jininsa a hannunka. 9 Amma idan ka faɗakar da mugu don ya juyo, ya bar muguwar hanyarsa, idan bai juyo ya bar muguwar hanyarsa ba, zai mutu saboda laifinsa, amma za ka tsira da ranka.

Ayyukan Allah daidai Ne

10 “Kai ɗan mutum, sai ka faɗa wa mutanen Isra'ila, ‘Kuna cewa, “Laifofinmu da zunubanmu suna nawaita mana, muna kuwa lalacewa, yanzu fa, ta ƙaƙa za mu rayu?” ’ 11 Ka faɗa musu, ni Ubangiji Allah, na ce, ‘Hakika, ba na murna da mutuwar mugu, amma na fi so mugun ya bar hanyarsa ya rayu. Ku juyo, ku juyo daga mugayen hanyoyinku, gama don me za ku mutu, ya mutanen Isra'ila?’ 12 “Ɗan mutum, sai kuma ka faɗa wa mutanenka, cewa adalcin adali ba zai cece shi ba sa'ad da ya yi laifi, muguntar mugu kuma ba za ta sa ya mutu ba idan ya bar muguntarsa. Adalcin adali ba zai cece shi ba, idan ya shiga aikata zunubi. 13 Idan na ce wa adali, ba shakka zai rayu, amma idan ya dogara ga adalcin da ya riga ya yi, sa'an nan ya shiga aikata laifi, ba za a tuna da ayyukan adalcinsa na dā ba. Zai mutu saboda laifin da ya yi. 14 Idan kuma na ce wa mugu ba shakka zai mutu, amma idan ya bar laifinsa, ya shiga aikata adalci, 15 idan kuma ya mayar da jingina, ya mayar da abin da ya ƙwace, sa'an nan ya kiyaye dokokin rai, ya daina yin laifi, hakika, zai rayu, ba zai mutu ba. 16 Ba za a tuna da laifofin da ya aikata a dā ba, gama ya aikata adalci da gaskiya, zai rayu. 17 “Amma mutanenka sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce,’ alhali kuwa tasu ce ba daidai ba. 18 Sa'ad da adali ya daina aikata adalci, ya shiga aikata laifi, zai mutu saboda laifinsa. 19 Sa'ad da kuma mugu ya daina aikata mugunta, ya shiga aikata adalci da gaskiya, zai rayu saboda adalcinsa. 20 Amma duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ya mutanen Isra'ila, zan hukunta kowane ɗayanku gwargwadon ayyukansa.”

Labarin Faɗuwar Urushalima

21 A rana ta biyar ga watan goma, a shekara ta goma sha biyu ta zaman bautar talala da aka kai mu, sai wani ɗan gudun hijira daga Urushalima ya zo wurina, ya ce, “Birnin ya fāɗi.” 22 A maraicen da ya wuce kafin ɗan gudun hijirar ya iso, Ubangiji ya ƙarfafa ni, ya kuma buɗe bakina a lokacin da mutum ya zo wurina da safe. Bakina kuwa ya buɗe, ban zama bebe ba kuma. 23 Ubangiji kuma ya yi magana da ni, ya ce, 24 “Ɗan mutum, mazaunan wuraren nan da aka lalatar a ƙasar Isra'ila, suna cewa, ‘Ibrahim shi kaɗai ne, duk da haka an ba shi ƙasar duka, balle fa mu da muke da yawa, lalle ƙasar tamu ce.’ 25 “Domin haka, sai ka faɗa musu, ‘Ubangiji Allah ya ce, “Kuna cin nama da jininsa, kuna bautar gumaka, kuna kuma yin kisankai, da haka za ku mallaki ƙasar? 26 Kun sa dogararku ga takobi kuna aikata abubuwan bankyama, kowannenku kuma yana zina da matar maƙwabcinsa, da haka za ku iya mallakar ƙasar?” ’ 27 “Ka faɗa musu, ‘Ubangiji ya ce, “Hakika, waɗanda ke a wuraren da aka lalatar, za a kashe su da takobi, wanda kuma ke a saura zan sa namomin jeji su cinye shi. Waɗanda kuma ke cikin kagara, da kogwannin duwatsu, annoba za ta kashe su. 28 Zan mai da ƙasar kufai marar amfani, fariya za ta ƙare. Tuddan Isra'ila za su zama kufai, ba wanda zai ratsa ta cikinsu. 29 Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na mai da ƙasar kufai marar amfani saboda dukan ayyukansu na banƙyama.” ’ ”

Sakamakon Wa'azin Annabin

30 Ubangiji ya ce, “Ɗan mutum, mutanenka sun taru a kan garu da cikin ƙofofin gidaje, suna magana da juna a kanka cewa, ‘Ku zo mu tafi mu ji maganar da ta zo daga wurin Ubangiji.’ 31 Sukan zo wurinka su zauna, sai ka ce su mutanena ne, sukan ji abin da ka ce, amma ba za su aikata ba, gama suna nuna ƙauna da baka, amma sun ƙwallafa zuciyarsu a kan ƙazamar riba. 32 A gare su ka zama gwanin kiɗa da waƙa, gama suna so su ji abin da kake faɗa, amma ba za su aikata ba. 33 Sa'ad da abin da kake faɗa ya cika (ba shakka kuwa zai cika), sa'an nan za su sani akwai annabi a tsakiyarsu.”

Ezekiyel 34

Annabci a kan Makiyayan Isra'ila

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra'ila, ka ce musu, ‘Ku masu kiwon mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah na ce, kaito, kaito, ku masu kiwon mutanen Isra'ila, kuna kiwon kanku kawai! Ashe, ba makiyaya ne ke kiwon tumaki ba? 3 Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba. 4 Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ba ku warkar da marasa lafiya ba, ba ku ɗora karayyu ba, waɗanda kuma suka yi makuwa ba ku komar da su ba, waɗanda suka ɓace ba ku nemo su ba, amma kuka mallake su ƙarfi da yaji. 5 Sai suka warwatsu saboda rashin makiyayin kirki, suka zama abincin namomin jeji. 6 Tumakina sun watse, suna yawo a kan dukan duwatsu da tuddai, sun warwatsu a duniya duka, ba wanda zai nemo su.’ 7 “Domin haka, ku ji maganata, ku makiyaya. 8 Ni Ubangiji Allah na ce, ‘Hakika da ya ke tumakina sun zama ganimar dukan namomin jeji, saboda rashin makiyayin kirki, makiyayana kuma ba su nemo su ba, amma suka yi kiwon kansu, ba su yi kiwon tumakin ba, 9 to, ku makiyaya, sai ku saurara ga maganata. 10 Ga shi, ina gāba da ku, zan nemi tumakina a hannunku. Zan hana ku yin kiwon tumakin, ku kuma ba za ku ƙara yin kiwon kanku ba. Zan ƙwace tumakina daga hannunku, domin kada su ƙara zama abincinku.’ ”

Makiyayi Mai Kyau

11 “Ni Ubangiji Allah na ce, ni kaina zan nemi tumakina. 12 Kamar yadda makiyayi yakan nemo tumakin da suka watse daga cikin garkensa, haka zan nemi tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu. 13 Zan fito da su daga cikin sauran al'umma, in tattaro su daga ƙasashe dabam dabam, in kawo su ƙasarsu, in yi kiwonsu a kan tuddan Isra'ila, kusa da maɓuɓɓugai, da cikin dukan wuraren da mutane ke zaune a ƙasar. 14 Zan yi kiwonsu a makiyaya mai kyau. Ƙwanƙolin tuddan Isra'ila zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a makiyaya mai kyau, za su yi kiwo a makiyaya mai dausayi a kan tuddan Isra'ila. 15 Ni kaina zan yi kiwon tumakin, in ba su hutawa, ni Ubangiji Allah na faɗa. 16 “Zan nemo ɓatattu, in komo da waɗanda suka yi makuwa, in ɗora karyayyu, in ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafan makiyayan nan masu taiɓa, zan hukunta su. 17 “Ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ku kuma garkena, zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin rago da bunsuru. 18 A ganinku abu mai kyau ne, bayan da kun yi kiwo a makiyaya mai kyau, sa'an nan ku tattake sauran makiyayar da ƙafafunku? Sa'ad da kuka sha ruwa mai kyau, sai kuma ku gurɓata sauran da ƙafafunku? 19 Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake da ƙafafunku, su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku!’ 20 “Saboda haka, ni, Ubangiji Allah, na ce, ‘Zan shara'anta tsakanin turkakkun tumaki da ramammu. 21 Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku, har kun watsar da su. 22 Zan ceci garken tumakina, ba za su ƙara zama ganima ba. Zan kuma shara'anta tsakanin tunkiya da tunkiya. 23 Zan sa musu makiyayi guda, wato bawana Dawuda. Zai yi kiwonsu, ya zama makiyayinsu. 24 Ni kuma, Ubangiji, zan zama Allahnsu. Bawana Dawuda kuwa zai zama sarkinsu.’ Ni Ubangiji na faɗa. 25 “Zan yi alkawarin salama da su. Zan kuwa kori namomin jeji daga ƙasar, domin tumakin su zauna lafiya a jeji, su kwana cikin kurmi. 26 Zan sa su, da wuraren da ke kewaye da tuduna dalilin samun albarka. Zan aiko da ruwan sama a lokacinsa, zai kuma zama ruwan albarka. 27 Itatuwan saura za su yi 'ya'ya, ƙasa kuma za ta ba da amfani. Za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su sani ni ne Ubangiji, sa'ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su. 28 Ba za su ƙara zama ganimar al'ummai ba, namomin jejin ƙasar kuma ba za su cinye su ba. Za su yi zamansu lafiya, ba wanda zai tsorata su. 29 Zan ba su gonaki masu dausayi don kada yunwa ta ƙara far musu a ƙasar, kada kuma su ƙara shan zargi wurin sauran al'umma. 30 Za su sani ni Ubangiji Allahnsu, ina tare da su, mutanen Isra'ila kuwa su ne mutanena, ni Ubangiji Allah na faɗa. 31 “Ku tumakin makiyayata, ku mutane ne, ni kuwa Allahnku ne, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 35

Annabci a kan Dutsen Seyir

1 Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Dutsen Seyir, ka yi annabci a kansa. 3 Ka faɗa masa, ni Ubangiji Allah na ce, Ga shi, ina gāba da shi, wato Dutsen Seyir. Zan miƙa hannuna gāba da shi, Zan maishe shi kufai, in lalatar da shi. 4 Zan lalatar da biranensa, In maishe su kufai marar amfani, Sa'an nan zai sani ni ne Ubangiji. 5 “Saboda ya riƙe ƙiyayya din din din, ya ba da mutanen Isra'ila domin a kashe su da takobi a lokacin masifarsu, da lokacin da adadin horonsu ya cika, 6 don haka, ni Ubangiji na ce, hakika zan sa a zub da jininsa. Mai zub da jini zai fafare shi, da ya ke shi ma ya zub da jini, domin haka mai zub da jini zai fafare shi. 7 Zan mai da Dutsen Seyir kufai marar amfani. Zan kashe duk mai shiga ko mai fita a cikinsa. 8 Zan cika duwatsunsa da gawawwaki. Waɗanda za a kashe da takobi za su faɗi a kan tuddansa, da cikin kwarurukansa, da cikin dukan kwazazzabansa. 9 Zan maishe shi kufai marar amfani har abada. Ba wanda zai zauna a cikin biranensa. Sa'an nan zai sani ni ne Ubangiji. 10 “Da ya ke ya ce al'umman nan biyu, da ƙasashen nan biyu za su zama nasa, ya mallake su, ko da ya ke Ubangiji yana cikinsu, 11 domin haka, ni Ubangiji Allah na ce, hakika zan saka masa gwargwadon fushinsa, da kishinsa, da ƙiyayyar da ya nuna musu. Zan sanar da kaina a gare su sa'ad da na hukunta shi. 12 Zai sani Ubangiji ne wanda ya ji dukan zarge zargen da ya yi wa duwatsun Isra'ila, da ya ce, ‘An maishe su kufai marar amfani, an ba mu su mu cinye!’ 13 Na ji tsiwa da dukan surutan da ya yi mini. 14 “Ni Ubangiji Allah zan maishe shi kufai marar amfani, domin dukan duniya ta yi farin ciki. 15 Kamar yadda ya yi farin ciki saboda gādon jama'ar Isra'ila, da ya zama kufai marar amfani, hakanan zan yi da shi, wato Seyir. Zai zama kufai marar amfani, wato Dutsen Seyir da dukan Edom. Sa'an nan mutane za su sani ni ne Ubangiji!”

Ezekiyel 36

Albarkar Ubangiji a kan Ƙasar Isra'ila a Gaba

1 “Kai ɗan mutum, ka yi annabci a kan duwatsun Isra'ila, ka ce, ‘Ya duwatsun Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji.’ 2 Ubangiji Allah ya ce, da ya ke maƙiya suna cewa, ‘Madalla, tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu,’ 3 sai ka yi annabci ka ce, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Da ya ke sun maishe ku kufai marar amfani, sun kuma murƙushe ku ta kowace fuska, har kun zama abin mallakar sauran al'umma, kun zama abin magana da abin tsegumi ga mutane. 4 Domin haka, ku duwatsun Isra'ila, sai ku ji maganar Ubangiji Allah. Ni Ubangiji Allah, na ce wa duwatsu, da tuddai, da kwazazzabai, da kwaruruka, da kufai, da yasaassun birane waɗanda suka zama ganima da abin ba'a ga al'umman da ke kewaye, 5 ni, Ubangiji Allah, ina yin magana da zafin kishina gāba da sauran al'umma, da dukan Edom, gama da farin ciki da raini suka mallaki ƙasata, suka washe ta.’ 6 “Domin haka ka yi wa ƙasar Isra'ila annabci, ka ce wa duwatsu, da tuddai, da kwazazzabai, da kwaruruka, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al'ummai.’ 7 “Domin haka ni Ubangiji Allah na rantse, cewa al'umman da ke kewaye da ku su ma za su sha zargi. 8 Amma ku, ya duwatsun Isra'ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanen Isra'ila, gama za su komo gida ba da jimawa ba. 9 Ga shi, ni naku ne, zan juyo wurinku. Za a kafce ku, a yi shuka! 10 Zan sa dukan mutanen Isra'ila su riɓaɓɓanya a cikinku. Za su zauna cikin biranen, su gina rusassun wurare. 11 Zan sa mutum da dabba su yawaita a cikinku, su kuma ba da amfani. Zan sa a zauna a cikinku kamar dā, sa'an nan zan nuna muku alheri fiye da dā. Daganan za ku sani, ni ne Ubangiji. 12 Zan kuma sa mutanena, Isra'ila, su yi tafiya a kanku, za ku zama gādonsu, ba za ku ƙara kashe 'ya'yansu ba. 13 “Ni Ubangiji Allah na ce, da ya ke mutane sukan ce muku, 'Kuna cinye mutane, kuna kuma kashe 'ya'yan al'ummarku, 14 saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ba, ba kuwa za ku ƙara kashe 'ya'yan al'ummarku ba. Ni Ubangiji Allah na faɗa. 15 Ba zan ƙara bari ku sha zargi wurin sauran al'umma ba, ba kuwa za ku ƙara shan kunya a gaban jama'a ba, ba kuma zan ƙara sa al'ummarku ta yi tuntuɓe ba, ni Ubangiji Allah na faɗa.” 16 Ubangiji Kuma ya yi magana da ni, ya ce, 17 “Ɗan mutum, sa'ad da mutanen Isra'ila suka zauna a ƙasar kansu, sun ƙazantar da ita ta wurin hanyoyinsu da ayyukansu. Halinsu a gare ni ya zama kamar rashin tsarkin mace a lokacin hailarta. 18 Sai na husata da su saboda jinin da suka zuba a cikin ƙasar, da kuma yadda suka ƙazantar da ƙasar da gumakansu. 19 Na warwatsa su cikin al'ummai, suka kuwa warwatsu cikin ƙasashe. Na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu. 20 Amma sa'ad da suka tafi cikin al'ummai, sai suka ɓata sunana mai tsarki a duk inda suka tafi. Sai mutane suka yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan jama'ar Ubangiji ne, amma dole ne su fita daga cikin ƙasarsa.’ 21 Amma na damu saboda sunana mai tsarki wanda mutanen Isra'ila suka sa aka ɓata shi a wurin al'ummai inda suka tafi. 22 “Domin haka sai ka faɗa wa mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah na ce, ‘Ba saboda ku ba ne, ya mutanen Isra'ila, zan yi wani abu, amma saboda sunana mai tsarki wanda kuka ɓata a wurin al'ummai inda kuka tafi. 23 Zan ɗauki fansa saboda sunana mai tsarki, mai girma, wanda aka ɓata a wurin al'ummai, ku kuma kuka ɓata shi a cikinsu. Al'ummai kuwa za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na tabbatar da tsarkina a wurinku a kan idonsu. 24 Zan kwaso ku daga cikin al'ummai, in tattaro ku daga dukan ƙasashe, in kawo ku cikin ƙasarku. 25 Zan yayyafa muku tsabtataccen ruwa, za ku kuwa tsarkaka daga dukan ƙazantarku, da kuma daga dukan gumakanku. 26 Zan ba ku sabuwar zuciya, in sa sabon ruhu a cikinku. Zan cire zuciya mai tauri daga gare ku, sa'an nan in sa muku zuciya mai taushi. 27 Zan sa ruhuna a cikinku, in sa ku bi dokokina, ku kiyaye ka'idodina. 28 Za ku zauna cikin ƙasar da na ba kakanninku. Za ku zama mutanena, ni kuma in zama Allahnku. 29 Zan tsarkake ku daga dukan ƙazantarku. Zan kuma sa hatsi ya yi yalwa, ba zan bar yunwa ta same ku ba. 30 Zan sa 'ya'yan itatuwa da amfanin gona su yalwata, don kada ku ƙara shan kunya saboda yunwa a wurin al'ummai. 31 Sa'an nan za ku tuna da mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau. Za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda muguntarku da ayyukanku na banƙyama. 32 Ni Ubangiji Allah na ce, sai ku sani, ba saboda ku ba ne zan aikata wannan. Ku kunyata, ku gigita saboda hanyoyinku, ya mutanen Isra'ila!’ ” 33 Ubangiji Allah ya ce, “A ranar da zan tsarkake ku daga dukan muguntarku, zan sa ku zauna cikin biranenku, ku gina rusassun wurare. 34 Ƙasar da take kufai a dā za ku kafce ta maimakon yadda take kufai a kan idon dukan masu wucewa. 35 Za su ce, ‘Wannan ƙasa wadda take kufai a dā ta zama kamar gonar Aidan, ga kuma rusassun wuraren da suka zama kufai, da rusassun birane, yanzu ana zaune a cikinsu, an kuma gina musu garu.’ 36 Sa'an nan al'umman da suka ragu kewaye da ku za su sani, ni Ubangiji na sāke gina rusassun wuraren da suka zama kufai. Ni Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata.” 37 Ubangiji Allah ya ce, “Ga abin da zan sa mutanen Isra'ila su roƙe ni, in yi musu. Za su roƙe ni in yawaita su kamar garken tumaki. 38 Kamar garken tumaki na hadaya, kamar garken tumaki a Urushalima a lokacin ƙayyadaddun idodi, haka rusassun birane za su cika da ɗumbun mutane. Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 37

Kwarin Busassun Ƙasusuwa

1 Ikon Ubangiji kuwa ya sauko a kaina, Ruhunsa kuma ya fito da ni ya ajiye ni a tsakiyar kwari wanda ke cike da ƙasusuwa. 2 Sai ya zagaya da ni cikinsu, ga su kuwa, suna da yawa a cikin kwarin, busassu ragau. 3 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan ƙasusuwa kuwa za su rayu?” Ni kuwa na amsa na ce, “Ya Ubangiji Allah, sani na gare ka.” 4 Sai ya ce mini, “Ka yi annabci a kan ƙasusuwan nan ka faɗa musu su saurari maganata. 5 Gama ni Ubangiji Allah zan hura musu numfashi, za su kuwa rayu. 6 Zan sa musu jijiyoyi da tsoka, in rufe da fata, in kuma hura musu numfashi, sa'an nan za su rayu, su sani ni ne Ubangiji.” 7 Sai na yi annabci kamar yadda ya umarce ni. Da na yi annabcin sai aka ji motsi da girgiza. Sai ƙasusuwan suka harhaɗu da juna, ƙashi ya haɗu da ƙashi a mahaɗinsu. 8 Da na duba, sai ga jijiyoyi a kansu, nama kuma ya baibaye su, sa'an nan fata ta rufe su, amma ba numfashi a cikinsu. 9 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan iska, ka ce mata, ni Ubangiji Allah na ce ta zo daga kusurwa huɗu, ta hura a kan waɗannan matattu domin su rayu.” 10 Na kuwa yi annabci kamar yadda aka umarce ni, sai numfashi ya shiga cikinsu, suka rayu, suka tashi, suka tsaya da ƙafafunsu. Sun zama babbar runduna ƙwarai. 11 Sa'an nan Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum waɗannan ƙasusuwa su ne mutanen Isra'ila duka. Ga shi, suna cewa, ‘Ƙasusuwa sun bushe, zuciyarmu kuwa ta karai, an share mu ƙaƙaf.’ 12 “Domin haka ka yi annabci ka ce musu, ni Ubangiji Allah na ce zan buɗe kaburburansu, in tashe su daga cikin kaburburansu. Zan kuma komar da su gida zuwa ƙasar Isra'ila. 13 Mutanena za su sani ni ne Ubangiji sa'ad da na buɗe kaburburansu na tashe su daga cikinsu. 14 Zan sa Ruhuna a cikinsu za su kuwa rayu. Zan sa su a ƙasarsu sa'an nan za su sani ni Ubangiji na faɗa, na kuwa aikata.”

Mutanen Yahuza da Isra'ila za su Zama Mulki Guda

15 Ubangiji ya kuma yi magana da ni, ya ce, 16 “Ɗan mutum, ka ɗauki sanda, ka rubuta a kansa, ‘Domin Yahuza da magoyan bayansa.’ Ka kuma ɗauki wani sanda, ka rubuta a kansa, ‘Domin Yusufu, sandan Ifraimu, da dukan mutanen Isra'ila, magoyan bayansa.’ 17 Ka haɗa su su zama sanda guda a hannunka. 18 Sa'ad da kuma jama'arka suka ce maka ka nuna musu abin da kake nufi da waɗannan, 19 sai ka faɗa musu, cewa ni Ubangiji Allah na ce zan karɓe sandan Yusufu, wanda ke a hannun Ifraimu da mutanen Isra'ila magoyan bayansa, in haɗa shi da sandan Yahuza in maishe su sanda guda a hannuna. 20 “Sa'ad da sandunan da ka yi rubutu a kansu suna hannunka a gabansu, 21 sai ka faɗa musu, cewa ni Ubangiji Allah na ce, zan komo da jama'ar Isra'ila daga wurin al'ummai inda suka warwatsu, zan tattaro su daga ko'ina, in maido su ƙasarsu. 22 Zan maishe su al'umma guda a ƙasar Isra'ila. Sarki ɗaya zai sarauce su duka, ba za su ƙara zama al'umma biyu ba, ba kuwa za su ƙara zama masarauta biyu ba. 23 Ba za su ƙara ƙazantar da kansu da gumaka da abubuwan banƙyama da kowane irin laifi ba. Zan komo da su daga riddar da suka yi, in tsarkake su. Za su zama jama'ata, ni kuma zan zama Allahnsu. 24 Bawana Dawuda zai sarauce su. Dukansu za su sami shugaba guda. Za su bi ka'idodina su kiyaye dokokina. 25 Za su zauna a ƙasar da kakanninsu suka zauna, wadda na ba bawana Yakubu. Su da 'ya'yansu da jikokin 'ya'yansu za su zauna a can har abada. Bawana Dawuda kuwa zai sarauce su har abada. 26 Zan ƙulla dawwamammen alkawarin salama da su. Zan sa musu albarka, in yawaita su. Zan kafa Haikalina a tsakiyarsu har abada. 27 Wurin Zamana zai kasance a tsakiyarsu, zan zama Allahnsu, su kuma za su zama mutanena. 28 Sa'an nan al'ummai za su sani, ni ne na tsarkake Isra'ila sa'ad da na kafa Haikalina a tsakiyarsu har abada.”

Ezekiyel 38

Annabci a kan Gog

1 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ɗan mutum, ka fuskanci Gog na ƙasar Magog, babban shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal, ka yi annabci a kansa, 3 ka ce Ubangiji Allah ya ce, ‘Ga shi, ina gaba da kai, ya Gog, babban shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal. 4 Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi cikin muƙamuƙanka, in fitar da kai, da dukan sojojinka, da dawakai da mahayansu. Su babbar runduna ce saye da makamai, wato garkuwoyi, da takuba a zāre, 5 mutanen Farisa, da Habasha, duk da Fut. Dukansu suna saye da garkuwa da kwalkwali, 6 da Gomer tare da dukan sojojinsa, da Bet-togarma daga ƙurewar arewa, da dukan sojojinsa, su jama'a mai yawa, suna tare da kai. 7 Ka shirya, ka kuma zama da shiri, kai da dukan rundunar da suka tattaru kewaye da kai, ka zama ɗan tsaronsu. 8 Bayan kwanaki masu yawa zan ziyarce ka, a cikar waɗannan shekaru, za ka koma ƙasar duwatsun Isra'ila, wadda ta farfaɗo daga masifar yaƙin da ta sha, ƙasa inda jama'a suka tattaru daga sauran al'umma masu yawa, wadda a dā ta yi ta lalacewa, sai da aka fito da mutanenta daga cikin al'ummai, yanzu kuwa dukansu suna zaman lafiya. 9 Za ka ci gaba, kana zuwa kamar hadiri, za ka rufe ƙasar kamar gizagizai, kai da rundunarka, da jama'a masu yawa tare da kai.’ ” 10 Ubangiji Allah ya ce, “A wannan rana tunani zai shiga cikin zuciyarka, za ka ƙirƙiro muguwar dabara, 11 ka ce, ‘Zan haura, in tafi ƙasar da garuruwanta ba su da garu, in fāɗa wa mutanen da ke zama cikin salama, dukansu kuwa suna zaman lafiya, garuruwansu ba garu, ba su da ko ƙyamare, 12 don in washe su ganima, in fāda wa wuraren da aka ɓarnatar waɗanda ake zaune a cikinsu yanzu, in kuma fāɗa wa jama'ar da aka tattaro daga cikin al'ummai waɗanda suka sami shanu da dukiya, suna zaune a cibiyar duniya.’ 13 Sheba da Dedan, da 'yan kasuwar Tarshish, da dukan garuruwa za su ce maka, ‘Ka zo kwasar ganima ne? Ko ka zo ka tattaro rundunarka don ka yi waso, ka kwashe azurfa da zinariya, da bisashe, da dukiya, ka kwashe babbar ganima?’ 14 “Saboda haka ɗan mutum, yi annabci, ka faɗa wa Gog, cewa ni Ubangiji Allah na ce, ‘A wannan rana sa'ad da jama'ata Isra'ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba? 15 Za ka taso daga wurin da kake, can ƙurewar arewa, da jama'a mai yawa tare da kai, babbar rundunar mayaƙa mai ƙarfi, dukansu a kan dawakai. 16 Za ka zo ka yi yaƙi da mutanen Isra'ila, za ka rufe su kamar yadda girgije yakan rufe sararin sama. A kwanaki na ƙarshe zan kawo ka ka yi yaƙi da ƙasata domin al'ummai su san ni sa'ad da na bayyana tsarkina a gabansu ta wurin abin da ka yi.’ ” 17 Ubangiji Allah ya ce, “Kai ne wanda na yi magana a kanka a zamanin dā ta wurin bayina annabawan Isra'ila, cewa a shekaru masu zuwa zan kawo ka, ka yaƙe su. 18 Amma a wannan rana sa'ad da Gog zai kawo wa ƙasar Isra'ila yaƙi, ni Ubangiji Allah zan hasala. 19 Gama a kishina da zafin hasalata na hurta, cewa a wannan rana za a yi babbar girgiza a ƙasar Isra'ila. 20 Kifayen teku, da tsuntsayen sararin sama, da bisashe, da dukan masu rarrafe, da dukan mutanen da ke duniya, za su yi makyarkyata a gabana. Za a jefar da duwatsu ƙasa, tsaunuka za su fādi, kowane bango zai rushe. 21 Zan razana Gog da kowace irin razana, ni Ubangiji Allah na faɗa. Mutanensa za su sassare junansu da takubansu. 22 Zan hukunta shi da annoba da kuma zub da jini. Zan yi masa ruwa da ƙanƙara, da wuta, da kibritu za a makaka a kansa da rundunarsa, da dukan jama'ar da ke tare da shi. 23 Da haka kuwa zan bayyana girmana da tsarkina in kuma sanar da kaina ga al'ummai. Ta haka za su sani ni ne Ubangiji.”

Ezekiyel 39

Cin Nasara a kan Gog

1 “Kai ɗan mutum, sai ka faɗa wa Gog shugaban Rosh, da Meshek, da Tubal cewa, ‘Ni Ubangiji Allah ina gāba da kai. 2 Zan juya ka in sa ka gaba in tashi daga ƙurewar arewa, in kawo ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra'ila. 3 Sa'an nan zan karya bakan da ke a hannun hagunka, in sa kiban da ke a hannun damanka su fāɗi. 4 Za ka fāɗi matacce a kan duwatsun Isra'ila, kai da dukan rundunanka, da jama'ar da ke tare da kai. Zan ba da gawawwakinka ga tsuntsaye da dabbobi masu cin nama. 5 Za ka mutu a filin saura, gama haka ni Ubangiji Allah na faɗa.’ 6 Zan aika da wuta a kan Magog, da a kan waɗanda suke zaman lafiya a ƙasashen gāɓar teku, za su kuwa sani ni ne Ubangiji. 7 Zan sanar da sunana mai tsarki a tsakiyar jama'ata, wato Isra'ila, ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, al'ummai kuwa za su sani ni ne Ubangiji Mai Tsarki a cikin Isra'ila. 8 “Ga shi, ranar da na ambata tana zuwa, hakika kuwa tana zuwa, ni Ubangiji Allah na faɗa. 9 Sa'an nan su mazaunan biranen Isra'ila za su tattara makaman mutane, wato garkuwoyi, da bakuna, da kibau da kulake, da māsu, su yi ta hura wuta da su, har ya kai shekara bakwai. 10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don nemo itacen wuta ba, gama za su yi ta hura wuta da makaman. Za su washe waɗanda suka washe su a dā, ni Ubangiji na faɗa. 11 “A wannan rana zan ba Gog makabarta a Isra'ila, a kwarin matafiya a gabashin teku. Makabartar za ta kashe hanyar matafiya, gama a can za a binne Gog da dukan rundunar da ke tare da shi. Za a kira wurin Hamongog, wato Kwarin Rundunar Gog. 12 Jama'ar Isra'ila za su yi wata bakwai suna binne su don su tsabtace ƙasar. 13 Dukan jama'ar ƙasar za su yi aikin binnewar, zai zama daraja a gare su a ranar da zan bayyana ɗaukakata, ni Ubangiji Allah na faɗa. 14 A ƙarshen wata bakwai ɗin za su keɓe waɗansu mutane domin su bi ko'ina cikin ƙasar, su binne sauran gawawwakin da suka ragu a ƙasar don su tsabtace ta. 15 Sa'ad da waɗannan suke bibiyawa a cikin ƙasar, duk wanda ya ga ƙashin mutum, sai ya kafa wata alama kusa da ƙashin don masu binnewa su gani, su ɗauka, su binne a Kwarin Rundunar Gog. 16 Akwai gari a wurin, za a sa masa suna Hamona, wato runduna. Ta haka za su tsabtace ƙasar. 17 “Ni Ubangiji Allah na ce, kai ɗan mutum, sai ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan bisashe daga ko'ina, su zo idi wanda nake shirya musu a duwatsun Isra'ila. Za su ci nama su kuma sha jini. 18 Za su ci naman mutane masu iko, su sha jinin shugabannin duniya, waɗanda aka kashe kamar yadda ake yanka raguna, da 'yan tumaki, da awaki, da bijimai, da dukan turkakkun Bashan. 19 Za su ci kitse, har su gundura, su sha jini kuma, har su bugu a idin da nake shirya musu. 20 Za a ƙosar da su da naman dawakai, da na mahayansu da na mutane masu iko, da na dukan mayaƙa, ni Ubangiji na faɗa.”

Komowar Mutanen Isra'ila

21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al'ummai, dukan al'ummai kuwa za su ga hukuncin da na yi da ikon da na nuna kansu. 22 Tun daga wannan rana har zuwa gaba, jama'ar Isra'ila za su sani, ni ne Ubangiji Allahnsu. 23 Al'ummai kuma za su sani an kai jama'ar Isra'ila zaman bautar talala saboda muguntarsu, domin sun yi mini ha'inci, ni kuwa na kawar da fuskata daga gare su, na bashe su a hannun abokan gābansu, suka ci su da yaƙi. 24 Na yi gwargwadon lalatarsu da laifofinsu, na kawar da fuskata daga gare su. 25 “Saboda haka, ni Ubangiji Allah, na ce yanzu zan komo da zuriyar Yakubu daga bauta in nuna mata jinƙai. Zan yi kishi domin sunana mai tsarki. 26 Sa'ad da suka komo suka zauna lafiya a ƙasarsu, za su manta da abin kunyar da suka yi da dukan ha'incin da suka yi mini. Ba wanda zai ƙara firgita su, ba kuwa mai tsorata su. 27 Zan nuna wa sauran al'umma ni mai tsarki ne ta wurin komo da mutanen Isra'ila daga cikin al'ummai, da ƙasashen al'ummai magabtansu. 28 Sa'an nan za su sani ni ne Ubangiji Allahnsu, domin na kore su daga ƙasarsu zuwa bautar talala cikin al'ummai, sa'an nan na sāke tattaro su zuwa cikin ƙasarsu. Daga cikinsu ba zan bar ko ɗaya a cikin al'ummai ba. 29 Ba kuma zan ƙara kawar da fuskata daga gare su ba, sa'ad da na saukar da Ruhuna a kan jama'ar Isra'ila, ni Ubangiji na faɗa.”

Ezekiyel 40

Wahayin Haikalin da Ezekiyel ya Gani

1 A ranar goma ga wata na farko a shekara ta ashirin da biyar ta zamanmu a bautar talala, a shekara ta goma sha huɗu da cin birnin, ikon Ubangiji ya sauko a kaina. 2 A cikin wahayi, sai Allah ya kai ni ƙasar Isra'ila, ya zaunar da ni a kan wani dutse mai tsayi ƙwarai, inda na ga wani fasali kamar birni daura da ni. 3 Sa'ad da ya kai ni can sai ga wani mutum, kamanninsa sai ka ce tagulla, yana riƙe da igiyar rama da wani irin ƙara na awo a hannunsa, yana tsaye a bakin ƙofa. 4 Sai mutumin nan ya ce mini, “Ɗan mutum ka duba da idonka, ka ji da kunnuwanka, ka kuma mai da hankali ga dukan abin da zan nuna maka, gama saboda haka aka kawo ka nan. Sai ka sanar wa jama'ar Isra'ila abin da ka gani duka.” 5 Abin da na gani Haikali ne. Akwai katanga kewaye da filin Haikalin. Tsawon karan awon kuma da ke a hannun mutumin kamu shida ne. Sai ya auna faɗin katangar ya sami kamu shida, tsayinta kuma kamu shida. 6 Ya tafi kuma wajen ƙofar gabas ya hau matakanta, ya auna dokin ƙofar, faɗinta kamu shida ne. 7 Tsawon ɗakin 'yan tsaro kamu shida ne, faɗinsa kuma kamu shida. Kamu biyar ne ke tsakanin ɗaki da ɗaki. Dokin ƙofa kuma da ke kusa da shirayin bakin ƙofar Haikali kamu shida ne. 8 Ya kuma auna shirayin bakin ƙofar da ke fuskantar Haikali, kamu shida. 9 Sa'an nan ya auna shirayin bakin ƙofar kamu takwas ne. Sai kuma ya auna ginshiƙan shirayin kamu biyu ne. Shirayin ƙofar yana fuskantar ciki. 10 Akwai ɗakuna uku na 'yan tsaro a kowane gefe na ƙofar gabas, girmansu iri ɗaya ne. Ginshiƙansu kuma girmansu ɗaya ne. 11 Ya kuma auna fāɗin bakin ƙofar, kamu goma ne, tsayin ƙofar kuwa kamu goma sha uku ne. 12 Akwai, 'yar katanga a gaban ɗakunan 'yan tsaron, faɗinta kamu ɗaya ne a kowane gefe. Girman ɗakunan 'yan tsaron kuwa kamu shida ne a kowane gefe. 13 Daga bayan rufin ɗaya ɗakin 'yan tsaro zuwa bayan ɗayan rufin ya auna filin ya sami kamu ashirin da biyar. 14 Ya yi ginshiƙai kamu sittin. Akwai ɗakuna kewaye da shirayin da ke bakin ƙofa. 15 Daga gaban ƙofar shiga, zuwa kurewar shirayi na can ciki kamu hamsin ne. 16 Akwai tagogi masu murfi da ke fuskantar ɗakunan 'yan tsaro da kuma ginshikansu waɗanda ke wajen ƙofa a kewaye, hakanan kuma shirayin. Daga ciki kuma akwai tagogi a kewaye. A kowane ginshiƙi an zana siffar itatuwan dabino. 17 Sai ya kawo ni a fili na waje, ga ɗakuna da daɓe kewaye da filin. Akwai ɗakuna talatin a gaban daɓen. 18 Daɓen ya bi ta daidai gefen ƙofofin. Wannan shi ne daɓen da ke ƙasa ƙasa. 19 Sai ya auna nisan da ke tsakanin fuskar ciki ta ƙofar da ke ƙasa zuwa fuskar waje ta filin ciki, ya sami kamu ɗari wajen gabas da arewa. 20 Ya kuma auna tsayin ƙofar arewa da faɗinta wadda ke fuskantar filin waje. 21 Tana da ɗakuna uku na 'yan tsaro a kowane gefe. Girman ginshiƙanta da shirayinta, daidai suke da ƙofa ta fari. Tsayinta kamu hamsin ne, faɗinta kuwa kamu ashirin da biyar. 22 Girman tagoginta, da na shirayin, da na siffar itatuwan dabinon da aka zana iri ɗaya ne da na ƙofar da ta fuskanci gabas. Tana da matakai bakwai. Shirayinta yana daga can ciki. 23 Fili na ciki yana da ƙofa daura da ƙofar arewa da ta gabas. Ya auna daga ƙofa zuwa ƙofa kamu ɗari. 24 Ya kuma kai ni wajen kudu, sai kuma ga wata ƙofa. Ya auna ginshiƙanta da shirayinta. Girmansu ɗaya ne, kamar na sauran. 25 Akwai tagogi kewaye da ƙofar, da shirayinta kamar na sauran. Tsayinta kamu hamsin ne, faɗinta kuwa kamu ashirin da biyar. 26 Tana da matakai bakwai. Shirayinta yana daga can ciki. An zana siffar itatuwan dabino a ginshiƙanta, ɗaya a kowane gefe. 27 Akwai wata ƙofa a kudancin fili na can ciki. Ya auna daga ƙofa zuwa ƙofa kamu ɗari. 28 Ya kuma kai ni fili na can ciki, wajen ƙofar kudu, sai ya auna ƙofar, girmanta daidai yake da na sauran. 29 Haka kuma ɗakunanta na 'yan tsaro, da ginshiƙanta, da shirayinta, girmansu ɗaya yake da na sauran. Tana da tagogi kewaye da ita da shirayinta. Tsayinta kamu hamsin ne, faɗinta kamu ashirin da biyar ni. 30 Akwai shirayi kewaye, tsawonsa kamu ashirin da biyar ne, faɗinsa kuma kamu biyar ne. 31 Shirayinta yana fuskantar filin da ke waje. An zana siffar itatuwan dabino a ginshikanta. Tana kuma da matakai takwas. 32 Sai kuma ya kai ni a fili na can ciki wajen gabas. Ya auna ƙofar, girmanta daidai yake da na sauran. 33 Hakanan kuma ɗakunanta na 'yan tsaro, da ginshiƙanta, da shirayinta, girmansu daidai yake da na sauran. Tana da tagogi kewaye da ita da shirayinta. Tsayinta kamu hamsin ne, faɗinta kuma kamu ashirin da biyar. 34 Shirayinta yana fuskantar filin da ke waje. Aka zana siffar itatuwan dabino a kan ginshiƙanta a kowane gefe. Tana da matakai takwas. 35 Sa'an nan kuma ya kai ni ƙofar arewa, ya auna ta. Girmanta daidai yake da na sauran. 36 Haka kuma ɗakunanta na 'yan tsaro, da ginshiƙanta, da shirayinta. Tana da tagogi kewaye da ita da shirayinta. Tsayinta kamu hamsin ne, faɗinta kuma kamu ashirin da biyar. 37 Ginshiƙai suna fuskantar filin da ke waje. Aka zana siffar itatuwan dabino a kan ginshiƙanta a kowane gefe. Ita ma matakanta takwas ne. 38 Akwai ɗaki, wanda ƙofarsa ke duban ginshiƙan gyaffan ƙofofin, a wurin ake wanke hadayar ƙonawa. 39 A shirayin ƙofar akwai tebur biyu a kowane gefe, inda ake yanka hadayar ƙonawa, da hadaya don zunubi da laifi. 40 Akwai tebur biyu a sashin waje na shirayin ƙofar arewa, akwai kuma waɗansu tebur biyu a ɗayan sashin shirayin ƙofar. 41 A gab da ƙofar akwai tebur huɗu, a waje ɗaya kuma akwai huɗu. Duka guda takwas ke nan, inda za a riƙa yanka dabbobin da za a yi hadaya da su. 42 Akwai kuma tebur huɗu da aka yi da sassaƙaƙƙun duwatsu, tsawon da faɗin kowanne kamu ɗaya da rabi rabi ne, tsayi kuwa kamu guda ne. A nan za a ajiye kayan yanka hadayar ƙonawa, da ta sadaka. 43 Aka kakkafa ƙugiyoyi kewaye da cikin ɗakin, tsawonsu taƙi-taƙi. Za a riƙa ajiye naman hadaya a kan teburorin. 44 Ya kai ni fili na can ciki, sai ga ɗakuna biyu a filin. Ɗaya yana wajen ƙofar arewa, yana fuskantar kudu. Ɗayan kuma yana wajen ƙofar kudu yana fuskantar arewa. 45 Sai ya ce mini, “Wannan ɗaki wanda ke fuskantar kudu na firistoci ne waɗanda ke lura da Haikalin. 46 Ɗakin da ke fuskantar arewa na firistoci ne waɗanda ke lura da bagade. Waɗannan su ne zuriyar Zadok waɗanda su kaɗai ne daga cikin Lawiyawa da suke da iznin kusatar Ubangiji don su yi masa hidima.” 47 Ya auna filin, tsawonsa kamu ɗari ne, faɗinsa kuma kamu ɗari, wato murabba'i ke nan. Bagade kuma yana a gaban Haikalin. 48 Ya kuma kai ni a shirayin Haikalin. Ya auna ginshiƙan shirayin, kamu biyar ne a kowane gefe. Faɗin ƙofar kuwa kamu uku ne a kowane gefe. 49 Tsawon shirayin kamu ashirin ne, faɗinsa kuwa kamu goma sha ɗaya. Akwai matakan hawa, akwai kuma ginshiƙai a kowane gefe.

Ezekiyel 41

1 Sai ya kai ni cikin Haikalin, sa'an nan ya auna ginshiƙai. Fāɗin ginshiƙan kamu shida ne a kowane gefe. 2 Fāɗin ƙofar kamu goma ne. Madogaran ƙofar kamu biyar ne a kowane gefe. Sai ya auna Haikalin, tsawonsa kamu arba'in ne faɗinsa kuma kamu ashirin ne. 3 Sai ya shiga ɗaki na can ciki, ya auna madogaran ƙofar, ya sami kamu biyu biyu. Tsayin ƙofar kuma kamu shida ne. Faɗin ƙofar kamu bakwai ne. 4 Ya kuma auna ɗaki na ƙurewar ciki, tsawonsa kamu ashirin ne, faɗinsa kuma kamu ashirin. Sai ya ce mini, “Wannan shi ne Wuri Mafi Tsarki.” 5 Sai kuma ya auna bangon Haikalin, kaurinsa kamu shida ne. Faɗin ɗakunan da ke kewaye da Haikalin kamu huɗu ne. 6 Ɗakunan benaye ne masu hawa uku. Akwai ɗakuna talatin a kowane hawa. Akwai katanga kewaye da Haikalin don ta tokare ɗakunan, domin ba a so ɗakunan su jingina da bangon Haikalin. 7 Faɗin ɗakunan yana ƙaruwa daga hawa zuwa hawa, gama katangar da ke kewaye da Haikali ta yi ta ƙaruwa daga hawa zuwa hawa. A gefen Haikalin akwai matakan hawa. Don haka ana iya hawa daga ɗaki na ƙasa zuwa hawa na uku ta hanyar hawa na biyu. 8 Na ga harsashi mai faɗi kewaye da Haikalin. Tsawon harsashin gini na ɗakunan karan awo mai tsawon kamu shida ne. katangar waje ta ɗakunan kamu biyar ne. Faɗin filin da ke tsakanin ɗakunan waje da na Haikali kamu ashirin ne kewaye da Haikalin. 11 Ana buɗe ƙofofin ɗakuna a wajen filin da ke tsakanin ɗakuna. Ƙofa ɗaya tana fuskantar wajen arewa, ɗaya kuma tana fuskantar wajen kudu. Faɗin filin da ya ragu kamu biyar ne. 12 Ginin da ke fuskantar farfajiyar Haikali a wajen yamma, faɗinsa kamu saba'in ne. Kaurin ginin kamu biyar ne, tsawonsa kuma kamu tasa'in ne. 13 Sai ya auna Haikalin, tsawonsa kamu ɗari. Tsawon farfajiyar, da ginin, da katangarsa, kamu ɗari. 14 Faɗin Haikalin da farfajiyar a fuskar gabas, kamu ɗari. kuma auna tsawon ginin da ke fuskantar farfajiyar da ke wajen yamma da hanyar fita, kamu ɗari ne. Cikin Haikalin, da ɗaki na can ciki, da shirayi, dukansu uku suna da tagogi masu gagara badau. An manne bangon Haikalin da ke fuskantar shirayin da katako, tun daga ƙasa har zuwa tagogi. (Tagogin kuma an rufe su.) zana siffofin kerubobi da na itatuwan dabino a bangon Haikali ciki da waje har zuwa kan ƙofar shiga. Zanen siffar itacen dabino yana a tsakanin kerub da kerub. Kowane kerub yana da fuska biyu. 19 Fuska ɗaya kamar ta mutum tana fuskantar zānen siffar itacen dabino a wannan gefe. Ɗaya fuskar kamar ta sagarin zaki tana fuskantar zānen siffar itacen dabino na wancan gefe. Haka aka zana dukan jikin bangon Haikalin da su. 20 Daga ƙasa zuwa ɗaurin ƙofa, an zana siffofin kerubobi da na itatuwan dabino. 21-22 Madogaran ƙofofin Haikalin murabba'i ne. Akwai wani abu mai kama da bagaden itace a gaban Wuri Mai Tsarki, tsayinsa kamu uku ne, tsawonsa kamu biyu ne. Kusurwoyinsa da gindinsa, da jikinsa na itace ne. Sai ya ce mini, “Wannan shi ne tebur da ke a gaban Ubangiji.” 23 Haikali da Wuri Mai Tsarki suna da ƙofa biyu a haɗe. 24 Kowace ƙofa tana da murfi biyu masu buɗewa ciki da waje. 25 A ƙofofin Haikalin an zāna siffofin kerubobi da na itatuwan dabino kamar yadda aka zāna a bangon Haikalin. Akwai rumfar da aka yi da itace a gaban shirayin waje. 26 Akwai tagogi masu gagara badau a kowane gefen ɗakin. An kuma zāna bangon da siffar itatuwan dabino.

Ezekiyel 42

1 Sa'an nan ya kai ni a farfajiya da ke waje, ya kuma kai ni ɗakunan da ke kusa da farfajiyar Haikali, daura da ginin da ke wajen arewa. 2 Tsawon ginin da ke wajen gefen arewa kamu ɗari ne, faɗinsa kuma kamu hamsin. 3 A gaban kamu ashirin na farfajiyar da ke can ciki, da kuma a gaban daɓen farfajiyar da ke waje, akwai jerin ɗakuna hawa uku uku. 4 A gaban ɗakunan akwai hanya mai faɗin kamu goma, tsawonta kuwa kamu ɗari. Ƙofofinsu suna fuskantar arewa. 5 Ɗakunan da ke a hawa na uku ba su da fāɗi, gama hanyar benen ya cinye wuri fiye da ɗakunan da ke a hawa na ƙasa da na tsakiya. 6 Ɗakunan suna da hawa uku, amma ba su da ginshiƙai kamar na farfajiyar da ke waje. Saboda haka ɗakunan da ke a hawa na uku ba su kai girman waɗanda ke a hawa na ƙasa da na tsakiya ba. 7 Tsawon katangar waje wadda ke gefen ɗakunan farfajiyar waje wanda ke daura da ɗakunan kamu hamsin ne. 8 Tsawon ɗakunan da ke fuskantar farfajiyar waje kamu hamsin ne. Waɗanda ke fuskantar Haikalin kuwa tsawonsu kamu ɗari ne. 9 Ƙasa da ɗakunan nan akwai ƙofa a gefen gabas, in za a shiga cikinsu daga farfajiyar waje. 10 Akwai kuma ɗakuna a faɗin katangar farfajiyar a wajen gabas a gaban wata farfajiyar da gaban wani gini. 11 Akwai hanya a gaban ɗakunan, sun kuma yi kama da ɗakunan da ke wajen arewa. Tsawonsu, da faɗinsu, da yadda aka shirya su, da ƙofofinsu duk iri ɗaya ne. 12 Kamar ƙofofin ɗakunan da ke wajen kudu, hakanan kuma akwai ƙofa a hanyar da ke gaban katanga a wajen gabas, in za a shiga. 13 Sa'an nan ya ce mini, “Ɗakunan da ke wajen kudu da na wajen arewa gaban farfajiya, su ne tsarkakan ɗakuna inda firistoci waɗanda ke kusatar Ubangiji za su ci hadayu mafi tsarki. A nan kuma za su ajiye hadayu mafi tsarki, wato hadaya ta gari, da hadaya domin zunubi, da hadaya domin laifi, gama wurin tsattsarka ne. 14 Sa'ad da firistoci suka shiga Wuri Mai Tsarki, ba za su fita daga cikinsa zuwa farfajiyar da ke waje ba, sai sun tuɓe rigunan aikinsu, gama rigunan tsarkakakku ne. Za su sa waɗansu riguna kafin su tafi inda mutane suke.” 15 Sa'ad da ya gama auna cikin Haikalin, ya fito da ni ta ƙofar gabas, sa'an nan ya auna filin da ke kewaye da Haikalin. 16 Ya auna kusurwar gabas da karan awo, kamu ɗari biyar. 17 Sai kuma ya auna kusurwar arewa, kamu ɗari biyar. 18 Kusurwar kudu kamu ɗari biyar. 19 Kusurwar yamma, ita ma kamu ɗari biyar. 20 Ya auna dukan kusurwoyi huɗu. Filin yana kewaye da katanga mai tsawo kamu ɗari biyar ne, fāɗi kuma kamu ɗari biyar don ya raba Wuri Mai Tsarki da sauran wurin.

Ezekiyel 43

Zatin Ubangiji ya Koma Haikalin

1 Bayan haka kuma sai ya kai ni ƙofar da ke fuskantar gabas. 2 Sai ga zatin Allah na Isra'ila yana tahowa daga gabas. Muryar Allah ta yi amo kamar rurin teku. Duniya kuwa ta haskaka da zatinsa. 3 Wahayin da na gani ya yi kama da wahayin da na gani lokacin da ya hallaka birnin, kamar kuma wanda na gani a bakin kogin Kebar. Sai na fāɗi rubda ciki. 4 Zatin Ubangiji ya shiga Haikalin ta ƙofar gabas. 5 Ruhu kuwa ya ɗaga ni, ya kai ni a farfajiya ta can ciki, sai ga zatin Ubangiji ya cika Haikali. 6 Sa'ad da mutumin ke tsaye kusa da ni, sai Ubangiji ya yi magana da ni daga cikin Haikalin. 7 Ya ce mini, “Ɗan mutum, wannan wuri shi ne kursiyin sarautata da kilisaina, inda zan zauna tsakiyar mutanen Isra'ila har abada. Mutanen Isra'ila da sarakunansu ba za su ƙara ɓata sunana mai tsarki ta wurin bauta wa gumaka da gina siffofin sarakunansu da suka mutu ba, 8 ko kuwa ta wurin sa dokin ƙofarsu kusa da dokin ƙofata, da kuma ta kafa madogaran ƙofarsu kusa da nawa, sai dai katangar da ta yi mana tsakani. Sun ɓata sunana mai tsarki da ayyukansu masu banƙyama, don haka na hallaka su saboda sun sa na husata. 9 Yanzu sai su zubar da gumakansu da siffofin sarakunansu nesa da ni, ni kuwa zan zauna a cikinsu har abada.

Ka'idodin Haikali da Bagade

10 “Kai kuwa ɗan mutum, sai ka bayyana Haikalin ga mutanen Isra'ila domin su kunyata saboda muguntarsu, ka kuma sa su auna fasalin Haikalin. 11 Idan sun ji kunyar dukan abin da suka aikata, sai ka nuna musu fasalin Haikalin, da tsarinsa, da wuraren fita, da wuraren shiga, da fasalinsa duka. Ka kuma sanashe su dukan ka'idodinsa, da dukan dokokinsa. Ka rubuta a gaban idanunsu don su kiyaye, su aikata dukan dokokinsa da dukan ka'idodinsa. 12 Wannan ita ce dokar Haikalin. Dukan filin da ke kewaye a kan dutsen, za ta zama wuri mai tsarki ƙwarai. 13 “Wannan shi ne girman bagaden bisa ga tsawon kamu. A nan kamu guda daidai yake da kamu guda da taƙi. Gindinsa kamu ɗaya ne, faɗinsa kuma kamu ɗaya, faɗin da'irarsa taƙi guda ne. 14 Tsayin bagaden zai zama kamu biyu daga gindinsa zuwa ƙaramin mahaɗinsa fāɗinsa kuma kamu ɗaya ne. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗi zai zama kamu huɗu, faɗinsa kuwa kamu ɗaya. 15 Tsayin murhun bagaden zai zama kamu huɗu. A kan murhun akwai zanko guda huɗu sun miƙe sama, tsawonsu kamu guda ne. 16 Murhun bagaden zai zama murabba'i ne, wato tsawonsa kamu goma sha biyu, faɗinsa kuma kamu goma sha biyu. 17 Mahaɗin kuma zai zama kamu goma sha huɗu, murabba'i. Faɗin da'irarsa zai zama rabin kamu, kewayen gindinsa zai zama kamu ɗaya. Matakan bagaden za su fuskanci gabas.” 18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ni Ubangiji Allah, na ce waɗannan su ne ka'idodin bagaden. A ranar da za a kafa shi don miƙa hadayun ƙonawa da yayyafa jini a kansa, 19 sai ka ba firistoci na zuriyar Zadok, masu yi mini hidima, bijimai na yin hadaya domin zunubi. 20 Za ka ɗibi jininsa, ka shafa shi a kan zankaye huɗu na bagaden, da kan kusurwa huɗu na mahaɗin da kan da'irarsa. Ta haka za ka tsarkake bagaden, ka yi kafara dominsa. 21 Za ka kuma ɗauki bijimi na yin hadaya domin zunubi, ka kai shi waje, a wurin da aka shirya a bayan Haikalin, ka ƙone shi. 22 A kan rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin yin hadaya don zunubi, bagaden kuma zai tsarkaka, kamar yadda aka tsarkake shi da bijimin. 23 Sa'ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa bijimi da rago marar lahani. 24 Za ka kawo su a gaban Ubangiji, firistoci za su barbaɗe su da gishiri, su miƙa su hadayar ƙonawa ga Ubangiji. 25 Kowace rana za ka riƙa miƙa akuya, da bijimi, da rago, marasa lahani domin yin hadaya don zunubi, har kwana bakwai. 26 Za su yi kafara har kwana bakwai don su tsarkake bagaden, su keɓe shi. 27 Sa'ad da suka cika kwanakin nan bakwai, sa'an nan a kan rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayun ƙonawa da na salama a kan bagaden. Ni kuwa zan karɓe ku, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 44

Hidimar Haikali

1 Ya kuma komo da ni ƙofar waje ta Haikali wadda ke wajen gabas. Ƙofar kuwa tana rufe. 2 Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofa za ta kasance a rufe, ba za a buɗe ta ba, ba wanda kuma zai shiga ta cikinta, gama Ubangiji Allah na Isra'ila ya shiga ta cikinta, saboda haka za ta kasance a rufe. 3 Sai dai ɗan sarki zai zauna a cikinta ya ci abinci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin ƙofar, ya kuma fita ta wannan shirayi.” 4 Sa'an nan ya kawo ni a gaban haikalin ta hanyar ƙofar arewa. Da na duba, na ga zatin Ubangiji cike da Haikalin, sai na faɗi rubda ciki. 5 Ubangiji kuwa ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka gani da idanunka, ka kuma ji da kunnuwanka dukan abin da zan faɗa maka a kan dukan ka'idodin Haikalin Ubangiji da dukan dokokinsa. Ka lura sosai da waɗanda aka yardar musu su shiga Haikalin, da waɗanda ba a yarda musu su shiga ba. 6 “Ka ce wa 'yan tawaye, mutanen Isra'ila, ni Ubangiji Allah, na ce, ‘Ku daina ayyukanku na banƙyama. 7 Gama kuna ƙazantar da Haikalina ta wurin shigar da baƙi marasa imani da marasa kaciya, sa'ad da kuke miƙa mini hadayu na kitse da jini. Kun ta da alkawarina da ayyukanku na banƙyama. 8 Ba ku lura da hidimomina masu tsarki ba, amma kuka sa baƙi su lura da wurina mai tsarki.’ ” 9 Ubangiji Allah ya ce, “Ba wani baƙo marar imani da marar kaciya, daga cikin dukan baƙin da ke cikin jama'ata Isra'ila da zai shiga wurina mai tsarki. 10 “Amma Lawiyawa waɗanda suka yi nisa da ni, suka rabu da ni, suna bin gumakansu, sa'ad da mutanen Isra'ila suka karkata, za su ɗauki alhakin muguntarsu. 11 Za su zama masu hidima a cikin wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin Haikali, suna hidima a cikin Haikalin. Za su yanka hadayar ƙonawa da ta sadaka domin mutane. Za su lura da mutanen, su yi musu hidima. 12 Da ya ke sun hidimta wa mutane a gaban gumakansu, suka zama sanadin mugun tuntuɓe ga mutanen Isra'ila, don haka ni Ubangiji Allah, na yi rantsuwa cewa za su karɓi hakkin muguntarsu. 13 Ba za su zo kusa da ni a matsayin firistoci don su yi mini hidima ba. Ba za su zo kusa da abubuwana masu tsarki ba, amma za su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama. 14 Amma duk da haka zan sa su lura da Haikalin, su yi dukan hidimomin da za a yi a cikinsa. 15 “Amma Lawiyawan da suke firistoci daga zuriyar Zadok, waɗanda suka lura da Wuri Mai Tsarki sa'ad da mutanen Isra'ila suka karkace, suka bar bina, su ne za su zo kusa da ni, su yi mini hidima, za su kusace ni domin su miƙa hadaya ta kitse da jini, ni Ubangiji Allah na faɗa. 16 Za su shiga Wuri Mai Tsarki, su kusaci teburina, su yi mini hidima, su kuma kiyaye umarnina. 17 Sa'ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, sai su sa rigunan lilin, kada su sa abin da aka yi shi da ulu, sa'ad da suke hidima a ƙofofin fili na can ciki, da cikin Haikalin. 18 Za su naɗa rawunan lilin, su sa wandunan lilin. Kada su sa abin da zai sa su yi zuffa. 19 Sa'ad da suka fita zuwa filin da ke waje, wurin mutane, sai su tuɓe tufafin da suka yi hidima da su, su ajiye su a tsarkakakkun ɗakuna, sa'an nan su sa waɗansu tufafi domin kada su tsarkake mutane da tsarkakakkun tufafinsu. 20 “Ba za su aske kansu ba, ba kuma za su bar zankayensu su yi tsayi ba, sai su sausaye gashin kansu. 21 Kada firist ya sha ruwan inabi sa'ad da zai shiga fili na can ciki. 22 Ba za su auri gwauruwa ba, wato wadda mijinta ya rasu, ko sakakkiya, sai budurwa daga zuriyar Isra'ila, ko kuwa matar firist wanda ya rasu. 23 “Za su koya wa jama'ata bambancin halal da haram, su kuma nuna musu yadda za su rarrabe tsakanin tsattsarka da marar tsarki. 24 Za su zama masu raba gardama, za su yanke magana bisa ga doka. Za su kiyaye idodina bisa ga tsarinsu. Za su kuma kiyaye ranakun Asabar masu tsarki. 25 “Ba za su kusaci gawa ba, don kada su ƙazantar da kansu, amma saboda mahaifi, ko mahaifiya, ko ɗa, ko 'ya, ko 'yar'uwar da ba ta kai ga yin aure ba, ko ɗan'uwa, sa iya ƙazantar da kansu. 26 Bayan ya tsarkaka, sai ya dakata har kwana bakwai. 27 A ranar da zai shiga Wuri Mai Tsarki, can fili na ciki, domin ya yi hidima a wurin, sai ya miƙa hadayarsa don zunubi, ni Ubangiji Allah na faɗa. 28 “Ba za su sami rabon gādo ba, gama ni ne rabon gādonsu. Ba za ku ba su abin mallaka a cikin Isra'ila ba, ni ne abin mallakarsu. 29 Za su ci hadaya ta gari, da hadaya don zunubi, da hadaya domin laifi, kowane keɓaɓɓen abu kuma cikin Isra'ila zai zama nasu. 30 Dukan nunan fari, da kowace hadaya daga dukan hadayunku, za su zama na firistoci. Za ku ba firistoci tumun farinku don albarka ta kasance a gidajenku. 31 Firistoci ba za su ci mushen kowane irin tsuntsu ko dabba ba, ba kuma za su ci waɗanda wata dabba ta kashe ba.”

Ezekiyel 45

Yankin Ƙasar da za a Keɓe wa Ubangiji

1 “Sa'ad da kuka rarraba ƙasar gādo, sai ku keɓe wa Ubangiji wani wuri domin ya zama yanki mai tsarki, tsawonsa zai zama kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), faɗinsa kuwa kamu dubu goma (10,000 ). Dukan yankin zai zama wuri mai tsarki. 2 Daga cikin wannan, murabba'i mai tsawo kamu ɗari biyar, da faɗi ɗari biyar, zai zama wuri mai tsarki, fili kuma mai kamu hamsin zai kewaye wurin nan mai tsarki. 3 A cikin yanki mai tsarki za ka auna tsawo kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), da faɗi kamu dubu goma (10,000 ), inda Wuri Mafi Tsarki zai kasance. 4 Wannan yanki shi ne zai zama wuri mai tsarki na ƙasar. Zai zama na firistoci waɗanda ke hidima a cikin Haikali, waɗanda ke kusatar Ubangiji don su yi masa hidima. Wurin zai zama wurin gina gidajensu da kuma wuri mai tsarki domin Haikalin. 5 Wani sashi kuma mai tsawo kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), da faɗi kamu dubu goma (10,000 ), zai zama na Lawiyawa masu hidima cikin Haikalin, zai zama wurin da za su mallaka, su zauna a ciki. 6 Za ku tsaga wa birnin hurumi mai fāɗi kamu dubu biyar, da tsawo kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), rabe da yankin nan mai tsarki. Hurumin zai zama na mutanen Isra'ila duka.”

Ƙasar Sarki

7 “Ƙasar da ke a sashin yankin nan mai tsarki, da hurumin birnin, zai zama na sarki. Zai zama hannun riga da yanki mai tsarki da hurumin birnin a wajen yamma da gabas. Tsawonta zai zama daidai da yanki ɗaya na yankunan kabilan. Za ta miƙe daga yamma zuwa iyakar ƙasar daga gabas. 8 Wannan zai zama yankin ƙasarsa a cikin Isra'ila. Sarakunana kuma ba za su ƙara zaluntar mutanena ba, amma za su ba mutanen Isra'ila ƙasar bisa ga kabilansu.”

Ma'aunai na Gaskiya

9 “Ni Ubangiji Allah na ce ku sarakunan Isra'ila, danniya da zaluncin da kuke yi sun isa! Ku yi shari'a bisa ga gaskiya da adalci, ku bar korar mutanena, ni Ubangiji Allah na faɗa. 10 “Sai ku kasance da ma'aunai na gaskiya, kamar su mudu da garwa. 11 “Kwanon awo na mudu da na garwa girmansu ɗaya ne. Garwa goma ganga guda ne. Ganga ita ce za ta zama fitaccen ma'auni. 12 “Shekel zai zama gera ashirin. Mainanku ɗaya zai zama shekel sittin.”

Hadayu da Sadakoki

13 “Wannan ita ce bayarwar da za ku yi. Za ku ba da ɗaya daga cikin shida na mudu daga kowace ganga ta alkama, da ɗaya daga cikin shida na mudu daga kowace ganga ta sha'ir. 14 Za ku ba da ɗaya daga cikin goma ta garwa daga kowace ganga ta mai. Ganga tana cin garwa goma. 15 Za ku ba da tunkiya ɗaya daga kowane garke mai tumaki ɗari biyu, a cikin Isra'ila. “Waɗannan su ne hadayu na gari, da na ƙonawa, da na salama, domin a yi musu kafara, ni Ubangiji Allah na faɗa. 16 “Dukan mutanen ƙasar za su yi wannan bayarwar domin Sarkin Isra'ila. 17 Sarki ne da nawayar ba da hadayun ƙonawa, da na gari, da na sha a lokacin idodi da na amaryar wata, da ranakun Asabar, da lokacin dukan ƙayyadaddun idodin mutanen Isra'ila. Zai kuma ba da hadayu don zunubi da na salama domin a yi wa mutanen Isra'ila kafara.”

Idin Ƙetarewa

18 “Ni Ubangiji Allah na ce, rana ta fari ga watan fari, za ku ɗauki bijimi marar lahani don a tsarkake Haikalin. 19 Firist zai ɗibi jinin hadaya domin zunubi ya shafa shi a madogaran ƙofar Haikalin, da kusurwa huɗu na dakalin bagaden, da ginshiƙan ƙofar fili na can ciki. 20 Za ku yi haka kuma a rana ta bakwai ga watan, saboda wanda ya yi laifi da kuskure, ko da rashin sani. Ta haka ne za ku yi wa Haikalin kafara. 21 “A kan rana ta goma sha huɗu ga watan fari kuma za ku kiyaye Idin Ƙetarewa. Za ku riƙa cin abinci marar yisti har kwana bakwai. 22 A ranar, sarki zai ba da bijimi domin kansa da jama'ar ƙasar, saboda yin hadaya don zunubi. 23 A ranaku bakwai na Idin, zai ba da bijimi bakwai da raguna bakwai marasa lahani hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji. Kowace rana kuma zai ba da bunsuru hadaya don zunubi. 24 Zai kuma ba da hadaya ta gari, mudu guda domin kowane bijimi, da mudu guda domin kowane rago, da wajen kwalaba shida na mai tare da kowane mudu. 25 “A rana ta goma sha biyar ga watan bakwai, zai kuma ba da abubuwan nan har kwana bakwai domin yin hadaya don zunubi, da hadaya ta ƙonawa, da hadaya ta gari game da mai.”

Ezekiyel 46

Sarki da Hidimomin Idodi

1 “Ni Ubangiji Allah na ce za a rufe ƙofar fili ta can ciki wadda ke fuskantar gabas dukan ranaku shida na aiki, amma za a buɗe ta a ranar Asabar da a amaryar wata. 2 Sarki zai shiga ta ƙofar shirayi daga waje, sa'an nan ya tsaya kusa da ginshiƙin ƙofar. Sai firistoci su miƙa hadayarsa ta ƙonawa, da hadayunsa na salama, shi kuwa ya yi sujada s bakin ƙofar, sa'an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da maraice. 3 Jama'ar ƙasar za su yi wa Ubangiji sujada a bakin wannan ƙofa a ranakun Asabar da a amaryar wata. 4 Hadaya ta ƙonawa da sarki zai miƙa wa Ubangiji a ranar Asabar 'yan raguna shida ne da rago ɗaya marasa lahani. 5 Gārin hadaya da za a yi tare da rago wajen garwa guda ne. Wanda za a yi tare da 'yan raguna kuwa zai zama gwargwadon ƙarfinsa. Zai ba da mai wajen kwalaba shida domin kowace garwa ta gari. 6 A amaryar wata kuwa zai miƙa bijimi, da 'yan raguna shida, da rago, dukansu marasa lahani. 7 Gārin hadayar da za a yi tare da bijimin wajen garwa guda ne, haka kuma gari na wadda za a yi tare da ragon, da gari na wadda za a yi tare da 'yan raguna kuma, zai zama gwargwadon ƙarfinsa. Zai ba da man zaitun wajen kwalaba shida domin kowace garwa ta garin. 8 Sa'ad da sarki zai shiga, sai ya shiga ta ƙofar shirayin, ya kuma fita ta nan. 9 “Sa'ad da jama'ar ƙasar sun zo yi wa Ubangiji sujada a lokatan ƙayyadaddun idodi, wanda ya shiga ta ƙofar arewa, sai ya fita ta ƙofar kudu. Wanda kuma ya shiga ta ƙofar kudu, sai ya fita ta ƙofar arewa. Kada kowa ya fita ta ƙofar da ya shiga, amma sai kowa ya fita ta akasin ƙofar da ya shiga. 10 Sa'ad da suka shiga, sai sarki ya shiga tare da su, sa'ad da suka fita kuma, sai ya fita. 11 A lokacin idodi da ƙayyadaddun lokatai, gārin hadayar da za a yi tare da bijimi wajen garwa guda ne, haka kuma na wadda za a yi tare da ragon, na wadda za a yi tare da 'yan ragunan kuwa, sai mutum ya kawo gwargwadon ƙarfinsa. A kuma kawo wajen kwalaba shida na man zaitun domin kowace garwa ta gari. 12 “Sa'ad da sarki ya kawo hadayar ƙonawa ko hadayar salama ta yardar rai ga Ubangiji, sai a buɗe masa ƙofar da ke fuskantar gabas. Zai kuwa miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko ta salama kamar yadda yakan yi a ranar Asabar. Bayan da ya fita, sai a rufe ƙofa. 13 “Kowace safiya za a yi hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji da ɗan rago bana ɗaya marar lahani. 14 Tare da hadaya ta ƙonawa, za a ba da wajen ɗaya bisa shida na garwar gari, da kwalaba biyu na man zaitun don cuɗa gari, domin a yi hadaya ga Ubangiji. Wannan ita ce ka'idar hadaya ta ƙonawa ta yau da kullum. 15 Za a ba da ɗan rago, da gari, da mai, kowace safiya domin yin hadaya ta ƙonawa. 16 “Ni Ubangiji Allah na ce, idan sarki ya yi wa wani daga cikin 'ya'yansa kyauta daga cikin gādonsa, sai kyautar ta zama ta 'ya'yansa, dukiyarsu ce ta gādo. 17 Amma idan sarki ya yi wa wani daga cikin barorinsa kyauta daga cikin gādonsa, kyautar za ta zama tasa har shekarar 'yantarwa, sa'an nan kyautar za ta koma a hannun sarki. 'Ya'yansa maza ne kaɗai za su riƙe kyauta daga cikin gādonsa din din din. 18 Kada sarki ya ƙwace rabon gādon jama'a, ya hana musu. Sai ya ba 'ya'yansa maza rabon gādo daga cikin abin da ke nasa, amma kada ya ƙwace wa jama'ata abin da suka mallaka har su warwatse.” 19 Sai mutumin ya bi da ni ta hanyar da ke gefen ƙofa mai fuskantar arewa, wajen jerin tsarkakakkun ɗakuna na firistoci, waɗanda ke fuskantar arewa. Na kuma ga wani wuri daga can ƙurewar yamma. 20 Sai ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya domin laifi, da hadaya domin zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gāri, domin kada su kai su a filin waje, su sa wa mutane tsarki.” 21 Ya kuma kai ni a farfajiyar waje, ya bi da ni zuwa kusurwa huɗu na farfajiya. Akwai ɗan fili a kowace kusurwa. 22 Girman kowane ɗan fili tsawonsa kamu arba'in ne, faɗin kuma kamu talatin. 23 A cikin kowane ɗan fili na kusurwa huɗu ɗin akwai jerin duwatsu. Aka gina murhu ƙarƙashin jerin duwatsun. 24 Sa'an nan ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a Haikali za su dafa hadayun da jama'a suka kawo.”

Ezekiyel 47

Kogin da ke Malalowa daga Haikali

1 Ya komo da ni zuwa ƙofar Haikalin, sai ga ruwa yana bulbulowa daga ƙarƙashin bakin ƙofar Haikalin a wajen gabas, gama Haikalin na fuskantar gabas. Ruwan kuwa yana gangarowa daga gefen kudancin bakin ƙofar Haikalin, a kudancin bagaden. 2 Sai ya fito da ni ta hanyar ƙofar arewa, ya kewaya da ni zuwa ƙofar waje wadda take fuskantar gabas. Ruwan kuwa yana gangarowa kaɗan kaɗan daga wajen kudu. 3 Mutumin ya nufi wajen gabas da ma'auni a hannunsa, ya auna kamu dubu, sa'an nan ya sa ni in haye ruwan. Zurfin ruwan ya kama ni idon ƙafa. 4 Sai kuma ya auna kamu dubu, ya sa ni in haye ruwan. Zurfin ruwan kuwa ya kama ni gwiwa. Sai ya sāke auna kamu dubu, ya sa in haye ruwan, sai zurfin ruwan ya kai ga kama ni gindi. 5 Ya sāke auna kamu dubu kuma, sai ruwan ya zama kogi har ban iya in haye ba, gama ruwan ya hau, ya zama da zurfin da ya isa ninƙaya. Ya zama kogin da ba za a iya hayewa ba. 6 Sai ya tambaye ni, ya ce. “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa'an nan ya komo da ni zuwa gāɓar kogin. 7 Sa'ad da nake tafiya, sai na ga itatuwa da yawa a kowace gāɓar kogin. 8 Ya kuma ce mini, “Wannan ruwa yana gangarowa zuwa wajen gabas har zuwa cikin Araba. Zai shiga ruwan teku marar gudu, ruwan tekun kuwa zai zama ruwan daɗi. 9 Kowace halitta mai rai da ke cikin wannan ruwa za ta rayu. Za a sami kifaye da yawa a ciki, domin wannan ruwa zai kai wurin ruwan tekun, zai kuwa zama ruwan daɗi. Duk inda ruwan nan ya tafi kowane abu zai rayu. 10 Masunta za su tsaya a gāɓar tekun daga En-gedi zuwa En-eglayim. Gāɓar teku za ta zama wurin shanya taruna. Za a sami kifaye iri iri a cikinta kamar kifaye na Bahar Rum. 11 Amma ruwan fadamunsa ba zai yi daɗi ba, za a bar shi a gishirinsa. 12 A kowace gāɓar kogin, itatuwa iri iri na abinci za su yi girma. Ganyayensu ba za su bushe ba, itatuwan kuma ba za su fasa yin 'ya'ya ba, amma su za su yi ta bayarwa a kowane wata, gama ruwansu yana malalowa daga Haikalin. 'Ya'yansu abinci ne, ganyayensu kuwa magani ne.”

Iyakar Ƙasar

13 Ubangiji Allah ya ce, “Waɗannan su ne kan iyaka da za su raba ƙasar gādo ga kabilan Isra'ila goma sha biyu. Yusufu zai sami rabo biyu. 14 Za ku raba daidai, gama na rantse zan ba kakanninku wannan ƙasa, za ta kuwa zama gādonku. 15 “A wajen arewa, iyakar za ta kama daga Bahar Rum, ta bi ta hanyar Hetlon zuwa Zedad, 16 da Hamat, da Berota, da Sibrayim, wadda ke a iyakar tsakanin Dimashƙu da Hamat, har zuwa Hazer-hattikon wadda ke iyakar Hauran. 17 Iyakar za ta bi daga teku zuwa Hazar-enan wadda ke iyakar Dimashƙu. Iyakar Hamat tana wajen arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa. 18 “A wajen gabas, iyakar za ta kama daga Hazar-enan tsakanin Hauran da Dimashƙu, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra'ila zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas. 19 “A wajen kudu, iyakar za ta kama daga Tamar har zuwa ruwan Meribakadesh, ta bi ta rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu. 20 “A wajen yamma, Bahar Rum shi ne iyakar zuwa ƙofar Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma. 21 “Za ku kuwa raba ƙasar a tsakaninku bisa ga kabilan Isra'ila. 22 Za ku raba ƙasar gādo a tsakaninku da baƙin da ke zaune tare da ku, waɗanda suka haifi 'ya'ya a cikinku. Za su zama kamar 'ya'yan Isra'ila haifaffu na gida. Za a ba su gādo tare da kabilan Isra'ila, 23 a cikin kabilar da baƙon yake zaune, nan ne za ku ba shi nasa gādo, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ezekiyel 48

Rarraba Ƙasar

1 “Ga sunayen kabilan da rabon gādonsu. Yankin Dan, shi ne daga iyakar arewa daga tekun. Ya bi ta Hetlon zuwa ƙofar Hamat, har zuwa Hazar-enan wadda ke iyakar Dimashƙu daga arewa, daura da Hamat. Ya zarce daga gabas zuwa yamma. 2 Yankin Ashiru yana kusa da yankin Dan, daga gabas zuwa yamma. 3 Yankin Naftali yana kusa da yankin Ashiru daga gabas zuwa yamma. 4 Yankin Manassa yana kusa da yankin Naftali daga gabas zuwa yamma. 5 Yankin Ifraimu yana kusa da yankin Manassa daga gabas zuwa yamma. 6 Yankin Ra'ubainu yana kusa da yankin Ifraimu daga gabas zuwa yamma. 7 Yankin Yahuza yana kusa da yankin Ra'ubainu daga gabas zuwa yamma. 8 “Kusa da yankin Yahuza daga gabas zuwa yamma, sai yankin da za ku keɓe. Faɗinsa kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), tsawonsa kuma daidai da tsawon yankunan kabilai daga gabas zuwa yamma. Haikali zai kasance a tsakiyar yankin. 9 “Yankin da za ku keɓe wa Ubangiji, tsawonsa zai zama kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), faɗinsa kuwa kamu dubu goma (10,000 ). 10 Wannan tsattsarkan yanki shi ne rabon firistoci. Tsawonsa wajen arewa, kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ) ne, faɗinsa a wajen yamma kuwa, kamu dubu goma (10,000 ) ne, a wajen gabas faɗinsa kamu dubu goma (10,000 ), a wajen kudu tsawonsa kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ). Haikalin Ubangiji zai kasance a tsakiyarsa. 11 Wannan zai zama na keɓaɓɓun firistoci daga zuriyar Zadok waɗanda suka kiyaye umarnina, ba su karkace kamar yadda Lawiyawa suka yi lokacin da jama'ar Isra'ila suka karkace ba. 12 Zai zama rabonsu daga tsattsarkan yankin ƙasar da ke kusa da yankin Lawiyawa. 13 Gab da yankin firistoci, Lawiyawa za su sami rabo mai tsawon kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), faɗi kuma kamu dubu goma (10,000 ). Tsawonsa duka zai zama kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), faɗi kuwa kamu dubu goma (10,000 ). 14 Daga cikinsa ba za su sayar ba, ko su musayar, ba kuma za su jinginar da wannan keɓaɓɓen yankin ƙasa ba, gama tsattsarka ne na Ubangiji. 15 “Ragowar yankin mai faɗin kamu dubu biyar (5,000 ), da tsawon kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), zai zama hurumin birnin, inda za a yi gidaje da wurin kiwo. Birnin zai kasance a tsakiyar yankin. 16 Ga yadda girman birnin zai kasance, a wajen arewa kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ), a wajen kudu kuwa kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ), a wajen gabas kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ), a wajen yamma kuma kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ). 17 Birnin zai kasance da hurumi a kewaye da shi. A wajen gabas kamu metan da hamsin, a wajen yamma kamu metan da hamsin, a wajen kudu kamu metan da hamsin, a wajen arewa kuma kamu metan da hamsin. 18 Ragowar tsawon yankin da ke gab da tsattsarkan yankin, zai zama kamu dubu goma (10,000 ) a wajen gabas, a wajen yamma kamu dubu goma (10,000 ). Amfanin da yankin zai bayar, zai zama abincin ma'aikatan birnin. 19 Ma'aikatan birnin za su samu daga dukan kabilan Isra'ila, za su noma yankin. 20 “Dukan yankin da za ku keɓe zai zama murabba'i mai kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ), wato tsattsarkan yankin tare da hurumin birnin. 21 “Ragowar kowane gefe na tsattsarkan yankin da hurumin birnin, zai zama na sarki. Tun daga kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ) na tsattsarkan yankin, zuwa iyakar da ke wajen gabas, daga kamu dubu ashirin da dubu biyar (25,000 ) kuma zuwa iyakar wajen yamma, hannun riga da yankunan kabilan zai zama na sarki. Tsattsarkan yankin da wuri mai tsarki na Haikali za su kasance a tsakiyarsa. 22 Rabon Lawiyawa da hurumin birnin za su kasance a tsakiyar yankin da ke na ɗan sarki. Yankin ɗan sarki zai kasance a tsakanin yankin Yahuza da yankin Biliyaminu. 23 “Sauran kabilan kuwa za su samu. Biliyaminu zai sami yankinsa daga gabas zuwa yamma. 24 Yankin Saminu yana kusa da yankin Biliyaminu daga gabas zuwa yamma. 25 Yankin Issaka yana kusa da yankin Saminu daga gabas zuwa yamma. 26 Yankin Zabaluna yana kusa da yankin Issaka daga gabas zuwa yamma. 27 Yankin Gad yana kusa da yankin Zabaluna daga gabas zuwa yamma. 28 “Kusa da yankin Gad zuwa kudu, iyakar za ta bi ta Tamar zuwa ruwan Meriba-kadesh, sa'an nan ta bi rafin Masar zuwa Bahar Rum.” 29 Ubangiji ya ce, “Wannan ita ce hanyar da za ku raba gādo tsakanin kabilan Isra'ila. Waɗannan kuwa su ne yankunansu, ni Ubangiji Allah na faɗa.”

Ƙofofin Birni

30 “Ƙofofin birnin a gefen arewa, kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ) ne. 31 Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Ra'ubainu, da Ƙofar Yahuza, da Ƙofar Lawi. Ana kiran sunayen ƙofofin birnin da sunayen kabilan Isra'ila. 32 A gefen gabas, kamu dubu huɗu ne da ɗari biyar (4,500 ). Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Yusufu, da Ƙofar Biliyaminu, da Ƙofar Dan. 33 A gefen kudu, kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ). Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Saminu, da Ƙofar Issaka, da Ƙofar Zabaluna. 34 A gefen yamma, kamu dubu huɗu da ɗari biyar (4,500 ) ne. Ƙofofi uku ne, wato Ƙofar Gad, da Ƙofar Ashiru, da Ƙofar Naftali. 35 Da'irar birnin kamu dubu goma sha takwas (18,000 ) ne. Daga wannan lokaci za a kira birnin, ‘Ubangiji Yana Nan!’ ”

Daniyel 1

Tarbiyyar Daniyel da Abokansa

1 A shekara ta uku ta mulkin Yehoyakim, Sarkin Yahuza, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babila, ya zo Urushalima ya kewaye ta da yaƙi. 2 Ubangiji kuwa ya ba Nebukadnezzar nasara a kan Yehoyakim, Sarkin Yahuza, sai ya kwashe waɗansu kayayyakin Haikalin Allah, ya kawo su ƙasar Shinar a gidan gunkinsu, ya ajiye kayayyakin a baitulmalin gunkinsa. 3 Sa'an nan Sarkin Babila ya umarci sarkin fādarsa, Ashfenaz, ya zaɓo masa waɗansu samari daga cikin Yahudawa, waɗanda ke daga gidan sarauta, da kuma daga gidan manya, 4 su kasance samari ne kyawawa, waɗanda ba su da wata naƙasa, masu fasaha cikin kowane abu, masu fahimta, da masu saurin ganewa, waɗanda suke da halin iya hidima a fādar sarki. Nebukadnezzar ya umarci Ashfenaz ya koya musu littattafan Kaldiyawa da harshen Kaldiyawa. 5 Sarki kuwa ya sa a riƙa ba su abinci da ruwan inabi irin nasa kowace rana. A kuma koyar da su har shekara uku. Bayan shekara uku za su shiga yi wa sarki hidima. 6 A cikin waɗanda aka zaɓa akwai Daniyel, da Hananiya, da Mishayel, da Azariya, daga kabilar Yahuza. 7 Sai sarkin fāda ya laƙaba musu sababbin sunaye. Ya kira Daniyel, Belteshazzar, ya kira Hananiya, Shadrak, ya kira Mishayel, Meshak, sa'an nan ya kira Azariya, Abed-nego. 8 Daniyel kuwa ya ƙudura a ransa, ba zai ƙazantar da kansa da cin abinci iri na sarki da shan ruwan inabinsa ba, don haka ya roƙi sarkin fāda, kada ya ba shi wannan abinci da zai ƙazantar da shi. 9 Allah kuwa ya sa Daniyel ya sami farin jini da soyayya a wurin sarkin fāda. 10 Sa'an nan sarkin fāda ya ce wa Daniyel, “Ina jin tsoro kada shugaban sarki wanda ya umarta a riƙa ba ku wannan abinci da ruwan inabi ya ga jikinku ba su yi kyau kamar na samarin tsaranku ba, ta haka za ku sa in shiga uku a wurin sarki.” 11 Sai Daniyel ya ce wa baran da sarkin fāda ya sa ya lura da su Daniyel, da Hananiya, da Mishayel, da Azariya, 12 “Ka jarraba barorinku har kwana goma. A riƙa ba mu kayan lambu mu ci, a kuma riƙa ba mu baƙin ruwa mu sha. 13 Sa'an nan ka duba fuskokinmu da na samari waɗanda ke cin abinci irin na sarki. Ka yi da barorinku gwargwadon yadda ka gan mu.” 14 Ya yarda da abin da Daniyel ya ce, ya kuwa jarraba su har kwana goma ɗin. 15 A ƙarshen kwana goma ɗin, sai aka ga fuskokinsu suna sheƙi, sun kuma yi ƙiba fiye da samarin da ke cin abinci irin na sarki. 16 Don haka baran ya janye shirin ba su abinci da ruwan inabi irin na sarki, ya ci gaba da ba su kayan lambu. 17 Waɗannan samari huɗu kuwa, Allah ya ba su ilimi, da sanin littattafai, da hikima. Ya kuma yi wa Daniyel baiwar ganewar wahayi da mafarkai. 18 Sa'ad da lokacin da sarki ya ƙayyade ya ƙare, sarkin fāda ya gabatar da su a gaban Nebukadnezzar. 19 Da sarki ya yi magana da su, sai ya tarar a cikinsu duka, ba wani kamar Daniyel, da Hananiya, da Mishayel, da Azariya. Don haka aka maishe su 'yan majalisar sarki. 20 A cikin dukan abin da ya shafi hikima da ganewa wanda sarki ya nemi shawararsu, sai ya tarar sun fi dukan masu sihiri da bokaye waɗanda ke cikin mulkinsa har sau goma. 21 Daniyel kuwa ya ci gaba har shekarar farko ta sarki Sairus.

Daniyel 2

Daniyel ya Fasarta Mafarkin Nebukadnezzar

1 Nebukadnezzar ya yi mafarki a shekara ta biyu ta sarautarsa, ya kuwa damu ƙwarai har barci ya gagare shi. 2 Sai sarki ya umarta a kirawo masa masu sihiri, da masu dabo, da bokaye, da Kaldiyawa, su zo su fassara masa mafarkin da ya yi. Sai suka hallara a gaban sarki. 3 Sarki kuwa ya ce musu, “Na yi mafarki, na kuwa matsu ƙwarai in san mafarkin.” 4 Sai Kaldiyawa suka yi magana da sarki da Aramiyanci, suka ce, “Ran sarki ya daɗe! Ka faɗa wa barorinka mafarkin, za mu kuwa yi maka fassararsa.” 5 Sai sarki ya amsa wa Kaldiyawa, ya ce, “Na mance da abin, idan ba ku tuno mini da mafarkin, duk da fassararsa ba, to, za a daddatse ku gunduwa gunduwa, a mai da gidajenku juji. 6 Amma idan kun tuna mini mafarkin, duk da fassararsa, to, zan ba ku lada, da kyautai, da girma mai yawa. Don haka sai ku faɗa mini mafarkin, duk da fassararsa.” 7 Suka amsa, suka ce, “Bari sarki ya faɗa wa barorinsa mafarkin, mu kuwa za mu yi maka fassararsa.” 8 Sarki kuwa ya amsa ya ce, “Na sani kuna ƙoƙari ku ɓata lokaci ne kawai domin kun ga na manta da abin. 9 Idan ba ku tuno mini da mafarkin ba, hukuncin kisa ne ke jiranku. Kun haɗa kai don ku yi mini maganganun ƙarya na wofi har lokaci ya wuce. Sai ku faɗa mini mafarkin, ta haka kuwa zan sani za ku iya yi mini fassararsa.” 10 Sa'an nan Kaldiyawa suka amsa wa sarki, suka ce, “Ba wani mahaluki a duniya wanda zai iya biyan wannan bukata ta sarki, gama ba wani sarki wanda ya taɓa yin irin wannan tambaya a wurin mai sihiri, ko mai dabo, ko Bakaldiye. 11 Abin nan da sarki ke so a yi masa yana da wuya, ba wanda zai iya biya wa sarki wannan bukata, sai dai ko alloli waɗanda ba su zama tare da 'yan adam.” 12 Saboda haka sarki ya husata ƙwarai, ya umarta a karkashe duk masu hikima na Babila. 13 Sai doka ta fita cewa a karkashe masu hikima. Aka nemi Daniyel da abokansa don a kashe su. 14 Daniyel kuwa ya amsa wa Ariyok, shugaban dogaran sarki, a hankali da hikima, sa'ad da Ariyok ya fita don ya karkashe masu hikima na Babila. 15 Daniyel ya ce wa Ariyok shugaban dogaran sarki, “Me ya sa ake gaggauta dokar sarki haka?” Sai Ariyok ya bayyana wa Daniyel yadda al'amarin yake. 16 Sa'an nan Daniyel ya shiga wurin sarki, ya roƙe shi ya ba shi lokaci domin ya yi masa fassarar. 17 Sai Daniyel ya tafi gidansa, ya sanar wa abokansa, wato su Hananiya, da Mishayel, da Azariya da al'amarin. 18 Ya faɗa musu su nemi jinƙai daga wurin Allah na Sama game da wannan matsala, domin kada Daniyel da abokansa su halaka tare da sauran masu hikima a Babila. 19 Sai aka bayyana wa Daniyel asirin ta cikin wahayi da dare. Daganan Daniyel ya yabi Allah na Sama. 20 Ya ce, “Yabo ya tabbata ga sunan Allah har abada abadin, Wanda hikima da iko nasa ne. 21 Yana da ikon sāke lokatai, Yakan tuɓe sarakuna, ya kuma naɗa waɗansu. Yana ba masu hikima hikima, masu ilimi kuwa fahimi, 22 Yana bayyana zurfafan abubuwa masu wuyar ganewa, Ya san abin da ke cikin duhu. Haske kuma yana zaune tare da shi. 23 A gare ka nake ba da godiya da yabo, ya Allah na kakannina, Gama ka ba ni hikima da iko, Har ka sanar mini da abin da muka roƙe ka, Ka sanar mana da matsalar da ta dami sarki.” 24 Sa'an nan Daniyel ya tafi wurin Ariyok wanda sarki ya sa ya karkashe masu hikima na Babila, ya ce masa, “Kada ka karkashe masu hikima na Babila, ka kai ni gaban sarki, ni kuwa zan yi wa sarki fassarar.” 25 Nan da nan kuwa Ariyok ya kai Daniyel gaban sarki, ya ce masa, “Na sami wani daga cikin kamammun ƙasar Yahuza wanda zai iya sanar wa sarki da fassarar.” 26 Sarki kuwa ya ce wa Daniyel, mai suna Belteshazzar, “Ka iya faɗa mini mafarkin duk da fassararsa?” 27 Daniyel ya amsa wa sarki, ya ce, “Ba masu hikima, ko masu dabo, ko masu sihiri, ko masu duba, da za su iya su warware wa sarki wannan matsala da ta dame shi. 28 Amma akwai Allah a Sama mai bayyana asirai, shi ne ya sanar wa sarki Nebukadnezzar da abin da zai faru a kwanaki masu zuwa. Mafarkinka da wahayinka waɗanda suka zo cikin tunaninka, sa'ad da kake kwance bisa gadonka ke nan. 29 “Ya maigirma, sa'ad da kake kwance a gadonka sai tunanin abin da zai faru nan gaba ya zo maka. Shi kuma wanda ke bayyana asirai ya sanar da kai abin da zai faru nan gaba. 30 Amma ba a bayyana mini wannan asiri saboda ina da wata hikima fiye da sauran mutane ba, sai dai domin a sanar wa sarki da fassarar, ka kuma san tunanin da ya shiga zuciyarka. 31 “Ya sarki, ka ga wani babban mutum-mutum mai walƙiya, mai bantsoro, yana tsaye a gabanka. 32 An yi kan mutum-mutumin da zinariya tsantsa. Ƙirji da damutsa, an yi su da azurfa, cikinsa da cinyoyinsa, an yi su da tagulla. 33 Da baƙin ƙarfe aka yi sharaɓansa, an yi ƙafafunsa da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu. 34 Sa'ad da kake cikin dubawa, sai aka gutsuro wani dutse ba da hannun mutum ba, aka bugi ƙafafunsa na baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, aka ragargaza shi. 35 Sa'an nan baƙin ƙarfen, da yumɓun, da tagullar, da azurfar, da zinariyar suka ragargaje gaba ɗaya, duka suka zama kamar ƙaiƙayi na masussuka da kaka. Iska kuwa ta kwashe su ta tafi da su, har ba a iya ganin ko alamarsu. Amma wannan dutse da ya buge mutum-mutumin ya girke, ya zama babban dutse ya cika duniya duka. 36 “Wannan shi ne mafarkin, yanzu kuma za mu faɗa wa sarki fassararsa. 37 Ya sarki, kai ne sarkin sarakuna wanda Allah na Sama ya ba ka sarauta, da iko, da ƙarfi, da daraja. 38 A hannunka kuma ya ba da dukan wurare inda 'yan adam, da dabbobi, da tsuntsaye suke zama. Ya sa ka ka mallake su duka. Kai ne kan zinariyan nan na mutum-mutumin. 39 A bayanka kuma za a yi wani mulki wanda bai kai kamar naka ba. Za a yi wani mulki kuma na uku mai darajar tagulla, wanda zai mallaki dukan duniya. 40 Za a kuma yi mulki na huɗu, mai ƙarfi kamar baƙin ƙarfe. Da ya ke baƙin ƙarfe yakan kakkarya, ya ragargaje abubuwa, hakanan wannan mulki zai ragargaje sauran mulkoki. 41 Ka kuma ga an yi ƙafafun da yatsotsin da baƙin ƙarfe gauraye da yumɓu, wato mulkin zai rabu, amma zai kasance da ƙarfi kamar na baƙin ƙarfe da ke gauraye da yumɓu. 42 Kamar yadda yatsotsin ƙafafun rabi baƙin ƙarfe, rabi kuma yumɓu ne, hakanan mulkin zai kasance, rabi da ƙarfi, rabi kuma da gautsi. 43 Kamar yadda ka ga baƙin ƙarfen ya gauraya da yumɓun, hakanan mulkokin za su gauraye da juna ta wurin aurayya, amma ba za su haɗu da juna ba, kamar yadda baƙin ƙarfe da yumɓu ba su haɗuwa. 44 A kwanakin waɗannan sarakuna, Allah na Sama zai kafa wani mulki wanda ba zai taɓa rushewa ba har abada, ba kuma za a gādar da shi ga waɗansu mutane ba. Wannan mulki zai ragargaje dukan waɗannan mulkoki, ya kawo ƙarshensu. Wannan mulki zai dawwama har abada. 45 Kamar yadda ka ga an gutsuro dutse ba da hannun ɗan adam ba, ya kuwa ragargaje baƙin ƙarfen, da tagullar, da yumɓun, da azurfar, da zinariyar, Allah Maɗaukaki ya sanar wa sarki abin da zai faru nan gaba. Mafarkin tabbatacce ne, fassarar kuma gaskiya ce.”

Sarki ya Girmama Daniyel

46 Sarki Nebukadnezzar kuwa ya fāɗi a gaban Daniyel, ya gaishe shi, sa'an nan ya umarta a miƙa hadaya, da hadaya ta turare ga Daniyel. 47 Ya kuma ce wa Daniyel, “Hakika, Allahnka, Allahn alloli ne da Ubangijin sarakuna, mai bayyana asirai, gama ka iya bayyana wannan asiri.” 48 Sai sarki ya ba Daniyel girma mai yawa, da manya manyan kyautai masu yawa. Ya kuma naɗa shi mai mulki bisa dukan lardin Babila. Ya shugabantar da shi bisa dukan masu hikima waɗanda ke Babila. 49 Daniyel kuwa ya roƙi sarki ya naɗa Shadrak, da Meshak, da Abed-nego su zama masu kula da harkokin lardin Babila, amma Daniyel yana fādar sarki.

Daniyel 3

Ceto daga Tanderun Gagarumar Wuta

1 Sarki Nebukadnezzar ya yi gunki na zinariya wanda tsayinsa kamu sittin ne, fāɗinsa kuma kamu shida. Ya kafa shi a filin Dura wanda ke a lardin Babila. 2 Sa'an nan ya aika a kirawo su hakimai, da wakilai, da su muƙaddasai, da 'yan majalisa, da su ma'aji, da alƙalai, da masu mulki, da dukan ma'aikatan larduna, su zo, su halarci bikin keɓewar gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa. 3 Sai hakimai, da wakilai, da su muƙaddasai, da 'yan majalisa, da su ma'aji, da alƙalai, da masu mulki, da dukan ma'aikatan larduna suka taru don keɓewar gunkin da sarki Nebukadnezzar ya kafa. Suka kuma tsaya a gaban gunkin. 4 Mai shela ya ta da murya da ƙarfi, ya ce, “An umarce ku, ya ku jama'a, da al'ummai, da harsuna mabambanta, 5 cewa sa'ad da kuka ji ƙarar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo, da algaita, da kowane irin abin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, sai ku fāɗi, ku yi sujada ga gunkin zinariyan nan da sarki Nebukadnezzar ya kafa. 6 Duk wanda bai fāɗi ƙasa ya yi sujada ba, nan take za a jefa shi a tanderun gagarumar wuta.” 7 Don haka da dukan mutane, da al'ummai, da harsuna mabambanta sun ji ƙarar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo, da algaita, da kowane irin abin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, sai suka fāɗi ƙasa, suka yi sujada ga gunkin zinariya wanda sarki Nebukadnezzar ya kafa. 8 A lokacin sai waɗansu Kaldiyawa suka tafi, suka yi ƙarar Yahudawa. 9 Suka ce wa sarki Nebukadnezzar, “Ranka ya daɗe. 10 Kai ne ka yi doka, cewa duk mutumin da ya ji ƙarar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo, da algaita, da kowane irin abin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, sai ya fāɗi ƙasa, ya yi sujada ga gunkin zinariya. 11 Duk wanda bai faɗi ƙasa ya yi sujada ba, za a jefa shi a tanderun gagarumar wuta. 12 Akwai waɗansu Yahudawa waɗanda ka naɗa su su lura da harkokin lardin Babila, wato Shadrak, da Meshak, da Abed-nego. Waɗannan mutane fa, ya sarki, ba su kula da kai ba, ba su bauta wa allolinka ba, ba su kuma yi sujada ga gunkin zinariya da ka kafa ba.” 13 Nebukadnezzar fa, ya husata ya umarta a kawo Shadrak, da Meshak, da Abed-nego. Sai aka kawo su gaban sarki. 14 Nebukadnezzar ya ce musu, “Ko gaskiya ne, wai kai Shadrak, da Meshak, da Abed-nego ba ku bauta wa allolina ba, ba ku kuma yi sujada ga gunkin zinariya da na kafa ba? 15 Yanzu, idan kuna so, sa'ad da kuka ji ƙarar ƙaho, da sarewa, da garaya, da goge, da molo, da algaita, da kowane irin abin kaɗe-kaɗe da bushe-bushe, sai ku fāɗi ƙasa, ku yi sujada ga gunkin zinariya da na kafa. Idan kun yi haka, da kyau. Amma idan ba ku yi sujadar ba, nan take za a jefa ku a tanderun gagarumar wuta, in ga kowanene allahn nan da zai kuɓutar da ku daga hannuna?” 16 Shadrak, da Meshak, da Abed-nego kuwa suka amsa wa sarki suka ce, “Ya maigirma Nebukadnezzar, ba mu bukatar mu amsa maka da kome a kan wannan al'amari. 17 Idan haka ne, Allahnmu wanda muke bauta wa, yana da iko ya cece mu daga tanderun gagarumar wuta, zai kuwa kuɓutar da mu daga hannunka, ya sarki. 18 Ko ma bai cece mu ba, ka sani fa ya sarki, ba za mu bauta wa allolinka, ko kuma mu yi wa gunkin zinariya da ka kafa sujada ba.” 19 Sai Nebukadnezzar ya husata ƙwarai da Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, har fuskarsa ta sāke. Sai ya umarta a ƙara zuga wutar, har sau bakwai fiye da yadda take a dā. 20 Sa'an nan ya umarci waɗansu ƙarfafan mutane daga cikin sojojinsa su ɗaure Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, su jefa su a tanderun gagarumar wuta. 21 Sai aka ɗaure su suna saye da rigunansu da wandunansu, da hulunansu, da sauran tufafinsu, aka jefa su a tanderun gagarumar wuta. 22 Tsananin umarnin sarki ya sa aka haɓaka wutar, sai harshen wutar ya kashe waɗanda suka jefa su Shadrak, da Meshak, da Abed-nego cikin wutar. 23 Sa'an nan mutanen nan uku, wato Shadrak, da Meshak, da Abed-nego suka faɗi a tanderun gagarumar wuta a ɗaure. 24 Sarki Nebukadnezzar kuwa ya zabura ya miƙe tsaye, cike da mamaki. Ya ce wa manyan fādawansa, “Ashe, ba mutum uku ne muka jefa a wuta ba?” Su kuwa suka amsa wa sarki suka ce, “Ba shakka, haka yake, ranka ya daɗe.” 25 Sarki ya ce, “Amma ina ganin mutum huɗu a sake, suna tafiya a tsakiyar wuta, ba kuma abin da ya same su, kamannin na huɗun kuwa kamar na ɗan alloli.”

An Saki Samari Uku na Yahudawa tare da Ƙarin Girma

26 Nebukadnezzar fa ya matso kusa da ƙofar tanderun gagarumar wuta, ya ce, “Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, bayin Allah Maɗaukaki, ku fito, ku zo nan!” Sai Shadrak, da Meshak, da Abed-nego suka fita daga cikin wutar. 27 Sa'an nan su hakimai, da wakilai, da muƙaddasai, da manyan 'yan majalisa suka taru, suka ga lalle wutar ba ta yi wa jikunan mutanen nan lahani ba, gashin kawunansu bai ƙuna ba, tufafinsu ba su ci wuta ba, ko warin wuta babu a jikinsu. 28 Nebukadnezzar ya ce, “Yabo ya tabbata ga Allah na Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, wanda ya aiko da mala'ikansa, ya ceci bayinsa masu dogara gare shi, waɗanda kuma ba su yarda su bi umarnin sarki ba, amma suka gwammace a ƙone su maimakon su bauta wa gunki, ko su yi masa sujada, sai dai ga Allahnsu kaɗai. 29 Domin haka ina ba da wannan umarni cewa, ‘Dukan jama'a, ko al'umma, ko harshe wanda zai yi saɓon Allah na Shadrak, da Meshak, da Abed-nego, za a yanyanka su gunduwa gunduwa, a ragargaje gidajensu, gama ba wani allah wanda zai yi wannan irin ceto.’ ” 30 Sa'an nan sarki ya ƙara wa Shadrak, da Meshak, da Abed-nego girma a lardin Babila.

Daniyel 4

Haukar Nebukadnezzar

1 “Daga sarki Nebukadnezzar zuwa ga dukan mutane, da al'ummai, da harsuna mabambanta waɗanda ke zaune a duniya duka. Salama mai yawa ta tabbata a gare ku! 2 Na ga ya yi kyau in sanar muku da alamu da abubuwan al'ajabi waɗanda Allah Maɗaukaki ya nuna mini. 3 “Alamunsa da girma suke! Al'ajabansa da bantsoro suke! Sarautarsa ta har abada ce, Mulkinsa kuma daga zamani zuwa zamani ne. 4 “Ni, Nebukadnezzar ina cikin gidana, ina nishaɗi a fādata. 5 Sa'ad da nake kwance a gādona, sai na yi mafarki wanda ya tsorata ni. Tunanina da wahayi suka firgitar da ni. 6 Don haka na umarta a kirawo mini dukan masu hikima na Babila don su yi mini fassarar mafarkin. 7 Sai masu sihiri, da masu dabo, da Kaldiyawa, da masu duba suka zo, na faɗa musu mafarkin, amma ba su iya yi mini fassararsa ba. 8 Daga baya sai Daniyel wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar, wato irin sunan allahna, yana kuwa da ruhun alloli tsarkaka, ya shigo wurina. Na kuwa faɗa masa mafarkin, na ce, 9 ‘Ya Belteshazzar shugaban masu sihiri, tun da ya ke na san ruhun alloli tsarkaka yana a cikinka, ba wani asirin da zai fi ƙarfin ganewarka. Ga mafarkin da na yi, sai ka faɗa mini fassararsa. 10 “ ‘Wahayin da na gani ke nan sa'ad da nake kwance a gadona. Na ga wani itace mai tsayi ƙwarai a tsakiyar duniya. 11 Itacen ya yi girma, ya ƙasaita, Ƙwanƙolinsa ya kai har sama, Ana iya ganinsa ko'ina a duniya. 12 Yana da ganyaye masu kyau Da 'ya'ya jingim don kowa da kowa ya ci. Namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa, Tsuntsayen sama kuma suka zauna a rassansa. Dukan masu rai a gare shi suka sami abinci. 13 “ ‘A cikin wahayin da na gani sa'ad da nake kwance a gado, sai ga wani mai tsaro, tsattsarka, ya sauko daga sama. 14 Sai ya yi magana da ƙarfi, ya ce, “A sare itacen, a daddatse rassansa, A zage ganyayensa ƙaƙaf, a warwatsar da 'ya'yansa. A sa namomin jeji su gudu daga ƙarƙashinsa, Tsuntsaye kuma su tashi daga rassansa. 15 Amma a bar kututturen da saiwoyinsa a ƙasa Ɗaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla. A bar shi can cikin ɗanyar ciyawar saura, Ya jiƙe da raɓa, Ya yi ta cin ciyawa tare da namomin jeji. 16 A raba shi da hankali irin na mutane, A ba shi irin na dabba. Zai zauna a wannan hali har shekara bakwai. 17 Wannan shi ne hukuncin da tsarkaka, Masu tsaro suka shawarta, Suka yanke domin masu rai su sani Maɗaukaki ke sarautar 'yan adam, Yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama, Yakan sa talaka ya zama sarki.” 18 “ ‘Mafarkin da ni sarki Nebukadnezzar na yi ke nan. Kai Belteshazzar kuma, sai ka faɗa mini ma'anarsa, domin dukan masu hikima na cikin mulkina ba su iya faɗar mini ma'anar, amma kai ka iya, gama ruhun alloli tsarkaka yana cikinka.’ ”

Daniyel ya Faɗi Ma'anar Mafarkin

19 Daniyel kuwa wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar, ya tsaya zugum da ɗan daɗewa, tunaninsa ya ba shi tsoro. Sarki ya ce, “Belteshazzar, kada ka bar mafarkin ko ma'anarsa ya ba ka tsoro.” Sai Belteshazzar ya amsa, ya ce, “Ya shugabana, Allah ya sa mafarkin nan, da ma'anarsa, su zama a kan maƙiyanka. 20 Itacen nan da ka gani wanda ya yi girma, ya ƙasaita, ƙwanƙolinsa ya kai sama, har ana iya ganinsa daga ko'ina a duniya, 21 yana da ganyaye masu kyau da 'ya'ya jingim don kowa da kowa ya ci, namomin jeji suka sami inuwa a ƙarƙashinsa, tsuntsaye kuma suka zauna a rassansa, 22 kai ne wannan itace, ya sarki. Ka yi girma, ka ƙasaita. Girmanka ya kai har sama, mulkinka kuma ya kai ko'ina a duniya. 23 Ka kuma ga mai tsaro tsattsarka yana saukowa daga sama, yana cewa a sare itacen nan, a ragargaje shi, amma a bar kututturen da saiwoyinsa cikin ƙasa ɗaure da sarƙar baƙin ƙarfe da tagulla. An ce a bar shi can a ɗanyar ciyawar saura, ya jiƙe da raɓa, ya zauna tare da namomin jeji har shekara bakwai. 24 “Ga ma'anarsa, ya sarki, wannan ƙaddara ce wadda Maɗaukaki zai aukar wa shugabana sarki da ita. 25 Za a kore ka daga cikin mutane zuwa jeji ka zauna tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa, za ka jiƙe da raɓa har shekara bakwai cur, sa'an nan za ka sani Maɗaukaki ne ke sarautar 'yan adam, yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama. 26 Kamar yadda aka umarta a bar kututturen itacen da saiwoyinsa, hakanan za a tabbatar maka da sarautarka sa'ad da ka gane Mai Sama ne ke mulki. 27 Saboda haka, ya sarki, sai ka karɓi shawarata, ka daina zunubanka, ka yi adalci. Ka bar muguntarka, ka aikata alheri ga waɗanda ake wulakantawa, watakila za a ƙara tsawon kwanakinka da salama.” 28 Wannan duka kuwa ya sami sarki Nebukadnezzar. 29 Bayan wata goma sha biyu, sa'ad da yake yawatawa a kan benen fādar Babila, 30 sai ya ce, “Ashe, wannan ba ita ce Babila babba wadda ni da kaina na gina, da ƙarfin ikona don ta zama fādar sarauta, don darajar ɗaukakata?” 31 Kafin sarki ya rufe baki sai ga murya daga sama, tana cewa, “Ya sarki Nebukadnezzar, da kai ake magana, yanzu an tuɓe ka daga sarauta. 32 Za a kuma kore ka daga cikin mutane zuwa jeji, ka zauna tare da namomin jeji. Za ka ci ciyawa kamar sa har shekara bakwai cur, sa'an nan za ka gane Maɗaukaki ne ke sarautar 'yan adam, yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama.” 33 Nan take sai abin da aka faɗa a kan Nebukadnezzar ya tabbata. Aka kore shi daga cikin mutane. Ya shiga cin ciyawa kamar sa. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har gashinsa ya yi tsawo kamar gashin gaggafa, akaifunsa kuma suka yi tsawo kamar na tsuntsu.

Nebukadnezzar ya Yabi Allah

34 “A ƙarshen kwanakin, sai ni Nebukadnezzar, na ɗaga ido sama, sai hankalina ya komo mini, na ɗaukaka Maɗaukaki, na yabe shi, na girmama shi wanda yake rayayye har abada. “Gama mulkinsa madawwamin mulki ne, Sarautarsa kuwa daga zamani zuwa zamani. 35 Dukan mazaunan duniya ba a bakin kome suke a gare shi ba. Yakan yi yadda ya nufa da rundunar sama da mazaunan duniya, Ba mai hana shi, ba kuma mai ce masa, ‘Me kake yi?’ 36 “A lokacin nan hankalina ya komo mini, sai aka mayar mini da masarautata mai daraja, da martabata, da girmana. 'Yan majalisata da fādawana suka nemo ni. Aka maido ni kan gadon sarautata da daraja fiye da ta dā. 37 Yanzu ni, Nebukadnezzar, ina yabon Sarkin Samaniya, ina ɗaukaka shi, ina kuma girmama shi saboda dukan ayyukansa daidai ne, al'amuransa kuma gaskiya ne. Yakan ƙasƙantar da masu girmankai.”

Daniyel 5

Rubutu a Bango

1 Sarki Belshazzar ya yi wa dubban manyan mutanensa liyafa, ya kuwa sha ruwan inabi a gabansu. 2 Da Belshazzar ya kurɓa ruwan inabin, sai ya umarta a kawo tasoshi na zinariya da na azurfa waɗanda Nebukadnezzar ubansa ya kwaso daga Haikali a Urushalima, domin sarki, da manyan mutanensa, da matansa, da ƙwaraƙwaransa su sha ruwan inabi da su. 3 Sai suka kawo tasoshin zinariya da na azurfa waɗanda aka kwaso daga cikin Haikali, wato Haikalin Allah a Urushalima. Sai sarki da manyan mutanensa, da matansa, da ƙwaraƙwaransa, suka yi ta sha da su. 4 Da suka bugu da ruwan inabi, sai suka yi yabon gumakansu na zinariya, da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse. 5 Nan da nan sai yatsotsin hannun mutum suka bayyana, suka yi rubutu a kan shafen bangon fādar sarkin, wanda ke daura da fitila. Sarki kuwa yana ganin hannun sa'ad da hannun yake rubutu. 6 Sai fuskar sarki ta turɓune, tunaninsa suka razanar da shi, gaɓoɓinsa suka saki, gwiwoyinsa suka soma bugun juna. 7 Sai sarki ya yi kira da babbar murya, cewa a kawo masu dabo, da bokaye, da masu duba. Sai sarki ya ce wa masu hikima na Babila, “Dukan wanda ya karanta wannan rubutu, ya faɗa mini ma'anarsa, to, za a sa masa rigar shunayya, a kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa, zai zama shi ne na uku a cikin masu mulkin ƙasar.” 8 Sai dukan masu hikima na sarki suka shigo, amma ba wanda ya iya karanta rubutun balle ya faɗa wa sarki ma'anarsa. 9 Belshazzar sarki fa ya firgita ƙwarai, fuskarsa ta turɓune, fādawansa duk suka ruɗe. 10 Da sarauniya ta ji maganganun sarki da na manyan fādawansa, sai ta shiga babban ɗakin da ake liyafar, ta ce, “Ran sarki, ya daɗe! Kada ka firgita, kada kuma fuskarka ta turɓune. 11 Ai, a cikin mulkinka akwai wani mutum wanda yake da ruhun alloli tsarkaka. A zamanin ubanka, an iske fahimi, da ganewa, da hikima irin na alloli a cikinsa. Sarki Nebukadnezzar ubanka, ya naɗa shi shugaban masu sihiri, da masu dabo, da bokaye, da masu duba. 12 Yana da ruhu nagari, da ilimi, da ganewa don yin fassarar mafarkai, da bayyana ma'anar ka-cici-ka-cici, da warware al'amura masu wuya. Shi ne wanda sarki ya laƙaba wa suna Belteshazzar. Don haka sai a kirawo maka Daniyel, shi kuwa zai sanar maka da ma'anar.”

Daniyel ya Karanta Rubutun ya kuma Faɗi Ma'anarsa

13 Sai aka kawo Daniyel a gaban sarki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Kai ne Daniyel ɗin nan, ɗaya daga cikin kamammu waɗanda ubana ya kawo daga Yahuza? 14 Na ji labari, cewa kana da ruhun alloli tsarkaka, da fahimi, da ganewa, da mafificiyar hikima. 15 Yanzun nan aka kawo mini masu hikima, da masu dabo don su karanta wannan rubutu, su kuma bayyana mini ma'anarsa, amma sun kāsa faɗar ma'anar rubutun. 16 Amma na ji ka iya fassara, ka kuma iya warware al'amura masu wuya. Idan fa ka iya karanta rubutun nan, har kuma ka iya bayyana mini ma'anarsa, to, za a sa maka riga shunayya, a kuma sa sarƙar zinariya a wuyanka. Za ka zama na uku a cikin mulkin ƙasar.” 17 Daniyel kuwa ya amsa, ya ce wa sarki, “Riƙe kyautarka, ka ba wani duk da haka zan karanta wa sarki rubutun, in kuma bayyana masa ma'anarsa. 18 “Ya sarki, Allah Maɗaukaki ya ba Nebukadnezzar ubanka sarauta, da girma, da daraja, da martaba. 19 Saboda girman da Allah ya ba shi, shi ya sa dukan jama'a, da al'ummai, da harsuna suka ji tsoronsa suka yi rawar jiki a gabansa. Bisa ga ganin damarsa yakan kashe wani, ya bar wani da rai, haka kuma yakan ɗaukaka wani, ya ƙasƙantar da wani. 20 Amma sa'ad da ya kumbura, ya taurare ransa yana ta yin girmankai, sai aka kore shi daga gadon sarautarsa, aka raba shi kuma da darajarsa. 21 Aka kore shi daga cikin mutane, aka ba shi hankali irin na dabba. Ya tafi ya zauna tare da jakunan jeji, yana ta cin ciyawa kamar sa. Jikinsa ya jiƙe da raɓa, har zuwa lokacin da ya gane, ashe, Allah Maɗaukaki ne ke sarautar 'yan adam, yakan kuma ba da ita ga wanda ya ga dama. 22 “Kai kuma Belshazzar, da kake ɗansa, ka san wannan duka, amma ba ka ƙasƙantar da kanka ba. 23 Maimakon haka, sai ka nuna wa Ubangiji girmankai, har ka sa aka kawo maka, kai da fādawanka, da matanka, da ƙwaraƙwaranka, tasoshin Haikalin Ubangiji, kuka sha ruwan inabi a cikinsu. Kuka yabi gumakan zinariya da na azurfa, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na itace, da na dutse waɗanda ba su ji, ba su gani, ba su da ganewar kome. Amma ba ka girmama Allah ba, wanda ranka da dukan harkokinka suna a hannunsa. 24 “Domin haka Allah ya aiko da wannan hannu da ya yi rubutun nan. 25 Wannan shi ne rubutun da aka yi, MENE, MENE, TEKEL, da UPHARSIN. 26 Ma'anar wannan ita ce, MENE, wato Allah ya sa kwanakin mulkinka su ƙare, sun kuwa ƙare. 27 Ma'anar TEKEL ita ce an auna ka a ma'auni, aka tarar ka kāsa. 28 Ma'anar PERES ita ce an raba mulkinka, an ba mutanen Mediya da na Farisa.” 29 Sai Belshazzar ya ba da umarni, aka sa wa Daniyel rigar shunayya, aka sa sarƙar zinariya a wuyansa, aka kuma yi shela, cewa yanzu shi ne na uku cikin masu mulkin ƙasar. 30 A wannan dare kuwa aka kashe Belshazzar Sarkin Kaldiyawa. 31 Dariyus kuwa Bamediye ya karɓi mulkin, yana da shekara sittin da biyu.

Daniyel 6

Daniyel a Kogon Zakoki

1 Dariyus ya ga ya yi kyau ya naɗa muƙaddas guda ɗari da ashirin a dukan mulkinsa. 2 Sai ya naɗa Daniyel da waɗansu mutum biyu su zama shugabannin muƙaddasan nan. Su muƙaddasan kuwa za su riƙa ba shugabannin labarin aikinsu, don kada sarki ya yi hasarar kome. 3 Sai Daniyel ya shahara fiye da sauran shugabannin, da su muƙaddasan, domin yana da nagarin ruhu a cikinsa. Sarki kuwa ya shirya ya gabatar da shi kan dukan mulkin. 4 Sai shugabannin, da su muƙaddasan suka nemi Daniyel da laifi game da ayyukan mulki, amma ba su sami laifin da za su tuhume shi da shi ba, domin shi amintacce ne, ba shi da kuskure ko ha'inci. 5 Sai mutanen nan suka ce, “Ba za mu sami Daniyel da laifin da za mu kama shi da shi ba, sai dai ko mu neme shi da laifi wajen dokokin Allahnsa.” 6 Sa'an nan waɗannan shugabanni da muƙaddasai suka ƙulla shawara, suka zo wurin sarki, suka ce masa, “Ran sarki Dariyus ya daɗe! 7 Dukan shugabannin ƙasar da masu mulki da muƙaddasai, da 'yan majalisa, da wakilai, sun tsai da shawara, cewa ya kamata sarki ya kafa doka, ya yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu'a ga wani gunki ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, sai a tura shi cikin kogon zakoki. 8 Yanzu, ya sarki, sai ka tabbatar da dokar, ka sa hannu, don kada a sāke ta, gama dokar Mediya da Farisa ba a soke ta.” 9 Sai sarki Dariyus ya sa hannu a dokar. 10 Sa'ad da Daniyel ya sani an sa hannu a dokar, sai ya tafi gidansa. Ya buɗe tagogin benensa waɗanda ke fuskantar Urushalima. Sau uku kowace rana yakan durƙusa ya yi addu'a, yana gode wa Allahnsa kamar yadda ya saba. 11 Sai mutanen nan suka tafi, suka iske Daniyel yana kai koke-kokensa da roƙonsa ga Allahnsa. 12 Sai suka taho wurin sarki, suka yi magana a kan dokar sarki, suka ce, “Ran sarki ya daɗe! Ashe, ba ka sa hannu a dokar ba, cewa cikin kwana talatin nan gaba kada kowa ya yi addu'a ga wani gunki ko mutum, in ba a gare ka ba, sai a jefa shi a kogon zakoki?” Sai sarki ya amsa, ya ce, “Dokar tabbatacciya ce, gama dokar Mediya da Farisa, ba ta sokuwa.” 13 Sa'an nan suka amsa wa sarki cewa, “Ya sarki, Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga ƙasar Yahuza, bai kula da kai ba, balle fa dokar da ka kafa, amma yana ta yin addu'a sau uku kowace rana.” 14 Sa'ad da sarki ya ji wannan magana, sai ransa ya ɓaci ƙwarai, sai ya shiga tunani ta yadda zai yi ya kuɓutar da Daniyel. Ya yi ta fama har faɗuwar rana yadda zai yi ya kuɓutar da shi. 15 Sai waɗannan mutane suka zo wurin sarki, suka ce masa, “Ka sani fa ya sarki, doka ce ta Mediya da Farisa, cewa ba dama a soke doka ko umarni wanda sarki ya kafa.” 16 Sarki kuwa ya umarta a kawo Daniyel, a tura shi cikin kogon zakoki. Sarki kuma ya ce wa Daniyel, “Ina fata Allahn nan wanda kake bauta masa kullum zai cece ka.” 17 Sai aka kawo dutse aka rufe bakin kogon, sarki kuwa ya hatimce shi da hatiminsa, da hatimin fādawansa, don kada a sāke kome game da Daniyel. 18 Sarki ya koma fādarsa, ya kwana yana azumi, bai ci abinci ba, ya kuma kāsa yin barci. 19 Gari na wayewa, sai sarki ya tashi, ya tafi da gaggawa wurin kogon zakoki. 20 Da ya zo kusa da kogon da Daniyel yake, sai ya ta da murya ya yi kira da damuwa, ya ce wa Daniyel, “Ya Daniyel, bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta masa kullum, yana da ikon cetonka daga zakoki?” 21 Sai Daniyel ya ce wa sarki, “Ran sarki ya daɗe! 22 Allahna ya aiko mala'ikansa ya rufe bakunan zakoki, ba su iya yi mini lahani ba, domin ban yi wa Allah laifi ba, ban kuma yi maka ba.” 23 Sarki ya cika da murna ƙwarai, ya umarta a fito da Daniyel daga kogon. Sai aka fito da Daniyel daga kogon, aka ga ba wani lahani a jikinsa saboda ya dogara ga Allahnsa. 24 Sai sarki ya umarta a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da 'ya'yansu, da matansu cikin kogon zakoki. Tun ba su kai ƙurewar kogon ba, sai zakoki suka hallaka su, suka kakkarye ƙasusuwansu gutsi-gutsi. 25 Dariyus sarki kuwa ya rubuta wa dukan jama'a da al'ummai, waɗanda ke zaune a duniya duka, ya ce, “Salama ta yalwata a gare ku. 26 Ina umartar mutanen da ke cikin mulkina su yi rawar jiki, su ji tsoron Allah na Daniyel, Gama shi Allah ne mai rai, Madawwami, Sarautarsa ba ta tuɓuwa, Mulkinsa kuma madawwami ne. 27 Yakan yi ceto, yakan kuma kuɓutar, Yana aikata alamu da mu'ujizai a sama da duniya. Shi ne wanda ya ceci Daniyel daga bakin zakoki.” 28 Daniyel kuwa ya bunƙasa a zamanin mulkin Dariyus da na Sairus mutumin Farisa.

Daniyel 7

Dabbobi Huɗu da Daniyel ya Gani cikin Wahayi

1 A shekara ta farko ta sarautar Belshazzar Sarkin Babila, Daniyel ya yi mafarki, ya kuma ga wahayi sa'ad da yake kwance a gadonsa. Sai ya rubuta mafarkin. Ga abin da ya faɗa. 2 Daniyel ya ce, “A wahayi da dare na ga iskar samaniya daga kusurwa huɗu tana gurɓata babbar teku. 3 Sai manyan dabbobi huɗu iri dabam dabam suka fito daga cikin tekun. 4 Kamannin dabba ta fari irin ta zaki ce, amma tana da fikafikan gaggafa. Ina kallo, sai aka fige fikafikanta, aka ɗaga ta sama, aka sa ta tsaya a kan ƙafafu biyu kamar mutum, aka ba ta tunani irin na mutum. 5 “Sai kuma ga dabba ta biyu mai kama da beyar. Gefe guda na jikinta ya ɗara ɗaya. Tana riƙe da haƙarƙari uku a haƙoranta! Sai aka ce mata, ‘Tashi ki cika cikinki da nama.’ 6 “Bayan wannan kuma, sai ga wata dabba mai kama da damisa tana da fikafikai huɗu irin na tsuntsu a bayanta, tana kuma da kai huɗu. Sai aka ba ta mulki. 7 “Bayan wannan kuma a wahayi na dare na ga dabba ta huɗu mai ƙarfi ƙwarai, mai bantsoro da banrazana. Tana da haƙoran ƙarfe, zaga-zaga. Ta cinye, ta ragargaza, sa'an nan ta tattake sauran da ƙafafunta. Dabam take da sauran dabbobin da suka riga ta. Tana kuma da ƙaho goma. 8 Ina duban ƙahonin, sai ga wani ƙaho, ɗan ƙanƙane, ya ɓullo a tsakiyarsu. Sai aka tumɓuke ƙaho uku na fari daga cikinsu. Wannan ƙaramin ƙaho yana da idanu kamar na mutum, yana kuma da baki, yana hurta maganganu na fariya.”

Wahayi na Wanda ya Dawwama har Adaba

9 “Ina dubawa sai na ga an ajiye gadajen sarauta, Sai wani wanda yake Tun Fil Azal ya zauna kursiyinsa. Rigarsa fara fat kamar dusar ƙanƙara, Gashin kansa kamar uku ne tsantsa, Kursiyinsa harshen wuta ne, Ƙafafun kursiyin masu kamar karusa, wuta ne. 10 Kogin wuta yana gudu daga gabansa. Dubun dubbai suna ta yi masa hidima, Dubu goma sau dubu goma suka tsaya a gabansa, Aka kafa shari'a, aka buɗe littattafai. 11 “Na yi ta dubawa saboda manya manyan maganganun fariya da ƙahon ke hurtawa, sai na ga an kashe dabbar, an jefar da gawar cikin wuta don ta ƙone. 12 Sauran dabbobi kuwa aka karɓe mulkinsu, amma aka bar su da rai har wani ƙayyadadden lokaci. 13 “A cikin wahayi na dare, na ga wani kamar Ɗan Mutum. Yana zuwa cikin gizagizai, Ya zo wurin wanda yake Tun Fil Azal, Aka kai shi gabansa. 14 Aka kuwa danƙa masa mulki, da ɗaukaka, da sarauta, Domin dukan jama'a, da al'ummai, da harsuna su bauta masa. Mulkinsa, madawwamin mulki ne, Wanda ba zai ƙare ba. Sarautarsa ba ta tuɓuwa.”

Ma'anar Wahayin

15 “Amma ni Daniyel raina ya damu, wahayin da na gani ya tsorata ni. 16 Sai na matsa kusa da ɗaya daga cikin waɗanda ke tsaye a wurin, na tambaye shi ma'anar waɗannan abubuwa duka. Sai ya bayyana mini, ya kuma ganar da ni ma'anar waɗannan abubuwa. 17 Waɗannan manyan dabbobi guda huɗu, sarakuna ne huɗu waɗanda za su taso a duniya. 18 Amma tsarkaka na Maɗaukaki za su karɓi mulki, su kuwa riƙe mulkin har abada abadin. 19 “Sai na nemi in san ainihin ma'anar dabba ta huɗu, wadda ta bambanta da sauran. Tana da bantsoro ƙwarai, tana kuma da haƙoran baƙin ƙarfe da faratan tagulla. Ta cinye, ta ragargaje, sa'an nan ta tattake sauran da ƙafafunta. 20 Na kuma so in san ma'anar ƙahoninta goma, da ɗaya ƙahon wanda da ya tsiro, wanda aka tumɓuke ƙahoni uku a gabansa. Ƙahon nan yake da idanu da bakin da yake hurta manyan maganganun fariya, wanda girmansa ya fi na sauran. 21 “Ina dubawa ke nan sai ga wannan ƙaho yana yaƙi da tsarkaka har ya rinjaye su, 22 sai da Tun Fil Azal ya zo ya yanke shari'a, aka ba tsarkaka na Maɗaukaki gaskiya. Da lokaci ya yi aka ba tsarkaka mulkin. 23 “Ga abin da ya ce, ‘Dabba ta huɗu za ta zama mulki na huɗu a duniya, wanda zai bambanta da sauran mulkokin. Zai cinye duniya duka, ya ragargaje ta, ya tattake ta. 24 Ƙahonin nan goma kuwa, sarakuna goma ne waɗanda za su taso daga cikin mulkin. Sa'an nan wani sarki zai taso a bayansu wanda zai bambanta da sauran da suka fara tasowa, zai kā da sarakuna uku. 25 Zai yi maganganun saɓo a kan Maɗaukaki, zai tsananta wa tsarkaka na Maɗaukaki, zai yi ƙoƙari ya sāke lokatai, da shari'a, za a kuwa bashe su a hannunsu, har shekara uku da rabi. 26 Amma majalisa za ta zauna ta yanke shari'a, za a karɓe mulkinsa, a hallaka shi har abada. 27 Sa'an nan za a ba da sarauta da girman dukan mulkokin duniya ga tsarkaka na Maɗaukaki. Mulkinsa madawwamin mulki ne. Dukan sarakunan duniya za su bauta masa, su kuma yi masa biyayya.’ 28 “Ni Daniyel na firgita ƙwarai, fuskata ta yi yaushi. Amma na riƙe al'amarin duka a zuciyata.”

Daniyel 8

Wahayi na Rago da Bunsuru

1 A shekara ta uku ta sarautar Belshazzar, sai ni Daniyel na ga wahayi bayan wancan na fari. 2 A wahayin sai na gani ina a bakin kogin Ulai a Shushan, masarautar lardin Elam. 3 Da na ta da idanuna, sai na ga rago a tsaye a gāɓar kogin. Yana da ƙaho biyu dogaye, amma ɗaya ya ɗara ɗaya tsawo. Wanda ya ɗara tsawon shi ne ya tsiro daga baya. 4 Na ga ragon ya kai karo wajen yamma da wajen kudu, da wajen arewa. Ba wata dabbar da ta iya karawa da shi, ba wanda kuma zai iya kuɓuta daga ikonsa, ya yi yadda ya ga dama, ya ɗaukaka kansa. 5 Sa'ad da nake cikin tunani, sai ga bunsuru ya ɓullo daga wajen yamma, ya ratsa dukan duniya, ba ya ko taɓa ƙasa. Akwai ƙaho na gaske a tsakanin idanunsa. 6 Sai ya zo wurin ragon, mai ƙahoni biyu, wanda na gani a tsaye a gāɓar kogi. Bunsurun kuwa ya tasar masa da fushi mai zafi. 7 Na ga ya zo kusa da ragon, ya husata da shi ƙwarai, sai ya gabza wa ragon karo. Ya kakkarya ƙahonin nan nasa biyu. Ƙarfin ragon ya kāsa, ba ya iya kare kansa daga bunsurun. Bunsurun ya buge shi ƙasa ya tattake shi. Ba wanda ya iya ceton ragon daga bunsurun. 8 Sa'an nan bunsurun ya ɗaukaka kansa ƙwarai, amma sa'ad da ya ƙasaita sai babban ƙahon nan ya karye, a maimakonsa sai waɗansu ƙahoni huɗu na gaske suka tsiro suna fuskantar kusurwa huɗu. 9 Wani ƙarami ƙaho kuma ya tsiro daga cikin ɗayansu, ya yi girma ya ƙasaita ƙwarai. Ya nuna ikonsa wajen gabas, da wajen kudu, da wajen ƙasa mai albarka. 10 Ya ƙasaita, har ya kai cikin rundunar sama. Ya jawo waɗansu taurari zuwa ƙasa, ya tattake su. 11 Ya ɗaukaka kansa, har ya mai da kansa daidai da shugaban runduna. Ya hana yin hadayar ƙonawa ta yau da kullum ga Sarkin sarakuna, ya kuma rushe masa wuri mai tsarki. 12 Saboda zunubi sai aka ba da runduna duk da hadayar ƙonawa ta yau da kullum ga ƙahon. Sai ya yi watsi da gaskiya, ya yi abin da ya ga dama, ya kuwa yi nasara. 13 Sai na ji wani mai tsarki yana magana, wani kuma mai tsarki ya tambayi wancan mai tsarki da ya yi magana, ya ce, “Sai yaushe za a tsai da abubuwan da ke a wahayin nan, wato hana yin hadayar ƙonawa ta yau da kullum, da zunubin da ke lalatarwa, da ba da wuri mai tsarki ga rundunar mutane don a tattake?” 14 Ya ce mini, “Sai an yi kwana dubu biyu da ɗari uku, sa'an nan za a mai da wuri mai tsarki daidai da yadda yake a dā.”

Jibra'ilu ya Fasarta Wahayin

15 Sa'ad da ni Daniyel, na ga wahayin, ina so in gane, sai ga wani kamar mutum ya tsaya a gabana. 16 Na kuma ji muryar mutum a gāɓar Ulai ta ce, “Jibra'ilu, ka sa wannan mutum ya gane wahayin.” 17 Don haka sai ya zo kusa da inda nake tsaye. Da ya zo sai na firgita, na faɗi rubda ciki. Amma ya ce mini, “Ɗan mutum, wannan wahayi yana a kan lokaci na ƙarshe ne.” 18 Sa'ad da yake magana da ni, sai barci mai nauyi ya kwashe ni da nake kwance rubda ciki, amma sai ya taɓa ni, ya tashe ni tsaye. 19 Ya ce mini, “Zan sanar da kai abubuwan banhaushi, da za su faru nan gaba, gama wahayin ya shafi ƙayyadadden lokaci na ƙarshe. 20 “Ragon nan mai ƙaho biyu da ka gani, sarakunan Mediya ne da na Farisa. 21 Bunsurun kuwa Sarkin Hellas ne. Babban ƙahon nan da ke tsakanin idanunsa shi ne sarki na farko. 22 Ƙahoni huɗu da suka tsiro bayan karyewar na farin, sarakuna huɗu ne da za su fito daga cikin al'ummarsa, amma ba za su sami iko irin nasa ba. 23 “A wajen ƙarshen mulkinsu, sa'ad da muguntarsu ta kai intaha, wani mugun sarki mai izgili, mayaudari, zai fito. 24 Zai ƙasaita, amma ba ta wurin ikon kansa ba. Zai yi mummunar hallakarwa. Zai hallaka manyan mutane, da tsarkaka. Zai yi nasara cikin abin da zai yi. 25 Ta wurin mugun wayonsa zai sa cin hanci ya haɓaka. Zai ɗaukaka kansa a ransa. Zai hallaka mutane da yawa, ba zato ba tsammani, har ma zai tasar wa Sarkin sarakuna, amma za a hallaka shi ba ta hannun mutum ba. 26 Wannan wahayi na kwanaki wanda aka nuna maka gaskiya ne, asiri ne kuma, kada ka faɗa, gama zai daɗe kafin a yi.” 27 Ni Daniyel kuwa na siƙe, na yi ciwo, har na kwanta 'yan kwanaki, sa'an nan na tashi na ci gaba da aikin sarki. Wahayin ya shige mini duhu, ban gane shi ba.

Daniyel 9

Daniyel ya yi Addu'a domin Mutanensa

1 A shekara ta fari ta sarautar Dariyus ɗan Ahazurus Bamediye wanda ya ci sarautar Kaldiyawa, 2 a wannan shekara ta sarautarsa ni Daniyel, ina nazarin littattafai, sai na ga labarin shekara saba'in ɗin nan da Ubangiji ya faɗa wa annabi Irmiya. Su ne yawan shekarun da Urushalima za ta yi tana zaman kango. 3 Sai na mai da hankalina wajen Ubangiji Allah, ina nemansa ta wurin addu'a, da roƙe-roƙe tare da azumi, ina saye da tufafin makoki, na zauna cikin toka. 4 Na yi addu'a ga Ubangiji Allahna, na tuba. Na ce, “Ya Ubangiji, Allah maigirma, mai banrazana, kai mai cika alkawari ne, kana ƙaunar masu ƙaunarka waɗanda ke kiyaye dokokinka. 5 “Mun yi zunubi, mun yi laifi, mun aikata mugunta, mun yi tawaye. Mun kauce daga bin umarnanka da ka'idodinka. 6 Ba mu kasa kunne ga bayinka annabawa ba, waɗanda kuwa suka yi magana da sunanka ga sarakunanmu, da shugabanninmu, da kakanninmu, da dukan jama'ar ƙasa. 7 Ya Ubangiji, kai mai adalci ne, amma mu sai kunya, kamar yadda yake a yau ga mutanen Yahuza, da mazaunan Urushalima da dukan Isra'ilawa, waɗanda ke kusa da waɗanda ke nesa a dukan ƙasashen da ka kora su saboda rashin amincin da suka yi maka. 8 Ya Ubangiji kunya ta rufe mu, mu da sarakunanmu, da shugabanninmu, da kakanninmu, saboda mun yi maka zunubi. 9 Ubangiji Allahnmu mai jinƙai ne mai gafara, amma mu, mun tayar masa. 10 Ba mu yi biyayya ga Ubangiji Allahnmu ta wurin kiyaye dokokinsa ba, waɗanda ya ba mu ta hannun bayinsa annabawa. 11 Dukan Isra'ilawa sun karya dokokinka, sun kauce, sun ƙi bin maganarka. La'ana da rantsuwa waɗanda ke a rubuce cikin dokokin Musa, bawan Allah, sun kama mu domin mun yi maka zunubi. 12 Ya tabbatar da maganarsa wadda ya yi a kanmu da shugabanninmu waɗanda suka yi mulkinmu. Ya aukar mana da babban bala'i, gama a duniya duka ba a taɓa yin irin abin da aka yi wa Urushalima ba. 13 Kamar yadda aka rubuta a dokokin Musa, haka wannan bala'i ya auko a kanmu, duk a haka ba mu nemi jinƙan Ubangiji Allahnmu ba, ba mu daina aikata muguntarmu ba, ba mu lizimci gaskiyarka ba. 14 Domin haka Ubangiji ya shirya bala'i, ya kuma aukar mana da shi, gama Ubangiji Allahnmu mai adalci ne cikin dukan abin da ya aikata, amma mu ba mu bi maganarsa ba. 15 “Ya Ubangiji Allahnmu, kai ne ka fito da jama'arka daga ƙasar Masar da iko mai girma, da haka ka bayyana ikonka kamar yadda yake a yau, amma mun yi zunubi, mun aikata mugunta. 16 Ya Ubangiji, saboda dukan ayyukanka na adalci, ka huce daga fushinka da hasalarka da ka yi da birninka Urushalima, tsattsarkan tudunka. Gama saboda zunubanmu da muguntar kakanninmu, Urushalima da jama'arka sun zama abin ba'a ga waɗanda ke kewaye da mu. 17 Yanzu ya Allahnmu, ka ji addu'ar bawanka da roƙe-roƙensa. Sabili da sunanka da idon rahama ka dubi tsattsarkan wurinka wanda ya zama kango. 18 Ya Allahna, ka karkato kunnenka ka ji, ka buɗe idanunka ka ga yadda mu da birnin da ake kira da sunanka muka lalace. Ba cewa muna da wani adalci na kanmu shi ya sa muka kawo roƙe-roƙenmu ba, amma saboda yawan jinƙanka. 19 Ya Ubangiji, ka ji mu. Ya Ubangiji, ka garfarce mu. Ya Ubangiji, ka saurare mu, ka yi wani abu saboda sunanka. Ya Allahna, kada ka yi jinkiri domin da sunanka ake kiran birninka da jama'arka.”

Annabci a kan Mako Saba'in

20 Sa'ad da nake ta addu'a, ina faɗar zunubina, da na jama'ata Isra'ila, ina kawo roƙe-roƙena wurin Ubangiji Allahna saboda tsattsarkan tudun Allahna. 21 Sa'ad da nake yin addu'a, sai mutumin nan Jibra'ilu, wanda na gani a wahayin da ya wuce, ya zo wurina a gaggauce wajen lokacin yin hadaya ta maraice. 22 Ya zo, ya ce mini, “Ya Daniyel, na zo ne don in ba ka hikima da ganewa. 23 A lokacin da ka fara roƙe-roƙenka sai aka ba da umarni, na kuwa zo domin in faɗa maka, gama ana sonka ƙwarai. Sai ka fahimci maganar da wahayin. 24 “An ƙayyade wa jama'arka da tsattsarkan birninka shekara ɗari huɗu da tasa'in domin a kawo ƙarshen laifi da zunubi, domin a yi kafarar laifi, sa'an nan a shigo da adalci madawwami, a rufe wahayi da annabci, a tsarkake Haikali. 25 Sai ka sani, ka kuma gane, daga lokacin da aka umarta a sāke gina Urushalima har zuwa lokacin da shugaba, Masiha, zai zo, za a yi shekara arba'in da tara, da shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu. Za a sāke gina ta a yi mata tituna da kagara. 26 Za ta kasance har shekara ɗari huɗu da talatin da huɗu, sa'an nan za a kashe Naɗaɗɗe, ba zai sami kome ba. Jama'ar shugaban da zai zo za su hallaka birnin da Haikali. A ƙarshensa za a yi rigyawa, da yaƙe-yaƙe, da hallakarwa kamar yadda aka ƙaddara. 27 Wannan shugaba zai yi alkawari mai ƙarfi na shekara bakwai da mutane da yawa. Amma bayan shekara uku da rabi za a hana a yi sadaka da hadaya. Abin ƙyama zai kasance a ƙwanƙolin Haikali, har lokacin da ƙaddara za ta auko wa wanda ya sa abin ƙyama.”

Daniyel 10

Wahayin da Daniyel ya Gani a bakin Kogin Taigiris

1 A shekara ta uku ta sarautar Sairus Sarkin Farisa, sai aka aiko da saƙo wurin Daniyel, wanda aka laƙaba wa suna Belteshazzar. Saƙon kuwa gaskiya ne, ya shafi zancen yaƙi, Daniyel kuwa ya fahimci saƙon. 2 A waɗannan kwanaki, ni Daniyel, ina fama da baƙin ciki har mako uku. 3 A makon nan uku ban ci wani abincin kirki ba, balle nama ko shan ruwan inabi, ban kuma shafa mai ba. 4 A rana ta ashirin da huɗu ga watan fari, ina tsaye a gāɓar babban kogin Taigiris. 5 Da na ɗaga kaina sai na ga wani sāye da rigar lilin, ya ɗaura ɗamara ta zinariya tsantsa. 6 Jikinsa kamar lu'ulu'u yake, fuskarsa kamar walƙiya, idanunsa kuma kamar harshen wuta, hannunwansa da ƙafafunsa kuwa kamar gogaggiyar tagulla, muryarsa kamar ta babban taron jama'a. 7 Ni kaɗai na ga wahayin, gama mutanen da ke tare da ni ba su ga wahayin ba, sai dai babbar razana ta auko musu, har suka gudu, suka ɓuya. 8 Aka bar ni, ni kaɗai, na ga wannan babban wahayi, ni kuwa ba ni da sauran ƙarfi. Fuskata ta sauya, ta turɓune, ba ni da sauran ƙarfi. 9 Sa'an nan na ji muryarsa, da jin muryarsa, sai na faɗi rubda ciki, barci mai nauyi ya kwashe ni. 10 Sai hannu ya taɓa ni, ya tashe ni, sa'an nan hannuwana da gwiwoyina suna ta kaɗuwa. 11 Ya ce mini, “Ya Daniyel, mutumin da ake sonka ƙwarai, ka lura da maganar da zan faɗa maka. Ka miƙe tsaye, gama a wurinka aka aiko ni.” Sa'ad da ya faɗi wannan magana, sai na miƙe tsaye, ina rawar jiki. 12 Sai ya ce mini, “Kada ka ji tsoro, Daniyel, gama tun daga ran da ka fara sa zuciya ga neman ganewa, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allahnka, an ji addu'arka, amsar addu'arka ce ta kawo ni. 13 Shugaban ƙasar Farisa ya tare ni har kwana ashirin da ɗaya, amma Mika'ilu, ɗaya daga cikin shugabanni, ya zo ya taimake ni, ya tsaya wurin sarakunan Farisa. 14 Na zo ne don in ganar da kai a kan abin da zai faru da mutanenka nan gaba, gama wahayin yana a kan kwanaki na nan gaba ne.” 15 Sa'ad da ya faɗa mini wannan magana, na sunkuyar da kaina ƙasa, na yi shiru, ba magana. 16 Sai wani mai kama da ɗan adam ya taɓa leɓunana, sa'an nan na buɗe baki, na yi magana, na ce wa wanda ke tsaye gabana, “Ya shugabana saboda wannan wahayi ciwo ya kama ni, ba ni da sauran ƙarfi. 17 Ƙaƙa zan iya magana da kai, ya shugabana? Yanzu ba ni da sauran ƙarfi, ba ni kuma da sauran numfashi.” 18 Mai kamannin mutum ɗin nan kuma ya sake taɓa ni, ya kuma ƙarfafa ni. 19 Ya ce, “Ya kai, mutumin da ake sonka ƙwarai, kada ka ji tsoro, salama a gare ka, ka ƙarfafa, ka yi ƙarfin hali!” Sa'ad da ya yi magana da ni, na sami ƙarfi na ce, “Yanzu sai shugabana ya yi magana, ka sa na sami ƙarfi.” 20 Shi kuwa ya ce, “Ka san dalilin zuwana wurinka? Yanzu zan koma in yi yaƙi da shugaban Farisa, sa'ad da na murƙushe shi, shugaban Hellas zai taso. 21 Zan faɗa maka abin da ke rubuce a littafin gaskiya. Ba wanda zai taimake ni yaƙi da waɗannan, sai dai Mika'ilu shugabanka.

Daniyel 11

1 “A shekara ta fari ta sarautar Dariyus Bamediye, na tashi na tabbatar da shi, na kuma ƙarfafa shi.”

Sarkin Kudu da Sarkin Arewa

2 “Yanzu zan faɗa maka gaskiya. Za a ƙara samun sarakuna uku a Farisa, amma na huɗun zai fi dukansu dukiya. Sa'ad da ya ƙasaita saboda dukiyarsa, zai kuta dukan daularsa ta yi gaba da mulkin Hellas. 3 “Sa'an nan wani sarki babba zai taso wanda zai yi mulki da babban iko yadda ya ga dama. 4 Sa'ad da ya ƙasaita mulkinsa zai faɗi, a rarraba shi kashi huɗu a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, amma ba za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki mulkinsa saboda waɗansu. 5 “Sarkin kudu zai yi ƙarfi, amma ɗaya daga cikin jarumawansa zai ƙasaita fiye da shi, mulkinsa kuma zai zama babba. 6 Bayan waɗansu shekaru za su ƙulla zumunci. Sarkin kudu zai aurar wa sarkin arewa da 'yarsa don sāda zumunci, amma ba za ta sami iko ba. Shi da zuriyarsa ba za su amince da ita ba. Za a yi watsi da ita, ita da masu yi mata hidima, da mahaifinta, da waliyyinta. 7 Ba za a daɗe ba, wani daga cikin danginta zai tasar wa sojojin sarkin arewa da yaƙi, ya shiga kagararsu, ya ci su da yaƙi. 8 Zai kwashe gumakansu ganima, da siffofinsu na zubi, ya kai Masar, tare da tasoshinsu na azurfa da na zinariya masu daraja. Zai yi shekaru bai kai wa sarkin arewa yaƙi ba. 9 Bayan wannan sarkin arewa zai kai wa sarkin kudu yaƙi, amma tilas zai janye, ya koma ƙasarsa. 10 “'Ya'yansa maza za su tara babbar rundunar yaƙi. Ɗayansu zai mamaye kamar rigyawa, har ya kai kagara wurin da abokan gāba suke. 11 Sarkin kudu zai husata ya kai wa sarkin arewa yaƙi, za a ba da rundunar sojojin sarkin arewa a hannunsa. 12 Ganin ya kashe sojoji masu ɗumbun yawa, sai ya yi girmankai, amma nasararsa ba mai ɗorewa ba ce. 13 Sarkin arewa kuwa zai tara babbar rundunar soja fiye da ta dā. Bayan waɗansu shekaru kuwa zai kama hanya da babbar rundunar soja, da kayan faɗa masu yawan gaske. 14 “A waɗannan kwanaki mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin kudu. Amma waɗansu 'yan kama-karya za su taso daga jama'arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattaka su. 15 Sa'an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin garun birni don ya ci birnin da yaƙi. Sojojin kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansa ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa. 16 Amma wanda ya kawo masa yaƙin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai tsaya a ƙasa mai albarka, ya mallake ta duka. 17 Zai yunƙuro da dukan ƙarfin mulkinsa, zai zo ya gabatar da shawarar salama, ya aikata ta. Zai aurar masa da 'yarsa don ta lalatar da mulkin abokin gābansa, amma wannan dabara ba za ta ci ba. 18 Daganan zai yunƙura zuwa ƙasashen gaɓar teku, ya ci da yawa daga cikinsu, amma wani jarumi zai kawo ƙarshen fāɗin ransa. Zai sa fāɗin ransa ya koma masa. 19 Sa'an nan zai juya, ya nufi kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe, ya fāɗi, ba za a ƙara ganinsa ba.”

Mugun Sarki

20 “Wani sarki zai ɗauki matsayinsa, zai aiki mai karɓar haraji cikin daularsa, amma ba da daɗewa ba za a kashe shi, ba cikin hargitsin yaƙi ba. 21 “Wani kuma rainanne zai maye gurbin wancan, shi kuwa ba ɗan jinin sarauta ba ne. Zai taso ba zato ba tsammani, ya ƙwace sarautar ta hanyar zamba. 22 Zai shafe rundunonin sojoji har da rantsattsen shugaba. 23 Daga lokacin da aka ƙulla yarjejeniya da shi, zai yi munafunci. Zai sami iko ta wurin goyon bayan mutane kima. 24 Ba zato ba tsammani zai kai wa lardi mafi arziki hari. Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba wa mabiyansa kwason yaƙi, da ganima, da dukiya. Zai kuma yi shiri ya kai wa kagara hari amma domin ɗan lokaci ne kawai. 25 “Zai iza kansa ya yi ƙarfin hali ya kai wa sarkin kudu yaƙi da babbar rundunar soja. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya. 26 Waɗanda ke na jikinsa, su ne za su zama sanadin faɗuwarsa. Za a kashe rundunar sojojinsa, a shafe su duk. 27 Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna. 28 “Sarkin arewa zai koma gida da dukiya mai ɗumbun yawa. Zuciyarsa za ta yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai yi yadda ya ga dama sa'an nan ya koma ƙasarsa. 29 “A ƙayyadadden lokaci kuma zai koma kudu, amma a wannan karo abin ba zai zama kamar dā ba, 30 gama jiragen ruwa na Kittim za su tasar masa, shi kuwa zai ji tsoro, ya janye. “Zai koma ya huce fushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai kula da waɗanda suka yi banza da tsattsarkan alkawarin. 31 Sojojinsa za su ɓata tsattsarkan wuri da kagararsa. Za su kuma hana yin hadayu na yau da kullum, su kafa abin banƙyama da ke lalatarwa. 32 Waɗanda suka ta da alkawarin kuma, sarki zai ƙara dulmuyar da su ta wurin daɗin bakinsa. Amma waɗanda suka san Allahnsu za su tsaya da ƙarfi su yi wani abu. 33 Waɗansu daga cikin mutane waɗanda ke da hikima, za su wayar da kan mutane da yawa. Amma duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta. 34 Sa'ad da suka fāɗi ba za su sami wani taimakon kirki ba, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci. 35 Waɗanda suke da hikima, za a kashe su, don a tsabtace su, a tsarkake su, su yi tsab tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi. 36 “Sa'an nan sarki zai yi yadda ya ga dama. Zai ɗaukaka kansa, ya aza ya fi kowane allah. Zai kuma yi maganganu na saɓo a kan Allahn alloli, zai yi nasara, sai lokacin da aka huce haushi, gama abin da aka kaddara zai cika. 37 Ba zai kula da gumakan kakanninsa ba, ko begen da mata ke yi. Ba kuwa zai kula da kowane irin gunki ba, domin zai aza kansa ya fi su duka. 38 A maimakon haka zai girmama gunkin kagarai, gunkin da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tamani. 39 Zai tasar wa kagara mafi ƙarfi da taimakon baƙon gunki. Waɗanda suka yarda da shi, zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu. 40 “A lokaci na ƙarshe sarkin kudu zai tasar masa, sarkin arewa kuwa zai tunzura, ya tasar masa da karusai da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, ya ci su da yaƙi, ya wuce. 41 Zai shiga kyakkyawar ƙasa ya kashe dubban mutane. Amma ƙasar Edom, da ta Mowab, da yawancin ƙasar Ammonawa za su kuɓuta daga hannunsa. 42 Zai kai wa waɗansu ƙasashe yaƙi, ƙasar Masar kuwa ba za ta kuɓuta ba. 43 Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tamani na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Habasha da yaƙi. 44 Labarin da zai zo masa daga gabas da arewa zai firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, ya karkashe mutane da yawa, ya shafe su. 45 Zai kafa manyan alfarwai na sarauta a tsakanin teku da tsattsarkan dutse. Amma zai mutu ba kuwa wanda zai taimake shi.”

Daniyel 12

Lokaci Na Ƙarshe

1 “A wannan lokaci Mika'ilu babban shugaba wanda ke lura da jama'arka zai bayyana. A lokacin za a yi tashin hankali irin wanda ba a taɓa yi ba, tun da aka yi duniya. Amma a lokacin za a ceci jama'arka waɗanda aka rubuta sunayensu cikin littafi. 2 Waɗanda suka rasu za su tashi, waɗansu zuwa rai madawwami, waɗansu kuwa zuwa kunya da madawwamin ƙasƙanci. 3 Waɗanda ke da hikima za su haskaka kamar sararin sama, waɗanda kuma suka juyar da mutane da yawa zuwa adalci, za su zama kamar taurari har abada abadin. 4 “Amma kai, Daniyel, sai ka rufe maganar, ka kuma kulle littafin, har zuwa ƙarshen lokaci. Mutane da yawa za su yi ta kai da kawowa, ilimi kuma zai ƙaru.” 5 Sa'an nan ni Daniyel na duba, sai ga waɗansu biyu a tsaye, ɗaya a wannan gāɓa ɗayan kuma a waccan gāɓar kogin. 6 Dayansu ya ce wa mutumin da ke sāye da rigar lilin, wanda ke tsaye a gaɓar kogin, “Sai yaushe waɗannan abubuwan banmamaki za su ƙare?” 7 Sai mutumin da ke sāye da rigar lilin ɗin, wanda ke tsaye a gaɓar kogin ya ɗaga hannuwansa sama, sa'an nan ya rantse da wanda yake rayayye har abada, ya ce, “Za a yi shekara uku da rabi. Za a kammala waɗannan abubuwa, sa'ad da aka gama ragargaje ikon tsarkakan mutane.” 8 Na ji, amma ban gane ba. Sai na ce, “Ya shugabana, menene ƙarshen waɗannan abubuwa?” 9 Sai ya ce, “Yi tafiyarka, Daniyel, gama an rufe wannan magana, an kuma kulle ta har ƙarshen lokaci. 10 Mutane da yawa za su tsarkake kansu, su zama masu tsabta tsab tsab, amma mugaye ba za su gane ba, za su yi ta muguntarsu, amma masu hikima za su gane. 11 “Tun daga lokacin da za a hana miƙa hadayar ƙonawa ta yau da kullum, a kafa abin banƙyama, wanda ke lalatarwa, za a yi kwana dubu da ɗari biyu da tasa'in. 12 Masu farin ciki ne waɗanda suka daure, har suka kai ƙarshen kwana dubu da ɗari uku da talatin da biyar. 13 “Ka yi tafiyarka ka huta, a ƙarshen kwanaki za ka tashi ka karɓi naka rabo.”

Yusha’u 1

Matar Yusha'u wadda ta Ci Amanarsa da 'Ya'yanta

1 Ubangiji kuwa ya yi magana da Yusha'u ɗan Beyeri a zamanin mulkin Azariya, da Yotam, da Ahaz, da Hezekiya, sarakunan Yahuza, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yehowash, Sarkin Isra'ila. 2 Sa'ad da Ubangiji ya fara yin magana da Yusha'u ya ce masa, “Tafi ka auro karuwa, ka haifi 'ya'yan karuwanci, gama ƙasar tana yin fasikanci sosai, wato ta bar bin Ubangiji.” 3 Sai ya tafi ya auri Gomer, 'yar Diblayim. Ta yi ciki, ta haifi masa ɗa namiji. 4 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Yezreyel, gama ba da daɗewa ba zan ziyarci gidan Yehu da hukunci saboda jinin da ya zubar a Yezreyel. Zan sa mulkin Isra'ila ya ƙare. 5 A wannan rana zan karya bakan Isra'ila a kwarin Yezreyel.” 6 Gomer ta kuma ɗauki ciki, ta haifi 'ya mace. Ubangiji kuma ya ce wa Yusha'u, “Ka raɗa mata suna Bajinƙai, gama ba zan ƙara yi wa jama'ar Isra'ila jinƙai ba, har da zan gafarta mata. 7 Amma zan yi wa mutanen Yahuza jinƙai. Ni kaina zan cece su ba da baka ba, ba kuwa da takobi, ko da yaƙi, ko da yaƙi, ka da dawakai, ko da sojojin dawakai ba.” 8 Sa'ad da ta yaye Ba-jinƙai, ta sāke ɗaukar ciki, ta haifi ɗa namiji. 9 Ubangiji kuma ya ce masa, “Ka raɗa masa suna, Ba-mutanena-ba-ne, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne. 10 “Duk da haka yawan mutanen Isra'ila Zai zama kamar yashi a bakin teku, Wanda ba za a iya aunawa ko ƙidayawa ba. Maimakon kuma a ce, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ Za a ce, ‘Ku mutanen Allah ne mai rai.’ 11 Mutanen Yahuza da mutanen Isra'ila za su haɗu su zama ɗaya, Za su zaɓa wa kansu shugaba ɗaya. Za su shugabanci ƙasar Gama ranahakuncir Yezreyel babba ce.”

Yusha’u 2

Ubangiji yana Ƙaunar Mutanensa Marasa Aminci

1 “Ka ce wa 'yan'uwanka maza, ‘Ku mutanena ne,’ ka kuma ce wa 'yar'uwarka, ‘Kin sami jinƙai!’ 2 Ku roƙi uwarku, Gama ita ba matata ba ce, Ni kuma ba mijinta ba ne. Ku roƙe ta ta daina karuwancinta, Ta rabu da masu rungumar mamanta. 3 In ba haka ba, sai in yi mata tsiraici, In bar ta kamar ran da aka haife ta. In maishe ta kamar jeji, In bar ta kamar busasshiyar ƙasa, In kashe ta da ƙishi. 4 Ba zan yi wa 'ya'yanta jinƙai ba, Domin su 'ya'yan karuwanci ne 5 Gama uwarsu ta yi karuwanci. Ita wadda ta haife su ta yi abin kunya. Gama ta ce, ‘Zan bi samarina Waɗanda ke ba ni ci da sha, Da ulu, da lilin, da mai, da ruwan inabi.’ 6 “Don haka zan shinge hanyarta da ƙaya, Zan gina mata garu don kada ta sami hanyar fita. 7 Za ta bi samarinta, amma ba za ta tarar da su ba. Za ta neme su, amma ba za ta same su ba. Sa'an nan za ta ce, ‘Zan koma wurin mijina na fari, Gama zamana na dā ya fi na yanzu!’ 8 “Amma ba ta sani ni nake ba ta hatsi, da ruwan inabi, da mai, Da azurfa, da zinariya da yawa Waɗanda suka bauta wa gunkin nan Ba'al da su ba. 9 Don haka zan hana mata hatsi a kakarsa, Da ruwan inabi a kakarsa, da kuma ulu da lilin Waɗanda suka zama abin rufe tsiraicinta. 10 Yanzu zan buɗe tsiraicinta A idon samarinta, Ba kuwa wanda zai cece ta daga hannuna. 11 Zan sa ta daina farin cikinta, Da idodinta, da kiyaye lokatan amaryar wata, Da hutawar ranar Asabar, Da ƙayyadaddun idodinta. 12 Zan ɓata inabinta da itatuwan ɓaure Waɗanda take cewa, ‘Waɗannan su ne hakkina Wanda samarina suka ba ni.’ Zan sa su zama kurmi, Namomin jeji su cinye su. 13 Zan hukunta ta saboda kwanakin idodin gunkin nan Ba'al. A kwanakin nan takan ƙona musu turare, Ta yi ado da zobe da lu'ulu'ai, Ta bi samarinta, amma ta manta da ni.” In ji Ubangiji. 14 “Don haka, ga shi, zan rarrashe ta, In kai ta cikin jeji, In ba ta magana. 15 Can zan ba ta gonar inabi, In mai da kwarin Akor, wato wahala, ƙofar bege. A can za ta amsa mini kamar a kwanakin ƙuruciyarta, Kamar lokacin da ta fito daga ƙasar Masar. 16 Ni Ubangiji na ce, a waccan rana Za ta ce da ni, ‘Mijina,’ ba za ta ƙara ce da ni Ba'al ba. 17 Zan kawar da sunayen Ba'al daga bakinta. Ba za a ƙara kiransu da sunayensu ba. 18 “A waccan rana zan yi alkawari Da namomin jeji, da tsuntsaye, Da abubuwa masu rarrafe saboda Isra'ila. Zan kuma kakkarya baka da takobi, In kuma sa yaƙi ya ƙare a ƙasar, Sa'an nan za su yi zamansu lami lafiya. 19 Zan ɗaura aure da ke cikin adalci, Da bisa kan ka'ida, da ƙauna. 20 Zan ɗaura aure da ke cikin aminci, Za ki kuwa sani, ni ne Ubangiji. 21 “A waccan rana, zan amsa wa sammai, Su kuma za su amsa wa ƙasa. 22 Ƙasa kuma za ta amsa wa hatsi, da ruwan inabi, da mai, Su ma za su amsa wa Yezreyel. 23 Zan dasa ta a ƙasa domin kaina. Zan kuma yi wa ‘Ba-jinƙai,’ jinƙai, In kuma ce wa ‘Ba-mutanena ba,’ ‘Mutanena!’ Su ma za su ce, ‘Kai ne Allahna!’ ”

Yusha’u 3

Yusha'u da Karuwa

1 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka sāke tafiya, ka ƙaunaci karuwa wadda take tare da kwartonta. Ka ƙaunace ta kamar yadda ni Ubangiji nake ƙaunar mutanen Isra'ila, ko da ya ke suna bin gumaka, suna ƙaunar wainar zabibi da aka miƙa wa gumaka.” 2 Sai na ba da sadakinta a bakin tsabar azurfa goma sha biyar, da buhu biyu na sha'ir. 3 Sa'an nan na ce mata, “Ki keɓe kanki kwanaki da yawa domina, kada ki yi kwartanci, ki kwana da wani, ni kuma ba zan shiga wurinki ba.” 4 Gama mutanen Isra'ila za su zauna kwanaki da yawa ba sarki, ba shugaba, ba sadaka, ba al'amudi, ba falmaran, ba kan gida. 5 Bayan wannan mutanen Isra'ila za su komo su nemi Ubangiji Allahnsu, da Dawuda, sarkinsu. Da tsoro za su komo zuwa wurin Ubangiji domin alheransa a kwanaki na ƙarshe.

Ubangiji ya Soki Mutanen Isra'ila

Yusha’u 4

1 Ya ku mutanen Isra'ila, ku ji maganar Ubangiji, Gama Ubangiji yana da shari'a da ku, ku mazaunan ƙasar. “Gama ba gaskiya, ko ƙauna, Ko sanin Ubangiji a ƙasar. 2 Akwai rantsuwa, da ƙarya, da kisankai, da sata, da zina, Da kama-karya, da zub da jini a kai a kai. 3 Saboda haka ƙasar za ta yi makoki, Dukan waɗanda ke zaune a cikinta za su yi yaushi. Namomin jeji kuma, da tsuntsaye, da kifaye za su ƙare. 4 “Duk da haka kada wani ya sa wa mutum laifi, Kada wani kuma ya tsautar. Da ku nake magana, ku firistoci. 5 Za ku yi tuntuɓe da rana, Annabi kuma zai yi tuntuɓe tare da kai da dare, Ni kuwa zan hallaka mahaifiyarku. 6 Mutanena sun lalace saboda jahilci. Tun da ya ke sun ƙi ilimi, Ni ma na ƙi ku da zan firist ɗina. Tun da ya ke kun manta da umarnan Allahnka, Ni ma zan manta da 'ya'yanku. 7 “Yawan ƙaruwar firistoci, yawan ƙaruwar zunubi. Zan sāke darajarsu ta zama kunya. 8 Suna ciyar da kansu da zunubin mutanena, Suna haɗamar ribar muguntarsu. 9 Kamar yadda mutane suke, haka firistocin suke, Zan hukunta su saboda al'amuransu, Zan sāka musu gwargwadon ayyukansu. 10 Za su ci, amma ba za su ƙoshi ba. Za su yi karuwanci, amma ba za su ƙaru ba. Gama sun rabu da Ubangiji don su bauta wa gumaka. 11 “Karuwanci, da ruwan inabi, Da ruwan inabin da bai sa hauka ba sukan kawar da hankali. 12 Mutanena sukan yi tambaya a wurin abin da aka yi da itace, Sandansu yakan faɗa musu gaiɓu, Gama ruhun karuwanci ya ɓad da su, Sun rabu da Allahnsu don su yi karuwanci. 13 Suna miƙa sadaka a bisa ƙwanƙolin duwatsu. Suna yin hadaya a bisa tuddai, Da kuma a gindin itacen oak, da aduruku, da katambiri, Domin suna da inuwa mai kyau. “Don haka 'ya'yanku mata suke karuwanci, Surukanku mata suke yin zina. 14 Ba zan hukunta 'ya'yanku mata sa'ad da suka yi karuwanci ba, Ko kuwa surukanku mata sa'ad da suka yi zina ba, Gama mazan da kansu sukan shiga wurin karuwai. Sukan miƙa sadaka tare da karuwai a Haikali, Mutane marasa fahimi za su lalace. 15 “Ko da ya ke mutanen Isra'ila suna karuwanci, Kada kuma mutanen Yahuza su yi laifi. Kada ku tafi Gilgal, Ko ku haura zuwa Bet-awen. Kada ku yi rantsuwa da cewa, ‘Har da zatin Ubangiji!’ 16 Mutanen Isra'ila masu taurinkai ne kamar alfadari. Ta yaya Ubangiji zai yi kiwonsu Kamar 'ya'yan tumaki a makiyaya mai fāɗi? 17 Mutanen Ifraimu sun haɗa kai da gumaka, Sai a rabu da su. 18 Su taron mashaya ne kawai, Karuwai ne kuma. Suna ƙaunar abin kunya. 19 Iska ta ƙunshe su cikin fikafikanta. Za suji kunyar bagadansu.”

Hukunci a kan Riddar Isra'ilawa

Yusha’u 5

1 “Ku ji wannan, ya ku firistoci! Ku saurara, ya mutanen Isra'ila! Ku kasa kunne, ya gidan sarki! Gama za a yi muku hukunci, Domin kun zama tarko a Mizfa, Da ragar da aka shimfiɗa a bisa Tabor. 2 Sun tayar, sun yi zurfi cikin zunubi, Zan hore su duka. 3 Na san Ifraimu, Isra'ila kuma ba a ɓoye take a gare ni ba. Gama Ifraimu ta yi aikin karuwanci, Isra'ila kuma ta ƙazantu. 4 “Ayyukansu ba su bar su Su koma wurin Allahnsu ba, Gama halin karuwanci yana cikinsu, Don haka kuma ba su san Ubangiji ba. 5 Girmankan mutanen Isra'ila yana ba da shaida a kansu. Mutanen Ifraimu za su yi tuntuɓe cikin laifinsu. Mutanen Yahuza kuma za su yi tuntuɓe tare da su. 6 Da garkunan tumaki da na awaki, da na shanunsu Za su tafi neman Ubangiji, Amma ba za su same shi ba, Gama ya rabu da su. 7 Sun ci amanar Ubangiji. Su haifi shegu. Yanzu amaryar wata za ta cinye su da gonakinsu.

Yaƙi Tsakanin Mutanen Yahuza da na Isra'ila

8 “Ku busa ƙaho cikin Gibeya, Ku busa kakaki cikin Rama, Ku yi gangami cikin Bet-awen, Ku yi rawar yaƙi, ya ku Biliyaminu! 9 Ifraimu za ta zama kango a ranar hukunci. A kabilan Isra'ila na sanar da abin da zai faru, ba makawa. 10 “Shugabannin Yahuza sun zama kamar masu cin iyaka, Zan zubo musu da fushina kamar ruwa. 11 An danne Ifraimu, shari'a ta murƙushe ta, Domin ta ƙudura ta bi banza. 12 Domin haka na zama kamar asu ga Ifraimu, Kamar ruɓa ga mutanen Yahuza. 13 “Sa'ad da Ifraimu ta ga ciwonta, Yahuza kuma ta ga rauninta, Sai Ifraimu ta aika zuwa Assuriya, Wurin babban sarki. Amman ba zai iya warkar da ciwonki, ko rauninki ba. 14 Zan zama kamar zaki ga Ifraimu, Kamar sagarin zaki ga mutanen Yahuza. Ni kaina zan yayyage, in yi tafiyata. Zan ɗauka, in tafi, ba wanda zai yi ceto.

Isra'ila ta Yi Tuban Muzuru

15 “Zan koma wurin zamana Sai lokacin da suka yarda sun yi zunubi, su neme ni. A cikin ƙuncinsu za su neme ni.”

Yusha’u 6

1 Mutane sun ce, “Zo, mu koma wurin Ubangiji, Gama shi ne ya yayyaga, Shi ne kuma zai warkar. Shi ne ya yi mana rauni, Shi ne kuma zai ɗaure raunin da maɗauri. 2 Bayan kwana biyu zai rayar da mu. A rana ta uku kuwa zai tashe mu Mu yi zammanmu a gabansa. 3 Mu nace domin mu san Ubangiji Zuwansa tabbatacce ne kamar wayewar gari. Zai zo wurinmu kamar ruwan sama, Kamar ruwan bazara da ke shayar da ƙasa.”

Amsar Ubangiji

4 Ubangiji ya ce, “Me zan yi da ke, ya Ifraimu? Me zan yi da ke, ya Yahuza? Ƙaunarku tana kama da ƙāsashi, Kamar kuma raɓar da ke watsewa da wuri. 5 Domin haka na sassare su ta wurin annabawansu, Na karkashe su da maganar bakina. Hukuntaina suna kama da hasken da ke ketowa. 6 Gama ƙauna nake so, ba sadaka ba, Sanin Allah kuma fiye da hadayu na ƙonawa. 7 “Amma sun ta da alkawarina kamar Adamu, Sun ci amanata. 8 Gileyad gari ne na masu aikata mugunta. Tana da tabban jini. 9 Kamar yadda mafasa sukan yi fakon mutum, Hakanan firistoci suka haɗa kansu Don su yi kisankai a hanyar Shekem, Ai, sun aikata mugayen abubuwa. 10 Na ga abin banƙyama a cikin Isra'ila, Karuwancin Ifraimu yana wurin, Isra'ila ta ƙazantar da kanta. 11 “Ku kuma, ya mutanen Yahuza, an shirya muku ranar girbi, A lokacin da zan mayar wa mutanena da dukiyarsu.”

Yusha’u 7

Zunubin Isra'ila da Tayarwarta

1 “Sa'ad da zan warkar da mutanen Isra'ila, Sai zunubin Ifraimu da muguntar Samariya su bayyana, Gama suna cin amana. Ɓarawo yakan fasa, ya shiga, 'Yan fashi suna fashi a fili, 2 Amma ba su tunani, Cewa zan tuna da dukan muguntarsu. Yanzu ayyukansu sun kewaye su, Ina ganinsu. 3 “Suna faranta zuciyar sarki da muguntarsu, Na shugabanni kuma da ƙarairayinsu. 4 Dukansu mazinata ne, Suna kama da tanda da aka zafafa, Wadda matoyi ya daina iza mata wuta, Tun daga lokacin cuɗe kullu Har zuwa lokacin da yisti ya tasar da shi. 5 A ranar bikin sarki, Sukan sa sarki da shugabanni su bugu da ruwan inabi. Yakan yi cuɗanya da shakiyai. 6 Zukatansu suna ƙuna da ƙullaƙulle kamar tanderu. Fushinsu na ci dare farai, Da safe fushinsu yana ci ba-ba kamar harshen wuta. 7 “Dukansu suna da zafi kamar tanderu. Suna kashe masu mulkinsu. Dukan sarakunansu sun faɗi. Ba wanda ya kawo mini kuka.”

Ifraimu ta Haɗu da Al'ummai

8 Ubangiji ya ce, “Mutanen Ifraimu sun haɗa kansu da al'ummai, Sun zama kamar wainar da ba a juya ba. 9 Baƙi sun cinye ƙarfinsu, su kuwa ba su sani ba, Furfura ta faso musu, amma ba su sani ba. 10 Girmankan mutanen Isra'ila ya kai ƙararsu, Duk da haka ba wanda ya komo wurin Ubangiji Allahnsu, Ba su kuwa neme shi ba. 11 Ifraimu kamar kurciya take, marar wayo, marar hankali, Takan tafi Masar da Assuriya neman taimako. 12 Lokacin da suke tafiya, zan shimfiɗa musu ragata, Zan saukar da su ƙasa kamar yadda akan yi wa tsuntsun da ke tashi sama. Zan hukunta su saboda mugayen ayyukansu. 13 “Tasu ta ƙare, gama sun ratse, sun rabu da ni. Halaka za ta auka musu domin sun tayar mini. Ko da ya ke zan cece su, duk da haka suna faɗar karya a kaina. 14 Ba su yi kuka gare ni da zuciya ɗaya ba, Sa'ad da suke kuka a gadajensu, Sun tsattsaga jikinsu domin abinci da ruwan inabi. Sun yi mini tawaye. 15 Ko da ya ke na horar da su, na ƙarfafa damatsansu, Duk da haka suna shirya mini maƙarƙashiya. 16 Sun juya mini baya, suna bin gunkin nan Ba'al. Suna kama da tankwararren baka. Za a kashe shugabanninsu da takobi Saboda maganganunsu na fariya. Za su zama abin ba'a a ƙasar Masar.”

Yusha’u 8

An Tsauta Wa Isra'ila don Tsafi

1 Ubangiji ya ce, “Ki sa ƙaho a bakinki, Kamar gaggafa, haka maƙiyi ya kawo sura a kan ƙasar Ubangiji, Domin mutanena sun ta da alkawarina, Sun kuma keta dokokina. 2 Sun yi kuka a wurina, Suna cewa, ‘Ya Allah, mu Isra'ila mun san ka!’ 3 Isra'ila ta ƙi abin da ke mai kyau, Don haka abokan gāba sun fafare ta. 4 “Suna naɗa sarakuna, amma ba da iznina ba. Suna naɗa shugabanni amma ba da yardata ba. Suna ƙera gumaka da azurfarsu da zinariyarsu, Wannan kuwa zai zama sanadin halakarsu. 5 Ya mutanen Samariya, ina ƙin maraƙinku na siffa. Ina jin haushinsu ƙwarai! Sai yaushe za su rabu da gumaka? 6 Ai, mai aikin hannu ne ya yi shi a Isra'ila! Gunki ne ba Allah ba ne. Za a farfashe siffar maraƙin Samariya. 7 Gama sun shuka iska Don haka zu su girbe guguwa. Hatsin da ke tsaye ba shi da zangarniya, Ba zai yi tsaba ba. Ko da ya yi tsaba ma, baƙi ne za su ci, 8 Isra'ila kamar kowace al'umma ce. Suna cikin al'ummai Kamar kaskon da ba shi da amfani, 9 Gama sun haura zuwa Assuriya, Kamar jakin jeji da ke yawo shi kaɗai. Mutanen Ifraimu sun yi ijara da abokan tsafinsu. 10 Ko da ya ke sun yi ijara da abokai daga cikin al'ummai, Yanzu zan tattara su, in hukunta su. Sa'an nan za su fara ragowa, Ta wurin tunanin nawayar Sarkin sarakuna. 11 “Da ya ke Ilfraimu ta yawaita bagadan zunubi, Sun zama mata bagadai na yin zunubi. 12 Ko da na rubuta mata dokokina sau kam, Za ta ɗauke su wani baƙon abu ne kawai. 13 Suna jin daɗin miƙa hadayu don cin naman, Amma Ubangiji ba ya jin daɗinsu. Ubangiji zai tuna da muguntarsu, Zai hukunta su saboda zunubansu. Za su koma Masar. 14 “Gama mutanen Isra'ila sun manta da Mahaliccinsu, Sai sun gina manyan gidaje masu daraja. Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu, Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu, Ta ƙone fādodinsu.”

Yusha’u 9

Hukuncin da za a Yi wa Isra'ila domin Rashin Aminci

1 Kada ku yi farin cikin, ya mutanen Isra'ila! Kada ku yi murna kamar sauran mutane! Gama kun yi karuwanci, kun rabu da Allahnku. Kuna ƙaunar ijarar karuwanci a kowane masussuka. 2 Masussuka da wurin matsa ruwan inabi ba za su ciyar da su ba. Sabon ruwan inabi kuma ba zai ishe su ba. 3 Ba za su zauna a ƙasar Ubangiji ba, Amma mutanen Ifraimu za su koma Masar. Za su ci haramtaccen abinci a Assuriya. 4 Ba za su yi wa Ubangiji hadaya ta sha ba. Ba za su faranta zuciyarsa da sadakoki ba. Abincinsu zai zama irin na masu makoki. Duk wanda ya ci shi zai haramta. Gama abincinsu zai yi musu maganin yunwa ne kawai, Ba za su kai shi Haikalin Ubangiji ba. 5 Me za ku yi a ƙayyadaddiyar ranar idi? Da a ranar idin Ubangiji? 6 Ga shi kuma, suna tafiya zuwa halaka, Masar za ta tattara su, Memfis za ta binne su. Ƙayayuwa za su mallaki abubuwan tamaninsu na azurfa. Sarƙaƙƙiya za ta tsiro a cikin alfarwansu. 7 Ranar hukunci ta zo, ranar ramako ta iso, Isra'ila za ta sani! An ce annabi wawa ne, Mutumin da ke da ruhu kuwa mahaukaci ne, Saboda yawan muguntarku da ƙiyayyarku. 8 Ifraimu mai tsaro ne a gaban Allahna, annabi kuwa, Duk da haka sun zama kamar mai kafa tarkon kama tsuntsu, a farkon kaka. Akwai ƙiyayya a cikin Haikalin Allahnsu. 9 Sun yi zurfi cikin rashin gaskiya Kamar a kwanakin Gibeya, Ubangiji zai tuna da muguntarsu. Zai hukunta su saboda zunubansu. 10 Ubangiji ya ce, “Na iske Isra'ila a jeji kamar inabi, Na ga kakanninku kamar nunan fari na 'ya'yan ɓaure, Amma da suka zo Ba'al-feyor, sai suka keɓe kansu ga Ba'al. Suka zama abin ƙyama kamar abin da suke ƙauna. 11 Darajar Ifraimu za ta tashi kamar tsuntsu, Ba haihuwa, ba juna biyu, ba ɗaukar ciki! 12 Ko sun goyi 'ya'ya, Zan sa su mutu tun ba su balaga ba. Tasu ta ƙare sa'ad da na rabu da su!” 13 Ya Ubangiji, na ga yadda Ifraimu Ta mai da 'ya'yanta ganima Tana fitar da su zuwa wurin yanka. 14 Ya Ubangiji, me zan ce ka ba su? Me za ka ba su? Ka ba su cikin da ba ya haihuwa da busassun mama. 15 Ubangiji ya ce, “Kowace irin muguntarsu tana a Gilgal, A can na ƙi su! Saboda mugayen ayyukansu, zan kore su daga ƙasata, Ba kuma zan ƙaunace su ba. Dukan shugabanninsu 'yan tayarwa ne. 16 An ka da mutanen Ifraimu, saiwarsu ta bushe. Ba za su yi 'ya'ya ba. Ko ma sun haihu, zan kashe 'ya'yan nan nasu waɗanda suke ƙauna.” 17 Allahna zai ƙi su Domin ba su yi masa biyayya ba. Za su zama masu yawo cikin al'ummai.

Yusha’u 10

1 Isra'ila kurangar inabi ce mai bansha'awa Wadda ke ba da 'ya'ya da yawa. Ƙara yawan arzikinsu, Ƙara gina bagadansu. Ƙara yawan wadatar ƙasarsu. Ƙara kyautata ginshiƙansu. 2 Zuciyarsu ta munafunci ce, Yanzu tilas za su ɗauki hakkin laifinsu, Ubangiji zai farfashe bagadansu da ginshiƙansu. 3 Gama yanzu za su ce, “Ba mu da sarki, Domin ba mu ji tsoron Ubangiji ba. Amma me sarki zai yi mana?” 4 Surutai kawai suke yi, Suna yin alkawaran ƙarya, Don haka hukunci zai zaburo kamar muguwar ciyawa mai dafi a kunyoyin gona. 5 Mazaunan Samariya suna rawar jiki Domin ɗan maraƙin Bet-awen, Mutane za su yi makoki dominsa, Firistoci matsafa, za su yi kururuwa dominsa, Da kuma darajarsa wadda ta rabu da shi. 6 Za a kai ɗan maraƙin a Assuriya Don a biya wa sarki haraji. Za da kunyatar da Ifraimu, Isra'ila kuwa za ta ji kunya saboda shawararta. 7 Sarakunan Samariya za su ɓace, Kamar kumfa a bisa ruwa. 8 Za a hallaka masujadan tuddai na Awen inda Isra'ila suke yin zunubi, Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma a bagadansu. Za su ce wa manyan duwatsu, “Ku rufe mu!” Su ce wa tuddai, “Ku faɗo bisa kanmu!” 9 Ubangiji ya ce, “Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra'ila! Tun daga wancan lokaci kuka yi ta ci gaba. Ashe, yaƙi ba zai tarshe su a Gibeya ba? 10 Zan fāɗa wa waɗannan mutane masu zunubi, in hukunta su. Za a tattara al'ummai, su yi gāba da su, Za a hukunta su saboda yawan zunubansu. 11 “Ifraimu horarriyar karsana ce, Wadda ke jin daɗin yin sussuka, Amma na sa wa kyakkyawan wuyanta karkiya, Na sa Yahuza ta ja garmar noma, Yakubu kuwa za ta ja garmar bajiya. 12 Ku shuka wa kanku adalci, Kugirbe albarkun ƙauna, Ku yi kautun saurukanku, Gama lokacin neman Ubangiji ya yi, Domin ya zo, ya koya muku adalci. 13 Kun shuka mugunta, Kun girbe rashin adalci, Kun ci amfanin ƙarya. “Da ya ke dogara ga hanyarku da ɗumbun sojojinku, 14 Domin haka hayaniyar yaƙi za ta tashi a tsakanin jama'arku. Dukan kagaranku za a hallaka su. Kamar yadda Shalmanesar ya hallaka Bet-arbel a ranar yaƙi. An fyaɗa uwaye da 'ya'yansu a ƙasa. 15 Haka za a yi muku, ya mutanen Betel, saboda yawan muguntarku. Da asuba za a datse Sarkin Isra'ila.”

Yusha’u 11

Ƙaunar Allah Zuwa ga Mutanensa Masu Tayarwa

1 “A lokacin da Isra'ila ke yaro, na ƙaunace shi, Daga cikin Masar na kirawo ɗana. 2 Yawan kiransu, yawan tayarwar da suke yi mini, Sai ƙara miƙa wa Ba'al sadaka suke yi, Suna ƙona turare ga gumaka. 3 Ko da ya ke ni ne na koya wa Ifraimu tafiya. Na ɗauke su a hannuna, Amma ba su sani ni ne na lura da su ba. 4 Na bishe su da linzamin alheri da ragamar ƙauna, Na zama musu kamar wanda ke ɗauke musu karkiya daga muƙamuƙansu. Na sunkuya, na ciyar da su. 5 “Ba su koma ƙasar Masar ba, Amma Assuriya za ta zama sarkinsu Gama sun ƙi yarda su koma wurina. 6 Takobi zai ragargaje biranensu, Zai lalatar da sandunan ƙarafan ƙofofinsu, Zai cinye su domin muguwar shawararsu. 7 Mutanena sun himmantu su rabu da ni, Ko da ya ke an kira su ga Ubangiji, Ba wanda ya girmama shi. 8 “Ƙaƙa zan iya rabuwa da ke, ya Ifraimu? Ƙaƙa zan miƙa ki, ya Isra'ila? Ƙaƙa zan maishe ki kamar Adma? Ƙaƙa zan yi da ke kamar Zeboyim? Zuciyata tana motsawa a cikina, Juyayina ya huru. 9 Ba zan aikata fushina mai zafi ba, Ba zan ƙara hallaka Ifraimu ba, Gama ni Allah ne, ba mutum ba, Maitsarki wanda ke tsakiyarku, Ba zan zo wurinku da hasala ba. 10 “Za su bi Ubangiji, Zai yi ruri kamar zaki, hakika zai yi ruri 'Ya'yansa za su zo da rawar jiki da yamma. 11 Da sauri za su zo kamar tsuntsaye daga Masar, Kamar kurciyoyi daga ƙasar Assuriya, Zan komar da su gidajensu, ni Ubangiji na faɗa.”

An Tsauta wa Ifraimu don Ƙarya da Zalunci

12 Ubangiji ya ce, “Ifraimu ta kewaye ni da ƙarairayi, Jama'ar Isra'ila kuwa ta kewaye ni da munafuncinta, Yahuza kuma ta tayar wa Allah, Wato tana gāba da Mai Tsarki, mai aminci.

Yusha’u 12

1 Ifraimu tana kiwon iska, Tana ta bin iskar gabas dukan yini. Tana riɓaɓɓanya ƙarya da kamakarya. Tana ƙulla yarjejeniya da Assuriya, Tana kai mai a Masar.” 2 Ubangiji yana da magana game da mutanen Yahuza, Zai hukunta Isra'ila saboda hanyoyinta, Zai sāka mata gwargwadon ayyukanta. 3 A cikin mahaifa kakansu Yakubu ya kama diddigen ɗan'uwansa, Sa'ad da ya zama baligi ya yi kokawa da Allah. 4 Ya yi kokawa da mala'ika ya yi rinjaye. Ya yi kuka, ya roƙi albarka. Ya sadu da Allah a Betel, A can Allah ya yi magana da shi. 5 Ubangiji Allah Mai Runduna, Sunansa Ubangiji, 6 Sai ku koma wurin Allahnku, Ku yi alheri, ku yi adalci, Ku saurari Allahnku kullayaumin. 7 Ubangiji ya ce, “Ɗan kasuwa wanda ke da ma'aunin algus a hannunsa. Yana jin daɗin yin zalunci. 8 Mutanen Ifraimu sun ce, ‘Hakika, mun zama attajirai, Mun samar wa kanmu dukiya. A cikin harkokinmu ba za a sami wata mugunta ba.’ 9 Ni ne Ubangiji Allahnku tun daga ƙasar Masar, Zan kuma sa ku zauna cikin alfarwai, Kamar lokatan ƙayyadaddun idodi. 10 “Na yi magana da annabawa, Ni ne na ba da wahayi da yawa, Da misalai kuma ta wurin annabawa. 11 Idan akwai laifi a Gileyad, Hakika za su zama wofi. A Gilgal ana sadaka da bijimai, Bagadansu za su zama kamar tsibin duwatsu A gyaffan kunyoyin gona.” 12 Kakanmu Yakubu ya gudu zuwa ƙasar Aram, A can Isra'ila ya yi barantaka saboda mace, Saboda mace ya yi kiwon tumaki. 13 Ta wurin annabi Ubangiji ya fito da mutanen Isra'ila daga Masar, Ta wurin annabi kuma ya kiyaye su. 14 Mutanen Ifraimu sun yi muguwar tsokana mai ta da fushi, Domin haka Ubangiji zai ɗora musu hakkin jini a kansu, Zai saka musu cin mutuncin da suka yi.

Yusha’u 13

Za a Hallaka a Ifraimu

1 Sa'ad da Ifraimu ta yi magana, mutane suka yi rawar jiki. An ɗaukaka ta cikin Isra'ila, Amma ta yi laifi ta wurin bauta gunkin nan Ba'al, Ta kuwa mutu. 2 Har yanzu suna ta ƙara yin zunubi, Suna yi wa kansu gumaka na zubi, Da gwaninta sukan yi gumaka da azurfarsu, Dukansu aikin hannu ne. Sukan ce, “Ku miƙa wa waɗannan hadayu!” Mutane sukan sumbaci siffofin maruƙa. 3 Don haka za su zama kamar ƙāsashi da akan yi da safe, Ko kuwa kamar raɓa mai kakkaɓewa da wuri. Za su zama kamar ƙaiƙayi wanda ake shiƙarsa cikin iska a masussuka, Ko kuwa kamar hayaƙin da ke fita ta bututu. 4 Ubangiji ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku Tun daga ƙasar Masar. Banda ni ba ku san wani Allah ba, Banda ni kuma ba wani mai ceto. 5 Ni ne wanda ya san ku a cikin jeji, A ƙasar da ke da ƙarancin ruwan sama. 6 Sa'ad da suka sami wurin kiwo, suka ƙoshi, Sai suka yi girmankai, Suka manta da ni. 7 Zan zama musu kamar zaki, Kamar damisa zan yi kwanto a gefen hanya. 8 Zan auka musu kamar beyar, Wadda aka ƙwace mata 'ya'ya. Zan yage ƙirjinsu, in cinye su kamar zaki, Kamar mugun naman jeji zan yayyage su. 9 “Zan hallaka ku, ya mutanen Isra'ila! Wanene zai taimake ku? 10 Yanzu ina sarkinku da zai cece ku? Ina kuma dukan shugabanninku da za su kāre ku? Su waɗanda kuka roƙa, kun ce, ‘Ku naɗa mana sarki da shugabanni.’ 11 Da fushina na naɗa muku sarki, Da hasalata kuma na tuɓe shi. 12 “An ƙunshe muguntar Ifraimu, Zunubinsa kuwa an ajiye shi a rumbu. 13 Naƙudar haihuwarsa ta zo, Amma shi wawan yaro ne, Bai fito daga mahaifar ba. 14 Zan fanshe su daga ikon lahira. Zan fanshe su daga mutuwa. Ya mutuwa, ina annobanki? Ya kabari, ina halakarka? Kan kawar da juyayi daga wurina. 15 Ko da ya ke Isra'ila tana bunƙasa kamar ciyayi, Iskar gabas, wato iskar da za ta zo daga jeji, Za ta busar da maɓuɓɓugarsu da idon ruwansu, Za ta lalatar da abubuwa masu amfani da ke cikin taskarsu. 16 Samariya za ta ɗauki hakkin zunubinta, Gama ta tayar wa Allahnta. Za a kashe mutanenta da takobi. Za a fyaɗa jariranta a ƙasa, A kuma tsage matanta masu ciki.”

Yusha’u 14

Ana Roƙon Isra'ila ta Komo wurin Ubangiji

1 Ya mutanen Isra'ila, ku komo wurin Ubangiji Allahnku, Gama zunubinku ya sa kun yi tuntuɓe. 2 Ku komo wurin Ubangiji, ko roƙe shi, Ku ce, “Ka gafarta mana zunubanmu, Mu kuwa za mu yabe ka da bakinmu. 3 Assuriya ba za mu hau dawakai ba. Ba za mu kuma ƙara ce da aikin hannuwanmu, ‘Kai ne Allahnmu,’ ba. A wurinka ne maraya yakan sami jinƙai.”

Ubangiji ya Yi wa Isra'ila Alkawarin Sabon Rai

4 Ubangiji ya ce, “Zan warkar musu da riddarsu. Zan kuma ƙaunace su sosai, Gama fushina zai huce. 5 Zan ama kamar raɓa ga Isra'ila, Isra'ila za ta yi fure kamar lili, Saiwarta za ta shiga kamar itacen al'ul. 6 Tohonta zai buɗo, Kyanta zai zama kamar itacen zaitun, Ƙashinta kuwa kamar itacen al'ul na Lebanon. 7 Waɗanda za su komo, za su zauna a inuwarta, Za su yi noman hatsi da yawa. Za su yi fure kamar kurangar inabi. Ƙanshinsu zai zama kamar ruwan inabi na Lebanon. 8 Ya mutanen Ifraimu, me zan yi da gumaka? Ni ne wanda ke amsa muku, mai lura da ku kuma. Ni kamar itacen fir ne mai ganyaye kore shar. Daga gare ni, kuke samun 'ya'ya.” 9 Duk wanda ke da hikima, bari ya fahimci abubuwan nan. Duk wanda ke da ganewa, bari ya san abubuwan nan, Gama hanyoyin Ubangiji masu gaskiya ne, Masu adalci kuwa za su yi tafiya a cikinsu, Amma masu zunubi za su yi tuntuɓe a kansu.

Yowel 1

Ɓarnar Fāra

1 Maganar Ubangiji zuwa ga Yowel, ɗan Fetuwel. 2 Ku dattawa, ku kasa kunne, Bari kowa da kowa da ke cikin Yahuza, ya kasa kunne. Wani abu mai kamar wannan ya taɓa faruwa a lokacinku, Ko a lokacin kakanninku? 3 Ku faɗa wa 'ya'yanku labarinsa, 'Ya'yanku kuma su faɗa wa 'ya'yansu, 'Ya'yansu kuma su faɗa wa tsara mai zuwa. 4 Abin da ɗango ya bari fara ta ci, Abin da fara ta bari burduduwa ta ci. 5 Ku farka, ku yi ta kuka, ku bugaggu, Ku yi kuka, ku mashayan ruwan inabi, An lalatar da 'ya'yan inabin Da ake yin sabon ruwan inabi da su. 6 Rundunar ta aukar wa ƙasarmu, Tana da ƙarfi, ba ta kuma ƙidayuwa, Haƙoranta suna da kaifi kamar na zaki. 7 Ta lalatar da kurangar inabinmu, Ta cinye itatuwan ɓaurenmu. Ta gaigaye ɓawo duka, Saboda haka rassan sun zama fari fat. 8 Ya jama'a, ku yi kuka Kamar yarinyar da ke makokin rasuwar saurayinta. 9 Ba hatsi ko ruwan inabin Da za a yi hadaya da su cikin Haikalin. Firistoci masu miƙa wa Ubangiji hadaya suna makoki. 10 Ba kome a gonaki, Ƙasa tana makoki, Domin an lalatar da hatsin, 'Ya'yan inabi sun bushe, Itatuwan zaitun kuma sun yi yaushi. 11 Ya ku manoma, ku yi baƙin ciki, Ku yi kuka, ku da kuke lura da gonakin inabi, Gama alkama, da sha'ir, Da dukan amfanin gonaki sun lalace. 12 Kurangar inabi ta bushe, Itatuwan ɓaure kuma sun yi yaushi, Rumman, da dabino, da gawasa, Da dukan itatuwan gonaki sun bushe. Murna ta ƙare a wurin mutane. 13 Ya ku firistoci masu miƙa hadayu a bagaden Ubangiji, Ku sa tufafin makoki, ku yi kuka! Ku shiga Haikali, ku kwana, Kuna saye da tufafin makoki, Gama ba hatsi ko ruwan inabi da za a yi hadaya da su, A cikin Haikalin Allahnku. 14 Ku sa a yi azumi, Ku kira muhimmin taro. Ku tara dattawa da dukan mutanen ƙasar A Haikalin Ubangiji Allahnku, Ku yi kuka ga Ubangiji. 15 Taku ta ƙare a wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, Halaka daga wurin Maɗaukaki ta zo. 16 An lalatar da amfanin gonaki a kan idonmu, Ba murna a Haikalin Allahnmu. 17 Itatuwa sun mutu a busasshiyar ƙasa, Ba hatsin da za a adana a rumbu, Rumbuna sun lalace domin ba hatsi. 18 Dabbobi suna nishi! Garkunan shanu sun ruɗe Domin ba su da makiyaya. Garkunan tumaki da awaki kuma suna shan azaba. 19 Ina kuka a gare ka, ya Ubangiji, Domin ciyayi da itatuwa sun bushe, Sai ka ce wuta ce ta ƙone su. 20 Har ma namomin jeji suna kuka a gare ka, Domin rafuffuka sun bushe, Ciyayi kuma sun bushe, Sai ka ce wuta ce ta ƙone su.

Yowel 2

Fāra ta Zama musu Alamar Ranar Ubangiji

1 Ku busa ƙaho, ku yi gangami, A cikin Sihiyona, tsattsarkan dutsen Allah! Duk mutanen ƙasar za su yi rawar jiki, Domin ranar Ubangiji tana zuwa, ta yi kusa. 2 Za ta zama rana ce mai duhu dulum, Ranar gizagizai ce baƙi ƙirin. Runduna mai ƙarfi tana tasowa, Kamar ketowar hasken safiya bisa tsaunuka. Faufau ba a taɓa ganin irinta ba, Ba kuwa za a sāke ganin irinta ba. 3 Tana cinye shuke-shuke kamar wuta, Ƙasa kamar gonar Adnin take kafin ta zo, Amma a bayanta ta zama hamada, Ba abin da ya tsere mata. 4 Kamar doki take, Tana gudu kamar dokin yaƙi. 5 Motsin tsallenta a kan duwatsu kamar Motsin karusa ne. Kamar kuma amon wutar da ke cin tattaka. Kamar runduna mai ƙarfi wadda ta ja dāgar yaƙi. 6 Da zuwanta mutane sukan firgita, Dukan fuskoki sukan ɓaci. 7 Takan auka kamar mayaƙa, Takan hau garu kamar sojoji, Takan yi tafiya, Kowa ta miƙe sosai inda ta sa gaba, Ba ta kaucewa. 8 Ba ta hawan hanyar juna, Kowa tana bin hanyarta. Takan kutsa cikin abokan gāba, ba a iya tsai da ita. 9 Takan ruga cikin birni, Takan hau garu a guje, Takan hau gidaje, Takan shiga ta tagogi kamar ɓarawo. 10 Duniya takan girgiza saboda ita, Sammai sukan yi rawar jiki. Rana da wata sukan duhunta, Taurari kuwa sukan daina haskakawa. 11 Ubangiji yakan umarci rundunarsa, Rundunarsa mai cika umarninsa babba ce, mai ƙarfi, Gama ranar Ubangiji babba ce mai banrazana. Wa zai iya daurewa da ita?

Jinƙan Ubangiji

12 “Koyanzu,” in ji Ubangiji, “Ku juyo wurina da zuciya ɗaya, Da azumi, da kuka, da makoki, 13 Ku kyakkece zuciyarku, ba tufafinku kaɗai ba.” Ku komo wurin Ubangiji Allahnku. Gama shi mai alheri ne, mai jinƙai, Mai jinkirin fushi ne, mai yawan ƙauna, Yakan tsai da hukunci. 14 Wa ya sani ko Ubangiji Allahnmu zai sāke nufinsa, Ya sa mana albarka, Har mu miƙa masa hadaya ta gari da ta sha? 15 Ku busa ƙaho a Sihiyona, Ku sa a yi azumi, Ku kira muhimmin taro. 16 Ku tattara jama'a wuri ɗaya, Ku tsarkake taron jama'a, Ku tattara dattawa da yara, Har da jarirai masu shan mama. Ku sa ango ya fito daga cikin turakarsa, Amarya kuma ta fito daga cikin ɗakinta. 17 Sai firistoci masu hidimar Ubangiji, Su yi kuka a tsakanin shirayi da bagade, Su ce, “Ya Ubangiji, ka ceci jama'arka, Kada ka bar gādonka ya zama abin zargi Da abin ba'a a tsakiyar al'ummai. Don kada al'ummai su ce, ‘Ina Allahnsu?’ ” 18 Sai Ubangiji ya ji kishin ƙasarsa, Ya kuma ji ƙan mutanensa. 19 Sa'an nan ya ce musu, “Ga shi, zan ba ku hatsi da ruwan inabi, da mai, Za ku ƙoshi. Ba zan sa ku ƙara zama abin zargi ga al'ummai ba. 20 Zan kawar muku da waɗanda suka zo daga arewa, Zan kori waɗansunsu zuwa cikin hamada. Zan kori sahunsu na gaba zuwa cikin Tekun Gishiri, Zan kori sahunsu na baya, zuwa cikin Bahar Rum. Gawawwakinsu za su yi ɗoyi. Zan yi musu haka saboda dukan abin da suka yi muku.” 21 Kada ki ji tsoro, ya ƙasa, Ki yi farin ciki, ki yi murna, Gama Ubangiji ne ya yi waɗannan manyan al'amura. 22 Kada ku ji tsoro, ku dabbobin saura, Gama wuraren kiwo a jeji sun yi kore shar. Itatuwa suna ta yin 'ya'ya, Itacen ɓaure da kurangar inabi suna ta yin 'ya'ya sosai. 23 Ya ku mutanen Sihiyona, ku yi murna, Ku yi farin ciki da Ubangiji Allahnku, Gama ya ba ku ruwan farko Domin shaidar gafarar da ya yi muku, Ya kwararo muku da ruwan farko da na ƙarshe da yawa kamar dā. 24 Masussukai za su cika da hatsi, Wuraren matse ruwan inabi za su malala da ruwan inabi. 25 “Zan mayar muku da abin da kuka yi hasararsa A shekarun da fara ta cinye amfaninku, Wato ɗango da fara mai gaigayewa, da mai cinyewa, Su ne babbar rundunata wadda na aiko muku. 26 Yanzu za ku ci abinci a wadace ku ƙoshi, Za ku yabi sunan Ubangiji Allahnku, Wanda ya yi muku abubuwa masu banmamaki, Ba kuma za a ƙara kunyatar da mutanena ba. 27 Ku mutanen Isra'ila, za ku sani ina cikinku, Ni ne kuwa Ubangiji Allahnku, ba wani kuma, Ba kuma za a ƙara kunyatar da mutanena ba.”

Za a Ba da Ruhun Allah

28 “Bayan wannan zan zubo Ruhuna a kan jama'a duka, 'Ya'yanku mata da maza za su iyar da saƙona, Tsofaffinku kuwa za su yi mafarkai, Samarinku za su ga wahayi da yawa. 29 A lokacin zan zubo Ruhuna, Har a kan barori mata da maza. 30 “Zan yi faɗakarwa a kan wannan rana A sararin sama da a duniya. Za a ga jini, da wuta, da murtukewar hayaƙi, 31 Rana za ta duhunta, Wata zai zama ja wur kamar jini, Kafin isowar babbar ranan nan mai bantsoro ta Ubangiji. 32 Amma dukan waɗanda suka nemi Ubangiji za su tsira. Kamar yadda Ubangiji ya ce, Akwai waɗanda ke a Dutsen Sihiyona da Urushalima Da za su tsira, Waɗannan da Ubangiji ya zaɓa za su tsira.”

Yowel 3

Shari'ar Al'ummai

1 “A wannan lokaci zan mayar wa Yahuza da Urushalima da wadatarsu. 2 Zan tattara dukan al'ummai, In kai su kwarin Yehoshafat. A can zan yi musu shari'a A kan dukan abin da suka yi wa jama'ata. Sun warwatsa Isra'ilawa a sauran ƙasashe, Suka rarraba ƙasata. 3 Sun jefa kuri'a a kan mutanena, Sun sayar da yara, mata da maza, zuwa bauta Don su biya karuwai da ruwan inabi. 4 “Taya da Sidon, da dukan Filistiya, me kuke so ku yi mini? Kuna ƙoƙari ku rama mini saboda wani abu? Idan haka ne, zan rama muku da gaggawa. 5 Kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe taskata, kun kai cikin haikalinku. 6 Kun kwashe mutanen Yahuza da Urushalima, kun kai su nesa da ƙasarsu, sa'an nan kun sayar da su ga Helenawa. 7 Yanzu zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, zan yi muku abin da kuka yi musu. 8 Zan sa a sayar wa mutanen Yahuza 'ya'yanku mata da maza, su kuma za su sayar da su ga Sabiyawa, can nesa. Ni Ubangiji na faɗa.” 9 Ku sanar wa al'ummai da wannan, Su yi shirin yaƙi, Su kira mayaƙa! Su tattaro sojoji, su zo! 10 Su bubbuge allunan garmunansu, Su yi takuba da su. Su ƙera māsu da wuƙaƙen da ake yi wa itatuwa aski. Sai marar ƙarfi ya ce, “Ni jarumi ne!” 11 Su gaggauta, su zo su al'ummai da ke kewaye, Su tattaru a kwarin. “Ya Ubangiji, ka saukar da rundunarka mai ƙarfi.” 12 “Sai al'ummai su yi shiri, Su zo kwarin Yehoshafat, Gama a can zan zauna in shara'anta al'umman da ke kewaye, 13 Su sa lauje gama hatsin ya isa girbi. Su shiga su tattaka, Gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika. Manyan randuna sun cika suna tumbatsa, Gama muguntarsu da yawa take.” 14 Dubun dubbai suna cikin kwarin da za a yanke shari'a! Gama ranar Ubangiji ta kusa zuwa a kwarin yanke shari'a. 15 Rana da wata sun yi duhu, Taurari kuma ba su haskakawa.

Ceton Yahuza

16 Ubangiji yana magana da ƙarfi daga Sihiyona, Yana tsawa daga Urushalima, Sammai da duniya sun girgiza. Amma Ubangiji shi ne mafakar jama'arsa, Shi ne kagarar mutanen Isra'ila. 17 “Sa'an nan za ku sani ni ne Ubangiji Allahnku, Wanda ke zaune a Sihiyona, tuduna tsattsarka. Urushalima kuma za ta tsarkaka, Sojojin abokan gāba ba za su ƙara ratsawa ta cikinta ba. 18 “A wannan lokaci tsaunuka za su rufu da kurangar inabi, Tuddai za su cika da shanu, Dukan rafuffukan Yahuza za su gudano da ruwa, Maɓuɓɓuga za ta gudano daga Haikalin Ubangiji, Ta shayar da kwarin Shittim. 19 “Masar za ta zama hamada, Edom kuma za ta zama kufai, Saboda kama-karya da suka yi wa mutanen Yahuza, Saboda sun zubar da jinin marasa laifi a ƙasarsu, 20 Za a zauna a Yahuza da Urushalima dukan tsararraki har abada. 21 Zan sāka alhakin jininsu, Ba zan kuɓutar da mai laifi ba, Gama Ubangiji yana zaune a Sihiyona.”

Amos 1

Horon Allah a kan Maƙwabtan Isra'ila

1 Ga zantuttukan Amos, ɗaya daga cikin makiyayan ƙauyen Tekowa. Allah ya bayyana wa Amos wannan saƙo, tun shekara biyu kafin girgizar duniya, a lokacin da Azariya ke sarautar Yahuza, Yerobowam ɗan Yehowash kuwa ke sarautar Isra'ila. 2 Amos ya ce, “Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona, Muryarsa za ta yi tsawa daga Urushalima. Da jin wannan, sai wuraren kiwo za su bushe, Ƙwanƙolin Dutsen Karmel, da ke kore zai yi yaushi.”

Suriya

3 Ubangiji ya ce, “Mutanen Dimashƙu sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun zalunci mutanen Gileyad da zalunci mai tsanani. 4 Don haka zan aukar da wuta a kan fādar Sarkin Suriya. Za ta ƙone kagarar Ben-hadad, sarki. 5 Zan ragargaje ƙyamaren ƙofofin birnin Dimashƙu, In kawar da masu sarautar Bet-eden da na kwarin Awen. Za a kwashe mutanen Suriya ganima zuwa ƙasar Kir.”

Filistiya

6 Ubangiji ya ce, “Mutanen Gaza sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun kwashe al'umma duka, sun sayar wa mutanen Edom. 7 Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Gaza ta ƙone kagarar birnin. 8 Zan kawar da masu sarautar biranen Ashdod da Ashkelon, Zan karɓe sandan mulkin Ekron. Sauran Filistiyawa da suka ragu kuma, Za su mutu duka.”

Taya

9 Ubangiji ya ce, “Mutanen Taya sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun kwashe mutanen sun kai ƙasar Edom. Suka karya yarjejeniyar abuta wadda suka yi. 10 Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Taya, Ta ƙone kagarar birnin.”

Edom

11 Ubangiji ya ce, “Mutanen Edom sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun farauci 'yan'uwansu, Isra'ilawa, Suka ƙi su nuna musu jinƙai. Ba su yarda su huce daga fushinsu ba. 12 Saboda haka zan aukar da wuta a kan Teman, Ta ƙone kagarar Bozara.”

Ammon

13 Ubangiji ya ce, “Mutanen Ammon sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don haɗamarsu ta ƙasa, Suka tsaga mata masu ciki a Gileyad. 14 Saboda haka zan aukar da wuta a kan garun Rabba, Ta ƙone kagarar birnin. Za a yi kururuwa a ranar yaƙi, Faɗan kuwa zai yi rugugi kamar hadiri. 15 Sarkinsu da manyan mutanensu za a kai su wata ƙasa dabam.”

Amos 2

Mowab

1 Ubangiji ya ce, “Mutanen Mowab sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun ƙone ƙasusuwan Sarkin Edom Don su yi toka da su. 2 Zan aukar da wuta a ƙasar Mowab, Ta ƙone kagarar Keriyot. Jama'ar Mowab za su mutu a hargitsin yaƙi, Sa'ad da sojoji ke sowa, ana busa ƙahoni. 3 Zan kashe Sarkin Mowab da shugabannin ƙasar.”

Yahuza

4 Ubangiji ya ce, “Mutanen Yahuza sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun raina koyarwata sun ƙi bin umarnaina. Allolinsu na ƙarya waɗanda kakanninsu suka bauta wa, Sun sa su su ratse daga hanya. 5 Saboda haka zan aukar da wuta a kan Yahuza Ta ƙone kagarar Urushalima.”

Allah ya Hukunta Isra'ila

6 Ubangiji ya ce, “Mutanen Isra'ila sun ci gaba da yin zunubi. Hakika, zan hukunta su, Don sun sayar da salihai waɗanda suka kāsa biyan bashinsu. Sun kuma sayar da matalauta Waɗanda bashinsu bai kai ko kuɗin bi-shanu ba. 7 Sun tattake marasa ƙarfi da kāsassu, Suna tunkuɗe matalauta su wuce. Tsofaffi da samari sukan tafi wurin karuwan Haikali. Ta haka suke ɓata sunana mai tsarki. 8 A duk wuraren sujadarsu sukan kwanta A bisa tufafin da suka karɓe jingina. A cikin Haikalin Allahnsu, sukan sha ruwan inabi Da suka karɓo daga wurin waɗanda suke bi bashi. 9 “Amma ga shi, saboda ku na hallakar da Amoriyawa, Dogayen mutanen nan masu kama da itatuwan al'ul, Ƙarfafa kuma kamar itatuwan oak, Na hallaka su ƙaƙaf. 10 Na fito da ku, wato jama'ata daga Masar. Na bi da ku cikin jeji shekara arba'in, Na kuwa ba ku ƙasar Amoriyawa ta zama taku. 11 Na zaɓi waɗansu daga cikin 'ya'yanku su zama annabawa, Waɗansu kuma daga cikin samarinku su zama keɓaɓɓu. Ko ba haka ba ne, ya ku Isra'ilawa? Ni, Ubangiji, na yi magana. 12 Amma kun sa keɓaɓɓu shan ruwan inabi, Kuka kuma umarci annabawa kada su isar da saƙona. 13 Zan danƙare ku a inda kuke Kamar yadda ake danƙare amalanke da kayan tsaba. 14 Ko masu saurin gudu ma ba za su tsere ba, Ƙarfafa za su zama kumamai, Sojoji kuma ba za su iya ceton kansu ba. 15 'Yan baka ba za su iya ɗagewa ba. Masu saurin gudu ba za su tsira ba. Mahayan dawakai kuma ba za su tsere da rayukansu ba. 16 Ko sojojin da suka fi jaruntaka duka ma, Za su gudu tsirara a ran nan.” Ubangiji ne ya faɗa.

Amos 3

Aikin Annabi

1 Jama'ar Isra'ila, ku kasa kunne ga wannan saƙo da Ubangiji ya aiko muku, ya ce, “Na fitar da iyalanku duka daga Masar. 2 Daga cikin dukan al'umman da nake ƙauna a duniya, Ku kaɗai ne na sani, Nake kuma kulawa da ku, Don haka zan hukunta ku saboda zunubanku.” 3 Zai yiwu a ce mutum biyu za su yi tafiya tare, Amma su rasa shirya magana? 4 Zai yiwu zaki ya yi ruri a jeji Ba tare da ya kama nama ba? Zai yiwu sagarin zaki ya yi gurnani a kogonsa In bai kama wani abu ba? 5 Zai yiwu tsuntsu ya fāɗi ƙasa In ba a kafa masa tarko ba? Zai yiwu tarko ya zargu In bai kama wani abu ne ba? 6 Zai yiwu mutane su rasa firgita, Idan aka busa ƙahon yaƙi a birni? Zai yiwu wata babbar masifa ta auko wa birni Ba da yardar Ubangiji ba? 7 Hakika Ubangiji ba yakan aikata kome ba, Sai da sanin bayinsa annabawa. 8 Zaki ya yi ruri! Wa ba zai ji tsoro ba? Sa'ad da Ubangiji ya yi magana! Wa zai ƙi yin shelar maganarsa?

Faɗuwar Samariya

9 Ka yi shela ga mazaunan fādar Ashdod da Masar, ka ce, “Duk ku taru a Samariya ku ga irin babban shashancin da ake yi a can, ku ga irin laifofin da ake aikatawa a birnin.” 10 Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane suka cika gidajensu masu daraja da abubuwan da suka samo ta hanyar zamba, da ta kama-karya. Ta yadda za su yi su yi aminci ma, ba su sani ba. 11 “Saboda haka abokan gaba za su kewaye ƙasarsu, Su hallakar da kagaransu, Su washe gidajen nan nasu masu daraja.” 12 Ubangiji ya ce, “Kamar yadda makiyayi yakan ceci ƙafafu biyu Ko kunne ɗaya na tunkiya daga bakin zaki, Hakanan kuma kima daga cikin mutanen Samariya Waɗanda ke zaman jin daɗi za su tsira. 13 Ku saurara yanzu, Ku yi wa zuriyar Yakubu kashedi,” In ji Ubangiji, Maɗaukaki. 14 “Ran da na hukunta mutanen Isra'ila saboda zunubansu, Zan hallakar da bagadan Betel. Za a kakkarya zankayen bagaden, Su fāɗi ƙasa. 15 Zan murmushe gidajensu na rani da na damuna. Zan hallakar da gidajen da aka ƙawata da hauren giwa, Kowane babban gida kuwa za a rushe shi.”

Amos 4

1 Ku kasa kunne ga wannan, ya ku matan Samariya, Ku da kuka yi ƙiba kamar turkakkun shanu, Ku da kuke wulakanta kasassu, Kuna yi wa matalauta danniya, Kukan umarci mazajenku, Ku ce, “Kawo mini abin sha!” 2 Da ya ke Ubangiji Mai Tsarki ne Ya riga ya yi alkawari, Ya ce, “Hakika kwanaki za su zo Da za a jawo ku da ƙugiyoyi, Kowannenku zai zama kamar kifi a ƙugiya. 3 Za a kwashe ku, a fitar da ku Ta inda garu ya tsage na mafi kusa duka, a jefar.”

Isra'ila Sun Kāsa Koyo

4 Ubangiji ya ce, “Jama'ar Isra'ila, Ku tafi Betel, tsattsarkan wuri, Ku yi ta zunubi! Ku tafi Gilgal ku ƙara zunubi! Ku yi ta kawo dabbobi sadaka kowace safiya. A kowace rana ta uku Ku yi ta ba da zaka. 5 Ku miƙa abincinku hadaya ta godiya. Ku yi ta yin fariya da hadayarku ta yardar rai! Gama irin abin da kuke jin daɗin yi ke nan.” 6 Ubangiji ya ce, “Ai, ni ne, na sa a yi yunwa a biranenku. Shi ya sa ba ku da abinci. Duk da haka ba ku juyo gare ni ba. 7 Na hana wa shuke-shukenku ruwa A lokacin da suka fi bukata. Na sa a yi ruwa a wani birni, A wani birni kuwa na hana, Wata gonar ta sami ruwan sama, Amma wadda ba ta samu ba ta bushe. 8 Ƙishirwa ta sa jama'a su tafke har birane biyu ko uku Suka tafi neman ruwa a birnin da suke maƙwabtaka da shi, A nan ma ba su sami isasshen ruwan sha ba, Duk da haka ba ku komo wurina ba. 9 “Na sa darɓa, da domana Su lalatar da amfanin gonakinku. Fāra kuma ta cinye lambunanku Da gonakin inabinku, da itatuwan ɓaurenku, Da na zaitun ɗinku. Duk da haka ba ku komo wurina ba. 10 “Na aukar muku da annoba irin wadda na aukar wa Masar. Na karkashe samarinku a wurin yaƙi, Na kwashe dawakanku. Na cika hancinku da ɗoyin sansaninku. Duk da haka ba ku komo wurina ba. 11 “Na hallakar da waɗansunku Kamar yadda na hallakar da Saduma da Gwamrata. Kamar sanda kuke, wanda aka fizge daga wuta. Duk da haka ba ku komo wurina ba. 12 Saboda haka, jama'ar Isra'ila, Ga abin da zan yi muku, Zan kuwa yi shi duk, Sai ku yi shirin zuwa gaban Ubangiji.” 13 Allah ne ya yi duwatsu Ya kuma halicci iska. Ya sanar da nufinsa ga mutum, Ya juya rana ta zama dare. Yana sarautar duniya duka. Sunansa kuwa Ubangiji Maɗaukaki!

Amos 5

Kira Zuwa Tuba

1 Ku kasa kunne, ku jama'ar Isra'ila, ga waƙar makoki da zan yi a kanku. 2 Isra'ila ta fāɗi, Ba kuwa za ta ƙara tashi ba. Tana fa kwance a ƙasa, Ba wanda zai tashe ta. 3 Ubangiji ya ce, “Wani birnin Isra'ila ya aika da soja dubu, Ɗari ne kaɗai suka komo, Wani birni kuma ya aika da soja ɗari ne, Amma goma kaɗai suka komo.” 4 Ubangiji ya ce wa jama'ar Isra'ila, “Ku zo gare ni, za ku tsira. 5 Kada ku tafi ku yi sujada a Biyer-sheba. Kada ku yi ƙoƙarin nemana a Betel, Gama Betel lalacewa za ta yi. Kada ku tafi Gilgal, Gama an ƙaddara wa jama'arta su yi ƙaura.” 6 Ku tafi wurin Ubangiji ku tsira. Idan kuwa kun ƙi, Shi zai babbaka jama'ar Yusufu Kamar yadda a kan babbaka da wuta. Wuta za ta ƙone jama'ar Betel, Ba kuwa mai kashe wutar. 7 Abin tausayi ne ku da kuke ɓata shari'a, Kuna hana wa mutane hakkinsu. 8 Ubangiji ne ya yi taurarin Kaza da 'ya'yanta Da mai farauta da kare. Ya mai da duhu haske, Rana kuwa dare. Shi ya kirawo ruwan teku ya bayyana, Ya shimfiɗa shi a bisa ƙasa. Sunansa Ubangiji ne. 9 Ya kawo halaka a kan ƙarfafa, Da a kan birane masu garu. 10 Kun ƙi wanda ya tsaya a kan adalci, Da mai faɗar ainihin gaskiya a gaban shari'a. 11 Kun matsa wa talakawa lamba, Kun ƙwace musu abincinsu. Saboda haka kyawawan gidajen nan da kun gina da dutse, Ba za ku zauna a cikinsu ba, Ba kuwa za ku sha ruwan inabin nan Daga kyawawan gonakin inabinku ba. 12 Na san irin zunuban da kuke yi, Da mugayen laifofin da kuka aikata. Kuna wulakanta mutanen kirki, Kuna cin hanci, Kuna hana a yi wa talakawa shari'ar adalci a majalisa. 13 Ashe, ba abin mamaki ba ne, Da masu hankali suka kame bakinsu A waɗannan kwanaki na mugunta. 14 Ku yi ƙoƙari, ku yi nagarta, ba mugunta ba, Domin ku tsira. Sa'an nan ne Ubangiji Allah Maɗaukaki Zai kasance tare da ku sosai, Kamar yadda kuka ɗauka! 15 Ku ƙi mugunta, ku ƙaunaci nagarta, Ku yi adalci cikin majalisar alƙalanku! Watakila Ubangiji Allah Mai Runduna Zai yi wa sauran da suka ragu na wannan al'umma alheri. 16 Haka Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Za a yi kuka, a yi kururuwa a titunan birninku saboda azaba. Daga ƙauyuka za a kirawo mutane Su zo su yi makokin. Waɗanda suka mutu, tare da masu makoki da aka ijarar da su. 17 Za a yi kuka ko'ina cikin dukan gonakin inabinku Gama zan zo in yi muku horo.” 18 Taku ta ƙare, ku da kuke marmarin zuwan ranan nan ta Ubangiji! Wane amfani wannan rana za ta yi muku? Rana ta baƙin ciki ce, Ba ta murna ba. 19 Zai zama kamar wanda ya tsere wa zaki Ya fāɗa a bakin beyar! Ko kuwa kamar wanda ya komo gida, Ya dāfa bango, maciji ya sare shi. 20 Ranar Ubangiji za ta kawo baƙin ciki, Ba murna ba. Rana ce ta damuwa ba ta fara'a ba. 21 Ubangiji ya ce, “Na ƙi bukukuwanku na addini. Ina ƙyamarsu! 22 Sa'ad da kuka kawo mini hadayun ƙonawa Da hadayunku na tsaba, ba zan karɓa ba. Ba kuma zan karɓi turkakkun dabbobinku Waɗanda kuka miƙa mini hadayun godiya ba. 23 Ku yi shiru da yawan hargowar waƙoƙinku. Ba na so in saurari kaɗe-kaɗenku da bushe-bushenku. 24 Sai ku sa adalci da nagarta su gudano a yalwace Kamar kogin da ba ya ƙafewa. 25 “Ya ku, jama'ar Isra'ila, ai, a waɗannan shekaru arba'in da kuka yi cikin jeji kuka kawo mini sadaka da hadayu, 26 duk da haka, kuka ɗauki siffofin gumakanku na taurari, wato Sakkut da Kaiwan, waɗanda kuka yi wa kanku. 27 Ni kuwa zan sa ku yi ƙaura zuwa wata ƙasa gaba da Dimashƙu.” Ubangiji, Allah Mai Runduna, shi ne ya faɗa.

Amos 6

Halakar Isra'ila

1 Taku ta ƙare, ku da kuke zaman sakewa a Sihiyona, Da ku da kuke tsammani kuna zaman lafiya a Samariya, Ku da kuke manyan mutane Na wannan babbar al'umma ta Isra'ila, Waɗanda jama'a ke zuwa a gare su neman taimako! 2 Ku je ku duba a birnin Kalne. Sa'an nan ku zarce zuwa babban birnin Hamat, Har zuwa birnin Gat ta Filistiyawa. Sun fi mulkin Yahuza da Isra'ila ne? Ko kuwa, yankin ƙasarsu ya fi naku? 3 Kuna ƙoƙari ku kauce wa wannan rana ta masifa, Amma ga shi, goyon bayan hargitsi kuke ta yi, Ta wurin ayyukanku. 4 Taku ta ƙare, ku da kuke kwance kan gadajen hauren giwa, Kuna jin daɗin miƙe jiki a dogayen kujerunku, Ku ci naman maraƙi da na rago. 5 Kukan so ku tsara waƙoƙi kamar yadda Dawuda ya yi, Ku raira su da garayu. 6 Da manyan kwanoni kuke shan ruwan inabi, Ku shafe jiki da mai mafi kyau, Amma ba ku yin makoki saboda lalacewar Isra'ila. 7 Don haka, ku ne na fari da za a sa su yi ƙaura Bukukuwanku da shagulgulanku za su ƙare. 8 Ubangiji kansa ne ya rantse. Ubangiji Allah Mai Runduna ya ce, “Ba na son girmankai na jama'ar Isra'ila. Ba na son fādodinsu. Zan ba da birnin da dukan abin da ke cikinsa ga abokan gābansu.” 9 Ko da a ce mutum goma ne suka ragu a gida guda, duk za su mutu. 10 Sa'ad da dangin mamacin ya shiga don ya fitar da gawar, ya ƙone, sai ya yi kira ga kowanene da ke ɓoye a gidan, ya ce, “Ko akwai wani kuma a nan?” Sai a amsa, “A'a.” Zai ce, “Kul! Kada a ambaci sunan Ubangiji.” 11 Sa'ad da Ubangiji ya ba da umarni, babban gida da ƙarami rushewa za su yi. 12 Dawakai sukan yi sukuwa a duwatsu? Ana huɗan teku da garmar shanu? Duk da haka kuka mai da adalci dafi, Kuka mai da nagarta, mugunta. 13 Kuna fariyar cin garin Lodebar, wato wofi, da yaƙi. Kun ce, “Ƙarfinmu ya isa har mu ci Karnayim, wato ƙaho biyu, da yaƙi.” 14 Ubangiji Allah Mai Runduna kansa, ya amsa ya ce, “Zan aiko da wata al'umma ta yi gāba da ku, ya Isra'ilawa. Za ta matse muku Tun daga mashigin Hamat wajen arewa, Har zuwa Kwarin Urdun a kudu.”

Amos 7

Wahayin Fāra

1 A wahayin da Ubangiji ya nuna mini, sai na ga ya yi cincirindon fara nan da nan bayan da aka ƙarasa yankan rabon ingiricin da ke na sarki, ciyawar kuma ta soma tohuwa. 2 A wahayin, na ga fara ta cinye kowane ɗanyen ganye a ƙasar. Sai na ce, “Ka gafarta wa jama'arka, ya Ubangiji! Ƙaƙa za su tsira? Ga su 'yan kima ne, marasa ƙarfi.” 3 Ubangiji kuwa ya dakatar da nufinsa, Ya ce, “Abin da ka gani, ba zai faru ba.”

Wahayin Wuta

4 A wahayin da Ubangiji ya nuna mini, na gan shi yana shirin hukunta jama'arsa da wuta. Wutar ta ƙone babbar teku, har ma ta fara ƙone ƙasar. 5 Sa'an nan na ce, “Ya Ubangiji, in nufinka ne ka bari! Ƙaƙa jama'arka za su tsira? Ga su 'yan kima ne, marasa ƙarfi.” 6 Ubangiji kuwa ya dakatar da nufinsa, ya ce, “Wannan me ba zai faru ba.”

Wahayin Ma'auni

7 Ubangiji kuma ya nuna mini wani wahayi. A wahayin sai na gan shi, yana tsaye kusa da bangon da ake ginawa. Yana riƙe da igiyar awon gini. 8 Ya tambaye ni, ya ce, “Amos, me ka gani?” Sai na ce, “Igiyar awon gini na gani.” Ya kuma ce, “Duba, da wannan zan nuna yadda jama'ata sun zama kamar bangon da ya karkace. Ba zan sāke nufina a kan yi musu hukunci ba. 9 Zan hallakar da wuraren sujada na zuriyar Ishaku. Za a hallakar da tsarkakan wurare na Isra'ila. Zan fāɗa wa zuriyar sarki Yerobowam da yaƙi.”

Amos da Amaziya

10 Amaziya, firist, na Betel kuwa, ya tafi ya faɗa wa Yerobowam Sarkin Isra'ila, ya ce, “Amos yana shirya maka maƙarƙashiya a cikin jama'ar Isra'ila. Maganganunsa za su hallakar da ƙasar. 11 Abin da ya faɗa ke nan, ‘Za a kashe Yerobowam a bakin dāga, a sa jama'ar Isra'ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ” 12 Amaziya kuwa ya ce wa Amos, “Kai maƙaryaci ne na ainihi! Koma ƙasar Yahuza ka nemi abin zaman gari, ka yi ta annabcinka a can. 13 Amma a nan Betel kada ka ƙara yin annabci. Nan wurin yin sujada na sarki ne, haikali ne na al'umma.” 14 Sai Amos ya amsa ya ce, “Ni ba annabi ba ne. Wannan ba aikina ba ne. Ni makiyayi ne, mai kuma lura da itatuwan ɓaure. 15 Amma Ubangiji ya raba ni da aikina na kiwo, ya umarce ni in tafi in yi magana da jama'arsa, wato Isra'ila. 16 Domin haka, sai ka kasa kunne ga abin da Ubangiji ya ce. Saboda ka ce mini in daina yin annabci gāba da jama'ar Isra'ila, kada kuwa in yi wa zuriyar Ishaku ɓaɓatu, 17 to, ga abin da Ubangiji ya ce maka, ya kai Amaziya, ‘Matarka za ta zama karuwa a birni, za a karkashe 'ya'yanka a cikin yaƙi. Za a rarraba wa waɗansu ƙasarka, kai kanka kuwa za ka mutu a ƙasar arna. Za a sa jama'ar Isra'ila su yi ƙaura zuwa wata ƙasa.’ ”

Amos 8

Wahayi na Huɗu, Kwandon Ɓaure na Ci

1 Ubangiji ya nuna mini wahayi, sai na ga kwandon ɓaure na ci. 2 Sai Ubangiji ya ce, “Amos, me ka gani?” Na ce, “Kwandon ɓaure na ci.” Ubangiji kuma ya ce mini, “Ƙarshen jama'ata Isra'ila ya zo. Ba zan sāke nufina a kan yi musu hukunci ba. 3 Waƙoƙin da akan raira a fāda, za su zama na makoki a wannan rana. Za a iske gawawwaki ko'ina. Ba za a ji motsin kome ba.”

An kai Ƙarshen Isra'ila

4 Ku ji wannan, ku da kuke tattake masu bukata, kuna ƙoƙari ku hallakar da matalautan ƙasar. 5 Kuna ce wa kanku, “Mun ƙosa keɓaɓɓun kwanakin nan su wuce, Mu sami damar yin kasuwancinmu. Yaushe Asabar ɗin za ta ƙare ne? Ko mā sami damar kai hatsinmu kasuwa, Mu sayar musu da tsada, Mu yi awo da ma'aunin zalunci, Mu daidaita ma'auni yadda za mu cuci mai saya? 6 Za mu sayi matalauci da azurfa ya zama bawa, Mai fatara kuma da takalma bi-shanu. Za mu sayar da ruɓaɓɓen hatsi, Mu ci riba mai yawa.” 7 Ubangiji Allahn Isra'ila ya riga ya rantse, Ya ce, “Ba zan manta da mugayen ayyukanku ba. 8 Shi ya sa ƙasar za ta girgiza, Duk wanda ke cikinta zai yi baƙin ciki. Ƙasa duka za ta girgiza. Za ta hau ta sauka kamar Kogin Nilu. 9 A wannan lokaci rana za ta fāɗi da tsakar rana, Duniya ta duhunta da rana kata. Ni, Ubangiji ne na faɗa. 10 Zan mai da bukukuwanku makoki, In sa waƙoƙinku na murna su zama na makoki. Zan sa muku tufafin makoki, In sa ku aske kanku. Za ku yi makoki kamar iyayen da suka rasa tilon ɗansu. Ranan nan mai ɗaci ce har ƙarshe. 11 “Lokaci yana zuwa da zan aiko da yunwa a ƙasar. Mutane za su ji yunwa, Ba ta abinci ba, Za su ji ƙishi, Ba na ruwa ba. Za su ji yunwar rashin samun saƙo daga wurin Ubangiji. Ni Ubangiji ne, na faɗa. 12 Mutane za su raunana, su riƙa kai da kawowa, Daga gabas zuwa yamma, daga kuma kudu zuwa arewa. Za su dudduba ko'ina suna neman saƙo daga Ubangiji, Ba kuwa za su samu ba. 13 A ranan nan kyawawan 'yan mata da samari Za su faɗi saboda ƙishirwa. 14 Waɗanda suka yi rantsuwa da gumakan Samariya, Waɗanda suka ce, ‘Na rantse da gunkin Dan, Da ran gunkin Biyer-sheba,’ Irin waɗannan mutane za su fāɗi, Ba za su ƙara tashi ba.”

Amos 9

Ba a Kauce wa Hukuncin Allah

1 Na ga Ubangiji na tsaye a wajen bagade. Ya yi umarni, ya ce, “Bugi ginshiƙan Haikali don shirayi duka ya girgiza. Farfasa su, su fāɗi a kan mutane! Sauran mutane kuwa, Zan kashe su a wurin yaƙi. Ba wanda zai tsere, ko ɗaya. 2 Ko da za su nutsa zuwa lahira, Zan kama su. Ko sun hau Sama, Zan turo su. 3 Ko da za su hau su ɓuya a bisa ƙwanƙolin Dutsen Karmel, Zan neme su in cafko su. Ko da za su ɓuya mini a ƙarƙashin teku, Sai in sa dodon ruwa ya yayyage su. 4 Idan kuwa abokan gābansu ne suka kama su, In umarce su su hallaka su da takobi, Tun da na yi ƙudurin ƙare su.” 5 Ubangiji Allah Mai Runduna Ya taɓi duniya, ta girgiza. Duk waɗanda ke zaune cikinta Suna baƙin ciki. Duniya duka takan hau Ta kuma gangara kamar ruwan Kogin Nilu. 6 Ubangiji ya gina al'arshinsa a sama, Ya shimfiɗa samaniya a bisa duniya. Ya sa ruwan teku ya zo, Ya kwarara shi a bisa duniya. Sunansa Ubangiji ne! 7 Ubangiji ya ce, “Jama'ar Isra'ila, Ina yi da ku daidai yadda nake yi da Habashawa. Na fito da Filistiyawa daga Kaftor, Suriyawa kuwa daga Kir, Daidai yadda na fito da ku daga Masar. 8 Ina dai kallon mulkin nan mai zunubi. Zan hallaka su daga duniya, Amma ba zan hallaka dukan jama'ar Yakubu ba. 9 “Zan umarta a rairayi jama'ar Isra'ila Da matankaɗi kamar hatsi. Zan rairaye su daga cikin sauran al'umma, Duk da haka ko ƙwaya ɗaya ba za ta salwanta ba. 10 Masu zunubi daga cikin jama'ata za su mutu a yaƙi, Wato dukansu da ke cewa, ‘Allah ba zai bar wata masifa ta kusace mu ba!’ ”

Ceton da Za a Yi wa Isra'ila Nan Gaba

11 “Wata rana zan sāke tayar da birnin Dawuda Tankar yadda akan ta da gidan da ya rushe. Zan gyara garunsa, in sāke mai da shi. Zan sāke gina shi in mai da shi kamar yadda yake tun dā. 12 Ta haka jama'ar Isra'ila za ta ci nasara bisa sauran ƙasar Edom wadda ta ragu, Da bisa dukan al'umman da a dā su nawa ne,” In ji Ubangiji, wanda zai sa al'amarin ya auku. 13 Ubangiji ya ce, “Kwanaki suna zuwa, Sa'ad da girbi zai bi bayan huda nan da nan, Matsewar ruwan inabi kuma Za ta bi bayan shuka nan da nan. Duwatsu za su zubo da ruwan inabi mai zaƙi, Tuddai kuma su gudano da shi. 14 Zan komo da mutanena ƙasarsu, Za su giggina biranensu da suka rurrushe, Su zauna a cikinsu. Za su shuka gonakin inabi, su sha ruwan inabin. Za su yi lambuna, su ci amfaninsu. 15 Zan dasa su a ƙasar da na ba su, Ba kuwa za a ƙara tumɓuke su ba.” Ubangiji Allahnku ne ya faɗa.

Obadiya 1

Ƙasƙancin Edom

1 Annabcin Obadiya ke nan. Wannan shi ne abin da Ubangiji Allah ya ce a kan al'ummar Edom. Ubangiji ya aiki manzonsa wurin sauran al'umma, Mun kuwa ji saƙonsa cewa, “Ku zo! Mu tafi mu yi yaƙi da Edom!” 2 Ubangiji ya ce wa al'ummar Edom, “Zan maishe ki ƙanƙanuwa a cikin sauran al'umma, Za a raina ki ƙwarai. 3 Girmankanki ya yaudare ki, Kina zaune a kagara, a kan dutse, Wurin zamanki yana can ƙwanƙolin duwatsu. Don haka a zuciya kike cewa, ‘Wa zai saukar da ni ƙasa?’ 4 Ko da ya ke kina shawagi can sama kamar gaggafa, Gidanki kuma yana can cikin taurari, Daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji 5 “Idan ɓarayi sun shiga gidanki, Idan kuma 'yan fashi sun shiga gidanki da dare, Yaya za su washe ki? Za su sace abin da ya ishe su ne kaɗai, Idan kuma ɓarayin 'ya'yan inabi sun shiga gonar inabinki, Za su bar miki kala kurum. 6 Isuwa, wato Edom, ga taskarka, An washe ta ƙaƙaf! 7 Waɗanda kake amana da su, Za su kore ka daga ƙasarka. Mutanen da suke amana da kai, Za su yaudare ka, Su ci ka da yaƙi. Abokan nan naka da kake ci tare da su za su kafa maka tarko, Sa'an nan su ce, ‘Ina dukan wayon nan nasa?’ ” 8 Ni Ubangiji na ce, “A ranar da zan hukunta Edom, Zan hallaka masu hikimarka, Zan shafe hikima daga dutsen Isuwa. 9 Jarumawanka za su firgita, ya Teman, Za a kashe kowane mutum daga dutsen Isuwa. 10 “Saboda kama-karyar da ka yi wa Yakubu ɗan'uwanka, Za a sa ka ka sha kunya, Za a hallaka ka har abada. 11 A ranan nan ka tsaya kawai, A ranar da abokan gāba suka fasa ƙofofinsa. Suka kwashe dukiyarsa, Suka jefa kuri'a a kan Urushalima. Ka zama kamar ɗaya daga cikinsu. 12 Ba daidai ba ne ka yi murna Saboda wahalar da ta sami ɗan'uwanka. Ba daidai ba ne ka yi farin ciki Saboda halakar mutanen Yahuza. Ba daidai ba ne ka yi musu dariya A ranar wahalarsu. 13 Ba daidai ba ne ka shiga ƙofar jama'ata A ranar da suke shan masifa. Ba daidai ba ne ka yi murna A kan bala'in ɗan'uwanka. Ba daidai ba ne ka washe dukiyarsa A ranar masifarsa. 14 Ba daidai ba ne ka tsaya a mararraba, Don ka kashe waɗanda ke ƙoƙarin tserewa. Ba daidai ba ne ka ba da waɗanda suka tsere a hannun maƙiyansu A ranar wahala.”

Hukuncin Al'ummai

15 “Ranar da ni Ubangiji zan shara'anta al'ummai duka ta zo kusa, Ke, Edom, abin da kika yi, Shi ne za a yi miki. Ayyukanki za su koma a kanki. 16 Kamar yadda kuka sha hukunci a kan tsattsarkan dutsena, Haka dukan sauran al'umma za su yi ta sha. Za su sha, su yi tangaɗi, Su zama kamar ba su taɓa kasancewa ba.”

Cin Nasarar Isra'ila

17 “Amma za a sami waɗanda za su tsira daga Dutsen Sihiyona, Dutsen zai zama wuri ne mai tsarki. Jama'ar Yakubu za ta mallaki mallakarta. 18 Jama'ar Yakubu za ta zama kamar wuta, Jama'ar Yusufu kuwa kamar harshen wuta, Jama'ar Isuwa za ta zama kamar tattaka. Za su ƙone ta, su ci ta, ba wanda zai tsira. Ni Ubangiji na faɗa.” 19 Isra'ilawan da ke Negeb za su mallaki dutsen Isuwa, Waɗanda ke a filaye na Yahuza za su mallaki ƙasar Filistiya. Isra'ilawa za su mallaki yankin ƙasar Ifraimu da Samariya, Jama'ar Biliyaminu za su mallaki Gileyad. 20 Rundunar masu zaman talala na Isra'ilawa Za su mallaki Kan'aniyawa har zuwa Zarefat. Masu zaman talala na Urushalima da ke a Sefarad Za su mallaki biranen Negeb. 21 Isra'ilawa za su hau Dutsen Sihiyona, su cece shi, Za su mallaki dutsen Isuwa, Ubangiji ne Sarki.

Yunusa 1

Yunusa ya Yi Gudun Ubangiji

1 Ana nan sai Ubangiji ya yi magana da Yunusa, ɗan Amittai, ya ce, 2 “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka faɗakar da su, gama na ga irin muguntarsu.” 3 Amma maimakon Yunusa ya tafi, sai ya gudu daga wurin Ubangiji zuwa Tarshish. Ya tafi Yafa, nan ya sami jirgin ruwa yana gab da tashi zuwa Tarshish, ya kuwa biya kuɗinsa, ya shiga tare da masu jirgin zuwa can don ya tsere wa Ubangiji. 4 Amma Ubangiji ya aika da iska mai ƙarfi a tekun, hadirin ya tsananta ƙwarai har jirgin yana bakin farfashewa. 5 Dukan matuƙan jirgin suka firgita, sai kowannensu ya shiga roƙon allahnsa. Suka yi ta jefar da kayan da ke cikin jirgin a ruwa don su sami sauƙi. Yunusa kuwa yana can cikin jirgi, a kwance, yana ta sharar barci. 6 Can shugaban jirgin ya iske shi, ya ce masa, “Me ya sa kake barci? Tashi ka roƙi allahnka, watakila allahnka zai ji tausayinmu, ya cece mu.” 7 Matuƙan jirgin kuwa suka ce wa junansu, “To, bari mu jefa kuri'a mu gani ko alhakin wanene ya jawo mana wannan bala'i da muke ciki.” Sai suka jefa kuri'a, kuri'ar kuwa ta fāɗa a kan Yunusa. 8 Suka ce masa, “Ka faɗa mana, laifin wanene ya jawo mana wannan masifa? Menene aikinka? Daga ina ka fito? Daga wace al'umma kake?” 9 Sai Yunusa ya ce, “Ni Ba'ibrane ne, ina bin Ubangiji Allah na Sama, wanda ya yi teku da ƙasa.” 10 Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” Sun sani ya gudu ne daga wurin Ubangiji, gama ya riga ya faɗa musu. 11 Hadirin kuwa sai ƙaruwa yake ta yi. Matuƙan jirgin kuwa suka ce masa, “Me za mu yi maka domin tekun ya lafa?” 12 Yunusa ya ce, “Sai ku ɗauke ni ku jefa ni cikin tekun, sa'an nan hadirin zai lafa. Gama na sani saboda ni ne wannan hadiri mai banrazana ya auko muku.” 13 Matuƙan jirgin kuwa suka yi ta tuƙi da iyakar ƙarfinsu don su kai gaɓa, amma suka kāsa domin hadirin yana ta ƙaruwa. 14 Suka yi kuka ga Ubangiji, suka ce, “Ya Ubangiji, muna roƙonka kada ka bar mu mu halaka saboda ran mutumin nan, kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka yi abin da ya gamshe ka.” 15 Sai suka ɗauki Yunusa suka jefa shi cikin teku, nan take teku ta lafa. 16 Sai matuƙan jirgin suka ji tsoron Ubangiji ƙwarai, har suka ba da sadaka, suka kuma yi wa'adi ga Ubangiji. 17 Ubangiji kuwa ya umarci wani babban kifi ya haɗiye Yunusa. Yunusa kuwa ya yi yini uku da dare uku a cikin cikin kifin.

Yunusa 2

Addu'ar Yunusa ta Godiya

1 Sai Yunusa ya yi addu'a ga Ubangiji Allah a cikin cikin kifin, 2 ya ce, “A cikin wahalata na yi kira gare ka, ya Ubangiji, Ka a kuwa amsa mini. Daga can cikin lahira na yi kira, Ka kuwa ji muryata. 3 Ka jefa ni cikin zurfi, Can cikin tsakiyar teku, Inda igiyoyin ruwa suka kewaye ni, Kumfa da raƙuman ruwanka suka bi ta kaina. 4 Na ce, an kore ni daga wurinka, Duk da haka zan sāke ganin Haikalinka mai tsarki. 5 Ruwa ya sha kaina, Tekun ta rufe ni ɗungum. Tsire-tsiren teku suka naɗe kaina. 6 Na tafi can ƙasa ƙarƙashin tussan duwatsu. Ƙasar da ƙofarta ke rufe har abada, Amma ka fitar da ni daga cikin ramin, ya Ubangiji Allahna. 7 Sa'ad da na ji raina yana rabuwa da ni, Sai na tuna da kai, ya Ubangiji. Addu'ata kuwa ta kai gare ka a Haikalinka tsattsarka. 8 Su waɗanda ke yin sujada ga gumaka marasa amfani Sun daina yi maka biyayya. 9 Amma ni zan raira yabbai gare ka, Zan miƙa maka sadaka, Zan cika wa'adin da na yi. Ceto daga wurin Ubangiji yake.” 10 Ubangiji kuwa ya umarci kifin, kifin kuwa ya amayar da Yunusa a gaɓar teku.

Yunusa 3

Tuban Ninebawa

1 Ubangiji kuma ya sāke ce wa Yunusa, 2 “Ka tashi ka tafi Nineba, babban birnin nan, ka yi musu shelar saƙon da zan faɗa maka.” 3 Sai Yunusa ya tashi ya tafi Nineba kamar yadda Ubangiji ya faɗa masa. Nineba kuwa babban birni ne kwarai da gaske. Zai kai mutum tafiyar kwana uku kafin ya ƙure birnin. 4 Sai Yunusa ya kama tafiya yana ratsa birnin, da ya yi tafiyar yini guda, sai ya yi shela ya ce, “Nan da kwana arba'in za a hallaka Nineba.” 5 Sai mutanen Nineba suka gaskata Allah, suka tsai da shawara, cewa kowa da kowa ya yi azumi. Dukan mutane kuwa babba da yaro, suka sa tufafin makoki. 6 Sa'ad da Sarkin Nineba ya ji labarin, sai ya sauka daga kursiyinsa, ya tuɓe rigarsa, ya sa rigar makoki, ya zauna cikin toka. 7 Sai ya aika wa mutanen Nineba da sanarwa cewa, “Wannan doka ce daga sarki da majalisarsa. Kada kowa ya ci wani abu, mutane, da shanu, da tumaki, da awaki duka, kada kowa ya ci, ko ya sha ruwa. 8 Sai dukan mutane da dabbobi su sa tufafin makoki. Kowa ya roƙi Allah da gaske, kowa kuma ya bar mugayen ayyukan da yake yi. 9 Kila Allah zai dakatar da nufinsa, fushinsa ya huce, ya bar mu mu tsira daga mutuwa!” 10 Allah kuwa ya ga abin da suka yi, ya ga yadda suka bar mugayen ayyukansu, sai ya dakatar da nufinsa, bai hallaka su ba.

Yunusa 4

Fushin Yunusa a kan Jinƙan Allah

1 Zuciyar Yunusa ta ɓaci ƙwarai a kan wannan abu, har ya yi fushi. 2 Saboda haka ya yi addu'a ga Ubangiji ya ce, “Ina roƙonka, ya Ubangiji, ashe, dā ma can ban faɗa ba, kafin in bar gida, cewa irin abin da za ka yi ke nan? Ai, dalilin da ya sa na yi iyakar ƙoƙarina in gudu zuwa Tarshish ke nan. Na sani kai mai taushin hali ne, mai jinƙai, mai haƙuri. Kai kullum mai alheri ne, a shirye kake kuma ka dakatar da nufinka na yin hukunci. 3 Domin haka fa, ya Ubangiji, ina roƙonka ka ɗauki raina, gama yanzu gara in mutu da in zauna da rai.” 4 Ubangiji kuwa ya amsa ya ce, “Daidai ne ka yi fushi?” 5 Yunusa ya fita daga birnin, ya yi wajen gabas, ya zauna. Ya yi wa kansa rumfa, ya zauna a inuwarta, yana jira ya ga abin da zai sami birnin. 6 Sai Ubangiji ya sa wata 'yar kuranga ta tsiro ta yi girma a inda Yunusa yake, don ta inuwantar da shi, ya ji daɗi. Yunusa kuwa ya yi murna da wannan 'yar kuranga ƙwarai. 7 Amma kashegari da fitowar rana, sai Allah ya sa tsutsa ta cinye 'yar kurangar har ta mutu. 8 A sa'ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro. Yunusa ya ji kamar zai suma saboda zafin rana da ke bugun kansa. Sai ya so ya mutu, ya ce, “Gara in mutu da ina zaune da rai.” 9 Amma Allah ya ce masa, “Daidai ne ka yi fushi saboda 'yar kurangar?” Yunusa ya amsa, “Hakika, daidai ne a gare ni in yi fushi, har ma in yi fushin da ya isa in mutu!” 10 Ubangiji kuma ya amsa, ya ce masa, “Ai, wannan 'yar kurangar dare ɗaya ta girma, kashegari kuma ta mutu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓaci saboda ita! 11 Ashe, dole ne ni kuma in ji tausayin Nineba, babban birni mai 'yan yara fiye da dubu ɗari da dubu ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa.”

Mika 1

1 Ubangiji ya yi magana da Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da na Hezekiya, sarakunan Yahuza. Ya yi masa magana a kan Samariya da Urushalima.

Makoki don Samariya da Urushalima

2 Dukanku ku ji, ku al'ummai! Ki kasa kunne, ya duniya, da dukan abin da yake cikinki. Bari Ubangiji Allah Daga Haikalinsa mai tsarki ya zama shaida a kanku. 3 Ga shi, Ubangiji yana fitowa daga wurin zamansa, Zai sauko, ya taka kan tsawawan duwatsun duniya. 4 Duwatsu za su narke a ƙarƙashinsa, Kwaruruka za su tsattsage kamar kakin zuma a gaban wuta, Kamar ruwa yana gangarowa daga tsauni. 5 Duk wannan kuwa saboda laifin Yakubu ne, Da laifin Isra'ila. Mene ne laifin Yakubu? Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin da ake yi a Samariya ba? Mene ne kuma laifin Yahuza? Ashe, ba bautar gumaka da zaluncin da ake yi a Urushalima ba? 6 “Domin haka zan mai da Samariya jujin kufai a karkara, Wurin dasa kurangar inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari, In tone harsashin gininta. 7 Za a farfashe dukan siffofinta na zubi, Za a ƙaƙƙone dukiyarta da wuta, Zan lalatar da gumakanta duka, Gama ta wurin karuwanci ta samo su, Ga karuwanci kuma za su koma.” 8 Mika ya ce, “Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka, Zan tuɓe, in yi tafiya huntu. Zan yi kuka kamar diloli, In yi baƙin ciki kamar jiminai. 9 Gama raunin Samariya, ba ya warkuwa, Gama ya kai Yahuza, Ya kuma kai ƙofar jama'ata a Urushalima.” 10 Kada a faɗe shi a Gat, Sam, kada a yi kuka. Yi birgima cikin ƙura a Bet-leyafra. 11 Ku mazaunan Shafir, ku wuce abinku da tsiraici da kunya. Mazaunan Za'anan ba su tsira ba. Bet-ezel ta yi kururuwa, “Zai tumɓuke harasashin gininki.” 12 Mutanen Marot sun ƙosa su ga alheri, Amma masifa ta zo ƙofar Urushalima daga wurin Ubangiji. 13 Ku mutanen Lakish, ku ɗaura wa dawakai karusai, Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, Gama an iske laifofin Isra'ila cikinku. 14 Domin haka sai ku ba Moreshet-gat guzuri, Mutanen Akzib za su yaudari sarakunan Isra'ila. 15 Ku mazaunan Maresha, Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi, Darajar Isra'ila za ta shiga Adullam. 16 Ku aske kanku saboda ƙaunatattun 'ya'yanku. Ku yi wa kanku ƙwaƙwal kamar ungulu, Gama 'ya'yanku za su tafi bautar talala.

Mika 2

Taku ta Ƙare, ku masu Zaluntar Matalauta

1 Taku ta ƙare, ku masu shirya mugunta, Masu tsara mugunta a gadajensu! Sa'ad da gari ya waye, sai su aikata ta, Domin ikon aikatawa yana hannunsu. 2 Sukan yi ƙyashin gonaki da gidaje, sai su ƙwace. Sukan zalunci mutum, su ƙwace gidansa da gādonsa. 3 Domin haka Ubangiji ya ce, Ga shi, yana shirya wa wannan jama'a masifa, Wadda ba za ku iya kuɓuta daga cikinta ba. Ba kuma za ku yi tafiyar alfarma ba, Gama mugun lokaci ne. 4 A wannan rana za su yi karin magana a kanku, Za su yi kuka da baƙin ciki mai zafi, Su ce, “An lalatar da mu sarai! Ya sāke rabon mutanena, Ya kawar da shi daga gare ni! Ya ba da gonakinmu ga waɗanda suka ci mu da yaƙi.” 5 Don haka ba za ku sami wanda zai sa muku ma'auni A taron jama'ar Ubangiji ba. 6 “Kada su yi wa'azi,” amma sun yi wa'azi. “Idan ba su yi wa'azi a kan abubuwan nan ba, Raini ba zai ƙare ba. 7 Daidai ne a faɗi haka, ya jama'ar Yakubu? ‘Ruhun Ubangiji ya yi rashin haƙuri ne? Waɗannan ayyukansa ne?’ ” “Ashe, maganata ba takan amfana wanda yake tafiya daidai ba?” 8 Ubangiji ya amsa ya ce, “Ba da daɗewa ba mutanena sun tashi kamar maƙiyi, Kukan tuɓe rigar masu wucewa da salama, masu komawa da yaƙi. 9 Kukan kori matan mutanena Daga gidajensu masu kyau, Kukan kawar da darajata har abada daga wurin 'ya'yansu. 10 Ku tashi, ku tafi, Gama nan ba wurin hutawa ba ne, Saboda ƙazantarku wadda take kawo muguwar hallaka. 11 “Idan mutum ya tashi yana iskanci, yana faɗar ƙarya, ya ce, ‘Zan yi muku wa'azi game da ruwan inabi da abin sa maye,’ To, shi ne zai zama mai wa'azin mutanen nan! 12 “Hakika zan tattara ku duka, ya Yakubu, Zan tattara ringin Isra'ila. Zan haɗa su tare kamar tumaki a garke, Kamar garken tumaki a makiyaya Za su zama taron jama'a mai hayaniya. 13 “Wanda zai huda garu, shi zai yi musu jagora, Za su fita ƙofar, su wuce, su fice ta cikinta. Sarkinsu zai wuce gabansu, Ubangiji kuma yana kan gaba.”

Mika 3

An yi wa Shugabannin Isra'ila Faɗa

1 Ni kuwa na ce, “Ku ji, ya ku shugabannin mutanen Yakubu, Da ku sarakunan Isra'ila. Ya kamata ku san shari'a. 2 Amma kuna ƙin nagarta, kuna ƙaunar mugunta, Kuna feɗe mutanena, Kuna kuma fizge naman jikinsu daga ƙasusuwansu. 3 Kuna cin naman mutanena, kuna feɗe fatar jikinsu, Kuna kakkarya ƙasusuwansu, Kuna yanyanka su gunduwa gunduwa kamar naman da za a sa a tukunya.” 4 Sa'an nan za su yi kuka ga Ubangiji, Amma Ubangiji ba zai amsa musu ba. Zai ɓoye musu fuskarsa a wannan lokaci, Saboda mugayen ayyukansu. 5 Ga abin da Ubangiji ya ce a kan annabawan da suka bi da mutanensa a karkace, Waɗanda suke cewa, “Salama,” sa'ad da suke da abinci, Amma sukan kai yaƙin shahada Ga wanda bai ba su abin sawa a baka ba. 6 Saboda haka kome zai zama dare da duhu, ba wahayi ko duba. Rana za ta fāɗi a kan annabawa, Yini zai zama musu duhu baƙi ƙirin. 7 Masu gani za su sha kunya, Masu duba kuwa za su ruɗe, Dukansu za su rufe bakinsu, Gama ba amsa daga wurin Allah. 8 Amma ni ina cike da iko, Da Ruhun Ubangiji, Da shari'a da ƙarfin hali, Don in sanar wa Yakubu da laifinsa, Isra'ila kuma da zunubinsa. 9 Ku ji wannan, ya ku shugabannin jama'ar Yakubu, Da ku sarakunan mutanen Isra'ila, Ku da kuke ƙyamar shari'ar gaskiya, Kuna karkatar da dukan gaskiya. 10 Kuna gina Sihiyona da jini, Kuna kuwa gina Urushalima da zalunci. 11 Shari'ar shugabannin ƙasar ta cin hanci ce. Firistocinta suna koyarwa don neman riba, Haka kuma annabawa suna annabci don neman kuɗi. Duk da haka suna dogara ga Ubangiji, suna cewa, “Ai, Ubangiji yana tsakiyarmu, Ba masifar da za ta same mu.” 12 Saboda ku kuwa za a nome Sihiyona kamar gona, Urushalima kuwa za ta zama tsibin kufai, Dutse inda Haikali yake zai zama kurmi.

Mika 4

Mulkin Salama na Ubangiji

1 Zai zama nan gaba, dutse inda Haikalin Ubangiji yake Zai zama shi ne mafi tsawo duka a cikin duwatsu, Zai fi tuddai tsayi, Mutane kuwa za su riƙa ɗunguma zuwa wurinsa. 2 Al'umman duniya za su zo, su ce, “Bari mu haura zuwa tudun Ubangiji, Zuwa Haikalin Allah na Isra'ila, Za mu koyi abin da yake so mu yi, Za mu yi tafiya a hanyar da ya zaɓa.” Koyarwar Ubangiji daga Urushalima take zuwa, Daga Sihiyona yake magana da jama'arsa. 3 Zai shara'anta tsakanin al'umman duniya masu yawa, Zai sulhunta jayayyar da take tsakanin manyan al'ummai, Za su mai da takubansu garemani, Māsunsu kuma su maishe su wuƙaƙen aske itace. Al'umma ba za ta ƙara fita zuwa yaƙi ba, Ba za su ƙara koyon yaƙi ba. 4 Kowa zai zauna gindin kurangar inabinsa da gindin ɓaurensa. Ba wanda zai tsoratar da shi, Gama Ubangiji Mai Runduna ne ya faɗa. 5 Ko da yake al'ummai suna bin gumakansu, Amma mu za mu bi Ubangiji Allahnmu har abada abadin.

Kuɓutar Isra'ila daga Zaman Talala

6 Ubangiji ya ce, “A waccan rana zan tattara guragu, Da waɗanda aka kora, Da waɗanda na wahalshe su. 7 Zan sa guragu su wanzu, Korarru kuwa su zama al'umma mai ƙarfi, Ni, Ubangiji, zan yi mulkinsu a Sihiyona har abada. 8 “Ke kuma hasumiyar garken tumaki, tudun Sihiyona, Mulki na dā zai komo wurinki, Wato sarautar Urushalima.” 9 Yanzu, me ya sa kike kuka da ƙarfi? Ba sarki a cikinki ne? Mashawarcinki ya hallaka ne, Da azaba ta auka miki kamar ta mace mai naƙuda? 10 Ki yi makyarkyata, ki yi nishi, ke Sihiyona, Kamar mace mai naƙuda, Gama yanzu za ki fita daga cikin birni, Ki zauna a karkara, Za ki tafi Babila, daga can za a cece ki. Daga can Ubangiji zai cece ki daga hannun maƙiyanki. 11 Yanzu al'ummai sun taru suna gāba da ke, suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, Bari mu zura mata ido.” 12 Amma ba su san nufin Ubangiji ba, Ba su gane shirinsa ba, Gama ya tara su ne kamar dammunan da za a kai masussuka. 13 “Ya Sihiyona, ki tashi, ki tattaka! Gama zan mai da ƙahonki ƙarfe, kofatanki kuwa tagulla, Za ki ragargaje al'ummai da yawa.” Za ki ba Ubangijin dukan duniya dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, Wadatarsu kuma ga Ubangijin dukan duniya.

Mika 5

1 Ki tattara sojojinki, gama an kewaye mu da yaƙi. Za su bugi kumatun Sarkin Isra'ila da sanda.

Mulkin Mai Ceto daga Baitalami

2 “Baitalami cikin Efrata, Wadda kike 'yar ƙarama a cikin kabilar Yahuza, Amma daga cikinki wani zai fito wanda zai sarauci Isra'ila Wanda asalinsa tun fil azal ne.” 3 Domin haka zai yashe su, Sai lokacin da wadda take naƙuda ta haihu. Sa'an nan sauran 'yan'uwansa Za su komo wurin mutanen Isra'ila. 4 Shi kuwa zai tashi ya ciyar da garkensa da ƙarfin Ubangiji, Da ɗaukakar sunan Ubangiji Allahnsa. Za su kuwa zauna lafiya, Gama zai zama mai girma cikin duniya duka. 5 Zai zama salamarmu. Ceto da Hukunci Sa'ad da kuma Assuriyawa za su kawo mana yaƙi, Za su tattake kagaranmu, Za mu sa makiyaya bakwai da shugabanni takwas su yi gāba da su. 6 Za su mallaki ƙasar Assuriya da takobi, Su shiga ƙofofin ƙasar Nimrod da zararren takobi, Zai cece mu daga hannun Ba'assuriye, Sa'ad da ya kawo wa ƙasarmu yaƙi, Sa'ad da kuma ya tattake ƙasarmu. 7 Sa'an nan ringin Yakubu zai zamar wa mutane Kamar raɓa daga wurin Ubangiji, Kamar kuma yayyafi a kan tsire-tsire, Wanda ba ya jinkiri ko ya jira mutane. 8 Ringin Yakubu kuma zai zamar wa al'umman duniya, Kamar yadda zaki yake a tsakanin namomin jeji, Kamar kuma yadda zaki yake a tsakanin garkunan tumaki, Wanda, sa'ad da ya ratsa, yakan tattaka, Ya yi kacakaca da su, Ba wanda zai cece su. 9 Za a ƙarfafa hannunka a kan maƙiyanka, Za a datse maƙiyanka duka. 10 “A wannan rana, ni Ubangiji na ce, Zan kashe dawakanku, in hallaka karusanku. 11 Zan shafe biranen ƙasarku, In rushe garunku. 12 Zan kawar da maita daga ƙasarku, Ba za ku ƙara samun bokaye ba. 13 Zan sassare siffofinku da ginshiƙanku, Ba za ku ƙara sunkuya wa aikin hannuwanku ba. 14 Zan tumɓuke gumakan nan Ashtarot daga cikinku, Zan hallaka biranenku. 15 Da fushi da hasala zan yi sakayya A kan al'umman da ba su yi biyayya ba.”

Mika 6

Ubangiji yana Gāba da Isra'ila

1 “Ku ji abin da ni Ubangiji nake cewa, Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu, Ku bar tuddai su ji muryarku. 2 “Ku duwatsu da madawwaman tussan duniya, Ku ji tuhumar da Ubangiji yake yi muku. Gama Ubangiji, yana da magana gāba da mutanensa, Zai tuhumi Isra'ila. 3 “Ya ku jama'ata, me na yi muku? Wace irin fitina nake yi muku? Ku amsa mini! 4 Gama na fito da ku daga ƙasar Masar, Na fanshe ku daga gidan bauta. Na aika muku da Musa, da Haruna, da Maryamu. 5 Ya ku jama'ata, ku tuna Da abin da Balak, Sarkin Mowab, ya ƙulla, Da yadda Bal'amu ɗan Beyor ya amsa masa, Da abin da ya faru daga Shittim, har zuwa Gilgal, Don ku san ayyukan adalci na Ubangiji.”

Abin da Allah yake So ga Mutane

6 Da me zan zo gaban Ubangiji, In sunkuyar da kaina a gaban Allah na Sama? Ko in zo gabansa da maraƙi bana ɗaya domin yin hadaya ta ƙonawa? 7 Ubangiji zai yi murna da raguna dubbai Ko kuwa da kogunan mai dubbai? Zan ba da ɗan farina ne don laifina? Ko kuwa zan ba da 'ya'yana saboda zunubina? 8 Ya kai mutum, ya riga ya nuna maka abin da yake mai kyau. Abin da Ubangiji yake so gare ka, shi ne Ka yi adalci, ka ƙaunaci aikata alheri, Ka bi Allah da tawali'u. 9 Ubangiji yana kira ga birnin. Hikima ce ƙwarai a ji tsoron sunanka. “Ki ji ya kabila, wa ya sa miki lokacinki? 10 Ba zan manta da dukiya ta mugunta a gidan mugu ba, Ba kuwa zan manta da bugaggen mudun awo ba. 11 Zan kuɓutar da mutum mai ma'auni na cuta Da ma'aunin ƙarya? 12 Attajiran birnin sun cika zalunci, Mazaunansa kuwa maƙaryata ne, Harshensu na yaudara ne. 13 Domin haka zan buge ku da ciwo, In maishe ku kufai saboda zunubanka. 14 Za ka ci, amma ba za ku ƙoshi ba, Yunwa za ta kasance a cikinku, Za ku tanada, amma ba zai tanadu ba, Abin da kuma kuka tanada zan bai wa takobi. 15 Za ku shuka, amma ba za ku girbe ba. Za ku matse 'ya'yan zaitun, amma ba za ku shafa mansa ba, Za ku kuma matse 'ya'yan inabi, amma ba za ku sha ruwansa ba. 16 Domin kun kiyaye dokokin Omri, Kun bi halin gidan Ahab, Kun kuma bi shawarwarinsu. Domin haka zan maishe ku kufai, In mai da ku abin dariya, Za ku sha raini a wurin mutanena.”

Mika 7

Lalacewar Isra'ila

1 Tawa ta ƙare, gama na zama kamar lokacin da aka gama tattara amfanin gona, Kamar lokacin da aka gama kalar 'ya'yan inabi, Ba nonon inabi da za a tsinka, a ci, Ba kuma 'ya'yan ɓaure da suka harba wanda raina yake so. 2 Mutanen kirki sun ƙare a duniya, Ba nagarta a cikin mutane. Dukansu suna kwanto don su zub da jini. Kowa yana farautar ɗan'uwansa da tarko. 3 Sun himmantu su aikata abin da yake mugu da hannuwansu. Sarki da alƙali suna nema a ba su hanci, Babban mutum kuma yana faɗar son zuciyarsa, Da haka sukan karkatar da zance. 4 Mutumin kirkinsu kamar ƙaya yake, Mai gaskiyarsu kuwa kamar shingen ƙaya yake. Ranar da kuka sa mai tsaro, A ran nan za a aukar muku da hukunci. Yanzu ruɗewarku ta zo, 5 Kada ka dogara ga maƙwabcinka, Kada kuma ka amince da abokinka. Ka kuma kame bakinka daga matarka Wadda take kwance tare da kai. 6 Gama ɗa yana raina mahaifi, 'Ya kuma tana tayar wa mahaifiyarta, Matar ɗa kuma tana gāba da surukarta, Mutanen gidan mutum su ne maƙiyansa.

Ubangiji zai Kawo Haske da Ceto

7 Amma ni zan kafa ido ga Ubangiji, Zan jira ceton Allahna, Allahna zai ji ni. 8 Ya maƙiyina, kada ka yi murna a kaina, Gama sa'ad da na fāɗi, zan tashi kuma. Sa'ad da na zauna cikin duhu, Ubangiji zai haskaka ni. 9 Zan ɗauka fushin Ubangiji ne, Gama na yi masa zunubi, Sai lokacin da ya ji da'awata, Har ya yanke mini shari'a. Zai kawo ni zuwa wurin haske, Zan kuwa ga cetonsa. 10 Sa'an nan maƙiyina wanda yake ce mini, “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, ya kuma ji kunya. Idanuna za su gan shi lokacin da aka tattake shi Kamar taɓo a titi. 11 Za a faɗaɗa iyakarka A ranar da za a gina garunka. 12 A waccan rana mutane za su zo wurinka, Daga Assuriya har zuwa Masar, Daga Masar zuwa Kogin Yufiretis, Daga teku zuwa teku, daga dutse zuwa dutse. 13 Duniya kuwa za ta zama kufai, Saboda mazaunan da suke cikinta, Saboda hakkin ayyukansu.

Juyayin Ubangiji a kan Isra'ila

14 Sai ka yi kiwon mutanenka da sandanka, Wato garken mallakarka, Wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi A tsakiyar ƙasa mai albarka. Bari su yi kiwo cikin Bashan da Gileyad Kamar a kwanakin dā. 15 “Zan nuna muku abubuwa masu banmamaki, Kamar a kwanakin da kuka fito ƙasar Masar.” 16 Al'umman duniya za su gani, Su kuwa ji kunyar ƙarfinsu duka. Za su sa hannuwansu a baka, Kunnuwansu za su kurmance. 17 Za su lashi ƙura kamar maciji da abubuwa masu rarrafe, Za su fito da rawar jiki daga wurin maɓuyarsu, Da tsoro za su juyo wurin Ubangiji Allahnmu, Za su ji tsoronka. 18 Akwai wani Allah kamarka, mai yafe mugunta, Mai kawar da laifin ringin gādonsa? Ba ya riƙon fushi har abada, gama shi mai alheri ne. 19 Zai sāke jin juyayinmu, Ya tattake muguntarmu a ƙarƙashin ƙafafunsa. Za ka jefar da zunubanmu a cikin zurfin teku. 20 Za ka nuna wa Yakubu aminci, Ga Ibrahim kuma madawwamiyar ƙauna, Kamar yadda ka rantse wa kakanninmu Tun a zamanin dā.

Nahum 1

Fushin Ubangiji a kan Nineba

1 Jawabi a kan Nineba ke nan, a littafin wahayin Nahum na Elkosh. 2 Ubangiji Allah mai kishi ne, mai sakayya, Ubangiji mai sakayya ne, mai hasala. Ubangiji yakan ɗauki fansa a kan maƙiyansa. Yana tanada wa maƙiyansa fushi. 3 Ubangiji mai jinkirin fushi ne, Mai Iko Dukka. Ubangiji ba zai kuɓutar da mai laifi ba. Hanyarsa tana cikin guguwa da cikin hadiri, Gizagizai su ne ƙurar ƙafafunsa. 4 Yakan tsauta wa teku, sai teku ta ƙafe. Yakan busar da koguna duka. Bashan da Karmel sukan bushe, Tohon Lebanon yakan yanƙwane. 5 Duwatsu sukan girgiza a gabansa, Tuddai kuma su narke. Duniya ta murtsuke a gabansa, Da dukan mazauna a cikinta. 6 Wa zai iya tsaya wa fushinsa? Wa kuma zai iya daurewa da hasalarsa? Yana zuba hasalarsa mai kama da wuta, Duwatsu sukan farfasu a gabansa. 7 Ubangiji mai alheri ne, Shi mafaka ne a ranar wahala. Ya san waɗanda suke fakewa a gare shi. 8 Zai shafe maƙiyansa da ambaliyar ruwa, Zai kuma runtumi maƙiyansa zuwa cikin duhu. 9 Me kuke ƙullawa game da Ubangiji? Ubangiji zai wofintar da abin nan da kuke ƙullawa, Sau ɗaya kawai zai hallaka ku. 10 Suna maye da abin shansu, Za su ƙone kamar sarƙaƙƙiyar ƙaya, Da busasshiyar ciyawa. 11 Daga cikinki wani ya fito, Wanda ya ƙulla wa Ubangiji makirci, Ya ƙulla shawara marar amfani. 12 Ni Ubangiji na ce, “Ko da yake suna da ƙarfi, suna kuma da yawa, Za a datse su, su ƙare. Ko da yake na wahalar da kai, Ba zan ƙara wahalar da kai ba. 13 Yanzu zan karya karkiyarsa daga wuyanka, Zan kuma tsinke sarƙarta.” 14 Ubangiji ya riga ya yi umarni a kanka cewa, “Sunanka ba zai ci gaba ba, Zan farfashe sassaƙaƙƙun siffofi Da siffofi na zubi daga gidan gumakanka. Zan shirya maka kabari, gama kai rainanne ne.”

Labarin Fāɗuwar Nineba

15 Duba a kan duwatsu, ƙafafun wanda yake kawo albishir, Wanda yake shelar salama! Ya Yahuza, ka yi bikin idodinka, Ka kuma cika wa'adodinka. Gama mugun ba zai sāke zuwa ya yi gāba da kai ba, An datse shi ƙaƙaf.

Nahum 2

1 Wanda yake farfashewa ya auko maka, Sai ka sa mutane a kagara, a yi tsaron hanya, Ka yi ɗamara, ka tattaro ƙarfinka duka. 2 Gama Ubangiji zai mayar wa Yakubu da darajarsa kamar ta Isra'ila. Ko da masu washewa sun washe su, Sun kuma lalatar da rassan inabinsu. 3 Garkuwoyin jarumawansa jajaye ne, Sojojinsa kuma suna saye da mulufi. Da ya shirya tafiya, Karusai suna walƙiya kamar harshen wuta, Ana kaɗa mashi da bantsoro. 4 Karusai sun zabura a tituna a haukace. Suna kai da kawowa a dandali, Suna walwal kamar jiniya, Suna sheƙawa a guje kamar walƙiya. 5 Sai aka kira shugabanni, Suka zo a guje suna tuntuɓe, Suka gaggauta zuwa garu, Suka kafa kagara. 6 An buɗe ƙofofin kogi, Fāda ta rikice. 7 An tsiraita sarauniya, an tafi da ita, 'Yan matanta suna makoki, suna kuka kamar kurciyoyi, Suna bugun ƙirjinsu. 8 Nineba tana kama da tafki wanda ruwansa yake zurarewa, Suna cewa, “Tsaya, tsaya,” Amma ba wanda ya waiga. 9 A washe azurfa! A washe zinariya! Dukiyar ba ta da adadi, Akwai dukiya ta kowane iri. 10 Nineba ta hallaka! Ta lalace, ta zama kufai! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa! Kwankwaso yana ciwo, Fuskoki duka sun kwantsare! 11 Ina kogon nan na zakoki, Inda aka ciyar da 'ya'yan zaki, Inda zaki da zakanya da kwiyakwiyansu sukan tafi, Su tsere daga fitina? 12 Zaki ya kashe abin da ya ishi kwiyakwiyansa. Ya kaso wa zakanyarsa abin da ya ishe ta. Ya cika kogonsa da ganima.

Ragargajewar Nineba

13 “Ga shi, ina gāba da ke. Ni Ubangiji Allah Mai Runduna na faɗa. Zan ƙone karusanki, Takobi kuwa zai karkashe sagarun zakokinki, Zan hana miki ganima a duniya. Ba za a ƙara jin muryoyin jakadunki ba.”

Nahum 3

1 Kaiton birnin jini, Wanda yake cike da ƙarairayi da ganima, Da waso kuma ba iyaka! 2 Ku ji amon bulala da kwaramniyar ƙafafu, Da sukuwar doki da girgizar karusai! 3 Sojojin dawakai suna kai sura, Takuba suna walƙiya, māsu suna ƙyalƙyali. Ga ɗumbun kisassu, da tsibin gawawwaki, Matattu ba su ƙidayuwa, Suna tuntuɓe a kan gawawwaki! 4 Ya faru saboda yawan karuwancin Nineba kyakkyawa mai daɗin baki, Wadda ta ɓad da al'umman duniya da karuwancinta, Ta kuma ɓad da mutane da daɗin bakinta. 5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ina gāba da ke, Zan kware fatarinki a idonki, Zan sa al'ummai da mulkoki su dubi tsiraicinki. 6 Zan watsa miki ƙazanta, In yi miki wulakanci, In maishe ki abin raini. 7 Dukan waɗanda za su dube ki Za su ja da baya su ce, ‘Nineba ta lalace, wa zai yi kuka dominta?’ A ina zan samo miki waɗanda za su ta'azantar da ke?” 8 Kin fi No ne? Wadda take a bakin Nilu, Wadda ruwa ya kewaye ta? Teku ce kagararta. Ruwa ne kuma garunta. 9 Habasha da Masar su ne ƙarfinta marar iyaka, Fut da Libiya su ne kuma mataimakanta. 10 Duk da haka an tafi da ita, an kai ta cikin bauta. An fyaɗa ƙanananta a ƙasa, An yi kacakaca da su a kowace mararraba. An jefa kuri'a a kan manyan mutanenta, Aka ɗaure dukan manyan mutanenta da sarƙoƙi. 11 Ke Nineba kuma za ki bugu, Za a ɓoye ki. Za ki nemi mafaka a wurin maƙiyinki. 12 Dukan kagaranki suna kama da itatuwan ɓaure, Waɗanda 'ya'yansu suka harba. Da an girgiza sai su faɗo a bakin mai sha. 13 Sojojinki kamar mata suke a tsakiyarki! An buɗe wa maƙiyanki ƙofofin ƙasarki. Wuta za ta cinye madogaran ƙofofinki. 14 Ki tanada ruwa domin za a kewaye ki da yaƙi! Ki ƙara ƙarfin kagaranki! Ki tafi kududdufi, ki kwaɓa laka! Ki ɗauki abin yin tubali! 15 A can wuta za ta cinye ki, Takobi zai sare ki, Zai cinye ki kamar fara. Ki riɓaɓɓanya kamar fara. Ki kuma riɓaɓɓanya kamar ɗango. 16 Kin yawaita 'yan kasuwanki suna da yawa fiye da taurari, Amma sun tafi kamar fara waɗanda sukan buɗe fikafikansu su tashi, su tafi. 17 Shugabanninki kamar ɗango suke, Manyan mutanenki kamar cincirindon fāra ne, Suna zaune a kan shinge a kwanakin sanyi, Sa'ad da rana ta fito, sukan tashi su tafi, Ba wanda ya san inda suke. 18 Ya Sarkin Assuriya, masu tsaronka suna barci, Manyan mutanenka suna kwankwance, Mutanenka sun watse cikin duwatsu, Ba wanda zai tattaro su. 19 Ba abin da zai rage zafin rauninka, Rauninka ba ya warkuwa. Duk wanda ya ji labarinka, zai tafa hannuwansa Gama wane ne ba ka musguna wa ba?

Habakuk 1

Damuwar Habakuk a kan Rashin Gaskiya

1 Jawabin da annabi Habakuk ya hurta ke nan. 2 Ya Ubangiji, ina ta kukan neman taimako, Amma ka ƙi ji, sai yaushe za ka ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci, Amma ba ka yi taimako ba. 3 Me ya sa ka sa ni in ga mugunta, In kuma dubi wahala? Hallaka da zalunci suna a gabana. Jayayya da gardama sun tashi. 4 Ba a bin doka, Shari'a kuma ba ta aiki. Mugaye sun fi adalai yawa nesa, Don haka shari'a tana tafe a karkace.

Kaldiyawa za su Hori Yahuza

5 Ubangiji ya ce, “Ka duba cikin al'umman duniya! Ka gani! Ka yi al'ajabi! Ka yi mamaki! Gama zan yi aiki a kwanakinka, Ko an faɗa maka ba za ka gaskata ba. 6 Ga shi, ina tā da Kaldiyawa, Al'umman nan mai zafi, mai fitina, Waɗanda suke tafiya ko'ina a duniya, Sun ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba. 7 Suna da bantsoro da firgitarwa. Adalcinsu da ikonsu sun danganta ga yadda suke so. 8 “Dawakansu sun fi damisa sauri, Sun fi kyarketan maraice zafin hali, Sojojin dawakansu suna zuwa a guje. Sojojin dawakansu suna zuwa daga nesa, Sukan tashi kamar gaggafa da sauri don su cinye. 9 “Sun zo don su yi kama-karya. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su zo. Sun tattara bayi kamar yashi. 10 Sukan yi wa sarakuna ba'a, Sukan mai da masu milki abin wasa. Kowace kagara abin dariya ce a wurinsu, Sukan tsiba ƙasa, su hau, su cinye ta. 11 Sukan wuce da sauri kamar iska, Su yi tafiyarsu. Su masu laifi ne, Ƙarfinsu shi ne gunkinsu.”

Habakuk ya Ƙara Kuka ga Ubangiji

12 Ba kai ne madawwami ba? Ya Ubangiji Allahna Mai Tsarki. Ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji, kai ne ka sa su su yi hukunci, Ya dutse, kai ne ka kafa su don su yi horo. 13 Kai mai tsarki ne, Ka fi ƙarfin ka dubi mugunta. Kai da ba ka duban laifi. Me ya sa kake duban marasa imani? Kana iya shiru sa'ad da mugu yake haɗiye Mutumin da ya fi shi adalci? 14 Gama ka mai da mutane kamar kifaye a cikin teku, Kamar abubuwa masu rarrafe da ba su da shugaba. 15 Kaldiyawa sukan kama mutane da ƙugiya, Sukan jawo su waje da tarunsu, Sa'an nan su tara su cikin ragarsu, Su yi murna da farin ciki. 16 Domin haka sukan miƙa hadaya ga tarunsa, Su ƙona turare ga ragarsu, Domin su ne suka jawo musu wadata, da abinci mai yawa. 17 Za su ci gaba da juye tarunsa ke nan? Su yi ta karkashe al'umman duniya ba tausayi?

Habakuk 2

Ubangiji ya Amsa wa Habakuk

1 Zan tsaya a wurin tsayawata, In zauna kuma a kan hasumiya, In jira in ji abin da zai ce mini, Da abin da zai amsa a kan kukata. 2 Sai Ubangiji ya ce mini, “Ka rubuta wahayin da kyau a kan alluna, Yadda kowa zai karanta shi a sawwaƙe. 3 Gama har yanzu wahayin yana jiran lokacinsa, Yana gaggautawa zuwa cikarsa, Ba zai zama ƙarya ba. Ka jira shi, ko da ka ga kamar yana jinkiri, Hakika zai zo, ba zai makara ba. 4 Wanda zuciyarsa ba daidai take ba, zai fāɗi, Amma adali zai rayu bisa ga bangaskiyarsa. 5 “Ruwan inabi kuma yana yaudarar mai fāriya, Don haka ba ya zama a gida. Haɗamarsa tana da fāɗi kamar Lahira, Kamar kuma mutuwa yake, ba ya ƙoshi. Ya tattara wa kansa al'ummai duka, Ya kwaso wa kansa mutane duka.”

Marasa Adalci, Tasu ta Ƙare

6 “Ai, waɗannan duka za su yi ta yi masa zambo, Su yi masa dariya ta raini, Su ce, ‘Tasa ta ƙare, shi wanda ya tattara abin da ba nasa ba, Har yaushe zai riƙa arzuta kansa ta hanyar ba da rance?’ 7 Mabartanka za su tasar maka nan da nan, Waɗanda suke binka bashi za su farka. Za ka zama ganima a gare su. 8 Saboda ka washe al'umman duniya da yawa, Sauran mutanen duniya duka za su washe ka, Saboda jinin mutane, da wulakancin da ka yi wa duniya, Da birane, da mazauna a cikinsu. 9 “Tasa ta ƙare, shi wanda ya arzuta gidansa da ƙazamar riba, Ya kuma gina gidansa a bisa don ya tsere wa masifa! 10 Ka jawo wa gidanka kunya, Saboda ka karkashe mutane da yawa, Ka hallaka kanka da kanka. 11 Dutse zai yi kuka daga garu, Katako kuwa zai amsa masa daga aikin da aka yi da itace. 12 “Tasa ta ƙare, shi wanda ya gina gari da jini, Ya kuma kafa birni da mugunta! 13 Ba Ubangiji Mai Runduna ne ya sa mutanen duniya, su yi wahala, wuta ta cinye ba? Sun kuma gajiyar da kansu a banza? 14 Duniya za ta cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, Kamar yadda ruwa ya cika teku. 15 “Taka ta ƙare, kai wanda kake sa maƙwabtanka su sha, Kana zuba musu dafinka har su bugu, Don ka dubi tsiraicinsu! 16 A maimakon daraja, za ka sha ƙasƙanci. Ka sha kai da kanka, ka yi tangaɗi. Ƙoƙon da yake a hannun Ubangiji zai fāɗo a kanka, Kunya za ta rufe darajarka. 17 Ɓarnar da aka yi wa Lebanon za ta komo kanka, Ka kashe dabbobinta, yanzu dabbobi za su tsorata ka, Saboda jinin mutanen da ka zubar, Da wulakancin da ka yi wa duniya, Da birane, da mazauna a cikinsu. 18 “Ina amfanin gunki sa'ad da mai yinsa ya siffata shi? Shi siffa ne da aka yi da ƙarfe, mai koyar da ƙarya. Gama mai yinsa yakan dogara ga abin da ya siffata, Sa'ad da ya yi bebayen gumaka. 19 Tasa ta ƙare, shi wanda ya ce da abin da aka yi da itace, ‘Farka!’ Ya kuma ce wa dutse wanda ba ya ji, ‘Tashi!’ Wannan zai iya koyarwa? Ga shi, an dalaye shi da zinariya da azurfa, Ba ya numfashi ko kaɗan. 20 “Amma Ubangiji yana cikin tsattsarkan Haikalinsa, Bari duniya ta yi tsit a gabansa.”

Habakuk 3

Addu'ar Habakuk

1 Addu'ar nasara wadda annabi Habakuk ya yi. 2 Ya Ubangiji, na ji labarinka, Sai tsoro ya kama ni. Ka maimaita manyan ayyukanka a zamaninmu, Ayyukan da ka saba yi. Ka yi jinƙai ko lokacin da kake fushi. 3 Daga Edom Allah ya zo, Daga dutsen Faran Mai Tsarki yake tahowa. Ɗaukakarsa ta rufe sammai, Duniya kuwa ta cika da yabonsa. 4 Walƙiyarsa kamar hasken rana ce, Haske yana haskakawa daga gare shi, A nan ne ya lulluɓe ikonsa. 5 Annoba tana tafe a gabansa, Cuta kuma tana bin bayansa kurkusa. 6 Ya tsaya, ya auna duniya, Ya duba, sai ya girgiza al'umman duniya. Sa'an nan madawwaman duwatsu suka farfashe, Madawwaman tuddai kuma suka zama bai ɗaya. Haka hanyoyinsa suke tun adun adun. 7 Na ga alfarwan Kushan suna cikin azaba, Labulen ƙasar Madayana suna rawar jiki. 8 Ya Ubangiji, ka hasala da koguna ne? Ko kuwa ka yi fushi da koguna? Ko kuwa ka hasala da teku ne, Sa'ad da ka hau dawakanka, kana bisa karusarka ta nasara? 9 Ka ja bakanka, Ka rantsar da sandunan horo. Ka rarratsa duniya da koguna. 10 Duwatsu sun gan ka, sun ƙame, Ruwaye masu hauka suka gudu. Zurfi kuma ya ta da muryarsa, Raƙuman ruwansa sun kwanta. 11 Rana da wata sun tsaya cik a inda suke, A lokacin da kibanka masu haske suke wucewa fyu, Da lokacin walƙatawar hasken māshinka. 12 Ka ratsa duniya da hasala, Ka kuma tattake al'umman duniya da fushi. 13 Ka fito saboda ceton mutanenka, Saboda ceton shafaffenka kuma. Ka fasa kan mugu, Ka kware shi daga cinya zuwa wuya. 14 Ka kuje kan mayaƙansa da sandunansa, Waɗanda suka zo kamar guguwa don su watsar da mu. Suna murna kamar waɗanda suke zaluntar matalauci a ɓoye. 15 Ka tattake teku da dawakanka, Da haukan ruwa mai ƙarfi. 16 Sa'ad da na ji, sai jikina ya yi rawa, Leɓunana suka raurawa. Ƙasusuwana suka ruɓe, sai na yi rawar jiki. Zan yi shiru in jira ranar wahala da za ta zo A kan waɗanda suka kawo mana yaƙi. 17 Ko da yake itacen ɓaure bai yi toho ba, Ba kuma 'ya'ya a kurangar inabi, Zaitun kuma bai ba da amfani ba, Gonaki ba su ba da abinci ba, An kuma raba garken tumaki daga cikin garke, Ba kuma shanu a turaku, 18 Duk da haka zan yi farin ciki da Ubangiji, Zan yi murna da Allah Mai Cetona. 19 Ubangiji Allah shi ne ƙarfina, Ya sa ƙafafuna su zama kamar na bareyi, Ya kuma sa ni in yi tafiya a cikin maɗaukakan wurare.

Zafaniya 1

Ranar Hasalar Ubangiji a kan Yahuza

1 Ubangiji ya yi magana da Zafaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon, Sarkin Yahuza. 2 “Ni Ubangiji na ce, zan shafe dukan kome Da yake a duniya. 3 Zan shafe mutum da dabba, Zan shafe tsuntsayen sararin sama da kifayen teku, Zan kuma rushe gumakansu tare da mugaye, Zan kuma datse ɗan adam daga duniya. 4 “Zan miƙa hannuna gāba da Yahuza Da dukan mazaunan Urushalima. A wurin nan zan datse saura waɗanda suke bauta wa Ba'al, Da kuma sunayen firistocin gumaka tare da firistocina, 5 Da kuma waɗanda suke durƙusa wa rundunan sama a kan bene, Waɗanda sukan durƙusa, su rantse da Ubangiji, Duk da haka kuma sai su rantse da Milkom, 6 Da kuma waɗanda suka juya, suka bar bin Ubangiji, Waɗanda ba su neman Ubangiji, ba su kuma roƙonsa.” 7 Ku yi tsit a gaban Ubangiji Allah! Gama ranar Ubangiji ta gabato. Ubangiji ya shirya ranar shari'a, Ya kuma keɓe waɗanda za su aikata hukuncinsa. 8 “A ranar shari'a, ni Ubangiji zan hukunta shugabanni da hakimai, Da dukan waɗanda suke bin al'adun ƙasashen waje. 9 A wannan rana zan hukunta duk wanda yake tsalle a bakin ƙofa, Da waɗanda suke cika gidan maigidansu da zalunci da ha'inci. 10 “Ni Ubangiji na ce, a wannan rana, za a ji kuka a Ƙofar Kifi, Za a ji kururuwa kuma daga unguwa ta biyu, Da amon ragargajewa daga kan tuddai. 11 Ku yi kururuwa, ku mazaunan Maktesh, Gama 'yan kasuwa sun ƙare, An kuma datse dukan waɗanda suke awon azurfa. 12 “A lokacin nan, Zan bincike Urushalima da fitilu, Zan kuwa hukunta marasa kulawa Waɗanda suke zaman annashuwa, Waɗanda suke cewa a zukatansu, ‘Ubangiji ba zai yi alheri ba, Ba kuma zai yi mugunta ba!’ 13 Za a washe dukiyarsu, Za a kuwa rurrushe gidajensu, Ko da yake sun gina gidaje, ba za su zauna a ciki ba, Ko da yake sun dasa inabi, ba za su sha ruwansa ba.” 14 Babbar ranar Ubangiji ta gabato, Tana gabatowa da sauri. Ku ji muryar ranar Ubangiji! Jarumi zai yi kuka mai zafi. 15 Wannan rana ta hasala ce, Ranar azaba da wahala, Ranar lalatarwa da hallakarwa, Ranar duhu baƙi ƙirin, Ranar gizagizai da baƙin duhu, 16 Ranar busar ƙaho da yin kururuwar yaƙi Gāba da birane masu garu da hasumiyai masu tsawo. 17 “Zan aukar wa mutane da wahala, Za su kuwa yi tafiya kamar makafi, Domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura, Namansu kuwa kamar taroso.” 18 Azurfarsu da zinariyarsu ba za su cece su A ranar hasalar Ubangiji ba, A cikin zafin kishinsa Dukan duniya za ta hallaka. Zai kawo ƙarshen duniya duka nan da nan.

Zafaniya 2

Za a Hallaka Al'umman da suke Kewaye da Su

1 Ya ke al'umma marar kunya, ku tattaru, ku yi taro, 2 Kafin a zartar da umarni, Kafin a kore ku kamar ƙaiƙayi, Kafin kuma zafin fushin Ubangiji ya auko muku, Kafin ranar hasalar Ubangiji ta auko muku. 3 Ku nemi Ubangiji, Dukanku masu tawali'u na duniya, Ku waɗanda kuke bin umarninsa. Ku nemi adalci da tawali'u. Watakila za a ɓoye ku a ranar hasalar Ubangiji. 4 Za a bar Gaza ba kowa, Ashkelon za ta zama kufai, Za a kori mutanen Ashdod da tsakar rana, Ekron kuwa za a tumɓuke ta. 5 Taku ta ƙare, ku mazaunan gaɓar teku, ke al'ummar Keretiyawa! Ya Kan'ana, ƙasar Filistiyawa, Maganar Ubangiji tana gāba da ke, Za a hallaka ki har ba wanda zai ragu. 6 Gāɓar teku za ta zama makiyaya, da wurin zaman masu kiwo, Da kuma garakan tumaki. 7 Gaɓar teku za ta zama ta mutanen Yahuza waɗanda suka ragu, Wurin da za su yi kiwo. Za su kwanta da maraice a gidajen Ashkelon, Gama Ubangiji Allahnsu zai kula da su, Zai kuwa mayar musu da albarkarsu ta dā. 8 “Na ji ba'ar da Mowab ta yi, da zagin Ammonawa, Yadda suka yi wa mutanena ba'a, Sun yi alwashi, cewa za su cinye ƙasarsu. 9 Domin haka, ni Ubangiji Mai Runduna Allah na Isra'ila, Na rantse cewa, Mowab za ta zama kamar Saduma, Ammonawa kuma za su zama kamar Gwamrata. Za su zama ƙasar ƙayayuwa Da kwazazzaban gishiri marar amfani har abada. Mutanena waɗanda suka ragu za su washe su, su mallake su.” 10 Wannan shi ne hakkin girmankansu, Saboda sun raina jama'ar Ubangiji Mai Runduna, Sun yi musu alfarma. 11 Ubangiji zai tsananta musu, Zai kawo wa dukan gumakan da suke a duniya yunwa. Kowane mutum a duniya zai yi masa sujada a inda yake, Har da ƙasar sauran al'umma. 12 “Ku kuma, Habashawa, za a kashe ku da takobina.” 13 Zai miƙa hannunsa gāba da arewa, Zai hallaka Assuriya, Zai mai da Nineba busasshen kufai Marar amfani kamar hamada. 14 Tumaki za su kwanta a tsakiyarta, Da kuma kowace irin dabba ta kowace ƙasa. Mujiya da bushiya za su zauna a kan ginshiƙanta, Ga muryar kuka a taga. Ga risɓewa a bakin ƙofa, Gama za a kware rufin katakan itacen al'ul. 15 Wannan shi ne birnin da yake da harka, mai zaman lafiya, Wanda yake ce wa kansa, “Ba wani sai ni.” Ga shi, ya zama kufai, Wurin zaman dabbobi! Duk wanda ya wuce ta wurin, Zai yi tsaki, ya kaɗa kai.

Zafaniya 3

Zunubin Urushalima da Fansarta

1 Taka ta ƙare, kai mai tayarwa, Ƙazantaccen birni mai zalunci! 2 Ba ya kasa kunne ga muryar kowa, Ba ya karɓar horo. Bai dogara ga Ubangiji ba, Bai kuma kusaci Allahnsa ba. 3 Shugabanninsa zakoki ne masu ruri, Alƙalansa kuma kyarketai ne da sukan fito da maraice, Waɗanda ba su rage kome kafin wayewar gari. 4 Annabawansa sakarkari ne, maciya amana. Firistocinsa sun ƙazantar da abin da yake mai tsarki. Sun kuma keta dokoki. 5 Ubangiji wanda yake cikinsa mai adalci ne, Ba ya kuskure. Yakan nuna adalcinsa kowace safiya, Kowace safiya kuwa bai taɓa fāsawa ba. Amma mugu bai san kunya ba. 6 Ubangiji ya ce, “Na datse al'umman duniya, Hasumiyansu sun lalace. Na kuma lalatar da hanyoyinsu, Ba mai tafiya a kansu. An mai da biranensu kufai, Ba mutumin da yake zaune ciki. 7 Na ce, hakika za ka ji tsorona, Ka kuma karɓi horo. Ba za a rushe wurin zamanta ba Bisa ga hukuncin da na yi mata. Amma suka ɗokanta su lalatar da ayyukansu. 8 “Domin haka ni Ubangiji na ce, Ku jira ni zuwa ranar da zan tashi in yi tuhuma. Gama na ƙudura zan tattara al'umman duniya, da mulkoki, Don in kwarara musu hasalata Da zafin fushina, Gama zafin kishina Zai ƙone dukan duniya. 9 “Sa'an nan zan sauye harshen mutane da harshe mai tsabta, Domin dukansu su yi kira ga sunan Ubangiji, Su kuma bauta masa da zuciya ɗaya. 10 Gama daga hayin kogunan Habasha, Masu yi mini sujada, Mutanena da suke warwatse, Za su kawo mini hadaya. 11 A wannan rana ba za a kunyatar da kai ba, Saboda tayarwar da ka yi mini ta wurin ayyukanka. Gama a sa'an nan zan fitar da masu girmankai Da masu fankama daga cikinka, Ba za ka ƙara yin alfarma ba A dutsena tsattsarka. 12 Zan kuwa bar mutane masu tawali'u, Da masu ladabi a cikinka, Su kuwa za su nemi mafaka a wurin Ubangiji. 13 Waɗanda suka ragu cikin Isra'ila, Ba za su aikata mugunta ba, Ba kuma za su faɗi ƙarya ba, Gama harshen ƙarya ba zai kasance a bakinsu ba. Za su yi kiwo, su kwanta, Ba wanda zai tsorata su.”

Waƙar Murna

14 Ki raira waƙa da ƙarfi, ya ke Sihiyona! Ki ta da murya, ya Isra'ila! Ki yi murna, ki yi farin ciki, Ya ke Urushalima! 15 Ubangiji ya kawar miki da hukuncinsa, Ya kuma kori abokan gābanki. Ubangiji Sarkin Isra'ila, yana a tsakiyarki, Ba za ki ji tsoro ba. 16 A wannan rana za a ce wa Urushalima, “Kada ki ji tsoro, ke Sihiyona, Kada ki bar hannuwanki su raunana. 17 Ubangiji Allahnki yana tsakiyarki, Mayaƙi mai cin nasara ne. Zai yi murna, ya yi farin ciki da ke. Zai sabunta ki da ƙaunarsa. Zai kuma yi murna da ke ta wurin raira waƙa da ƙarfi. 18 Zan tara waɗanda suka yi makoki domin idi, Waɗanda suke tare da ke, Wato waɗanda nawayar zaman talala Ta zamar musu abin zargi. 19 Ga shi kuwa, a wannan lokaci Zan hukunta masu zaluntarki, Zan kuma ceci gurgu, Zan tattara korarru, Zan mai da kunyarsu ta zama yabo, Za su yi suna a duniya duka. 20 A wannan lokaci zan komo da ku gida, In tattara ku wuri ɗaya. Zan sa ku yi suna, Ku sami yabo a wurin mutanen duniya duka, A sa'ad da na mayar muku da arzikinku, Ni Ubangiji na faɗa.”

Haggai 1

An Zuga Mutane su Gina Haikali

1 A rana ta fari ga watan shida a shekara ta biyu ta sarautar sarki Dariyus, Ubangiji ya yi magana da annabi Haggai, cewa ya yi magana da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, mai mulkin Yahuza, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. 2 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Mutanen nan suna cewa lokaci bai yi ba tukuna da za a sāke gina Haikalin Ubangiji.” 3 Ubangiji kuwa ya yi magana da annabi Haggai ya ce, 4 “Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi wa rufin katako, amma Haikalin nan yana zaman kufai? 5 Yanzu, ni Ubangiji Mai Runduna na ce, ku lura da al'amuranku! 6 Kun yi shuka da yawa, kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha ruwa, amma bai kashe muku ƙishi ba. Kun sa tufafi, amma ba wanda ya ji ɗumi. Wanda yake karɓar albashi kuwa, sai ka ce yana sawa a huɗajjen aljihu.” 7 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Ku lura da al'amuranku! 8 Ku haura zuwa kan tuddai, ku kawo itace don ku gina Haikalina, in ji daɗinsa, a kuma ɗaukaka ni. 9 “Kun sa zuciya za ku sami da yawa, sai kuka sami kaɗan. Sa'ad da kuma kuka kawo shi gida, sai na hurar da shi. Me ya sa haka? Saboda Haikalina da yake zaman kufai, amma ko wannenku yana fama da ginin gidansa. 10 Domin haka sama ta ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani. 11 Na kawo fari a kan ƙasa, da kan tuddai, da kan hatsi, da kan 'ya'yan inabi, da kan 'ya'yan zaitun, da kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da kan mutane, da kan dabbobi, da kan ayyukansu.” 12 Zarubabel ɗan Sheyaltiyel kuwa, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da dukan sauran mutane, suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu, suka kuma yi biyayya da maganar annabi Haggai, kamar yadda Ubangiji Allahnsu ya faɗa masa. Mutane kuwa suka yi tsoron Ubangiji. 13 Sai Haggai, manzon Ubangiji, ya faɗa wa mutane maganar Ubangiji, ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Ni Ubangiji ina tare da ku.’ ” 14 Ubangiji kuwa ya zuga zuciyar Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, mai mulkin Yahuza, da zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da zuciyar dukan sauran mutane. Suka zo, suka fara aikin Haikalin Ubangiji Allahnsu Mai Runduna 15 a ranar ashirin da huɗu ga watan shida a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus.

Haggai 2

Darajar Sabon Haikalin

1 A rana ta ashirin da ɗaya ga watan bakwai sai Ubangiji ya yi magana da annabi Haggai ya ce, 2 “Ka yi magana da Zarubabel ɗan Sheyaltiyel, mai mulkin Yahuza, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da dukan sauran mutane, ka ce, 3 ‘Wa ya ragu a cikinku da ya ga wannan Haikali da darajarsa ta dā? Ƙaƙa kuke ganinsa yanzu? A ganinku ba a bakin kome yake ba? 4 Duk da haka yanzu sai ku yi ƙarfin hali, kai Zarubabel, da kai Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da dukanku mutanen ƙasar, ku kama aikin, gama ina tare da ku. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 5 Na yi muku alkawari a sa'ad da kuka fito daga Masar, cewa Ruhuna zai zauna tare da ku, haka yake yanzu, kada ku ji tsoro!’ 6 “Ni Ubangiji Mai Runduna, ina cewa ba da jimawa ba, zan girgiza sammai, da duniya, da teku, da sandararriya ƙasa. 7 Zan kuma girgiza al'umman duniya duka don dukiyar al'umman duniya ta samu. Zan kuwa cika Haikalin nan da daraja. 8 Azurfa tawa ce, zinariya kuma tawa ce. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 9 Darajar Haikalin nan ta nan gaba za ta fi ta dā. A wannan wuri zan ba da salama. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

An Tsauta wa Mutane saboda Rashin Amincinsu

10 A rana ta ashirin da huɗu ga watan tara a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus, Ubangiji kuma ya yi magana da annabi Haggai ya ce, 11 “Ka tambayi firistoci a kan wannan doka. 12 ‘Idan mutum yana riƙe da nama tsattsarka a rigarsa, idan rigar ta taɓa gurasa, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin ya tsarkaka?’ ” Sai firistocin suka amsa suka ce, “A'a.” 13 Sai kuma Haggai ya ce, “Idan wanda ya ƙazantu ta wurin taɓa gawa, ya taɓa ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa, wannan zai sa abin ya ƙazantu?” Sai firistoci suka ce, “Wannan zai sa abin ya ƙazantu!” 14 Sai Haggai ya ce, “Ubangiji ya ce, ‘Haka yake da wannan jama'a da wannan al'umma da suke gabana da kowane irin aikinsu. Abin da suke miƙawa kuma marar tsarki ne. 15 “ ‘Ina roƙonku, ku tuna a ran nan tun kafin a ɗora dutse a kan dutse na gina Haikalin Ubangiji, yaya kuke? 16 A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai ya iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don ya ɗebo mudu hamsin, sai ya tarar da mudu ashirin kawai. 17 Na aukar muku da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara a kan amfanin gonakinku, duk da haka ba ku komo wurina ba, ni Ubangiji na faɗa. 18 Yanzu ku tuna a ran nan, wato rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, tun daga ranar da aka aza harsashin ginin Haikalin Ubangiji. 19 Ba sauran iri a rumbu. Kurangar inabi kuma, da itacen ɓaure, da rumman, da itacen zaitun ba su ba da amfani ba tukuna. Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’ ”

Ubangiji ya yi wa Zarubabel Alkawari

20 Ubangiji kuma ya yi magana da Haggai a rana ta ashirin da huɗu ga watan, ya ce, 21 “Ka faɗa wa Zarubabel, mai mulkin Yahuza cewa, ‘Ina cikin shirin girgiza sammai da duniya. 22 Zan kuma hamɓare gadon sarautan daula, in kuma karya ƙarfin daular al'umman. Zan kuma hallaka karusai da mahayansu. Sojojin dawakai kuma za su kashe junansu da takuba. 23 A wannan rana, ni Ubangiji Mai Runduna, zan ɗauke ka, kai Zarubabel, bawana ɗan Sheyaltiyel, in maishe ka kamar zobe mai hatimi, gama na zaɓe ka, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.’ ”

Zakariya 1

Ubangiji ya Kira Mutanensa su Komo gare Shi

1 A watan takwas a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus, Ubangiji ya yi magana da annabi Zakariya, ɗan Berekiya, ɗan Iddo, ya ce, 2 “Ubangiji ya yi fushi da kakanninku. 3 Domin haka sai ka ce musu, Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Ku komo wurina, ni kuma zan komo wurinku, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.’ 4 Kada ku zama kamar kakanninku, waɗanda annabawa na dā suka yi ta yi musu shela suna cewa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, ku bar mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku.’ Amma ba su ji ba, ba su kuwa kula ba, ni Ubangiji na faɗa. 5 To, ina kakannin nan naku suke? Annabawan fa? Suna da rai har wa yau? 6 Amma maganata da dokokina waɗanda na umarta wa bayina annabawa, sun tabbata a kan kakanninku, sai suka tuba, suka ce, ‘Kamar yadda Ubangiji Mai Runduna ya yi niyya ya yi da mu saboda hanyoyinmu da ayyukanmu, haka kuwa ya yi da mu.’ ”

Wahayin Dawakai da Zakariya ya Gani

7 A rana ta ashirin da huɗu ga watan goma sha ɗaya, wato watan Shebat, a shekara ta biyu ta sarautar Dariyus, Ubangiji ya kuma yi magana da annabi Zakariya, ɗan Berekiya, ɗan Iddo. 8 Da dare, na ga mutum yana kan aharashin doki, yana tsaye a cikin itatuwan ci-zaƙi, a kwari. A bayansa kuma ga wani aharashin doki, da bidi, da kili. 9 Sai na ce, “Mene ne waɗannan, ya Ubangiji?” Mala'ikan da ya yi magana da ni ya ce, “Zan bayyana maka ma'anarsu.” 10 Sai mutumin da yake tsaye a cikin itatuwan ci-zaƙin ya amsa ya ce, “Waɗannan su ne Ubangiji ya aike su su yi tsaron duniya, suna kai da kawowa.” 11 Sai suka ce wa mala'ikan Ubangiji wanda yake tsaye a cikin itatuwan ci-zaƙin, “Mun yi ta kai da kawowa a duniya, sai muku ga duniya duka tana zaman lafiya.” 12 Sa'an nan mala'ikan Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Mai Runduna, har yaushe za ka ƙi nuna jinƙai ga Urushalima da biranen Yahuza, waɗanda kake jin haushinsu shekara saba'in ke nan?” 13 Sai Ubangiji ya amsa wa mala'ikan da yake magana da ni da magana ta alheri da ta ta'azantarwa. 14 Mala'ikan kuma da yake magana da ni ya ce, in yi shela in ce, “Ubangiji Mai Runduna ya ce yana jin ƙishin Urushalima da Sihiyona ƙwarai. 15 Yana fushi ƙwarai da al'umman duniya da suke zaman lafiya, gama ya yi ɗan fushi da mutanena, amma su suka yi musu hukuncin da ya zarce. 16 Saboda haka shi Ubangiji zai koma ya ji juyayin Urushalima. Za a gina Haikalinsa a cikinta, zai kuma auna Urushalima da ma'auni.” 17 Ya ce, in kuma yi shela, in ce, “Ubangiji Mai Runduna ya ce wadata za ta sake bunƙasa cikin biranensa, zai kuma ta'azantar da Sihiyona, ya kuma zaɓi Urushalima.”

Wahayin Ƙahoni da Maƙera da Zakariya ya Gani

18 Da na ɗaga idona, sai na ga ƙahoni huɗu. 19 Sai na ce wa mala'ikan da ya yi magana da ni, “Mene ne waɗannan?” Shi kuwa ya ce mini, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka warwatsa Yahuza, da Isra'ila, da Urushalima.” 20 Sa'an nan kuma Ubangiji ya nuna mini waɗansu maƙera, su huɗu. 21 Sai na ce, “Me waɗannan suke zuwa su yi?” Sai ya ce, “Waɗannan su ne ƙahonin da suka warwatsa Yahuza don kada mutum ya ɗaga kansa. Waɗannan kuwa sun zo don su tsorata su, su karya ƙahonin al'umman duniya waɗanda suka ɗaga ƙahoninsu gāba da ƙasar Yahuza don su warwatsa ta.”

Zakariya 2

Wahayin Mutum da Igiyar Awo da Zakariya ya Gani

1 Da na ɗaga idona, sai ga wani mutum yana riƙe da igiyar awo. 2 Sai na ce, “Ina za ka?” Ya ce mini, “Zan tafi in auna Urushalima don in san fāɗinta da tsawonta.” 3 Sai ga mala'ikan da yake magana da ni, ya fita, sai wani mala'ika kuma ya zo ya sadu da shi. 4 Ya ce masa, “Ka yi gudu, ka faɗa wa saurayin can, cewa za a zauna a Urushalima kamar a ƙauyuka marasa garu, saboda yawan mutane da dabbobi da suke cikinta. 5 Gama zan zama mata garu na wuta kewaye da ita, zan zama daraja a tsakiyarta, in ji Ubangiji.”

An Kirawo 'Yan Bautar Talala

6 Ubangiji ya ce, “Yanzu ku gudu daga ƙasar arewa, gama na warwatsa ku a waje kamar iska ta kusurwoyi huɗu na duniya! 7 Ya ke Sihiyona, ku tsere, ku waɗanda kuke zaune a Babila.” 8 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Bayan ɗaukaka ya aike ni zuwa wurin al'umman duniyar nan da suka washe ku, gama wanda ya taɓe ku, ya taɓi ƙwayar idona. 9 Ga shi, zan nuna ikona a kansu, za su kuwa zama abin waso ga waɗanda suka bauta musu. Sa'an nan za ku sani Ubangiji Mai Runduna ya aike ni. 10 “Ki raira waƙa, ki yi farin ciki, ya Sihiyona, gama ina zuwa, in zauna a tsakiyarki! Ni Ubangiji na faɗa. 11 “A wannan rana al'umman duniya da yawa za su haɗa kai da Ubangiji, za su kuwa zama jama'ata, ni kuma zan zauna a tsakiyarki. Za ki sani Ubangiji Mai Runduna ya aike ni gare ki. 12 Yahuza za ta zama abin mallakar Ubangiji a cikin tsattsarkar ƙasar. Zai kuma zaɓi Urushalima.” 13 Bari dukan 'yan adam su yi tsit a gaban Ubangiji, gama ya taso daga wurin zamansa mai tsarki.

Zakariya 3

Wahayin Yoshuwa Babban Firist da Zakariya ya Gani

1 Ubangiji ya nuna mini Yoshuwa, babban firist, yana tsaye a gaban mala'ikan Ubangiji. Shaiɗan kuma yana tsaye dama da mala'ikan, yana saran Yoshuwa. 2 Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsauta maka, kai Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima ya tsauta maka. Ai, wannan mutum kamar itace ne wanda aka fizge daga cikin wuta.” 3 Yoshuwa dai yana tsaye a gaban mala'ikan saye da riguna masu dauɗa. 4 Mala'ikan kuwa ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku tuɓe masa rigunan nan masu dauɗa.” Sa'an nan ya ce wa Yoshuwa, “Ga shi, na kawar maka da laifinka, zan sa maka riguna masu daraja.” 5 Sai ni kuma na ce, “Bari kuma su naɗa masa rawani mai tsabta.” Suka kuwa naɗa masa rawani mai tsabta, suka kuma sa masa riguna sa'ad da mala'ikan Ubangiji yana nan a tsaye. 6 Sa'an nan mala'ikan Ubangiji ya gargaɗi Yoshuwa, ya ce, 7 “Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Idan ka yi tafiya a hanyata, ka kuma kiyaye umarnina, zan sa ka zama shugaban Haikalina, ka lura da shirayina, zan kuma sa ka sami damar zuwa wurin waɗannan da suke tsaye. 8 Ka ji, ya Yoshuwa, babban firist, kai da abokanka da suke zaune gabanka, ku alama ce mai kyau. Ga shi, zan kawo bawana mai suna Reshe. 9 Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, a kan dutsen da na kafa a gaban Yoshuwa, dutse mai ido bakwai zan yi rubutu, zan kawar da laifin al'umman nan rana ɗaya. 10 A wannan rana kowane ɗayanku zai gayyaci maƙwabcinsa zuwa gindin kurangar inabinsa da itacen ɓaurensa.’ ”

Zakariya 4

Wahayin Alkuki da Itatuwan Zaitun da Zakariya ya Gani

1 Mala'ikan da yake magana da ni ya komo ya farkar da ni kamar yadda akan farkar da mutum daga barci. 2 Sa'an nan ya ce mini, “Me ka gani?” Sai na ce, “Na ga alkuki wanda aka yi da zinariya tsantsa, da kwano a kansa, da fitilu bakwai a kansa, da butoci bakwai a kan kowace fitilar da take bisa alkukin. 3 Akwai itatuwan zaitun biyu kusa da alkukin, ɗaya a wajen dama da kwano, ɗaya kuma a wajen hagun.” 4 Sai ni kuma na ce wa mala'ikan da yake magana da ni, “Mene ne waɗannan, ya ubangijina?” 5 Sa'an nan mala'ikan da yake magana da ni ya ce, “Ba ka san abubuwan nan ba?” Na ce, “A'a, ubangijina.” 6 Sa'an nan ya ce, “Wannan ita ce maganar Ubangiji zuwa ga Zarubabel cewa, ‘Ba da ƙarfi, ko iko ba, amma da Ruhuna,’ in ji Ubangiji Mai Runduna. 7 ‘Mene ne kai, ya babban dutse? Za ka zama fili a gaban Zarubabel, zai kuwa kwaso duwatsun da suke a ƙwanƙoli da sowa, yana cewa alheri, alheri ne ya kawo haka.’ ” 8 Ubangiji kuma ya yi magana da ni ya ce, 9 “Zarubabel ne ya ɗora harsashin ginin Haikalin nan da hannunsa, shi ne kuma zai gama ginin da hannunsa. Sa'an nan za ka sani Ubangiji Mai Runduna ya aike ni zuwa gare ka. 10 Gama wane ne ya taɓa raina ranar ƙananan abubuwa? Amma za su yi murna da ganin igiyar awo a hannun Zarubabel. Waɗannan fitilu bakwai su ne alama Ubangiji yana kai da kawowa a duniya.” 11 Na ce masa, “Mece ce ma'anar waɗannan itatuwan zaitun da suke wajen dama da hagun alkukin?” 12 Na kuma sāke tambayarsa na ce, “Mece ce ma'anar waɗannan rassan itatuwan zaitun, waɗanda suke kusa da bututu biyu na zinariya, inda mai yake fitowa?” 13 Sai ya ce mini, “Ba ka san ma'anar waɗannan ba?” Na ce, “A'a, ubangijina.” 14 Sa'an nan ya ce, “Waɗannan su ne keɓaɓɓu biyu waɗanda suke tsaye kusa da Ubangijin dukan duniya.”

Zakariya 5

Wahayin Littafi na Tashi Sama

1 Da na ɗaga idona sama kuma, sai na ga littafi mai tashi a sama. 2 Sai mala'ikan ya tambaye ni ya ce, “Me ka gani?” Na amsa, “Na ga littafi mai tashi a sama, tsawonsa kamu ashirin ne, fāɗinsa kuma kamu goma.” 3 Sa'an nan ya ce mini, “Wannan la'ana ce wadda take tashi bisa ƙasa duka. Gama za ta datse ɓarawo da mai rantsuwa da ƙarya. 4 Ubangiji Mai Runduna ya ce, ‘Zan aika da littafin a gidan ɓarawo da gidan mai rantsuwa da sunana a kan ƙarya. Littafin zai zauna a gidansa, ya ƙone gidan, da katakan, da duwatsun.’ ”

Wahayin Mace a cikin Kwando

5 Sa'an nan mala'ikan da yake magana da ni ya matso, ya ce mini, “Ka ɗaga idonka, ka ga abin nan da yake fitowa.” 6 Ni kuwa na ce masa, “Mene ne wannan?” Ya ce, “Wannan babban kwando ne wanda ya fita.” Ya kuma ce, “Wannan mugunta ce a dukan ƙasar.” 7 Da aka ɗaga murfin kwando na darma, sai ga mace tana zaune a cikin kwandon! 8 Sai ya ce, “Wannan mugunta ce.” Sa'an nan ya tura ta cikin kwandon, ya rufe bakin kwandon da murfi na darma mai nauyi. 9 Da na ɗaga idona, sai na ga mata biyu suna matsowa. Iska tana hura fikafikansu, gama suna da fikafikai kamar na shamuwa. Suka ɗaga kwandon sama. 10 Sai na tambayi mala'ikan da yake magana da ni, na ce, “Ina za su kai kwandon?” 11 Ya ce mini, “Za su tafi da shi ƙasar Shinar don su gina masa haikali, sa'ad da suka gama ginin, za su ajiye shi a ciki.”

Zakariya 6

Wahayin Karusai Huɗu

1 Na kuma ɗaga idona, sai na ga karusa huɗu suna fitowa daga tsakanin duwatsu biyu. Duwatsun kuwa na tagulla ne. 2 Dawakai aharasai ne suke jan karusa ta fari, ta biyu kuwa akawalai ne suke janta. 3 Na uku kuma dawakai kiliyai ne suke janta, ta huɗu kuwa hurde ne ke janta. 4 Sa'an nan na ce wa mala'ikan da yake magana da ni, “Mene ne waɗannan, ya ubangijina?” 5 Ya ce mini, “Waɗannan su ne ruhohi huɗu waɗanda suka fito daga sama bayan da sun nuna kansu a gaban Ubangijin duniya duka. 6 Karusar da akawalai suke ja, za ta tafi ƙasar arewa, wadda kuma dawakai kiliyai suke ja, za ta bi su. Wadda kuwa hurde take ja, za ta tafi ƙasar kudu.” 7 Sa'ad da ingarmun suka fita, sai suka ƙagauta su zagaya duniya don su bincike ta. Ya ce musu kuwa, “Ku tafi, ku bincike duniya, kuna kai da kawowa.” Har kuwa suka yi. 8 Ya kuma kira ni, ya ce, “Duba, waɗanda suka tafi ƙasar arewa sun sa fushin Ubangiji ya huce.”

Kwatancin Naɗawar Yoshuwa

9 Ubangiji ya yi magana da ni, ya ce, 10 “Ka karɓi sadaka daga Heldai, da Tobiya, da Yedaiya waɗanda suka komo daga bautar talala a Babila. A ranar kuma ka tafi gidan Yosiya ɗan Zafaniya. 11 Ka karɓi azurfa da zinariya a wurinsu, ka ƙera kambi, ka sa shi a kan Yoshuwa, ɗan Yehozadak, babban firist. 12 Ka kuwa ce masa, ‘Ubangiji Mai Runduna ya ce, mutumin da sunansa Reshe, zai yi girma a inda yake, zai kuma gina Haikalin Ubangiji. 13 Shi ne zai gina Haikalin Ubangiji, ya kuma sami girma, ya yi mulki kamar sarki, ya kuma zama firist. Kome kuwa zai tafi daidai.’ 14 Kambin zai kasance a Haikalin Ubangiji don tunawa da Heldai, da Tobiya, da Yedaiya, da Yosiya ɗan Zafaniya. 15 “Waɗanda suke nesa za su zo su gina Haikalin Ubangiji. Za ku kuwa sani Ubangiji Mai Runduna ya aiko ni wurinku. Wannan zai faru idan kun yi biyayya sosai da muryar Ubangiji Allahnku.”

Zakariya 7

An La'anci Azumi na Rashin Gaskiya

1 A rana ta huɗu ga watan tara, wato watan Kisle, a shekara ta huɗu ta sarautar sarki Dariyus, Ubangiji ya yi magana da Zakariya. 2 Sai mutanen Betel suka aiki Sharezer da Regem-melek da mutanensu su nemi tagomashi a wurin Ubangiji, 3 su kuma tambayi firistocin Haikalin Ubangiji da annabawa, cewa ko ya kamata su yi baƙin ciki da azumi a watan biyar kamar yadda suka saba yi a shekarun baya? 4 Sa'an nan Ubangiji Mai Runduna ya yi mini magana, ya ce, 5 in faɗa wa dukan mutanen ƙasar da firistoci, in ce, “Sa'ad da kuka yi azumi da baƙin ciki a watan biyar da na bakwai dukan shekarun nan saba'in, saboda ni ne kuka yi azumin? 6 Sa'ad da kuma kuke ci, kuna sha, ba don kanku ne kuke ci, kuke sha ba?” 7 Maganar ke nan da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabawan dā, a lokacin akwai mutane da arziki cikin Urushalima da garuruwa kewaye da ita, a lokacin kuma akwai mutane a Negeb da gindin tuddai.

Rashin Biyayya ne ya Jawo Bautar Talala

8 Ubangiji kuma ya yi magana da Zakariya, ya ce, 9 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce ku yi shari'ar gaskiya, bari kowa ya nuna alheri da jinƙai ga ɗan'uwansa. 10 Kada kuma ku zalunci gwauruwa, wato wadda mijinta ya rasu, da maraya, da baƙo, da matalauci, kada kuma waninku ya shirya wa ɗan'uwansa mugunta a zuciyarsa. 11 “Amma suka ƙi ji, suka ba da baya, suka toshe kunnuwansu don kada su ji. 12 Suka taurare zuciyarsu kamar dutse don kada su ji dokoki da maganar da ni Ubangiji Mai Runduna na aiko ta wurin Ruhuna zuwa ga annabawa na dā. Domin haka ni Ubangiji Mai Runduna na aukar musu da hasala mai zafi. 13 Kamar yadda na yi kira suka ƙi ji, haka kuma suka yi kira, ni ma na ƙi ji. 14 Na sa guguwa ta warwatsa su a cikin al'ummai da ba su san su ba. Ƙasar da suka bari ta zama kango, ba mai kai da kawowa a cikinta. Ƙasa mai kyau ta zama kango.”

Zakariya 8

Ubangiji zai Sāke Rayar da Urushalima

1 Ubangiji Mai Runduna kuma ya yi magana da ni, ya ce, 2 “Ni Ubangiji Mai Runduna ina kishin Sihiyona ƙwarai. 3 Zan koma wurin Sihiyona, in zauna a tsakiyar Urushalima. Za a ce da Urushalima birnin gaskiya, da kuma dutsen Ubangiji Mai Runduna, tsattsarkan dutse. 4 Tsofaffi, mata, da maza, za su zauna a titunan Urushalima, kowa yana tokare da sanda saboda tsufa. 5 Samari da 'yan mata zan sa su cika titunan Urushalima, suna wasa. 6 “Idan abin nan ya zama mawuyaci ga sauran jama'a a kwanakin nan, zai zama mawuyacin abu ne a gare ni? 7 Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, zan ceci mutanena daga ƙasar gabas da ƙasar yamma. 8 Zan kawo su su zauna a Urushalima. Za su zama jama'ata, ni kuma zan zama Allahnsu da gaskiya da adalci. 9 “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, ku himmantu, ku da kuke jin magana ta bakin annabawa a waɗannan kwanaki tun lokacin da aka ɗora harsashin ginin Haikalin Ubangiji Mai Runduna, don a gina Haikalin. 10 Gama kafin waɗannan kwanaki, mutum da dabba ba su da abin yi. Ba kuma zaman lafiya ga mai fita da shiga saboda maƙiya, gama na sa kowane mutum ya ƙi ɗan'uwansa. 11 Amma yanzu ba zan yi da sauran jama'ar nan kamar yadda na yi a kwanakin dā ba, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 12 Gama za a yi shuka da salama. Kurangar inabi za ta yi 'ya'ya, ƙasa kuma za ta ba da amfani, za a yi isasshen ruwan sama. Ni kuwa zan sa sauran jama'ar nan su ci moriyar abubuwan nan duka. 13 Ya jama'ar Yahuza da jama'ar Isra'ila, kamar yadda kuka zama abin la'antarwa a cikin al'ummai, haka kuma zan cece ku, ku zama masu albarka, kada ku ji tsoro, amma ku himmantu. 14 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce, kamar yadda na ƙudura in aukar muku da masifa, ban kuwa fasa ba, lokacin da kakanninku suka tsokane ni, suka sa na yi fushi. 15 Haka kuma na ƙudura a waɗannan kwanaki in yi wa Urushalima da jama'ar Yahuza alheri. Kada ku ji tsoro! 16 Abubuwan da za ku yi ke nan, ku faɗa wa juna gaskiya, ku yi shari'a ta gaskiya a majalisunku, domin zaman lafiya. 17 Kada ku ƙulla wa junanku sharri, kada kuma ku so yin rantsuwa ta ƙarya, gama ina ƙin waɗannan abubuwa duka, ni Ubangiji na faɗa.” 18 Ubangiji Mai Runduna ya yi magana da ni, ya ce, 19 “Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, azumi na watan huɗu, da na watan biyar, da na watan bakwai, da na watan goma, za su zama lokatan murna, da farin ciki, da idodin farin ciki, ga jama'ar Yahuza, saboda haka sai ku ƙaunaci gaskiya da salama. 20 “Mutanen birane da yawa za su hallara. 21 Mutanen wani birni za su tafi wurin mutanen wani birni, su ce musu, ‘Za mu tafi mu roƙi alherin Ubangiji, mu kuma nemi Ubangiji Mai Runduna. Ku zo mu tafi.’ 22 Jama'a da yawa da al'ummai masu iko za su zo Urushalima su nemi Ubangiji Mai Runduna, su kuma roƙi alherin Ubangiji. 23 Ni Ubangiji Mai Runduna na ce, a waɗannan kwanaki mutum goma daga kowace al'umma da kowane harshe za su kama kafa wurin Bayahude, su ce, ‘Ka yardar mana mu tafi tare da kai, gama mun ji Allah yana tare da ku.’ ”

Zakariya 9

Hukuncin da za a Yi wa Al'umman da suke Kewaye

1 Ubangiji ya yi magana gāba da ƙasar Hadrak, da kuma gāba da Dimashƙu. Ubangiji ne yake lura da 'yan adam duk da kabilan Isra'ila. 2 Ubangiji kuma yana gāba da Hamat wadda take kan iyaka, yana kuma gāba da Taya da Sidon ko da yake suna da hikima ƙwarai. 3 Taya ta gina wa kanta kagara, Ta kuma tara azurfa kamar ƙura, Zinariya kuma kamar sharar titi. 4 Amma Ubangiji zai washe ta, Ya zubar da dukiyarta a cikin teku, Wuta kuma za ta cinye ta. 5 Ubangiji ya ce, “Ashkelon za ta gani ta ji tsoro, Gaza kuma za ta yi makyarkyata da azaba, Haka kuma Ekron za ta fid da zuciya, Sarki zai hallaka cikin Gaza, Ashkelon za ta zama kufai. 6 Tattarmuka za su zauna a Ashdod, Zan kuma sa alfarmar Filistiya ta ƙare. 7 Zan kawar da jininsu daga bakinsu, Da kuma haramtattun abubuwa daga haƙoransu. Sauransu za su zama jama'ar Allahnmu, Za su zama kamar sarki cikin Yahuza. Mutanen Ekron za su zama kamar Yebusiyawa. 8 Zan kafa sansani kewaye da Haikalina saboda maƙiya, Don masu kai da kawowa. Ba wani azzalumi da zai ci su da yaƙi, Gama yanzu ni kaina na gani.”

Sarki Mai Zuwa

9 Ki yi murna ƙwarai, ya Sihiyona! Ta da murya ya Urushalima! Ga Sarkinki yana zuwa wurinki, Shi mai adalci ne, mai nasara, Shi kuma mai tawali'u ne, Yana bisa kan jaki, a kan aholaki. 10 Ubangiji ya ce, “Zan datse karusa daga Ifraimu, In datse ingarman yaƙi a Urushalima, Zan kuma karya bakan yaƙi. Sarkinki zai tabbatar wa al'umman duniya da salama, Mulkinsa zai zama daga teku zuwa teku, Daga Kogin Yufiretis zuwa matuƙar duniya.”

Za a Rayar da Sihiyona

11 Ubangiji ya ce, “Ke kuma, saboda jinin alkawarina da yake tsakanina da ke, Zan 'yantar da waɗanda suke cikin rami, Waɗanda aka kama daga cikinki. 12 Ku koma mafakarku, ku ɗaurarru masu sa zuciya. Gama yanzu zan sāka muku har ninki biyu. 13 Gama na tankwasa Yahuza ta zama bakana, Na kuma mai da Ifraimu ta zama kibiya, Zan yi amfani da mutanen Sihiyona kamar takobi, Su yi yaƙi da mutanen Hellas.” 14 Ubangiji kuwa zai bayyana kansa gare su, Kibiyarsa za ta fita kamar walƙiya, Ubangiji Allah zai busa ƙaho, Zai taho ta cikin guguwa daga kudu. 15 Ubangiji Mai Runduna zai tsare su, Za su tattake duwatsun majajjawa, Za su sha jini kamar ruwan inabi, Za su cika kamar tasar ruwan inabi, Kamar kuma kusurwoyin bagade. 16 A wannan rana Ubangiji Allahnsu zai cece su, Gama su jama'arsa ne, garkensa kuma, Kamar yadda lu'ulu'u yake haske a kambi, Haka za su yi haske a ƙasarsa. 17 Wane irin kyau da bansha'awa alherinsa yake! Hatsi zai sa samari su yi murna. Sabon ruwan inabi kuma zai sa 'yan mata su yi farin ciki.

Zakariya 10

Alkawarin Mai Ceto

1 Ku roƙi ruwan sama daga wurin Ubangiji a lokacin bazara, Gama Ubangiji ne yake yin gizagizan hadiri, Shi ne yake bai wa mutane yayyafi. Shi ne kuma yake ba kowane mutum tsire-tsiren saura. 2 Gama maganar shirme kan gida yake yi, Masu d�ba suna ganin wahayin ƙarya, Masu mafarkai suna faɗar ƙarya, Ta'aziyyarsu ta banza ce. Domin haka mutane suna ta yawo kamar tumaki, Suna shan wahala saboda rashin makiyayi. 3 Ubangiji ya ce, “Ina fushi ƙwarai da makiyayan, Zan kuwa hukunta shugabannin, Gama ni Ubangiji Mai Runduna za lura da garkena, Wato jama'ar Yahuza. Zan mai da su dawakaina na yaƙi. 4 Daga cikinsu za a sami mafificin dutsen gini, Daga cikinsu kuma za a sami turken alfarwa, Daga cikinsu za a sami bakan yaƙi, Daga cikinsu kuma kowane mai mulki zai fito. 5 Za su zama kamar ƙarfafan mutane cikin yaƙi, Za su tattaka maƙiyi a cikin taɓon tituna. Za su yi yaƙi, gama Ubangiji yana tare da su, Za su kunyatar da sojojin doki. 6 “Zan sa jama'ar Yahuza ta yi ƙarfi, Zan ceci jama'ar Yusufu. Zan dawo da su domin ina jin tausayinsu. Za su zama kamar waɗanda ban taɓa ƙyale su ba, Gama ni Ubangiji Allahnsu ne, Zan amsa musu. 7 Sa'an nan mutanen Ifraimu za su zama kamar ƙarfafan jarumawa, Za su yi farin ciki kamar sun sha ruwan inabi, 'Ya'yansu za su gani su yi murna, Zukatansu za su yi murna da Ubangiji. 8 “Zan yafato su in tattaro su, Gama zan fanshe su, Zan sa su su yi yawa kamar yadda suke yi a dā. 9 Ko da yake na watsar da su cikin al'ummai, Duk da haka za su riƙa tunawa da ni daga ƙasashe masu nisa. Su da 'ya'yansu za su rayu, su komo. 10 Zan dawo da su gida daga ƙasar Masar, In tattaro su daga Assuriya, Zan kawo su a ƙasar Gileyad da ta Lebanon, Har su cika, ba sauran wuri. 11 Za su bi ta cikin tekun wahala, Zan kwantar da raƙuman teku, Kogin Nilu zai ƙafe duk da zurfinsa, Za a ƙasƙantar da Assuriya, Sandan sarautar Masar zai rabu da ita. 12 Zan ƙarfafa su, Za su yi tafiya da sunansa, Ni Ubangiji na faɗa.”

Zakariya 11

1 Ki buɗe ƙofofinki, ke Lebanon, Don wuta ta cinye itatuwan al'ul naki. 2 Ka yi kuka, kai itacen kasharina, Gama itacen al'ul ya riga ya fāɗi, Itatuwa masu daraja sun lalace, Ku yi kuka, ku itatuwan oak na Bashan, Saboda an sassare itatuwan babban kurmi. 3 Ku ji kukan makiyaya, Gama an ɓata musu darajarsu. Ji rurin zakoki, Gama an lalatar da jejin Urdun.

Makiyaya Marasa Amfani

4 Ga abin da Ubangiji Allah ya faɗa, “Ka zama makiyayin garken tumakin da za a yanka. 5 Masu sayensu za su yanyanka su, ba za a kuwa hukunta su ba. Masu sayar da su kuma za su yi hamdala gare ni, su ce sun sami dukiya. Makiyayansu kuwa ba su ji tausayinsu ba. 6 “Gama ba zan ƙara jin tausayin mazaunan ƙasan nan ba, ni Ubangiji na faɗa. Ga shi, zan sa su fāɗa a hannun junansu da a hannun sarkinsu. Za su lalatar da ƙasar, ba kuwa zan cece su daga hannunsu ba.” 7 Sai na zama makiyayi na masu tumakin kore. Na kuwa ɗauko sanda biyu, na ce da ɗaya “Alheri,” ɗaya kuma na ce da shi “Haɗa Kai.” Sai na yi kiwon tumakin. 8 A wata guda na hallaka makiyayan nan uku, gama ban jure da su ba, su ma sun gaji da ni. 9 Sai na ce wa tumakin, ba zan yi kiwonsu ba, “Waɗanda za su mutu sai su mutu, waɗanda kuma za su hallaka, to, sai su hallaka. Sauran da suka ragu kuma, su yi ta cin naman junansu!” 10 Sa'an nan na ɗauki sandana, wato “Alheri,” na karya shi, alama ke nan da ta nuna na keta alkawarin da na yi wa al'ummai duka. 11 Da haka aka karya alkawarina a wannan rana. Masu tumakin kore suna tsaye suna kallon abin da na yi, sai suka gane lalle wannan maganar Ubangiji ce. 12 Sai na ce musu, “Idan kun ga daidai ne sai ku biya ni hakkina, idan kuwa ba haka ba ne, to, ku riƙe abinku!” Sai suka biya ni tsabar azurfa talatin, ladana. 13 Ubangiji kuma ya ce mini, “Ka zuba kuɗin a baitulmalin Haikali.” Sai na ɗauki kuɗin da suka kimanta shi ne tamanina, na zuba su a baitulmalin Haikalin Ubangiji. 14 Sa'an nan kuma na karya sandana na biyun mai suna “Haɗa Kai,” wato alama ke nan da ta nuna na kawar da 'yan'uwancin da yake tsakanin Yahuza da Isra'ila. 15 Ubangiji kuwa ya ce mini, “Ka sāke ɗaukar kayan aiki na makiyayi marar amfani. 16 Gama ga shi, zan sa wani makiyayi a ƙasan nan, wanda ba zai kula da masu lalacewa ba, ko waɗanda suka warwatse, ko ya warkar da gurgu, ko ya ciyar da waɗanda suka ragu, amma zai ci naman masu ƙiba, ya farfashe kofatonsu. 17 Taka ta ƙare, kai makiyayi marar amfani, Wanda yakan bar tumakin! Da ma takobi ya sari dantsensa da idonsa na dama! Da ma hannunsa ya shanye sarai, Idonsa na dama kuma ya makance!”

Zakariya 12

Za a Ceci Urushalima nan Gaba

1 Ga maganar Ubangiji game da Isra'ila. Ubangiji wanda ya shimfiɗa sammai, ya kirkiro duniya, ya kuma sa rai a cikin mutum, ya ce, 2 “Ga shi, ina gab da sa Urushalima ta zama ƙoƙon sa tangaɗi ga dukan al'ummai da suke kewaye. Yaƙin da zai kewaye Urushalima zai shafi Yahuza ita ma. 3 A ran nan zan sa Urushalima ta zama dutse mai nauyi ga dukan al'ummai. Duk wanda ya ɗaga ta zai ji wa kansa mugun rauni. Dukan al'umman duniya za su taru su kewaye ta. 4 A wannan rana zan firgita kowane doki, in sa mahayinsa ya haukace. Zan lura da mutanen Yahuza, amma zan makantar da dawakan abokan gābansu. 5 Sa'an nan iyalan Yahuza za su ce wa kansu, ‘Ubangiji Allah Maɗaukaki yana ƙarfafa mutanensa waɗanda suke zaune a Urushalima.’ 6 “A ranan nan zan sa iyalan Yahuza su zama kamar wuta a kurmi, ko kuwa a gonar da hatsi ya nuna. Za su hallaka dukan al'umman da suke kewaye da su. Amma mutanen Urushalima za su yi zamansu lami lafiya. 7 “Ubangiji zai fara ba mutanen Yahuza nasara, domin kada darajar jama'ar Dawuda da ta mazaunan Urushalima ta fi ta mutanen Yahuza. 8 A ranar, Ubangiji zai kiyaye mazaunan Urushalima, har wanda yake marar ƙarfi a cikinsu zai zama mai ƙarfi kamar Dawuda. Jama'ar Dawuda za ta zama kamar Allah, kamar mala'ikan Ubangiji a gabansu. 9 A ranar kuma zan hallaka dukan al'umman da suka zo su yi yaƙi da Urushalima. 10 “Zan cika zuriyar Dawuda da mutanen Urushalima da ruhun tausayi da na addu'a. Za su dubi wanda suka soke shi, har ya mutu. Za su yi makoki dominsa kamar waɗanda aka yi musu rasuwar ɗan farinsu. 11 A ran nan za a yi babban makoki a Urushalima kamar mutane suka yi wa Hadadrimmon a filin Magiddo. 12 Kowane iyali a ƙasar za su yi makokinsu a keɓe, iyalin gidan Dawuda kuma za su yi nasu a keɓe, matansu za su yi nasu a keɓe. Iyalin gidan Natan su ma za su yi nasu makoki a keɓe, matansu kuma a keɓe. 13 Iyalin gidan Lawi za su yi makokinsu a keɓe, matansu kuma a keɓe. Iyalin gidan mutanen Shimai za su yi makokinsu a keɓe, matansu kuma a keɓe. 14 Sauran dukan iyalan da suka ragu za su yi nasu makoki a keɓe, matansu kuma a keɓe.”

Zakariya 13

1 “A ran nan za a buɗe maɓuɓɓuga don wanke zuriyar Dawuda da mazaunan Urushalima daga zunubi da rashin tsarki. 2 A wannan rana fa, ni Ubangiji Mai Runduna, zan shafe sunayen gumaka daga ƙasar, har da ba za a ƙara tunawa da su ba. Zan kuma kawar da annabawa da mugayen aljannu. 3 Idan har yanzu wani ya ci gaba da yin annabci, sai mahaifinsa da mahaifiyarsa su ce masa, ‘Ba za ka rayu ba, gama kana faɗar ƙarya da sunan Ubangiji.’ Sa'an nan mahaifinsa da mahaifiyarsa su soke shi sa'ad da yake annabcin. 4 A wannan rana ce kowane annabi zai ji kunyar wahayinsa sa'ad da ya yi annabcin. Ba zai sa rigar gashi don ya ruɗi jama'a ba. 5 Amma zai ce, ‘Ni ba annabi ba ne, ni manomi ne, gama ƙasa abar mallakata ce tun ina yaro.’ 6 Idan wani ya tambaye shi cewa, ‘Waɗannan raunukan da suke a hannuwanka fa?’ Zai ce, ‘Ai, raunuka ne da aka yi mini a gidan abokaina.’ ”

Za a Kashe Makiyayi na Ubangiji

7 “Ka farka, ya kai takobi, ka fāɗa wa makiyayina, Ka fāɗa wa mutumin da yake kusa da ni, Ka sari makiyayin domin tumakin su watse. Zan bugi ƙanana da hannuna, Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 8 Ni Ubangiji na ce sulusi biyu na ƙasar za su hallaka, Sulusi ɗaya ne kawai zai ragu. 9 Sulusi ɗayan da ya ragu kuwa zan tura cikin wuta, Zan tace su da wuta kamar yadda akan tace azurfa, Zan gwada su kamar yadda akan gwada zinariya. Za su kira gare ni, Zan kuwa amsa musu, Zan ce, ‘Su jama'ata ne,’ Su kuma za su ce, ‘Ubangiji shi ne Allahnmu.’ ”

Zakariya 14

Urushalima da Sauran Al'umma

1 Ga ranar Ubangiji tana zuwa sa'ad da za a raba ganimar da aka ƙwace daga gare ku a kan idonku. 2 Gama zan tattara dukan al'ummai su yi yaƙi da Urushalima. Za a ci birnin, a washe gidajen. Za a yi wa mata faɗe. Za a kai rabin mutanen birnin bauta, amma za a bar sauran mutanen a cikin birnin. 3 Sa'an nan Ubangiji zai tafi ya yi yaƙi da waɗannan al'ummai kamar yadda ya yi a dā. 4 A wannan rana ƙafafunsa za su tsaya a bisa Dutsen Zaitun wanda yake wajen gabas da Urushalima. Dutsen Zaitun zai tsage biyu daga gabas zuwa yamma, ya zama babban kwari. Sashi guda na dutsen zai janye zuwa wajen kudu. Ɗaya sashin kuma zai janye zuwa wajen arewa. 5 Za ku gudu zuwa kwarin duwatsuna, gama kwarin duwatsu zai kai har Azel, kamar yadda kakanninku suka gudu a zamanin Azariya, Sarkin Yahuza, a lokacin da aka yi girgizar ƙasa. Sa'an nan Ubangiji Allahna zai zo tare da dukan tsarkakansa! 6 A wannan rana ba haske. Masu ba da haske za su dushe. 7 Ubangiji ne ya san wannan rana. Ba rana ba dare. Da maraice ma akwai haske. 8 A wannan rana ruwa mai rai zai gudano daga Urushalima. Rabinsa zai nufi tekun Gishiri, rabi kuma zai nufi Bahar Rum. Zai riƙa malalowa rani da damuna. 9 A ranar, Ubangiji zai zama Sarkin Duniya duka, zai kuma zama shi ne Ubangiji shi kaɗai, ba wani suna kuma sai nasa. 10 Ƙasa dukka za ta zama fili, daga Geba zuwa Rimmon a kudancin Urushalima. Amma Urushalima za ta kasance a kan tudu, za ta miƙe daga Ƙofar Biliyaminu, zuwa wurin da ƙofa ta fari take a dā, har zuwa Ƙofar Kusurwa, sa'an nan ta miƙe daga Hasumiyar Hananel zuwa wuraren matsewar ruwan inabin sarki. 11 Za a zauna cikin Urushalima lami lafiya, ba sauran la'ana. 12 Ga annobar da Ubangiji zai bugi dukan al'ummai da ita, wato su da suka tafi su yi yaƙi da Urushalima. Naman jikunansu zai ruɓe lokacin da suke a tsaye. Idanunsu kuma za su ruɓe cikin kwarminsu. Harsunansu za su ruɓe a bakunansu. 13 A wannan rana babbar gigicewa daga wurin Ubangiji za ta faɗo musu, har kowa zai kama hannun ɗan'uwansa, ya kai masa d�ka. 14 Mutanen Yahuza za su yi yaƙi don su kāre Urushalima. Za a kuma tattara dukan dukiyar al'umman da suke kewaye, su zinariya, da azurfa, da riguna tuli. 15 Annoba irin wannan kuma za ta faɗo wa dawakai da alfadarai, da raƙuma, da jakuna, da dukan dabbobin da suke cikin sansaninsu. 16 Sa'an nan wanda ya ragu daga cikin dukan al'umman da suka kai wa Urushalima yaƙi zai riƙa haurawa zuwa Urushalima kowace shekara, domin yi wa Ubangiji Maɗaukakin Sarkin sujada a lokacin kiyaye Idin Bukkoki. 17 Idan kuwa wata al'umma a duniya ba ta haura zuwa Urushalima domin ta yi wa Ubangiji Maɗaukakin Sarki sujada ba, ba za a yi mata ruwan sama ba. 18 Idan al'ummar Masar ba ta halarci Idin Bukkoki ba, ba za a yi mata ruwan sama ba. Ubangiji kuma zai kawo mata irin annobar da ya kawo wa al'umman da suka ƙi halartar Idin Bukkoki. 19 Wannan shi ne hukuncin da za a yi wa Masar da dukan al'umman da suka ƙi halartar Idin Bukkoki. 20 A wannan rana za a zāna waɗannan kalmomi, wato “Mai Tsarki ga Ubangiji” a kan ƙararrawar dawakai. Tukwanen da suke Haikalin Ubangiji za su zama kamar kwanonin da suke a gaban bagade. 21 Kowace tukunya da take a Urushalima da Yahuza za ta zama tsattsarka ga Ubangiji Mai Runduna domin dukan masu miƙa hadaya su ɗauka su dafa naman hadaya a cikinsu. A wannan rana ba za a ƙara samun mai ciniki a Haikalin Ubangiji Mai Runduna ba.

Malakai 1

Ubangiji yana Ƙaunar Yakubu

1 Wannan shi ne jawabin da Ubangiji ya ba Malakai ya faɗa wa jama'ar Isra'ila. 2 Ubangiji ya ce, “Ina ƙaunarku.” Amma ku kuka amsa kuka ce, “Ta yaya kake ƙaunarmu?” Ubangiji ya amsa, ya ce, “Ashe, Isuwa da Yakubu ba 'yan'uwan juna ba ne? Amma zuriyar Yakubu nake ƙauna. 3 Na ƙi Isuwa da zuriyarsa, na hallaka ƙasarsa ta kan tudu, wurin zamansa kuwa na ba namomin jeji.” 4 Edomawa, wato zuriyar Isuwa, sun ce, “An rurrushe garuruwanmu, amma za su sāke gina su.” Sa'an nan Ubangiji zai amsa, ya ce, “To, su gina mana, ai, zan sāke rurrushe su. Mutane za su ce da ƙasarsu, Ƙasar mugaye, da al'ummar da Ubangiji yake fushi da ita har abada.” 5 “Da idanunku za ku ga wannan, za ku kuwa ce, Allah mai girma ne yake a ƙasar da ba ta Isra'ila ba ce!”

Ubangiji ya Tsauta wa Firistoci

6 Ubangiji Mai Runduna ya ce wa firistoci, “Ɗa yakan girmama mahaifinsa, bara kuwa yakan girmama maigidansa. Ni Ubanku ne, me ya sa ba ku girmama ni ba? Ni kuma Maigidanku ne, me ya sa ba ku ganin darajata? Kun raina ni, duk da haka kuna tambaya cewa, ‘Ƙaƙa muka raina ka?’ 7 Yadda kuka yi ke nan. Kun miƙa haramtacciyar hadaya ta abinci a kan bagadena, sa'an nan kuna cewa, ‘Ta ƙaƙa muka raina ka?’ To, zan faɗa muku, don kun ƙazantar da bagadena. 8 Sa'ad da kuka kawo makauniyar dabba don ku miƙa mini hadaya, kuna tsammani wannan daidai ne? Ko kuwa sa'ad da kuka kawo gurguwar dabba ko marar lafiya wannan daidai ne? Ku ba mai mulkinku irin wannan ku gani. Zai yi murna? Ko za ku sami tagomashi, a wurinsa? Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.” 9 To, firistoci ku gwada, ku roƙi Allah domin ya yi mana alheri. Ai, ba zai amsa addu'arku ba, wannan kuwa laifinku ne. Ubangiji Mai Runduna ya faɗa. 10 “Da ma wani daga cikinku ya rufe ƙofofin Haikali don kada ku shiga, ku hura wuta marar amfani a bisa bagadena! Ban ji daɗinku ba. Ba zan karɓi hadayun da kuke kawo mini ba,” in ji Ubangiji Mai Runduna. 11 “Mutane daga kowaɗanne sassa na duniya za su girmama ni. Ko'ina za su ƙona mini halattacciyar hadaya, gama dukansu za su girmama ni,” in ji Ubangiji Mai Runduna. 12 “Amma ku kun raina ni da yake kuka ce bagadena ba kome ba ne, kuna raina abincin da kuke ajiyewa a kai. 13 Kuka kuma ce, ‘Mun gaji da wannan irin abu fa!’ Kuna hura mini hanci. Kukan kawo satacciyar dabba, ko gurguwa ko marar lafiya, ku yi mini hadaya da ita! Kuna tsammani zan karɓi wannan daga gare ku? 14 La'ananne ne macucin da yake da lafiyayyun dabbobi da ya alkawarta zai ba ni daga cikin garkensa ya kuwa miƙa mini hadaya ta haramtacciyar dabba. Gama ni babban Sarki ne, dukan al'ummai kuwa suna jin tsoron sunana, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”

Malakai 2

1 “Yanzu firistoci, ga umarni dominku. 2 Idan ba za ku kasa kunne ba, idan ba za ku sa a zuciyarku ku girmama sunana ba, to, zan aukar muku da la'ana, zan la'antar da albarkunku. Koyanzu ma na riga na la'antar da su domin ba ku riƙe umarnina a zuciyarku ba, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 3 Ga shi, zan tsauta wa 'ya 'yanku, in watsa kāshin dabbobin hadayunku a fuskokinku, sa'an nan zan kore ku daga gabana. 4 Ta haka za ku sani ni na ba ku wannan umarni domin alkawarin da na yi wa Lawi ya tabbata, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 5 “Alkawarin da na yi masa na rai ne da salama. Na yi masa alkawaran kuma domin ya ji tsorona, yana kuwa tsorona. Yana kuma tsoron sunana ƙwarai. 6 Koyarwar gaskiya tana cikin bakinsa, ba a sami kuskure a bakinsa ba. Ya yi tafiya tare da ni da salama da gaskiya. Ya kuwa juyo da mutane da yawa daga mugunta. 7 Gama ya kamata bakin firist ya kiyaye ilimi, wajibi ne firistoci su koyar da ilimin gaskiya na Allah, a gare su mutane za su tafi su koyi nufina, domin su manzannina ne, ni Ubangiji Mai Runduna. 8 “Amma ku firistoci kun kauce daga hanya. Kun sa mutane da yawa su karkace saboda koyarwarku. Kun keta alkawarin da na yi da ku, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 9 Saboda haka, ni ma zan sa jama'ar Isra'ila su raina ku, su ƙasƙantar da ku a gaban dukan mutane, domin ba ku kiyaye umarnina ba, sa'ad da kuke koyar da nufina, kun yi tara.”

Rashin Amincin Isra'ilawa

10 Ashe, ba dukanmu Ubanmu ɗaya ba ne? Ba Allah nan ɗaya ya halicce mu ba? To, me ya sa muke keta alkawarin da muka yi wa junanmu, muna raina alkawarin da Allah ya yi wa kakanninmu? 11 Mutanen Yahuza sun keta alkawarin da yake tsakaninsu da Allah, sun aikata mugun abu a Isra'ila, da a Urushalima. Gama sun ƙazantar da Haikalin da Ubangiji yake ƙauna, sun kuma auro matan da suke bauta wa gumaka. 12 Ubangiji zai lalatar da dukan wanda ya aikata wannan, wato wanda ya farka da wanda ya amsa, ko wanda yake kawo hadayu ga Ubangiji Mai Runduna. 13 Ga kuma abin da kuke yi. Kuna cika bagaden Ubangiji da hawaye, da kuka, da kururuwa domin ba zai ƙara karɓar hadayun da kuke kawo masa ba. 14 Kuna tambaya cewa, “Me ya sa ba ya karɓar hadayunmu?” Ai, domin ya sani ka keta alkawarin da ka yi wa matarka ta ƙuruciya ne, wadda ka ci amanarta ko da yake ita abokiyar zamanka ce, da matarka. 15 Ashe, ba kai da ita Allah ya maishe ku jiki ɗaya da ruhu ɗaya ba? Me Allah yake nufi da wannan? Yana so 'ya'yanmu su zama 'yan halal masu tsoron Allah. Domin haka ku kula fa, kada kowa ya ci amanar matarsa ta ƙuruciya. 16 “Ni Ubangiji Mai Runduna, Allah na Isra'ila, na ce ina ƙin kisan aure, ina ƙinsa sa'ad da waninku ya yi wa matarsa hakanan. Domin haka sai ku kula da kanku kada ku keta alkawari, mutum ya zama mai aminci ga matarsa.”

Ranar Hukunci ta Gabato

17 Kun gajiyar da Ubangiji Mai Runduna da maganganunku, amma kun ce, “Ƙaƙa muka gajiyar da shi?” Kuna cewa, “Ubangiji yana ganinsu, dukan masu aikata mugunta mutanen kirki ne, yana kuwa ƙaunarsu.” Kuna kuma cewa, “Ina Allah yake wanda yake shi adali ne?”

Malakai 3

1 A kan wannan ga abin da Ubangiji Mai Runduna ya amsa, ya ce, “Zan aiki manzona don ya shirya mini hanya, sa'an nan Ubangiji wanda kuke nema zai zo farat ɗaya a cikin Haikalinsa. Manzon da kuke sa zuciyar zuwansa, yana zuwa, zai yi shelar alkawarina.” 2 Amma wa zai iya jurewa da ranar zuwansa? Wa kuma zai tsira sa'ad da ya bayyana? Zai zama kamar wutar da take narka ƙarfe, kamar kuma sabulu salo. 3 Zai zo ya yi hukunci kamar wanda yake tace azurfa, ya tsarkake ta. Zai tsarkake firistoci, ya tace su kamar yadda ake yi wa azurfa da zinariya. A sa'an nan ne za su kawo wa Ubangiji hadayun da suka dace. 4 Sa'an nan kuma Ubangiji zai yarda da hadayun mutanen Yahuza da na Urushalima kamar yadda yake a zamanin dā. 5 Ubangiji Mai Runduna ya ce, “Zan zo wurinku domin in yi shari'a. Nan da nan zan tabbatar da laifin masu yin sihiri, da na mazinata, da na masu shaidar zur, da na masu zaluntar ma'aikata a kan albashinsu, da waɗanda suke ƙwarar gwauraye, wato matan da mazansu suka mutu, da marayu, da baƙi, da waɗanda ba su ganin girmana.”

Ba da Zaka

6 “Ni ne Ubangiji, ba na sākewa, domin haka ku zuriyar Yakubu, ba ku ƙāre ɗungum ba. 7 Ku kamar kakanninku kuke, kun bar bin dokokina, ba ku kiyaye su ba. Ku komo wurina, ni ma zan koma wurinku,” in ji Ubangiji Mai Runduna. “Amma kun ce, ‘Ƙaƙa za mu yi, mu koma gare ka?’ 8 Mutum zai iya zambatar Allah? Amma ku kuna zambatata, kuna kuwa cewa, ‘Ta ƙaƙa muka zambace ka?’ A wajen al'amarin zaka da hadayu, kuke zambatata. 9 Dukanku la'antattu ne gama al'ummar duka zamba take yi mini! 10 Ku kawo dukkan zaka a ɗakin ajiyata domin abinci ya samu a cikin Haikalina. Ku gwada ni, za ku gani, zan buɗe taskokin sama in zubo muku da albarka mai yawan gaske. 11 Ba zan bar ƙwari su lalatar da amfanin gonaki ba. Kurangar inabinku za ta cika da 'ya'ya, ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa. 12 Sa'an nan jama'ar dukan al'ummai za su ce ku masu farin ciki ne, gama ƙasarku za ta yi daɗin zama.”

Bambancin Adalai da Mugaye

13 “Kun faɗi mugun abu a kaina,” in ji Ubangiji, “Amma kun ce, ‘Me muka ce a kanka?’ 14 Kun ce, ‘Ba amfani a bauta wa Ubangiji. Ina amfani a kiyaye abin da ya ce, ko mu yi ƙoƙarin nuna cewa zuciyarmu ta ɓāci saboda ayyukan da muka yi wa Ubangiji Mai Runduna. 15 A ganinmu masu girmankai suna jin daɗi. Masu aikata mugunta kuwa ba arziki kaɗai suke yi ba, amma sukan jarraba Allah da mugayen ayyukansu su kuwa zauna lafiya.’ ” 16 Sa'an nan mutane waɗanda suke tsoron Ubangiji suka yi magana da junansu, Ubangiji kuwa ya kasa kunne ya ji abin da suke cewa. A gabansa aka rubuta a littafin tarihin waɗanda suke tsoron Ubangiji, suna kuwa girmama shi. 17 “Ni Ubangiji Mai Runduna, na ce, za su zama mutanena na ainihi, a ranar da na aikata. Zan ji ƙansu kamar yadda mahaifi yakan ji ƙan ɗansa wanda yake masa hidima. 18 Sa'an nan za ku ga bambanci tsakanin masu adalci da mugaye, da tsakanin mutumin da yake bauta mini da wanda ba ya bauta mini.”

The New Testament of our Lord and Saviour Jesus Christ

Matiyu 1

Asalin Yesu Almasihu

1 Littafin asalin Yesu Almasihu, ɗan Dawuda, zuriyar Ibrahim ke nan. 2 Ibraham ya haifi Ishaku, Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu ya haifi Yahuza da 'yan'uwansa, 3 Yahuza kuwa ya haifi Feresa da Zera (mahaifiyarsu Tamar ce), Feresa ya haifi Hesruna, Hesruna ya haifi Aram, 4 Aram ya haifi Amminadab, Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon, 5 Salmon ya haifi Bo'aza (mahaifiyarsa Rahab ce), Bo'aza ya haifi Obida (mahaifiyarsa Rut ce), Obida ya haifi Yesse, 6 Yesse ya haifi sarki Dawuda. Dawuda kuma ya haifi Sulemanu (wanda mahaifiyarsa dā matar Uriya ce), 7 Sulemanu ya haifi Rehobowam, Rehobowam ya haifi Abiya, Abiya ya haifi Asa, 8 Asa ya haifi Yehoshafat, Yehoshafat ya haifi Yoram, Yoram ya haifi Azariya, 9 Azariya ya haifi Yotam, Yotam ya haifi Ahaz, Ahaz ya haifi Hezekiya, 10 Hezekiya ya haifi Manassa, Manassa ya haifi Amon, Amon ya haifi Yosiya. 11 Yosiya ya haifi Yekoniya da 'yan'uwansa, wato, a lokacin da aka ɗebe su zuwa Babila. 12 Bayan an ɗebe su zuwa Babila, sai Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel, Shayeltiyel ya haifi Zarubabel, 13 Zarubabel ya haifi Abihudu, Abihudu ya haifi Eliyakim, Eliyakim ya haifi Azuro, 14 Azuro ya haifi Saduƙu, Saduƙu ya haifi Akimu, Akimu ya haifi Aliyudu, 15 Aliyudu ya haifi Ele'azara, Ele'azara ya haifi Matana, Matana ya haifi Yakubu, 16 Yakubu ya haifi Yusufu mijin Maryamu wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Almasihu. 17 Wato, dukkan zuriya daga Ibrahim zuwa kan Dawuda, zuriya goma sha huɗu ce. Daga Dawuda zuwa ga ɗebe su a kai Babila kuwa, zuriya goma sha huɗu. Daga ɗebe su zuwa Babila zuwa kan Almasihu, zuriya goma sha huɗu.

Haihuwar Yesu Almasihu

18 Ga yadda haihuwar Yesu Almasihu take. Sa'ad da Yusufu yake tashin Maryamu mahaifiyar Yesu, tun ba a ɗauke ta ba, sai aka ga tana da juna biyu daga Ruhu Mai Tsarki. 19 Yusufu mijinta kuwa da yake shi mutumin kirki ne, ba ya kuma so ya ba ta kunya a gaban jama'a, sai ya yi niyyar rabuwa da ita a asirce. 20 Amma tun yana cikin wannan tunani, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana a gare shi a mafarki, ya ce, “Yusufu ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukar Maryamu matarka, domin cikin nan nata daga Ruhu Mai Tsarki ne. 21 Za ta haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu, domin shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.” 22 An yi wannan ne duk, don a cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, 23 “Ga shi, budurwa za ta yi juna biyu, ta haifi ɗa, Za a kuma sa masa suna Immanuwel.” (Ma'anar Immanuwel kuwa itace Allah yana tare da mu.) 24 Da Yusufu ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala'ikan Ubangiji, ya ɗauki matarsa, 25 amma bai san ta ba, sai bayan da ta haifi ɗanta, ya kuma sa masa suna Yesu.

Matiyu 2

Ziyarar Masana Taurari daga Gabas

1 Sa'ad da aka haifi Yesu a Baitalami ta ƙasar Yahudiya, a zamanin sarki Hirudus, sai ga waɗansu masana taurari daga gabas suka zo Urushalima, suna cewa, 2 “Ina wanda aka haifa Sarkin Yahudawa? Domin mun ga tauraronsa a gabas, mun kuma zo mu yi masa sujada.” 3 Da sarki Hirudus ya ji haka, sai ya damu ƙwarai, haka kuma dukan mutanen Urushalima. 4 Sai ya tara dukan manyan firistoci da malaman Attaura na jama'a, ya tambaye su inda za a haifi Almasihu. 5 Sai suka ce masa, “A Baitalami ne, ta ƙasar Yahudiya, domin haka annabin ya rubuta cewa, 6 ‘Ke ma Baitalami, ta kasar Yahuza, Ko kusa ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin manyan garuruwan Yahuza ba, Domin daga cikinki za a haifi wani mai mulki, Wanda zai zama makiyayin jama'ata, Isra'ila.’ ” 7 Sai Hirudus ya kira masanan nan a asirce, ya tabbata daga bakinsu ainihin lokacin da tauraron nan ya bayyana. 8 Sa'an nan ya aike su Baitalami, ya ce, “Ku je ku binciko mini ɗan yaron nan sosai. In kun same shi, ku kawo mini labari, don ni ma in je in yi masa sujada.” 9 Su kuwa da suka ji maganar sarki, sai suka yi tafiyarsu. Ga shi kuwa, tauraron da suka gani a gabas yana tafe a gabansu, har ya zo ya tsaya bisa inda ɗan yaron nan yake. 10 Da suka ga tauraron sai suka yi matuƙar farin ciki. 11 Da suka shiga gidan kuwa, sai suka ga ɗan yaron, tare da mahaifiyarsa Maryamu, suka fāɗi gabansa suka yi masa sujada. Sa'an nan suka kwance kayansu, suka miƙa masa gaisuwa tare da zinariya, da lubban, da mur. 12 Amma da aka gargaɗe su a mafarki kada su koma wurin Hirudus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Gudu zuwa Masar

13 Da suka tashi, sai ga wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki, ya ce, “Tashi ka ɗauki ɗan yaron da mahaifiyarsa, ka gudu zuwa ƙasar Masar, ka zauna a can sai na faɗa maka, don Hirudus yana shirin binciko ɗan yaron yă hallaka shi.” 14 Yusufu kuwa ya tashi ya ɗauki ɗan yaron da mahaifiyarsa da daddare, ya tafi Masar, 15 ya zauna a can har mutuwar Hirudus. Wannan kuwa domin a cika abin da Ubangiji ya faɗa ne ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kirawo Ɗana.”

Kisan 'Yan Yara

16 Da Hirudus ya ga masanan nan sun mai da shi wawa, sai ya hasala ƙwarai, ya aika a karkashe dukan 'yan yara maza da suke Baitalami da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, gwargwadon lokacin da ya tabbatar a gun masanan nan. 17 A lokacin ne aka cika faɗar Annabi Irmiya cewa, 18 “An ji wata murya a Rama, Ta kuka da baƙin ciki mai zafi, Rahila ce take kuka saboda 'ya'yanta. Ba za ta ta'azantu ba, don ba su.”

Komowa daga Masar

19 Amma bayan mutuwar Hirudus, sai ga mala'ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusufu a mafarki a Masar, ya ce, 20 “Tashi ka ɗauki ɗan yaron da mahaifiyarsa, ka tafi ƙasar Isra'ila, don masu neman ran ɗan yaron sun mutu.” 21 Sai ya tashi, ya ɗauki ɗan yaron da mahaifiyarsa, ya zo ƙasar Isra'ila. 22 Amma da ya ji Arkilayus ya gāji ubansa Hirudus, yana mulkin ƙasar Yahudiya, sai ya ji tsoron isa can. Amma da aka yi masa gargaɗi a mafarki, sai ya ratse zuwa ƙasar Galili. 23 Sai ya je ya zauna a wani gari da ake kira Nazarat, domin a cika faɗar annabawa cewa, “Za a kira shi Banazare.”

Matiyu 3

Wa'azin Yahaya Maibaftisma

1 A wannan zamani ne Yahaya Maibaftisma ya zo, yana wa'azi a jejin Yahudiya, 2 yana cewa, “Ku tuba, domin Mulkin Sama ya kusato.” 3 Wannan shi ne wanda Annabi Ishaya ya yi maganarsa, ya ce, “Muryar mai kira a jeji yana cewa, ‘Ku shirya wa Ubangiji tafarki, Ku miƙe hanyoyinsa.’ ” 4 Yahaya kuwa yana saye da tufa ta gashin raƙumi, yana kuma ɗaure da ɗamara ta fata, abincinsa kuwa fara ce da ruwan zuma. 5 Sai mutanen Urushalima, da na dukan Yahudiya, da na duk ƙasashen bakin Kogin Urdun, suka yi ta zuwa wurinsa, 6 yana yi musu baftisma a Kogin Urdun, suna bayyana zunubansu. 7 Amma da Yahaya ya ga Farisiyawa da Sadukiyawa da yawa, sun taho domin a yi musu baftisma, sai ya ce musu, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku, ku guje wa fushin nan mai zuwa? 8 Ku yi aikin da zai nuna tubarku. 9 Kada kuwa ku ɗauka a ranku cewa, Ibrahim ne ubanku, domin ina gaya muku, Allah yana da ikon ya halitta wa Ibrahim 'ya'ya daga duwatsun nan. 10 Koyanzu ma an ɗora bakin gatari a gindin bishiya. Saboda haka duk bishiyar bata bada 'ya'ya masu kyau ba, sai a sare ta a jefa a wuta. 11 “Ni dai, da ruwa nake muku baftisma, shaidar tubarku, amma mai zuwa bayana, ya fi ni girma, wanda ko takalmansa ma ban isa in riƙe ba. Shi ne zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta. 12 Ƙwaryar shiƙarsa na hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai, ya taro alkamarsa ya sa a rumbunsa, amma ɓuntun, sai ya ƙone a wutar marar bituwa.”

An Yi wa Yesu Baftisma

13 A lokacin nan ne Yesu ya zo daga ƙasar Galili, ya je Kogin Urdun wurin Yahaya, domin ya yi masa baftisma. 14 Yahaya kuwa ya so ya hana shi, ya ce, “Ni da nake bukatar kai ka yi mini baftisma, ka zo gare ni?” 15 Amma Yesu ya amsa masa ya ce, “Bari ya zama haka a yanzu, domin haka ne ya dace mu cika dukan adalci.” Sa'an nan Yahaya ya yardar masa. 16 Da aka yi wa Yesu baftisma, nan da nan da ya fito daga ruwan, sai ga sama ta dāre, ya ga Ruhun Allah yana saukowa da kamar kurciya, har ya sauka a kansa. 17 Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai.”

Matiyu 4

Shaiɗan ya Gwada Yesu

1 Sa'an nan sai Ruhu ya kai Yesu cikin jeji, domin Iblis yă gwada shi. 2 Da ya yi azumi kwana arba'in ba dare ba rana, daga baya yunwa ta kama shi. 3 Sai Mai Gwadawar nan ya zo, ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.” 4 Amma Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da gurasa kaɗai mutum zai rayu ba, Sai dai da kowace maganar da ke fitowa daga wurin Allah.’ ” 5 Sa'an nan Iblis ya kai shi tsattsarkan birni, ya ɗora shi can kan tsororuwar Haikali, 6 ya ce masa, “In kai Ɗan Allah ne, to dira ƙasa. Don a rubuce yake cewa, ‘Zai yi wa mala'ikunsa umarni game da kai,’ da kuma ‘Za su tallafe ka, Don kada ka buga kafarka a dutse.’ ” 7 Sai Yesu ya ce masa, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’ ” 8 Har wa yau dai, sai Iblis ya kai shi kan wani dutse mai tsayi ƙwarai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da ɗaukakarsu. 9 Ya kuma ce masa, “Duk waɗannan zan ba ka in ka faɗi a gabana ka yi mini sujada.” 10 Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, kai Shaiɗan! Domin a rubuce yake cewa, ‘Kă yi wa Ubangiji Allahnka sujada, Shi kaɗai za ka bauta wa.’ ” 11 Sa'an nan Iblis ya rabu da shi. Sai ga mala'iku sun zo suna yi masa hidima.

Yesu ya Fara Hidima a Galili

12 To, da Yesu ya ji an tsare Yahaya, sai ya tashi zuwa ƙasar Galili. 13 Ya kuma bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin teku, a kan iyakar ƙasar Zabaluna da Naftali, 14 domin a cika faɗar Annabi Ishaya cewa, 15 “Ƙasar Zabaluna da ƙasar Naftali, Da bakin bahar, da hayin Kogin Urdun, Da kuma ƙasar Galili ta al'ummai, 16 Mazaunan duhu sun ga babban haske, Mazaunan bakin mutuwa da fargabarta, Haske ya keto musu.” 17 Tun daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin Mulkin Sama ya kusato.”

Yesu ya Kira Masunta Huɗu

18 Yana tafiya a bakin Tekun Galili ke nan, sai ya ga waɗansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, don su masunta ne. 19 Sai ya ce musu, “Ku bi ni, zan mai da ku masuntan mutane.” 20 Nan da nan, sai suka bar tarunsu, suka bi shi. 21 Da ya ci gaba sai ya ga waɗansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu ɗan Zabadi, da ɗan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunansu. Sai ya kira su. 22 Nan take suka bar jirgin duk da ubansu, suka bi shi.

Yesu ya yi wa Mutane Masu Yawa Hidima

23 Sai ya zazzaga duk ƙasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar Mulkin Allah, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya na mutane. 24 Ta haka ya shahara a cikin duk ƙasar Suriya. Aka kuwa kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farraɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25 Taro masu yawan gaske suka bi shi daga ƙasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da ƙasar Yahudiya, har ma daga hayin Kogin Urdun.

Matiyu 5

Wa'azi a kan Dutse

1 Da Yesu ya ga taro masu yawa sai ya hau dutse. Da ya zauna, almajiransa kuma suka zo gunsa. 2 Sai ya buɗe baki ya koya musu.

Albarku

3 “Albarka tā tabbata ga waɗanda suka san talaucinsu na ruhu, domin Mulkin Sama nasu ne. 4 “Albarka tā tabbata ga masu nadāma, domin za a sanyaya musu rai. 5 “Albarka tā tabbata ga masu tawali'u, domin za su gāji duniya. 6 “Albarka tā tabbata ga masu kwaɗaita ga adalci, domin za a biya musu muradi. 7 “Albarka tā tabbata ga majiya tausayi, domin su ma za a ji tausayinsu. 8 “Albarka tā tabbata ga masu tsarkakakkiyar zuciya, domin za su ga Allah. 9 “Albarka tā tabbata ga masu ƙulla zumunci, domin za a ce da su 'ya'yan Allah. 10 “Albarka tā tabbata ga masu shan tsanani saboda aikata adalci, domin Mulkin Sama nasu ne. 11 “Albarka tā tabbata gare ku sa'ad da mutane suka zage ku, suka tsananta muku, suka kuma ƙaga muku kowace irin mugunta, saboda ni. 12 Ku yi murna da farin ciki matuƙa, domin sakamakonku mai yawa ne a Sama, gama haka aka tsananta wa annabawan da suka riga ku.”

Gishiri da Haske

13 “Ku ne gishirin duniya. Amma in gishiri ya sāne, da me za a daɗaɗa shi? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar, mutane kuma su tattake. 14 “Ku ne hasken duniya. Ai, birnin da aka gina bisa tudu ba shi ɓoyuwa. 15 Ba a kunna fitila a rufe ta da masaki, sai dai a ɗora ta a kan maɗorinta, sa'an nan ta ba duk mutanen gida haske. 16 To, haskenku yă riƙa haskakawa haka a gaban mutane, domin su ga kyawawan ayyukanku, su kuma ɗaukaka Ubanku da yake cikin Sama.”

Koyarwar Yesu a kan Attaura

17 “Kada ku yi zaton na zo ne in shafe Attaura da koyarwar annabawa. Na zo ne ba domin in shafe su ba, sai dai domin in ciccika su. 18 Hakika ina gaya muku, kafin sararin sama da ƙasa su shuɗe, ko wasali ko ɗigo na Attaura ba za su shuɗe ba, sai an cika dukan kome. 19 Don haka duk wanda ya yar da umarni ɗaya mafi ƙanƙanta daga cikin umarnan nan, har ya koya wa mutane haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a Mulkin Sama. Duk wanda ya bi su kuwa, har ya koyar da su, za a ce da shi mai girma a Mulkin Sama. 20 Ina dai gaya muku, in adalcinku bai fi na malaman Attaura da Farisiyawa ba, ba za ku shiga Mulkin Sama ba faufau.”

Koyarwar Yesu a kan Fushi

21 “Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā, ‘Kada ka yi kisankai, kowa ya yi kisa kuwa, za a hukunta shi.’ 22 Amma ni ina gaya muku, kowa yake fushi da ɗan'uwansa ma, za a hukunta shi. Kowa ya ce da ɗan'uwansa wawa, za a kai shi gaban majalisa. Kowa kuma ya ce, ‘Kai wofi!’ Hakkinsa shiga Gidan Wuta. 23 Saboda haka, in kana cikin miƙa hadayarka a kan bagadin hadaya, a nan kuma ka tuna ɗan'uwanka yana da wata magana game da kai, 24 sai ka dakatar da hadayarka a gaban bagadin hadaya tukuna, ka je ku shirya da ɗan'uwanka, sa'an nan ka zo ka miƙa hadayarka. 25 Ka hanzarta shiryawa da mai ƙararka tun kuna tafiya gaban shari'a, don kada mai kararka ya bashe ka ga alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga dogari, a kuma jefa ka a kurkuku. 26 Hakika ina gaya maka, ba za ka fita daga nan ba, sai ka biya duk, babu sauran ko anini a kanka.”

Koyarwar Yesu a kan Zina

27 “Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’ 28 Amma ni ina gaya muku, kowa ya dubi mace duban sha'awa, ya riga ya yi zinar zuci ke nan da ita. 29 In idonka na dama yana sa ka yi laifi, to, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓinka da a jefa jikinka ɗungum a Gidan Wuta. 30 In kuma hannunka na dama, yana sa ka yi laifi, to, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓinka da a jefa jikinka ɗungum a Gidan Wuta.”

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

31 “An kuma ce, ‘Kowa ya saki matarsa, sai ya ba ta takardar saki.’ 32 Amma ni ina gaya muku, kowa ya saki matarsa, in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta hanyar zina ke nan. Wanda kuma ya auri sakakkiya, ya yi zina.”

Koyarwar Yesu a kan Rantsuwa

33 “Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutanen dā, ‘Kada ka rantse a kan ƙarya, sai dai ka cika wa'adin da ka ɗaukar wa Ubangiji.’ 34 Amma ni ina gaya muku, kada ma ku rantse sam, ko da sama, domin ita ce kursiyin Allah, 35 ko da ƙasa, domin ita ce matashin ƙafarsa, ko kuma da Urushalima, domin ita ce birnin Babban Sarki. 36 Kada kuwa ka rantse da kanka, don ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya fari ko baƙi ba. 37 Abin da duk za ku faɗa ya tsaya a kan ‘I’ ko ‘A'a’ kawai. In dai ya zarce haka, to, daga Mugun ya fito.”

Koyarwar Yesu a kan Ramawa

38 “Kun dai ji an faɗa, ‘Sakayyar ido, ido ce, sakayyar haƙori kuma haƙori ce.’ 39 Amma ni ina gaya muku, kada ku ƙi a cuce ku. Amma ko wani ya mare ka a kuncin dama, to, juya masa ɗayan kuma. 40 In kuwa wani ya yi ƙararka da niyyar karɓe taguwarka, to, ka bar masa mayafinka ma. 41 In kuma wani ya tilasta maka ku yi tafiyar mil guda tare, to, ku yi tafiyar mil biyu ma. 42 Kowa ya roƙe ka, ka ba shi, mai neman rance a wurinka kuwa, kada ka hana shi.”

Ƙaunar Magabta

43 “Kun dai ji an faɗa, ‘Ka so ɗan'uwanka, ka ƙi magabcinka.’ 44 Amma ni ina gaya muku, ku ƙaunaci magabtanku, ku yi wa masu tsananta muku addu'a, 45 domin ku zama 'ya'yan Ubanku wanda yake cikin Sama. Domin yakan sa rana tasa ta fito kan mugaye da kuma nagargaru, ya kuma sako ruwan sama ga masu adalci da marasa adalci. 46 In masoyanku kawai kuke ƙauna, wace lada ce da ku? Ashe, ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba? 47 In kuwa 'yan'uwanku kaɗai kuke gayarwa, me kuka yi fiye da waɗansu? Ashe, ko al'ummai ma ba haka suke yi ba? 48 Saboda haka sai ku zama cikakku, kamar yadda Ubanku na Sama yake cikakke.”

Matiyu 6

Koyarwar Yesu a kan Ba da Sadaka

1 “Ku yi hankali kada ibadarku ta zama ta ganin ido. Domin in kun yi haka, ba za ku sami sakamako wurin Ubanku da yake a Sama ba. 2 “Wato, in za ka yi sadaka, kada ka yi kwakwazo yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma a kan hanya don dai mutane su yabe su. Gaskiya nake faɗa muku, sun sami iyakar ladarsu ke nan. 3 Amma in kana yin sadaka, kada hannunka na hagu ya san abin da hannunka na dama yake yi, 4 domin sadakarka tă zama a asirce, Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.”

Koyarwar Yesu a kan Addu'a

5 “In za ku yi addu'a, kada ku zama kamar munafukai, don sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'u da kan hanyoyi don dai mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun sami iyakar ladansu. 6 Amma in za ka yi addu'a, sai ka shiga lollokinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu'a ga Ubanka wanda yake ɓoye, Ubanka kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka. 7 “In kuwa kuna addu'a, kada ku yi ta maimaitawar banza, kamar yadda al'ummai suke yi, a zatonsu za a saurare su saboda yawan maganarsu. 8 Kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatarku tun kafin ku roƙe shi. 9 Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka, ‘Ya Ubanmu, wanda yake cikin Sama, A kiyaye sunanka da tsarki. 10 Mulkinka yă zo, A aikata nufinka a duniya kamar yadda ake yi a Sama. 11 Ka ba mu abincinmu na yau. 12 Ka gafarta mana laifofinmu, Kamar yadda mu ma muke gafarta wa waɗanda suke yi mana laifi. 13 Kada ka kai mu wurin jaraba, Amma ka cece mu daga Mugun.’ 14 Domin in kun yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku na Sama zai yafe muku. 15 In kuwa ba ku yafe wa mutane laifofinsu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku naku ba.”

Koyarwar Yesu a kan Azumi

16 “In kuma kuna yin azumi, kada ku turɓune fuska kamar munafukai, don sukan yanƙwane fuska, don dai mutane su ga suna azumi ne. Hakika, ina gaya muku, sun sami iyakar ladansu ke nan. 17 Amma in kana azumi, ka shafa mai a ka, ka kuma wanke fuska, 18 don kada mutane su ga alama kana azumi, sai dai Ubanku da yake ɓoye ya gani. Ubanku kuma da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai sāka maka.”

Tara Dukiya a Sama

19 “Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda ɓarayi kuma ke fasawa suke yi sata. 20 Sai dai ku tara wa kanku dukiya a Sama, inda ba asu da tsatsa da za su ɓata, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa su yi sata. 21 Domin kuwa inda dukiyarka take, a can zuciyarka ma take.”

Fitilar Jiki

22 “Ido shi ne fitilar jiki. In idonka lafiyayye ne, duk jikinka ma sai ya cika da haske. 23 In kuwa idonka da lahani, duk jikinka sai ya cika da duhu. To, in hasken da yake gare ka duhu ne, ina misalin yawan duhun!”

Bauta wa Allah ko Dukiya

24 “Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu; ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗaya, ko kuwa ya amince wa ɗayan, ya raina ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah da dukiya gaba ɗaya.”

Damuwa da Alhini

25 “Saboda haka ina gaya muku, kada ku damu a kan rayuwarku game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha, ko kuwa jikinku, abin da za ku yi sutura. Ashe, rai bai fi abinci ba? Jiki kuma bai fi tufafi ba? 26 Ku dubi dai tsuntsaye. Ai, ba sa shuka, ba sa girbi, ba sa kuma tarawa a rumbuna, amma kuwa Ubanku na Sama yana ci da su. Ashe, ko ba ku fi martaba nesa ba? 27 Wane ne a cikinku, don damuwarsa, zai iya ƙara ko da taƙi ga tsawon rayuwarsa? 28 To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi dai furannin jeji, yadda suke girma, ba sa aikin fari, ba sa na baƙi, 29 duk da haka ina gaya muku, ko Sulemanu ma, shi da adonsa duk, bai taɓa yin adon da ya fi na ɗayansu ba. 30 To, ga shi, Allah yana ƙawata tsire-tsiren jeji ma haka, waɗanda yau suke raye, gobe kuwa a jefa su a wuta, balle ku? Ya ku masu ƙarancin bangaskiya! 31 Don haka kada ku damu, cewa, ‘Me za mu ci?’ ko, ‘Me za mu sha?’ ko kuwa, ‘Me za mu sa?’ 32 Ai, al'ummai ma suna ta neman duk irin waɗannan abubuwa, Ubanku na Sama kuwa ya san kuna bukatarsu duka. 33 Muhimmin abu na farko, sai ku ƙwallafa rai ga al'amuran Mulkin Allah, da kuma adalcinsa, har ma za a ƙara muku dukan waɗannan abubuwa. 34 “Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe ta Allah ce. Dawainiyar yau ma ta isa, wahala.”

Matiyu 7

Kada ku Ɗora wa Kowa Laifi

1 “Kada ku ɗora wa kowa laifi, don kada a ɗora muku. 2 Don da irin hukuncin da kuka zartar, da shi za a zartar muku. Mudun da kuka auna, da shi za a auna muku. 3 Don me kake duban ɗan hakin da yake idon ɗan'uwanka, amma gungumen da yake a naka ido ba ka kula ba? 4 Ko kuwa yaya za ka iya ce wa ɗan'wanku, ‘Bari in cire maka ɗan hakin daga idonka,’ alhali kuwa da gungume naka ido? 5 Kai munafuki! Sai ka fara cire gungumen da yake idonka tukuna, sa'an nan ka gani sosai yadda za ka cire ɗan hakin daga idon ɗan'uwanka. 6 “Kada ku ba karnuka abin da yake tsattsarka. Kada kuma ku jefa wa alhanzir lu'ulu'unku, don kada su tattake su, su juyo su kyakketa ku.”

Ku Roƙa, ku Nema, ku Ƙwanƙwasa

7 “Ku yi ta roƙo, za a ba ku. Ku yi ta nema, za ku samu. Ku yi ta ƙwanƙwasawa, za a kuwa buɗe muku. 8 Duk wanda ya roƙa, akan ba shi, mai nema yana tare da samu. Wanda ya ƙwanƙwasa kuma za a buɗe masa. 9 To, wane ne a cikinku, ɗansa zai roƙe shi gurasa, ya ba shi dutse? 10 Ko kuwa ya roƙe shi kifi, ya ba shi maciji? 11 To, ku da kuke mugaye ma, kuka san yadda za ku ba 'ya'yanku kyautar kyawawan abubuwa, balle Ubanku na Sama da zai ba da abubuwan alheri ga masu roƙonsa? 12 Saboda haka duk abin da kuke so mutane su yi muku, ku ma sai ku yi musu, domin wannan shi ne Attaura da koyarwar annabawa.”

Ƙunƙuntar Ƙofa

13 “Ku shiga ta ƙunƙuntar ƙofa, gama ƙofa zuwa hallaka faffaɗa ce, hanyarta mai sauƙin bi ce, masu shiga ta cikinta suna da yawa. 14 Domin kuwa ƙofar zuwa rai ƙunƙunta ce, hanyarta mai wuyar bi ce, masu samunta kuwa kaɗan ne.”

Akan Gane Itace ta 'Ya'yansa

15 “Ku kula da annabawan ƙarya, waɗanda sukan zo muku da siffar tumaki, amma a zuci kyarketai ne masu ƙāwa. 16 Za ku gane su ta irin aikinsu. A iya ciran inabi a jikin ƙaya, ko kuwa ɓaure a jikin sarƙaƙƙiya? 17 Haka kowane itacen kirki yakan haifi kyawawan 'ya'ya. Mummunan itace kuwa yakan haifi munanan 'ya'ya. 18 Kyakkyawan itace ba dama ya haifi munanan 'ya'ya. Haka kuma mummunan itace ba dama ya haifi kyawawan 'ya'ya. 19 Duk itacen da ba ya 'ya'ya masu kyau, sai a sare shi a jefa a wuta. 20 Don haka, da irin aikinsu za a gane su.”

Ban Taɓa Saninku ba

21 “Ba duk mai ce mini, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji,’ ne zai shiga Mulkin Sama ba, sai dai wanda ya yi abin da Ubana da yake cikin Sama yake so. 22 A ranar nan da yawa za su ce mini, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji, ashe, ba mu yi annabci da sunanka ba? Ba mu fitar da aljannu da sunanka ba? Ba mu kuma yi ayyukan al'ajabi masu yawa da sunanka ba?’ 23 Sa'an nan zan ce musu, ‘Ni ban taɓa saninku ba. Ku rabu da ni, ku masu yin mugun aiki.’ ”

Kafa Harsashin Gini Iri Biyu

24 “Saboda haka, kowa da yake jin maganar nan tawa, yake kuma aikata ta, za a kwatanta shi da mutum mai hikima, wanda ya gina gidansa a kan fā. 25 Da ruwa ya sauko, koguna suka yi cikowa, iska ta taso ta bugi gidan, amma bai faɗi ba, domin an gina shi a kan fā ne. 26 Kowa ya ji maganar nan tawa, bai aikata ta kuma ba, za a misalta shi da wawan mutum, wanda ya gina gidansa a kan rairayi. 27 Da ruwa ya sauko, koguna suka yi cikowa, sai iska ta taso ta bugi gidan har ya rushe, mummunar ragargajewa kuwa!”

Hakikancewar Yesu

28 Da Yesu ya gama duk wannan magana, sai taro suka yi mamakin koyarwarsa, 29 domin yana koya musu da hakikancewa, ba kamar malamansu na Attaura ba.

Matiyu 8

Yesu ya Warkar da Kuturu

1 Da ya sauko daga dutsen, sai taro masu yawan gaske suka bi shi. 2 Sai ga wani kuturu ya zo gunsa ya yi masa sujada, ya ce, “Ya Ubangiji, in dai ka yarda, kana da iko ka tsarkake ni.” 3 Sai Yesu ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce, “Na yarda, ka tsarkaka.” Nan take kuturtarsa ta warke. 4 Sai Yesu ya ce masa, “Ka kula fa, kada ka gaya wa kowa kome. Sai dai ka je wurin firist ya gan ka, ka kuma yi sadaka domin tabbatarwa a gare su, kamar yadda Musa ya umarta.”

Yesu ya Warkar da Yaron Wani Jarumi

5 Yana shiga Kafarnahum ke nan, sai wani jarumi ya zo gunsa ya roƙe shi, 6 ya ce, “Ya Ubangiji, yarona yana kwance a gida, ya zama shanyayye, yana shan azaba ƙwarai.” 7 Yesu ya ce masa, “Zan zo in warkar da shi.” 8 Sai jarumin, ya ce, “Ya Ubangiji, ban isa har ka zo gidana ba, amma sai ka yi magana kawai, yarona kuwa zai warke. 9 Don ni ma a hannun wani nake, da kuma soja a hannuna, sai in ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai ya je, wani kuwa in ce masa, ‘Zo,’ sai ya zo, in ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai ya yi.” 10 Da Yesu ya ji haka, sai ya yi mamaki, har ya ce wa mabiyansa, “Gaskiya, ina gaya muku, ko a cikin Isra'ila ban taɓa samun bangaskiya mai ƙarfi irin wannan ba. 11 Ina kuma gaya muku, da yawa za su zo daga gabas da yamma su zauna cin abinci tare da Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu a Mulkin Sama, 12 'ya'yan Mulki kuwa sai a jefa su matsanancin duhu. Nan za su yi kuka da cizon haƙora.” 13 Sai Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka, ya zama maka gwargwadon bangaskiyar da ka yi.” Nan take yaronsa ya warke.

Yesu ya Warkar da Surukar Bitrus

14 Da Yesu ya shiga gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance da zazzaɓi. 15 Sai ya taɓa hannunta, zazzaɓin kuwa ya sake ta, ta kuma tashi ta yi masa hidima.

Yesu ya Warkar da Mutane da yawa da Maraice

16 Da maraice ya yi, sai suka kakkawo masa masu aljannu da yawa. Da magana kawai ya fitar da aljannun, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17 Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa, “Da kansa ya ɗebe rashin lafiyarmu, ya ɗauke cucecucenmu.”

Masu Cewa, za su Bi Yesu

18 To, da Yesu ya ga taro masu yawan gaske sun kewaye shi, sai ya yi umarni a koma wancan hayi. 19 Sai wani malamin Attaura ya zo ya ce masa, “Malam, zan bi ka duk inda za ka je.” 20 Yesu ya ce masa, “Yanyawa da ramummukansu, tsuntsaye kuma da sheƙunan, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin shaƙatawa.” 21 Sai ɗaya daga almajiran ya ce masa, “Ya Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne tsohona.” 22 Amma Yesu ya ce masa, “Bi ni. Bari matattu su binne 'yan'uwansu matattu.”

Yesu ya Tsawata wa Hadiri

23 Da ya shiga jirgi, almajiransa suka bi shi. 24 Sai ga wani babban hadiri ya taso a teku, har raƙuman ruwa suka fara shan kan jirgin, amma yana barci. 25 Sai almajiransa suka je suka tashe shi, suka ce, “Ya Ubangiji, ka cece mu, za mu hallaka!” 26 Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka, ya ku masu ƙarancin bangaskiya?” Sa'an nan ya tashi, ya tsawata wa iskar da ruwan. Sai wurin duk ya yi tsit! 27 Mutanen suka yi al'ajabi, suka ce, “Wane irin mutum ne wannan, wanda har iska da ruwan teku ma suke masa biyayya?”

Warkar da Masu Aljannu na Garasinawa

28 Da ya isa wancan hayi a ƙasar Garasinawa, mutum biyu masu aljannu suka fito daga makabarta suka tarye shi. Don kuwa su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bi ta wannan hanya. 29 Sai suka ƙwala ihu suka ce, “Ina ruwanka da mu, kai Ɗan Allah? Ka zo nan ne ka yi mana azaba tun kafin lokaci ya yi?” 30 Nesa kuma kaɗan akwai wani babban garken aladu suna kiwo. 31 Sai aljannun suka roƙe shi, suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.” 32 Ya ce musu, “To, ku je.” Sai suka fita, suka shiga aladun. Sai kuwa duk garken suka rugungunta ta gangaren, suka faɗa tekun, suka hallaka a ruwa. 33 Masu kiwon aladun suka gudu, suka shiga gari, suka yi ta ba da labarin kome da kome, da kuma abin da ya auku ga masu aljannun. 34 Sai ga duk jama'ar garin sun firfito su taryi Yesu. Da suka gan shi, sai suka roƙe shi ya bar musu ƙasarsu.

Matiyu 9

Yesu ya Warkar da Shanyayye

1 Da ya shiga jirgi, ya haye ya je garinsu. 2 Sai aka kawo masa wani shanyayye, kwance a gado. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, ka yi farin ciki, an gafarta maka zunubanka.” 3 Sai waɗansu malaman Attaura suka ce a ransu, “Wannan mutum, ai, saɓo yake!” 4 Yesu kuwa, da yake ya san tunaninsu, ya ce, “Don me kuke mugun tunani a zuciyarku? 5 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi ka yi tafiya?’ 6 Amma domin ku sakankance Ɗan Mutum yana da ikon gafarta zunubi a duniya”�sai ya ce wa shanyayyen�“Tashi, ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.” 7 Shi kuwa ya tashi ya tafi gida. 8 Da taron suka ga haka, sai tsoro ya kama su, suka ɗaukaka Allah, wanda ya ba mutane iko haka.

Kiran Matiyu

9 Da Yesu ya yi gaba, ya ga wani mutum mai suna Matiyu a zaune, yana aiki a wurin karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.” Sai ya tashi ya bi shi. 10 Sa'ad da kuwa Yesu yake cin abinci a gida, sai ga masu karɓar haraji da masu zunubi da yawa sun zo, sun zauna tare da shi da almajiransa. 11 Da Farisiyawa suka ga haka, sai suka ce wa almajiransa, “Don me malaminku yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?” 12 Amma da Yesu ya ji haka ya ce, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. 13 Sai ku fahimci ma'anar wannan tukuna, ‘Ni kam, zaman jinƙai nake nema a gare ku, ba hadaya ba.’ Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai dai masu zunubi.”

Tambaya a kan Azumi

14 Sai almajiran Yahaya suka zo wurinsa, suka ce, “Don me mu da Farisiyawa mukan yi azumi, amma naka almajiran ba sa yi?” 15 Sai Yesu ya ce musu, “Abokan ango sa yi baƙin ciki tun ango yana tare da su? Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa'an nan ne fa za su yi azumi. 16 Ba mai mahon tsohuwar tufa da sabon ƙyalle, don mahon zai kece tsohuwar tufar, har ma ta fi dā kecewa. 17 Ba kuma mai ɗura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ma an ɗura, sai salkunan su fashe, ruwan inabin ya zube, salkunan kuma su lalace. Sabon ruwan inabi, ai, sai sababbin salkuna. Ta haka an tserar da duka biyu ke nan.”

'Yar Shugaban Jama'a da Matar da ta Taɓa Gezar Mayafin Yesu

18 Yana cikin yi musu magana haka, sai ga wani shugaban jama'a ya zo, ya yi masa sujada, ya ce, “Yanzu yanzu 'yata ta rasu, amma ka zo ka ɗora mata hannu, za ta rayu.” 19 Sai Yesu ya tashi, ya bi shi tare da almajiransa. 20 Ga kuma wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta raɓo ta bayansa, ta taɓa gezar mayafinsa, 21 domin ta ce a ranta, “Ko da mayafinsa ma na taɓa, sai in warke.” 22 Sai Yesu ya juya, yā gan ta, ya ce, “'Yata, ki yi farin ciki, bangaskiyarki ta warkar da ke.” Nan take matar ta warke. 23 Da Yesu ya isa gidan shugaban jama'ar, ya kuma ga masu busar sarewa da taro suna ta hayaniya, 24 sai ya ce, “Ku ba da wuri, ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci take yi.” Sai suka yi masa dariyar raini. 25 Amma da aka fitar da taron waje, ya shiga ya kama hannunta, sai kuwa yarinyar ta tashi. 26 Wannan labarin kuwa ya bazu a duk ƙasar.

Makafi Biyu sun Sami Ganin Gari

27 Da Yesu ya yi gaba daga nan, sai waɗansu makafi biyu suka bi shi, suna ɗaga murya suna cewa, “Ya Ɗan Dawuda, ka yi mana jinƙai.” 28 Da ya shiga wani gida sai makafin suka zo gare shi. Yesu ya ce musu, “Kun gaskata ina da ikon yin haka?” Sai suka ce masa, “I, ya Ubangiji!” 29 Sa'an nan ya taɓa idanunsu, ya ce, “Yă zama muku gwargwadon bangaskiyarku.” 30 Sai idanunsu suka buɗe. Amma Yesu ya kwaɓe su ƙwarai, ya ce, “Kada fa kowa ya ji labarin.” 31 Amma suka tafi suka yi ta baza labarinsa a duk ƙasar.

Bebe ya Yi Magana

32 Sun tashi ke nan, sai aka kawo masa wani bebe mai aljan. 33 Bayan an fitar da aljanin, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki, suka ce, “Kai! Ba a taɓa ganin irin wannan a cikin Isra'ila ba.” 34 Amma sai Farisiyawa suka ce, “Ai, da ikon sarkin aljannu yake fitar da aljannu.”

Yesu ya Ji Tausayin Mutane

35 Sai Yesu ya zazzaga dukan garuruwa da ƙauyuka, yana koyarwa a majami'unsu, yana yin bisharar Mulkin Allah, yana kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya. 36 Amma da ya ga taro masu yawa sai ya ji tausayinsu, domin suna shan wahala, suna nan a warwatse kamar tumaki da ba makiyayi. 37 Sai ya ce wa almajiransa, “Girbin yana da yawa, amma masu yinsa kaɗan ne. 38 Saboda haka ku roƙi Ubangijin girbin ya turo masu girbi, su yi masa girbi.”

Matiyu 10

Yesu ya Zaɓi Almajirai Sha Biyu

1 Sai ya kira almajiransa goma sha biyu, ya kuma ba su ikon fitar da baƙaƙen aljannu, su warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya. 2 To, ga sunayen manzannin nan goma sha biyu. Da fari, Saminu, wanda ake kira Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, da Yakubu ɗan Zabadi, da ɗan'uwansa Yahaya, 3 da Filibus, da Bartalamawas, da Toma, da Matiyu mai karɓar haraji, da Yakubu ɗan Halfa, da Yahuza, 4 da Saminu Bakan'ane, da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bashe shi.

Yesu ya Aiki Sha Biyu Ɗin

5 Su sha biyun nan ne Yesu ya aika, ya yi musu umarni, ya ce, “Kada ku shiga ƙasar al'ummai, ko kuma kowane garin Samariyawa. 6 Sai dai ku je wurin batattun tumakin jama'ar Isra'ila, 7 kuna wa'azi, kuna cewa, ‘Mulkin Sama ya kusato.’ 8 Ku warkar da marasa lafiya, ku ta da matattu, ku tsarkake kutare, ku kuma fitar da aljannu. Kyauta kuka samu, ku kuma bayar kyauta. 9 Kada ku riƙi kuɗin zinariya, ko na azurfa, ko na tagulla a ɗamararku, 10 kada kuma ku ɗauki burgami a tafiyarku, ko taguwa biyu, ko takalma, ko sanda, don ma'aikaci ya cancanci hakkinsa. 11 Duk gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a cikinsa, ku kuma baƙunce shi har ku tashi. 12 In za ku shiga gidan ku ce, ‘Salama a gare ku.’ 13 In gidan na kirki ne, salamarku tă tabbata a gare shi. In kuwa ba na kirki ba ne, to, tă komo muku. 14 Kowa kuma ya ƙi yin na'am da ku, ko kuwa ya ƙi sauraron maganarku, da fitarku gidan ko garin, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku. 15 Hakika, ina gaya muku, a Ranar Shari'a za a fi haƙurce wa ƙasar Saduma da ta Gwamrata a kan garin nan.”

Tsanani Mai Zuwa

16 “Ga shi, na aike ku kamar tumaki a tsakiyar kyarketai. Don haka sai ku zama masu azanci kamar macizai, da kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi. 17 Ku yi hankali da mutane, don za su kai ku gaban majalisa, su kuma yi muku bulala a majami'arsu. 18 Za su kuma ja ku gaban mahukunta da sarakuna saboda ni, domin ku ba da shaida a gabansu, a gaban al'ummai kuma. 19 A lokacin da suka ba da ku, kada ku damu da yadda za ku yi magana, ko kuwa abin da za ku faɗa, domin za a ba ku abin da za ku faɗa a lokacin. 20 Domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhun Ubanku ne yake magana ta bakinku. 21 'Dan'uwa zai ba da ɗan'uwansa a kashe shi, uba kuwa ɗansa. 'Ya'ya kuma za su tayar wa iyayensu, har su sa a kashe su. 22 Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har ƙarshe, zai sami ceto. 23 In sun tsananta muku a wannan gari, ku gudu zuwa na gaba. Gaskiya, ina gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan garuruwan Isra'ila, Ɗan Mutum zai zo. 24 “Almajiri ba ya fin malaminsa, bawa kuma ba ya fin ubangijinsa. 25 Ya isa wa almajiri ya zama kamar malaminsa, bawa kuma kamar ubangijinsa. In har sun kira maigida Ba'alzabul, to, mutanen gidansa kuma fa?”

Wanda za a Ji Tsoro

26 “Don haka kada ku ji tsoronsu, domin ba abin da yake a rufe da ba zai tonu ba, ko kuwa abin da yake a ɓoye da ba za a bayyana ba. 27 Abin da nake gaya muku a asirce, ku faɗa a sarari. Abin da kuma kuka ji a raɗe, ku yi shelarsa daga kan soraye. 28 Kada ku ji tsoron masu kisan mutum, amma ba sa iya kashe kurwarsa. Sai dai ku ji tsoron wannan da yake da ikon hallaka kurwar da jikin duka a Gidan Wuta. 29 Ashe, ba gwara biyu ne kobo ba? Ba kuwa ɗayarsu da za ta mutu, ba da yardar Ubanku ba. 30 Ai, ko da gashin kanku ma duk a ƙidaye yake. 31 Kada ku ji tsoro. Ai, martabarku ta fi ta gwara masu yawa.”

Bayyana Yarda da Almasihu gaban Mutane

32 “Kowa ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da ke cikin Sama. 33 Duk wanda kuwa ya yi musun sanina a gaban mutane, ni ma zan yi musun saninsa a gaban Ubana da yake cikin Sama.”

Ban Kawo Salama ba, sai Takobi

34 “Kada dai ku zaci na zo ne in kawo salama a duniya. A'a, ban zo domin in kawo salama ba, sai dai takobi. 35 Domin na zo ne in haɗa mutum da mahaifinsa gāba, 'ya da mahaifiyarta, matar ɗa kuma da surukarta. 36 Zai zamana kuma magabtan mutum su ne mutanen gidansa. 37 Wanda duk ya fi son mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. Wanda kuma ya fi son ɗansa ko 'yarsa fiye da ni, bai cancanci zama nawa ba. 38 Wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai cancanci zama nawa ba. 39 Duk mai son adana ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, adana shi yake yi.”

Ayyukan Lada

40 “Wanda ya yi na'am da ku, ya yi na'am da ni ke nan. Wanda ya yi na'am da ni kuwa, to, ya yi na'am da wanda ya aiko ni. 41 Wanda ya yi na'am da wani annabi domin shi annabi ne, zai sami ladar annabi. Wanda kuma ya yi na'am da adali domin shi adali ne, zai sami ladar adali. 42 Kowa ya ba ɗaya daga cikin 'yan yaran nan, ko da moɗa guda ta baƙin ruwa, kan shi almajirina ne, hakika, ina gaya muku, ba zai rasa ladarsa ba.”

Matiyu 11

'Yan Saƙo daga Yahaya Maibaftisma

1 Da Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya ci gaba daga nan domin ya koyar, yă kuma yi wa'azi a garuruwansu. 2 To, da Yahaya ya ji a kurkuku labarin ayyukan Almasihu, sai ya aiki almajiransa, 3 su ce masa, “Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?” 4 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka ji, da abin da kuka gani. 5 Makafi suna samun gani, guragu suna tafiya, ana tsarkake kutare, kurame suna ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara. 6 Albarka tā tabbata ga wanda ba ya tuntuɓe sabili da ni.” 7 Sun tafi ke nan, sai Yesu ya fara yi wa taro maganar Yahaya, ya ce, “Kallon me kuka je yi a jeji? Kyauron da iska take kaɗawa? 8 To, kallon me kuka fita? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon alharini a fada suke. 9 To, don me kuka fita? Ku ga wani annabi? I, lalle kuwa, har ya fi annabi nesa. 10 Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa, ‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba, Wanda zai shirya maka hanya gabanninka.’ 11 Hakika ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya bayyana da ya fi Yahaya Maibaftisma girma. Duk da haka, wanda ya fi ƙanƙanta a Mulkin Sama ya fi shi. 12 Tun daga zamanin Yahaya Maibaftisma har ya zuwa yanzu, Mulkin Sama yana shan kutse, masu kutsawa kuwa sukan riske shi. 13 Domin dukan annabawa da Attaura sun yi annabci har ya zuwa kan Yahaya. 14 In kuma za ku karɓa, shi ne Iliya da dā ma zai zo. 15 Duk mai kunnen ji, yă ji. 16 “To, da me zan kwatanta zamanin nan? Kamar yara ne da suke zaune a kasuwa, suna kiran abokan wasansu, suna cewa, 17 ‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba, Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba!’ 18 “Ga shi, Yahaya ya zo, ya ƙi ciye-ciye da shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da iska.’ 19 Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’ Duk da haka hikimar Allah, ta aikinta ne ake tabbatar da gaskiyarta.”

Tsawata wa Garuruwan da ba su Tuba Ba

20 Sai ya fara tsawata wa garuruwan da ya yi yawancin ayyukansa na al'ajabi a cikinsu, don ba su tuba ba. 21 “Kaitonki, Korasinu! Kaitonki, Betsaida! Da mu'ujizan da aka yi a cikinku, su aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba, suna sanye da tsumma, suna hurwa da toka. 22 Amma ina gaya muku, a Ranar Shari'a, za a fi haƙurce wa Taya da Sidon a kanku. 23 Ke kuma Kafarnahum, ɗaukaka ki sama za a yi? A'a, ƙasƙantar da ke za a yi, har Hades. Da mu'ujizan da aka yi a cikinki, su aka yi a Saduma, da ta wanzu har ya zuwa yau. 24 Amma ina gaya muku, a Ranar Shari'a, za a fi haƙurce wa Saduma a kanki.”

Ku Zo gare ni, ku Huta

25 A wanna lokaci sai Yesu ya ce, “Na gode maka ya Uba, Ubangijin Sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan al'amura ga masu hikima da masu basira, ka kuma bayyana su ga jahilai. 26 Hakika na gode maka ya Uba, domin wannan shi ne nufinka na alheri. 27 Kowane abu Ubana ne ya mallakar mini. Ba kuwa wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban sai Ɗan, da kuma wanda Ɗan ya so ya bayyana wa. 28 Ku zo gare ni dukanku masu wahala, masu fama da kaya, ni kuwa zan hutasshe ku. 29 Ku shiga bautata, ku kuma koya a gare ni, domin ni mai tawali'u ne, marar girmankai, za ku kuwa sami kwanciyar rai. 30 Domin bautata sassauƙa ce, kayana kuma marar nauyi ne.”

Matiyu 12

Almajirai na Zagar Alkama Ran Asabar

1 A lokacin nan a ran Asabar, Yesu yana ratsa gonakin alkama. Almajiransa kuwa suna jin yunwa, sai suka fara zagar alkamar suna ci. 2 Amma da Farisiyawa suka ga haka, suka ce masa, “Ka ga! Almajiranka suna yin abin da bai halatta a yi ran Asabar ba.” 3 Sai ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba sa'ad da ya ji yunwa, shi da abokan tafiyarsa? 4 Yadda ya shiga Ɗakin Allah ya ci keɓaɓɓiyar gurasar nan, wadda bai halatta ya ci, ko abokan tafiyarsa ma su ci ba, sai dai firistoci kaɗai? 5 Ko kuwa ba ku taɓa karantawa a Attaura ba, yadda a ran Asabar, firistoci a Haikalin sukan keta dokar Asabar, ba tare da yin wani laifi ba kuwa? 6 Ina dai gaya muku, ga wanda ya fi Haikali a nan. 7 Da kun san ma'anar wannan cewa, ‘Ni kam, zaman jinƙai nake nema a gare ku, ba hadaya ba,’ da ba ku ga laifin marasa laifi ba. 8 Domin Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabar.”

Mai Shanyayyen Hannu

9 Sai ya ci gaba daga nan ya shiga majami'arsu. 10 Akwai wani mutum a nan kuwa mai shanyayyen hannu. Sai suka tambayi Yesu, suka ce, “Ya halatta a warkar a ran Asabar?” Wannan kuwa don su samu su kai ƙararsa ne. 11 Ya ce musu, “Misali, wane ne a cikinku in yana da tunkiya, ta faɗa a rami ran Asabar, ba zai kama ta ya fitar da ita ba? 12 Sau nawa mutum ya fi tunkiya daraja? Domin haka ya halatta a yi alheri a ran Asabar.” 13 Sa'an nan ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Ya miƙa. Sai ya koma lafiyayye kamar ɗayan. 14 Amma Farisiyawa suka fita, suka yi shawara a kansa, yadda za su hallaka shi.

Zaɓaɓɓen Bara

15 Da Yesu ya gane haka, ya tashi daga nan. Sai jama'a da yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su duka. 16 Sai ya kwaɓe su, kada su bayyana shi. 17 Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa, 18 “Ga barana wanda na zaɓa! Ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai. Zan sa masa Ruhuna, zai kuma sanar da al'ummai hanyar gaskiya. 19 Ba zai yi husuma ko magana sama sama ba, Ba kuma wanda zai ji muryarsa a hanya. 20 Kyauron da ya tanƙwasa ba zai kakkarye shi ba, Fitilar da ta yi kusan mutuwa ba zai bice ta ba, Har ya sa gaskiya ta ci nasara. 21 Al'ummai kuma za su sa zuciya ga sunansa.”

Yesu da Ba'alzabul

22 Sai aka kawo masa wani bebe kuma makaho mai aljan, ya kuwa warkar da shi, har beben ya yi magana, ya kuma sami gani. 23 Mutane duk suka yi al'ajabi, suka ce, “Shin, ko wannan shi ne Ɗan Dawuda?” 24 Amma da Farisiyawa suka ji haka sai suka ce, “Ai, da ikon Ba'alzabul sarkin aljannu ne kawai, wannan yake fitar da aljannu.” 25 Da yake Yesu ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da ya rabu a kan gāba, zai lalace. Ba kuma gari ko gidan da ya rabu a kan gāba, da zai ɗore. 26 In Shaiɗan yana fitar da Shaiɗan, yā rabu a kan gāba ke nan. To, ta yaya mulkinsa zai ɗore? 27 In kuwa da ikon Ba'alzabul nake fitar da aljannu, to, 'ya'yanku fa, da ikon wa suke fitarwa? Saboda haka su ne za su zama alƙalanku. 28 Ni kuwa in da ikon Ruhun Allah nake fitar da aljannu, ashe, Mulkin Allah ya zo muku ke nan. 29 Yaya za a iya shiga gidan ƙaƙƙarfan mutum a washe kayansa, in ba an fara ɗaure ƙaƙƙarfan mutumin ba? Sa'an nan ne za a iya washe gidansa. 30 Wanda ba nawa ba ne, gāba yake yi da ni. Wanda kuma ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi. 31 “Don haka ina gaya muku, za ā gafarta wa mutane kowane zunubi da saɓo, amma wanda ya saɓi Ruhun, ba za a gafarta masa ba. 32 Kowa ya aibata Ɗan Mutum, za ā gafarta masa. Amma wanda ya aibata Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba, duniya da lahira.”

Itace da 'Ya'yansa

33 “Ko dai ku ce itace kyakkyawa ne, 'ya'yansa kuma kyawawa, ko kuwa ku ce itace mummuna ne, 'ya'yansa kuma munana. Don itace, ta 'ya'yansa ake gane shi. 34 Ku macizai! Yaya za ku iya yin maganar kirki, alhali kuwa ku mugaye ne? Don abin da ya ci rai, shi mutum yake faɗa. 35 Mutumin kirki kam, ta kyakkyawar taskar zuciyarsa yakan yi abin kirki, mugu kuwa, ta mummunar taskar zuciyarsa yakan yi mugun abu. 36 Ina dai gaya muku, a Ranar Shari'a duk hululun da mutum ya yi, za a bincike shi. 37 Maganarka ce za ta kuɓutar da kai, ko kuma ta hukunta ka.”

'Yan Zamani suna Neman Alama

38 Waɗansu malaman Attaura da Farisiyawa suka amsa masa suka ce, “Malam, muna so mu ga wata alama daga gare ka.” 39 Sai ya amsa musu ya ce, “'Yan zamani, mugaye, maciya amana, suke nema su ga wata alama! Amma ba wata alama da za a nuna musu sai dai ta Annabi Yunusa. 40 Wato, kamar yadda Yunusa ya yi kwana uku dare da rana cikin wani babban kifi, haka kuma Ɗan Mutum zai yi kwana uku dare da rana a cikin ƙasa. 41 A Ranar Shari'a mutanen Nineba za su tashi tare da mutanen zamanin nan, su kā da su, don sun tuba saboda wa'azin Yunusa. Ga kuma wanda ya fi Yunusa a nan. 42 A Ranar Shari'a Sarauniyar Kudu za ta tashi tare da mutanen zamanin nan, ta kā da su, don ta zo ne daga bangon duniya ta ji hikimar Sulemanu. Ga kuma wanda ya fi Sulemanu a nan.

Komawar Baƙin Aljan

43 “Baƙin aljan in ya rabu da mutum, sai ya bi ta wurare marasa ruwa don neman hutu, amma ba ya samu. 44 Sa'an nan sai ya ce, ‘Zan koma gidana da na fito.’ Sa'ad da kuwa ya koma, ya tarar da gidan ba kowa a ciki, shararre, ƙawatacce. 45 Daga nan ya je ya ɗebo waɗansu aljannu bakwai da suka fi shi mugunta. Sai su shiga su zauna a wurin. Wannan mutum ƙarshen zamansa ya fi na fari lalacewa. Haka zai zama wa wannan mugun zamani.”

Mahaifiyar Yesu da 'Yan'uwansa

46 Yana cikin magana da taro, sai ga mahaifiyarsa da 'yan'uwansa suna tsaye a waje, suna nema su yi magana da shi. 47 Wani ya ce masa, “Ga tsohuwarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna so su yi magana da kai.” 48 Sai ya amsa wa wanda ya gaya masa, ya ce, “Wace ce tsohuwata, su wane ne kuma 'yan'uwana?” 49 Sai ya miƙa hannu wajen almajiransa, ya ce, “Ga tsohuwata da 'yan'uwana nan! 50 Ai, kowa ya yi abin da Ubana da yake cikin Sama yake so, shi ne ɗan'uwana, shi ne 'yar'uwata, shi ne kuma tsohuwata.”

Matiyu 13

Misali da Mai Shuka

1 A ran nan Yesu ya fita daga gidan, ya je ya zauna a gabar teku. 2 Taro masu yawan gaske suka haɗu a wurinsa, har ya kai shi ga shiga jirgi, ya zauna. Duk taron kuwa suka tsaya a bakin gaci. 3 Sai ya gaggaya musu abubuwa da yawa da misalai, ya ce, “Wani mai shuka ya je shuka. 4 Yana cikin yafe iri sai waɗansu ƙwayoyi suka faɗa a hanya, sai tsuntsaye suka zo suka tsince su. 5 Waɗansu kuma suka faɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan sai suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa. 6 Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe. 7 Waɗansu kuma suka faɗa cikin ƙaya, sai ƙaya ta tashi ta sarƙe su. 8 Waɗansu kuma suka faɗa a ƙasa mai kyau, suka yi ƙwaya, waɗansu riɓi ɗari ɗari, waɗansu sittin sittin, waɗansu kuma talatin talatin. 9 Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Manufar Misalan

10 Sai almajiran suka zo, suka ce masa, “Me ya sa kake yi musu magana da misalai?” 11 Ya amsa musu ya ce, “Ku kam, an yarje muku ku san asiran Mulkin Sama, amma su ba a ba su ba. 12 Domin mai abu akan ƙara wa, har ya yalwata. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa. 13 Shi ya sa nake yi musu magana da misalai, don ko sun duba ba sa gani, ko sun saurara ba sa ji, ba sa kuma fahimta. 14 Lalle a kansu ne aka cika annabcin Ishaya cewa, ‘Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau, Za ku kuma gani, amma ba za ku gane ba faufau, 15 Don zuciyar jama'ar nan ta yi kanta, Sun toshe kunnuwansu, Sun kuma runtse idanunsu, Don kada su gani da idanunsu, Su kuma ji da kunnuwansu, Su kuma fahimta a zuciyarsu, Har su juyo gare ni in warkar da su.’ 16 Albarka tā tabbata ga idanunku domin suna gani, da kuma kunnuwanku domin suna ji. 17 Hakika, ina gaya muku, annabawa da adalai da yawa sun yi ɗokin ganin abin da kuke gani, amma ba su gani ba, su kuma ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.

Yesu ya Ba da Bayanin Misalin Mai Shuka

18 “To, ga ma'anar misalin mai shukar nan. 19 Wanda duk ya ji Maganar Mulki bai kuma fahimce ta ba, sai Mugun ya zo ya zăre abin da aka shuka a zuciyarsa. Wannan shi ne irin da ya faɗa a hanya. 20 Wanda ya faɗa a wuri mai duwatsu kuwa, shi ne wanda da zarar ya ji Maganar Allah, sai ya karɓa da farin ciki. 21 Amma kuwa ba shi da tushe, rashin ƙarƙo gare shi kuma, har in wani ƙunci ko tsanani ya faru saboda Maganar, sai ya yi tuntuɓe. 22 Wanda ya faɗa cikin ƙaya kuwa, shi ne wanda ya ji Maganar, amma taraddadin duniya da jarabar dukiya sukan sarƙe Maganar, har ta zama marar amfani. 23 Wanda aka shuka a ƙasa mai kyau kuwa, shi ne wanda yake jin Maganar, ya kuma fahimce ta. Hakika shi ne mai yin amfani har ya yi albarka, wani riɓi ɗari, wani sittin, wani kuma talatin.”

Ciyayi a cikin Alkama

24 Ya kawo musu wani misali kuma, ya ce, “Za a kwatanta Mulkin Sama da mutumin da ya yafa iri mai kyau a gonarsa. 25 Sa'ad da mutane suke barci, sai magabcinsa ya je ya yafa irin wata ciyawa a cikin alkamar, ya tafi abinsa. 26 Da shukar ta tashi, ta yi ƙwaya, sai ciyawar ta bayyana. 27 Sai bayin maigidan suka zo, suka ce masa, ‘Maigida, ashe, ba kyakkyawan iri ka yafa a gonarka ba? To, ta yaya ke nan ta yi ciyawa?’ 28 Sai ya ce musu, ‘Wani magabci ne ya yi wannan aiki.’ Bayin suka ce masa, ‘To, kana so mu je mu ciccire mu tara ta?’ 29 Amma ya ce, ‘A'a, kada garin cire ciyawar ku tumɓuke har da alkamar ma. 30 Ku bari su kasance tare har zuwa lokacin yanka. A lokacin yanka kuma zan gaya wa masu yankan su fara yanke ciyawar su tara, su ɗaure dami dami a ƙone, alkamar kuwa su taro ta su sa a taskata.’ ”

Misali da Ƙwayar Mastad

31 Ya kawo musu wani misali, ya ce, “Mulkin Sama kamar ƙwayar mastad yake, wadda wani mutum ya je ya shuka a lambunsa. 32 Ita ce mafi ƙanƙanta a cikin ƙwayoyi, amma in ta girma, sai ta fi duk sauran ganyaye, har ta zama itace, har ma tsuntsaye su zo su yi sheƙarsu a rassanta.”

Misali na Yisti

33 Ya kuma ba su wani misali, ya ce, “Mulkin Sama kamar yisti yake, wanda wata mace ta ɗauka ta cuɗe da mudu uku na garin alkama, har duk garin ya game da yistin.”

Yesu ya Yi Amfani da Misalai

34 Yesu ya gaya wa taro duk waɗannan abubuwa da misalai. Ba ya faɗa musu kome sai da misali. 35 Wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Ishaya ne cewa, “Zan yi magana da misalai, Zan sanar da abin da yake ɓoye tun farkon duniya.”

Yesu ya Ba da Bayanin Misalin Ciyayi a cikin Alkama

36 Sai ya bar taron, ya shiga gida. Almajiransa kuma suka zo gare shi, suka ce, “Ka fassara mana misalin nan na ciyawa a gonar.” 37 Ya amsa ya ce, “Mai yafa kyakkyawan irin nan, shi ne Ɗan Mutum. 38 Gonar kuwa ita ce duniya, kyakkyawan irin nan, su ne 'ya'yan Mulkin Allah, ciyawar kuwa, 'ya'yan Mugun ne. 39 Magabcin nan da ya yafa ta kuwa, Iblis ne. Lokacin yankan kuwa, ƙarshen duniya ne, masu yankan kuma, mala'iku ne. 40 Kamar yadda ake tara ciyawa a ƙone ta, haka zai kasance a ƙarshen duniya. 41 Ɗan Mutum zai aiko mala'ikunsa, za su tattaro duk masu sa mutane laifi, da kuma duk masu yin mugun aiki, su fitar da su daga Mulkinsa, 42 su kuma jefa su cikin wuta mai ruruwa. Nan za su yi kuka da cizon hakora. 43 Sa'an nan ne masu adalci za su haskaka kamar rana a Mulkin Ubansu. Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Dukiyar da Ke Binne

44 “Mulkin Sama kamar dukiya yake da take binne a gona, wadda wani ya samu, ya sāke binnewa. Yana cikin murnarsa, sai ya je yă sayar da dukan mallakarsa, ya sayi gonar.”

Lu'ulu'u Mai Tamanin Gaske

45 “Har wa yau kuma Mulkin Sama kamar attajiri yake, mai neman lu'ulu'u masu daraja. 46 Da ya sami lu'ulu'u ɗaya mai tamanin gaske, sai ya je ya sai da dukan mallakarsa, ya saye shi.”

Taru

47 “Har wa yau kuma Mulkin Sama kamar taru yake da aka jefa a teku, ya kamo kifi iri iri. 48 Da ya cika, aka jawo shi gaci, aka zauna, aka tsince kyawawan kifi, aka zuba a goruna, munanan kuwa aka watsar. 49 Haka zai kasance a ƙarshen duniya. Mala'iku za su fito, su ware mugaye daga masu adalci, 50 su jefa su cikin wuta mai ruruwa. Nan za su yi kuka da cizon hakora.”

Sabuwar Dukiya da Tsohuwa

51 “Kun fahimci duk wannan?” Suka ce masa, “I.” 52 Sai ya ce musu, “To, duk malamin Attaura da ya zama almajirin Mulkin Sama, kamar maigida yake, wanda ya ɗebo dukiya sabuwa da tsohuwa daga taskarsa.”

An Ƙi Yesu a Nazarat

53 Da Yesu ya gama waɗannan misalai, sai ya tashi daga nan. 54 Da ya zo garinsu, ya koya musu a majami'arsu, har suka yi mamaki, suka ce, “Daga ina mutumin nan ya sami wannan hikima haka, da kuma mu'ujizan nan? 55 Ashe, wannan ba ɗan masassaƙin nan ba ne? Mahaifiyarsa ba sunanta Maryamu ba? 'Yan'uwansa kuwa ba su ne Yakubu, da Yusufu, da Saminu, da kuma Yahuza ba? 56 'Yan'uwansa mata ba duk tare da mu suke ba? To a ina ne mutumin nan ya sami waɗannan abu duka?” 57 Sai suka yi tuntuɓe sabili da shi. Amma Yesu ya ce musu, “Ai, annabi ba ya rasa girma sai dai a garinsa da kuma a gidansu.” 58 Bai kuma yi mu'ujizai masu yawa a can ba, saboda rashin bangaskiyarsu.

Matiyu 14

Mutuwar Yahaya Maibaftisma

1 A lokacin nan sarki Hirudus ya ji labarin shaharar Yesu. 2 Sai ya ce wa barorinsa, “Wannan, ai, Yahaya Maibaftisma ne, shi aka tasa daga matattu, shi ya sa mu'ujizan nan suke aiki ta wurinsa.” 3 Don dā ma Hirudus ya kama Yahaya ya ɗaure shi, ya sa shi kurkuku saboda Hirudiya, matar ɗan'uwansa Filibus. 4 Don dā ma Yahaya ya ce masa bai halatta ya aure ta ba. 5 Ko da yake yana son kashe shi, yana jin tsoron jama'a, don sun ɗauka shi annabi ne. 6 To, da ranar haihuwar Hirudus ta kewayo, sai 'yar Hirudiya ta yi rawa a gaban taron, har ta gamshi Hirudus, 7 har ma ya yi mata rantsuwa zai ba ta duk abin da ta roƙa. 8 Amma da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “A ba ni kan Yahaya Maibaftisma a cikin akushi yanzu yanzu.” 9 Sai sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma kunyar baƙinsa, ya yi umarni a ba ta. 10 Ya aika aka fille wa Yahaya kai a kurkuku, 11 aka kuwa kawo kan a cikin akushi, aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta. 12 Almajiransa suka zo suka ɗauki gangar jikin, suka binne, suka kuma je suka gaya wa Yesu.

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

13 Da Yesu ya ji haka sai ya tashi daga nan, ya shiga jirgi zuwa wani wuri inda ba kowa, domin ya kaɗaita. Amma da taron jama'a suka ji haka, suka fito daga garuruwa suka bi shi da ƙafa. 14 Da ya fita daga jirgin ya ga babban taron mutane. Sai ya ji tausayinsu, ya kuma warkar da marasa lafiya a cikinsu. 15 Da maraice ya yi, almajiransa suka zo gare shi, suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuwa, rana ta sunkuya. Sai ka sallami taron, su tafi ƙauyuka su saya wa kansu abinci.” 16 Yesu ya ce, “Ba lalle su tafi ba. Ku ku ba su abinci mana.” 17 Sai suka ce masa, “Ai, gurasa biyar da kifi biyu kawai muke da su a nan.” 18 Sai ya ce, “Ku kawo mini su.” 19 Sa'an nan ya umarci taron su zazzauna a ɗanyar ciyawa. Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyun, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura gurasar, ya yi ta ba almajiransa, almajiran kuma suna bai wa jama'a. 20 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har suka kwashe ragowar gutsattsarin, cike da kwando goma sha biyu. 21 Waɗanda suka ci kuwa misalin maza dubu biyar ne banda mata da yara.

Yesu yana Tafiya a kan Ruwan Teku

22 Sai ya sa almajiransa suka shiga jirgi su riga shi hayewa kafin ya sallami taron. 23 Bayan ya sallami taron, ya hau dutse shi kaɗai domin ya yi addu'a. Har magariba ta yi yana can shi kaɗai. 24 Sa'an nan kuwa jirgin yana tsakiyar teku, raƙuman ruwa suna mangararsa, gama iska tana gāba da su. 25 Wajen ƙarfe uku na dare sai Yesu ya nufo su, yana tafe a kan ruwan tekun. 26 Sa'ad da kuwa almajiran suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka firgita suka ce, “Fatalwa ce!” Suka yi kururuwa don tsoro. 27 Sai nan da nan ya yi musu magana ya ce, “Ba kome, Ni ne, kada ku ji tsoro.” 28 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, in kai ne, to, ka umarce ni in zo gare ka a kan ruwan.” 29 Ya ce, “Zo mana.” Sai Bitrus ya fita daga jirgin, ya taka ruwa ya nufi gun Yesu. 30 Amma da ya ga iska ta yi ƙarfi sai ya ji tsoro. Da ya fara nutsewa sai ya yi kururuwa, ya ce, “Ya Ubangiji, ka cece ni!” 31 Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi, ya ce masa, “Ya kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?” 32 Da shigarsu jirgin iska ta kwanta. 33 Na cikin jirgin suka yi masa sujada, suka ce, “Hakika kai Ɗan Allah ne.”

Yesu ya Warkar da Marasa Lafiya a Janisarata

34 Da suka haye, suka sauka a ƙasar Janisarata. 35 Da mutanen garin suka shaida shi, sai suka aika ko'ina a duk karkarar, aka kakkawo masa dukan marasa lafiya, 36 suka roƙe shi su taɓa ko da gezar mayafinsa ma, iyakar waɗanda suka taɓa kuwa suka warke.

Matiyu 15

Al'adun Shugabanni

1 Waɗansu Farisiyawa da malaman Attaura suka zo wurin Yesu daga Urushalima, suka ce, 2 “Don me almajiranka suke keta al'adun shugabanni? Domin ba sa wanke hannu kafin su ci abinci.” 3 Sai ya amsa musu ya ce, “Ku kuma don me kuke keta umarnin Allah saboda al'adunku? 4 Domin Allah ya yi umarni ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ kuma ‘Wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa lalle a kashe shi.’ 5 Amma ku kukan ce, ‘Kowa ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni an ba Allah,” to, ba lalle ya girmama mahaifinsa ba ke nan.’ 6 Wato, saboda al'adunku kun mai da Maganar Allah banza. 7 Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, da ya ce, 8 ‘Al'ummar nan a baka kawai suke girmama ni, Amma a zuci nesa suke da ni. 9 A banza suke bauta mini, Don ka'idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’ ”

Abubuwan da ke Ƙazantarwa

10 Ya kira taro ya ce musu, “Ku saurara, ku fahimta. 11 Ba abin da yake shiga mutum ta baka ne yake ƙazanta shi ba, abin da yake fita ta baka yake ƙazanta mutum.” 12 Sai almajiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisiyawa sun ji haushi da suka ji maganar nan?” 13 Ya amsa ya ce, “Duk dashen da ba Ubana da yake Sama ne ya dasa ba, za a tumɓuke shi. 14 Ƙyale su kawai, makafin jagora ne. In kuwa makaho ya yi wa makaho jagora, ai, duk biyu sai su faɗa a rami.” 15 Amma Bitrus ya ce masa, “A yi mana fassarar misalin nan.” 16 Yesu ya ce, “Ku ma, ashe, har yanzu ba ku fahimta ba? 17 Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum ta baka, cikinsa ya shiga, ta haka kuma zai fice? 18 Amma abin da ya fito ta baka, daga zuci yake, shi ne kuwa yake ƙazantar da mutum. 19 Don daga zuci mugayen tunani suke fitowa, kamar su kisankai, da zina, da fasikanci, da sata, da shaidar zur, da yanke. 20 Waɗannan suke ƙazantar da mutum. Amma a ci da hannu marar wanki ba ya ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar Mace Bakan'aniya

21 Yesu ya tashi daga nan, ya tafi zuwa ƙasar Taya da Sidon. 22 Ga wata Bakan'aniya mutuniyar ƙasar, ta zo, ta ɗaga murya ta ce, “Ya Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mani jinƙai. Wani aljani ya bugi 'yata, ba yadda take.” 23 Amma bai ce da ita kanzil ba. Sai almajiransa suka zo suka roƙe shi, suka ce, “Sallame ta mana, tana binmu tana cika mana kunne da kuka.” 24 Ya amsa ya ce, “Ni wurin ɓatattun tumakin jama'ar Isra'ila kaɗai aka aiko ni.” 25 Amma ta zo ta durƙusa a gabansa, ta ce, “Ya Ubangiji, ka taimake ni mana!” 26 Ya amsa ya ce, “Ai, bai kyautu a bai wa karnuka abincin 'ya'ya ba.” 27 Sai ta ce, “I, haka ne, ya Ubangiji, amma ai, karnuka sukan ci suɗin 'ya'ya.” 28 Sai Yesu ya amsa mata ya ce, “Kai, uwargida, bangaskiyarki da yawa take! Yă zamar miki yadda kike so.” Nan take 'yarta ta warke.

Yesu ya Warkar da Mutane Masu Yawa

29 Yesu ya tashi daga nan, ya bi ta bakin Tekun Galili. Sai ya hau dutse ya zauna a can. 30 Taro masu yawan gaske suka zo wurinsa, suka zazzo da guragu, da masu dungu, da makafi, da bebaye, da kuma waɗansu da yawa, suka ajiye su a gabansa, ya kuwa warkar da su. 31 Har jama'ar suka yi ta al'ajabi da ganin bebaye suna magana, masu dungu sun sami gaɓoɓinsu, guragu suna tafiya, makafi kuma suna gani, duk suka ɗaukaka Allah na Isra'ila.

Ciyar da Mutum Dubu Huɗu

32 Yesu ya kira almajiransa, ya ce, “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna ba su da wani abinci. Ba na kuwa so in sallame su da yunwa haka, kada su kasa a hanya.” 33 Sai almajiran suka ce masa, “Ina za mu samo gurasa a jeji haka da za ta isa ciyar da ƙasaitaccen taro haka?” 34 Yesu ya ce musu, “Gurasa nawa ke gare ku?” Suka ce, “Bakwai, da ƙananan kifaye kaɗan.” 35 Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. 36 Da ya ɗauki gurasa bakwai ɗin da kifayen nan, ya yi godiya ga Allah, sai ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiran, almajiran kuma suna, bai wa jama'a. 37 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har suka kwashe ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai. 38 Waɗanda suka ci kuwa maza dubu huɗu ne, banda mata da yara. 39 Da ya sallami taron ya shiga jirgi ya tafi ƙasar Magadan.

Matiyu 16

Neman Alama

1 Farisiyawa da Sadukiyawa suka zo suka roƙe shi ya nuna musu wata alama daga Sama, domin su gwada shi. 2 Ya amsa musu ya ce, “In magariba ta yi, kuka ga sama ta yi ja, kukan ce, ‘Aha, gari zai yi sarari.’ 3 Da safe kuma in kun ga sama ta yi ja, ta kuma gama gari, kukan ce, ‘Yau kam, za a yi hadiri.’ Kuna iya gane yanayin sararin sama, amma ba kwa iya gane alamun zamanin nan. 4 'Yan zamani, mugaye, maciya amana, suke nema su ga wata alama, amma ba wata alamar da za a nuna musu, sai dai ta Yunusa.” Sai ya bar su ya tafi.

Yistin Farisiyawa da Sadukiyawa

5 Da almajiran suka isa wancan ƙetare, ashe, sun manta ba su kawo gurasa ba. 6 Sai Yesu ya ce musu, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Sadukiyawa.” 7 Sai suka yi magana da juna suka ce, “Ba mu kawo gurasa ba fa!” 8 Da Yesu ya lura da haka sai ya ce, “Ya ku masu ƙarancin bangaskiya, don me kuke magana da juna a kan ba ku zo da gurasa ba? 9 Ashe, har yanzu ba ku gane ba? Ba ku tuna da gurasa biyar ɗin nan na mutum dubu biyar ba? Kwando nawa kuka ɗauka? 10 Ko kuma gurasan nan bakwai na mutum dubu huɗu, manyan kwanduna nawa kuka ɗauka? 11 Yaya kuka kasa ganewa? Ba zancen gurasa na yi ba, sai dai ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Sadukiyawa.” 12 Sa'an nan ne fa suka fahimta cewa, ba ce musu ya yi, su yi hankali da yistin gurasa ba, sai dai su yi hankali da koyarwar Farisiyawa da ta Sadukiyawa.

Hurcin Bitrus a kan Yesu

13 To, da Yesu ya shiga ƙasar Kaisariya Filibi, sai ya tambayi almajiransa ya ce, “Wa mutane suke cewa, Ɗan Mutum yake?” 14 Sai suka ce, “Waɗansu suna cewa, Yahaya Maibaftisma, waɗansu kuwa Iliya, waɗansu kuma Irmiya, ko kuwa ɗaya daga cikin annabawa.” 15 Ya ce musu, “Amma ku fa, wa kuke cewa, nake?” 16 Sai Bitrus ya amsa, ya ce, “Kai ne Almasihu, Ɗan Allah Rayayye.” 17 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai mai albarka ne, Saminu, ɗan Yunusa! Domin ba ɗan adam ne ya bayyana maka wannan ba, sai dai Ubana da yake cikin Sama. 18 Ina dai gaya maka, kai ne Bitrus, a kan dutsen nan ne zan gina ikilisiyata, wadda ikon Hades ba zai rinjaye ta ba. 19 Zan ba ka mabuɗan Mulkin Sama. Kome ka ƙulla a duniya, zai zama abin da aka riga ƙullewa a Sama ne. Kome ka warware a duniya, zai zama abin da aka riga warwarewa a Sama ne.” 20 Sai ya kwaɓi almajiransa ƙwarai kada su gaya wa kowa shi ne Almasihu.

Yesu ya Faɗi irin Mutuwar da zai Yi

21 Tun daga lokacin nan Yesu ya fara bayyana wa almajiransa, lalle ne ya tafi Urushalima, ya sha wuya iri iri a hannun shugabanni da manyan firistoci da malaman Attaura, har a kashe shi, a rana ta uku kuma a tashe shi. 22 Sai Bitrus ya ja shi waje ɗaya, ya fara tsawata masa, ya ce, “Allah ya sawwaƙe, ya Ubangiji! Wannan har abada ba zai same ka ba!” 23 Amma Yesu ya juya ya ce wa Bitrus, “Ka yi nesa da ni, ya Shaiɗan! Tarko kake a gare ni. Ba ka tattalin al'amuran Allah, sai dai na mutane.” 24 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Duk mai son bina, sai ya ƙi kansa, ya ɗauki gicciyensa, ya bi ni. 25 Duk mai son tattalin ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, zai same shi. 26 Me mutum ya amfana in ya sami duniya duka a bakin ransa? Me kuma mutum zai iya bayarwa ya fanshi ransa? 27 Domin Ɗan Mutum zai zo da ɗaukakar Ubansa tare da mala'ikunsa. A sa'an nan ne zai sāka wa kowane mutum gwargwadon aikinsa. 28 Hakika, ina gaya muku, akwai waɗansu tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba, sai sun ga Ɗan Mutum yana zuwa cikin Mulkinsa.”

Matiyu 17

Sākewar Kamanninsa

1 Bayan kwana shida sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da ɗan'uwansa Yahaya, ya kai su a kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai. 2 Sai kamanninsa suka sāke a gabansu, fuskarsa ta yi annuri kamar hasken rana, tufafinsa kuma suka yi fari fat suna haske. 3 Ga shi, Musa da Iliya sun bayyana a gare su, suna magana da Yesu. 4 Sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, ya kyautu da muke nan wurin. In kana so, sai in kafa bukkoki uku a nan, ɗaya taka, ɗaya ta Musa, ɗaya kuma ta Iliya.” 5 Yana magana ke nan sai ga wani gajimare mai haske ya zo ya rufe su. Aka kuma ji wata murya daga cikin gajimaren, ta ce, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai. Ku saurare shi.” 6 Da almajiran suka ji haka, sai suka faɗi ƙasa, tsoro ya kama su. 7 Sai Yesu ya zo ya taɓa su, ya ce, “Ku tashi, kada ku ji tsoro.” 8 Da suka ɗaga kai ba su ga kowa ba, sai Yesu kaɗai. 9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai Yesu ya kwaɓe su ya ce, “Kada ku gaya wa kowa abin da kuka gani, sai an ta da Ɗan Mutum daga matattu.” 10 Almajiran suka tambaye shi suka ce, “To, yaya malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya ya riga zuwa?” 11 Ya amsa ya ce, “Lalle Iliya zai zo ne, zai kuwa raya dukan abubuwa. 12 Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, ba su kuwa san shi ne ba, har ma suka yi masa abin da suka ga dama. Haka kuma Ɗan Mutum zai sha wuya a hannunsu.” 13 Sa'an nan ne almajiran suka gane, ashe, zancen Yahaya Maibaftisma yake yi musu.

Yesu ya Warkar da Yaro Mai Farfaɗiya

14 Da suka isa wurin taro, sai wani mutum ya zo gare shi, ya durƙusa a gabansa, ya ce, 15 “Ya Ubangiji, ka ji tausayin ɗana, yana farfaɗiya, yana shan wuya ƙwarai, sau da yawa yakan faɗa wuta da kuma ruwa. 16 Na kuwa kai shi wurin almajiranka, amma ba su iya warkar da shi ba.” 17 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku marasa bangaskiya, kangararru na wannan zamani! Har yaushe zan zama da ku? Har yaushe kuma zan jure muku? Ku kawo mini shi nan.” 18 Sai Yesu ya tsawata masa, aljanin kuma ya rabu da shi. Nan take yaron ya warke. 19 Sa'an nan almajiran suka zo wurin Yesu a keɓe, suka ce, “Me ya sa mu muka kasa fitar da shi?” 20 Ya ce musu, “Saboda ƙarancin bangaskiyarku. Domin hakika ina gaya muku, da kuna da bangaskiya, ko misalin ƙwayar mustad, da za ku ce wa dutsen nan, ‘Kawu daga nan, ka koma can!’ sai kuwa ya kawu. Ba kuwa abin da zai gagare ku. 21 Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a da azumi.”

Yesu ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

22 Tun suna ƙasar Galili, sai Yesu ya ce musu, “Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane, 23 za su kuwa kashe shi, a rana ta uku kuma za a tashe shi.” Sai duk tsananin baƙin ciki ya rufe su.

Ba da Gudunmawar Haikali

24 Da suka zo Kafarnahum masu karɓar rabin shekel na gudunmawar Haikali suka je wurin Bitrus, suka ce, “Malaminku yana ba da gudunmawar?” 25 Ya ce, “I, yakan bayar.” Da ya dawo gida kuma, sai Yesu ya fara yi masa magana ya ce, “Me ka gani, Bitrus? Wurin wa sarakunan duniya suke karɓar kuɗin fito haraji, a wurin 'ya'yansu, ko kuwa daga wurin waɗansu?” 26 Sa'ad da kuma ya ce, “Daga wurin waɗansu,” sai Yesu ya ce masa, “Wato, 'ya'yan an ɗauke musu ke nan. 27 Duk da haka, don kada mu ba su haushi, ka je teku ka yi fatsa, kifin da ka fara kamawa kuwa shi za ka ɗauka. In ka buɗe bakinsa za ka sami shekel guda a ciki. To, sai ka ɗauki shekel ɗin nan ka kai musu, wato, nawa da naka.” 18 .1 Wane ne Mafi Girma? Wane ne Mafi Girma?

Matiyu 18

1 A lokacin nan almajirai suka zo wurin Yesu, suka ce, “Wa ya fi girma duka a Mulkin Sama?” 2 Sai ya kira wani ƙaramin yaro, ya sa shi a tsakiyarsu, 3 ya ce, “Hakika, ina gaya muku, in ba kun juyo kun zama kamar ƙananan yara ba, har abada ba za ku shiga Mulkin Sama ba. 4 Duk wanda ya ƙasƙantar da kansa kamar ɗan yaron nan, ai, shi ne mafi girma a Mulkin Sama. 5 “Wanda duk ya karɓi ƙaramin yaro ɗaya kamar wannan saboda sunana, Ni ya karɓa. 6 Amma fa duk wanda ya sa ɗaya daga cikin waɗannan 'yan yara masu gaskatawa da ni ya yi laifi, zai fiye masa a rataya babban dutsen niƙa a wuyarsa, a kuma nutsar da shi a zurfin teku.”

Sanadodin Yin Zunubi

7 “Kaiton duniya saboda sanadodin tuntuɓe! Lalle sanadodin tuntuɓe ba su da makawa, duk da haka kaiton wanda shi ne sanadin! 8 In kuwa hannunka ko ƙafarka suna sa ka laifi, to, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai dungu ko da gurguntaka, da a jefa ka madawwamiyar wuta da hannu biyu ko ƙafa biyu. 9 In kuwa idonka yana sa ka laifi, to ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka shiga rai da ido ɗaya, da a jefa ka Gidan Wuta da ido biyu.”

Misali na Ɓatacciyar Tunkiya

10 “Ku dai lura, kada ku raina ɗaya daga cikin waɗannan 'yan yara. Ina gaya muku, mala'ikunsu a Sama kullum suna duban fuskar Ubana da yake cikin Sama. 11 Domin Ɗan Mutum ya zo ne musamman ceton abin da ya ɓata. 12 To, me kuka gani? In wani na da tumaki ɗari, ɗayarsu ta băce, ashe, ba zai bar tasa'in da taran nan a gindin dutse, ya je neman wadda ta ɓăce ba? 13 In kuwa ya samo ta, labudda, ina gaya muku, ai, farin cikin da yake yi a kanta ya fi na tasa'in da taran nan da ba su taɓa ɓăcewa ba. 14 Haka ma, ba nufin Ubanku da yake cikin Sama ba ne ɗaya daga cikin waɗannan 'yan yara ya hallaka.”

Ɗan'uwan da ya Yi Laifi

15 “In ɗan'uwanka ya yi maka laifi, sai ka je, ka gaya masa laifinsa, kai da shi, ku kaɗai. In ya saurare ka, to, kā maido da ɗan'uwanka ke nan. 16 In kuwa bai saurare ka ba, sai ka tafi da mutum ɗaya ko biyu, don a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku. 17 In kuma ya ƙi sauraronsu, sai ka shaida wa ikilisiya. In kuma har ya ƙi sauraron ikilisiyar, ka maishe shi kamar bare, ko mai karɓar haraji.”

Kullewa da Warwarewa

18 “Hakika, ina gaya muku, kome kuka ƙulla a duniya, zai zama abin da aka riga ƙullewa a Sama ne. Kome kuka warware a duniya, zai zama abin da aka riga warwarewa a Sama ne. 19 Har wa yau dai ina gaya muku, in mutum biyu daga cikinku, ra'ayinsu ya zo ɗaya a nan duniya a kan wani abin da za su roƙa, Ubana kuwa da yake Sama zai yi musu shi. 20 Gama kuwa inda mutum biyu ko uku suka taru saboda sunana, ni ma ina nan a tsakiyarsu.”

Misali na Bawa Wanda bai Yafe Ba

21 Sai Bitrus ya matso ya ce masa, “Ya Ubangiji, sau nawa ɗan'uwana zai yi mini laifi in yafe masa? Har sau bakwai?” 22 Yesu ya ce masa, “Ba sau bakwai kawai na ce maka ba, sai dai bakwai har saba'in. 23 “Saboda haka za a misalta Mulkin Sama da wani sarkin da yake so ya yi ƙididdigar dukiyarsa da take hannun bayinsa. 24 Da ya fara ƙididdigar, sai aka kawo masa wanda yake bi talanti dubu goma bashi. 25 Da yake ya gagara biya, sai ubangidansa ya yi umarni a sayar da shi da matarsa da 'ya'yansa da kuma duk abin da ya mallaka, a biya kuɗin. 26 Sai bawan ya faɗi a gabansa ya yi masa ladabi, ya ce, ‘Ya ubangida, ka yi mini haƙuri, zan biya ka tsaf.’ 27 Saboda tausayin bawan nan ubangidansa ya sake shi, ya yafe masa bashin. 28 Amma wannan bawa, da fitarsa sai ya tarar da wani abokin bautarsa, wanda yake bi dinari ɗari bashi. Ya cafi wuyarsa, ya ce, ‘Biya ni abin da nake binka.’ 29 Sai abokin bautarsa ya faɗi a gabansa, ya yi ta roƙonsa ya ce, ‘Ka yi mini haƙuri, ai, zan biya ka.’ 30 Amma ya ƙi, ya kuma je ya sa shi a kurkuku, har yā biya bashin. 31 Da abokan bautarsa suka ga abin da ya faru, suka yi baƙin ciki gaya, har suka je suka gaya wa ubangidansu duk abin da ya gudana. 32 Sai ubangidansa ya kira shi, ya ce masa, ‘Kai mugun bawa ne! Na yafe maka duk bashin nan saboda ka roƙe ni, 33 ashe, bai kyautu kai ma ka ji tausayin abokin bautarka, kamar yadda na ji tausayinka ba?’ 34 Ubangidansa ya yi fushi, ya ba da shi ga masu azabtarwa har yā biya duk bashin da ake binsa. 35 Haka kuma Ubana da yake Sama zai yi da ko wannenku, in ba ku yafe wa 'yan'uwanku da zuciya ɗaya ba.”

Matiyu 19

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

1 To, da Yesu ya gama duk wannan magana, sai ya bar ƙasar Galili, ya shiga ta Yahudiya, wadda take ƙetaren Kogin Urdun. 2 Taro mai yawan gaske suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can. 3 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa su gwada shi, suka ce, “Halal ne mutum ya saki matarsa a kan kowane dalili?” 4 Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karantawa ba, cewa, wanda ya halicce su tun farko, dā ma ya yi su, namiji da tamata?” 5 Ya kuma ce, “Don haka fa sai mutum ya bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, ya manne wa matarsa. Haka su biyun nan su zama jiki guda. 6 Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne. Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.” 7 Sai suka ce masa, “To, don me Musa ya yi umarni a ba da takardar kisan aure, a kuma saki matar?” 8 Ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya yardar muku ku saki matanku, amma ba haka yake ba tun farko. 9 Ina kuma gaya muku, kowa ya saki matarsa, in ba a kan laifin zina ba, ya kuma auri wata, ya yi zina ke nan. Wanda ma ya auri sakakkiya, ya yi zina.” 10 Sai almajiran suka ce masa, “In ko haka tsakanin mutum da matarsa yake, ashe ma, rashin yin aure ya fi amfani.” 11 Amma ya ce musu, “Ba duk mutum ne zai iya ɗaukar maganar nan ba, sai dai waɗanda aka yardar wa. 12 Akwai waɗanda aka haifa babanni, akwai waɗanda mutane ne suka mai da su babanni. Akwai kuma waɗanda suka mai da kansu babanni domin ƙaunar Mulkin Sama. Duk mai iya ɗaukar maganar nan, yă ɗauka.”

Yesu ya Sa wa 'Yan Yara Albarka

13 Sa'an nan aka kawo masa yara ƙanana domin ya ɗora musu hannu, ya yi musu addu'a, amma almajiran suka kwaɓe su. 14 Yesu kuwa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Sama na irinsu ne.” 15 Sai ya ɗora musu hannu ya yi tafiyarsa.

Saurayi Mai Dukiya

16 Sai ga wani ya matso wurinsa, ya ce, “Malam, wane aiki nagari ne da lalle zan yi in sami rai madawwami?” 17 Sai ya ce masa, “Don me kake tambayata a kan abin da yake nagari? Ai, Managarci ɗaya ne. In kuwa kana so ka sami wannan rai, to, ka kiyaye umarnan nan.” 18 Sai ya ce masa, “Waɗanne?” Yesu ya ce, “Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. 19 Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, ka kuma ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.” 20 Saurayin ya ce masa, “Ai, duk na kiyaye waɗannan, me kuma ya rage mini?” 21 Yesu ya ce masa, “In kana so ka zama kammalalle, sai ka je ka sayar da duk mallakarka, ka bai wa talakawa, ka sami wadata a Sama. Sa'an nan ka zo ka bi ni.” 22 Da saurayin nan ya ji haka, sai ya tafi, yana baƙin ciki, don yana da arziki ƙwarai. 23 Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Hakika, ina gaya muku, da wuya mai arziki ya sami shiga Mulkin Sama. 24 Har wa yau ina gaya muku, zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.” 25 Da almajiran suka ji haka, sai suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ce, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?” 26 Amma Yesu ya dube su, ya ce musu, “Ga mutane kam, ba mai yiwuwa ba ne, amma gun Allah kowane abu mai yiwuwa ne.” 27 Sai Bitrus ya amsa ya ce, “To, ai, ga shi mun bar kome, mun bi ka. Me za mu samu ke nan?” 28 Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, a sabon zamani, sa'ad da Ɗan Mutum ya zauna a maɗaukakin kursiyinsa, ku da kuka bi ni, ku ne kuma za ku zauna a kursiyi goma sha biyu, kuna hukunta kabilan nan goma sha biyu na Isra'ila. 29 Kowa ya bar gidaje, ko 'yan'uwa maza, ko 'yan'uwa mata, ko mahaifi, ko mahaifiya, ko 'ya'ya, ko gonaki, saboda sunana, zai sami ninkinsu ɗari, ya kuma gāji rai madawwami. 30 Da yawa na farko za su koma na ƙarshe, na ƙarshe kuma za su zama na farko.”

Matiyu 20

Ma'aikata a Garkar Inabi

1 “Mulkin Sama kamar wani maigida yake, wanda ya fita da sassafe ya ɗauki ma'aikata don aikin garkarsa ta inabi. 2 Da ya yi lada da su a kan dinari guda a yini, sai ya tura su garkarsa. 3 Wajen ƙarfe tara kuma da ya fita, sai ya ga waɗansu suna zaman banza a bakin kasuwa. 4 Sai ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi garkata, zan kuwa biya ku abin da yake daidai.’ Sai suka tafi. 5 Da ya sāke fita wajen tsakar rana, da kuma ƙarfe biyu na rana, ya sāke yin haka dai. 6 Wajen ƙarfe huɗu na yamma kuma ya fita ya sami waɗansu a tsaitsaye, ya ce musu, ‘Don me kuke zaman banza yini zubur?’ 7 Sai suka ce masa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi garkata.’ 8 Da magariba ta yi, mai garkar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kirawo ma'aikatan, ka biya su hakkinsu, ka fara daga na ƙarshe har zuwa na farko.’ 9 Da waɗanda aka ɗauka wajen ƙarfe hudu na yamma suka zo, sai ko wannensu ya sami dinari guda. 10 To, da na farkon suka zo suka zaci za su sami fiye da haka. Amma su ma aka ba ko wannensu dinari guda. 11 Da suka karɓa sai suka yi ta yi wa maigidan gunaguni, 12 suna cewa, ‘Na bayan nan, ai, aikin sa'a guda kawai suka yi, ka kuwa daidaita mu, mu da muka yini zubur muna shan wahala da zafin rana.’ 13 Sai ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Abokina, ai, ban cuce ka ba. Ashe, ba mu yi fada da kai a kan dinari guda ba? 14 Sai ka karɓi halalinka ka tafi. Ni ne na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka. 15 Ashe, ba ni da ikon yin abin da na ga dama da abin da ke mallakata? Ko kuwa kana jin haushin alherina ne?’ 16 Saboda haka na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma za su koma na ƙarshe.”

Yesu kuma ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

17 Yesu na tafiya Urushalima, ya ɗauki almajiran nan goma sha biyu waje ɗaya. Suna tafiya ke nan sai ya ce musu, 18 “To, ga shi, za mu Urushalima, za a kuma ba da Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman Attaura, za su kuwa yi masa hukuncin kisa, 19 su bashe shi ga al'ummai, su yi masa ba'a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma za a tashe shi.”

Roƙon da Mahaifiyar Yakubu da Yahaya ta Yi

20 Sa'an nan mahaifiyar 'ya'yan Zabadi ta matso wurinsa tare da 'ya'yanta, ta durƙusa a gabansa, ta roƙe shi wani abu. 21 Sai ya ce mata, “Me kike bukata?” Ta ce masa, “Ka yi umarni waɗannan 'ya'yana biyu su zauna, ɗaya a damanka, ɗaya a hagunka, a mulkinka.” 22 Amma Yesu ya amsa ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Kwa iya shan ƙoƙon da ni zan sha?” Suka ce masa, “Ma iya.” 23 Sai ya ce musu, “Lalle kwa sha ƙoƙona, amma zama a damana da haguna, ba nawa ba ne da zan bayar, ai, na waɗanda Ubana ya riga ya shirya wa ne.” 24 Da almajiran nan goma suka ji haka, sai suka ji haushin 'yan'uwan nan biyu. 25 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani sarakunan al'ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko. 26 Ba haka zai zama a tsakaninku ba. Amma duk wanda yake son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku. 27 Wanda duk kuma yake so ya shugabance ku, lalle ne ya zama bawanku, 28 kamar yadda Ɗan Mutum ma ya zo ba domin a bauta masa ba sai dai domin shi ya yi bautar, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”

Makafi Biyu sun Sami Ganin Gari

29 Suna fita daga Yariko ke nan, sai wani babban taro ya bi shi. 30 Ga mutum biyu makafi zaune a bakin hanya. Da suka ji dai Yesu ne yake wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, ya Ɗan Dawuda!” 31 Jama'a suka kwaɓe su su yi shiru. Amma sai ƙara ɗaga murya suke yi ƙwarai da gaske, suna cewa, “Ya Ubangiji, ka yi mana jinƙai, ya Ɗan Dawuda!” 32 Sai Yesu ya tsaya, ya yi kiransu ya ce, “Me kuke so in yi muku?” 33 Suka ce masa, “Ya Ubangiji, mu dai mu sami gani!” 34 Domin tausayi, sai Yesu ya taɓa idanunsu, nan take suka gani, suka bi shi.

Matiyu 21

Mutanen Urushalima sun Marabci Yesu

1 Da suka kusato Urushalima suka zo Betafaji, wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu, 2 ya ce musu, “Ku shiga ƙauyen can da yake gabanku. Da shigarku za ku ga wata jaka a ɗaure, da kuma ɗanta. Ku kwanto su. 3 Kowa ya yi muku magana, ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsu,’ zai kuwa aiko da su nan da nan.” 4 An yi wannan kuwa domin a cika faɗar Annabi Zakariya cewa, 5 “Ku ce wa 'yar Sihiyona, Ga Sarkinki yana zuwa gare ki, Mai tawali'u ne, Yana kan aholaki, wato, ɗan jaki.” 6 Sai almajiran suka tafi suka bi umarnin Yesu. 7 Suka kawo jakar da ɗanta, suka shimfiɗa masu mayafansu, ya hau. 8 Yawancin jama'a suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka kakkaryo ganye suna bazawa a hanya. 9 Taron jama'a da suke tafiya a gabansa da kuma a bayansa, sai suka ɗauki sowa suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji! Hosanna ga Allah!” 10 Da ya shiga Urushalima dukkan birnin ya ruɗe, ana ta cewa, “Wane ne wannan?” 11 Sai jama'a suka ce, “Ai, wannan shi ne Annabi Yesu daga Nazarat ta ƙasar Galili.”

Yesu ya Tsabtace Haikalin

12 Sai Yesu ya shiga Haikalin ya kakkori dukkan masu saye da sayarwa a ciki, ya birkice teburorin 'yan canjin kuɗi da kujerun masu sayar da tattabarai. 13 Ya ce musu, “A rubuce yake cewa, ‘Za a kira gidana ɗakin addu'a,’ amma ku kun maishe shi kogon 'yan fashi.” 14 Sai makafi da guragu suka zo wurinsa a Haikalin, ya kuwa warkar da su. 15 Amma manyan firistoci da malaman Attaura suka ga abubuwan al'ajabi da ya yi, har yara suna sowa a Haikalin suna cewa, “Hosanna ga Ɗan Dawuda!” sai suka ji haushi. 16 Suka ce masa, “Kana jin abin da waɗannan suke faɗa?” Yesu kuwa ya ce musu, “I. Amma ba ku taɓa karantawa ba cewa, ‘Kai ne ka shiryar da 'yan yara da masu shan mama su yabe ka?’ ” 17 Sai ya bar su, ya fita daga birnin, ya tafi Betanya, ya sauka a can.

La'antar da Itacen Ɓaure

18 Kashegari da sassafe yana komowa birni, sai ya ji yunwa. 19 Da ya ga wani ɓaure a gefen hanya, ya je wurin, amma bai sami kome ba, sai ganye kawai. Sai ya ce wa ɓauren, “Kada ka ƙara yin 'ya'ya har abada!” Nan take ɓauren ya bushe. 20 Da almajiran suka ga haka, suka yi mamaki suka ce, “Yaya ɓauren nan ya bushe haka nan da nan?” 21 Yesu ya amsa musu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, in dai kuna da bangaskiya, ba tare da wata shakka ba, ba abin da aka yi wa ɓauren nan kaɗai za ku yi ba, har ma in kun ce wa dutsen nan, ‘Ka ciru, ka faɗa teku,’ sai kuwa ya auku. 22 Kome kuka roƙa da addu'a, in dai kuna da bangaskiya, za ku samu.”

Ana Shakkar Izinin Yesu

23 Ya shiga Haikali yana cikin koyarwa, sai manyan firistoci da shugabannin jama'a suka zo wurinsa, suka ce, “Da wane izini kake yin abubuwan nan, wa ya ba ka izinin?” 24 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. In kun ba ni amsa, ni ma sai in gaya muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan. 25 To, baftismar da Yahaya ya yi, daga ina take? Daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?” Sai suka yi ta muhawwara da juna, suna cewa, “In muka ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce mana, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’ 26 In kuwa muka ce, ‘Ta mutum ce,’ ai, muna jin tsoron jama'a, don duk kowa ya ɗauki Yahaya a kan annabi ne.” 27 Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Shi kuma ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan ba.”

Misali na Mai 'Ya'ya Biyu Maza

28 “To, me kuka gani? An yi wani mutun mai 'ya'ya biyu maza. Ya je wurin na farkon, ya ce, ‘Ɗana, yau je ka ka yi aiki a garkar inabi.’ 29 Sai ya ce, ‘Na ƙi.’ Amma daga baya sai ya tuba, ya tafi. 30 Sai ya je gun na biyun ya faɗa masa haka. Shi kuwa ya amsa ya ce, ‘To, za ni, baba,’ amma bai je ba. 31 To, wane ne a cikin su biyun ya yi abin da mahaifinsu yake so?” Sai suka ce, “Na farkon.” Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, masu karɓar haraji da karuwai suna riga ku shiga Mulkin Allah. 32 Ga shi, Yahaya ya zo ya bayyana muku hanyar adalci, ba ku gaskata shi ba. Amma masu karɓar haraji da karuwai sun gaskata shi, duk da ganin haka kuma, daga baya ba ku tuba kun gaskata shi ba.”

Misali na Manoman da suka Yi Ijarar Garkar Inabi

33 “To, ga kuma wani misali. An yi wani maigida da ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabi a ciki, ya kuma gina wata 'yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma ijarar garkar, sa'an nan ya tafi wata ƙasa. 34 Da kakar inabi ta kusa, sai ya aiki bayinsa wurin manoman nan su karɓo masa gallar garkar. 35 Manoman kuwa suka kama bayinsa, suka yi wa ɗaya d�ka, suka kashe ɗaya, suka kuma jajjefi ɗaya. 36 Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi fiye da na dā, suka kuma yi musu haka. 37 Daga baya sai ya aiki ɗansa gare su, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’ 38 Amma da manoman suka ga ɗan, suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magajin, ku zo mu kashe shi, gādonsa ya zama namu.’ 39 Sai suka kama shi, suka jefa shi bayan shinge, suka kashe shi. 40 To, sa'ad da ubangijin garkar nan ya zo, me zai yi wa manoman nan?” 41 Sai suka ce masa, “Zai yi wa mutanen banzan nan mugun kisa, ya ba waɗansu manoma ijararta, waɗanda za su riƙa ba shi gallar garkar a lokacin nunanta.” 42 Yesu ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karantawa a Littattafai ba? cewa, ‘Dutsen da magina suka ƙi, Shi ne ya zama mafificin dutsen gini. Wannan aikin Ubangiji ne, A gare mu kuwa abin al'ajabi ne.’ 43 Domin haka ina gaya muku, za a karɓe Mulkin Allah daga gare ku, a bai wa wata al'umma wadda za ta ba da amfani nagari. 44 Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje. Amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.” 45 Da manyan firistoci da Farisiyawa suka ji misalan nan da ya yi, sai suka gane, ashe, da su yake. 46 Amma da suka nemi kama shi, suka ji tsoron jama'a, don su sun ɗauke shi shi annabi ne.

Matiyu 22

Misali na Bikin Aure

1 Yesu ya sāke yi musu magana da misalai ya ce, 2 “Za a kwatanta Mulkin Sama da wani sarki, wanda ya yi wa ɗansa biki. 3 Sai ya aiki bayinsa su kirawo waɗanda aka gayyata bikin, amma waɗanda aka gayyatar suka ƙi zuwa. 4 Har wa yau ya sāke aiken waɗansu bayi, ya ce, ‘Ku gaya wa waɗanda aka gayyata, “Ga shi, na shisshirya abinci, an yanka shanuna da kiwatattun maruƙana, duk an shirya kome, ku zo bikin mana!” ’ 5 Amma suka ƙi kula, suka tafi abinsu, wani ya tafi gonarsa, wani kuma cinikinsa. 6 Sauran kuwa suka kame bayinsa, suka wulakanta su, suka kashe su. 7 Sarki ya yi fushi, ya tura sojansa, suka hallaka masu kisankan nan, suka ƙone garinsu ƙurmus. 8 Sa'an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin fa ya shiryu sosai, amma waɗanda aka gayyata ba su cancanta ba. 9 Saboda haka ku tafi ƙofofin gari, ku gayyato duk waɗanda kuka samu, su zo bikin.’ 10 Sai bayin suka yi ta bin hanyoyin garin, suka tattaro duk waɗanda suka samu, mugaye da nagargaru duka, har wurin bikin ya cika maƙil da baƙi. 11 “Da sarki ya shigo ganin baƙin sai ya ga wani mutum a can wanda bai sa riga irin ta biki ba. 12 Sai ya ce masa, ‘Malam, ta yaya ka shigo nan ba tare da sa riga irin ta biki ba?’ Mutumin kuwa ya rasa ta cewa. 13 Sai sarki ya ce wa barorinsa, ‘Ku ɗaure shi ƙafa da hannu, ku jefa shi cikin matsanancin duhu. Nan za a yi kuka da cizon hakora.’ 14 Gama da yawa ake kira, amma kaɗan ne zaɓaɓɓu.”

Biyan Haraji ga Kaisar

15 Sai Farisiyawa suka je suka yi shawara yadda za su burma shi cikin maganarsa. 16 Suka aiko almajiransu wurinsa tare da waɗansu mutanen Hirudus, suka ce, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi, ba ka kuma zaɓen kowa, don ka ɗauki kowa da kowa daidai. 17 To, faɗa mana abin da ka gani. Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa?” 18 Yesu kuwa domin ya gane muguntarsu, sai ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku munafukai! 19 Ku nuna mini kuɗin harajin.” Sai suka kawo masa dinari. 20 Yesu ya ce musu, “Surar nan da sunan nan na wane ne?” 21 Suka ce, “Na Kaisar ne.” Sa'an nan ya ce musu, “To, sai ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” 22 Da suka ji haka, sai suka yi mamaki, suka rabu da shi, suka yi tafiyarsu.

Tambaya a kan Tashin Matattu

23 A ran nan sai waɗansu Sadukiyawa (su da suke cewa, ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka yi masa tambaya, 24 suka ce, “Malam, Musa dai ya ce, ‘In mutum ya rasu, bai bar na baya ba, sai lalle ɗan'uwansa ya auri matar, ya haifa wa ɗan'uwansa 'ya'ya.’ 25 To, an yi waɗansu 'yan'uwa maza bakwai a cikinmu. Na farkon ya yi aure, da ya rasu, da yake bai haifu kuma ba, sai ya bar wa ɗan'uwansa matarsa. 26 Haka ya faru ga na biyun da na ukun, har ya kai kan na bakwai ɗin. 27 Bayansu duka sai matar ta rasu. 28 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu, su bakwai ɗin? Don duk sun aure ta.” 29 Amma Yesu ya amsa musu ya ce, “Kun ɓăta ne, domin ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba. 30 Domin a tashin matattu, ba a aure, ba a aurarwa, sai dai kamar mala'ikun da suke Sama ake. 31 Game da tashin matattu, ashe, ba ku taɓa karanta abin da Allah ya ce muku ba? cewa, 32 ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu.’ Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba.” 33 Da jama'a suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.

Umarni Mafi Girma

34 Amma da Farisiyawa suka ji ya ƙure Sadukiyawa, suka taru. 35 Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Attaura, ya yi masa tambaya, yana gwada shi, ya ce, 36 “Malam, wane umarni ne mafi girma a cikin Attaura?” 37 Ya ce masa, “Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka. 38 Wannan shi ne babban umarni na farko. 39 Na biyu kuma kamarsa yake, ‘Ka ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.’ 40 A kan umarnin nan biyu duk Attaura da koyarwar annabawa suka rataya.”

Tambaya a kan Ɗan Dawuda

41 Tun Farisiyawa suna tare gu ɗaya, sai Yesu ya yi musu tambaya, 42 ya ce, “Yaya kuka ɗauki Almasihu? Shi ɗan wane ne?” Sai suka ce masa, “Ɗan Dawuda ne.” 43 Ya ce musu, “To, yaya kuwa Dawuda, ta ikon Ruhu, ya ce da shi Ubangiji? Har ya ce, 44 ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, Zauna a damana, Sai na ɗora ka a kan maƙiyanka.’ 45 Tun da Dawuda ya kira shi Ubangiji ne, to, ƙaƙa zai zama ɗansa?” 46 Ba kuwa wanda ya iya tanka masa. Daga ran nan kuwa ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.

Matiyu 23

Yesu ya Fallashi Malaman Attaura da Farisiyawa

1 Sa'an nan Yesu ya yi wa jama'a da almajiransa magana, ya ce, 2 “Malaman Attaura da Farisiyawa suka tsaya a matsayin Musa. 3 Don haka, sai ku kiyaye, ku kuma aikata duk abin da suka gaya muku, amma banda aikinsu. Don suna faɗa ne, ba aikatawa. 4 Sukan ɗaura kaya masu nauyi, masu wuyar ɗauka, su jibga wa mutane a kafaɗa. Amma su kansu ko tallafa musu da ɗan yatsa ba sa yi. 5 Duk ayyukansu suna yi ne don idon mutane, suna yin layunsu fantam-fantam, lafin rigunansu kuma har gwiwa. 6 Suna son mazaunan alfarma a wurin biki, da mafifitan mazaunai a majami'u, 7 a gaishe su a kasuwa, a kuma riƙa ce da su ‘Malam.’ 8 Amma ku kam, kada a ce muku ‘Malam,’ domin Malaminku ɗaya ne, ku duka kuwa 'yan'uwa ne. 9 Kada ku kira kowa ‘Uba’ a duniya, domin Uba ɗaya ne ke gare ku, wanda yake cikin Sama. 10 Kada kuma a kira ku ‘Shugabanni,’ domin Shugaba ɗaya gare ku, wato, Almasihu. 11 Amma wanda yake babba a cikinku shi zai zama baranku. 12 Duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Mai ƙasƙantar da kansa kuma, ɗaukaka shi za a yi. 13 “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kun toshe wa mutane ƙofar Mulkin Sama. Ku kanku ba ku shiga ba, kuna kuwa hana masu niyyar shiga shiga. 14 Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan ci kayan mata gwauraye, kukan yi doguwar addu'a don ɓad da sawu. Saboda haka za a yi muku hukunci mafi tsanani. 15 Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan kewaye ƙasashe da tekuna don samun almajiri ɗaya tak, in kuwa kun samu, kukan mai da shi ɗan wuta fiye da ku, ninkin ba ninkin. 16 “Kaitonku, makafin jagora, ku da kuke cewa, ‘Kowa ya rantse da Haikalin, ba kome, amma duk wanda ya rantse da zinariyar Haikalin, sai rantsuwarsa ta kama shi.’ 17 Ku makafi, wawaye! Wanne ya fi girma, zinariyar ce ko kuwa Haikalin da yake tsarkake zinariyar? 18 Kukan ce, ‘Kowa ya rantse da bagaden hadaya, ba kome. Amma duk wanda ya rantse da sadakar da aka ɗora a kai, sai rantsuwarsa ta kama shi.’ 19 Ku makafi! Wanne ya fi girma, sadakar ko kuwa bagaden hadaya da yake tsarkake sadakar? 20 Don haka kowa ya rantse da bagaden hadaya, ya rantse ke nan da shi, da duk abin da yake a kansa. 21 Duk kuma wanda ya rantse da Haikalin ya rantse da shi, da kuma wanda yake zaune a cikinsa. 22 Kowa kuma ya rantse da Sama, ya rantse da kursiyin Allah, da kuma wanda yake zaune a kansa. 23 “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan fitar da zakkar na'ana'a, da anise, da lafsur, amma kun yar da muhimman jigajigan Attaura, wato, gaskiya, da jinƙai, da aminci. Waɗannan ne ya kamata ku yi, ba tare da yar da sauran ba. 24 Makafin jagora, kukan tace ƙwaro ɗan mitsil, amma kukan haɗiye raƙumi! 25 “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan wanke bayan ƙwarya da akushi, amma a ciki cike suke da zalunci da zari. 26 Kai makahon Bafarisiye! Sai ka fara tsarkake cikin ƙwaryar da akushin don bayansu ma ya tsarkaka. 27 “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kamar kaburburan da aka shafa wa farar ƙasa kuke, masu kyan gani daga waje, daga ciki kuwa sai ƙasusuwan matattu da ƙazanta iri iri. 28 Haka nan a idon mutane ku adalai ne, amma ciki sai munafunci da mugun aiki. 29 “Kaitonku, malaman Attaura da Farisiyawa, munafukai! Kukan yi gini a kan kaburburan annabawa, kuna ƙawata gubbobin adalai. 30 Kuna cewa, ‘Da mun zauna a zamanin kakanninmu, da ba mu taya su zub da jinin annabawa ba.’ 31 Ta haka kuka shaidi kanku ku ne 'ya'yan masu kisan annabawa. 32 To, sai ku cikasa ayyukan kakanninku! 33 Ku macizai! Yaya za ku tsere wa hukuncin Gidan Wuta? 34 Saboda haka nake aiko muku da annabawa, da masu hikima, da masanan Attaura, za ku kashe waɗansunsu, ku gicciye waɗansu, ku kuma yi wa waɗansu bulala a majami'unku, kuna binsu gari gari kuna gwada musu azaba. 35 Don alhakin jinin dukan adalai da aka zubar a duniya yă komo a kanku, tun daga jinin Habila adali, har ya zuwa na Zakariya ɗan Berikiya, wanda kuka kashe a tsakanin Haikalin da bagaden hadaya. 36 Hakika, ina gaya muku, duk wannan zai auko wa mutanen wannan zamani.”

Yesu ya Ji Juyayin Urushalima

37 “Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko a gare ku! Sau nawa ne na so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta cikin fikafikanta, amma kun ƙi! 38 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe! 39 Ina dai gaya muku, ba za ku ƙara ganina ba, sai ran da kuka ce, ‘Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.’ ”

Matiyu 24

Yesu ya Faɗi irin Rushewar da za ta Sami Haikalin

1 Yesu ya fita Haikalin, yana cikin tafiya, sai almajiransa suka zo suka nuna masa gine-ginen Haikalin. 2 Amma ya amsa musu ya ce, “Kun ga duk waɗannan ko? Hakika, ina gaya muku, ba wani dutsen da za a bari nan a kan ɗan'uwansa ba a baje shi ba.”

Farkon Azaba

3 Yana zaune a kan Dutsen Zaitun sai almajiransa suka zo wurinsa a kaɗaice, suka ce, “Gaya mana, yaushe za a yi waɗannan abubuwa? Mece ce kuma alamar dawowarka, da ta ƙarewar zamani?” 4 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku kula fa kada kowa ya ɓad da ku, 5 domin mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa, su ne Almasihu, har su ɓad da mutane da yawa. 6 Za ku kuma riƙa jin labarin yaƙe-yaƙe da jitajitarsu. Kada fa hankalinku ya tashi, don lalle ne a yi haka, amma ƙarshen tukuna. 7 Al'umma za ta tasar wa al'umma, mulki ya tasar wa mulki. Za a kuma yi yunwa da raurawar ƙasa a wurare dabam dabam. 8 Amma fa duk wannan masomin azaba ne tukuna. 9 “Sa'an nan za su bashe ku, a ƙuntata muku, su kuma kashe ku. Duk al'ummai za su ƙi ku saboda sunana. 10 A sa'an nan da yawa za su yi tuntuɓe, su ci amanar juna, su kuma ƙi juna. 11 Annabawan ƙarya da yawa za su firfito, su ɓad da mutane da yawa. 12 Saboda kuma yaɗuwar mugun aiki, sai ƙaunar yawancin mutane ta yi sanyi. 13 Amma duk wanda ya jure har ƙarshe, zai cetu. 14 Za a kuma yi bisharar nan ta Mulkin Sama ko'ina a duniya domin shaida ga dukkan al'ummai. Sa'an nan kuma sai ƙarshen ya zo.”

Matsananciyar Wahala

15 “Don haka sa'ad da kuka ga mummunan aikin saɓo mai banƙyama, wanda Annabi Daniyel ya faɗa, an tsai da shi a Wuri Mai Tsarki (mai karatu fa yă fahimta), 16 to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu. 17 Wanda yake kan soro, kada ya sauko garin ɗaukar kayan da yake a gidansa. 18 Wanda yake a gona kuma, kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa. 19 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci! 20 Ku yi addu'a kada gudunku ya zo da damuna, ko ran Asabar. 21 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada. 22 Ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan za a taƙaita kwanakin. 23 A sa'an nan kowa ya ce muku, ‘Kun ga, ga Almasihu nan!’ ko, ‘Ga shi can!’ kada ku yarda. 24 Don almasihan ƙarya da annabawan ƙarya za su firfito, su nuna manyan alamu da abubuwan al'ajabi, don su ɓad da ko da zaɓaɓɓu ma in dai zai yiwu. 25 To, na dai gaya muku tun da wuri. 26 Saboda haka in sun ce da ku, ‘Ga shi can a jeji,’ kada ku fita. In kuwa sun ce, ‘Yana can cikin lolloki,’ kada ku yarda. 27 Kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka komowar Ɗan Mutum za ta zama. 28 Inda mushe yake, ai, a nan ungulai sukan taru.

Komowar Ɗan Mutum

29 “Bayan tsabar wahalar nan, nan da nan sai a duhunta rana, wata kuma ba zai yi haske ba. Taurari kuma za su farfaɗo daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke sararin sama. 30 A sa'an nan ne alamar Ɗan Mutum za ta bayyana a sararin sama, duk kabilan duniya kuma za su yi kuka, za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gajimare, da iko da ɗaukaka mai yawa. 31 Zai kuwa aiko mala'ikunsa su busa ƙaho mai tsananin ƙara, su kuma tattaro zaɓaɓɓunsa daga gabas da yamma, kudu da arewa, wato, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.”

Aya a kan Itacen Ɓaure

32 “Ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa sun fara sakuwa, suna toho, kun san damuna ta yi kusa ke nan. 33 Haka kuma in kun ga duk waɗannan abubuwa, ku sani ya kusato, a bakin ƙofa ma yake. 34 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun auku. 35 Sararin sama da kasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”

Ba Wanda ya San Ranar ko Sa'ar

36 “Amma fa wannan rana da wannan sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun da suke Sama, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai. 37 Kamar yadda aka yi a zamanin Nuhu, haka dawowar Ɗan Mutum za ta zama. 38 Kamar a kwanakin nan ne gabannin Ruwan Tsufana, ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har ya zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi, 39 ba su farga ba har Ruwan Tsufana ya zo ya share su. Haka komowar Ɗan Mutum za ta zama. 40 A sa'an nan za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. 41 Za a ga mata biyu suna niƙa, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. 42 To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san ranar da Ubangijinku zai dawo ba. 43 Amma dai ku sani, da maigida zai san ko a wane lokaci ne da dare ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake ya hana a shigar masa gida. 44 Don haka ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba, Ɗan Mutum zai zo.”

Amintaccen Bawa ko Marar Aminci

45 “Wane ne amintaccen bawan nan mai hikima, da ubangidansa ya ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari? 46 Albarka tā tabbata ga bawan da in ubangidansa ya dawo zai samu yana yin haka. 47 Hakika, ina gaya muku, sai ya ɗora shi a kan dukan mallakarsa. 48 Amma in bawan nan mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Ubangidana ya jinkirta zuwansa,’ 49 sa'an nan ya soma d�kan abokan bautarsa, yana ci yana sha tare da mashaya, 50 ai, ubangidan wannan bawa zai zo a ranar da zai zata ba, a kuma lokacin da bai sani ba, 51 yă faffasa masa jiki da bulala, ya ba shi rabonsa tare da munafukai. Nan za a yi kuka da cizon hakora.”

Matiyu 25

Misali na Budurwai Goma

1 “Sa'an nan za a kwatanta Mulkin Sama da 'yan mata goma da suka ɗauki fitilunsu suka tafi taryen ango. 2 Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuwa masu hikima. 3 Don kuwa a lokacin da wawayen nan suka ɗauki fitilunsu, ashe, ba su riƙo mai ba. 4 Masu hikimar nan kuwa sun riƙo kwalaben mai da fitilunsu. 5 Da yake angon ya yi jinkiri, duk sai suka yi gyangyaɗi, har barci ya share su. 6 Can tsakar dare sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito ku tarye shi!’ 7 Duk budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu. 8 Sai wawayen nan suka ce wa masu hikimar, ‘Ku zuba mana ɗan manku kaɗan mana, fitilunmu na mutuwa!’ 9 Amma masu hikimar suka amsa suka ce, ‘Ai, watakila ba zai ishe mu mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’ 10 Tun suna wajen sayen, sai angon ya iso, waɗanda suke shirye suka shiga wurin biki tare da shi, aka kuma rufe ƙofa. 11 Daga baya sai waɗancan budurwai ma suka iso, suka ce, ‘Ya Ubangiji, ya Ubangiji, ka buɗe mana!’ 12 Sai ya amsa ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, ni ban san ku ba.’ 13 Don haka, sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ba, ko kuwa sa'ar.”

Misali na Talanti

14 “Kamar mutum ne da zai yi tafiya, ya kira bayinsa, ya danƙa musu dukiyarsa. 15 Ya ba ɗaya talanti biyar, ɗaya talanti biyu, wani kuma ya ba shi ɗaya, kowa dai gwargwadon ƙarfinsa. Sa'an nan ya tafi. 16 Shi wanda ya karɓi talanti biyar ɗin nan, nan da nan sai ya je ya yi ta jujjuya su, har wuri ya bugi wuri. 17 Haka kuma wanda ya karɓi talanti biyu, shi ma sai wuri ya bugi wuri. 18 Amma wannan da ya karɓi talanti ɗaya ɗin, sai ya je ya tona rami ya ɓoye kuɗin ubangidansa. 19 To, da aka daɗe sai ubangidan bayin nan ya dawo ya daidaita lissafi da su. 20 Shi wannan da ya karɓi talanti biyar sai ya matso ya kawo waɗansu talanti biyar, ya ce, ‘Ya ubangida, kā ba ni talanti biyar, ga shi kuma, na ci ribar biyar.’ 21 Sai ubangidansa ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki, mai aminci. Kā yi gaskiya a kan ƙaramin abu, zan ɗora ka a kan mai yawa. Ka zo ku yi farin ciki tare da ubangidanka.’ 22 Sai mai talanti biyun nan kuma ya matso, ya ce, ‘Ya ubangida, kā ba ni talanti biyu, ga shi kuma, na ci ribar biyu.’ 23 Sai ubangidansa ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki, mai aminci. Kā yi gaskiya a kan ƙaramin abu, zan ɗora ka a kan mai yawa. Ka zo ku yi farin ciki tare da ubangidanka.’ 24 Shi kuma wanda ya karɓi talanti guda ɗin, sai ya matso, ya ce, ‘Ya ubangida, na sani kai mutum ne mai tsanani, kana son girbi inda ba kai ka shuka ba, mai son banza ne. 25 Shi ya sa na ji tsoro, har na je na yi tono na ɓoye talantinka. To, ga kayanka nan!’ 26 Sai ubangidansa ya amsa masa ya ce, ‘Kai mugun bawa, malalaci! Ashe, ka sani ina girbi inda ba ni na shuka ba, ni kuma mai son banza ne? 27 Ya kamata ka sa kuɗina a ma'aji, da na dawo kuma da sai in karɓi abina har da riba! 28 Don haka sai ku karɓe talantin daga gunsa, ku bai wa mai goman nan. 29 Don duk mai abu a kan ƙara wa, har ya yalwata. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa. 30 Ku kuma jefa banzan bawan nan a baƙin duhu. Nan za a yi kuka da cizon hakora.’ ”

Shara'anta wa Al'ummai

31 “Sa'ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa tare da mala'iku duka, sa'an nan ne zai zauna a maɗaukakin kursiyinsa. 32 Za a tara dukan al'ummai a gabansa, zai kuma ware su dabam dabam, kamar yadda makiyayi yake ware tumaki da awaki. 33 Zai sa tumaki a damansa, awaki kuwa a hagunsa. 34 Sa'an nan ne Sarki zai ce wa waɗanda suke dama da shi, ‘Ku zo, ya ku da Ubana ya yi wa albarka, sai ku gāji mulkin da aka tanadar muku tun daga farkon duniya. 35 Domin na ji yunwa, kun ba ni abinci. Na ji ƙishirwa, kun ba ni na sha. Na yi baƙunci, kun saukar da ni. 36 Na yi huntanci, kun tufasar da ni. Na yi rashin lafiya, kun ziyarce ni. Ina kurkuku, kun kula da ni.’ 37 Sa'an nan ne masu adalci za su amsa masa su ce, ‘Ya Ubangiji, a yaushe muka gan ka da yunwa muka cishe ka, ko kuwa da ƙishirwa muka shayar da kai? 38 A yaushe kuma muka gan ka baƙo muka sauke ka, ko kuwa huntu muka tufasar da kai? 39 Ko kuma a yaushe muka gan ka da rashin lafiya, ko a kurkuku muka kula da kai?’ 40 Sai Sarkin zai amsa musu ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, tun da yake kun yi wa ɗaya daga cikin waɗannan 'yan'uwana mafi ƙanƙanta, ai, ni kuka yi wa.’ 41 Sa'an nan zai ce wa waɗanda suke na hagun, ‘Ku rabu da ni, la'anannu, ku shiga madawwamiyar wuta, wadda aka tanadar wa Iblis da mala'ikunsa. 42 Don na ji yunwa, ba ku ba ni abinci ba. Na ji ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba. 43 Na yi baƙunci, ba ku sauke ni ba. Na yi huntanci, ba ku tufasar da ni ba. Na yi rashin lafiya, ina kuma kurkuku, ba ku kula da ni ba.’ 44 Sa'an nan su ma za su amsa su ce, ‘Ya Ubangiji, a yaushe muka gan ka da yunwa, ko da ƙishirwa, ko da baƙunci, ko da huntanci, ko da rashin lafiya, ko a kurkuku, ba mu kula da kai ba?’ 45 Sa'an nan zai amsa musu ya ce, ‘Hakika, ina gaya muku, tun da yake ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ai, ni ne ba ku yi mini ba.’ 46 Waɗannan ne za su shiga madawwamiyar azaba, masu adalci kuwa rai madawwami.”

Matiyu 26

Shugabanni sun Ƙulla Shawara gaba da Yesu

1 Da Yesu ya gama duk wannan magana, sai ya ce wa almajiransa, 2 “Kun san Idin Ƙetarewa saura kwana biyu, za a kuma ba da Ɗan Mutum a gicciye shi.” 3 Sai manyan firistoci da shugabannin jama'a suka taru a gidan babban firist, mai suna Kayafa. 4 Suka ƙulla shawara su kama Yesu da makirci su kashe shi. 5 Amma suka ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kada jama'a su yi hargitsi.”

An Shafi Yesu da Man Ƙanshi a Betanya

6 To, sa'ad da Yesu yake a Betanya a gidan Saminu kuturu, 7 sai wata mace ta zo wurinsa da wani ɗan tandu na man ƙanshi mai tsadar gaske, ta tsiyaye masa a kā, a lokacin da yake cin abinci. 8 Amma da almajiran suka ga haka, sai suka ji haushi suka ce, “Wannan almubazzaranci fa! 9 Da ma an sayar da man nan kuɗi mai yawa, an ba talakawa!” 10 Yesu kuwa da ya lura da haka, sai ya ce musu, “Don me kuke damun matar nan? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa. 11 Kullum kuna tare da talakawa, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba. 12 Zuba man nan da ta yi a jikina, ta yi shi ne domin tanadin jana'izata. 13 Hakika, ina gaya muku, duk inda za a yi bisharar nan a duniya duka, abin da matar nan ta yi za a riƙa faɗarsa don tunawa da ita.”

Yahuza ya Yarda ya Ba da Yesu

14 Sai ɗaya daga cikin sha biyun nan, mai suna Yahuza Iskariyoti, ya je wurin manyan firistoci, 15 ya ce, “Me za ku ba ni, in na bashe shi a gare ku?” Sai suka ƙirga kuɗi azurfa talatin, suka ba shi. 16 Tun daga lokacin nan ne ya riƙa neman hanyar da zai bashe shi.

Yesu ya Ci Idin Ƙetarewa tare da Almajiransa

17 To, a ranar farko ta idin abinci marar yisti sai almajiran suka zo wurin Yesu suka ce, “Ina kake so mu shirya maka cin Idin Ƙetarewa?” 18 Sai ya ce, “Ku shiga gari wurin wāne, ku ce masa, ‘Malam ya ce lokacinsa ya yi kusa, zai ci Idin Ƙetarewa a gidanka tare da almajiransa.’ ” 19 Almajiran kuwa suka yi yadda Yesu ya umarce su, suka shirya Idin Ƙetarewa. 20 Da maraice ya yi, sai ya zauna cin abinci tare da almajiran nan goma sha biyu. 21 Suna cikin cin abinci, sai ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bashe ni.” 22 Sai suka yi baƙin ciki gaya, suka fara ce masa da ɗaya ɗaya, “Ni ne, ya Ubangiji?” 23 Sai ya amsa ya ce, “Wanda muke ci a ƙwarya ɗaya, shi ne zai bashe ni. 24 Ɗan Mutum zai tafi ne, yadda labarinsa yake a rubuce, duk da haka kaiton mutumin nan da yake ba da Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da zai fiye masa.” 25 Sai Yahuza da ya bashe shi ya ce, “Ko ni ne, ya Shugaba?” Yesu ya ce masa, “Ga shi, kai ma ka faɗa.”

Cin Jibin Ubangiji

26 Suna cikin cin abinci, sai Yesu ya ɗauki gurasa, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya ba almajiran, ya ce, “Ungo, ku ci. Wannan jikina ne.” 27 Sai ya ɗauki ƙoƙo kuma, bayan da ya yi godiya ga Allah, sai ya ba su, ya ce, “Dukkanku ku shassha. 28 Wannan jinina ne na tabbatar da alkawari, wanda za a zubar saboda mutane da yawa, domin gafarar zunubansu. 29 Ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranar nan da za mu sha wani sabo tare da ku a Mulkin Ubana.” 30 Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun.

Bitrus zai Yi Musun Sanin Yesu

31 Sai Yesu ya ce musu, “Duk za ku yi tuntuɓe sabili da ni a wannan dare domin a rubuce yake cewa, ‘Zan bugi makiyayi, tumakin garken kuwa za su fasu.’ 32 Amma fa bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa ƙasar Galili.” 33 Bitrus ya ce masa, “Ko duk sun yi tuntuɓe sabili da kai, ni kam ba zan yi tuntuɓe ba faufau.” 34 Yesu ya ce masa, “Hakika, ina gaya maka, ko a wannan dare, kafin carar zakara, za ka yi musun sanina sau uku.” 35 Bitrus ya ce masa, “Ko za a kashe ni tare da kai, ba zan yi musun saninka ba.” Haka ma duk almajiran suka ce.

Yesu ya Yi Addu'a a Gatsemani

36 Sa'an nan Yesu ya zo da su wani wuri da ake kira Gatsemani. Ya ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan, Ni kuwa zan je can in yi addu'a.” 37 Sai ya ɗauki Bitrus da 'ya'yan nan na Zabadi biyu, ya fara baƙin ciki da damuwa ƙwarai. 38 Sai ya ce musu, “Raina yana shan wahala matuƙa, har ma kamar in mutu. Ku dakata a nan, ku zauna a faɗake tare da ni.” 39 Da ya ci gaba kaɗan, sai ya fāɗi a ƙasa, ya yi addu'a ya ce, “Ya Ubana, in mai yiwuwa ne, ka ɗauke mini ƙoƙon wahalar nan. Duk da haka dai ba nufina ba, sai naka.” 40 Ya komo wurin almajiran, ya ga suna barci, sai ya ce wa Bitrus, “Ashe, ba za ku iya zama a faɗake tare da ni ko da na sa'a ɗaya ba? 41 Ku zauna a faɗake, ku yi addu'a, kada ku faɗa ga gwaji. Lalle ruhu ya ɗauka, amma jiki rarrauna ne.” 42 Har wa yau a komawa ta biyu, sai ya je ya yi addu'a, ya ce, “Ya Ubana, in wannan ba zai wuce ba sai na sha shi, to, a aikata nufinka.” 43 Har yanzu dai ya dawo ya ga suna barci, don duk barci ya cika musu ido. 44 Har wa yau ya sāke barinsu, ya koma ya yi addu'a ta uku, yana maimaita maganar dā. 45 Sai ya komo wurin almajiran, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi, kuna hutawa? To, ga shi, lokaci ya yi kusa. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi. 46 Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bashe ni nan, ya matso!”

An Ba da Yesu, an Kama Shi

47 Kafin ya rufe baki ga Yahuza, ɗaya daga cikin sha biyun nan, da babban taron mutane riƙe da takuba da kulake, manyan firistoci da shugabanni ne suka turo su. 48 To, mai bashe shi ɗin ya riga ya ƙulla da su cewa, “Wanda zan yi wa sumba, shi ne mutumin. Ku kama shi.” 49 Nan da nan ya matso wurin Yesu, ya ce, “A gaishe ka, ya Shugaba!” Sai ya yi ta sumbantarsa. 50 Yesu ya ce masa, “Abokina, abin da ya kawo ka ke nan?” Suka matso suka kama Yesu, suka danƙe shi. 51 Sai ga ɗaya daga cikin waɗanda suke tare da Yesu ya miƙa hannu ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne. 52 Sai Yesu ya ce masa, “Mai da takobinka a kubensa. Duk wanda ya zare takobi, takobi ne ajalinsa. 53 Kuna tsammani ba ni da iko in roƙi Ubana nan da nan kuwa ya aiko mini fiye da rundunar mala'iku goma sha biyu? 54 To, ta yaya ke nan za a cika Littattafai a kan lalle wannan abu ya kasance?” 55 Nan take Yesu ya ce wa taron jama'a, “Kun fito ne da takuba da kulake ku kama ni kamar ɗan fashi? Kowace rana nakan zauna a Haikali ina koyarwa, amma ba ku kama ni ba. 56 Amma duk wannan ya auku ne domin a cika littattafan annabawa.” Daga nan duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansu.

Yesu a Gaban 'Yan Majalisa

57 Sai waɗanda suka kama Yesu suka tafi da shi wurin Kayafa, babban firist, inda malaman Attaura da shugabanni suke tare. 58 Amma Bitrus ya bi shi daga nesa, har cikin gidan babban firist. Da ya shiga, sai ya zauna tare da dogaran Haikali, don ya ga ƙarshen abin. 59 To, sai manyan firistoci da 'yan majalisa duka suka nemi shaidar zur da za a yi wa Yesu don su sami dama su kashe shi. 60 Amma ba su samu ba, ko da yake masu shaidar zur da yawa sun zazzaburo. Daga baya sai waɗansu biyu suka matso, 61 suka ce, “Wannan ya ce, zai iya rushe Haikalin nan na Allah, ya kuma gina shi a cikin kwana uku.” 62 Sai babban firist ya miƙe ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan ke yi a kanka fa?” 63 Amma Yesu ya yi shiru. Sai babban firist ya ce masa, “Na gama ka da Allah Rayayye, ka faɗa mana ko kai ne Almasihu, Ɗan Allah.” 64 Sai Yesu ya ce masa, “Yadda ka faɗa. Ina kuwa gaya muku a nan gaba za ku ga Ɗan Mutum zaune a dama da Mai Iko, yana kuma zuwa a kan gajimare.” 65 Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa, ya ce, “Ya yi saɓo! Wace shaida kuma za mu nema? Yanzu kun ji saɓon da ya yi! 66 Me kuka gani?” Suka amsa suka ce, “Ya cancanci kisa!” 67 Sai suka tattofa masa yau a fuska, suka bubbuge shi, waɗansu kuma suka mammare shi, 68 suna cewa, “Yi mana annabci, kai Almasihu! Faɗi wanda ya buge ka!”

Bitrus ya Yi Musun Sanin Yesu

69 To, Bitrus kuwa yana zaune a tsakar gida a waje, sai wata baranya ta zo ta tsaya a kansa, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Yesu Bagalile!” 70 Amma ya yi musu a gabansu duka ya ce, “Ni ban san abin da kike nufi ba.” 71 Da ya fito zaure, sai wata baranya kuma ta gan shi, ta ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Ai, mutumin nan tare yake da Yesu Banazare!” 72 Sai ya sāke yin musu har da rantsuwa ya ce, “Ban ma san mutumin nan ba.” 73 Jim kaɗan sai na tsaitsayen suka matso, suka ce wa Bitrus, “Lalle kai ma ɗayansu ne, don irin maganarka ta tona ka.” 74 Sai ya fara la'anar kansa, yana ta rantse-rantse, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan ba.” Nan da nan sai zakara ya yi cara. 75 Sai Bitrus ya tuna da maganar Yesu cewa, “Kafin carar zakara za ka yi musun sanina sau uku.” Sai ya fita waje, ya yi ta rusa kuka.

Matiyu 27

Yesu a gaban Bilatus

1 Da gari ya waye sai duk manyan firistoci da shugabannin jama'a suka yi shawara a kan Yesu su kashe shi. 2 Sai suka ɗaure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga mai mulki Bilatus.

Mutuwar Yahuza

3 Sa'ad da Yahuza mai bashe shi ya ga an yanke masa hukuncin kisa, sai ya yi nadama, ya mayar wa manyan firistoci da shugabanni da kuɗi azurfa talatin ɗin nan, 4 ya ce, “Na yi zunubi da na ba da marar laifi a kashe shi.” Suka ce, “Ina ruwanmu? Kai ka jiyo!” 5 Sai ya watsar da kuɗin azurfan nan a Haikali, ya fita, ya je ya rataye kansa. 6 Amma manyan firistoci suka tsince kuɗin suka ce, “Bai halatta mu zuba su a Baitulmalin Haikali ba, don kuɗin ladan kisankai ne.” 7 Sai suka yi shawara, suka sayi filin maginin tukwane da kuɗin don makabartar baƙi. 8 Don haka, har ya zuwa yau, ana kiran filin nan filin jini. 9 Ta haka aka cika faɗar Annabi Irmiya cewa, “Sun ɗauki kuɗin azurfa talatin ɗin nan, wato, awalajar shi wannan da waɗansu Isra'ilawa suka yi wa kima, 10 suka sayi filin maginin tukwane da su, yadda Ubangiji ya umurce ni.”

Bilatus ya Tuhumi Yesu

11 To, sai Yesu ya tsaya a gaban mai mulki, mai mulkin kuma ya tambaye shi, “Ashe, kai ɗin nan kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya ce masa, “Yadda ka faɗa.” 12 Amma da manyan firistoci da shugabanni suka kai ƙararrakinsa, bai ce kome ba. 13 Sai Bilatus ya ce masa, “Ba ka ji yawan maganganun da suke ba da shaida a kanka ba?” 14 Amma bai ba shi wata amsa, ko da ta kalma ɗaya ba, har mai mulki ya yi mamaki ƙwarai.

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

15 To, a lokacin idi kuwa mai mulki ya saba sakar wa jama'a kowane ɗaurarre guda da suka so. 16 A lokacin kuwa da wani shahararren ɗan sarƙa, mai suna Barabbas. 17 Da suka taru sai Bilatus ya ce musu, “Wa kuke so in sakar muku? Barabbas ko kuwa Yesu da ake kira Almasihu?” 18 Don ya sani saboda hassada ne suka bashe shi. 19 Banda haka kuma, a lokacin da yake zaune a kan gadon shari'a, sai matarsa ta aiko masa da cewa, “Ka fita daga sha'anin mara laifin nan, don yau na sha wahala ƙwarai a mafarkin da na yi a game da shi.” 20 To, sai manyan firistoci da shugabanni suka rarrashi jama'a su zaɓi Barabbas, Yesu kuwa a kashe shi. 21 Sai mai mulki ya sāke ce musu, “Wane ne a cikin biyun nan kuke so in sakar muku?” Sai suka ce, “Barabbas.” 22 Bilatus ya ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da Yesu da ake kira Almasihu?” Duk sai suka ce, “A gicciye shi!” 23 Ya ce, “Ta wane halin? Wane mugun abu ya yi?” Amma su sai ƙara ɗaga murya suke ta yi, suna cewa, “A gicciye shi!” 24 Da Bilatus ya ga bai rinjaye su ba, sai dai hargitsi yana shirin tashi, sai ya ɗibi ruwa ya wanke hannunsa a gaban jama'a, ya ce, “Ni kam, na kuɓuta daga alhakin jinin mai adalcin nan. Wannan ruwanku ne.” 25 Sai duk jama'a suka amsa suka ce, “Alhakin jininsa a wuyarmu, mu da 'ya'yanmu!” 26 Sa'an nan ya sakar musu Barabbas. Bayan ya yi wa Yesu bulala, sai ya ba da shi a gicciye shi.

Sojoji sun Yi wa Yesu Ba'a

27 Sai sojan mai mulki suka kai Yesu cikin fadar mai mulki, suka tara dukan ƙungiyar soja a kansa. 28 Sai suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar alkyabba. 29 Suka yi wani rawani na ƙaya, suka sa masa a kā, suka danƙa masa sanda a hannunsa na dama, suka kuma durƙusa a gabansa, suna yi masa ba'a suna cewa, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!” 30 Suka tattofa masa yau, suka karɓe sandan, suka ƙwala masa a ka. 31 Da suka gama yi masa ba'a, sai suka yaye masa alkyabbar, suka sa masa nasa tufafi, suka tafi da shi domin su gicciye shi.

An Gicciye Yesu

32 Suna tafiya ke nan, sai suka gamu da wani Bakurane, mai suna Saminu. Shi ne suka tilasta wa ya ɗauki gicciyen Yesu. 33 Da suka isa wurin da ake kira Golgota, wato, wurin ƙoƙwan kai, 34 suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha, amma da ya ɗanɗana sai ya ƙi sha. 35 Da suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu ta jefa kuri'a. 36 Suka zauna a nan suna tsaronsa. 37 A daidai kansa aka kafa sanarwar laifinsa cewa, “Wannan shi ne Yesu, Sarkin Yahudawa.” 38 Sai kuma aka gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a dama, ɗaya a hagun. 39 Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, 40 suna cewa, “Kai da za ka rushe Haikalin, ka kuma gina shi a cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, to sauko daga gicciyen mana!” 41 Haka kuma manyan firistoci da malaman Attaura da shugabanni suka riƙa yi masa ba'a, suna cewa, 42 “Ya ceci waɗansu, ya kuwa kasa ceton kansa. Ai, Sarkin Isra'ila ne, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mā gaskata da shi. 43 Yā dogara ga Allah, to, Allah ya cece shi mana yanzu, in dai yana sonsa, don ya ce shi Ɗan Allah ne.” 44 Har 'yan fashin nan da aka gicciye su tare ma, su suka zazzage shi kamar waɗancan.

Mutuwar Yesu

45 To, tun daga tsakar rana, duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma. 46 Wajen ƙarfe uku kuma sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāni?” Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?” 47 Da waɗansu ɗa suke tsaitsayen suka ji haka, sai suka ce, “Mutumin nan na kiran Iliya ne.” 48 Sai nan da nan ɗaya daga cikinsu ya yiwo gudu, ya ɗauko soso ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha. 49 Amma sauran suka ce, “Ku bari mu gani ko Iliya zai zo ya ceci shi.” 50 Sai Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sa'an nan ya săki ransa. 51 Sai labulen da yake cikin Haikalin ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta yi girgiza, duwatsu kuma suka tsattsage. 52 Aka bubbuɗe kaburbura, tsarkaka da yawa da suke barci kuma suka tashi. 53 Suka firfito daga kaburburan, bayan ya tashi daga matattu, sai suka shiga tsattsarkan birnin, suka bayyana ga mutane da yawa. 54 Sa'ad da jarumin da waɗanda suke tare da shi suna tsaron Yesu suka ga rawar ƙasa da kuma abin da ya auku, sai duk tsoro ya kama su, suka ce, “Hakika wannan Ɗan Allah ne!” 55 Akwai kuma waɗansu mata da yawa a can suna hange daga nesa, waɗanda suka biyo Yesu tun daga ƙasar Galili, suna yi masa hidima. 56 A cikinsu da Maryamu Magadaliya, da Maryamu mahaifiyar Yakubu da Yusufu, da kuma mahaifiyar 'ya'yan Zabadi.

Jana'izar Yesu

57 Maraice lis sai wani mai arziki ya zo, mutumin Arimatiya, mai suna Yusufu, shi ma almajirin Yesu ne. 58 Ya je wurin Bilatus ya roƙa a ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya yi umarni a ba shi. 59 Yusufu ya ɗauki jikin, ya sa shi a likkafanin lilin mai tsabta, 60 ya sa shi a wani sabon kabari da ya tanadar wa kansa, wanda ya fafe a jikin dutse. Sai ya mirgina wani babban dutse a bakin kabarin, ya tafi. 61 Maryamu Magadaliya da ɗaya Maryamun suna nan zaune a gaban kabarin.

Masu Tsaron Kabarin

62 Kashegari, wato, bayan ranar shiri, sai manyan firistoci da Farisiyawa suka taru a gaban Bilatus, 63 suka ce, “Ya mai girma, mun tuna yadda mayaudarin nan, tun yana da rai ya ce bayan kwana uku zai tashi daga matattu. 64 Saboda haka sai ka yi umarni a tsare kabarin nan sosai har rana ta uku, kada almajiransa su sace shi, sa'an nan su ce wa mutane ya tashi daga matattu. Yaudarar ƙarshe za ta fi ta farkon muni ke nan.” 65 Sai Bilatus ya ce musu, “Shi ke nan, ku ɗibi soja, ku je ku tsare shi iyakar ƙoƙarinku.” 66 Sai suka tafi suka tsare kabarin, suka buga wa dutsen nan hatimi, suka kuma sa sojan tsaro.

Matiyu 28

Tashin Yesu daga Matattu

1 To, bayan Asabar, da asussuba a ranar farko ta mako, sai Maryamu Magadaliya da ɗaya Maryamun, suka je ganin kabarin. 2 Sai kuwa aka yi wata babbar rawar ƙasa, domin wani mala'ikan Ubangiji ne ya sauko daga Sama, ya zo ya mirgine dutsen, ya zauna a kai. 3 Kamanninsa suna haske kamar walƙiya, tufafinsa kuma farare fat kamar alli. 4 Saboda tsoronsa sai masu tsaro suka ɗau makyarkyata, har suka yi kamar sun mutu. 5 Amma sai mala'ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na sani Yesu kuke nema, wanda aka gicciye. 6 Ai, ba ya nan. Ya tashi, yadda ya faɗa. Ku zo ku ga wurin da aka sa shi. 7 Ku tafi maza ku gaya wa almajiransa, cewa, ya tashi daga matattu. Ga shi kuma, zai riga ku zuwa ƙasar Galili, a can ne za ku gan shi. Ga shi, na gaya muku.” 8 Sai suka tashi daga kabarin da gaggawa da tsoro, game da matuƙar farin ciki, suka ruga a guje domin su kai wa almajiransa labari. 9 Sai kuwa ga Yesu ya tarye su, ya ce, “Salama a gare ku!” Suka matso suka rungume ƙafafunsa, suka yi masa sujada. 10 Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku je ku gaya wa 'yan'uwana su tafi ƙasar Galili, a can ne za su gan ni.”

Rahoton Masu Tsaron Kabarin

11 Suna tafiya ke nan, sai waɗansu daga cikin sojan nan suka shiga birni, suka ba manyan firistoci labarin da ya auku. 12 Su kuwa da suka taru da shugabannin jama'a suka yi shawara, sai suka ba sojan kuɗi masu tsoka, 13 suka ce, “Ku faɗa wa mutane almajiransa ne suka zo da daddare suka sace shi kuna barci. 14 In kuwa labarin nan ya kai ga kunnen mai mulki, mā rarrashe shi, mu tsare ku daga wahala.” 15 Sai suka karɓi kuɗin, suka yi yadda aka koya musu. Wannan magana kuwa, ta bazu cikin Yahudawa har ya zuwa yau.

Umarnin Yesu ga Goma Sha Ɗayan

16 To, almajirai goma sha ɗayan nan suka tafi ƙasar Galili, suka je dutsen da Yesu ya umarce su. 17 Da suka gan shi, suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka. 18 Sai Yesu ya matso, ya ce musu, “An mallaka mini dukkan iko a Sama da ƙasa. 19 Don haka sai ku je ku almajirtar da dukkan al'ummai, kuna yi musu baftisma da sunan Uba, da Ɗa, da Ruhu Mai Tsarki, 20 kuna koya musu su kiyaye duk iyakar abin da na umarce ku. Ga shi, ni kuma kullum ina tare da ku har ya zuwa matuƙar zamani.”

Markus 1

Wa'azin Yahaya Maibaftisma

1 Farkon bisharar Yesu Almasihu, Ɗan Allah, ke nan. 2 Yadda yake a rubuce a littafin Annabi Ishaya cewa, “Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba, Wanda zai shirya maka hanya. 3 Muryar mai kira a jeji tana cewa, Ku shirya wa Ubangiji tafarki, Ku miƙe hanyoyinsa.” 4 Yahaya Maibaftisma ya bayyana a jeji, yana wa'azi mutane su tuba a yi musu baftisma domin a gafarta musu zunubansu. 5 Sai duk mutanen ƙasar Yahudiya, da dukan mutanen Urushalima suka yi ta zuwa wurinsa, suna bayyana zunabansu, yana yi musu baftisma a Kogin Urdun. 6 Yahaya kuwa yana sanye da tufar gashin raƙumi, yana kuma ɗaure da ɗamara ta fata, abincinsa kuwa fara ce da ruwan zuma. 7 Ya yi wa'azi ya ce, “Wani yana zuwa bayana wanda ya fi ni girma, wanda ko takalminsa ma ban isa in sunkuya in kwance ba. 8 Ni da ruwa na yi muku baftisma, amma shi da Ruhu Mai Tsarki zai yi muku.”

An Yi wa Yesu Baftisma

9 Sai ya zamana a wannan lokaci Yesu ya zo daga Nazarat ta ƙasar Galili. Yahaya ya yi masa baftisma a Kogin Urdun. 10 Da fitowarsa daga ruwan sai ya ga sama ta dāre, Ruhu yana sauko masa kamar kurciya. 11 Aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Kai ne Ɗana ƙaunataccena, ina farin ciki da kai ƙwarai.”

Shaiɗan ya Gwada Yesu

12 Nan da nan sai Ruhu ya iza shi jeji. 13 Yana jeji har kwana arba'in, Shaiɗan yana gwada shi, yana tare da namomin jeji, mala'iku kuma suna yi masa hidima.

Yesu ya Fara Aiki a Galili

14 To, bayan an tsare Yahaya, sai Yesu ya shigo ƙasar Galili, yana yin bisharar Allah, 15 yana cewa, “Lokaci ya yi, Mulkin Allah ya kusato. Ku tuba, ku gaskata da bishara.”

Yesu ya Kira Masunta Huɗu

16 Yana wucewa ta bakin Tekun Galili, sai ya ga Bitrus da Andarawas ɗan'uwansa, suna jefa taru a teku, don su masunta ne. 17 Yesu ya ce musu, “Ku bi ni, zan mai da ku masuntan mutane.” 18 Nan da nan kuwa suka bar tarunansu suka bi shi. 19 Da ya ci gaba kaɗan, sai ya ga Yakubu ɗan Zabadi, da ɗan'uwansa Yahaya, suna cikin jirginsu suna gyaran taru. 20 Nan da nan da ya kira su, suka bar mahaifinsu Zabadi a cikin jirgin tare da ma'aikata, suka bi shi.

Mai Baƙin Aljan

21 Suka shiga Kafarnahum. Ran Asabar ne kuwa, ya shiga majami'a yana koyarwa. 22 Sun yi mamakin koyarwarsa, domin yana koya musu da Iko, ba kamar malaman Attaura ba. 23 Nan take sai ga wani mutum mai baƙin aljan a majami'arsu, yana ihu, 24 yana cewa, “Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne ka hallaka mu? Na san ko wane ne kai, Mai tsarkin nan ne na Allah.” 25 Yesu ya kwaɓe shi ya ce, “Yi shiru! fita daga cikinsa!” 26 Sai baƙin aljanin ya buge shi, jikinsa yana rawa, ya yi ihu, ya fita daga cikinsa. 27 Duk suka yi mamaki, har suka tanttambayi juna suna cewa, “Kai, mene ne haka? Tabɗi! Yau ga baƙuwar koyarwa! Har baƙaƙen aljannu ma yake yi wa umarni gabagaɗi, suna kuwa yi masa biyayya!” 28 Nan da nan sai ya shahara a ko'ina duk kewayen ƙasar Galili.

Yesu ya Warkar da Surukar Bitrus

29 Da fitarsu daga majami'a, sai suka shiga gidan su Bitrus da Andarawas, tare da Yakubu da Yahaya. 30 Surukar Bitrus kuwa tana kwance tana zazzaɓi, nan da nan suka ba shi labarinta. 31 Sai ya matso, ya kama hannunta, ya tashe ta, zazzaɓin kuwa ya sake ta, har ta yi musu hidima.

Yesu ya Warkar da Mutane da yawa da Maraice

32 Da magariba, bayan fāɗuwar rana, aka kakkawo masa dukan marasa lafiya, da masu aljannu. 33 Sai duk garin ya haɗu a ƙofar gidan. 34 Ya warkar da marasa lafiya da yawa, masu cuta iri iri, ya kuma fitar wa mutane aljannu da yawa. Bai ko yarda aljannun su yi wata magana ba, domin sun san shi.

Yesu ya Tafi Yin Wa'azi

35 Da assussuba ya tashi ya fita, ya tafi wani wuri inda ba kowa, ya yi addu'a a can. 36 Sai Bitrus da waɗanda suke tare da shi suka bi shi. 37 Da suka same shi, suka ce masa, “Duk ana nemanka.” 38 Ya ce musu, “Mu tafi garuruwan da suke gaba, in yi wa'azi a can kuma, domin saboda haka ne na fito.” 39 Ya gama ƙasar Galili duk yana wa'azi a majami'unsu, yana kuma fitar wa mutane da aljannu.

Yesu ya Warkar da Kuturu

40 Wani kuturu ya zo wurinsa, yana roƙonsa, yana durƙusawa a gabansa, yana cewa, “In ka yarda kana da iko ka tsarkake ni.” 41 Da tausayi ya kama Yesu, sai ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce masa, “Na yarda, ka tsarkaka.” 42 Nan take sai kuturtar ta rabu da shi, ya tsarkaka. 43 Ya kwaɓe shi ƙwarai, ya sallame shi nan da nan, 44 bayan ya ce masa, “Ka kula fa, kada ka gaya wa kowa kome. Sai dai ka je wurin firist ya gan ka, ka kuma yi hadaya saboda tsarkakewarka domin tabbatarwa a gare su, kamar yadda Musa ya umarta.” 45 Amma ya tafi, ya shiga sanar da maganar, yana baza labarin al'amarin ko'ina, har ya zamana Yesu bai ƙara shiga wani gari a sarari ba, sai ya zauna a waje a wuraren da ba kowa. Mutane kuwa suka yi ta zuwa wurinsa daga ko'ina.

Markus 2

Yesu ya Warkar da Shanyayye

1 Bayan 'yan kwanaki, da ya sāke komowa Kafarnahum, sai aka ji labari yana gida. 2 Aka kuwa taru maƙil har ba sauran wuri, ko a bakin ƙofa. Shi kuwa yana yi musu wa'azin Maganar Allah. 3 Sai suka kawo masa wani shanyayye, mutum huɗu suna ɗauke da shi. 4 Da suka kāsa kusatarsa don yawan mutane, suka buɗe rufin soron ta sama da shi. Da suka huda ƙofa kuwa, suka zura gadon da shanyayyen yake kwance a kai. 5 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, an gafarta maka zunubanka.” 6 To, waɗansu malaman Attaura suna nan zaune, suna ta waswasi a zuciyarsu, 7 suna cewa, “Don me mutumin nan yake faɗar haka? Ai, sāɓo yake yi! Wa yake da ikon gafarta zunubi in banda Allah kaɗai?” 8 Nan da nan, da Yesu ya gane a ransa suna ta wuswasi haka a zuci, sai ya ce musu, “Don me kuke a waswasi haka a zuciyarku? 9 Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta maka zunubanka’, ko kuwa a ce, ‘Tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka yi tafiya?’ 10 Amma don ku sakankance Ɗan Mutum yana da ikon gafarta zunubi a duniya”�sai ya ce wa shanyayyen� 11 “Na ce maka, tashi ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi gida.” 12 Sai ya tashi nan da nan, ya ɗauki shimfiɗarsa, ya fita a kan idon kowa, har suka yi mamaki duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin irin haka ba!”

Kiran Lawi

13 Yesu ya sāke fita bakin teku. Duk jama'a suka yi ta zuwa wurinsa, yana koya musu. 14 Yana cikin wucewa, sai ya ga Lawi ɗan Halfa a zaune yana aiki a wurin karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai ya tashi ya bi shi. 15 Wata rana Yesu yana cin abinci a gidan Lawi, masu karɓar haraji da masu zunubi da yawa kuma suna ci tare da shi da almajiransa, don kuwa da yawa daga cikinsu masu binsa ne; 16 da malaman Attaura na Farisiyawa suka ga yana cin abinci tare da masu zunubi da masu karɓar haraji, sai suka ce wa almajiransa, “Don me yake ci yake sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?” 17 Da Yesu ya ji haka, ya ce musu, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da likita, sai dai marasa lafiya. Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai dai masu zunubi.”

Tambaya a kan Azumi

18 To, almajiran Yahaya da na Farisiyawa suna azumi, sai aka zo aka ce masa, “Don me almajiran Yahaya da na Farisiyawa suke azumi, amma naka almajirai ba sa yi?” 19 Sai Yesu ya ce musu, “Ashe, abokan ango za su yi azumi tun ango yana tare da su? Ai, muddin suna tare da angon, ba za su yi azumi ba. 20 Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa'an nan ne fa za su yi azumi. 21 Ba mai mahon tsohuwar tufa da sabon ƙyalle. In ma an yi, ai, sai sabon ƙyallen ya kece tsohuwar tufar, har ma ta fi dā kecewa. 22 Ba kuma mai ɗura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ma an ɗura, sai ruwan inabin ya fasa salkunan, a kuma yi hasararsa da ta salkunan. Sabon ruwan inabi, ai sai sababbin salkuna.”

Almajirai suna Zagar Alkama Ran Asabar

23 Wata rana ran Asabar, yana ratsa gonakin alkama, suna cikin tafiya sai almajiransa suka fara zagar alkamar. 24 Farisiyawa suka ce masa, “Duba! Don me suke yin abin da bai halatta a yi ran Asabar ba?” 25 Sai ya ce musu, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa'ad da ya matsu da yunwa, shi da abokan tafiyarsa? 26 Yadda ya shiga masujadar Allah a zamanin Abiyata babban firist, ya ci keɓaɓɓiyar gurasar nan, wadda bai halatta kowa ya ci ba, sai firistoci kaɗai, har ma ya ba abokan tafiyarsa?” 27 Sai ya ce musu, “Ai, Asabar domin mutum aka yi ta, ba mutum aka yi domin Asabar ba. 28 Saboda haka Ɗan Mutum shi ne Ubangijin har ma da na ranar Asabar.”

Markus 3

Mai Shanyayyen Hannu

1 Sai ya sāke shiga majami'a. Akwai wani mutum a nan kuwa mai shanyayyen hannu. 2 Sai suka yi haƙwansa su ga ko zai warkar da shi ran Asabar, don su samu su kai ƙararsa. 3 Sai ya ce wa mai shanyayyen hannun, “Fito nan fili.” 4 Ya ce musu, “Ya halatta ran Asabar a yi alheri ko kuwa mugunta? A ceci rai, ko kuwa a kashe shi?” Amma sai suka yi shiru. 5 Da ya duddube su da fushi, yana baƙin ciki da taurin zuciyarsu, sai ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Sai ya miƙa, hannunsa kuwa ya koma lafiyayye. 6 Da Farisiyawa suka fita, nan da nan sai suka yi shawara da mutanen Hirudus a kansa, yadda za su hallaka shi.

Taro Mai Yawa a Bakin Teku

7 Sai Yesu ya tashi tare da almajiransa, suka je bakin tekun. Taro mai yawan gaske kuwa daga ƙasar Galili ya biyo shi, har ma daga ƙasar Yahudiya, 8 da Urushalima, da ƙasar Edom, da hayin Kogin Urdun, da kuma wajen Taya da Sidon, babban taro ya zo wurinsa, don sun ji labarin duk abin da yake yi. 9 Don gudun kada taron ya marmatse shi kuwa, sai ya ce wa almajiransa su keɓe masa ƙaramin jirgi guda, 10 saboda ya riga ya warkar da mutane da yawa, har ya kai ga duk masu cuta suna dannowa wurinsa domin su taɓa shi. 11 Baƙaƙen aljannu kuwa, duk sa'ad da suka gan shi, sai su fāɗi gabansa suna kururuwa, suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne.” 12 Sai ya kwaɓe su ƙwarai kada su bayyana shi.

Yesu ya Zaɓi Almajirai Sha Biyu

13 Ya hau dutse, ya kira waɗanda yake so, suka je wurinsa. 14 Ya zaɓi mutum goma sha biyu su zauna tare da shi domin ya riƙa aikensu suna wa'azi. 15 Ya kuma ba su ikon fitar da aljannu. 16 Ga waɗanda ya zaɓa, Bitrus, 17 da Yakubu ɗan Zabadi, da kuma ɗan'uwansa Yahaya, ya sa musu suna Buwanarjis, wato, 'ya'yan tsawa. 18 Sai kuma Andarawas, da Filibus, da Bartalamawas, da Matiyu, da Toma, da Yakubu ɗan Halfa, da Yahuza, da Saminu Bakan'ane, 19 da kuma Yahuza Iskariyoti wanda ya bāshe shi.

Yesu da Ba'alzabul

Sa'an nan ya shiga wani gida. 20 Taron kuwa ya sāke haɗuwa har ya hana su cin abinci. 21 Da 'yan'uwansa suka ji haka, sai suka fita su kamo shi, saboda sun ce, “Ai, ya ruɗe.” 22 Malaman Attaura kuwa da suka zo daga Urushalima sai suka ce, “Ai, Ba'alzabul ne ya hau shi, da ikon sarkin aljannu kuma yake fitar da aljannu.” 23 Sai Yesu ya kira su, ya ba su misali da cewa, “Ina Shaiɗan zai iya fitar da Shaiɗan? 24 Ai, in mulki ya rabu a kan gāba, wannan mulki ba zai ɗore ba. 25 Haka in gida ya rabu a kan gāba, wannan gida ba zai ɗore ba. 26 Shaiɗan kuma in ya tayar wa kansa, ya rabu, ba zai ɗore ba, ƙarewarsa ce ta zo. 27 Ba mai iya shiga gidan ƙaƙƙarfan mutum ya washe kayansa, sai ko ya fara ɗaure ƙaƙƙarfan mutumin, sa'an nan kuma ya washe gidansa. 28 “Hakika, ina gaya muku, za a gafarta wa 'yan adam duk zunubansu, da kowane sāɓon da suka hurta, 29 amma fa, duk wanda ya sāɓi Ruhu Mai Tsarki ba ya samun gafara har abada, ya yi madawwamin zunubi ke nan.” 30 Wannan kuwa don sun ce, “Yana da baƙin aljan ne.”

Mahaifiyar Yesu da 'Yan'uwansa

31 Sa'an nan mahaifiyarsa da 'yan'uwansa suka zo. Suna tsaye a waje, sai suka aika masa ya je. 32 Taro kuwa yana zaune kewaye da shi, sai suka ce masa, “Ga tsohuwarka da 'yan'uwanka suna nemanka a waje.” 33 Ya amsa musu ya ce, “Su wane ne tsohuwata da 'yan'uwana?” 34 Sai ya waiwayi waɗanda suke zaune kewaye da shi, ya ce, “Ga tsohuwata a nan da 'yan'uwana! 35 Ai, kowa ya yi abin da Allah ke so, shi ne ɗan'uwana, ita ce 'yar'uwata, ita ce kuma tsohuwata.”

Markus 4

Misali da Mai Shuka

1 Ya kuma fara koyarwa a bakin teku ke nan, sai babban taro ya haɗu a wurinsa, har ya kai shi ga shiga jirgi a tekun, ya kuwa zauna a ciki. Duk taron kuwa yana kan tudu a bakin tekun. 2 Sai ya koya musu abubuwa da yawa da misalai. A cikin koyarwarsa har ya ce musu, 3 “Ku saurara! Wani mai shuka ya tafi shuka. 4 Yana cikin yafa iri, sai waɗansu ƙwayoyi suka fāɗa a hanya, tsuntsaye kuma suka zo suka tsince su. 5 Waɗansu kuma suka fāɗa a wuri mai duwatsu inda ba ƙasa da yawa. Nan da nan kuwa suka tsiro saboda rashin zurfin ƙasa. 6 Da rana fa ta ɗaga, sai suka yanƙwane, da yake ba su da saiwa sosai, suka bushe. 7 Waɗansu kuma suka fāɗa cikin ƙaya, sai ƙayar ta tashi ta sarƙe su, ba su yi tsaba ba. 8 Waɗansu kuma suka fāɗa a ƙasa mai kyau, suka yi yabanya, suka girma, suka yi tsaba, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.” 9 Sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Manufar Misalan

10 Da suka kaɗaita, masu binsa da su goma sha biyun nan suka tambaye shi ma'anar misalan. 11 Sai ya ce musu, “Ku kam, an yardar muku ku san asirin Mulkin Allah, amma ga waɗanda ba sa cikinku, kome sai a cikin misali, 12 don gani da ido kam, za su gani, amma ba da zuci ba. Ji kuma, za su ji, amma ba za su fahimta ba, don dai kada su juyo a yafe musu.”

Yesu ya Ba da Bayanin Misalin Mai Shuka

13 Ya ce musu, “Ashe, ba ku fahimci wannan misali ba? Ƙaƙa za ku fahimci sauran ke nan? 14 Mai shukan nan fa Maganar Allah yake shukawa. 15 Waɗanda suka fāda a hanya kuwa, su ne kwatancin waɗanda aka shuka Maganar a zuciyarsu. Da zarar sun ji, nan da nan sai Shaiɗan ya zo ya ɗauke Maganar da aka shuka a zuciyarsu. 16 Haka kuma waɗanda aka shuka a wuri mai duwatsu, su ne waɗanda da zarar sun ji Maganar sai su karɓa da farin ciki. 17 Su kam ba su da tushe, rashin ƙarƙo gare su, har in wani ƙunci ko tsanani ya faru domin wannan Magana, nan da nan sai su yi tuntuɓe. 18 Waɗansu kuma su ne kwatancin waɗanda suka fāɗa cikin ƙaya, su ne waɗanda suke jin Maganar, 19 amma taraddadin duniya, da jarabar dukiya, da kuma kwaɗayin waɗansu abubuwa, sukan shiga su sarƙe Maganar, har ta zama marar amfani. 20 Waɗanda aka shuka a ƙasa mai kyau kuwa, su ne kwatancin waɗanda suke jin Maganar, su karɓa, su kuma amfana, waɗansu riɓi talatin talatin, waɗansu sittin sittin, waɗansu ma har ɗari ɗari.”

Fitila a Rufe da Masaki

21 Sai ya ce musu, “Shin, ana kawo fitila don a rufe ta da masaki, ko a ajiye ta a ƙarƙashin gado ne, ba don a ɗora ta a kan maɗorinta ba? 22 Ba abin da yake ɓoye, sai domin a bayyana shi a gaba. Ba kuma wani abin da yake asirce, sai domin a bayyana shi a gaba. 23 In da mai kunnen ji, yă ji.” 24 Sai ya ce musu, “Ku ji. Mudun da ka auna, da shi za a auna maka, har ma a ƙara. 25 Domin mai abu akan ƙara wa. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa.”

Misali na Irin da ya Tsiro

26 Ya ce kuma, “Mulkin Allah kamar mutum yake mai yafa iri a ƙasa. 27 A kwana a tashi har irin ya tsiro, ya girma, bai kuwa san ta yadda aka yi ba. 28 Ƙasa da kanta takan ba da amfani, tsiro shi na farko, sa'an nan kai, sai kuma ƙwaƙƙwarar ƙwaya a kan. 29 Sa'ad da amfani ya nuna, sai ya sa lauje ya yanke nan da nan, wato, kaka ta yi ke nan.”

Misali na Ƙwayar Mastad

30 Ya kuma ce, “Da me za mu kwatanta Mulkin Allah? Ko kuwa da wane misali za mu misalta shi? 31 Kamar ƙwayar mastad yake, wadda, in an shuka ta, ko da yake ita ce mafi ƙanƙantar ƙwayoyi a duniya, 32 duk da haka in an shuka ta, sai ta girma ta fi duk sauran ganye, ta yi manyan rassa, har tsuntsaye su iya sauka a inuwarta.”

Yesu ya Yi Amfani da Misalai

33 Da misalai da yawa irin waɗannan Yesu ya yi musu Maganar Allah, daidai gwargwadon ganewarsu. 34 Ba ya faɗa musu kome sai da misali, amma a keɓe yakan bayyana wa almajiransa kome.

Yesu ya Tsawata wa Hadiri

35 A ran nan da maraice ya ce musu, “Mu haye can ƙetare.” 36 Da suka bar taron, suka tafi da shi yadda yake a cikin jirgin, waɗansu jirage kuma suna tare da shi. 37 Sai babban hadari mai iska ya taso, raƙuman ruwa kuma suna ta fantsama cikin jirgin, har jirgin ya tasar wa cika da ruwa. 38 Yesu kuwa yana daga ƙarshen baya na jirgin a kan matashi, yana barci. Sai suka tashe shi, suka ce masa, “Malam, za mu hallaka ba ka kula ba ko?” 39 Sai ya farka, ya tsawata wa iskar, ya kuma ce wa ruwan tekun, “Natsu! Ka yi shiru!” Sai iskar ta kwanta, wurin duk ya yi tsit. 40 Ya ce musu, “Don me kuka firgita haka? Har yanzu ba ku da bangaskiya ne?” 41 Sai suka tsorata, matuƙar tsoro, suka ce wa juna, “Wa ke nan kuma, wanda har iska da ruwan teku ma suke yi masa biyayya?”

Markus 5

Warkar da Mai Aljan na Garasinawa

1 Suka iso hayin teku a ƙasar Garasinawa. 2 Da saukarsa daga jirgin, sai ga wani mai baƙin aljan daga makabarta ya tarye shi. 3 Shi kuwa makabarta ce mazauninsa. Ba mai iya ɗaure shi kuma, ko da sarƙa ma. 4 Don dā an sha ɗaure shi da mari da sarƙa, amma ya tsintsinka sarƙar, ya gutsuntsuna marin, har ma ba mai iya bi da shi. 5 Kullum kuwa dare da rana yana cikin makabarta, da kan duwatsu, yana ta ihu, yana kukkuje jikinsa da duwatsu. 6 Da dai ya hango Yesu, sai ya sheƙo a guje ya fāɗi a gabansa, 7 ya ƙwala ihu ya ce, “Ina ruwanka da ni, Yesu Ɗan Allah Maɗaukaki? Na gama ka da Allah, kada ka yi mini azaba.” 8 Ya faɗi haka ne domin Yesu ya ce masa, “Rabu da mutumin nan, kai wannan baƙin aljan!” 9 Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa ya ce, “Sunana Tuli, don muna da yawa.” 10 Sai ya roƙi Yesu da gaske kada ya kore su daga ƙasar. 11 To, wurin nan kuwa akwai wani babban garken alade suna kiwo a gangaren dutsen. 12 Aljannun nan suka roƙe shi suke ce, “Tura mu wajen aladun nan, mu shiga cikinsu.” 13 Ya kuwa yardar musu. Sai baƙaƙen aljannun suka fita, suka shiga aladun. Garken kuwa wajen alade dubu biyu, suka rugunguta ta gangaren, suka fāɗa tekun, suka hallaka a ruwa. 14 Daga nan sai 'yan kiwon aladun suka gudu, suka ba da labari birni da ƙauye. Jama'a suka zo su ga abin da ya auku. 15 Da suka zo wurin Yesu suka ga mai aljannun nan a zaune, sanye da tufa, cikin hankalinsa kuma, wato, mai aljannun nan masu yawa a dā, sai suka tsorata. 16 Waɗanda aka yi abin a kan idonsu kuwa, suka farfaɗi abin da ya gudana ga mai aljannun da kuma aladun. 17 Sai suka fara roƙon Yesu ya bar musu ƙasarsu. 18 Yana shiga jirgi ke nan, sai mai aljannun nan a dā ya roƙe shi izinin zama a gunsa. 19 Amma Yesu bai yardar masa ba, ya ce masa, “Tafi gida wurin 'yan'uwanka, ka faɗa musu irin manyan abubuwan da Ubangiji ya yi maka, da kuma yadda ya ji tausayinka.” 20 Sai ya tafi, ya shiga baza labari a Dikafolis na irin manyan abubuwan da Yesu ya yi masa. Duk mutane kuwa suka yi al'ajabi.

Warkar da 'Yar Yayirus da Matar da ta Taɓa Gezar Mayafin Yesu

21 Da Yesu ya sāke haye ƙetare cikin jirgi, sai babban taro ya kewaye shi. Shi kuwa yana bakin tekun. 22 Sai ga wani daga cikin shugabannin majami'a, mai suna Yayirus. Da ganin Yesu kuwa sai ya fāɗi a gabansa, 23 ya roƙe shi da gaske, yana cewa, “Ƙaramar 'yata tana bakin mutuwa. Idan za ka yarda ka zo ka ɗora mata hannu, sai ta warke ta rayu.” 24 Sai suka tafi tare. Babban taro kuwa yana biye da shi, suna matsarsa. 25 Sai ga wata mace wadda ta yi shekara goma sha biyu tana zub da jini, 26 ta kuma sha wahala ƙwarai da gaske a hannun masu magani da yawa, har ta ɓad da duk abin da take da shi, amma duk a banza, sai ma gaba-gaba cutar take yi. 27 Da ta ji labarin Yesu, ta raɓo ta bayansa cikin taron, ta taɓa mayafinsa. 28 Don tā ce a ranta, “Ko da tufarsa ma na taɓa, sai in warke.” 29 Nan take zubar jininta ta tsaya, ta kuma ji a jikinta an warkar da cutarta. 30 Nan da nan kuwa da Yesu ya ji wani iko ya fita daga gare shi, sai ya waiwaya a cikin taron, ya ce, “Wa ya taɓa tufata?” 31 Sai almajiransa suka ce masa, “Kana ganin taro yana matsarka, ka ce, wa ya taɓa ka?” 32 Sai Yesu ya juya domin ya ga wadda ta yi haka. 33 Matar kuwa da ta san abin da aka yi mata, sai ta zo a tsorace, tana rawar jiki, ta fāɗi a gabansa, ta faɗa masa ƙashin gaskiya. 34 Sai ya ce mata, “'Yata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya, ki warke daga cutarki.” 35 Yana cikin magana, sai ga waɗansu daga gidan shugaban majami'a suka ce, “Ai, 'yarka ta rasu, me kuma za ka wahalar da Malamin?” 36 Amma Yesu bai kula da abin da suka faɗa ba, ya ce wa shugaban majami'a, “Kada ka ji tsoro, ka ba da gaskiya kawai.” 37 Bai bar kowa ya bi shi ba sai Bitrus, da Yakubu, da kuma Yahaya ɗan'uwan Yakubu. 38 Da suka isa gidan shugaban majami'a, ya ji ana hayaniya, ana kuka, ana kururuwa ba ji ba gani. 39 Da shigarsa sai ya ce musu, “Don me kuke hayaniya kuna kuka haka? Ai, yarinyar ba matacciya take ba, barci take yi.” 40 Sai suka yi masa dariyar raini. Shi kuma bayan ya fitar da su duka waje, sai ya ɗauki mahaifin yarinyar, da mahaifiyarta, da kuma waɗanda suke tare da shi, ya shiga inda yarinyar take. 41 Ya rike hannunta, ya ce mata, “Talita ƙumi,” wato, “Ke yarinya, ina ce miki, tashi.” 42 Nan take yarinyar ta tashi ta yi tafiya, domin 'yar shekara goma sha biyu ce. Nan da nan kuwa mamaki ya kama su. 43 Sai ya kwaɓe su matuƙa kada kowa ya ji wannan labari. Ya kuma yi umarni a ba ta abinci.

Markus 6

An Ƙi Yesu a Nazarat

1 Ya tashi daga nan ya koma garinsu, almajiransa kuwa suka bi shi. 2 Da Asabar ta yi, sai ya fara koyarwa a majami'a. Mutane da yawa da suka saurare shi, suka yi mamaki, suna cewa, “Ina mutumin nan ya sami wannan abu duka? Wace hikima ce aka ba shi haka? Dubi irin waɗannan mu'ujizan da ake aikatawa ta hannunsa! 3 Shin, wannan ba shi ne masassaƙin nan ba, ɗan Maryamu, ɗan'uwan su Yakubu, da Yusufu, da Yahuza, da kuma Saminu? 'Yan'uwansa mata kuma ba ga su tare da mu ba?” Suka yi tuntuɓe sabili da shi. 4 Sai Yesu ya ce musu, “Ai, annabi ba ya rasa girma sai dai a garinsu, da cikin 'yan'uwansa, da kuma gidansu.” 5 Bai ko iya yin wata mu'ujiza a can ba, sai dai ya ɗora wa marasa lafiya kaɗan hannu ya warkar da su. 6 Ya yi mamakin rashin bangaskiyarsu. Sai ya zazzaga ƙauyuka yana koyarwa.

Yesu ya Aiki Sha Biyu Ɗin Nan

7 Sai ya kira goma sha biyun nan, ya fara aikensu biyu-biyu, ya kuma ba su iko a kan baƙaƙen aljannu. 8 Ya umarce su kada su ɗauki guzuri don tafiyar, ko gurasa, ko burgami, ko kuɗi ma a ɗamararsu, sai dai sanda kawai, 9 amma su sa takalmi, kada kuma su haɗa taguwa biyu. 10 Ya ce musu, “Duk gidan da kuka sauka, ku zauna a nan har ku tashi. 11 Duk inda aka ƙi yin na'am da ku, aka kuma ƙi sauraronku, in za ka tashi, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunka don shaida a kansu.” 12 Haka fa, suka fita, suna wa'azi don mutane su tuba. 13 Suka fitar da aljannu da yawa, suka kuma shafa wa marasa lafiya da yawa mai, suka warkar da su.

Mutuwar Yahaya Maibaftisma

14 Sai fa sarki Hirudus ya ji labari, domin sunan Yesu ya riga ya shahara, har waɗansu suka ce, “Yahaya Maibaftisma ne aka tāsa daga matattu, shi ya sa mu'ujizan nan suke aiki ta wurinsa.” 15 Amma waɗansu kuwa suka ce, “Iliya ne.” Waɗansu kuwa suka ce, “Ai, annabi ne, kamar ɗaya daga cikin annabawa.” 16 Amma da Hirudus ya ji haka, sai ya ce, “Yahaya, wanda na fille wa kai, shi ne aka tāsa.” 17 Don dā Hirudus da kansa ya aika aka kamo Yahaya, ya ɗaure shi a kurkuku saboda Hirudiya matar ɗan'uwansa Filibus, wadda shi Hirudus ya aura. 18 Don dā Yahaya ya ce wa Hirudus, “Bai halatta ka ƙwace matar ɗan'uwanka ba.” 19 Hirudiya kuwa tana riƙe da Yahaya cikin zuciyarta, har ta so ta kashe shi, amma ba ta sami hanya ba, 20 don Hirudus yana tsoron Yahaya, ya sani shi mutum ne adali, tsattsarka, shi ya sa ya kāre shi. Hirudus yakan damu da yawa sa'ad da yake sauraron Yahaya, ko da yake yana murna da jinsa. 21 Amma wani sanadi ya zo, da ranar haihuwar Hirudus ta kewayo, ya yi wa hakimansa, da sarakunan yaƙinsa, da kuma manyan ƙasar Galili biki. 22 Da 'yar Hirudiya ta shigo ta yi rawa, sai ta gamshi Hirudus da baƙinsa. Sai fa sarki ya ce wa yarinyar, “Ki roƙe ni kome, sai in ba ki.” 23 Ya kuma rantse mata, ya ce, “Kome kika roƙe ni zan ba ki, ko da rabin mulkina ne.” 24 Ta fita, ta ce wa mahaifiyarta, “Me zan roƙa?” Uwar ta ce, “Kan Yahaya Maibaftisma.” 25 Nan da nan sai ta shigo wurin sarki da gaggawa, ta roƙe shi, ta ce, “Ina so yanzu yanzu ka ba ni kan Yahaya Maibaftisma a cikin akushi.” 26 Sai sarki ya yi baƙin ciki matuƙa, amma saboda rantsuwar da ya yi da kuma kunyar baƙinsa, ba ya so ya hana ta. 27 Nan take sai sarki ya aiki dogari, ya yi umarni a kawo kan Yahaya. Dogarin ya tafi ya fille wa Yahaya kai a kurkuku, 28 ya kawo kan a cikin akushi, ya ba yarinyar, yarinyar kuwa ta ba mahaifiyarta. 29 Da almajiran Yahaya suka ji labari, sai suka zo suka ɗauki gangar jikinsa, suka sa ta a kabari.

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

30 Manzannin suka komo wurin Yesu, suka faɗa masa duk iyakar abin da suka yi, da abin da suka koyar. 31 Ya ce musu, “Ku zo mu kaɗaita a wurin da ba kowa, ku ɗan huta.” Domin mutane da yawa suna ta kaiwa da kawowa, ko damar cin abinci ma, manzannin ba su samu ba. 32 Sai suka tafi cikin jirgi wurin da ba kowa, su kaɗai. 33 Ashe, mutane da yawa sun ga tafiyarsu, sun kuwa shaida su, suka fa dunguma ta tudu daga garuruwa duka, suka riga su zuwa. 34 Da saukar Yesu sai ya ga taro mai yawa, ya kuma ji tausayinsu, domin kamar tumaki suke waɗanda ba su da makiyayi. Ya fara koya musu abubuwa da yawa. 35 Kusan fāɗuwar rana sai almajiransa suka zo gare shi, suka ce masa, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuwa, rana ta kusa faɗuwa. 36 Sai ka sallame su, su shiga karkara da ƙauyuka na kurkusa, su saya wa kansu abinci.” 37 Amma ya amsa musu ya ce, “Ku ku ba su abinci mana.” Sai suka ce masa, “Wato, mu je mu sayo gurasa ta dinari metan, mu ba su su ci?” 38 Ya ce musu, “Gurasa nawa ke gare ku? Ku je ku dubo.” Da suka binciko suka ce, “Ai, biyar ne, da kifi biyu.” 39 Sa'an nan ya yi umarni dukkansu su zazzauna ƙungiya ƙungiya a kan ɗanyar ciyawa. 40 Haka suka zauna jeri jeri, waɗansu ɗari ɗari, waɗansu hamsin hamsin. 41 Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyun, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura gurasar, ya yi ta ba almajiran, suna kai wa jama'a, duk kuma ya raba musu kifin nan biyu. 42 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, 43 har suka ɗauki kwando goma sha biyu cike da gutsattsarin gurasar da na kifin. 44 Waɗanda suka ci gurasar nan kuwa maza dubu biyar ne.

Yesu yana Tafiya a kan Ruwan Teku

45 Nan da nan ya sa almajiransa su shiga jirgi su riga shi hayewa zuwa Betsaida, kafin ya sallami taron. 46 Bayan ya sallame su, sai ya hau dutse domin ya yi addu'a. 47 Da magariba ta yi, jirgin yana tsakiyar teku, Yesu kuwa yana nan a kan tudu shi kaɗai. 48 Da ya ga suna fama da tuƙi, gama iska tana gāba da su, misalin ƙarfe uku na dare, sai ya nufo su, yana tafe a kan ruwan teku. Ya yi kamar zai wuce su, 49 amma da suka gan shi yana tafiya a kan ruwan, sai suka zaci fatalwa ce, suka yi kururuwa, 50 domin duk sun gan shi, sun kuwa firgita. Sai nan da nan ya yi musu magana ya ce, “Ba kome, ni ne, kada ku ji tsoro.” 51 Sa'an nan ya shiga jirgi wurinsu, iska kuma ta kwanta. Sai mamaki ya kama su ƙwarai, 52 don ba su fahimci al'amarin gurasar nan ba, saboda zuciyarsu ta taurare.

Yesu ya Warkar da Marasa Lafiya a Janisarata

53 Da suka haye, suka isa ƙasar Janisarata, suka ɗaure jirgin a gaɓa. 54 Da fitarsu daga jirgin sai mutane suka shaida shi. 55 Suka gama ƙasar da gudu, suka fara ɗaɗɗauko marasa lafiya a kan shimfiɗunsu zuwa duk inda suka ji yake. 56 Duk inda ya shiga kuma, birni ko ƙauye ko karkara, sukan kwantar da marasa lafiya a bakin kasuwa, su roƙe shi ya yarda su taɓa ko ma da gezar mayafinsa. Iyakar waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

Markus 7

Al'adun Shugabanni

1 To, da Farisiyawa suka taru a wurinsa tare da waɗansu daga cikin malaman Attaura da suka zo daga Urushalima, 2 suka lura waɗansu almajiransa suna cin abinci da hannuwa marasa tsarki, wato, marasa wanki. 3 Domin Farisiyawa da dukan Yahudawa ba sa cin abinci sai sun wanke hannu sarai tukuna, saboda bin al'adun shugabanninsu. 4 In sun komo daga kasuwa kuwa, ba sa cin abinci sai sun yi wanka tukuna. Akwai kuma waɗansu al'adu da yawa da suka gada suke kiyayewa, kamar su wankin ƙore, da tuluna, da daro. 5 Sai Farisiyawa da malaman Attaura suka tambaye shi, “Don me almajiranka ba sa bin al'adun shugabanni, sai su riƙa cin abinci da hannuwa marasa tsabta?” 6 Sai ya ce masu, “Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku, munafukai! Yadda yake a rubuce cewa, ‘Al'umman nan a baka kawai suke girmama ni, Amma a zuci nesa suke da ni. 7 A banza suke bauta mini, Domin ƙa'idodin da suke koyarwa umarnin ɗan adam ne.’ 8 Kuna yar da umarnin Allah, kuna riƙe da al'adun mutane.” 9 Sai ya ce musu, “Lalle kun iya yar da umarnin Allah don ku bi al'adunku! 10 Domin Musa ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’ da kuma, ‘Wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa, sai lalle a kashe shi.’ 11 Amma ku kukan ce, ‘In mutum ya ce wa ubansa ko mahaifiyarsa, “Duk abin da dā za ku samu a gare ni ya zama Korban,” ’ (wato, an sadaukar), 12 shi ke nan fa, ba saura ku bar shi ya yi wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa aikin kome. 13 Ta haka kuke banzanta Maganar Allah ta wajen al'adunku. Kun kuwa cika yin irin waɗannan abubuwa.”

Abubuwan da suke Ƙazantarwa

14 Sai ya sāke kiran jama'a, ya ce musu, “Ku saurare ni dukanku, ku kuma fahimta. 15 Ba abin da yake shiga mutum daga waje ya ƙazanta shi, sai abin da yake fita, yake ƙazantar da shi. 16 Duk mai kunnen ji, yă ji.” 17 Bayan rabuwarsa da taron, da ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi ma'anar misalin. 18 Ya ce musu, “Ashe, ku ma ba ku da fahimta ne? Ashe, ba ku gane ba, kome ya shiga mutum daga waje, ba yadda zai ƙazanta shi, 19 tun da yake ba zuciyarsa ya shiga ba, cikinsa ne, ta haka kuma zai fita?” Ta haka Yesu ya halatta kowane irin abinci. 20 Ya kuma ce, “Abin da yake fita daga cikin mutum yake ƙazantar da shi. 21 Don daga ciki ne, wato, daga zuciyar mutum, mugayen tunani suke fitowa, kamar su fasikanci, da sata, da kisankai, da zina, 22 da kwaɗayi, da mugunta, da ha'inci, da fajirci, da kishi, da yanke, da girmankai, da kuma wauta. 23 Duk waɗannan mugayen abubuwa daga ciki suke fitowa, suna kuwa ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar Mata Basurofinikiya

24 Daga nan kuma ya tashi ya tafi wajajen Taya da Sidon. Ya shiga wani gida, bai kuwa so kowa ya sani ba, amma ba ya ɓoyuwa. 25 Nan da nan sai wata mace, wadda karamar 'yarta take da baƙin aljan ta ji labarinsa, ta zo ta fāɗi a gabansa. 26 Matar kuwa Baheleniya ce, asalinta kuma Basurofinikiya ce. Sai ta roƙe shi ya fitar wa 'yarta da aljanin. 27 Yesu ya ce mata, “Bari 'ya'ya su ƙoshi tukuna, domin bai kyautu a bai wa karnuka abincin 'ya'ya ba.” 28 Amma ta amsa masa ta ce, “I, haka ne, ya Ubangiji, amma ai, karnuka sukan ci suɗin 'ya'ya.” 29 Sai ya ce mata, “Saboda wannan magana taki, koma gida, aljanin, ai, ya rabu da 'yarki.” 30 Sai ta koma gida ta iske 'yarta a kwance a gado, aljanin kuwa ya riga ya rabu da ita.

Yesu ya Warkar da Bebe

31 Sai ya komo daga wajen Taya, ya bi ta Sidon ya je Tekun Galili ta Dikafolis. 32 Suka kawo masa wani kurma kuma bebe, suka roƙe shi don ya ɗora masa hannu. 33 Yesu ya ɗauke shi suka koma waje ɗaya, rabe da taron, ya sa yatsotsinsa a kunnuwan kurma, ya tofar da yau, ya kuma taɓa harshen beben. 34 Ya ɗaga kai sama ya yi ajiyar zuciya, sai ya ce masa, “Iffata!” wato, “Buɗu!” 35 Sai aka buɗe kunnuwansa, aka saki kwaɗon harshensa, ya kuma yi magana sosai. 36 Yesu ya kwaɓe su kada su fada wa kowa, amma ƙara yawan kwaɓarsu ƙara yawan yaɗa labarin. 37 Suka yi mamaki gaba da kima, suka ce, “Kai, ya yi kome da kyau! Har kurma ma ya sa ya ji, bebe kuma ya yi magana.”

Markus 8

Ciyar da Mutum Dubu Huɗu

1 A lokacin nan da wani taro mai yawan gaske ya sāke haɗuwa, ba su kuwa da abinci, sai ya kira almajiransa, ya ce musu, 2 “Ina jin tausayin wannan taro, don yau kwanansu uku ke nan a guna, ba su da wani abinci. 3 In kuwa na sallame su su tafi gida da yunwa haka, ai, za su kasa a hanya, ga shi kuwa, waɗansunsu sun fito nesa.” 4 Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za a iya samun gurasar da za ta ciyar da mutanen nan a jeji haka?” 5 Sai ya tambaye su, “Gurasa nawa ke gare ku?” Suka ce, “Bakwai.” 6 Sai ya umarci taron su zauna a ƙasa. Da ya ɗauki gurasar nan bakwai, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya yi ta ba almajiransa su kai wa taron, suka kuwa kakkai musu. 7 Suna kuma da ƙananan kifaye kaɗan. Da ya yi wa Allah godiya, sai ya ce su ma a kai musu. 8 Suka ci, suka ƙoshi, har suka ɗauki ragowar gutsattsarin, cike da manyan kwanduna bakwai. 9 Mutanen kuwa sun yi wajen dubu huɗu. Sai ya sallame su. 10 Nan da nan kuwa sai ya shiga jirgi tare da almajiransa, ya tafi ƙasar Dalmanuta.

Neman Alama

11 Farisiyawa suka zo suka fara muhawwara da shi, suna nema ya nuna musu wata alama daga sama, don su gwada shi. 12 Sai ya yi wata doguwar ajiyar zuciya, ya ce, “Don me mutanen zamanin nan suke neman ganin alama? Hakika, ina gaya muku, ba wata alamar da za a nuna wa mutanen wannan zamani.” 13 Daga nan ya bar su, ya sāke shiga jirgi, ya haye wancan ƙetaren.

Yistin Farisiyawa da na Hirudus

14 Sun kuwa manta, ba su kawo gurasa ba, sai guda ɗaya kawai ke gare su a jirgin. 15 Ya gargaɗe su ya ce, “Ku kula, ku yi hankali da yistin Farisiyawa da na Hirudus.” 16 Suka yi magana da juna a kan ba su da gurasa. 17 Da yake Yesu ya gane haka, sai ya ce musu, “Don me kuke zancen ba ku da gurasa? Ashe, har yanzu ba ku gane ba, ba ku kuma fahimta ba? Zuciyarku a taurare take? 18 Kuna da idanu, ba kwa gani ne? Kuna da kunnuwa, ba kwa ji ne? Ba kwa kuma tunawa? 19 Da na gutsuttsura wa mutum dubu biyar gurasar nan biyar, kwando nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Sha biyu.” 20 “To, gurasa bakwai da na gutsuttsura wa mutum dubu huɗu fa? Manyan kwanduna nawa kuka ɗauka cike da gutsattsarin?” Suka ce masa, “Bakwai.” 21 Sai ya ce musu, “To, har yanzu ba ku fahimta ba?”

Warkar da Makaho a Betsaida

22 Suka iso Betsaida. Aka kawo masa wani makaho, aka roƙe shi ya taɓa shi. 23 Ya kama hannun makahon, ya kai shi bayan gari. Da ya tofa yau a idanunsa, ya ɗora masa hannu, sai ya tambaye shi cewa, “Kana iya ganin wani abu?” 24 Sai makahon ya ɗaga kai, ya ce, “Ina ganin mutane kam, amma kamar itatuwa nake ganinsu, suna yawo.” 25 Sai ya sāke ɗora hannu a idanunsa. Makahon kuwa ya zura ido ƙwar, ya warke, ya ga kome garau. 26 Sai Yesu ya sallame shi ya koma gida, ya ce, “Ko ƙauyen ma kada ka shiga.”

Hurcin Bitrus a kan Yesu

27 Yesu ya tashi, da shi da almajiransa, ya shiga ƙauyukan Kaisariya Filibi. A hanya kuwa ya tambayi almajiransa, “Wa mutane suke cewa, nake?” 28 Suka ce masa, “Yahaya Maibaftisma, waɗansu kuwa, Iliya, waɗansu kuma, wani daga cikin annabawa.” 29 Sai ya tambaye su, “Amma ku fa, wa kuke cewa, nake?” Bitrus ya amsa masa ya ce, “Kai ne Almasihu.” 30 Sai ya kwaɓe su kada su gaya wa kowa labarinsa.

Yesu ya Faɗi irin Mutuwar da zai Yi

31 Ya fara koya musu, cewa, lalle ne Ɗan Mutum ya sha wuya iri iri, shugabanni da manyan firistoci, da malaman Attaura su ƙi shi, har a kashe shi, bayan kwana uku kuma ya tashi da rai. 32 Ya kuwa faɗi wannan magana a sarari. Sai Bitrus ya ja shi waje ɗaya, ya fara tsawatar masa. 33 Amma da Yesu ya waiwaya ya ga almajiransa, ya tsawata wa Bitrus ya ce, “Kai yi nesa da ni, Shaiɗan! Ba ka tattalin al'amuran Allah sai na mutane.” 34 Ya kira taron tare da almajiransa, ya ce musu, “Duk mai son bina, sai yă ƙi kansa, yă ɗauki gicciyensa, yă bi ni. 35 Duk mai son tattalin ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, saboda bishara kuma, tattalinsa yake yi. 36 Me mutum ya amfana in ya sami duniya duka a bakin ransa? 37 Me kuma mutum zai iya bayarwa ya fanshi ransa? 38 Duk wanda zai ji kunyar shaida ni da maganata a wannan zamani na rashin amana da yawan zunubi, Ɗan Mutum ma zai ji kunyar shaida shi, sa'ad da ya zo da ɗaukakar Ubansa tare da mala'iku.”

Markus 9

1 Sai ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, akwai waɗansu tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba, sai sun ga Mulkin Allah ya bayyana da iko.”

Sākewar Kamanninsa

2 Bayan kwana shida, sai Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kai su kan wani dutse mai tsawo, su kaɗai. Sai kamanninsa suka sāke a gabansu, 3 tufafinsa suka yi fari fat suna sheƙi, yadda ba mai wankin da zai iya wanke su haka a duniya. 4 Sai Iliya da Musa suka bayyana a gare su, suna magana da Yesu. 5 Sai Bitrus ya ka da baki, ya ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, ya kyautu da muke nan wurin, mu kafa bukkoki uku, ɗaya taka, ɗaya ta Musa, ɗaya kuma ta Iliya.” 6 Ya rasa abin da zai faɗa ne, don sun tsorata da gaske. 7 Sai ga wani gajimare ya zo ya rufe su, aka kuma ji wata murya daga cikin gajimaren, tana cewa, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena. Ku saurare shi.” 8 Farat haka da suka dudduba, ba su ƙara ganin kowa ba, sai Yesu kaɗai tare da su. 9 Suna cikin gangarowa daga dutsen, sai ya kwaɓe su kada su gaya wa kowa abin da suka gani, sai bayan Ɗan Mutum ya tashi daga matattu tukuna. 10 Sai suka bar maganar yasu-yasu, suna tambayar juna ko mece ce ma'anar tashi daga matattu. 11 Suka tambaye shi suka ce, “To, yaya kuwa malaman Attaura suke cewa, lalle ne Iliya yă fara zuwa?” 12 Sai ya ce musu, “Lalle ne Iliya ya fara zuwa ya raya dukan abubuwa. Yaya kuwa yake a rubuce a kan Ɗan Mutum, cewa, zai sha wuya iri iri, a kuma wulakanta shi? 13 Amma ina gaya muku, Iliya ya riga ya zo, sun kuma yi masa abin da suka ga dama, yadda labarinsa yake a rubuce.”

Yesu ya Warkar da Yaro Mai Beben Aljan

14 To, da suka komo wurin almajiran, sai suka ga babban taro ya kewaye su, malaman Attaura kuma suna muhawwara da su. 15 Da ganin Yesu sai duk taron suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ɗungumo wurinsa a guje, suna gaishe shi. 16 Ya tambaye su, “Muhawwarar me kuke yi da su?” 17 Sai ɗaya daga cikin taron ya amsa masa ya ce, “Malam, ga shi, na kawo maka ɗana, don yana da beben aljan. 18 Duk inda ya hau shi, sai ya doka shi har ƙasa, bakinsa yana kumfa, yana tsukun haƙoransa, yana sandarewa. Na kuma yi wa almajiranka magana su fitar da shi, suka kasa.” 19 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Ya ku mutanen zamani marasa bangaskiya! Har yaushe zan iya zama da ku? Har yaushe kuma zan iya jure muku? Ku dai kawo mini shi.” 20 Suka kawo masa yaron. Da aljanin ya gan shi, nan da nan sai ya buge yaron, jikinsa na rawa, ya fāɗi yana ta birgima, bakinsa yana kumfa. 21 Yesu ya tambayi mahaifin yaron ya ce, “Tun yaushe wannan abu ya same shi?” Mahaifin ya ce, “Tun yana ƙarami. 22 Ya kuwa sha jefa shi a wuta da kuma ruwa, don ya hallaka shi. Amma in za ka iya yin wani abu, ka ji tausayinmu ka taimake mu.” 23 Sai Yesu ya ce masa, “In zan iya? Ai, dukkan abu mai yiwuwa ne ga mai ba da gaskiya.” 24 Nan da nan sai uban yaron ya ɗaga murya ya ce, “Na ba da gaskiya. A kore mini rashin bangaskiyata!” 25 Da Yesu ya ga taro yana ɗungumowa a guje, sai ya tsawata wa baƙin aljanin ya ce masa, “Kai, beben aljan, na umarce ka ka rabu da shi, kada kuma ka ƙara hawansa.” 26 Bayan da aljanin nan ya yi ihu, sai ya buge shi yaron da gaske, jikinsa yana rawa, ya rabu da shi. Yaron kuma ya zama kamar matacce, har ma yawancin mutane suka ce, “Ai, ya mutu!” 27 Amma Yesu ya kama hannunsa ya tashe shi, ya kuwa tashi tsaye. 28 Da Yesu ya shiga gida, almajiransa suka tambaye shi a keɓe suka ce, “Me ya sa mu muka kāsa fitar da shi?” 29 Sai ya ce musu, “Ai, irin wannan ba ya fita sai da addu'a.”

Yesu ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

30 Sai suka tashi daga nan, suka ratsa ƙasar Galili, bai kuwa so kowa ya sani ba, 31 domin yana koya wa almajiransa ne, yana ce musu, “Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane, za su kuwa kashe shi, sa'ad da aka kashe shi kuma, bayan kwana uku zai tashi.” 32 Amma fa ba su fahimci ba, suna kuma jin tsoron tambayarsa. 9 .33 Wane ne Mafi Girma? Wane ne Mafi Girma? 33 Suka zo Kafarnahum. Da ya shiga gida sai ya tambaye su, “Muhawwarar me kuka yi a hanya?” 34 Amma suka yi shiru, don a hanya sun yi muhawwarar ko wane ne babbansu. 35 Sai ya zauna, ya kira goma sha biyun nan, ya ce musu, “Kowa yake son ya zama shugaba, lalle ne yă zama na ƙarshe duka, baran kowa kuma.” 36 Sai ya ɗauki wani ƙaramin yaro, ya sa shi a tsakiyarsu, ya rungume shi, ya ce musu, 37 “Duk wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan saboda sunana, ni ya karɓa. Wanda kuma ya karɓe ni, ba ni ya karɓa ba, wanda ya aiko ni ne ya karɓa.”

Wanda ba ya Gāba da Mu, Namu Ne

38 Sai Yahaya ya ce masa, “Malam, mun ga wani yana fitar da aljannu da sunanka, mun kuwa hana shi, domin ba ya binmu.” 39 Amma Yesu ya ce, “Kada ku hana shi. Ai, ba wanda zai yi wata mu'ujiza da sunana, sa'an nan, nan da nan ya kushe mini. 40 Ai, duk wanda ba ya gāba da mu, namu ne. 41 Kowa kuma ya ba ku ruwan sha moɗa guda saboda ku na Almasihu ne, hakika ina gaya muku, ba zai rasa ladansa ba ko kaɗan.

Sanadodin Yin Zunubi

42 “Da dai wani yă sa ɗaya daga cikin waɗannan 'yan yara masu gaskatawa da ni yă yi laifi, zai fiye masa a rataya wani babban dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi cikin teku. 43 In kuwa hannunka yana sa ka laifi, to, yake shi. Zai fiye maka ka shiga rai da dungu, da ka shiga Gidan Wuta da hannu biyu, wuta marar kasuwa kuwa. 44 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta. 45 In kuwa ƙafarka tana sa ka laifi, to yanke ta. Zai fiye maka ka shiga rai da gurguntaka, da a jefa ka Gidan Wuta da ƙafa biyu. 46 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta. 47 In kuma idonka yana sa ka laifi, to, ƙwaƙule shi. Zai fiye maka ka shiga Mulkin Allah da ido ɗaya, da a jefa ka Gidan Wuta da ido biyu. 48 A wurin tsutsotsi masu cinsu ba sa mutuwa, wutar kuma ba a kashe ta. 49 Da wuta za a tsarkake kowa, kamar yadda ake tsarkake abu da gishiri. 50 Gishiri abu ne mai kyau, amma in gishiri ya sāne, dame za a daɗaɗa shi? Sai ku kasance da gishiri a zuciyarku, ku yizaman lafiya da juna.”

Markus 10

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

1 Sai Yesu ya tashi daga nan, ya tafi ƙasar Yahudiya, da kuma hayin Kogin Urdun. Taro kuma ya sāke haɗuwa wurinsa, ya kuma sāke koya musu kamar yadda ya saba. 2 Sai waɗansu Farisiyawa suka zo wajensa don su gwada shi, suka tambaye shi suka ce, “Halal ne mutum ya saki matarsa?” 3 Sai ya amsa musu ya ce, “Me Musa ya umarce ku?” 4 Suka ce, “Musa ya ba da izini a rubuta takardar kisan aure, a kuma saki matar.” 5 Yesu ya ce musu, “Don taurinkanku ne Musa ya rubuta muku wannan umarni. 6 Amma tun farkon halitta ‘Allah ya halicce su, namiji da tamata.’ 7 ‘Don haka fa sai mutum yă bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa. 8 Haka su biyun nan su zama jiki guda.’ Har nan gaba su zama ba jiki biyu ba ne, ɗaya ne. 9 Abin da Allah fa ya gama, kada mutum ya raba.” 10 A cikin gida kuma sai almajiransa suka sāke tambayarsa wannan magana. 11 Sai ya ce musu, “Kowa ya saki matarsa, ya auri wata, zina yake yi da ta biyun. 12 In kuma matar ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”

Yesu ya Sa wa 'Yan Yara Albarka

13 Suna kawo masa waɗansu yara ƙanana domin ya taɓa su, sai almajiransa suka kwaɓe su. 14 Da Yesu ya ga haka, sai ya ji haushi ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Allah na irinsu ne. 15 Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na'am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.” 16 Sai Yesu ya rungume su, yana ɗora musu hannu, yana sa musu albarka.

Saurayi Mai Dukiya

17 Ya fara tafiya ke nan, sai ga wani ya sheƙo a guje, ya durƙusa a gabansa, ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?” 18 Sai Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Ai, ba wani Managarci sai Allah kaɗai. 19 Ka dai san umarnan nan, ‘Kada ka yi kisankai. Kada ka yi zina. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. Kada ka yi zamba. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’ ” 20 Sai ya ce masa, “Malam, ai, duk na kiyaye waɗannan tun ƙuruciyata.” 21 Yesu ya dube shi duban ƙauna, ya ce masa, “Abu guda ne kawai ya rage maka. Sai ka je, ka sayar da duk mallakarka, ka ba talakawa, za ka sami wadata a Sama. Sa'an nan ka zo ka bi ni.” 22 Da jin wannan magana sai gabansa ya fāɗi, ya tafi yana da baƙin ciki, don yana da arziki ƙwarai. 23 Daga nan sai Yesu ya duddubi almajiransa, ya ce musu, “Da ƙyar kamar me masu dukiya su shiga Mulkin Allah!” 24 Almajiran kuwa suka yi mamakin maganarsa. Sai Yesu ya sāke ce musu, “Ya ku 'ya'yana, da ƙyar ne kamar me a shiga Mulkin Allah! 25 Zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.” 26 Sai suka yi mamaki ƙwarai da gaske, suka ce masa, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?” 27 Yesu ya dube su, ya ce, “Ga mutane kam ba mai yiwuwa ba ne, amma fa ba ga Allah ba. Domin kowane abu mai yiwuwa ne a gun Allah.” 28 Sai Bitrus ya fara ce masa, “To, ai, ga shi, mu mun bar kome, mun bi ka.” 29 Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ba wanda zai bar gida, ko 'yan'uwansa mata, ko 'yan'uwansa maza, ko mahaifinsa, ko mahaifiyarsa, ko 'ya'yansa, ko gonakinsa, sabili da ni da kuma bishara, 30 sa'an nan ya kasa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu, na gidaje, da 'yan'uwa mata, da 'yan'uwa maza, da uwaye, da 'ya'ya, da gonaki, amma game da tsanani, a lahira kuma ya sami rai madawwami. 31 Da yawa na farko za su koma na ƙarshe, na ƙarshe kuma za su zama na farko.”

Yesu kuma ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

32 Suna tafiya Urushalima, Yesu kuwa yana tafe gabansu, sai suka yi mamaki, mutanen da ke biye kuma suka tsorata. Ya sāke keɓe goma sha biyun nan, ya fara shaida musu abin da zai same shi. 33 Ya ce, “Ga shi, za mu Urushalima, za a ba da Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman Attaura, za su kuwa yi masa hukuncin kisa, su bāshe shi ga al'ummai. 34 Za su yi masa ba'a, su tofa masa yau, su yi masa bulala, su kashe shi, bayan kwana uku kuma ya tashi.”

Roƙon Yakubu da Yahaya

35 Yakubu da Yahaya, 'ya'yan Zabadi, suka kusato shi, suka ce masa, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙe ka.” 36 Sai ya ce musu, “Me kuke so in yi muku?” 37 Suka ce masa, “Ka yardar mana, ranar ɗaukakarka, mu zauna ɗaya a damanka, ɗaya a hagun.” 38 Amma Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Kwa iya sha da ƙoƙon da ni zan sha? Ko kwa iya a yi muku baftisma da baftismar da za a yi mini?” 39 Suka ce masa, “Ma iya.” Sai Yesu ya ce musu, “Ƙoƙon da ni zan sha, da shi za ku sha, baftismar da za a yi mini kuwa, da ita za a yi muku. 40 Amma zama a damana, ko a haguna, ba nawa ba ne da zan bayar, ai, na waɗanda aka riga aka shirya wa ne.” 41 Da almajiran nan goma suka ji haka, suka fara jin haushin Yakubu da Yahaya. 42 Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al'ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gāsa musu iko. 43 Ba haka zai zama a tsakaninku ba. Amma duk wanda yake son zama babba a cikinku, lalle ne ya zama baranku. 44 Wanda duk kuma ke so ya shugabance ku, lalle ne ya zama bawan kowa. 45 Domin Ɗan Mutum ma ya zo ba domin a bauta masa ba, sai dai domin shi ya yi bautar, ya kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”

Bartimawas Makaho ya Sami Ganin Gari

46 Sai suka iso Yariko. Yana fita daga Yariko ke nan, da shi, da almajiransa, da wani ƙasaitaccen taro, sai ga wani makaho yana bara, sunansa Bartimawas, ɗan Timawas, yana zaune a gefen hanya. 47 Da ya ji dai Yesu Banazare ne, sai ya fara ɗaga murya yana cewa, “Ya Yesu, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!” 48 Waɗansu da yawa suka kwaɓe shi, cewa, ya yi shiru. Amma sai ƙara ɗaga murya yake yi ƙwarai da gaske, yana cewa, “Ya Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai tausayina!” 49 Sai Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kirawo shi.” Sai suka kirawo makahon suka ce masa, “Albishirinka! Taso, yana kiranka.” 50 Sai ya yar da mayafinsa, ya zaburo wurin Yesu. 51 Yesu ya ce masa, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce masa, “Malam, in sami gani!” 52 Sai Yesu ya ce masa, “Yi tafiyarka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan take ya sami gani, ya bi Yesu, suka tafi.

Markus 11

Mutanen Urushalima sun Marabci Yesu

1 Da suka kusato Urushalima, da Betafaji, da Betanya, wajen Dutsen Zaitun, sai Yesu ya aiki almajiransa biyu, 2 ya ce musu, “Ku shiga ƙauyen can da yake gabanku. Da shigarku za ku ga wani aholaki a ɗaure, wanda ba a taɓa hawa ba. Ku kwanto shi. 3 Kowa ya ce muku, ‘Don me kuke haka?’ ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsa, Zai kuma komo da shi nan da nan.’ ” 4 Sai suka tafi, suka tarar da aholakin a ɗaure a ƙofar gida a bakin hanya, suka kwance shi. 5 Sai waɗanda suke tsaitsaye a gun suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?” 6 Suka faɗa musu abin da Yesu ya ce. Su kuwa suka ƙyale su suka tafi. 7 Suka kawo wa Yesu aholakin, suka shimfiɗa mayafansu a kai, ya hau. 8 Sai mutane da yawa suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya, waɗansu kuma suka baza rassan da suka kakkaryo a saura. 9 Da na gaba da na baya suka riƙa sowa suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji! 10 Albarka ta tabbata ga mulkin nan mai zuwa na ubanmu Dawuda! Hosanna ga Allah!” 11 Sai ya shiga Urushalima, ya shiga Haikalin. Da dai ya dudduba kome, da yake magariba ta yi, ya fita ya tafi Betanya tare da goma sha biyun nan.

La'antar da Itacen Ɓaure

12 Kashegari, da suka tashi daga Betanya, ya ji yunwa. 13 Da ya hango wani itacen ɓaure mai ganye kore shar, sai ya je ya ga ko ya sami 'ya'ya. Da ya isa wurinsa bai ga kome ba sai ganye, don ba lokacin 'ya'yan ɓaure ba ne. 14 Sai ya ce wa ɓauren, “Kada kowa ya ƙara cin 'ya'yanka har abada!” Almajiransa kuwa suna ji.

Yesu ya Tsabtace Haikalin

15 Suka iso Urushalima. Ya shiga Haikalin ya fara korar masu saye da sayarwa daga ciki, ya kuma birkice teburorin 'yan canjin kuɗi da kujerun masu sayar da tattabarai, 16 ya kuma hana kowa ya ratsa Haikalin ɗauke da wani abu. 17 Sai ya yi musu gargaɗi ya ce, “Ashe, ba a rubuce yake ba cewa, ‘Za a kira masujadata ɗakin addu'a na dukkan al'ummai?’ Amma ku kun maishe shi kogon 'yan fashi.” 18 Da manyan firistoci da malaman Attaura suka ji wannan magana, sai suka kuma nemi hanyar hallaka shi, saboda sun tsorata da shi, don duk jama'a suna mamaki da koyarwarsa. 19 Kowace yamma kuwa Yesu yakan fita gari.

Aya a kan Bushewar Itacen Ɓaure

20 Suna wucewa da safe, sai suka ga ɓauren nan ya bushe har saiwarsa. 21 Bitrus kuwa ya tuna, sai ya ce masa, “Ya Shugaba, dubi! Ɓauren nan da ka la'anta ya bushe!” 22 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku gaskata da Allah. 23 Hakika, ina gaya muku, kowa ya ce wa dutsen nan, ‘Ka ciru, ka fāɗa teku,’ bai kuwa yi shakka a zuciyarsa ba, amma ya gaskata abin da ya faɗa zai auku, sai a yi masa shi. 24 Don haka ina dai gaya muku, kome kuka roƙa da addu'a, ku gaskata cewa, samamme ne, za ku kuwa samu. 25 Koyaushe kuka tsaya yin addu'a, in akwai wanda kuke jin haushinsa, ku yafe masa, domin Ubanku da yake Sama shi ma yă yafe muku laifofinku. 26 Amma in ba kwa yafewa, haka Ubanku da yake Sama ma, ba zai yafe muku laifofinku ba.”

Ana Shakkar Izinin Yesu

27 Suka koma Urushalima. Yana zagawa cikin Haikalin sai manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabannin jama'a suka zo wurinsa, 28 suka ce masa, “Da wane izini kake yin waɗannan abubuwa, ko kuwa wa ya ba ka izinin yin haka?” 29 Sai Yesu ya ce musu, “Zan yi muku wata tambaya. Ku ba ni amsa, ni kuwa in gaya muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan. 30 To, baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce? Ku ba ni amsa.” 31 Sai suka yi muhawwara da juna, suka ce, “In muka ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’ 32 Ma kuwa ce, ‘Ta mutum ce?’ ” Suna kuwa jin tsoron jama'a, don duk kowa ya tabbata, cewa, Yahaya annabi ne. 33 Sai suka amsa wa Yesu suka ce, “Ba mu sani ba.” Yesu ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan ba.”

Markus 12

Misali na Manoman da suka Yi Sufurin Garkar Inabi

1 Sai Yesu ya fara yi musu magana da misalai ya ce, “Wani mutum ne ya yi garkar inabi, ya shinge ta, ya haƙa ramin matse inabin, ya kuma gina wata 'yar hasumiyar tsaro. Ya ba waɗansu manoma ijarar garkar, sa'an nan ya tafi wata ƙasa. 2 Da kakar inabin ta yi, sai ya aiki wani bawansa wurin manoman nan ya karɓo masa gallar garkar. 3 Manoman kuwa suka kama shi, suka yi masa d�ka, suka kore shi hannu banza. 4 Sai ya sāke aika musu wani bawan. Shi kuma suka yi masa rotsi, suka wulakanta shi. 5 Ya sāke aiken wani, shi kam, sai suka kashe shi. Haka fa aka yi ta yi da waɗansu da yawa, ana d�kan waɗansu, ana kashe waɗansu. 6 Har yanzu dai yana da sauran ɗaya tak, shi ne makaɗaicin ɗansa. Daga ƙarshe ya aike shi wurinsu, yana cewa, ‘Sā ga girman ɗana.’ 7 Amma manoman nan suka ce wa juna, ‘Ai, wannan shi ne magājin. Ku zo mu kashe shi, gādon yă zama namu.’ 8 Sai suka kama shi, suka kashe shi, suka jefar da shi bayan shinge. 9 To, me ubangijin garkar nan zai yi? Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar. 10 Ashe, ba ku taɓa karanta wannan Nassi ba? cewa, ‘Dutsen da magina suka ƙi, Shi ne ya zama mafificin dutsen gini. 11 Wannan aikin Ubangiji ne, A gare mu kuwa abin al'ajabi ne.’ ” 12 Sai suka nemi su kama shi, don sun lura a kansu ne ya yi misalin, amma suna jin tsoron jama'a. Don haka suka ƙyale shi, suka tafi.

Biyan Haraji ga Kaisar

13 Suka aiko masa da waɗansu Farisiyawa da mutanen Hirudus, don su burma shi cikin maganarsa. 14 Da suka zo, suka ce masa, “Malam, ai, mun sani kai mai gaskiya ne, ba ka kuma zaɓen kowa, domin ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. Shin, dai dai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa? 15 Mu biya, ko kada mu biya?” Shi kuwa da ya gane makircinsu, ya ce musu, “Don me kuke jarraba ni? Ku kawo mini dinari in gani.” 16 Suka kawo masa. Ya ce musu, “Surar nan da sunan nan na wane ne?” Suka ce masa, “Na Kaisar ne.” 17 Sai Yesu ya ce musu, “To, ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” Sai suka yi mamakinsa ƙwarai.

Tambaya a kan Tashin Matattu

18 Sai Sadukiyawa (su da suke cewa, ba tashin matattu) suka zo wurinsa, suka tambaye shi suka ce, 19 “Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa, idan ɗan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba ɗa, sai lalle mutumin ya auri matar, ya haifa wa ɗan'uwansa 'ya'ya. 20 To, an yi waɗansu 'yan'uwa maza guda bakwai. Na farkon ya yi aure, ya mutu bai bar baya ba. 21 Na biyun kuma ya aure ta, shi ma ya mutu, ba ɗa. Na ukun ma haka. 22 Haka dai duk bakwai ɗin, ba wanda ya bar ɗa. Daga ƙarshe kuma ita matar ta mutu. 23 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai ɗin sun aure ta.” 24 Sai Yesu ya ce musu, “Ba saboda wannan ne ya sa kuka ɓata ba? Wato, don ba ku san Littattafai ba, ba ku kuma san ikon Allah ba. 25 Domin in an tashi daga matattu, ba a aure, ba a aurarwa, amma kamar mala'ikun da suke Sama ake. 26 Game da tashin matattu kuma, ashe, ba ku taɓa karantawa a Littafin Musa ba, yadda Allah ya ce masa, ‘Ni ne Allahn Ibrahim, da Ishaku, da kuma Yakubu?’ 27 Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba. Kun ɓata da gaske.”

Umarni Mafi Girma

28 Sai wani malamin Attaura ya zo ya ji suna muhawwara da juna. Da dai ya ga Yesu ya ba su kyakkyawar amsa, sai ya tambaye shi, “Wane umarni ne mafi girma duka?” 29 Yesu ya amsa masa ya ce, “Mafi girma shi ne, ‘Ku saurara, ya Isra'ila, Ubangiji Allahnmu, Ubangiji ɗaya ne. 30 Sai ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan hankalinka, da kuma dukkan ƙarfinka.’ 31 Mabiyinsa shi ne, ‘Ka ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.’ Ba fa sauran wani umarni da ya fi waɗannan girma.” 32 Sai malamin Attaura ya ce masa, “Hakika gaskiyarka Malam, Ubangiji ɗaya ne, ba kuwa wani sai shi. 33 A ƙaunace shi kuma da dukkan zuciya, da dukan hankali, da dukkan ƙarfi, a kuma ƙaunaci ɗan'uwa kamar kai, ai, ya fi dukkan hadayar ƙone-ƙone da yanke-yanke nesa.” 34 Da Yesu ya ga ya yi masa magana da fasaha, sai ya ce masa, “Ba ka nesa da Mulkin Allah.” Bayan wannan kuma ba wanda ya yi ƙarfin halin sāke tambayarsa wani abu.

Tambaya a kan Ɗan Dawuda

35 Sa'ad da Yesu yake koyarwa a Haikalin sai ya ce, “Ƙaƙa malaman Attaura za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne? 36 Domin Dawuda da kansa, ta ikon Ruhu Mai Tsarki ya ce, ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, Zauna a damana, Sai na ɗora ka a kan maƙiyanka.’ 37 Dawuda da kansa ya kira shi Ubangiji. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?” Babban taron mutane kuwa sun saurare shi da murna.

Yesu ya Fallashi Malaman Attaura

38 A koyarwarsa har ya ce, “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo da manyan riguna, suna so a gaishe su a kasuwa, 39 da kuma mafifitan mazaunai a majami'u, da mazaunan alfarma a wurin biki. 40 Su ne masu ƙwace mallakar mata gwauraye, da yin doguwar addu'a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”

Baiko wadda aka Zuba

41 Sai ya zauna gaban baitulmalin Haikalin, yana duban yadda jama'a suke zuba kuɗi a ciki. Waɗansu masu arziki da yawa suna zuba kuɗi masu tsoka. 42 Sai ga wata gwauruwa ta zo, ta zuba rabin kobo biyu a ciki, wato, kobo ke nan. 43 Sai ya kira almajiransa, ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, abin da matalauciyar gwauruwar nan ta zuba cikin baitulmalin nan ya fi na sauran duka. 44 Su duk sun bayar daga yalwarsu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta ba da duk abin da take da shi, duk ma da kuɗinta na abinci.”

Markus 13

Yesu ya yi Faɗi a kan Rushewar Haikalin

1 Yesu na fita daga Haikalin, sai ɗaya daga cikin almajiransa ya ce masa, “Malam, dubi irin duwatsun nan da gine-ginen nan!” 2 Sai Yesu ya ce masa, “Ka ga manyan gine-ginen nan? Ba wani dutsen da za a bari nan a kan ɗan'uwansa, da ba za a baje shi ba.”

Farkon Azaba

3 Yana zaune a kan Dutsen Zaitun wanda yake fuskantar Haikalin sai Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, da Andarawas suka tambaye shi a keɓe suka ce. 4 “Gaya mana yaushe za a yi waɗannan abubuwa? Wace alama kuma za a gani sa'ad da suke shirin sukuwa?” 5 Sai Yesu ya fara ce musu, “Ku kula fa kada kowa ya ɓad da ku. 6 Mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa, su ne ni, har su ɓad da mutane da yawa. 7 In kuma kun jin labarin yaƙe-yaƙe da jita-jitarsu, kada hankalinku ya tashi. Lalle ne wannan ya auku, amma ƙarshen tukuna. 8 Al'umma za ta tasar wa al'umma, mulki ya tasar wa mulki. Za a yi ta raurawar ƙasa a wurare dabam dabam, da kuma yunwa. Amma fa duk wannan masomin azaba ne tukuna. 9 “Amma ku kula da kanku, don za su kai ku gaban majalisa, a kuma yi muku d�ka a majami'u. Za a kuma kai ku gaban mahukunta da sarakuna saboda sunana, domin ku ba da shaida a gabansu. 10 Amma lalle sai an fara yi wa dukan al'ummai bishara. 11 Sa'ad da suka kai ku gaban shari'a suka miƙa ku, kada ku damu kan abin da za ku faɗa. Amma duk abin da aka yi muku baiwa da shi a lokacin nan, shi za ku faɗa, domin ba ku ne kuke magana ba, Ruhu Mai Tsarki ne. 12 Ɗan'uwa zai ba da ɗan'uwansa a kashe shi, uba kuwa ɗansa. 'Ya'ya kuma za su tayar wa iyayensu har su sa a kashe su. 13 Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana. Amma duk wanda ya jure har ƙarshe zai tsira.”

Matsananciyar Wahala

14 “Sa'ad da kuka ga an kafa mummunan aikin sāɓo mai banƙyama a wurin da bai kamata ba (mai karatu fa yă fahimta), to, sai waɗanda suke ƙasar Yahudiya su gudu su shiga duwatsu. 15 Wanda yake kan soro kuma kada ya sauko ya shiga gida garin ɗaukar wani abu. 16 Wanda yake gona kuma kada ya koma garin ɗaukar mayafinsa. 17 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci! 18 Ku yi addu'a kada abin nan ya auku da damuna. 19 A lokacin nan za a yi wata matsananciyar wahala, irin wadda ba a taɓa yi ba tun farkon halittar da Allah ya yi, har ya zuwa yanzu, ba kuwa za a ƙara yi ba har abada. 20 Da ba don Ubangiji ya taƙaita kwanakin nan ba, da ba ɗan adam ɗin da zai tsira. Amma sabili da zaɓaɓɓun nan da ya zaɓa, sai ya taƙaita kwanakin. 21 To, a lokacin nan kowa ya ce muku, ‘Kun ga, ga Almasihu nan!’ ko, ‘Kun ga, ga shi can!’ kada ku yarda. 22 Don almasihan ƙarya da annabawan ƙarya za su firfito, su nuna alamu da abubuwan al'ajabi, don su ɓad da ko da zaɓaɓɓu ma, in zai yiwu. 23 Amma ku kula! Na dai gaya muku kome tun da wuri.”

Komowar Ɗan Mutum

24 “Amma lokacin nan, wato, bayan tsabar wahalar nan, za a duhunta rana, wata kuma ba zai yi haske ba. 25 Taurari za su riƙa fāɗowa daga sararin sama, za a kuma girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama. 26 A sa'an nan ne za a ga Ɗan Mutum yana zuwa a cikin gajimare, da iko mai girma da ɗaukaka. 27 Sa'an nan zai aiko mala'ikunsa su tattaro zaɓaɓɓunsa daga gabas da yamma, kudu da arewa, wato, daga iyakar duniya har ya zuwa iyakar sama.”

Aya a kan Itacen Ɓaure

28 “Ku yi koyi da itacen ɓaure. Da zarar rassansa sun fara sakuwa, suna toho, kun san damuna ta yi kusa ke nan. 29 Haka kuma sa'ad da kuka ga waɗannan abubuwa suna aukuwa, ku sani ya kusato, a bakin ƙofa ma yake, 30 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba sai duk abubuwan nan sun auku. 31 Sararin sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”

Ba Wanda ya San Ranar ko Sa'ar

32 “Amma fa wannan rana ko wannan sa'a ba wanda ya sani, ko mala'ikun da suke Sama, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai. 33 Ku kula, ku zauna a faɗake, kuna addu'a, domin ba ku san sa'ar da lokacin zai yi ba. 34 Kamar mutum ne mai tafiya, in ya bar gida ya wakilta barorinsa, kowanne da aikinsa, ya kuma umarci mai jiran ƙofa ya zauna a faɗake. 35 To, ku zauna a faɗake fa, don ba ku san lokacin da maigidan zai dawo ba, ko da yamma ne, ko da tsakar dare ne, ko da carar zakara ne, ko da safe ne, 36 kada ya zo kwaram, ya samu kuna barci. 37 Abin kuwa da na gaya muku, ina gaya wa kowa ne, shi ne ku zauna a faɗake.”

Markus 14

Shugabanni sun Ƙulla Shawara Gāba da Yesu

1 Sauran kwana biyu a yi Idin Ƙetarewa da idin abinci marar yisti, sai manyan firistoci da malaman Attaura suka nemi hanyar kama Yesu da makirci, su kashe shi, 2 don sun ce, “Ba dai a lokacin idi ba, don kaɗa jama'a su ta da hargitsi.”

An Shafa wa Yesu Man Ƙanshi a Betanya

3 Yesu yana Betanya a gidan Saminu kuturu, yana cin abinci ke nan, sai ga wata mace ta zo da wani ɗan tandu na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tsadar gaske. Sai ta fasa tandun, ta tsiyaye masa man a kā. 4 Waɗansu kuwa da suka ji haushi, suka ce wa juna, “Mene ne na ɓata mai haka? 5 Da ma an sayar da shi fiye da dinari ɗari uku, an ba talakawa!” Sai suka hasala da ita, suna gunaguni. 6 Amma Yesu ya ce, “Ku ƙyale ta. Don me kuke damunta? Ai, alheri ta yi mini, na gaske kuwa. 7 Kullum kuna tare da talakawa, koyaushe kuma kuke so, kwa iya yi musu alheri, amma ba kullum ne kuke tare da ni ba. 8 Ta yi iyakacin ƙoƙarinta. Ta shafe jikina da mai gabannin jana'izata. 9 Hakika kuwa ina gaya muku, duk inda za a yi bishara a duniya duka, abin da matar nan ta yi, za a riƙa faɗarsa domin tunawa da ita.”

Yahuza ya Yarda ya Ba da Yesu

10 Sai Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin goma sha biyun nan, ya je wurin manyan firistoci don ya bāshe shi a gare su. 11 Da suka ji haka suka yi murna, har suka yi alkawarin su ba shi kuɗi. Shi kuwa ya riƙa neman hanyar bāshe shi.

Yesu ya Ci Idin Ƙetarewa tare da Almajiransa

12 A ranar farko ta idin abinci marar yisti, wato, ranar da aka saba yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa, sai almajiransa suka ce masa, “Ina kake so mu je mu shirya maka wurin cin Idin Ƙetarewa?” 13 Sai ya aiki almajiransa biyu, ya ce musu, “Ku shiga gari, can za ku gamu da wani mutum ɗauke da tulun ruwa, ku bi shi. 14 Duk gidan da ya shiga, ku ce wa maigidan, ‘In ji Malam, ina masaukin da zai ci Idin Ƙetarewa da almajiransa?’ 15 Shi kuwa zai nuna muku wani babban soro bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.” 16 Sai almajiran suka tashi, suka shiga gari, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Idin Ƙetarewa. 17 Da magariba ta yi, sai ya zo tare da goma sha biyun nan. 18 Suna cin abinci ke nan, sai Yesu ya ce, “Hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bāshe ni, wanda kuwa muke ci tare.” 19 Suka fara baƙin ciki, suna ce masa da ɗaya ɗaya, “Ni ne?” 20 Sai ya ce musu, “Ɗaya daga cikin goma sha biyun nan ne dai, wanda kuwa muke ci tare. 21 Ga shi, Ɗan Mutum zai tafi ne, yadda labarinsa yake a rubuce, duk da haka kuwa, kaiton mutumin nan da yake ba da Ɗan Mutum! Da ma ba a haifi mutumin nan ba, da zai fiye masa.”

Cin Jibin Ubangiji

22 Suna cikin cin abinci, sai ya ɗauki gurasa, ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya ba su, ya ce, “Ungo, wannan jikina ne.” 23 Sai ya ɗauki ƙoƙo kuma, bayan ya yi godiya ga Allah, ya ba su, dukkansu kuwa suka shassha. 24 Sa'an nan ya ce musu, “Wannan jinina ne na tabbatar da alkawari, wanda za a bayar saboda mutane da yawa. 25 Hakika, ina gaya muku, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai dai a ranar nan da zan sha wani sabo a Mulkin Allah.” 26 Da suka yi waƙar yabon Allah, sai suka fita suka tafi Dutsen Zaitun. 14 .27 Bitrus zai Yi M�sun Sanin Yesu Bitrus zai Yi M�sun Sanin Yesu 27 Yesu ya ce musu, “Duk za ku yi tuntuɓe ne, domin a rubuce yake cewa, ‘Zan bugi makiyayi, tumaki kuwa su fasu.’ 28 Amma fa bayan an tashe ni, zan riga ku zuwa ƙasar Galili.” 29 Bitrus ya ce masa, “Ko duk sun yi tuntuɓe, ni kam, ba zan yi ba.” 30 Sai Yesu ya ce masa, “Hakika, ina gaya maka, ko a wannan dare, kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi m�sun sanina sau uku.” 31 Amma Bitrus ya yi ta nanatawa da ƙarfi yana cewa, “Ko da za a kashe ni tare da kai, ba zan yi m�sun saninka ba.” Dukansu ma haka suka ce.

Yesu ya Yi Addu'a a Getsamani

32 Sai suka isa wani wuri, da ake kira Getsamani. Ya ce wa almajiransa, “Ku zauna a nan sa'ad da nake yin addu'a.” 33 Sai ya ɗauki Bitrus, da Yakubu, da Yahaya, ya kuma fara jin wahala gaya, yana damuwa ƙwarai. 34 Sai ya ce musu, “Raina yana shan wahala matuƙa, har ma kamar zan mutu. Ku dakata nan, ku zauna a faɗake.” 35 Da ya ci gaba kaɗan, sai ya fāɗi ƙasa, ya yi addu'a ko ya yiwu a ɗauke masa wannan lokacin. 36 Sa'an nan ya ce, “Ya Abba, Uba, kowane abu mai yiwuwa ne a gare ka. Ka ɗauke mini ƙoƙon wahalar nan. Duk da haka dai ba nufina ba, sai naka.” 37 Ya komo ya samu suna barci, sai ya ce wa Bitrus, “Bitrus, barci kake yi? Ashe, ba za ka iya zama a faɗake ko da sa'a ɗaya ba? 38 Ku zauna a faɗake, ku yi addu'a kada ku fāɗa ga gwaji. Lalle ruhu ya ɗauka, amma jiki rarrauna ne.” 39 Sai ya sāke komawa, ya yi addu'a, yana maimaita maganar dā. 40 Har wa yau kuma ya sāke dawowa, ya samu suna barci, don duk barci ya cika musu ido ƙwarai, suka kuwa rasa abin da za su ce masa. 41 Ya sāke komowa zuwa na uku, ya ce musu, “Har yanzu barci kuke yi kuna hutawa? Ya isa haka. Lokaci ya yi. An ba da Ɗan Mutum ga masu zunubi. 42 Ku tashi mu tafi. Kun ga, ga mai bāshe ni ɗin nan ya matso!”

An Ba da Yesu, an Kama Shi

43 Nan da nan, kafin ya rufe baki, sai ga Yahuza, ɗaya daga cikin goma sha biyun nan, da taron mutane riƙe da takuba da kulake, waɗanda manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabanni suka turo. 44 To, mai bāshe shi ɗin nan ya riga ya ƙulla da su cewa, “Wanda zan yi wa sumba, shi ne mutumin. Ku kama shi, ku tafi da shi a rirriƙe.” 45 Da zuwansa kuwa ya zo wurin Yesu, ya ce masa, “Ya Rabbi!” sai ya yi ta sumbantarsa. 46 Su kuwa suka danƙe Yesu, suka kama shi. 47 Amma ɗaya daga cikin na tsaye, ya zaro takobinsa, ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunne. 48 Sai Yesu ya ce musu, “Kun fito ne da takuba da kulake ku kama ni kamar ɗan fashi? 49 Kowace rana ina tare da ku a Haikalin ina koyarwa, amma ba ku kama ni ba. Amma an yi haka ne fa domin a cika Littattafai.” 50 Daga nan sai duk almajiran suka yashe shi, suka yi ta kansa.

Saurayin da ya Gudu

51 Sai wani saurayi, daga shi sai mayafi, ya bi shi. Suka kai masa cafka, 52 shi kuwa ya bar musu mayafin, ya gudu huntu.

Yesu a gaban 'Yan Majalisa

53 Daga nan suka tafi da Yesu wurin babban firist. Duk manyan firistoci da shugabanni da malaman Attaura suka taru a wurinsa. 54 Bitrus kuma ya bi shi daga nesa nesa, har cikin gidan babban firist ɗin, ya zauna cikin dogaran Haikali, yana jin wuta. 55 To, manyan firistoci da 'yan majalisa duka suka nemi shaidar da za a tabbatar a kan Yesu, don su samu su kashe shi, amma ba su samu ba. 56 Da yawa kam, sun yi masa shaidar zur, amma bakinsu bai zo ɗaya ba. 57 Daga baya kuma waɗansu suka taso, suka yi masa shaidar zur suka ce, 58 “Mun ji ya ce, zai rushe Haikalin nan da mutane suka gina, ya gina wani cikin kwana uku, ba kuwa ginin mutum ba.” 59 Duk da haka dai shaidarsu ba ta zo ɗaya ba. 60 Sai babban firist ya miƙe a tsakiyarsu ya tambayi Yesu ya ce, “Ba ka da wata amsa? Shaidar da mutanen nan suke yi a kanka fa?” 61 Amma ya yi shiru abinsa, bai amsa da kome ba. Sai babban firist ɗin ya sāke tambayarsa, “To, ashe, kai ɗin nan ne Almasihu Ɗan Maɗaukaki?” 62 Yesu ya ce, “Ni ne. Za ku kuwa ga Ɗan Mutum zaune dama ga Mai Iko, yana kuma zuwa cikin gajimare.” 63 Sai babban firist ya kyakketa tufafinsa, ya ce, “Wace shaida kuma za mu nema? 64 Kun dai ji sāɓon da ya yi! Me kuka gani?” Duk suka yanke masa shari'a a kan ya cancanci kisa. 65 Waɗansu ma suka fara tattofa masa yau, suka ɗaure masa idanu, suka bubbuge shi, suna ce masa, “Yi annabci!” Dogaran Haikali kuma suka yi ta marinsa. 14 .66 Bitrus ya Yi M�sun Sanin Yesu Bitrus ya Yi M�sun Sanin Yesu 66 Bitrus kuwa yana ƙasa a filin gida, sai wata baranyar babban firist ta zo. 67 Da ta ga Bitrus yana jin wuta, ta zura masa ido, ta ce, “Kai ma, ai, tare kake da Banazaren nan Yesu!” 68 Amma ya m�sa ya ce, “Ni ban ma san abin da kike faɗa ba, balle in fahimta.” Sai ya fito zaure. Zakara kuwa ya yi cara. 69 Sai baranyar ta gan shi, ta sāke ce wa waɗanda suke tsaitsaye a wurin, “Wannan ma nasu ne.” 70 Amma ya sāke musawa. Jim kaɗan sai na tsaitsayen suka ce wa Bitrus, “Lalle kai ma ɗayansu ne, don Bagalile ne kai.” 71 Sai ya fara la'antar kansa, yana ta rantserantse, yana cewa, “Ban ma san mutumin nan da kuke faɗa ba.” 72 Nan da nan sai zakara ya yi cara ta biyu. Bitrus kuwa ya tuna da maganar da Yesu ya faɗa masa cewa, “Kafin zakara ya yi cara ta biyu, za ka yi m�sun sanina sau uku.” Ko da ya tuno haka, sai ya fashe da kuka.

Markus 15

Yesu a gaban Bilatus

1 Da wayewar gari sai manyan firistoci da shugabanni, da malaman Attaura, da dukkan 'yan majalisa suka yi shawara. Sai suka ɗaure Yesu, suka tafi da shi, suka ba da shi ga Bilatus. 2 Bilatus ya tambaye shi, “Ashe, kai ɗin nan kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa masa ya ce, “Yadda ka faɗa.” 3 Sai manyan firistoci suka yi ta kai ƙararsa a kan abubuwa da yawa. 4 Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba ka da wata amsa? Dubi yawan maganganu da suke ba da shaida a kanka!” 5 Yesu dai har yanzu bai yi wata magana ba, har Bilatus ya yi mamaki.

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

6 To, a lokacin idi kuwa Bilatus ya saba sakar musu kowane ɗan sarƙa guda da suka roƙa. 7 Akwai wani mai suna Barabbas da yake ɗaure, tare da waɗansu 'yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin tawayen. 8 Jama'a fa suka matso, suka fara roƙon Bilatus ya yi musu abin da ya saba yi. 9 Sai ya amsa musu, ya ce, “Wato, kuna so ne in sakar muku Sarkin Yahudawa?” 10 Don ya gane, saboda hassada ne manyan firistoci suka bāshe shi. 11 Amma manyan firistocin suka zuga jama'a, gwamma ya sakar musu Barabbas. 12 Sai Bilatus ya sāke ce musu, “To, ƙaƙa zan yi da wanda kuke kira Sarkin Yahudawa?” 13 Sai suka sāke yin ihu suka ce, “A gicciye shi!” 14 Bilatus ya ce musu, “Ta wane hali? Wane mugun abu ne ya yi?” Amma su, sai ƙara ɗaga murya suke yi, suna cewa, “A gicciye shi!” 15 Bilatus kuwa da yake yana son ƙayatar da jama'a, ya sakar musu Barabbas. Bayan ya yi wa Yesu bulala, ya ba da shi a gicciye shi.

Sojoji sun Yi wa Yesu Ba'a

16 Sai soja suka tafi da shi cikin fāda, wato, fadar mai mulkin, suka tara dukkan rundunar soja. 17 Suka yafa masa wata alkyabba mai ruwan jar garura, suka kuma yi wani kambi na ƙaya, suka sa masa a kā. 18 Sai suka fara gaishe shi, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!” 19 Suka riƙa ƙwala masa sanda a ka, suna tattofa masa yau, sa'an nan suka durƙusa, kamar suna masa ladabi. 20 Da suka gama yi masa ba'a haka, suka yaye masa alkyabba mai ruwan jar garura, suka sa masa nasa tufafi, suka kai shi waje don su gicciye shi.

An Gicciye Yesu

21 Sai ga wani mai wucewa, sunansa Saminu Bakurane, uban Iskandari da Rufas, yana zuwa daga ƙauye. Suka fa tilasta masa ya ɗauki gicciyen Yesu. 22 Suka kai Yesu wani wuri da ake kira Golgota, wato, wurin ƙoƙon kai. 23 Suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, amma ya ƙi sha. 24 Sa'an nan suka gicciye shi, suka rarraba tufafinsa a junansu, suna kuri'a a kansu, su ga abin da kowa zai samu. 25 Da ƙarfe tara na safe suka gicciye shi. 26 Aka kuma rubuta sanarwar laifinsa sama da shi, wato, “Sarkin Yahudawa.” 27 Suka kuma gicciye 'yan fashi biyu tare da shi, ɗaya dama da shi, ɗaya kuma a hagun. 28 Wannan shi ne cikar Nassin nan da ya ce, “An lasafta shi a cikin masu laifi.” 29 Masu wucewa suka yi ta yi masa baƙar magana, suna kaɗa kai, suna cewa, “Ahaf! Kai da za ka rushe Haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, 30 to, sauko daga gicciyen, ka ceci kanka mana!” 31 Haka kuma manyan firistoci da malaman Attaura suka riƙa yi masa ba'a a junansu suna cewa, “Ya ceci waɗansu, ya kuwa kāsa ceton kansa, 32 Almasihun nan, Sarkin Isra'ila, yă sauko mana daga gicciyen yanzu, mu kuwa mu gani mu ba da gaskiya.” Waɗanda aka gicciye tare da shi su ma suka zazzage shi.

Mutuwar Yesu

33 Da rana tsaka, sai duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma. 34 Da karfe ukun, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktāna?” wato, “Ya Allahna, Ya Allahna, don me ka yashe ni?” 35 Da waɗansu na tsaitsayen suka ji haka, suka ce, “Kun ji yana kiran Iliya.” 36 Sai ɗayansu ya yiwo gudu, ya jiƙo wani soso da ruwan tsami, ya soka a sanda, ya miƙa masa yă sha, yana cewa, “Bari mu gani ko Iliya zai zo ya sauko da shi.” 37 Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi, kāna ya cika. 38 Sa'an nan labulen Haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. 39 Sa'ad da jarumi ɗin da yake tsaye yana kallon Yesu, ya ga yadda ya mutu haka, sai ya ce, “Hakika mutumin nan Ɗan Allah ne!” 40 Akwai kuma waɗansu mata da suke hange daga nesa, a cikinsu da Maryamu Magadaliya, da Maryamu mahaifiyar Yakubu ƙarami da Yusufu, da kuma Salome, 41 su ne waɗanda suka biyo shi, sa'ad da yake ƙasar Galili, suna yi masa hidima, da kuma mata da yawa da suka rako shi Urushalima.

Jana'izar Yesu

42 Da maraice lis, da yake ranar shiri ce, wato, gobe Asabar, 43 Yusufu mutumin Arimatiya ya zo, wani ɗan majalisa mai mutunci, wanda shi ma yake sauraron bayyanar Mulkin Allah, ya yi ƙarfin hali ya shiga wurin Bilatus, ya roƙa a ba shi jikin Yesu. 44 Bilatus ya yi mamaki ko ya mutu. Sai ya kira jarumi ɗin, ya tambaye shi ko Yesu ya jima da mutuwa. 45 Da ya san haka daga bakin jarumi ɗin sai ya bai wa Yusufu jikin. 46 Sai Yusufu ya sayi likkafanin lilin. Da ya sauko da Yesu, ya sa shi a likkafanin lilin ɗin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe dutse aka yi, ya kuma mirgina wani dutse a bakin kabarin. 47 Maryamu Magadaliya da Maryamu mahaifiyar Yusufu sun ga inda aka sa shi.

Markus 16

Tashin Yesu daga Matattu

1 Da Asabar ta wuce, Maryamu Magadaliya, da Maryamu mahaifiyar Yakubu, da kuma Salome, suka sayo kayan ƙanshi, domin su je su shafa masa. 2 A ranar farko ta mako, da assussuba suka tafi kabarin, da fitowar rana sai suka isa. 3 Suna ce wa juna, “Wa zai mirgine mana dutsen nan daga bakin kabarin?” 4 Da suka ɗaga kai, suka ga, ashe, an mirgine dutsen waje ɗaya, ga shi kuwa, ƙato ne ƙwarai. 5 Suna shiga kabarin, sai suka ga wani saurayi a zaune daga dama, sanye da farar riga. Sai suka firgita. 6 Shi kuwa ya ce musu, “Kada ku firgita. Yesu Banazare kuke nema, wanda aka gicciye. Ai, ya tashi, ba ya nan. Kun ga ma wurin da suka sa shi! 7 Amma ku tafi ku gaya wa almajiransa, duk da Bitrus, cewa, zai riga ku zuwa ƙasar Galili, a can ne za ku gan shi, kamar yadda ya faɗa muku.” 8 Sai suka fita, suka ruga a guje daga kabarin, suna rawar jiki a ruɗe. Ba su kuma ce wa kowa kome ba, domin suna tsoro.

Yesu ya Bayyana ga Maryamu Magadaliya

9 Da ya tashi da rai da wuri ranar farko ta mako, ya fara bayyana ga Maryamu Magadaliya, wadda ya fitar wa da aljannu bakwai. 10 Ita kuwa ta tafi ta faɗa wa waɗanda dā suke tare da shi, ta tarar suna baƙin ciki, suna kuka. 11 Amma da suka ji yana da rai, har ma ta gan shi, sai suka ƙi gaskatawa.

Yesu ya Bayyana ga Almajirai Biyu

12 Bayan haka ya bayyana da wata kama ga waɗansu biyu daga cikinsu, sa'ad da suke tafiya ƙauye. 13 Suka koma suka gaya wa sauran, su ma kuwa ba su gaskata su ba.

Umarnin Yesu ga Goma Sha Ɗayan

14 Daga baya ya bayyana ga goma sha ɗayan nan, su kansu, sa'ad da suke cin abinci. Sai ya tsawata musu a kan rashin bangaskiyarsu da taurin kansu, domin ba su gaskata waɗanda suka gan shi bayan ya tashi ba. 15 Sai ya ce musu, “Ku tafi ko'ina a duniya, ku yi wa dukkan 'yan adam bishara. 16 Duk wanda ya ba da gaskiya, aka kuma yi masa baftisma, zai sami ceto. Amma wanda ya ƙi ba da gaskiya za a hukunta shi. 17 Za a ga waɗannan mu'ujizai wurin masu ba da gaskiya, wato, da sunana za su fitar da aljannu, za su yi magana da waɗansu baƙin harsuna, 18 za su iya ɗaukar maciji, kowace irin guba kuma suka sha, ba za ta cuce su ba ko kaɗan, za su kuma ɗora wa marasa lafiya hannu, su warke.”

An Ɗauke Yesu zuwa Sama

19 To, bayan da Ubangiji Yesu ya yi musu jawabi, aka ɗauke shi aka kai shi Sama, ya zauna dama ga Allah. 20 Su kuwa suka tafi, suka yi ta wa'azi ko'ina, Ubangiji yana taimakonsu, yana kuma tabbatar da maganarsu ta mu'ujizan nan da suke biye da maganar.

Luka 1

Gabatarwa

1 Tun da yake mutane da yawa sun ɗauka su tsara labarin waɗannan al'amura da suka tabbata a cikinmu, 2 daidai yadda waɗanda suke shaidu tun farkon al'amari, masu hidimar Maganar, suka rattaba mana, 3 da yake kuma na bi diddigin kowane abu daidai tun farko, ni ma dai na ga ya kyautu in rubuta maka su bi da bi, ya mafifici Tiyofalas, 4 domin kă san ingancin maganar da aka sanar da kai baki da baki.

An Yi Faɗin Haihuwar Yahaya Maibaftisma

5 A zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na ƙungiyar Abaija. Yana auren wata a cikin zuriyar Haruna, sunanta Alisabatu. 6 Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna bin umarnin Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi. 7 Amma ba su da ɗa, don Alisabatu bakararriya ce, dukansu biyu kuma sun tsufa. 8 Ana nan, wata rana Zakariya yana a kan hidimarsa ta firist, a kan ƙungiyarsu, 9 bisa ga al'adar hidimar firistoci, sai kuri'a ta nuna shi ne mai shiga Haikalin Ubangiji, ya ƙona turare. 10 A lokacin ƙona turare kuwa duk taron jama'a suna waje, suna addu'a, 11 sai wani mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, yana tsaye a dama da bagadin ƙona turare. 12 Da Zakariya ya gan shi ya firgita, tsoro ya kama shi. 13 Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro Zakariya, an karɓi addu'arka, matarka Alisabatu za ta haifa maka ɗa, za ka kuma sa masa suna Yahaya. 14 Za ka yi murna da farin ciki, Mutane da yawa kuma za su yi farin ciki da haihuwarsa. 15 Domin zai zama mai girma a wurin Ubangiji, Ba kuwa zai sha ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Za a cika shi da Ruhu Mai Tsarki Tun yana cikin mahaifiyarsa. 16 Zai kuma juyo da Isra'ilawa da yawa ga Ubangiji Allahnsu. 17 Zai riga shi gaba cikin ruhu da iko irin na Iliya. Yă mai da hankalin iyaye a kan 'ya'yansu, Yă kuma juyo da marasa biyayya su bi hikimar adalai, Ya tanada wa Ubangiji jama'a, domin ya same su a shirye.” 18 Sai Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta ƙaƙa zan san haka? Ga ni tsoho, maiɗakina kuma ta kwana biyu.” 19 Sai mala'ikan ya amsa ya ce, “Ni ne Jibra'ilu da nake tsaye a gaban Allah. An aiko ni ne in yi maka magana, in kuma yi maka wannan albishir. 20 To, ga shi, za ka babance, ba za ka iya magana ba, sai a ran da al'amuran nan suka auku, don ba ka gaskata maganata ba, za a kuwa cika ta a lokacinta.” 21 Jama'a suna ta jiran Zakariya, suna mamakin jinkirinsa a Haikali. 22 Da ya fito, ya kāsa yi musu magana. Sai suka gane lalle an yi masa wahayi ne a Haikalin. Sai ya riƙa yi musu nuni, amma ba ya magana. 23 Sa'ad da kuma kwanakin hidimarsa suka cika, ya koma gida. 24 Bayan kwanakin nan mata tasa Alisabatu ta yi ciki. Sai ta riƙa ɓuya har wata biyar, tana cewa, 25 “Haka Ubangiji ya yi mini a kwanakin da ya dube ni da rahama, domin yă kawar mini da wulakanci a wurin mutane.”

An Yi Faɗin Haihuwar Yesu

26 A wata na shida Allah ya aiko mala'ika Jibra'ilu zuwa wani gari a ƙasar Galili, mai suna Nazarat, 27 gun wata budurwa da aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu, na zuriyar Dawuda, sunan budurwar kuwa Maryamu. 28 Sai mala'ikan ya je wurinta, ya ce, “Salama a gare ki, yake zaɓaɓɓiya, Ubangiji yana tare da ke!” 29 Amma ta damu ƙwarai da maganar, ta yi ta tunani ko wannan wace irin gaisuwa ce. 30 Mala'ikan kuma ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah. 31 Ga shi kuma, za ki yi ciki, ki haife ɗa, ki kuma raɗa masa suna Yesu. 32 Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dawuda, 33 Zai kuma mallaki zuriyar Yakubu har abada, Mulkinsa kuwa ba shi da matuƙa.” 34 Sai Maryamu ta ce wa mala'ikan, “T ƙaƙa wannan zai yiwu, tun da yake ba a kai ni ɗaki ba?” 35 Mala'ikan ya amsa mata ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, Ikon Maɗaukaki kuma zai lulluɓe ki. Saboda haka Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah. 36 Ga shi kuma, 'yar'uwarki Alisabatu ma ta yi cikin ɗa namiji da tsufanta, wannan kuwa shi ne watanta na shaida, ita da ake ce wa bakararriya. 37 Ba wata faɗar Allah da za ta kāsa cika.” 38 Sai Maryamu ta ce, “To, ga shi, ni baiwar Ubangiji ce, yă zama mini yadda ka faɗa.” Sai mala'ikan ya tashi daga gare ta.

Maryamu ta Ziyarci Alisabatu

39 A kwanakin nan Maryamu ta tashi da hanzari, ta tafi wata ƙasa mai duwatsu, zuwa wani gari na ƙasar Yahuza. 40 Ta shiga gidan Zakariya ta gai da Alisabatu. 41 Sai ya zamana da Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, jariri ya motsa da ƙarfi a cikinta. Aka kuwa cika Alisabatu da Ruhu Mai Tsarki, 42 har ta tā da murya da ƙarfi, ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata, ɗan cikinki kuma mai albarka ne! 43 Ta yaya wannan alheri ya same ni, har da mahaifiyar Ubangijina za ta zo gare ni? 44 Domin kuwa da jin muryarki ta gaisuwa a kunnena, sai jaririn ya motsa da ƙarfi a cikina domin farin ciki. 45 Albarka tā tabbata ga wadda ta gaskata, domin za a cika abubuwan da Ubangiji ya aiko a faɗa mata.”

Waƙar Maryamu

46 Sai Maryamu ta ce, “Zuciyata tana ɗaukaka shi, Ubangiji, 47 Allah Mai Cetona, da shi ruhuna yake ta farin ciki, 48 Domin fa shi ya dubi ƙasƙancin baiwarsa. Ga shi, jama'a ta dukan zamanai na nan gaba, za su ce mini mai albarka ce nan gaba. 49 Domin fa shi da yake Mai Iko, Manyan al'amura ya yi mini, Sunansa labudda Mai Tsarki ne. 50 Daga zamanai ya zuwa wani zamani, Jinƙansa yana ga waɗanda suke tsoronsa. 51 Manyan ayyuka da ya yi, Masu girmankai, su da dabarbarunsu ya warwatsa. 52 Ya fiffitar da sarakuna a sarauta, Ya ɗaukaka ƙasƙantattu. 53 Mayunwata ya ƙosar da abubuwan alheri, Mawadata kuwa ya sallame su hannu wofi. 54 Ya taimaka wa baransa Isra'ila, Domin yana tunawa da jinƙansa. 55 Ya cika faɗarsa ga kakanninmu, Ga Ibrahim da zuciyarsa, har abada.” 56 Maryamu kuma ta zauna tare da Alisabatu wajen wata uku, sa'an nan ta koma gida.

Haihuwar Yahaya Maibaftisma

57 To, lokacin Alisabatu na haihuwa ya yi, ta kuwa haifi ɗa namiji. 58 Sai maƙwabta da 'yan'uwanta suka ji yadda Ubangiji ya yi ƙanta ƙwarai, har suka taya ta farin ciki. 59 Sai ya zamana a rana ta takwas suka zo yi wa ɗan yaron kaciya. A dā za su sa masa sunan mahaifinsa, Zakariya, 60 amma mahaifiyarsa ta ce, “A'a, Yahaya za a sa masa.” 61 Sai suka ce mata, “Ai kuwa, ba wani ɗan'uwanku mai suna haka.” 62 Sai suka alamta wa mahaifinsa, suna neman sunan da yake so a sa masa. 63 Sai ya nema a ba shi allo, sa'an nan ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Duka suka yi mamaki. 64 Nan da nan ya sami baki, kwaɗon harshensa ya saku, ya fara magana, yana yabon Allah. 65 Sai tsoro ya kama dukan maƙwabtansu. Aka yi ta baza labarin duk waɗannan al'amura ko'ina a dukan ƙasa mai duwatsu ta Yahudiya. 66 Duk waɗanda suka ji kuwa suka riƙe a zuciyarsu, suna cewa, “Me ke nan ɗan yaron nan zai zama?” Gama ikon Ubangiji yana tare da shi.

Waƙar Zakariya

67 Sai aka cika mahaifinsa Zakariya da Ruhu Mai Tsarki, ya yi annabci, ya ce, 68 “Ubangiji Allahn Isra'ila, A gare shi ne lalle yabo yake tabbata, Domin ya kula, ya yi wa jama'arsa fansa. 69 Ya ta da Mai Ceto mai iko dominmu, Daga zuriyar baransa Dawuda. 70 Yadda tun tuni ya faɗa ta bakunan Annabawa nasa tsarkakan nan, 71 Yă cece mu daga abokan gābanmu, Har ma daga dukan maƙiyanmu. 72 Domin nuna jinƙai ne ga kakanninmu, Yă tuna da alkawarinsa mai tsarkin nan. 73 Shi ne rantsuwar nan wadda ya yi wa ubanmu Ibrahim, 74 Domin yana cetonmu daga abokan gābanmu, Mu bauta masa ba da jin tsoro ba, 75 Sai dai da tsarki da adalci a gabansa, Dukan iyakar kwanakin nan namu. 76 Kai kuma, ɗan yarona, za a ce da kai annabin Maɗaukaki, Gama za ka riga Ubangiji gaba, Domin ka shisshirya hanyoyinsa, 77 Kă sanar da ceto ga jama'arsa, Wato ta samun gafarar zunubansu, 78 Saboda tsananin jinƙai na Allahnmu, Daga Sama hasken asubahi zai ɓullo mana, Daga can Sama ne fa zai keto mana, 79 Domin yă haskaka na zaune cikin duhu, Da waɗanda suke zaune a bakin mutuwa, Domin ya bishe mu a hanyar salama.” 80 Sai ɗan yaron ya girma, ya ƙarfafa a ruhu. Ya kuwa zauna a jeji har ranar bayyanarsa ga Isra'ila.

Luka 2

Haihuwar Yesu

1 A kwanakin nan Kaisar Augustas ya yi shela, cewa a rubuta dukkan mutanen da suke ƙarƙashin mulkinsa. 2 Wannan ita ce ƙidaya ta fari da aka yi a zamanin Kiriniyas, mai mulkin ƙasar Suriya. 3 Kowa sai ya tafi garinsu a rubuta shi. 4 Yusufu shi ma ya tashi daga birnin Nazarat, a ƙasar Galili, ya tafi ƙasar Yahudiya, ya je birnin Dawuda, da ake kira Baitalami (domin shi daga gidan Dawuda ne, na cikin zuriyarsa), 5 don a rubuta shi, duka da Maryamu wadda yake tashin, wadda take kuma da ciki. 6 Sa'ad da suke a can kuwa, sai lokacin haihuwarta ya yi. 7 Sai ta haifi ɗanta na fari, ta rufe shi da zanen goyo, ta kuma kwantar da shi a wani kwamin dabbobi, don ba su sami ɗaki a masaukin ba.

Makiyaya da Mala'iku

8 A wannan yankin ƙasa kuwa waɗansu makiyaya suna kwana a filin, suna tsaron garken tumakinsu da daddare. 9 Sai ga wani mala'ikan Ubangiji a tsaye kusa da su, ɗaukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, har suka tsorata gaya, 10 Sai mala'ikan ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ga shi, albishir na kawo muku na farin ciki mai yawa, wanda zai zama na dukan mutane. 11 Domin yau an haifa muku Mai Ceto a birnin Dawuda, wanda yake shi ne Almasihu, Ubangiji. 12 Ga alamar da za ku gani, za ku sami jariri a rufe da zanen goyo, kwance a kwamin dabbobi.” 13 Ba labari sai ga taron rundunar Sama tare da mala'ikan nan, suna yabon Allah, suna cewa, 14 “Ɗaukaka ga Allah ta tabbata, a can cikin Sama mafi ɗaukaka. A duniya salama ta tabbata, ga mutanen da yake murna da su matuƙa.” 15 Da mala'iku suka tafi daga gare su suka koma Sama, sai makiyayan suka ce wa juna, “Mu tafi Baitalami yanzu, mu ga abin nan da ya faru, wanda Ubangiji ya sanar da mu.” 16 Sai suka tafi da hanzari, suka sami Maryamu da Yusufu, da kuma jaririn a kwance cikin kwamin dabbobi. 17 Da suka gan shi, suka bayyana maganar da aka faɗa musu a game da wannan ɗan yaro. 18 Duk waɗanda suka ji kuma, suka yi ta al'ajabin abin da makiyayan nan suka faɗa musu. 19 Maryamu kuwa sai ta riƙe duk abubuwan da aka faɗa, tana bimbini a zuci. 20 Makiyayan suka koma, suna ta ɗaukaka Allah, suna yabonsa, saboda duk abin da suka ji, suka kuma gani, yadda aka gaya musu.

Kaciyar Yesu

21 Da rana ta takwas ta kewayo da za a yi masa kaciya, aka raɗa masa suna Yesu, wato sunan da mala'ika ya faɗa kafin ya zauna a ciki.

Miƙa Yesu a Haikali

22 Da kwanakin tsarkakewarsu suka cika bisa ga Shari'ar Musa, suka kawo shi Urushalima, su miƙa shi ga Ubangiji 23 (kamar dai yadda yake a rubuce a Shari'ar Ubangiji cewa, “Duk ɗan farin da aka haifa, za a ce tsattsarka ne shi na Ubangiji,”) 24 su kuma yi hadaya bisa ga abin da aka faɗa a Shari'ar Ubangiji cewa, “Kurciyoyi biyu, ko kuwa 'yan shila biyu.” 25 To, akwai wani mutum a Urushalima, mai suna Saminu, adali, mai bautar Allah, yana kuma ɗokin ganin ta'aziyyar Isra'ila. Ruhu Mai Tsarki kuwa yana tare da shi. 26 Ruhu Mai Tsarki kuwa ya riga ya bayyana masa, cewa ba zai mutu ba sai ya ga Almasihun Ubangiji. 27 Ruhu yana iza shi, sai ya shiga Haikalin. Da iyayen suka shigo da ɗan yaron nan Yesu, su yi masa yadda ka'idar Shari'ar ta ce, 28 sai Saminu ya rungume shi, ya yi wa Allah godiya, ya ce, 29 “Yanzu kam, ya Mamallaki, Sai ka sallami bawanka lafiya, Bisa ga abin da ka faɗa, 30 Don na ga cetonka zahiri, 31 Da ka shirya a gaban kabilai duka, 32 Haske mai bayyana wa alummai hanyarka, Da kuma ɗaukakar jama'arka Isra'ila.” 33 Mahaifiyarsa da mahaifinsa kuwa suna mamakin abin da aka faɗa a game da shi, 34 Sai Saminu ya sa musu albarka, ya ce wa Maryamu mahaifiyar Yesu, “Kin ga wannan yaro, shi aka sa ya zama sanadin fāɗuwar waɗansu, tashin waɗansu kuma da yawa a cikin Isra'ila, Zai kuma zama alama wadda ake kushenta, 35 Domin tunanin zukata da yawa su bayyana. I, ke ma, takobi zai zarta zuciyarki.” 36 Akwai kuma wata annabiya, mai suna Hannatu, 'yar Fanuyila, na kabilar Ashiru. Ta kuwa tsufa ƙwarai, ta yi zaman aure shekara bakwai bayan ɗaukarta na budurci, 37 da mijinta ya mutu kuma ta yi zaman gwauranci har shekara tamanin da huɗu. Ba ta rabuwa da Haikalin, tana bauta wa Allah dare da rana ta wurin yin addu'a da azumi. 38 Nan tāke ita ma ta zo, ta yi wa Allah godiya, ta kuma yi maganar ɗan yaron nan ga dukan masu sauraron fansar Urushalima.

Komawa Nazarat

39 Bayan sun ƙare kome da kome bisa ga Shari'ar Ubangiji, sai suka koma ƙasar Galili suka tafi garinsu Nazarat. 40 Ɗan yaron kuwa ya girma, ya kawo ƙarfi, yana mai matuƙar hikima. Alherin Allah kuwa yana tare da shi.

Saurayi Yesu ya Shiga Haikali

41 To, iyayensa sukan je Urushalima kowace shekara a lokacin Idin Ƙetarewa. 42 Da Yesu ya shekara goma sha biyu, sai suka tafi tare da shi bisa ga al'adarsu a lokacin idi. 43 Da aka gama idin kuma, suna cikin komowa, sai yaron, wato Yesu, ya tsaya a Urushalima, ba da sanin iyayensa ba. 44 Su kuwa suka yi ta tafiya yini guda, suna zaton yana cikin ayari. Sai suka yi ta cigiyarsa cikin 'yan'uwansu da idon sani. 45 Da ba su same shi ba, suka koma Urushalima, suna ta cigiyarsa. 46 Sai kuma a rana uku suka same shi a Haikalin yana zaune a tsakiyar malamai, yana sauraronsu, yana kuma yi musu tambayoyi. 47 Duk waɗanda suka ji shi kuwa suka yi al'ajiin irin fahimtarsa da amsoshinsa. 48 Da suka gan shi suka yi mamaki, sai mahaifiyarsa ta ce masa, “Ya kai ɗana, yaya ka yi mana haka? Ga shi nan, ni da babanka muna ta nemanka duk ranmu a ɓace.” 49 Sai ya ce musu, “Me ya sa kuka yi ta nemana? Ashe, ba ku sani wajibi ne in yi sha'anin Ubana ba?” 50 Amma ba su fahimci maganar da ya yi musu ba. 51 Sai ya koma Nazarat tare da su, yana yi musu biyayya. Mahaifiyarsa kuwa tana riƙe da dukan abubuwan nan a ranta. 52 Yesu kuwa ya yi ta ƙaruwa da hikima, da girma, da kuma tagomashi wurin Allah da mutane.

Luka 3

Wa'azin Yahaya Maibaftisma

1 A shekara ta goma sha biyar ta mulkin Kaisar Tibariyas, Buntus Bilatus yana mulkin Yahudiya, Hirudus yana sarautar Galili, ɗan'uwansa Filibus yana sarauta Ituriya da Tarakunitas, Lisaniyas kuma yana sarautar Abiliya, 2 a zamanin da Hanana da Kayafa suke manyan firistoci, Maganar Allah ta zaike wa Yahaya ɗan Zakariya a jeji. 3 Sai ya zaga duk lardin bakin Kogin Urdun, yana wa'azi, cewa mutane su tuba a yi musu baftisma, domin a gafarta musu zunubansu, 4 yadda yake a rubuce a Littafin Annabi Ishaya cewa, “Muryar mai kira a jeji tana cewa, Ku shirya wa Ubangiji tarfarki, Ku miƙe hanyoyinsa, 5 Za a cike kowane kwari, Kowane dutse da kowane tsauni za a baje su. Za a miƙe karkatattun wurare, Za a bi da hanyoyin da ba su biyu ba. 6 Dukkan 'yan adam kuma za su ga ceton Allah.” 7 Saboda haka, Yahaya ya ce wa taron jama'ar da suke zuwa domin ya yi musu baftisma, “Ku macizai! Wa ya gargaɗe ku ku guje wa fushin nan mai zuwa? 8 Ku yi aikin da nuna tubarku, kada ma ku ko fara cewa a ranku Ibrahim ne ubanku. Ina dai gaya muku Allah da iko ya halitta wa Ibrahim 'ya'ya daga duwatsun nan. 9 Ko yanzu ma an ɗora bakin gatari a gindin itatuwa. Saboda haka duk itacen da bai yi 'ya'ya masu kyau ba, sai a sare shi, a jefa a wuta.” 10 Sai taron suka tambaye shi suka ce, “Me za mu yi ke nan?” 11 Ya amsa musu ya ce, “Duk mai taguwa biyu, ya raba da marar ita, mai abinci ma haka.” 12 Masu karɓar haraji ma suka zo a yi musu baftisma, suka ce masa, “Malam, me za mu yi?” 13 Ya ce musu, “Kada ku karɓi fiye da abin da aka umarce ku.” 14 Waɗansu soja ma suka tambaye shi, “To, mu fa, me za mu yi?” Sai ya ce musu, “Kada ku yi wa kowa ƙwace ko ƙazafi. Ku dai dangana da albashinku.” 15 Da yake mutane duk sun zaƙu, kowa yana wuswasi a ransa a game da Yahaya, ko watakila shi ne Almasihu, 16 sai Yahaya ya amsa wa dukansu ya ce, “Ni kam, da ruwa nake yi muku baftisma, amma wani yana zuwa wanda ya fi ni girma, wanda ko maɗaurin takalminsa ma ban isa in kwance ba. Shi ne zai yi muku baftisma da Ruhu Mai Tsarki, da kuma wuta. 17 Ƙwaryar shiƙarsa tana hannunsa, zai kuwa share masussukarsa sarai sarai, ya taro alkama ya sa a rumbunsa, amma ɓuntun sai ya ƙone shi a wuta marar mutuwa.” 18 Ta haka, da waɗansu gargaɗi masu yawa, Yahaya ya yi wa jama'a bishara. 19 Amma sarki Hirudus, wanda Yahaya ya tsawata wa a kan maganar Hirudiya, matar ɗan'uwansa, da kuma dukan mugayen ayyukan da ya yi, 20 sai ya ƙara da kulle Yahaya a kurkuku.

An Yi wa Yesu Baftisma

21 To, da aka yi wa dukan mutane baftisma, Yesu ma aka yi masa baftisma, yana addu'a ke nan, sai sama ta dāre, 22 Ruhu Mai Tsarki ya sauko masa da wata siffa, kamar kurciya. Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Kai ne Ɗana ƙaunataccena, ina farin ciki da kai ƙwarai,”

Asalin Mutuntakar Yesu

23 Yesu kuwa sa'ad da ya fara koyarwa, yana da shekara wajen talatin. An ɗauke shi a kan, shi ɗan Yusufu ne, wanda yake ɗan Heli, 24 Heli ɗan Matat, Matat ɗan Lawi, Lawi ɗan Malki, Malki ɗan Yanna, Yanna ɗan Yusufu, 25 Yusufu ɗan Matatiya, Matatiya ɗan Amos, Amos ɗan Nahum, Nahum ɗan Azaliya, Azaliya ɗan Najaya, 26 Najaya ɗan Ma'ata, Ma'ata ɗan Matatiya, Matatiya ɗan Shimeya, Shimeya ɗan Yusufu, Yusufu ɗan Yahuza, 27 Yahuza ɗan Yowana, Yowana ɗan Refaya, Refaya ɗan Zarubabel, Zarubabel ɗan Shayaltiyel, Sheyaltiyel ɗan Niri, 28 Niri ɗan Malki, Malki ɗan Addi, Addi ɗan Kosama, Kosama ɗan Almadama, Almadama ɗan Er, 29 Er ɗan Yosi, Yosi ɗan Eliyezer, Eliyezar ɗan Yorima, Yorima ɗan Matat, Matat ɗan Lawi, 30 Lawi ɗan Saminu, Saminu ɗan Yahuza, Yahuza ɗan Yusufu, Yusufu ɗan Yonana, Yonana ɗan Eliyakim, 31 Eliyakim ɗan Malaya, Malaya ɗan Mainana, Mainana ɗan Matata, Matata ɗan Natan, Natan ɗan Dawuda, 32 Dawuda ɗan Yesse, Yesse ɗan Obida, Obida ɗan Bo'aza, Bo'aza ɗan Salmon, Salmon ɗan Nashon, 33 Nashon ɗan Amminadab, Amminadab ɗan Aram, Aram ɗan Hesruna, Hesruna ɗan Feresa, Feresa ɗan Yahuza, 34 Yahuza ɗan Yakubu, Yakubu ɗan Ishaku, Ishaku ɗan Ibrahim, Ibrahim ɗan Tera, Yera ɗan Nahor, 35 Nahor ɗan Serug, Serug ɗan Reyu, Reyu ɗan Feleg, Feleg ɗan Eber, Eber ɗan Shela, 36 Shela ɗan Kenan, Kenan ɗan Arfakshad, Arfakshad ɗan Shem, Shem ɗan Nuhu, Nuhu ɗan Lamek, 37 Lamek ɗan Metusela, Metusela ɗan Anuhu, Anuhu ɗan Yared, Yared ɗan Mahalel, Mahalel ɗan Kenan, 38 Kenan ɗan Enosh, Enosh ɗan Shitu, Shitu ɗan Adamu, Adamu kuma na Allah.

Luka 4

Shaiɗan ya Gwada Yesu

1 Yesu kuma cike da Ruhu Mai Tsarki sai ya dawo daga Kogin Urdun. Ruhu yana iza shi zuwa jeji, 2 har kwana arba'in, Iblis yana gwada shi. A kwanakin nan bai ci kome ba. Da suka ƙare kuwa ya ji yunwa. 3 Iblis ya ce masa, “In dai kai Ɗan Allah ne, ka umarci dutsen nan ya zama gurasa,” 4 Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake, ‘Ba da gurasa kaɗai mutum zai rayu ba.’ ” 5 Sai Iblis ya kai shi wani wuri a bisa, ya nunnuna masa dukkan mulkokin duniya a ƙyiftawar ido. 6 Iblis ya ce masa, “Kai zan bai wa ikon duk waɗannan, da ɗaukakarsu, don ni aka danƙa wa, nakan kuma bayar ga duk wanda na ga dama. 7 In kuwa za ka yi mini sujada, duk za su zama naka.” 8 Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai za ka bauta wa.’ ” 9 Sai kuma ya kai shi Urushalima, ya ɗora shi can kan tsororuwar Haikali, ya ce masa, “In dai kai Ɗan Allah ne, to, dira ƙasa daga nan, 10 don a rubuce yake cewa, ‘Zai yi wa mala'ikunsa umarni a game da kai, su kiyaye ka,’ 11 da kuma ‘Za su tallafe ka, Don kada ka yi tuntuɓe da dutse.’ ” 12 Sai Yesu ya amsa masa ya ce, “Ai kuwa an ce, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’ ” 13 Bayan da Iblis ya gama irin dukan gwaje-gwajensa, ya rabu da shi ɗan lokaci tukuna.

Yesu ya Fara Hidima a Galili

14 Yesu ya koma ƙasar Galili, ikon Ruhu yana tare da shi. Labarinsa ya bazu a dukan kewayen. 15 Ya yi ta koyarwa a majami'unsu, duk ana girmama shi.

An Ƙi Yesu a Nazarat

16 Ya zo Nazarat inda aka rene shi. Ya shiga majami'a a ran Asabar kamar yadda ya saba yi. Sai ya miƙe domin ya yi karatu. 17 Aka miƙa masa Littafin Annabi Ishaya, ya buɗe littafin, ya sami inda aka rubuta cewa, 18 “Ruhun Ubangiji yana tare da ni, Domin yā shafe ni in yi wa matalauta bishara. Ya aiko ni in yi shelar saki ga ɗaurarru, In kuma buɗe wa makafi ido, In kuma 'yanta waɗanda suke a danne, 19 In yi shelar zamanin samun karɓuwa ga Ubangiji.” 20 Ya rufe littafin ya mayar wa mai hidima, ya zauna. Duk waɗanda suke a cikin majami'a suka zuba masa ido. 21 Sai ya fara ce musu, “Yau Nassin nan ya cika a kunnenku.” 22 Duk suka yabe shi, suna mamakin maganarsa ta alheri da ya faɗa, har suka ce, “Ashe, wannan ba ɗan Yusufu ba ne?” 23 Yesu ya ce musu, “Lalle za ku faɗa mini karin maganar nan, ‘Likita, warkar da kanka.’ Za ku kuma ce mini, ‘Duk abin da muka ji ka yi a Kafarnaham, ka yi a nan garinku mana.’ ” 24 Ya ce kuma, “Hakika, ina gaya muku, ba annabin da yake yardajje a garinsu. 25 Amma gaskiya nake gaya muku, a zamanin Iliya akwai mata gwauraye da yawa a Isra'ila, wato a lokacin da aka hana ruwan sama har shekara uku da wata shida, sa'ad da babbar yunwa ta game dukan ƙasar. 26 Duk da haka ba a aiki Iliya gun ko ɗaya daga cikinsu ba, sai ga wata gwauruwa, kaɗai a Zarifat ta ƙasar Sidon. 27 A zamanin Annabi Elisha kuma akwai kutare da yawa a Isra'ila, ba kuwa ɗayansu da aka tsarkake sai Na'aman, mutumin Suriya, kaɗai.” 28 Da suka ji haka, duk waɗanda suke a majami'a suka husata ƙwarai. 29 Sai suka tashi suka fitar da shi bayan gari, har suka kai shi goshin dutsen da aka gina garinsu a kai, don su jefa shi ƙasa. 30 Amma ya ratsa ta tsakiyarsu, ya yi tafiyarsa

Mai Baƙin Aljan

31 Sai ya tafi Kafarnahum, wani gari a ƙasar Galili, yana koya musu a ran Asabar. 32 Suka yi mamakin koyarwarsa domin maganarsa da hakikancewa take. 33 A majami'ar kuwa akwai wani mutum mai baƙin aljan. Sai ya ta da murya da ƙarfi ya ce, 34 “Wayyo! Ina ruwanka da mu, Yesu Banazare? Ka zo ne ka hallaka mu? Na san ko wane ne kai, Mai Tsarkin nan ne kai na Allah.” 35 Sai Yesu ya kwaɓe shi ya ce, “Yi shiru! Rabu da shi!” Bayan da aljanin ya fyaɗa shi ƙasa a tsakiyarsu, ya rabu da shi, bai kuwa cuce shi ba. 36 Sai mamaki ya kama su duka, suna ce wa juna, “Wannan wace irin magana ce? Ga shi, da tabbatarwa, da gabagaɗi kuma yake umartar baƙaƙen aljannu, suna kuwa fita.” 37 Labarinsa duk ya bazu ko'ina a kewayen ƙasar.

Yesu ya Warkar da Surukar Bitrus

38 Sai ya tashi daga majami'a, ya shiga gidan Bitrus. Surukar Bitrus kuwa tana fama da mugun zazzaɓi, sai suka roƙe shi saboda ita. 39 Sai ya tsaya a kanta, ya tsawata wa zazzaɓin, ya kuwa sake ta. Nan take ta tashi ta yi musu hidima.

Yesu ya Warkar da Mutane da yawa da Maraice

40 A daidai fāɗuwar rana, duk waɗanda suke da marasa lafiya, masu cuta iri iri, suka kakkawo su wurinsa. Sai ya ɗaɗɗora wa kowannensu hannu, ya warkar da su. 41 Aljannu kuma suka fita daga mutane da yawa, suna ihu suna cewa, “Kai Ɗan Allah ne!” Amma ya tsawata musu, ya hana su magana, don su sani shi ne Almasihu.

Yesu ya Tafi Yin Wa'azi

42 Da gari ya waye ya fita, ya tafi wani wurin a inda ba kowa. Sai taro masu yawa suka yi ta nemansa, suka je wurinsa. Sonsu ne su tsaishe shi, don kada ya tashi daga gare su. 43 Amma ya ce musu, “Lalle ne in yi wa sauran garuruwa bisharar Mulkin Allah, domin saboda wannan nufi ne aka aiko ni.” 44 Sai ya yi ta yin wa'azi a majami'un ƙasar Galili.

Luka 5

An Kama Kifi Jingim

1 Wata rana taro suna matsarsa domin su ji Maganar Allah, shi kuwa yana tsaye a bakin Tekun Janisarata, 2 sai ya hangi ƙananan jirage biyu a bakin tekun, masuntan kuwa sun fita daga cikinsu, suna wankin tarunsu. 3 Sai ya shiga ɗaya jirgin, wanda yake na Bitrus, ya roƙe shi ya ɗan zakuɗa da jirgin daga bakin gaci. Sai ya zauna ya yi ta koya wa taro masu yawa daga jirgin. 4 Da ya gama magana, ya ce wa Bitrus, “Zakuɗa da jirgin zuwa wuri mai zurfi, ku saki tarunku, ku janyo kifi.” 5 Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Maigida, dare farai muna wahala, ba mu kama kome ba, amma tun da ka yi magana zan saki tarun.” 6 Da suka yi haka kuwa, suka kamo kifi jingim, har ma tarunsu suka fara kecewa. 7 Sai suka yafato abokan aikinsu a ɗaya jirgin su zo su taimake su. Suka kuwa zo, suka ciccika jiragen nan duka biyu kamar za su nutse. 8 Da Bitrus ya ga haka, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce. “Ya Ubangiji, wane ni da za ka tsaya kusa da ni, domin ni mutum ne mai zunubi.” 9 Domin shi da waɗanda ke tare da shi duka, mamaki ya kama su saboda kifin nan da duka janyo, 10 haka ma Yakubu da Yahaya 'ya'yan Zabadi, abokan sabgar Bitrus. Sai Yesu ya ce wa Bitrus, “Kada ka ji tsoro. Nan gaba mutane za ka riƙa kamowa.” 11 Da suka kawo jiragensu gaci, suka bar kome duka suka bi shi.

Yesu ya Warkar da Kuturu

12 Wata rana Yesu yana ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa ya zo. Da ya ga Yesu ya fāɗi a gabansa, ya roƙe shi ya ce, “Ya Ubangiji, in dai ka yarda kana da ikon tsarkake ni.” 13 Sai Yesu ya miƙa hannu, ya taɓa shi, ya ce, “Na yarda, ka tsarkaka.” Nan take sai kuturtar ta rabu da shi. 14 Yesu ya kwaɓe shi kada ya gaya wa kowa, ya ce, “Sai dai ka je wurin firist ya gan ka, ka kuma yi hadaya saboda tsarkakewarka, domin tabbatarwa a gare su, kamar yadda Musa ya umarta.” 15 Amma duk da haka labarinsa sai ƙara yaɗuwa yake yi, har taro masu yawan gaske suka yi ta zuwa domin su saurare shi, a kuma warkar da su daga rashin lafiyarsu. 16 Amma shi, sai ya riƙa keɓanta a wuraren da ba kowa, yana addu'a.

Yesu ya Warkar da Shanyayye

17 Wata rana yana koyarwa, waɗansu Farisiyawa kuwa da masanan Attaura da suka fito daga kowane gari na ƙasar Galili, da na ƙasar Yahudiya, daga kuma Urushalima, suna nan a zaune. Ikon Ubangiji na warkarwa kuwa yana nan. 18 Sai ga waɗansu mutane ɗauke da wani shanyayye a kan shimfiɗa, suna ƙoƙari su shigar da shi su ajiye shi a gaban Yesu. 19 Da suka kasa samun hanyar shigar da shi saboda taro, suka hau a kan soron, suka zura shi ta tsakanin rufin soron duk da shimfiɗarsa, suka ajiye shi a tsakiyar jama'a a gaban Yesu. 20 Da Yesu ya ga bangaskiyarsu sai ya ce, “Malam, an gafarta maka zunubanka.” 21 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka fara wuswasi cewa, “Wane ne wannan da yake maganar saɓo? Wa yake iya gafarta zunubi banda Allah shi kaɗai?” 22 Da Yesu ya gane wuswasinsu, ya amsa musu ya ce, “Don me kuke wuswasi haka a zuciyarku? 23 Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuwa a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya?’ 24 Amma domin ku sakankance Ɗan Mutum yana da ikon gafarta zunubi a duniya,” sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ka ɗauki shimfiɗarka, ka tafi gida.” 25 Nan take ya tashi a gaban idonsu, ya ɗauki abin kwanciyarsa, ya tafi gida, yana ɗaukaka Allah. 26 Sai suka yi mamaki matuƙa, su duka, suka yi ta ɗaukaka Allah, tsoro kuma ya kama su, suka ce, “Yau mun ga abubuwan al'ajabi!”

Kiran Lawi

27 Bayan haka ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, a zaune, yana aiki a wurin karɓar haraji. Ya ce masa, “Bi ni.” 28 Sai ya bar kome duka, ya tashi ya bi shi. 29 Sai Lawi ya yi masa ƙasaitacciyar liyafa a gidansa, akwai kuwa taron masu karɓar haraji da waɗansu mutane suna ci tare da su. 30 Sai Farisiyawa da malamansu na Attaura suka yi wa almajiransa gunaguni suka ce, “Don me kuke ci kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?” 31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, lafiyayyu ba ruwansu da magani, sai dai marasa lafiya. 32 Ba domin in kira masu adalci na zo ba, sai dai masu zunubi, su tuba.”

Tambaya a kan Azumi

33 Sai suka ce masa, “Almajiran Yahaya suna azumi a kai a kai, suna kuma addu'a, haka kuma almajiran Farisiyawa, amma naka suna ci suna sha.” 34 Sai Yesu ya ce musu, “Wato kwa iya sa abokan ango su yi azumi tun angon yana tare da su? 35 Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa'an nan ne fa za su yi azumi.” 36 Ya kuma yi musu misali, ya ce, “Ba mai tsage ƙyalle a jikin sabuwar tufa ya yi maho a tsohuwar tufa da shi. In ma an yi, ai, sai ya kece sabuwar tufar, sabon ƙyallen kuma ba za dace da tsohuwar tufar ba. 37 Ba kuma mai ɗura sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ma an ɗura, sai sabon ruwan inabin ya fasa salkunan, ya zube, salkunan kuma su lalace. 38 Sabon ruwan inabi, ai, sai sababbin salkuna. 39 Ba wanda zai so shan sabon ruwan inabin bayan ya sha tsohon, don ya ce, ‘Ai, tsohon yana da kyau.’ ”

Luka 6

Almajirai suna Zagar Alkama a Ran Asabar

1 Wata rana a ran Asabar, yana ratsa gonakin alkama, sai almajiransa suka zāgi alkamar, suna murtsukewa suna ci. 2 Sai waɗansu Farisiyawa suka ce, “Don me kuke yin abin da bai halatta a yi ba a ran Asabar?” 3 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba sa'ad da ya ji yunwa, shi da abokan tafiyarsa? 4 Yadda ya shiga masujadar Allah, ya ɗauki keɓaɓɓiyar gurasar nan ya ci, har ma ya ba abokan tafiyarsa, wadda ba ta halatta kowa ya ci ba, sai firistoci kaɗai?” 5 Sai ya ce musu, “Ai, Ɗan Mutum shi ne Ubangijin Asabar.”

Mai Shanyayyen Hannu

6 A wata Asabar kuma ya shiga majami'a, yana koyarwa. Akwai kuwa wani mutum a ciki wanda hannunsa na dama ya shanye. 7 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka yi haƙwansa su ga ko yā warkar a ran Asabar, don su samu su kai ƙararsa. 8 Shi kuwa ya san tunaninsu. Sai ya ce wa mai shanyayyen hannun, “Taso, ka tsaya nan a tsakiya.” Sai ya tashi, ya tsaya a wurin. 9 Yesu ya ce musu, “Ina yi muku tambaya. Ya halatta ran Asabar a yi alheri ko mugunta? A ceci rai, ko a hallaka shi?” 10 Sai ya duddube su d�ke, ya ce wa mutumin, “Miƙo hannunka.” Da ya miƙa, hannunsa kuwa sai ya koma lafiyayye. 11 Sai suka husata ƙwarai, suka yi shawarar abin da za su yi wa Yesu.

Yesu ya Zaɓi Almajirai Sha Biyu

12 A kwanakin nan Yesu ya fita ya hau dutse domin yin addu'a. Dare farai yana addu'a ga Allah. 13 Da gari ya waye ya kira almajiransa, ya zaɓi goma sha biyu a cikinsu, ya ce da su manzanni. 14 Su na Bitrus, da ɗan'uwansa Andarawas, da Yakubu, da Yahaya, da Filibus, da Bartalamawas, 15 da Matiyu, da Toma, da Yakubu ɗan Halfa, da Saminu, wanda ake ce da shi Zaloti, 16 da Yahuza ɗan Yakubu, da kuma Yahuza Iskariyoti, wanda ya zama maci amana.

Yesu ya yi wa Mutane Masu Yawa Hidima

17 Sai ya gangaro tare da su, ya tsaya a wani sarari. Ga kuwa babban taro masu binsa, da kuma taro masu yawan gaske daga duk ƙasar Yahudiya da Urushalima, da kuma yankin ƙasar Taya da Sidon da suke bakun bahar, waɗanda su zo su saurare shi, a kuma warkar da cuce-cucensu. 18 Waɗanda kuma baƙaƙen aljannu suke wahalshe su, aka warkar da su. 19 Duk taron suka nema su taɓa shi, domin iko yana fitowa daga gare shi, ya kuwa warkar da su duka.

Albarka da La'ana

20 Sai ya ɗaga kai, ya dubi almajiransa, ya ce, “Albarka tā tabbata a gare ku, ku matalauta, domin Mulkin Allah naku ne. 21 “Albarka tā tabbata a gare ku, ku da kuke mayunwata a yanzu, domin za a ƙosar da ku. “Albarka tā tabbata gare ku, ku da ke kuka a yanzu domin za ku yi dariya. 22 “Albarka tā tabbata a gare ku sa'ad da mutane suka ƙi ku, suka kama ware ku, suka zage ku, suka yi ƙyamar sunanku saboda Ɗan Mutum. 23 Ku yi farin ciki a wannan rana, ku yi tsalle don murna, domin ga shi, sakamakonku mai yawa ne a Sama. Haka kakanninsu ma suka yi wa annabawa. 24 “Amma kaitonku, ku masu arziki domin kun riga kun sami taku ta'aziyya. 25 “Kaitonku, ku da kuke ƙosassu a yanzu, don za ku ji yunwa. “Kaitonku, ku masu dariya a yanzu, don za ku yi baƙin ciki, ku yi kuka. 26 “Kaitonku in kowa yana yabonku. Haka kakanninsu ma suka yi wa annabawan ƙarya.”

Ƙaunar Magabta

27 “Amma ina gaya muku, ku masu sauraro, ku ƙaunaci magabtanku, ku yi wa maƙiyanku alheri. 28 Ku sa wa masu zaginku albarka. Masu wulakanta ku kuma, ku yi musu addu'a. 29 Wanda ya mare ka a kunci ɗaya, juya masa ɗaya kuncin kuma. Wanda ya ƙwace maka mayafi, kada ka hana masa taguwarka ma. 30 Duk wanda ya roƙe ka, ka ba shi. Wanda kuma ya ƙwace maka kaya, kada ka neme shi. 31 Yadda kuke so mutane su yi muku, to, ku yi musu haka. 32 “In masoyanku kawai kuke ƙauna wace lada ce da ku? Ai, ko masu zunubi ma suna ƙaunar masoyansu. 33 In kuma sai waɗanda suke muku alheri kawai kuke yi wa alheri, wace lada ce da ku? Ai, ko masu zunubi ma haka suke yi. 34 In kuma sai ga waɗanda kuke tsammani za su biya ku ne kuke ba da rance, wace lada ce da ku? Ai, ko masu zunubi ma, sukan ba masu zunubi rance, don a biya su daidai. 35 Amma ku ƙaunaci magabtanku, kuna yi musu alheri. Ku ba da rance, kada kuwa ku tsammaci biya. Ladarku kuma za ta yi yawa, za ku kuma zama 'ya'yan Maɗaukaki, domin shi mai alheri ne ga masu butulci da kuma mugaye. 36 Ku kasance masu tausayi kamar yadda Ubanku yake mai tausayi.”

Kada ku Ɗora wa Kowa Laifi

37 “Kada ku ɗora wa kowa laifi, ku ma ba za a ɗora muku ba. Kada ku yi wa kowa mugun zato, ku ma ba za a yi muku ba. Ku yafe, ku ma sai a yafe muku. 38 Ku bayar, ku ma sai a ba ku mudu a cike, a danƙare, har ya yi tozo, har yana zuba, za a juye muku a hannun riga. Mudun da kuka auna, da shi za a aunamuku.” 39 Ya kuma ba su wani misali ya ce, “Makaho yana iya yi wa makaho jagora? Ashe, dukansu biyu ba sai su fāɗa a rami ba? 40 Almajiri ba ya fin malaminsa. Amma kowa aka karantar da shi sosai, sai ya zama kamar malaminsa. 41 Don me kake duban ɗan hakin da ke a idon ɗan'awanka, amma gungumen da yake a naka ido ba ku kula ba? 42 Ƙaƙa kuma za ka iya ce wa ɗan'uwanka, ‘Ya ɗan'uwana, bari in cire maka ɗan hakin da yake a idonka,’ alhali kuwa kai kanka ba ka ga gungumen da yake a naka ido ba? Kai munafuki! Sai ka fara cire gungumen da yake a idonka tukuna sa'an nan ka yadda za ka cire ɗan hakin da yake a idon ɗan'uwanka.”

Akan Gane Itace ta 'Ya'yansa

43 “Ba kyakkyawan itace da yake haifar munanan 'ya'ya, ba kuma mummunan itace da yake haifar kyawawan 'ya'ya. 44 Domin kowane itace da irin 'ya'yansa ake saninsa. Ai, ba a ɗiban ɓaure a jikin ƙaya, ko kuwa inabi a jikin sarƙaƙƙiya. 45 Mutumin kirki kam ta kyakkyawar taskar zuciyarsa yakan yi abin kirki, mugu kuwa ta mummunar taskar zuciyarsa yakan yi mugun abu. Ai, abin da ya ci rai, shi mutum yake faɗa.”

Kafa Harsashin Gini Iri Biyu

46 “Don me kuke kirana, ‘Ubangiji, Ubangiji,’ ba kwa kuwa yin abin da na faɗa muku? 47 Duk mai zuwa wurina, yake yin maganata, yake kuma aikata ta, zan nuna muku kwatancinsa. 48 Kamar mutum yake mai gina gida, wanda ya yi haƙa mai zurfi, har ya sa harsashin ginin a kan fā. Da aka yi rigyawa, sai ruwan kogi ya bugi gidan, amma bai iya girgiza shi ba, saboda an gina shi da aminci. 49 Amma wanda ya ji maganata, bai kuwa aikata ba, kamar mutum yake wanda ya gina gida a kan turɓaya, ba harsashi. Ruwan kogi ya buge shi, nan da nan ya rushe. Wannan gida ya yi mummunar ragargajewa!”

Luka 7

Yesu ya Warkar da Bawan Wani Jarumi

1 Bayan da Yesu ya ƙare jawabinsa duka a gaban jama'a, ya shiga Kafarnahum. 2 To, sai bawan wani jarumi, wanda Ubangidansa ke jin daɗinsa, ya yi rashin lafiya, har ya kai ga bakin mutuwa. 3 Da jarumin ya ji labarin Yesu, sai ya aiki waɗansu shugabannin Yahudawa wurinsa, su roƙe shi ya zo ya warkar da bawansa. 4 Da suka isa wurin Yesu sai suka roƙe shi ƙwarai suka ce, “Ai, ya cancanci a yi masa haka, 5 don yana ƙaunar jama'armu, shi ne ma ya gina mana majami'armu.” 6 Sai Yesu ya tafi tare da su. Da ya matso kusa da gidan, sai jarumin ya aiki aminansa wurinsa su ce masa, “Ya Ubangiji, kada ka wahalar da kanka. Ban ma isa har ka zo gidana ba. 7 Shi ya sa ban ga ma na isa in zo wurinka ba, amma kă yi magana kawai, yarona kuwa sai ya warke. 8 Don ni ma a hannun wani nake, da kuma soja a hannuna, in ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai ya je, wani kuwa in ce masa, ‘Zo,’ sai ya zo, in ce wa bawana, ‘Yi abu kaza,’ sai ya yi.” 9 Da Yesu ya ji haka, ya yi mamakinsa, ya kuma juya ya ce wa taron da suke biye da shi, “Ina gaya muku, ko a cikin Isra'ila ban taɓa samun bangaskiya mai ƙarfi irin wannan ba.” 10 Da waɗanda aka aika suka koma gidan, suka sami bawan garau.

Yesu ya Tā da Ɗan Gwauruwa

11 Ba da daɗewa ba, Yesu ya tafi wani gari, mai suna Nayin, almajiransa da kuma babban taro suka tafi da shi. 12 Ya kusaci ƙofar garin ke nan, sai ga wani mamaci ama ɗauke da shi, shi kaɗai ne wajen mahaifiyarsa, gwauruwa. Mutanen gari da yawa sun rako ta. 13 Da Ubangiji ya gan ta, ya ji tausayinta, ya kuma ce mata, “Daina kuka.” 14 Sa'an nan ya matso, ya taɓa makarar, masu ɗauka kuma suka tsaya cik. Sai Yesu ya ce, “Samari, na ce maka ka tashi.” 15 Mamacin ya tashi zaune, ya fara magana. Yesu kuwa ya ba da shi ga mahaifiyarsa. 16 Sai tsoro ya kama su duka, suka ɗaukaka Allah suna cewa, “Lalle, wani annabi mai girma ya bayyana a cikinmu,” da kuma, “Allah ya kula da jama'arsa.” 17 Wannan labarin nasa kuwa ya bazu a dukan ƙasar Yahudiya da kewayenta.

'Yan Saƙo daga Yahaya Maibaftisma

18 Sai almajiran Yahaya suka gaya masa dukan abubuwan nan. 19 Sai Yahaya ya kira almajiransa biyu, ya aike su gun Ubangiji yana tambaya cewa, “Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?” 20 Da mutanen nan suka isa wurinsa, suka ce, “Yahaya Maibaftisma ne ya aiko mu a gare ka, yana tambaya, cewa, ‘Kai ne mai zuwan nan, ko kuwa mu sa ido ga wani?’ ” 21 Nan tāke Yesu ya warkar da mutane da yawa daga rashin lafiyarsu da cuce-cucensu da kuma baƙaƙen aljannu. Makafi da yawa kuma ya yi musu baiwar gani. 22 Sai ya amsa musu ya ce, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da kuka gani. Makafi suna samun gani, guragu suna tafiya, ana tsarkake kutare, kurame suna ji, ana ta da matattu, ana kuma yi wa matalauta bishara. 23 Albarka tā tabbata ga wanda ba ya tuntuɓe sabili da ni.” 24 Bayan da jakadun Yahaya sun tafi, sai Yesu ya fara yi wa taro maganar Yahaya, ya ce, “Kallon me kuka je yi a jeji? Kyauron da iska take kaɗawa? 25 To, kallon me kuka je yi? Wani mai adon alharini? Ai kuwa, masu adon gaske, masu zaman annashuwa, a fāda suke. 26 To, kallon me kuka ya yi? Annabi? Hakika, ina gaya muku, har ya fi annabi nesa. 27 Wannan shi ne wanda labarinsa yake rubuce cewa, ‘Ga shi, na aiko manzona ya riga ka gaba, Wanda zai shirya maka hanya gabaninka.’ 28 Ina gaya muku, a cikin duk waɗanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka wanda ya fi ƙasƙanta a Mulkin Allah ya fi shi.” 29 Da duk jama'a da masu karɓar haraji suka ji haka, suka tabbata Allah mai adalci ne, aka yi musu baftisma da baftismar Yahaya. 30 Amma Farisiyawa da masanan Attaura suka shure abin da Allah yake nufinsu da shi, da yake sun ƙi ya yi musu baftisma. 31 “To, da me zan kwatanta mutanen zamanin nan? Waɗanne iri ne su? 32 Kamar yara suke da suke zaune a bakin kasuwa, suna kiran juna, suna cewa, ‘Mun busa muku sarewa, ba ku yi rawa ba, Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.’ 33 Ga shi, Yahaya Maibaftisma ya zo, ba ya cin gurasa, ba ya shan ruwan inabi, amma kuna cewa, ‘Ai, yana da iska.’ 34 Ga Ɗan Mutum ya zo, yana ci yana sha, kuna kuma cewa, ‘Ga mai haɗama, mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi!’ 35 Duk da haka hikimar Allah, ta dukkan aikinta ne ake tabbatar da gaskiyarta.”

Yesu a Gidan Saminu Bafarisiye

36 Wani Bafarisiye ya kira shi cin abinci. Sai ya shiga gidan Bafarisiyen, ya ƙishingiɗa wurin cin abincin. 37 Sai ga wata matar garin, mai zunubi, da ta ji Yesu yana cin abinci a gidan Bafarisiyen, ta kawo wani ɗan tandu na man ƙanshi, 38 ta tsaya a bayansa a wajen ƙafafunsa, tana kuka. Sai hawayenta ya fara zuba a ƙafafunsa, ta goge su da gashinta, ta yi ta sumbantarsu, ta shafa musu man ƙanshin. 39 To, da Bafarisiyen da ya kira shi ya ga haka, sai ya ce a ransa, “Da mutumin nan annabi ne, da ya san ko wace ce, da kuma ko wace irin mace ce wannan da take taɓa shi, don mai zunubi ce.” 40 Yesu ya amsa ya ce, “Saminu, ina da magana da kai.” Sai shi kuma ya ce, “Malam, sai ka faɗa.” 41 Yesu ya ce, “Wani yana bin mutum biyu bashi, ɗaya dinari ɗari biyar, ɗayan kuma hamsin. 42 Da suka gagara biya, sai ya yafe musu dukansu biyu. To, a cikinsu wa zai fi ƙaunarsa?” 43 Saminu ya amsa masa ya ce, “A ganina, wanda ya yafe wa mai yawa.” Sai ya ce masa “Ka faɗa daidai.” 44 Da ya waiwaya wajen matar, ya ce wa Saminu. “Ka ga matar nan? Na shigo gidanka, ba ka ba ni ruwan wanke ƙafa ba, amma ita ta zub da hawayenta a ƙafafuna, ta kuma goge su da gashinta. 45 Kai ba ka sumbance ni ba, ita kuwa, tun shigowata nan ba ta daina sumbantar ƙafafuna ba. 46 Ba ka shafa mini mai a ka ba, amma ita ta shafa man ƙanshi a ƙafafuna. 47 Saboda haka ina gaya maka, zunubanta masu yawan nan duk an gafarta mata, domin ta yi ƙauna mai yawa. Wanda aka gafarta wa kaɗan kuwa, ƙauna kaɗan yake yi.” 48 Sai ya ce mata, “An gafarta miki zunubanki.” 49 Masu ci tare da shi kuwa suka fara ce wa juna, “Wannan kuwa wane ne wanda har yake gafarta zunubai?” 50 Sai Yesu ya ce matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki sauka lafiya.”

Luka 8

Waɗansu Mata sun Tafi tare da Yesu

1 Ba da daɗewa ba Yesu ya zazzaga birni da ƙauye yana wa'azi, yana yin bisharar Mulkin Allah. Su goma sha biyun nan kuwa suna tare da shi, 2 da waɗansu mata da aka raba su da baƙaƙen aljannu da kuma rashin lafiyarsu. A cikinsu da Maryamu mai suna Magadaliya, wadda aka fitar wa da aljannu bakwai, 3 da Yuwana matar Kuza, wakilin Hirudus, da Suzanatu, da kuma waɗansu da yawa da suka yi musu ɗawainiya da kayansu.

Misali da Mai Shuka

4 Da jama'a masu yawa suka taru, mutane suna ta zuwa gare shi gari da gari, sai ya yi musu misali ya ce. 5 “Wani mai shuka ya tafi shuka. Yana cikin yafa iri sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattake su, tsuntsaye suka tsince su. 6 Waɗansu kuma suka fāɗi a kan dutse. Da suka tsiro sai suka bushe, don ba danshi. 7 Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya, suka tashi tare, har ƙayar ta sarƙe su. 8 Waɗansu kuwa suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka girma, suka yi ƙwaya riɓi ɗari ɗari.” Da ya faɗi haka, sai ya ta da murya ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”

Ma'anar Misalin

9 Sai almajiransa suka tambaye shi ma'anar misalin. 10 Sai ya ce, “Ku kam, an yarda muku ku san asiran Mulkin Allah. Amma ga sauran sai da misali, don gani kam, za su gani, amma ba za su gane ba. Ji kuma, za su ji, amma ba za su fahimta ba.

Yesu ya Ba da Bayanin Misalin Mai Shuka

11 “To, misalin irin shi ne, Maganar Allah. 12 Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne kwatancin waɗanda suka ji Maganar Allah, sa'an nan iblis ya zo ya ɗauke Maganar daga zuciyarsu, don kada su ba da gaskiya su sami ceto. 13 Na kan dutsen kuwa su ne waɗanda da zarar sun ji Maganar, sai su karɓa da farin ciki. Su kam, ba su da tushe. Sukan ba da gaskiya 'yan kwanaki kaɗan, amma a lokacin gwaji, sai su bauɗe. 14 Waɗanda suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa su ne waɗanda suka ji Maganar, amma a kwana a tashi, sai yawan taraddadin duniya, da dukiya, da shagalin duniya suka sarƙe su, har su kāsa yin amfani. 15 Waɗanda suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa su ne waɗanda suka ji Maganar, suka riƙe ta kamkam da zuciya ɗaya kyakkyawa, suka jure har suka yi amfani.

Fitila a Rufe da Masaki

16 “Ba mai kunna fitila ya rufe da masaki, ko ya ajiye ta a ƙarƙashin gado. A'a, sai dai ya ɗora ta a a maɗorinta, don masu shiga su ga hasken. 17 Ba abin da yake a ɓoye da ba za a bayyana ba. Ba kuma asirin da ba sai tonu ya zama bayyananne ba. 18 Ku kula fa, ku iya ji, don mai abu akan ƙara wa. Marar abu kuwa, ko ɗan da yake tsammani yake da shi ma, sai a karɓe masa.”

Mahaifiyar Yesu da 'Yan'uwansa

19 Mahaifiyarsa da 'yan'uwansa suka zo wurinsa, amma suka kasa isa gunsa saboda taro. 20 Sai aka ce masa, “Tsohuwarka da 'yan'uwanka suna tsaye a waje, suna son ganinka.” 21 Amma ya amsa musu ya ce, “Masu jin Maganar Allah, suna kuma aikata ta, ai, su ne uwata, su ne kuma 'yan'uwana.”

Yesu ya Tsawata wa Hadiri

22 Wata rana ya shiga jirgi tare da almajiransa. Ya ce musu, “Mu haye wancan hayin teku.” Sai suka tashi. 23 Suna cikin tafiya sai barci ya kwashe shi. Hadiri mai iska ya taso a tekun, jirginsu ya tasar wa cika da ruwa, har suna cikin hatsari. 24 Suka je suka tashe shi, suka ce, “Maigida, Maigida, za mu hallaka!” Sai ya farka, ya tsawata wa iskar da kuma haukan ruwa. Sai suka kwanta, wurin ya yi tsit. 25 Ya ce musu, “Ina bangaskiyarku?” Suka kuwa tsorata suka yi mamaki, suna ce wa juna, “Wa ke nan kuma, har iska da ruwa ma yake yi wa umarni, suna kuwa yi masa biyayya?”

Warkar da Mai Aljan na Garasinawa

26 Sai suka iso ƙasar Garasinawa wadda ke hannun riga da ƙasar Galili. 27 Da saukarsa a gaci sai wani mai aljannu ya fito daga cikin gari ya tarye shi. Ya daɗe bai sa tufa ba, ba ya zama a gida kuwa, sai a makabarta. 28 Da ganin Yesu sai ya ƙwala ihu, ya fāɗi a gabansa, ya ɗaga murya ya ce, “Ina ruwanka da ni, ya Yesu Ɗan Allah Maɗaukaki? Ina roƙonka, kada ka yi mini azaba.” 29 Ya faɗi haka ne domin Yesu ya umarci baƙin aljanin ya rabu da mutumin. Gama sau da yawa aljanin yakan buge shi, akan kuma tsare shi, a ɗaure shi da sarƙa da mari, amma ya tsintsinka ɗaurin, aljanin ya kora shi jeji. 30 Sai Yesu ya tambaye shi, “Yaya sunanka?” Ya ce, “Tuli,” don aljannu da yawa sun shiga cikinsa. 31 Sai suka yi ta roƙansa kada ya umarce su su fāɗa a mahallaka. 32 A, wurin nan kuwa akwai wani babban garkin alade ne kiwo a gangaren dutse, suka roƙe shi ya yardar musu su shiga cikinsu. Ya kuwa yardar musu. 33 Sai aljannun suka rabu da mutumin, suka shiga aladun. Garken kuwa suka rungungunta ta gangaren, suka fāɗa tekun, suka hallaka a ruwa. 34 Da 'yan kiwon aladun nan suka ga abin da ya faru, suka gudu, suka ba da labari a birni da ƙauye. 35 Sai jama'a suka fiffito su ga abin da ya auku. Suka zo wurin Yesu, suka tarar da mutumin da aljannun suka rabu da shi, a zaune gaban Yesu, saye da tufa, yana cikin hankalinsa. Sai suka tsorata. 36 Waɗanda aka yi abin a gaban idonsu kuwa, suka gaya musu yadda aka warkar da mai aljannun nan. 37 Dukan mutanen kewayen ƙasar Garasinawa suka roƙi Yesu ya rabu da su, don tsoro mai yawa ya kama su. Sai ya shiga jirgi ya koma. 38 Mutumin da aljannun suka rabu da shi kuwa, ya roƙe shi izinin tafiya tare da shi. Amma ya sallame shi ya ce, 39 “Koma gida, ka faɗi irin manyan abubuwan da Allah ya yi maka.” Sai ya tafi ko'ina a cikin birnin yana sanar da manyan abubuwan da Yesu ya yi masa.

Warkar da 'Yar Yayirus da Matar da ta Taɓa Gezar Mayafin Yesu

40 To, da Yesu ya komo, taron suka yi masa maraba domin ko a dā ma duk suna jiransa ne. 41 Sai ga wani mutum mai suna Yayirus, wani shugaban majami'a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, ya roƙe shi ya je gidansa. 42 Yana da 'ya ɗaya tilo, mai shekara misalin goma sha biyu, tana kuma bakin mutuwa. Yana tafiya, taro masu yawa na matsarsa, 43 sai ga wata mace wadda ta shekara goma sha biyu tana zub da jini, ta kuma ɓad da duk abin hannunta wajen masu magani, ba wanda ya iya warkar da ita. 44 Ta raɓo ta bayansa, ta taɓa gezar mayafinsa. Nan take zubar jininta ta tsaya. 45 Sai Yesu ya ce, “Wa ya taɓa ni?” Da kowa ya yi m�su, sai Bitrus da waɗanda suke tare da shi suka ce, “Maigida, ai, taro masu yawa ne suke tutturarka, suna matsarka.” 46 Amma Yesu ya ce, “An dai taɓa ni, domin na ji wani iko ya fita daga gare ni.” 47 Da matar ta ga ba dama ta ɓuya, sai ta matso tana rawar jiki, ta fāɗi a gabansa, ta bayyana a gaban duk jama'a dalilin da ya sa ta taɓa shi, da kuma yadda ta warke nan take. 48 Sai ya ce mata, “Yata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.” 49 Yana cikin magana, sai ga wani ya zo daga gidan shugaban majami'ar, ya ce, “Ai, 'yarka ta rasu. Kada ka ƙara wahalar da Malamin.” 50 Amma da Yesu ya ji haka, ya amsa ya ce wa shugaban majami'ar, “Kada ka ji tsoro. Ka ba da gaskiya kawai, za ta kuwa warke.” 51 Da ya isa gidan bai yarda kowa ya shiga tare da shi ba, sai Bitrus, da Yahaya, da Yakubu, da kuma mahaifin yarinyar da mahaifiyarta, 52 Duk kuwa ana ta kuka da kururuwa saboda ita. Amma Yesu ya ce, “Ku daina kuka. Ai, ba matacciya take ba, barci take yi.” 53 Sai suka yi masa dariyar raina, don sun sani ta mutu. 54 Shi kuwa sai ya riƙe hannunta, ya ta da murya ya ce, “Yarinya, ki tashi.” 55 Ruhunta kuwa ya dawo, nan take ta tashi. Sai ya yi umarni a ba ta abinci. 56 Iyayenta suka yi mamaki. Amma ya kwaɓe su kada su gaya wa kowa abin da ya faru.

Luka 9

Yesu ya Aiki Goma Sha Biyun Nan

1 Sai ya tara goma sha biyun nan ya ba su iko da izini kan dukan aljannu, su kuma warkar da cuce-cuce, 2 ya kuma aike su su yi wa'azin Mulkin Allah, su kuma warkar da marasa lafiya. 3 Ya kuma ce musu, “Kada ku ɗauki wani guzuri a tafiyarku, ko sanda, ko burgami, ko gurasa, ko kuɗi. Kada kuma ka ɗauki taguwa biyu. 4 Duk gidan da kuka sauka, ku zauna a nan har ku tashi. 5 Duk waɗanda ba su yi na'am da ku ba, in za ku bar garin, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku don shaida a kansu.” 6 Sai suka tashi suka zazzaga ƙauyuka suna yin bishara, suna warkarwa a ko'ina.

Mutuwar Yahaya Maibaftisma

7 To, sarki Hirudus ya ji duk abin da ake yi, ya kuwa damu ƙwarai, don waɗansu suna cewa Yahaya ne aka tasa daga matattu. 8 Waɗansu kuwa suka ce Iliya ne ya bayyana. Waɗansu kuma suka ce ɗaya daga annabawan dā ne ya tashi. 9 Sai Hirudus ya ce, “Yahaya kam na fille masa kai. Wa ke nan kuma da nake jin irin waɗannan abubuwa a game da shi?” Sai ya nemi ganinsa.

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

10 Da manzanni suka dawo, suka gaya wa Yesu abin da suka yi. Sai ya tafi da su a keɓe zuwa wani gari mai suna Betsaida. 11 Ganin haka sai taro masu yawa suka bi shi. Ya kuwa yi musu maraba, ya yi musu maganar Mulkin Allah, ya kuma warkar da masu bukatar warkewa. 12 Da rana ta fara sunkuyawa, goma sha biyun suka matso, suka ce masa, “Sai ka sallami taron, su shiga ƙauyuka da karkara na kurkusa, su sauka, su nemi abinci, don inda muke ba mutane.” 13 Amma ya ce musu, “Ku ku ba su abinci mana.” Suka ce, “Ai, abin da muke da shi bai fi gurasa biyar da kifi biyu ba, sai dai in za mu je mu sayo wa dukkan jama'ar nan abinci ne.” 14 Maza sun kai wajen dubu biyar. Sai ya ce wa almajiransa, “Ku ce musu su zazzauna ƙungiya, kowace ƙungiya misali hamsin hamsin.” 15 Haka kuwa suka yi, suka sa dukkansu su zazzauna. 16 Da ya ɗauki gurasa biyar ɗin da kifi biyu, sai ya ɗaga kai sama, ya yi wa Allah godiya, ya gutsuttsura su, ya yi ta ba almajiran, suna kai wa jama'a. 17 Duka kuwa suka ci suka ƙoshi, har aka kwashe ragowar gutsattsarin, kwando goma sha biyu.

Hurcin Bitrus a kan Yesu

18 Wata rana yana addu'a shi kaɗai, almajiransa kuwa suka zo wurinsa. Sai ya tambaye su, ya ce, “Wa mutane suke cewa nake?” 19 Suka amsa suka ce, “Yahaya Maibaftisma, waɗansu kuwa, Iliya, waɗansu kuma, ɗaya daga cikin annabawan dā ne ya tashi.” 20 Ya ce musu, “Amma ku fa, wa kuke cewa nake?” Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Almasihu na Allah.”

Yesu ya Faɗi irin Mutuwar da zai Yi

21 Sai ya kwaɓe su matuƙa kada su gaya wa kowa wannan magana. 22 Ya ce, “Lalle ne Ɗan mutum yă sha wuya iri iri, shugabanni da manyan firistoci da malaman Attaura su ƙi shi, har a kashe shi, a rana uku kuma a tashe shi.” 23 Sai ya ce wa dukansu, “Duk mai son bina, sai ya ƙi kansa, ya ɗauki gicciyensa kowace rana, yă bi ni. 24 Duk mai son tattalin ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa saboda ni, tattalinsa yake yi. 25 Me mutum zai amfana in ya sami duniya duka a kan hasarar ransa, ko a bakin ransa? 26 Duk wanda zai ji kunyar shaida ni da maganata, Ɗan Mutum ma zai ji kunyar shaida shi sa'ad da ya zo da ɗaukakarsa, da kuma ɗaukakar Uba, da ta mala'iku tsarkaka. 27 Amma hakika ina gaya muku, akwai waɗansu a tsaitsaye a nan da ba za su mutu ba sai sun ga Mulkin Allah.”

Sākewar Kamanninsa

28 Bayan misalin kwana takwas da yin maganar nan, Yesu ya ɗauki Bitrus, da Yahaya, da Yakubu, ya hau wani dutse domin yin addu'a. 29 Yana yin addu'a, sai kamanninsa ta sāke, tufafinsa kuma suka yi fari fat, har suna ɗaukar ido. 30 Sai ga mutum biyu suna magana da shi, wato Musa da Iliya. 31 Sun bayyana da ɗaukaka, suna zancen ƙaunarsa ne, wadda yake gabannin yi a Urushalima. 32 Sai kuma Bitrus da waɗanda suke tare da shi, barci ya cika musu ido, amma da suka farka suka ga ɗaukakarsa, da kuma mutum biyun nan tsaye tare da shi. 33 Mutanen nan na rabuwa da shi ke nan, sai Bitrus ya ce wa Yesu, “Maigida, ya kyautu da muke nan wurin. Mu kafa bukkoki uku, ɗaya taka, ɗaya Musa, ɗaya kuma ta Iliya.” Bai ma san abin da yake faɗa ba. 34 Yana faɗar haka sai wani gajimare ya zo ya rufe su. Da kuma gajimaren ya lulluɓe su suka tsorata. 35 Sai aka ji wata murya daga cikin gajimaren, tana cewa, “Wannan shi ne Ɗana ƙuanataccena. Ku saurare shi!” 36 Bayan muryar ta yi magana, sai ga Yesu shi kaɗai. Suka yi shiru. A kwanakin nan kuwa ba su gaya wa kowa abin da suka gani ba.

Yesu ya Warkar da Yaro Mai Farfadiya

37 Kashegari da suka gangaro daga kan dutsen, wani babban taro ya tarye shi. 38 Sai ga wani daga cikin taron ya yi kira, ya ce, “Malam, ina roƙonka ka dubi ɗana da idon rahama, shi ne ke nan gare ni. 39 Ga shi, aljan yakan hau shi, yakan yi ihu ba zato ba tsammani. Aljanin yakan buge shi, jikinsa yana rawa, har bakinsa yana kumfa. Ba ya barinsa sai ya kukkuje shi ƙwarai. 40 Na kuwa roƙi almajiranka su fitar da shi, amma sun kasa.” 41 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ya ku tsara marasa bangaskiya, kangararru! Har yaushe zan zama da ku, ina jure muku? Kawo ɗan naka.” 42 Yana zuwa, sai aljanin ya buge shi ƙwarai, jikinsa yana rawa. Amma Yesu ya tsawata wa baƙin aljanin, ya warkar da yaron, ya kuma mayar wa mahaifinsa da shi. 43 Duk aka yi mamakin girman ikon Allah.

Yesu ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

Tun dukansu suna mamakin duk abubuwan da yake yi, sai ya ce wa almajiransa, 44 “Maganar nan fa tă shiga kunnenku! Za a ba da Ɗan Mutum ga mutane.” 45 Amma ba su fahimci maganar nan ba, an kuwa ɓoye musu ita ne don kada su gane. Su kuwa suna tsoron tambayarsa wannan magana. 9 .46 Wane ne Mafi Girma? Wane ne Mafi Girma? 46 Sai musu ya tashi a tsakaninsu a kan ko wane ne babbansu. 47 Amma da Yesu ya gane tunanin zuciyarsu, ya kama hannun wani ƙaramin yaro ya ajiye shi kusa da shi. 48 Ya ce musu, “Duk wanda ya karɓi ƙaramin yaro kamar wannan saboda sunana, ni ya karɓa. Wanda kuwa ka karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ke nan. Ai, wanda yake ƙarami a cikinku shi ne babba.”

Wanda ba ya Gāba da ku, Naku Ne

49 Sai Yahaya ya amsa ya ce, “Maigida, mun ga wani yana fitar da aljannu da sunanka, mun kuwa hana shi, domin ba ya binmu.” 50 Amma Yesu ya ce masa, “Kada ku hana shi. Ai, duk wanda ba ya gāba da ku, naku ne.”

Samariyawan wani Ƙauye sun Ƙi Karɓar Yesu

51 Da lokacin karɓarsa a Sama ya gabato, ya himmantu sosai ga zuwa Urushalima. 52 Sai ya aiki jakadu su riga shi gaba, suka kuwa tafi suka shiga wani ƙauyen Samariyawa sa shisshirya masa. 53 Amma Samariyawa suka ƙi karɓarsa, domin niyyarsa duk a kan Urushalima take. 54 Da almajiransa Yakubu da Yahaya ga haka suka ce, “Ya Ubangiji, ko kana so mu umarci wuta ta sauko daga sama ta lashe su?” 55 Amma ya juya, ya tsawata musu. 56 Sai suka ci gaba, suka tafi wani ƙauye.

Masu Cewa za su Bi Yesu

57 Suna tafiya a hanya, sai wani mutum ya ce masa, “Zan bi ka duk inda za ka.” 58 Yesu ya ce masa, “Yanyawa da ramummukansu, tsuntsaye kuma da shekunansu, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin shaƙatawa.” 59 Ya kuma ce wa wani, “Bi ni.” Sai ya ce, “Ya Ubangiji, ka bar ni tukuna in je in binne tsohona.” 60 Sai Yesu ya ce masa, “Bari matattu su binne 'yan'uwansu matattu. Amma kai kuwa, tafi ka sanar da Mulkin Allah.” 61 Wani kuma ya ce, “Ya Ubangiji, zan bi ka, amma ka bar ni tukuna in ji wa mutanen gida bankwana.” 62 Yesu ya ce masa “Wanda ya fara huɗa da keken noma, yana duban baya, bai dace da Mulkin Allah ba.”

Luka 10

Yesu ya Aiki Saba'in Ɗin

1 Bayan wannan Ubangiji ya zaɓi waɗansu mutum saba'in, ya aike su biyu biyu, su riga shi gaba zuwa kowane gari da kowane wuri da shi kansa za shi. 2 Ya ce musu, “Girbin yana da yawa, amma masu yinsa kaɗan ne. Saboda haka ku roƙi Ubangijin girbi ya turo masu girbi, su yi masa girbi. 3 To, sai ku tafi. Ga shi na aike ku kamar 'yan tumaki a tsakiyar kyarketai. 4 Kada ku ɗauki jakar kuɗi, ko burgami, ko takalma. Kada ku yi doguwar gaisuwa da kowa a hanya. 5 Duk gidan da kuka sauka, ku fara da cewa, ‘Salama a gare ku mutanen gidan nan!’ 6 In akwai da ɗan salama a gidan, to, salamarku za ta tabbata a gare shi. In kuwa babu, za ta komo muku. 7 Ku zauna a gidan, kuna ci kuna shan duk irin abin da suka ba ku, domin ma'aikaci ya cancanci ladarsa. Kada ku riƙa sāke masauki. 8 Duk garin da kuka shiga, in an yi na'am da ku, ku ci duk irin abin da aka kawo muku. 9 Ku warkar da marasa lafiya da ke cikinsa, ku kuma ce musu, ‘Mulkin Allah ya kusato ku.’ 10 Amma duk garin da kuka shiga ba a yi na'am da ku ba, sai ku zaga kwararo kwararo, kuna cewa, 11 ‘Ko da ƙurar garinku da ta ɗafe a jikin ƙafafunmu ma, mun karkaɗe muku. Amma duk da haka ku sani Mulkin Allah ya kusato.’ 12 Ina dai gaya muku, a ran nan, za a fi haƙurce wa Saduma a kan garin nan.”

Tsawata wa Garuruwan da ba su Tuba Ba

13 “Kaitonki, Korasinu! Kaitonki, Betsaida! Da mu'ujizar da aka yi a cikinku, su aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba, sun zauna sāye da tsumma, suna hurwa da toka. 14 Amma a Ranar Shari'a, za a fi haƙurce wa Taya da Sidon a kanku. 15 Ke kuma Kafarnahum, ɗaukaka ki sama za a yi? A'a, ƙasƙantar da ke za a yi har Hades. 16 “Duk mai sauraronku, ni yake saurare. Mai ƙinku kuma, ni yake ƙi. Duk mai ƙina kuwa, wanda ya aiko ni ne ya ƙi.”

Komowar Saba'in Ɗin

17 Sai kuma saba'in ɗin nan suka komo da farin ciki, suka ce, “Ya Ubangiji, har aljannu ma suna mana biyayya albarkacin sunanka!” 18 Sai ya ce musu, “Na ga Shaiɗan ya faɗo daga sama kamar walƙiya. 19 Ga shi, na ba ku ikon taka macizai da kunamai, ku kuma yi rinjaye a kan dukan ikon Maƙiyi, ba kuwa abin da zai cuce ku ko kaɗan. 20 Duk da haka, kada ku yi farin ciki aljannu suna yi muku biyayya, sai dai ku yi farin cikin an rubuta sunayenku a Sama.”

Yesu ya Yi Farin Ciki

21 A wannan lokaci ya yi farin ciki matuƙa ta Ruhu Mai Tsarki, ya ce, “Na gode maka ya Uba, Ubangijin sama da ƙasa, domin ka ɓoye waɗannan al'amura ga masu hikima da masu basira, ka kuma bayyana su ga jahilai. Hakika na gode maka ya Uba, domin wannan shi ne nufinka na alheri. 22 Kowane abu Ubana ne ya mallaka mini. Ba kuwa wanda ya san ko wane ne Ɗan sai dai Uban, ko kuma ya san ko wane ne Uban sai dai Ɗan, da kuma wanda Ɗan yake so ya bayyana wa.” 23 Sai ya juya wajen almajiransa, ya ce musu a keɓance, “Albarka tā tabbata ga idanun da suka ga abin da kuka gani. 24 Ina gaya muku, annabawa da sarakuna da yawa suna son ganin abin da kuke gani, amma ba su gani ba, suna kuma so su ji abin da kuke ji, amma ba su ji ba.”

Basamariyen da ya Nuna Jinƙai

25 Sai ga wani masanin Attaura ya tashi tsaye yana gwada shi, ya ce, “Malam, me zan yi in gaji rai madawwami?” 26 Yesu ya ce musu, “Me yake rubuce a Attaura? Yaya kake karantawa?” 27 Sai ya amsa ya ce, “Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukkan zuciyarka, da dukkan ranka, da dukkan ƙarfinka, da dukkan hankalinka. Ka kuma ƙaunaci ɗan'uwanka kamar kanka.” 28 Yesu ya ce masa, “Ka amsa daidai. Ka riƙa yin haka, za ka rayu.” 29 Shi kuwa mutumin, don yana son baratar da kansa, ya ce wa Yesu, “To, wane ne ɗan'uwa nawa?” 30 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Wani mutum ne ya tashi daga Urushalima za shi Yariko. Sai 'yan fashi suka fāɗa shi, suka tuɓe shi, suka yi masa mugun d�ka, suka tafi suka bar shi rai ga Allah. 31 Daga nan ya zamana wani firist ya biyo ta wannan hanya. Da ya gan shi sai ya zaga ta ɗaya gefen, ya wuce abinsa. 32 Haka kuma wani Balawe, da ya iso wurin ya gan shi, shi ma ya zaga ta ɗaya gefen, ya wuce abinsa. 33 Ana nan sai hanya ta kawo wani Basamariye inda yake. Da ya gan shi, sai tausayi ya kama shi, 34 ya je wurinsa, ya ɗaɗɗaure masa raunukansa, yana zuba musu mai da ruwan inabi. Sa'an nan ya ɗora shi a kan dabbarsa, ya kai shi masauki, ya yi ta jiyyarsa. 35 Kashegari ya ɗebo dinari biyu ya ba maigidan, ya ce, ‘Ka yi jiyyarsa, duk kuma abin da ka ɓatar bayan wannan, in na dawo sai in biya ka.’ 36 To, a cikin ukun nan, wa kake tsammani ya zama ɗan'uwa ga wanda 'yan fashin suka faɗa wa?” 37 Sai ya ce, “Wanda ya nuna masa jinƙai.” Sai Yesu ya ce masa, “Kai ma, ka je ka riƙa yin haka.”

Yesu ya Ziyarci Marta da Maryamu

38 Suna tafiya, sai ya shiga wani ƙauye, wata mace kuma mai suna Marta ta saukar da shi a gidanta. 39 Tana kuwa da 'yar'uwa mai suna Maryamu, wadda ta zauna a gaban Ubangiji tana sauraron maganarsa. 40 Marta kuwa yawan hidimomi ya ɗauke mata hankali, sai ta je gunsa, ta ce, “Ya Ubangiji, ba ku kula ba, 'yar'uwata ta bar ni ina hidima ni kaɗai? Gaya mata ta taimake ni mana.” 41 Amma Ubangiji ya amsa mata ya ce, “Marta, Marta! Hankalinki a tashe ya ke, kina kuma damuwa kan abu da yawa. 42 Bukatu kima ne, ta ainihi ɗaya ce. Maryamu ta zaɓi abu mai kyau, ba kuwa za a karɓe mata ba.”

Luka 11

Koyarwar Yesu a kan Addu'a

1 Wata rana Yesu yana addu'a a wani wuri. Bayan da ya gama, sai wani a cikin almajiransa ya ce masa, “Ya Ubangiji, ka koya mana addu'a, kamar yadda Yahaya ya koya wa almajiransa.” 2 Sai ya ce musu, “In kuna addu'a ku ce, ‘Ya Uba, a kiyaye sunanka da tsarki, Mulkinka yă zo, 3 Ka ba mu abincin yau da na kullum. 4 Ka gafarta mana zunubanmu, gama mu ma muna gafarta wa duk wanda yake yi mana laifi. Kada ka kai mu wurin jaraba.’ ” 5 Ya kuma gaya musu, “Misali, idan waninku yana da amini, ya je wurinsa da tsakar dare ya ce masa, ‘Wāne, ranta mini gurasa uku mana, 6 ga shi, wani abokina matafiyi ya sauka a wurina yanzu, ba ni kuwa da abincin da zan ba shi,’ 7 sa'an nan aminin ya amsa masa daga ciki ya ce, ‘Kada ka dame ni, ai, an kulle ƙofa, da ni da 'ya'yana duk mun kwanta, ba zan iya tashi in ba ka wani abu ba.’ 8 Ina gaya muku, ko da yake ba zai tashi ya ba shi wani abu don yana amininsa ba, amma saboda nacinsa zai tashi ya ba shi ko nawa yake bukata. 9 Ina dai gaya muku, ku yi ta roƙo, za a ba ku. Ku yi ta nema, za ku samu. Ku yi ta ƙwanƙwasawa, za a kuwa buɗe muku. 10 Duk wanda ya roƙa, akan ba shi, mai nema yana tare da samu, wanda ya ƙwanƙwasa kuma za a buɗe masa. 11 Wane uba ne a cikinku, da ɗansa zai roƙe shigurasa, ya ba shi dutse? Ko ya roƙe shi kifi, ya ba shi maciji? 12 Ko kuwa ya roƙe shi ƙwai, ya ba shi kunama? 13 To, ku da kuke mugaye ma kuka san yadda za ku ba 'ya'yanku kyautar kyawawan abubuwa, balle Ubanku na Sama zai ba da Ruhu Mai Tsarki ga masu roƙonsa.”

Yesu da Ba'alzabul

14 Wata rana Yesu yana fitar da beben aljan. Da aljanin ya fita, sai beben ya yi magana, taron kuwa suka yi mamaki. 15 Amma waɗansunsu suka ce, “Ai, da ikon Ba'alzabul sarkin aljannu yake fitar da aljannu.” 16 Waɗansu kuwa, don su gwada shi, suka nema ya nuna musu wata alama daga Sama. 17 Shi kuwa da ya san tunaninsu, sai ya ce musu, “Duk mulkin da ya rabu a kan gāba, zai lalace. Haka kuma, in gida ya rabu a kan gāba, zai baje. 18 In kuma Shaiɗan ya rabu a kan gāba, yaya mulkinsa zai ɗore? Ga shi, kun ce da ikon Ba'alzabul nake fitar da aljannu. 19 In kuwa da ikon Ba'alzabul nake fitar da aljannu, to, 'ya'yanku fa, da ikon wa suke fitarwa? Saboda haka, su ne za su zama alƙalanku. 20 Ni kuwa in da ikon Allah nake fitar da aljannu, ashe, Mulkin Allah ya zo muku ke nan. 21 In ƙaƙƙarfan mutum ya yi ɗamara sosai, yana tsaron gidansa, kayan gidansa lafiya suke. 22 In kuwa wanda ya fi shi ƙarfi ya fāɗa masa, ya kuma rinjaye shi, sai ya ƙwace duk makaman da ya dogara da su, ya kuma rarraba kayansa ganima, 23 Wanda ba nawa ba ne, gāba yake yi da ni. Wanda kuma ba ya taya ni tarawa, watsarwa yake yi.”

Komawar Baƙin Aljan

24 “Baƙin aljan, in ya rabu da mutum, sai ya bi ta wurare marasa ruwa, yana neman hutawa. In ya rasa, sai ya ce, ‘Zan koma gidana da na fito.’ 25 Sa'ad da kuwa ya komo gidan ya tarar da shi shararre, ƙawatacce, 26 Daga nan sai ya je ya ɗebo waɗansu aljannu bakwai da suka fi shi mugunta. Sai su shiga su zauna a wurin. Wannan mutum kuwa ƙarshen zamansa ya fi na fari lalacewa.”

Tabbatacciyar Albarka

27 Yana faɗar haka, sai wata mace a taron ta ɗaga murya ta ce masa, “Albarka tā tabbata ga wadda ta haife ka, wadda ka sha mamanta.” 28 Amma ya ce, “I, amma albarka tā fi tabbata ga waɗanda suke jin Maganar Allah, suke kuma kiyaye ta.”

'Yan Zamani Mugaye suna Neman Alama

29 Da taro ya riƙa ƙaruwa a wurinsa, sai ya fara cewa, “Wannan zamani mugun zamani ne. Suna neman ganin wata alama, amma ba wata alamar da za a nuna musu sai dai ta Yunusa. 30 Wato, kamar yadda Yunusa ya zama alama ga mutanen Nineba, haka kuma, Ɗan Mutum zai zamar wa zamanin nan. 31 A Ranar Shari'a Sarauniyar Kudu za ta tashi tare da mutanen zamanin nan ta kā da su. Don ta zo ne daga bangon duniya tă ga hikimar Sulemanu. Ga kuma wanda ya fi Sulemanu a nan. 32 A Ranar Shari'a mutanen Nineba za su tashi tare da mutanen zamanin nan su kā da su. Don sun tuba saboda wa'azin Yunusa. To, ga kuma wanda ya fi Yunusa a nan.”

Fitilar Jiki

33 “Ba mai kunna fitila ya ɓoye ta a rami, ko ya rufe ta da masaki. A'a, sai dai ya ɗora ta a maɗorinta, don masu shiga su ga hasken. 34 Ido shi ne fitilar jiki. In idonka lafiyayye ne, duk jikinka zai cika da haske. In kuwa idonka da lahani, sai jikinka ya cika da duhu. 35 Saboda haka, sai ka lura ko hasken da yake a gare ka duhu ne. 36 In kuwa duk jikinka ya cika da haske, ba inda yake da duhu, ai, duk sai ya haskaka gaba ɗaya, kamar yadda hasken fitila yake haskaka maka.”

Yesu ya Fallashi Farisiyawa da Masanan Attaura

37 Yesu yana magana, sai wani Bafarisiye ya kira shi cin abinci. Ya shiga cin abincin. 38 Sai Bafarisiyen ya yi mamakin ganin yadda Yesu zai ci abinci ba da fara wanke hannu ba. 39 Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ku Farisiyawa kam, kukan wanke bayan ƙwarya da akushi, amma a ciki a cike kuke da zalunci da mugunta. 40 Ku marasa azanci! Ashe, wanda ya yi bayan, ba shi ya yi cikin ba? 41 Gara ku tsarkake cikin, sa'an nan kome zai tsarkaka a gare ku. 42 “Kaitonku, Farisiyawa! Ga shi, kuna fitar da zakkar na'ana'a da karkashi, da kuma kowane ganyen miya. Amma kun ƙi kula da aikata gaskiya da ƙaunar Allah. Waɗannan ne ya kamata ku yi, ba tare da yar da waɗancan ba. 43 Kaitonku, Farisiyawa! Ga shi, kuna son mafifitan mazaunai a majami'u, da kuma gaisuwa a kasuwa. 44 Kaitonku! Kuna kama da kaburburan da ba a gani, waɗanda mutane suke takawa da rashin sani.” 45 Sai wani a cikin masanan Attaura ya amsa masa ya ce, “Malam, faɗar haka fa, mu ma, ai, ka ci mutuncinmu.” 46 Sai Yesu ya ce, “Ku kuma kaitonku, masanan Attaura! Don kuna jibga wa mutane kaya masu wuyar ɗauka, ku da kanku ko ɗan yatsa ba kwa sawa ku tallafa musu! 47 Kaitonku! Don kuna gina gubbobin annabawan da kakanninku suka kashe. 48 Wato, ku shaida ne a kan kun yarda da ayyukan kakanninku, ga shi, su ne fa suka kashe su, ku kuwa har kuka gina musu gubbobin! 49 Shi ya sa hikimar Allah ta ce, ‘Zan aika musu da annabawa da manzanni, su kashe waɗansu,’ 50 don alhakin jinin dukan annabawa da aka zubar tun daga farkon duniya, a bi shi a kan mutanen wannan zamani, 51 wato, tun daga jinin Habila, har ya zuwa na Zakariya, wanda aka kashe a tsakanin bagadin hadaya da Wuri Mai Tsarki. Hakika, ina gaya muku, duk za a bi shi a kan mutanen wannan zamani. 52 Kaitonku, masanan Attaura! Don kun ɗauke mabuɗin ilimi, ku kanku ba ku shiga ba, kun kuma hana masu son shiga su shiga.” 53 Da ya fito daga wurin, sai malaman Attaura da Farisiyawa suka fara matsa masa ƙwarai, suna tsokanarsa ya yi maganar abubuwa da yawa, 54 suna haƙwansa su burma shi a cikin maganarsa.

Luka 12

Faɗaka a kan Makirci

1 Sa'an nan kuwa da dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, da farko ya yi magana da almajiransa. Ya fara cewa, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, makirci. 2 Ba abin da yake a rufe da ba zai tonu ba, ko kuwa abin da yake a ɓoye da ba za a bayyana ba. 3 Don haka, kome kuka faɗa a asirce, za a ji shi a sarari. Abin kuma da kuka yi raɗa a lolloki, za a yi shelarsa daga kan soraye

Wanda za a Ji Tsoro

4 “Ya ku masoyana, ina dai gaya muku, kada ku ji tsoron masu kisan mutum, bayan sun kashe kuwa, ba abin da za su iya yi. 5 Amma zan gaya muku wanda za ku ji tsoro. Ku ji tsoron wannan da in ya kashe, yana da ikon jefawa a cikin Gidan Wuta. Hakika, ina gaya muku, shi za ku tsorata! 6 Ashe, ba gwara biyar ne kobo biyu ba? Ko ɗayarsu kuwa Allah bai manta da ita ba. 7 Kai! Ko da gashin kanku ma duk a ƙidaye yake. Kada ku ji tsoro. Ai, martabarku ta fi ta gwara masu yawa.”

Bayyana Yarda da Almasihu a gaban Mutane

8 “Ina kuma gaya muku, kowa ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai bayyana yarda a gare shi a gaban mala'ikun Allah. 9 Wanda kuwa ya yi m�sun sanina a gaban mutane, za a yi m�sun saninsa a gaban mala'ikun Allah. 10 Kowa ya kushe wa Ɗan Mutum, ā gafarta masa, amma wanda ya saɓi Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba. 11 Sa'ad da suka kai ku a gaban majami'u, da mahukunta da shugabanni, kada ku damu da yadda za ku mai da jawabi, ko kuwa abin da za ku faɗa, 12 domin Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya kamata ku faɗa a lokacin.”

Misali na Mai Arziki Marar Azanci

13 Sai wani a cikin taron ya ce masa, “Malam, kă ce wa ɗan'uwana ya raba gādo da ni.” 14 Amma Yesu ya ce masa, “Haba kai kuwa, wa ya sa ni in zama muku alƙali, ko in raba muku gādo?” 15 Ya kuma ce musu, “Ku kula fa, ku yi nesa da kowane irin kwaɗayi, don yawan kaya ba shi ne rai ba.” 16 Sai ya ba su misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta yi albarka ƙwarai. 17 Sai ya ce a ransa, ‘To, ƙaƙa zan yi? Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonata.’ 18 Ya kuma ce, ‘To, ga abin da zan yi. Sai in rushe rumbunana, in gina waɗansu manya, in zuba duk amfanin gonata da kayana a ciki. 19 Zan kuma ce wa raina, “Lalle ina da kaya masu yawa a jibge, tanadin shekara da shekaru. Bari in huta, in yi ta ci, in yi ta sha, ina shagali na.” ’ 20 Amma Allah ya ce masa, ‘Kai marar azanci! A daren nan za a karɓi ranka. To, kayan da ka tanada, na wa za su zama?’ 21 Haka, wanda ya tanada wa kansa dukiya yake, ba shi kuwa da wani tanadi a gun Allah.”

Damuwa da Alhini

22 Sai ya ce wa almajiransa, “Don haka, ina gaya muku, kada ku damu da batun rayuwarku, a game da abin da za ku ci, ko kuma jikinku, abin da za ku yi sutura. 23 Domin rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi. 24 Ku dubi dai hankaki! Ai, ba sa shuka, ba sa girbi, ba su da taska ko rumbu, amma kuwa Allah yana cishe su. Sau nawa martabarku ta ninka ta tsuntsaye!” 25 Wane ne a cikinku don damuwarsa zai iya ƙara ko da taƙi ga tsawon rayuwarsa? 26 To, in ba za ku iya yin ƙaramin abu irin wannan ba, don me kuke damuwa da sauran? 27 Ku dubi dai furanni yadda suke girma, ba sa aikin fari, ba sa na baƙi, duk da haka, ina gaya muku, ko Sulemanu ma, shi da adonsa duk, bai taɓa yin adon da ya fi na ɗayansu ba. 28 To, ga shi Allah yana ƙawata tsire-tsiren jeji ma haka, waɗanda yau suke a raye, gobe kuwa a jefa su a murhu, balle fa ku? Ya ku masu ƙarancin bangaskiya! 29 Ku ma kada ku damu a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada kuwa ku yi alhini. 30 Ai, al'umman duniya suna ta neman duk irin waɗannan abubuwa, ku kuwa, Ubanku ya san kuna bukatarsu. 31 Ku ƙwallafa rai ga al'amuran Mulkin Allah, sai a ƙara muku da waɗannan abubuwa kuma.

Tara Dukiya a Sama

32 “Ya ku ɗan ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, domin Ubanku yana jin daɗin ba ku rabo a cikin Mulkin. 33 Ku sayar da mallakarku, ku bayar taimako. Ku samar wa kanku jakar kuɗi da ba ta tsufa, wato, dukiya mara yankewa ke nan a Sama, a inda ba ɓarawon da zai gabato, ba kuma asun da zai ɓāta, 34 don kuwa a inda dukiyarka take, a nan zuciyarka ma take.”

Bayin da suke a Faɗake

35 “Ku yi ɗamara, fitilunku suna kunne. 36 Ku dai zama kamar mutane masu jiran Ubangijinsu ya dawo daga gidan biki, da zarar ya ƙwanƙwasa su buɗe masa. 37 Albarka tā tabbata ga bayin nan waɗanda Ubangijinsu da zuwansa zai same su a faɗake. Hakika, ina gaya muku, zai yi ɗamara, ya ce su zauna cin abinci, sa'an nan ya bi ta kan kowannensu yana yi masa hidima. 38 In kuwa ya zo da tsakar dare ne, ko kuwa bayan tsakar dare, ya same su a faɗake, bayin nan masu albarka ne. 39 Amma dai ku sani, da maigida zai san lokacin da ɓarawo zai zo, da ya zauna a faɗake, ya hana a shiga masa gida. 40 Ku ma sai ku zauna a kan shiri, domin a lokacin da ba ku zata ba Ɗan Mutum zai zo.”

Amintaccen Bawa ko Marar Aminci

41 Sai Bitrus ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa na kowa da kowa ne?” 42 Ubangiji ya ce, “Wane ne amintaccen wakilin nan mai hikima, da ubangidansa zai ba shi riƙon gidansa, yă riƙa ba su abincinsu a kan kari? 43 Albarka tā tabbata ga bawan da, in ubangidansa ya dawo, zai samu yana yin haka. 44 Hakika, ina gaya muku, sai ya ɗora shi a kan dukan mallakarsa. 45 In kuwa bawan nan ya ce a ransa, ‘Ubangidana ya jinkirta zuwansa,’ sa'an nan ya soma d�kan barori, maza da mata, ya shiga ci da sha har yana buguwa, 46 ai, ubangidan wannan bawa zai zo a ranar da bai zata ba, a lokacin kuma da bai sani ba, yă farfasa masa jiki da bulala, ya ba shi rabonsa tare da marasa riƙon amana. 47 Bawan nan kuma wanda ya san nufin ubangidansa, bai yi shiri ba, bai kuma bi nufinsa ba, za a yi masa matsanancin d�ka, 48 Wanda kuwa bai san ubangidansa ba, ya kuma yi abin da ya isa d�ka, za a doke shi kaɗan. Duk wanda aka ba abu mai yawa, a gunsa za a tsammaci abu mai yawa. Wanda kuma aka danƙa wa abu mai yawa, abu mafi yawa za a nema a gare shi.”

Yesu ya Kawo Rabuwa

49 “Wuta ce na zo in zuba wa duniya. Sona fa? A ce ta huru! 50 Ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa ɗokanta ƙwarai har a yi mini ita! 51 Kuna tsammani na zo ne in kawo salama a duniya? A'a, ina gaya muku, sai dai rabuwa. 52 Anan gaba, a gida guda mutum biyar za su kasu biyu, uku suna gāba da biyu, biyu kuma suna gāba da uku. 53 Ta haka, za su rabu. Mahaifi yana gāba da ɗansa, ɗan kuma yana gāba da mahaifinsa, mahaifiya tana gāba da 'yarta, 'yar kuma tana gāba da mahaifiyarta, suruka tana gāba da matar ɗanta, matar ɗan kuma tana gāba da surukarta.”

Gane Yanayin Lokatai

54 Ya kuma ce wa taron, “In kun ga girgije yana tasowa daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwa.’ Sai kuwa a yi. 55 In kuwa kun ga iskar kudu tana busowa, kukan ce, ‘Za a yi matsanancin zafi.’ Sai kuwa a yi. 56 Munafukai! Kuna iya gane yanayin ƙasa da na sararin sama, amma me ya sa ba ku iya gane alamun zamanin ba?”

Yi Jiyayya da Mai Ƙararka

57 “Me ya sa ku da kanku ma ba kwa iya rarrabewa da abin da yake daidai? 58 Misali, in kuna tafiya zuwa gaban shari'a da mai ƙararku, sai ka yi ƙoƙari ka yi jiyayya da shi tun a hanya, don kada ya ja ku zuwa gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa wa ɗan doka, ɗan doka kuma ya jefa ka a kurkuku. 59 Ina gaya maka, lalle ba za ka fita ba, sai ka biya duka, ba sauran ko anini.”

Luka 13

Tuba ko Hallaka

1 Anan take waɗansu da suke a wurin suke ba shi labarin Galilawan da Bilatus ya sa aka kashe, har jininsu ya gauraya da na yankan da suka yi na hadaya. 2 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Kuna tsammani waɗannan Galilawa sun fi duk sauran Galilawa zunubi ne, don sun sha wannan azaba? 3 Ina gaya muku ba haka ba ne! In kuwa ba ku tuba ba, duk za ku hallaka kamarsu. 4 Ko kuwa goma sha takwas ɗin nan da hasumiya ta faɗo a kansu, a Siluwam, ta kashe su, kuna tsammani sun fi duk sauran mutanen Urushalima laifi ne? 5 Ina gaya muku ba haka ba ne! In kuwa ba ku tuba ba, duk za ku hallaka kamarsu.”

Misali na Ɓaure Marar 'Ya'ya

6 Sai ya ba su misalin nan ya ce, “Wani mutum yana da ɓaure a garkar inabinsa. Sai ya zo neman 'ya'ya, amma bai samu ba. 7 Sai ya ce wa mai kula da garkar, ‘Ka ga, yau shekara uku ke nan nake zuwa neman 'ya'yan wannan ɓaure, amma ba na samu. A sare shi. Ƙaƙa zai tsare wuri a banza?’ 8 Sai ya amsa masa ya ce, ‘Ubangidana, bar shi dai bana ma, in yi masa kaftu, in zuba masa taki. 9 In ya yi 'ya'ya, to, in kuwa bai yi ba, sai a sare.’ ”

Warkar da Tanƙwararriyar Mace a Ran Asabar

10 Wata rana yana koyarwa a wata majami'a a ran Asabar, 11 sai ga wata mace wadda inna ta shanye tun shekara goma sha takwas, duk ta tanƙware, ko kaɗan ba ta iya miƙewa. 12 Da Yesu ya gan ta, sai ya kira ta ya ce mata, “Uwargida, an raba ki da rashin lafiyarki!” 13 Sai ya ɗora mata hannu, a nan take ta miƙe, ta kuma ɗaukaka Allah. 14 Amma shugaban majami'a ya ji haushi, don Yesu ya warkar a ran Asabar. Sai ya ce wa jama'a, “Akwai ranaku har shida da ya kamata a yi aiki. Ku zo mana a ranakun nan a warkar da ku, ba a ran Asabar ba.” 15 Amma Ubangiji ya amsa masa ya ce, “Munafukai! Ashe, kowannenku ba ya kwance takarkarinsa ko jakinsa a turke, ya kai shi banruwa a ran Asabar? 16 Ashe, bai kamata matar nan 'yar zuriyar Ibrahim, wadda Shaiɗan ya ɗaure, yau shekara goma sha takwas, a kwance ta daga wannan ƙuƙumi a ran Asabar ba?” 17 Da ya faɗi haka, sai duk abokan adawarsa suka kunyata, duk taron kuwa suka yi ta farin ciki da abubuwan al'ajabi da yake yi.

Misali na Ƙwayar Mastad

18 Sai Yesu ya ce, “Da me Mulkin Allah yake kama? Da me kuma zan kwatanta shi? 19 Kamar ƙwayar mastad yake, wadda wani mutum ya je ya shuka a lambunsa, ta kuma girma ta zama itace, har tsuntsaye suka yi sheƙarsu a rassanta.”

Misali na Yisti

20 Ya sāke cewa, “Da me zan kwatanta Mulkin Allah? 21 Kamar yisti yake wanda wata mace ta ɗauka ta cuɗa da mudu uku na garin alkama, har duk garin ya gama da yistin.”

Ƙunƙuntar Ƙofa

22 Sai ya ɗauki hanyarsa ta zuwa birane da ƙauyuka, yana koyarwa, yana dosar Urushalima. 23 Sai wani ya ce masa, “Ya Ubangiji, waɗanda za su sami ceto kam, kaɗan ne?” Sai ya ce musu, 24 “Ku yi famar shiga ta ƙunƙuntar ƙofa. Don ina gaya muku, mutane da yawa za su nemi shiga, amma ba su iya ba. 25 In dai maigida ya riga ya tashi ya rufe ƙofa, kun kuma fara tsayawa daga waje, kuna ƙwanƙwasa ƙofar, kuna cewa, ‘Ya Ubangiji, buɗe mana,’ sai ya amsa muku ya ce, ‘Ku kam, ban san daga inda kuke ba.’ 26 Sa'an nan za ku fara cewa, ‘Ai, mun ci mun sha a gabanka, har ka koyar a kan hanyoyinmu.’ 27 Shi kuwa sai ya ce, ‘Ina dai gaya muku, ku kam, ban san daga inda kuke ba. Ku tafi daga wurina, dukanku ku masu aikata mugunta!’ 28 Sa'ad da kuka ga Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, da dukan annabawa a Mulkin Allah, ku kuwa ana korarku, a nan ne za ku yi kuka da cizon haƙora. 29 Za a zo daga gabas da yamma, kudu da arewa, a zauna cin abinci a Mulkin Allah. 30 Ga shi fa, waɗansu da suke na ƙarshe za su zama na farko, waɗansu kuwa da suke na farko za su koma na ƙarshe.”

Yesu ya Ji Juyayin Urushalima

31 Anan take waɗansu Farisiyawa suka zo suka ce masa, “Ai, sai ka tashi, ka fita daga nan, gama Hirudus yana son kashe ka.” 32 Sai ya ce musu, “Ku tafi ku gaya wa dilan nan cewa, ‘Ka ga, a yau ina fitar da aljannu, ina warkarwa, a gobe ma haka, a rana ta uku kuwa zan gama aikina. 33 Duk da haka, lalle ne in ci gaba da tafiyata yau, da gobe, da kuma jibi, don kuwa bai dace a kashe annabi ba, in ba a Urushalima ba.’ 34 “Ya mutanen Urushalima! Ya mutanen Urushalima! Masu kisan annabawa, masu jifan waɗanda aka aiko a gare ku! Sau nawa ne nake so in tattaro ku kamar yadda kaza take tattara 'yan tsakinta a cikin fikafikanta, amma kun ƙi! 35 Ga shi, an bar muku gidanku a yashe! Ina kuwa gaya muku, ba za ku ƙara ganina ba, sai a ran da kuka ce, ‘Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji.’ ”

Luka 14

Warkar da Mai Ciwon Fara

1 Wata rana Asabar, ya shiga gidan wani shugaba Farisiyawa garin cin abinci, mutane kuwa suna haƙwansa. 2 Sai ga wani mai ciwon fara a gabansa. 3 Yesu ya amsa ya ce wa masanan Attaura da Farisiyawa, “Ya halatta a warkar a ran Asabar ko kuwa babu?” 4 Sai suka yi shiru, Yesu kuwa ya riƙe shi, ya warkar da shi, ya kuma sallame shi. 5 Sa'an nan ya ce musu, “Misali, wane ne a cikinku in yana da jaki ko takarkari ya faɗa a rijiya a ran Asabar, ba zai fitar da shi nan da nan ba?” 6 Sai suka kasa ba da amsar waɗannan abubuwa.

Aya ga Waɗanda aka Gayyato Biki da Mai Gayyar

7 To, ganin yadda waɗanda aka gayyato sun zaɓi mazaunan alfarma, sai ya ba su misali ya ce, 8 “In an gayyace ka zuwa biki, kada ka zauna a mazaunin alfarma, kada ya zamana an gayyato wani wanda ya fi ka daraja, 9 wanda ya gayyato ku duka biyu kuma yă zo ya ce maka, ‘Ba mutumin nan wuri.’ Sa'an nan a kunyace ka koma mazauni mafi ƙasƙanci. 10 Amma in an gayyace ka biki, sai ka je ka zauna a wuri mafi ƙasƙanci, don in mai gayyar ya zo, sai ya ce maka, ‘Aboki, hawo nan mana.’ Za ka sami girma ke nan a gaban dukan waɗanda kuke zaune tare. 11 Duk wanda ya ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Mai ƙasƙantar da kansa kuma, ɗaukaka shi za a yi.” 12 Ya kuma ce da mai gayyar, “In za ka kira mutum cin abinci ko biki, kada ka riƙa kiran abokanta kawai, ko 'yan'uwanka, ko danginka ko maƙwabtanka masu arziki, kada su ma su gayyace ka, su sāka maka. 13 Amma in za ka kira biki, sai ka gayyayo gajiyayyu, da masukai, da guragu, da makafi, 14 za ka kuwa sami albarka, da yake ba su da hanyar sāka maka. Sai kuwa a sāka maka a ranar tashin masu adalci.”

Misali na Babban Biki

15 Da jin haka, sai ɗaya daga cikin abokan cin abincin ya ce masa, “Albarka tā tabbata ga wanda zai ci abinci a Mulkin Allah.” 16 Amma ya ce masa, “Wani mutum ne ya shirya babban biki ya gayyaci mutane da yawa. 17 Da lokacin biki ya yi, sai ya aiki bawansa ya ce wa waɗanda aka gayyata, ‘Ku zo, duk an shirya kome,’ 18 Sai dukansu baki ɗaya suka fara kawo hanzari. Na farko ya ce masa, ‘Na sayi gona, lalle ne in je in gano ta. Ina roƙonka ka ɗauke mini,’ 19 Sai wani ya ce, ‘Na sayi shanun noma guda goma, za ni in gwada su. Ina roƙonka ka ɗauke mini.’ 20 Wani kuma ya ce, ‘Na yi aure, don haka ba zan iya zuwa ba.’ 21 Bawan ya dawo ya ba ubangidansa labari. Sai maigidan ya yi fushi, ya ce wa bawansa, ‘Fita maza, ka bi hanyoyin birni da kwararo-kwararo, ka ɗebo gajiyayyu, da musakai, da makafi, da guragu.’ 22 Sai bawan ya ce, ‘Ya ubangida, abin da ka umarta duk an gama, amma har yanzu da sauran wuri.’ 23 Sai ubangidan biki ya ce wa bawan, ‘Fita, ka bi gwadabe-gwadabe da hanyoyin karkara, ka rinjayi mutane su shigo, don a cika gidana. 24 Ina gaya muku, ba ko ɗaya daga cikin mutanen da na gayyata a dā da zai ɗanɗana bikina ba.’ ”

Wuyar Zama Almajiri

25 To, taro masu yawan gaske suna bin sa. Sai ya juya ya ce musu, 26 “Duk mai zuwa wurina, in bai fi ƙaunata da mahaifinsa, da mahaifiyarsa, da 'ya'yansa, da 'yan'uwansa maza da mata, har ma da ransa ba, ba zai iya zama almajirina ba. 27 Duk wanda bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, ba zai iya zama almajirina ba. 28 Misali, in wani daga cikinku yana son gina soron bene, da fari ba sai ya zauna ya yi lissafin abin da zai kashe ba, ya ga ko yana da isassun kuɗi da za su ƙare aikin? 29 Kada ya zamana bayan da ya sa harsashin ginin, yă kasa gamawa, har duk waɗanda suka gani, su fara yi masa ba'a, 30 su riƙa cewa, ‘A! Ka ga mutumin nan ya fara gini, amma ya kasa gamawa!’ 31 “Ko kuwa wane sarki ne, in za shi yaƙi da wani sarki, da fari ba ya zauna ya yi shawara, ya ga ko shi mai mutum dubu goma zai iya karawa da mai dubu ashirin ba? 32 In kuwa ba zai iya ba, to, tun wancan yana nesa, sai ya aiki jakadu, su tambayo sharuɗan amana. 33 Haka ma, kowannenku in bai saki duk abin da ya mallaka ba, ba zai iya zama almajirina ba.”

Sānannen Gishiri

34 “Gishiri abu ne mai kyau, amma in gishiri ya sāne, da me za a daɗaɗa shi? 35 Ba shi da wani amfani a gona, ko a taki, sai dai a zubar kawai. Duk mai kunnen ji, ya ji.”

Luka 15

Misali na Ɓatacciyar Tunkiya

1 To, sai duk masu karɓar haraji da masu zunubi suka yi ta matsowa wurinsa su saurare shi. 2 Sai Farisiyawa da malaman Attaura suka riƙa gunaguni suna cewa. “Haba! Wannan mutum yana karɓar masu zunubi, har ma tare suke cin abinci!” 3 Sai ya ba su wannan misali ya ce. 4 “In waninku yana da tumaki ɗari, ɗayarsu ta ɓace, to, ba sai ya bar tasa'in da taran nan a makiyaya, ya bi sawun wadda ta ɓata, har ya same ta ba? 5 In kuwa ya same ta, sai ya saɓo ta a kafaɗa, yana farin ciki. 6 In ya dawo gida, sai ya tara abokansa da maƙwabta ya ce musu, ‘Ku taya ni farin ciki, don na samo tunkiyata da ta ɓata.’ 7 Ina dai gaya muku, haka kuma, za a yi farin ciki a Sama, a kan mai zunubi guda da ya tuba, fiye da a kan adalai tasa'in da tara waɗanda ba su bukatar tuba.”

Misali na Ɓataccen Kuɗi

8 “Ko kuwa wace mace ce, in tana da kuɗi azurfa guda goma, in ta yar da ɗaya, ba sai ta kunna fitila ta share gidan, ta yi ta nacin nemansa, har ta same shi ba? 9 In kuwa ta same shi, sai ta tara ƙawayenta da maƙwabta mata, ta ce musu, ‘Ku taya ni farin ciki, don na sami kuɗin nan da na yar.’ 10 Haka nake gaya muku, abin farin ciki ne ga mala'ikun Allah in mai zunubi guda ya tuba.”

Misali na Ɓataccen Ɗa

11 Ya kuma ce, “An yi wani mutum mai 'ya'ya biyu maza. 12 Sai ƙaramin ya ce wa mahaifinsa, ‘Baba, ba ni rabona na gādo.’ Sai mahaifin ya raba musu dukiyarsa. 13 Bayan 'yan kwanaki kaɗan sai ƙaramin ya tattara duk mallakarsa, ya kama hanya zuwa ƙasa mai nisa. A can ya fallasar da kayansa a wajen masha'a. 14 Da ya ɓad da kome kakat, aka yi babbar yunwa a ƙasar, sai ya shiga fatara. 15 Ya je ya rāɓu da wani ɗan ƙasar, shi kuwa ya tura shi makiyayar kiwon alade. 16 Har ma ya so ya cika cikinsa da kwasfar da aladu suke ci, amma ba wanda ya ba shi wani abu 17 Amma da ya tara hankalinsa sai ya ce, ‘Kaitona! Nawa ne daga cikin barorin mahaifina da suke da abinci, da yake kamar ƙasa a gare su! Ga ni a nan kuwa, yunwa tana kisana! 18 Zan tashi, in tafi gun mahaifina, in ce masa, “Baba, na yi wa Mai Sama zunubi, na kuma saɓa maka. 19 Ban ma cancanci a ƙara kirana ɗanka ba. Ka mai da ni kamar ɗaya daga cikin barorinka.” ’ 20 Sai ya tashi, ya taho wurin mahaifinsa. Amma tun yana daga nesa, sai mahaifinsa ya hango shi, tausayi ya kama shi, ya yiwo gudu, ya rungume shi, ya yi ta sumbatarsa. 21 Sai kuma ɗan ya ce masa, ‘Baba, na yi wa Mai Sama zunubi, na kuma saɓa maka. Ban ma cancanci a ƙara kirana ɗanka ba.’ 22 Amma mahaifin ya ce wa bayinsa, ‘Maza ku kawo riga mafi kyau, ku sa masa. Ku sa masa zobe da takalma, 23 a kuma kawo kiwataccen ɗan maraƙin nan, a yanka, mu ci, mu yi murna. 24 Don ɗan nan nawa dā ya mutu ne, amma a yanzu ya komo, dā ya ɓata, amma a yanzu an same shi.’ Sai suka yi ta farin ciki. 25 “A sa'an nan kuwa, babban ɗansa yana gona. Yana dawowa, ya yi kusa da gida ke nan, sai ya ji ana kaɗe-kaɗe da raye-raye. 26 Sai ya kira wani baran gidan, ya tambayi dalilin wannan abu. 27 Shi kuwa ya ce masa, ‘Ai, ɗan'uwanka ne ya dawo, tsohonku ya yanka kiwataccen ɗan maraƙin nan saboda ya sadu da shi lafiya ƙalau.’ 28 Amma wan ya yi fushi, ya ƙi shiga. Mahaifinsa kuwa ya fito, ya yi ta rarrashinsa. 29 Amma ya amsa wa mahaifinsa ya ce, ‘Dubi yawan shekarun nan da na bauta maka. Ban taɓa ta da umarninka ba. Duk da haka, ba ka taɓa ba ni ko ɗan taure ba, da za mu yi shagali tare da abokaina. 30 Amma da ɗan nan naka ya zo, wanda ya fallasar da dukiyarka a kan karuwai, ga shi, ka yanka masa kiwataccen ɗan maraƙin nan!’ 31 Sai mahaifin ya ce masa, ‘Ya ɗana, ai, kullum kana tare da ni, duk abin da yake nawa naka ne. 32 Ai kuwa, daidai ne a yi ta murna da farin ciki, don ɗan'uwan nan naka dā ya mutu, a yanzu ya komo, dā ya ɓata, amma an same shi.’ ”

Luka 16

Misali na Wakili Marar Gaskiya

1 Ya kuma ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki da yake da wakili. Sai aka sari wakilin a wurinsa a kan yana fallasar masa da dukiya. 2 Sai ya kira shi ya ce masa, ‘Labarin me nake ji naka? Kawo lissafin wakilcinka, don ba sauran ka zama wakilina.’ 3 Sai wakilin ya ce a ransa, ‘Ƙaƙa zan yi, da yake maigida zai karɓe wakilci daga hannuna? Ga shi, ba ni da ƙarfin noma, in yi roƙo kuwa, ina jin kunya. 4 Yau wa! Na san abin da zan yi, don in an fisshe ni daga wakilcin, mutane su karɓe ni a gidajensu.’ 5 Sai ya kira mabartan maigidansa da ɗaya ɗaya, ya ce wa na farko, ‘Nawa maigida yake bin ka?’ 6 Ya ce, ‘Garwa ɗari ta mai.’ Sai ya ce masa, ‘Ga takardarka, maza ka zauna, ka rubutu hamsin,’ 7 Ya kuma ce wa wani, ‘Kai fa, nawa ake bin ka?’ Sai ya ce, ‘Buhu ɗari na alkama.’ Ya ce masa, ‘Ga takardarka, ka rubuta tamanin.’ 8 Sai maigidan ya yaba wa wakilin nan marar gaskiya saboda wayonsa. Don 'yan zamani a ma'ammalarsu da mutanen zamaninsu, sun fi mutanen haske wayo. 9 Ina gaya muku, ku yi abokai ta dukiya, ko da yake aba ce wadda take iya aikata mugunta, don sa'ad da ta ƙare su karɓe ku a gidaje masu dawwama. 10 “Wanda yake da aminci a ƙaramin abu, mai aminci ne a babban abu. Wanda yake marar gaskiya a ƙaramin abu, marar gaskiya ne a babban abu. 11 Idan fa ba ku yi aminci da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya? 12 In kuma ba ku yi aminci da kayan wani ba, wa zai ba ku halaliyarku? 13 Ba baran da zai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗaya, ko kuwa ya amince wa ɗayan, ya raina ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah da dukiya gaba ɗaya.”

Shari'a da Mulkin Allah

14 Farisiyawa kuwa da yake masu son kuɗi ne, da jin haka, suka yi masa tsaki. 15 Sai ya ce musu, “Ku ne masu baratar da kanku a gaban mutane. Amma Allah ya san zukatanku. Abin da mutane suke girmamawa ƙwarai, ai, abin ƙyama ne a gun Allah. 16 “Attaura da litattafin annabawa suna nan har ya zuwa ga Yahaya, daga lokacin nan kuwa ake yin bisharar Mulkin Allah, kowa kuma yana kutsawa zuwa ciki. 17 Duk da haka, zai fi sauƙi sararin sama da ƙasa su shuɗe, da ɗigo ɗaya na Attaura ya gushe.”

Koyarwar Yesu a kan Kisan Aure

18 “Kowa ya saki matarsa ya auri wata, ya yi zina ke nan. Wanda ma ya auri sakakkiya ya yi zina.”

Mai Arziki da Li'azaru

19 “An yi wani mai arziki, mai sa tufafin jan alharini da farare masu ƙawa, yana shan daularsa a kowace rana. 20 An kuma ajiye wani gajiyayye a ƙofarsa, mai suna Li'azaru, wanda duk jikinsa miki ne. 21 Shi kuwa yana marmarin ya ƙoshi da suɗin mai arzikin nan. Har ma karnuka sukan zo suna lasar miyakunsa. 22 Ana nan sai gajiyayyen nan ya mutu, mala'iku kuma suka ɗauke shi, suka kai shi wurin ibraham. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi. 23 Yana a cikin Hades yana shan azaba, sai ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim daga nesa, da Li'azaru a wurinsa. 24 Sai ya yi kira ya ce, ‘Baba Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiko da Li'azaru ya tsoma kan yatsarsa a ruwa ya sanyaya harshena, don azaba nake sha a cikin wannan wuta.’ 25 Amma ibraham ya ce, ‘Ɗana, ka tuna fa, a zamanka na duniya ka sha duniyarka, Li'azaru kuwa ya sha wuya. Amma a yanzu daɗi ake ba shi, kai kuwa kana shan azaba. 26 Banda wannan ma duka, a tsakaninmu da ku akwai wani gawurtaccen rami mai zurfi, zaunanne, don waɗanda suke son ƙetarewa zuwa wurinku kada su iya, kada kuma kowa ya ƙetaro zuwa wurinmu daga can.’ 27 Sai mai arzikin ya ce, ‘To, ina roƙonka, Baba, ka aika shi zuwa gidan mahaifina, 28 don ina da 'yan'uwa biyar maza, ya je ya yi musu gargaɗi, kada su ma su zo wurin azabar nan.’ 29 Amma Ibrahim ya ce, ‘Ai, suna da littattafan Musa da na annabawa, su saurare su mana.’ 30 Sai ya ce, ‘A'a, Baba Ibrahim, in dai wani daga cikin matattu ya je wurinsu sa tuba.’ 31 Ibrahim ya ce masa, ‘In dai har ba su saurari littattafan Musa da na annabawa ba, ko da wani ya tashi daga cikin matattu ma, ba za su rinjayu ba.’ ”

Luka 17

Sanadodin Yin Zunubi

1 Sai ya ce wa almajiransa, “Sanadodin tuntuɓe ba su da makawa, duk da haka kaiton wanda shi ne sanadinsu! 2 Da dai wani ya sa ɗaya daga cikin waɗannan 'yan yara ya yi laifi, zai fiye masa a rataya wani dutsen niƙa a wuyansa, a jefa shi a cikin teku. 3 Ku kula da kanku fa. In ɗan'uwanka ya yi laifi, ka tsauta masa. In kuwa ya tuba, ka yafe shi. 4 Ko ya yi maka laifi sau bakwai a rana ɗaya, sa'an nan ya juyo wurinka sau bakwai ya ce, ‘Na tuba,’ sai ka yafe shi.”

Ƙara Mana Bangaskiya

5 Sai manzanni suka ce wa Ubangiji, “Ka ƙara mana bangaskiya.” 6 Ubangiji kuwa ya ce, “Da kuna da bangaskiya, ko da misalin ƙwayar mastad, da za ku ce wa wannan durumi, ‘Ka ciru, ka dasu a cikin teku,’ sai kuwa ya bi umarninku.”

Wajibin Bawa

7 “Misali, wane ne a cikinku in yana da bawa mai yi masa noma ko kiwon tumaki, da zarar ya dawo daga jeji, zai ce, ‘Maza, zo ka zauna, ka ci abinci?’ 8 Ashe, ba ce masa zai yi, ‘Shirya mini jibi, ka kuma yi ɗamara, ka yi mini hidima, har in gama ci da sha, daga baya kai kuma ka ci ka sha,’ ba? 9 Yā gode wa bawan nan don ya bi umarni? 10 Haka ku ma, in kuka bi duk abin da aka umarce ku, sai ku ce, ‘Mu bayi ne marasa amfani. Mun dai yi abin da yake wajibinmu kurum.’ ”

Yesu ya Warkar da Kutare Goma

11 Wata rana yana tafiya Urushalima, sai ya bi iyakar ƙasar Samariya da Galili. 12 Yana shiga wani ƙauye ke nan, sai waɗansu kutare maza guda goma suka tarye shi, suna tsaye daga nesa. 13 Sai suka ɗaga murya suka ce, “Ya Maigida Yesu, ka ji tausayinmu,” 14 Da ya gan su, ya ce musu, “Ku je wurin firistoci su gan ku.” Suna tafiya ke nan, sai suka tsarkaka. 15 Ɗayansu kuma da ganin an warkar da shi, ya komo, yana ta ɗaukaka Allah da murya mai ƙarfi, 16 ya fāɗi a gaban Yesu, yana gode masa. Shi kuwa Basamariye ne. 17 Yesu ya amsa ya ce, “Ba goma ne aka tsarkake ba? Ina taran? 18 Ashe, ba wanda aka samu ya komo ya ɗaukaka Allah, sai baƙon nan kaɗai?” 19 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi, ka yi tafiyarka. Bangaskiyarka ta warkar da kai.”

Bayyanar Mulkin Allah

20 Da Farisiyawa suka tambaye shi lokacin bayyanar Mulkin Allah, ya amsa musu ya ce, “Ai, bayyanar Mulkin Allah ba ganinta ake yi da ido ba. 21 Ba kuwa za a ce, ‘A! Ga shi nan,’ ko kuwa, ‘Ga shi can,’ ba. Ai, Mulkin Allah a tsakaninku yake.” 22 Ya kuma ce wa almajiran, “Lokaci yana zuwa da za ku yi begen ganin rana ɗaya daga cikin ranakun Ɗan Mutum, amma ba za ku gani ba. 23 Za su ce muku, ‘A! ga shi nan,’ ko kuwa, ‘Ga shi can!’ Kada ku je, kada ku bi su. 24 Kamar yadda walƙiya take wulgawa walai, daga wannan bangon duniya zuwa wancan, haka ma, Ɗan Mutum zai zama a ranar bayyanarsa. 25 Amma lalle sai ya sha wuya iri iri tukuna, mutanen zamanin nan kuma su ƙi shi. 26 Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka kuma zai faru a lokacin bayyanar Ɗan Mutum. 27 Ana ci, ana sha, ana aure, ana aurarwa, har ya zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi, Ruwan Tsufana kuma ya zo, ya hallaka su duka. 28 Haka ma aka yi a zamanin Lutu, ana ci, ana sha, ana saye, ana sayarwa, ana shuke-shuke da gine-gine, 29 amma a ranar da Lutu ya fita daga Saduma, aka zubo wuta da duwatsun wuta daga sama, aka hallaka su duka. 30 Haka kuma zai zama a ranar bayyanar Ɗan Mutum. 31 A ran nan fa wanda yake a kan soro, kayansa kuma suna a cikin gida, kada ya sauko garin ɗaukarsu. Haka kuma wanda yake gona, kada ya juyo. 32 Ku tuna fa da matar Lutu. 33 Duk mai son adana ransa, zai rasa shi. Duk kuwa wanda ya rasa ransa, adana shi ya yi. 34 Ina gaya muku, a wannan dare za a ga mutum biyu a gado ɗaya, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. 35 Za a ga mata biyu suna niƙa tare, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya. 36 Za a ga mutum biyu a gona, a ɗau ɗaya, a bar ɗaya.” 37 Sai suka amsa suka ce, “A ina ne, ya Ubangiji?” Ya ce musu, “A inda mushe yake, ai, a nan ungulai sukan taru.”

Luka 18

Misali na wadda Mijinta ya Mutu da Alƙali

1 Ya kuma ba su wani misali cewa ya kamata kullum su yi addu'a, kada kuma su karai. 2 Ya ce, “A wani gari an yi wani alƙali marar tsoron Allah, marar kula da mutane. 3 A garin nan kuwa da wata gwauruwa, sai ta riƙa zuwa wurinsa, tana ce masa, ‘Ka shiga a tsakanina da abokin gābana.’ 4 Da fari ya ƙi, amma daga baya sai ya ce a ransa, ‘Ko da yake ba na tsoron Allah, ba na kuma kula da mutane, 5 amma saboda gwauruwar nan ta dame ni, sai in bi mata hakkinta, don kada ta gajishe ni da yawan zuwa.’ ” 6 Sai Ubangiji ya ce, “Ku ji fa abin da alƙalin nan marar gaskiya ya faɗa! 7 Ashe, Allah ba zai biya wa zaɓaɓɓunsa da suke yi masa kuka dare da rana hakkinsu ba? Zai yi jinkiri a wajen taimakonsu ne? 8 Ina gaya muku, zai biya musu hakkinsu, da wuri kuwa. Amma kuwa sa'ad da Ɗan Mutum ya zo, zai tarar da bangaskiya a duniya ne?”

Misali na Bafarisiye da Mai Karɓar Haraji

9 Sai kuma ya ba da misalin nan ga waɗansu masu amince wa kansu, cewa su masu adalci ne, har suna raina sauran mutane, ya ce, 10 “Waɗansu mutum biyu suka shiga Haikali yin addu'a, ɗaya Bafarisiye, ɗaya kuma mai karɓar haraji. 11 Sai Bafarisiyen ya miƙe, ya yi addu'a ga kansa ya ce, ‘Ya Allah, na gode maka, da yake ni ba kamar sauran mutane nake ba, mazambata, marasa adalci, mazinata, ko ma kamar mai karɓar harajin nan. 12 Duk mako ina azumi sau biyu. Kome na samu nakan fitar da zakka.’ 13 Mai karɓar haraji kuwa yana tsaye daga can nesa, bai yarda ya ɗaga kai sama ba, sai dai yana bugun ƙirjinsa, yana cewa, ‘Ya Allah, ka yi mini jinƙai, ni mai zunubi!’ 14 Ina dai gaya muku, wannan mutum ya koma gidansa baratacce, ba kamar ɗayan ba. Don duk mai ɗaukaka kansa, za a ƙasƙantar da shi. Mai ƙasƙantar da kansa kuwa, ɗaukaka shi za a yi.”

Yesu ya sa wa 'Yan Yara Albarka

15 Waɗansu suka kawo masa 'yan yaransu, domin ya taɓa su. Ganin haka, sai almajiransa suka kwaɓe su. 16 Amma Yesu ya kira 'yan yara wurinsa ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su. Ai, Mulkin Allah na irinsu ne. 17 Hakika, ina gaya muku, duk wanda bai yi na'am da Mulkin Allah kamar yadda ƙaramin yaro yake yi ba, ba zai shiga Mulkin ba har abada.”

Shugaban Jama'a Mai Arziki

18 Wani shugaban jama'a ya tambaye shi ya ce, “Malam managarci, me zan yi in gaji rai madawwami?” 19 Sai Yesu ya ce masa, “Don me ka kira ni managarci? Ai, ba wani Managarci, sai Allah kaɗai. 20 Kā dai san umarnan nan, ‘Kada ka yi zina. Kada ka yi kisankai. Kada ka yi sata. Kada ka yi shaidar zur. Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’ ” 21 Sai ya ce, “Ai, duk na kiyaye waɗannan tun ƙuruciyata.” 22 Da Yesu ya ji haka, ya ce masa, “Har yanzu abu guda ne kawai ya rage maka, ka sayar da duk mallakarka, ka rarraba wa gajiyayyu, za ka sami wadata a Sama. Sa'an nan ka zo ka bi ni.” 23 Da jin haka, sai ya yi baƙin ciki gaya, don shi mai arziki ne da gaske. 24 Yesu kuwa da ya gan shi haka, ya ce, “Kai! Da ƙyar kamar me masu dukiya su shiga Mulkin Allah! 25 Ai, zai fiye wa raƙumi sauƙi ya bi ta kafar allura, da mai arziki ya shiga Mulkin Allah.” 26 Waɗanda suka ji wannan magana suka ce, “To, in haka ne, wa zai sami ceto ke nan?” 27 Amma Yesu ya ce, “Abin da ya fi ƙarfin mutum, mai yiwuwa ne a gun Allah.” 28 Sai Bitrus ya ce, “To, ai, ga shi, mun bar mallakarmu, mun bi ka.” 29 Yesu ya ce musu, “Hakika, ina gaya muku, ba wanda zai bar gida, ko matarsa, ko 'yan'uwansa, ko iyayensa, ko kuma 'ya'yansa, saboda Mulkin Allah, 30 sa'an nan ya kasa samun ninkinsu mai yawa a yanzu, a Lahira kuma ya sami rai madawwami.”

Yesu ya Sāke Faɗar irin Mutuwar da zai Yi

31 Sai ya keɓe sha biyun nan, ya ce musu, “Ga shi, za mu Urushalima, duk abin da yake a rubuce kuma a game da Ɗan Mutum, ta hannun annabawa zai tabbata. 32 Gama za a bāshe shi ga al'ummai, a yi masa ba'a, a wulakanta shi, a kuma tofa masa yau. 33 Za su yi masa bulala, su kashe shi, a rana ta uku kuma ya tashi.” 34 Amma ko ɗaya ba su fahimci waɗannan abubuwa ba, domin zancen nan a ɓoye yake daga gare su, ba su ma gane abin da aka faɗa ba.

Warkar da Makaho Mai Bara a kusa da Yariko

35 Da ya kusato Yariko, ga wani makaho a zaune a gefen hanya, yana bara. 36 Da ya ji taro yana wucewa, sai ya tambaya ko mene ne. 37 Suka ce masa, “Ai, Yesu Banazare ne yake wucewa.” 38 Sai ya ɗaga murya ya ce, “Ya Yesu Ɗan Dawuda, ka ji tausayina!” 39 Sai waɗanda suke a gaba suka kwaɓe shi ya yi shiru. Amma ƙara ɗaga murya yake yi ƙwarai da gaske, yana cewa, “Ya Ɗan Dawuda, ka ji tausayina!” 40 Sai Yesu ya tsaya, ya yi umarni a kawo shi wurinsa. Da ya zo kusa, ya tambaye shi, 41 “Me kake so in yi maka?” Ya ce, “Ya Ubangiji, in sami gani!” 42 Yesu ya ce masa, “Karɓi ganin gari, bangaskiyarka ta warkar da kai.” 43 Anan take ya sami gani, ya bi Yesu, yana ɗaukaka Allah. Ganin haka, sai duk jama'a suka yabi Allah.

Luka 19

Yesu da Zakka

1 Yesu ya shiga Yariko. Yana ratsa garin, 2 sai wani mutum mai suna Zakka, babba ne a cikin masu karɓar haraji, mai arziki ne kuma, 3 ya nemi ganin ko wane ne Yesu, amma ya kasa ganinsa saboda taro, don shi gajere ne. 4 Sai ya yi gaba a guje, ya hau wani durumi don ya gan shi, don Yesu ta nan zai bi. 5 Da Yesu ya iso wurin, ya ɗaga kai ya ce masa, “Zakka, yi maza ka sauko, domin yau lalle a gidanka zan sauka.” 6 Sai ya yi hanzari ya sauko, ya karɓe shi da murna. 7 Da suka ga haka, duk suka yi ta gunaguni, suka ce, “A! A gidan mai zunubi dai ya sauka!” 8 Sai Zakka ya miƙe, ya ce wa Ubangiji, “Ya Ubangiji, ka ga, rabin mallakata zan ba gajiyayyu. Kowa na zalunta kuwa, zan mayar masa da ninki huɗu.” 9 Yesu ya ce masa, “Yau kam, ceto ya sauka a gidan nan, tun da yake shi ma ɗan Ibrahim ne. 10 Don Ɗan Mutum ya zo ne musamman garin neman abin da ya ɓata, yă cece shi kuma.”

Misali na Fam Goma

11 Da suka ji abubuwan nan, Yesu ya ci gaba da gaya musu wani misali, gama yana kusa da Urushalima, suna kuma tsammani Mulkin Allah zai bayyana nan da nan. 12 Sai ya ce, “Wani mutum mai asali ya tafi wata ƙasa mai nisa neman sarauta yă dawo. 13 Sai ya kira bayinsa goma, ya ba su fam guda guda, ya kuma ce musu, ‘Ku yi ta jujjuya su har in dawo.’ 14 Amma mutanensa suka ƙi shi, har suka aiki jakadu a bayansa, cewa ba sa so ya yi mulki a kansu. 15 Ana nan, da ya samo sarantar ya dawo, sai ya yi umarni a kirawo bayin nan da ya bai wa kuɗin, ya ga ribar da suka ci a wajen jujjuyawar. 16 Sai na farko ya zo a gabansa, ya ce, ‘Ya ubangida, fam ɗinka ya jawo fam goma.’ 17 Sai shi kuma ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki! Tun da ka yi gaskiya a kan ƙaramin abu, to, na ba ka mulkin gari goma.’ 18 Sai na biyun ya zo, ya ce, ‘Ya ubangida, fam ɗinka ya jawo fam biyar.’ 19 Shi kuma ya ce masa, ‘Kai ma na ba ka mulkin gari biyar.’ 20 Wani kuma ya zo, ya ce, ‘Ya ubangida, ga fam ɗinka nan! Dā ma a mayani na ƙulle shi, na ajiye. 21 Domin ina tsoronka, don kai mutum ne mai tsanani, son banza a gare ka, kakan girbi abin da ba kai ka shuka ba.’ 22 Sai ya ce masa ‘Kai mugun bawa! Zan yi maka shari'a bisa ga abin da ka faɗa da bakinka. Ashe, ka sani ni mutum ne mai tsanani, mai son banza, ina kuma girbar abin da ba ni na shuka ba? 23 To, in haka ne, don me ba ka ajiye kuɗin nawa a banki ba, da dawowata in ƙarɓa, har da riba?’ 24 Sai ya ce wa na tsaitsaye a wurin, ‘Ku karɓe fam ɗin daga gunsa, ku bai wa mai goman nan.’ 25 Suka ce masa, ‘Ya Ubangiji, ai, yana da fam goma.’ 26 ‘Ina dai gaya muku, duk mai abu a kan ƙara wa. Marar abu kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai a karɓe masa. 27 Waɗannan maƙiya nawa kuwa, da ba sa so in yi mulki a kansu, ku kawo su nan a kashe su a gabana.’ ”

Mutanen Urushalima sun Marabci Yesu

28 Da Yesu ya faɗi haka, ya yi gaba zuwa Urushalima. 29 Da ya kusato Betafaji da Betanya, a wajen dutsen da ake kira Dutsen Zaitun, ya aiki almajiransa biyu, 30 ya ce musu, “Ku shiga ƙauyen can da yake a gabanku. Da shigarku za ku ga wani aholaki a ɗaure, wanda ba a taɓa hawa ba. Ku kwanto shi. 31 Kowa ya tambaye ku, ‘Don me kuke kwance shi?’ ku ce, ‘Ubangiji ne yake bukatarsa.’ ” 32 Sai waɗanda aka aika suka tafi, suka tarar kamar yadda ya faɗa musu. 33 Suna a cikin kwance aholakin, masu shi suka ce musu, “Don me kuke kwance aholakin nan?” 34 Sai suka ce, “Ubangiji ne yake bukatarsa.” 35 Sai suka kawo shi wurin Yesu. Da suka shimfiɗa mayafansu a kan aholakin, suka ɗora Yesu. 36 Yana cikin tafiya, sai mutane suka shisshimfiɗa mayafansu a hanya. 37 Da ya zo gab da gangaren Dutsen Zaitun, sai duk taron almajiran suka ɗauki murna, suna yabon Allah da murya mai ƙarfi saboda duk mu'ujizan da suka gani. 38 Suka ce, “Albarka ta tabbata ga Sarkin nan mai zuwa da sunan Ubangiji! Salama ta tabbata a Sama, ɗaukaka kuma ga Allah!” 39 Sai waɗansu Farisiyawa a cikin taron suka ce masa, “Malam, ka kwaɓi almajirinka mana!” 40 Ya amsa ya ce, “Ina dai gaya muku, ko waɗannan sun yi shiru, to, duwatsu ma sai su ɗauki sowa.” 41 Da ya matso kusa, ya kuma hangi birnin, sai ya yi masa kuka, 42 ya ce, “Da ma a ce a yanzu kun san abubuwan da suke kawo salama. Amma ga shi, a yanzu a ɓoye suke a gare ku. 43 Don lokaci zai auko muku da maƙiyanku za su yi muku ƙawanya, su yi muku zobe, su kuma tsattsare ku ta kowane gefe, 44 su fyaɗa ku a ƙasa, ku mutanen birni duka, ba kuma za su bar wani dutse a kan ɗan'uwansa ba a birninku, don ba ku fahimci lokacin da ake sauko muku da alheri ba.”

Yesu ya Tsabtace Haikali

45 Sai ya shiga Haikali, ya fara korar masu sayarwa, 46 ya ce musu, “Ai, a rubuce yake cewa, ‘Ɗakina zai kasance ɗakin addu'a.’ Amma ku kun maishe shi kogon 'yan fashi.” 47 Kowace rana ya yi ta koyarwa a Haikali. Amma manyan firistoci, da malaman Attaura, da shugabannin jama'a suka nema su hallaka shi. 48 Suka kuwa rasa abin da za su yi, saboda maganarsa ta ɗauke wa duk jama'a hankali.

Luka 20

Ana Shakkar Izinin Yesu

1 Wata rana yana koyar da mutane a Haikali, yana yi musu bishara, sai ga manyan firistoci da malaman Attaura, da shugabanni suka matso, 2 suka ce masa, “Gaya mana da wane izini kake yin abubuwan nan, ko kuwa wa ya ba ka izinin?” 3 Sai ya amsa musu ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku gaya mini, 4 baftismar da Yahaya ya yi, daga Sama take, ko kuwa ta mutum ce?” 5 Sai suka yi muhawwara da juna suka ce, “In mun ce, ‘Daga Sama take,’ sai ya ce, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’ 6 In kuwa muka ce, ‘Ta mutum ce,’ sai duk jama'a su jajjefe mu, don sun tabbata Yahaya annabi ne.” 7 Sai suka amsa masa, suka ce, ba su san daga inda take ba. 8 Yesu ya ce musu, “Haka ni kuma ba zan faɗa muku ko da wane izini nake yin abubuwan nan ba.”

Misali na Manoman da suka Yi Ijarar Garkar Inabi

9 Sai ya shiga ba jama'a misalin nan, ya ce, “Wani mutum ne ya yi garkar inabi, ya ba waɗansu manoma ijararta, ya kuma tafi wata ƙasa, ya daɗe. 10 Da kakar inabi ta yi, ya aiki wani bawansa a gun manoman nan su ba shi gallar garkar. Amma manoman suka yi masa d�ka, suka kore shi hannu wofi. 11 Ya kuma aiki wani bawa, shi ma suka yi masa d�ka, suka wulakanta shi, suka kore shi hannu wofi. 12 Har wa yau dai ya aiki na uku, shi kuwa suka yi masa rauni, suka kore shi. 13 Sai mai garkar ya ce, ‘Me zan yi ke nan? Zan aiki ƙaunataccen ɗana. Kila sa ga girmansa.’ 14 Amma da manoman suka gan shi, suka yi shawara da juna suka ce, ‘Ai, wannan shi ne magajin. Mu kashe shi mana, gādon ya zama namu.’ 15 Sai suka jefa shi a bayan shinge, suka kashe shi. To, me ubangidan garkar nan zai yi da su? 16 Sai ya zo ya hallaka manoman nan, ya ba waɗansu garkar.” Da suka ji haka, suka ce, “Allah ya sawwaƙe!” 17 Amma ya dube su, ya ce, “Wannan da yake a rubuce fa cewa, ‘Dutsen da magina suka ƙi, Shi ne ya zama mafificin dutsen gini?’ 18 Kowa ya faɗo a kan dutsen nan, sai ya ragargaje, amma wanda dutsen nan ya faɗa wa, niƙe shi zai yi kamar gari.”

Biyan Haraji ga Kaisar

19 Anan take malaman Attaura da manyan firistoci suka nema su kama Yesu, don sun lura a kansu ne ya ba da misalin, amma suna jin tsoron jama'a. 20 Sai suka yi ta haƙwansa, suka aiki 'yan rahoto, su kuwa suka nuna kamar su masu adalci ne, da nufin su kama shi a maganarsa, su kuma ba da shi ga mai mulki ya hukunta shi. 21 Suka tambaye shi suka ce, “Malam, ai, mun sani maganarka da koyarwarka duk gaskiya ne. Ka ɗauki kowa da kowa daidai, sai koyar da tafarkin Allah sosai kake yi. 22 Shin, daidai ne mu biya Kaisar haraji, ko kuwa babu?” 23 Shi kuwa ya gane makircinsu, ya ce musu, 24 “Ku nuna mini dinari. Surar wa da sunan wa yake a jikinsa?” Suka ce, “Na Kaisar ne.” 25 Sai ya ce musu, “To, ku ba Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba Allah abin da yake na Allah.” 26 Sai suka kasa kama shi a kan wannan magana a gaban mutane. Saboda kuma mamakin amsarsa, suka yi shiru.

Tambaya a kan Tashin Matattu

27 Sai waɗansu Sadukiyawa suka zo wurinsa (su da suke cewa, ba tashin matattu), 28 suka tambaye shi suka ce, “Malam, Musa dai ya rubuta mana, cewa idan ɗan'uwan mutum ya mutu, ya bar matarsa ba ɗa, lalle mutumin ya auri matar, ya haifa wa ɗan'uwansa 'ya'ya. 29 To, an yi waɗansu 'yan'uwa maza guda bakwai. Na farko ya yi aure, ya mutu bai bar na baya ba. 30 Na biyun, 31 da na ukun kuma suka aure ta. Haka dai, duk bakwai ɗin suka aure ta, suka mutu, ba wanda ya bar ɗa. 32 Daga baya kuma ita matar ta mutu. 33 To, a tashin matattu, matar wa za ta zama a cikinsu? Don duk bakwai ɗin sun aure ta.” 34 Sai Yesu ya ce musu, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna aurarwa. 35 Amma waɗanda aka ga sun cancanci samun shiga wancan zamani da kuma tashin nan daga matattu, ba za su yi aure ko aurarwa ba. 36 Ba shi yiwuwa su sāke mutuwa, don daidai suke da mala'iku, 'ya'yan Allah ne kuwa, da yake 'ya'yan tashin matattu ne. 37 A game da tashin matattu kuwa, ai, Musa ma ya faɗa, a labarin kurmin, a inda ya kira Ubangiji, Allahn Ibrahim, da Allahn ishaku, da Allahn Yakubu. 38 Ai, waɗanda Allah shi ne Allahnsu rayayyu ne, ba matattu ba. Don a wurinsa duka rayayyu ne.” 39 Sai waɗansu malaman Attaura suka amsa suka ce, “Malam, ka faɗi daidai.” 40 Daga nan kuma ba su yi ƙarfin halin tambayarsa wani abu ba.

Tambaya a kan Ɗan Dawuda

41 Amma ya ce musu, “Ƙaƙa za su ce Almasihu ɗan Dawuda ne? 42 Domin Dawuda da kansa a Zabura ya ce, ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, “Zauna a damana, 43 Sai na sa ka take maƙiyanka.” ’ 44 Dawuda ya ce shi Ubangiji ne. To, ƙaƙa zai zama ɗansa?”

Yesu ya Fallashi Malaman Attaura

45 Ya ce wa almajiransa a gaban dukan jama'a, 46 “Ku yi hankali da malaman Attaura, masu son yawo a cikin manyan riguna, masu so a gaishe su a kasuwa, masu son mafifitan mazaunai a majami'u, da mazaunan alfarma a wurin biki. 47 Su ne masu cin kayan gwauraye mata, masu yin doguwar addu'a don ɓad da sawu. Su za a yi wa hukunci mafi tsanani.”

Luka 21

Sadaka wadda aka Saka

1 Yesu ya ɗaga kai ya ga waɗansu masu arziki suna saka sadakarsu a baitulmalin Haikali. 2 Sai ya ga wata matalauciya gwauruwa ta saka rabin kobo biyu a ciki. 3 Sai ya ce, “Hakika, ina gaya muku, abin da matalauciyar gwauruwar nan ta saka a ciki, ya fi na sauran duka. 4 Domin duk waɗannan sun bayar daga yalwarsu ne, ita kuwa daga cikin rashinta ta ba da duk kuɗinta na abinci.”

Yesu ya Faɗi irin Rushewar da za ta Sami Haikali

5 Waɗansu suna zancen Haikali, da yadda aka ƙawata shi da duwatsun alfarma da keɓaɓɓun kayan sadaka, sai ya ce, 6 “In don waɗannan abubuwa da kuke kallo ne, ai, lokaci yana zuwa da ba wani dutsen da za a bari a nan a kan ɗan'uwansa da ba a baje shi ba.”

Alamu da Tsanance-tsanance

7 Sai suka tambaye shi suka ce, “Malam, a yaushe za a yi waɗannan abubuwa? Wace alama kuma za a gani sa'ad da suke shirin aukuwa?” 8 Sai ya ce, “Ku kula fa kada a ɓad da ku. Don mutane da yawa za su zo da sunana, suna cewa su ne ni, suna kuma cewa, ‘Lokaci ya yi kusa.’ To, kada ku bi su. 9 In kuma kun ji labarin yaƙe-yaƙe da hargitsi, kada ku firgita. Lalle ne wannan ya fara aukuwa, amma ƙarshen tukuna.” 10 Sa'an nan ya ce musu, “Al'umma za ta tasar wa al'umma, mulki ya tasar wa mulki. 11 Za a yi raurawar ƙasa manya manya, da kuma yunwa, da annoba a wurare dabam dabam. Za a kuma yi al'amura masu bantsoro da manyan alamu daga sama. 12 Amma kafin wannan duka, za su kama ku, su tsananta muku. Za su miƙa ku ga majami'u da kurkuku, su kuma kai ku a gaban sarakuna da mahukunta saboda sunana. 13 Wannan zai zama muku hanyar ba da shaida. 14 Saboda haka, sai ku ƙudura a ranku, a kan ba za ku damu da yadda za ku mai da jawabi ba. 15 Domin ni ne zan ba ku ikon hurci, da kuma hikima wadda duk abokan adawarku, ba za su iya shanyewa ko musawa ba. 16 Ko da iyayenku ma da 'yan'uwanku, da danginku, da abokanku, sai sun bāshe ku, su kuma sa a kashe waɗansunku. 17 Kowa kuma zai ƙi ku saboda sunana. 18 Amma ba gashin kanku ko ɗaya da zai yi ciwo. 19 Jurewarku ce za ta fisshe ku.”

Yesu ya Faɗi irin Ribɗewa da za ta Sami Urushalima

20 “Sa'ad da kuka ga rundunonin yaƙi sun kewaye Urushalima, sa'an nan ku tabbata ana kusan ribɗe ta. 21 Sa'an nan waɗanda suke a ƙasar Yahudiya, su gudu su shiga duwatsu, na birni su fice, na ƙauye kuma kada su shiga birni. 22 Saboda lokacin sakamako ne, don a cika duk abin da yake a rubuce. 23 Kaiton masu juna biyu da masu goyo a wannan lokaci! Don matsanancin ƙunci zai saukar wa ƙasar, da kuma fushin Allah ga jama'ar nan. 24 Za a kashe waɗansu da kaifin takobi, a kuma kakkama waɗansu a kai su bauta zuwa ƙasashen al'ummai duka. Al'ummai kuma za su tattake Urushalima, har ya zuwa cikar zamaninsu.”

Komowar Ɗan Mutum

25 “Za a kuma ga alamu a rana, da wata, da taurari, a duniya kuma al'ummai su matsu ƙwarai, suna shan damuwa saboda ƙugin teku da na raƙuman ruwa. 26 Mutane za su suma don tsoro, da kuma fargaban al'amuran da suke aukuwa ga duniya, don za a girgiza manyan abubuwan da suke a sararin sama. 27 A sa'an nan ne za su ga Ɗan Mutum yana zuwa a cikin gajimare da iko da ɗaukaka mai yawa. 28 Sa'ad da waɗannan al'amura suka fara aukuwa, sai ku ɗaga kai ku dubi sama, domin fansarku ta yi kusa.”

Aya a kan Itacen Ɓaure

29 Sai ya ba su wani misali, ya ce, “Ku dubi itacen ɓaure da dukan itatuwa, 30 da zarar sun fara toho, kuna gani, ku da kanku kun san damuna ta yi kusa ke nan. 31 Haka kuma sa'ad da kuka ga waɗannan al'amura suna aukuwa, ku sani Mulkin Allah ya gabato. 32 Hakika, ina gaya muku, zamanin nan ba zai shuɗe ba, sai duk abubuwan nan sun auku. 33 Sararin sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za ta shuɗe ba.”

Gargaɗi a Zauna a Faɗake

34 “Ku kula da kanku fa, kada zuciyarku ta zarme da yawan shaye-shaye da buguwa, da kuma taraddadin wannan duniya, har ba labari ranar nan ta mamaye ku kamar tarko. 35 Don haka, za ta auka wa mazaunan duniya duk, kowa da kowa. 36 Koyaushe ku zauna a faɗake, kuna addu'a ku sami ikon tsere wa dukan waɗannan al'amura da za su auku, ku kuma tsaya a gaban Ɗan Mutum.” 37 Kullum da rana yakan koyar a Haikali, da dare kuma yakan fita ya kwana a dutsen da ake ce da shi Dutsen Zaitun. 38 Da sassafe kuma dukan mutane sukan zo wurinsa a Haikali su saurare shi.

Luka 22

An Ƙulla Shawara gāba da Yesu

1 To, idin abinci marar yisti, wanda ake ce da shi Idin Ƙetarewa, ya gabato. 2 Sai manyan firistoci da malaman Attaura suka yi ta neman yadda za su kashe shi, amma kuwa suna tsoron jama'a. 3 Sai Shaiɗan ya shiga a cikin Yahuza, wanda ake kira Iskariyoti, ɗaya daga cikin sha biyun nan. 4 Sai ya tafi ya yi shawara da manyan firistoci da shugabannin dogaran Haikali a kan yadda zai bāshe shi a gare su. 5 Sai suka yi murna, suka kuma yi alkawarin ba shi kuɗi. 6 Shi kuwa ya yarda, ya kuma nemi hanyar bāshe shi a gare su a bayan idon jama'a.

Yesu ya Ci Jibin Ƙetarewa tare da Almajiransa

7 Sai rana idin abinci marar yisti ta zo, wato, rana da ake yanka ɗan ragon Idin Ƙetarewa. 8 Sai Yesu ya aiki Bitrus da Yahaya, ya ce musu, “Ku je ku shirya mana Jibin Ƙetarewa mu ci.” 9 Suka ce masa, “A ina kake so mu shirya?” 10 Ya ce musu, “Ga shi, da shigarku gari, za ku gamu da wani mutum a ɗauke da tulun ruwa. Ku bi shi har zuwa cikin gidan da ya shiga. 11 Ku ce wa maigidan, ‘Malam ya ce, ina masaukin da zai ci Jibin Ƙetarewa da almajiransa?’ 12 Shi kuwa zai nuna muku wani babban soron bene mai kaya a shirye. A nan za ku shirya mana.” 13 Sai suka tafi, suka kuwa tarar kamar yadda ya faɗa musu, suka shirya Jibin Ƙetarewa.

Cin Jibin Ubangiji

14 Da lokaci ya yi, sai ya zauna cin abinci, manzanninsa kuma suna tare da shi. 15 Ya ce musu, “Ina so ƙwarai ko dā ma in ci jibin nan na Ƙetarewa tare da ku, kafin in sha wuya. 16 Gama ina gaya muku ba zan ƙara cin sa ba, sai an cika shi a Mulkin Allah.” 17 Sai ya karɓi ƙoƙo, bayan da ya yi godiya ga Allah, ya ce, “Ungo wannan, ku shassha. 18 Ina gaya muku, daga yanzu, ba zan ƙara shan ruwan inabi ba, sai Mulkin Allah ya bayyana.” 19 Sai ya ɗauki gurasa, bayan da ya yi godiya ga Allah, ya gutsuttsura, ya ba su, ya ce, “Wannan jikina ne da za a bayar dominku. Ku riƙa yin haka, domin tunawa da ni.” 20 Haka kuma, bayan jibi, ya ɗauki ƙoƙon, ya ce, “Ƙoƙon nan sabon alkawari ne, da aka tabbatar da jinina da za a bayar dominku. 21 Amma ga shi, mai bāshe ni ɗin nan yana ci a akushi ɗaya da ni. 22 Lalle Ɗan Mutum zai ƙaura kamar yadda aka ƙaddara, duk da haka, kaiton mutumin nan da yake ba da shi!” 23 Sai suka fara tambayar juna ko wane ne a cikinsu zai yi haka. 22 .24 M�su a kan Ko wane ne Babba M�su a kan Ko wane ne Babba 24 Sai m�su ya tashi a tsakaninsu, a kan ko wane ne babbansu. 25 Sai ya ce musu, “Sarakunan al'ummai sukan nuna musu iko, mahukuntansu kuma sukan nema a ce da su, ‘Mataimakan jama'a.’ 26 Amma ku kam ba haka ba. Sai dai wanda yake babba a cikinku yă zama kamar ƙarami, shugaba kuwa yă zama kamar mai hidima. 27 Wa ya fi girma? Wanda ya zauna cin abinci, ko kuwa mai hidimar? Ashe, ba wanda ya zauna cin abinci ba ne? Ga shi kuwa, ina a cikinku kamar mai hidima. 28 “Ku ne kuka tsaya a gare ni a gwaje-gwajen da na sha. 29 Kamar yadda Ubana ya ba ni mulki, haka, ni ma nake ba ku iko, 30 ku ci ku sha tare da ni a mulkina, ku kuma zauna a kursiyai, kuna hukunta kabilan nan goma sha biyu na Isra'ila. 22 .31 Bitrus zai yi M�sun Sanin Yesu Bitrus zai yi M�sun Sanin Yesu 31 “Bitrus, ya Bitrus, Shaiɗan ya nemi izinin sheƙe ku kamar alkama, ya kuwa samu. 32 Ni kuwa na yi maka addu'a, kada bangaskiyarka ta kāsa. Kai kuma, bayan da ka juyo, sai ka ƙarfafa 'yan'uwanka.” 33 Bitrus ya ce masa, “Ya Ubangiji, a shirye nake in bi ka har cikin kurkuku, ko kuma Lahira.” 34 Yesu ya ce, “Ina dai gaya maka Bitrus, a yau ma, kafin carar zakara, za ka yi m�sun sanina sau uku.”

Jakar Kuɗi, Burgami da Takobi

35 Ya kuma ce musu, “Sa'ad da na aike ku ba kuɗi a ɗamararku, ba burgami, ba takalma, akwai abin da kuka rasa?” Suka ce, “Babu.” 36 Ya ce musu, “Amma a yanzu duk mai jakar kuɗi yă ɗauka, haka kuma mai burgami. Wanda kuwa ba shi da takobi, ya sayar da mayafinsa ya saya. 37 Ina dai gaya muku, lalle ne a cika wannan Nassi a kaina cewa, ‘An lasafta shi a cikin masu laifi.’ Gama abin da aka faɗa a kaina, tabbatarsa ta zo.” 38 Sai suka ce, “Ya Ubangiji, ai ga takuba biyu.” Ya ce musu, “Ya isa.”

Yesu ya yi Addu'a a Gatsemani

39 Sai ya fita ya tafi Dutsen Zaitun, kamar yadda ya saba yi. Almajiransa kuwa suka bi shi. 40 Da ya iso wurin, ya ce musu, “Ku yi addu'a, kada ku faɗa ga gwaji.” 41 Sai ya ɗan rabu da su misalin nisan jifa, ya durƙusa, ya yi addu'a. 42 Ya ce, “Ya Uba, in dai ka yarda, ka ɗauke mini ƙoƙon wahalar nan. Duk da haka dai, ba nufina ba, sai naka za a bi” 43 Sai wani mala'ika ya bayyana a gare shi daga Sama, yana ƙarfafa shi. 44 Domin kuma yana shan wahala gaya, sai ya ƙara himmar addu'a, har jiɓinsa yana ɗiɗɗiga ƙasa kamar manyan ɗarsashin jini. 45 Da ya tashi daga addu'a, ya koma wurin almajiran, ya tarar suna barci saboda baƙin ciki. 46 Sai ya ce musu, “Don me kuke barci? Ku tashi, ku yi addu'a, kada ku faɗa ga gwaji.”

An Ba da Yesu, an Kama Shi

47 Kafin ya rufe baki, sai ga taron jama'a suka zo, mutumin da ake kira Yahuza, ɗaya daga cikin sha biyun nan, yake yi musu jagaba. Sai ya matso kusa da Yesu, don ya sumbace shi. 48 Amma Yesu ya ce masa, “Yahuza, ashe, da sumba za ka ba da Ɗan Mutum?” 49 Da na kusa da shi suka ga abin da za a yi, suka ce, “Ya Ubangiji, mu yi sara da takuba ne?” 50 Sai ɗayansu ya kai wa bawan babban firist sara, ya ɗauke masa kunnensa na dama. 51 Yesu ya amsa ya ce, “Ku ƙyale su haka.” Sai ya taɓa kunnen bawan, ya warkar da shi. 52 Yesu kuma ya ce wa waɗanda suka tasar masa, wato, manyan firistoci da shugabannin dogaran Haikali da shugabannin jama'a, “Kun fito ne da takuba da kulake, kamar masu kama ɗan fashi? 53 Sa'ad da nake tare da ku kowace rana a cikin Haikali, ba ku miƙa hannu garin ku kama ni ba. Amma wannan lokacinku ne da na ikon duhu.” 22 .54 Bitrus ya yi M�sun Sanin Yesu Bitrus ya yi M�sun Sanin Yesu 54 Sai suka kama shi, suka tafi da shi, suka kai shi a cikin gidan babban firist. Bitrus kuwa yana biye daga nesa nesa. 55 Da suka hura wuta a tsakar gida suka zazzauna, Bitrus ma ya zauna a cikinsu. 56 Sai wata baranya ta gan shi a zaune a hasken wuta, ta zura masa ido, ta ce, “Ai, mutumin nan ma, tare da shi yake.” 57 Amma ya musa ya ce, “Ke, ban ma san shi ba.” 58 Bayan ɗan lokaci kaɗan kuma, sai wani ya gan shi, ya ce, “Kai ma, ai, ɗayansu ne.” Amma Bitrus ya ce, “Ya mutum, ba haka ba ne.” 59 Bayan wajen sa'a guda sai wani ya nace, ya ce, “Ba shakka mutumin nan ma tare da shi yake, don Bagalile ne.” 60 Amma Bitrus ya ce, “Haba, ban ma san abin da kake faɗa ba.” Anan take, kafin ya rufe baki, sai zakara ya yi cara. 61 Sai Ubangiji ya juya ya dubi Bitrus. Bitrus kuwa ya tuna da maganar da Ubangiji ya faɗa masa cewa, “A yau ma kafin carar zakara, za ka yi musun sanina sau uku.” 62 Sai ya fita waje, ya yi ta rusa kuka.

An Yi wa Yesu Ba'a, an Duke Shi

63 Sai mutanen da suke riƙe da Yesu suka yi tayi masa ba'a, suna d�kansa. 64 Suka ɗaure masa idanu, suka tambaye shi, suka ce, “Yi annabci! Wa ya buge ka?” 65 Suka kuma yi tayi masa baƙaƙen maganganu masu yawa, suna zaginsa.

Yesu a gaban 'Yan Majalisa

66 Da gari ya waye sai majalisar shugabannin jama'a ta haɗu, da manyan firistoci da kuma malaman Attaura. Suka kai shi ɗakin majalisarsu suka ce, 67 “To, in kai ne Almasihu, gaya mana.” Amma ya ce musu, “Ko na gaya muku, ba za ku gaskata ba. 68 In kuma na yi muku tambaya, ba za ku mai da jawabi ba. 69 Amma a nan gaba, Ɗan Mutum zai zauna a dama na Allah Mai iko.” 70 Duk suka ce, “Ashe, kai ɗin nan Ɗan Allah ne?” Sai ya ce musu, “Yadda kuka faɗa, ni ne.” 71 Sai suka ce, “Wace shaida kuma za mu nema? Ai, mun ji da kanmu daga bakinsa.”

Luka 23

Yesu a gaban Bilatus

1 Duk taronsu sai suka tashi, suka kai shi a gaban Bilatus. 2 Sai suka fara kai ƙararsa, suna cewa, “Mun sami mutumin nan yana ɓad da jama'armu, yana hana a biya Kaisar haraji, yana cewa, shi ne Almasihu, sarki kuma.” 3 Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai ɗin nan, kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “Yadda ka faɗa.” 4 Bilatus ya ce wa manyan firistoci da taro masu yawa, “Ban sami mutumin nan da wani laifi ba.” 5 Sai suka fara matsa masa lamba, suna cewa, “Yana ta da hankalin jama'a, yana koyarwa a dukan ƙasar Yahudiya, tun daga ƙasar Galili har zuwa nan.”

Yesu a gaban Hirudus

6 Da Bilatus ya ji haka, ya tambaya ko mutumin nan Bagalile ne. 7 Da ya ji Yesu a ƙarƙashin mulkin Hirudus yake, sai ya aika da shi wurin Hirudus, don shi ma yana Urushalima a lokacin. 8 Da Hirudus ya ga Yesu, ya yi murna ƙwarai, saboda tun da daɗewa yake son ganinsa, don ya riga ya ji labarinsa, yana kuma fata ya ga wata mu'ujiza da Yesu zai yi. 9 Sai ya yi tayi masa tambayoyi da yawa, amma bai amsa masa da kome ba. 10 Manyan firistoci da malaman Attaura suna nan a tsaitsaye, suna tsananta kai ƙararrakinsa ainun. 11 Sai Hirudus da sojansa suka wulakanta shi, suka yi masa ba'a, da suka sa masa tufafi masu ƙawa kuma, suka mai da shi wurin Bilatus. 12 A ran nan sai Hirudus da Bilatus suka yi sulhu, don dā abokan gāba ne.

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

13 Bilatus ya tara manyan firistoci da shugabanni da kuma jama'a, 14 ya ce masu, “Kun kawo mini mutumin nan a kan, cewa yana ɓad da jama'a, na kuwa tuhunce shi a gabanku, amma ban same shi da wani laifi a ƙararrakinsa da kuka kawo ba. 15 Hirudus ma bai samu ba, don ya komo mana da shi. Ga shi kuwa, bai yi wani abu da ya cancanci kisa ba. 16 Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.” 17 A lokacin idi kuwa lalle ne ya sakar musu ɗaurarre guda. 18 Amma duk suka ɗauki ihu gaba ɗaya, suna cewa, “A yi da wannan ɗin, a sakar mana Barabbas!” 19 (Barabbas shi ne wani mutum da aka jefa a kurkuku, saboda wani tawayen da aka yi a birni, da kuma kisankai.) 20 Sai Bilatus ya sāke yi musu magana, don yana so ya saki Yesu. 21 Amma suka yi ta ƙwala ihu, suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!” 22 Ya sāke faɗa musu, a faɗa ta uku, “Ta wane hali? Wane mugun abu ya yi? Ai, ban sami dalilin kisa a gare shi ba. Saboda haka, zan yi masa bulala in sake shi.” 23 Amma suka yi ta matsa lamba, suna ɗaga murya, suna cewa a gicciye shi, har surutunsu ya yi rinjaye. 24 Sai Bilatus ya zartar da hukunci a biya musu bukata. 25 Ya kuwa sakar musu wanda suka roƙa, wato, wanda aka jefa a kurkuku a kan laifin tawaye da kuma kisankai. Amma ya ba da Yesu, su yi masa abin da suke so.

An Gicciye Yesu

26 Suna tafiya da Yesu ke nan, sai suka cafke wani, mai suna Saminu Bakurane, yana zuwa daga ƙauye, suka ɗora masa gicciye, yă ɗauka ya bi Yesu. 27 Sai taron mutane masu yawan gaske suka bi shi, da waɗansu mata da suke kuka, suke kuma gunji saboda shi. 28 Amma Yesu ya juya zuwa gare su, ya ce, “Ya ku matan Urushalima, ku bar yi mini kuka, sai dai ku yi wa kanku da kuma 'ya'yanku, 29 don lokaci yana zuwa da za ku ce, ‘Albarka tā tabbata ga matar bakararru, waɗanda ba su taɓa haihuwa ba, waɗanda kuma ba a taɓa shan mamansu ba.’ 30 Sa'an nan ne za su fara ce wa manyan duwatsu, ‘Ku faɗo a kanmu,’ su kuma ce da tsaunuka, ‘Ku binne mu.’ 31 In fa irin abubuwan nan suna faruwa ga ɗanye, yaya zai zama ga ƙeƙasasshe?” 32 Waɗansu mutum biyu kuma masu laifi, aka kai su a kashe su tare da shi. 33 Da suka isa wurin da ake ce da shi Ƙoƙwan Kai, a nan suka gicciye shi, da kuma masu laifin nan, ɗaya a damansa, ɗaya a hagun. 34 Sai Yesu ya ce, “Ya Uba, ka yi musu gafara, don ba su san abin da suke yi ba.” Suka rarraba tufafinsa, suna kari'a a kansu. 35 Mutane da suke a tsaitsaye, suna kallo. Shugabanni kuma suka yi masa ba'a, suka ce, “Ya ceci waɗansu, to, ya ceci kansa mana, in shi ne Almasihu na Allah zaɓaɓɓensa!” 36 Soja kuma suka yi masa ba'a, suka matso, suka miƙa masa ruwan tsami, 37 suna cewa, “In kai ne Sarkin Yahudawa, to, ka cece kanka mana!” 38 Sama da shi kuma aka yi wani rubutu cewa, “Wannan shi ne Sarkin Yahudawa.” 39 Sai ɗaya daga cikin masu laifin, da aka gicciye ya yi masa baƙar magana ya ce, “Shin, ba kai ne Almasihu ba? To, ceci kanku mana, duk da mu!” 40 Amma ɗayan ya amsa, ya kwaɓe shi, ya ce, “Kai ko tsaron Allah ma ba ka yi, kai, da yake hukuncinka daidai da nasa? 41 Mu kam, daidai aka yi mana, don hakika sakamakon aikinmu muka samu, amma mutumin nan bai yi wani laifi ba.” 42 Ya kuma ce, “Ya Yesu, ka tuna da ni, a sa'ad da ka shiga sarautarka.” 43 Yesu ya ce masa, “Hakika, ina gaya maka, yau ma za ka kasance tare da ni a Firdausi.”

Mutuwar Yesu

44 To, a wajen tsakar rana ne kuwa, sai duhu ya rufe ƙasa duka, har zuwa ƙarfe uku na yamma. 45 Hasken rana ya dushe. Labulen da yake a cikin Haikali ya tsage gida biyu. 46 Sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Ya Uba, na sa ruhuna a ikonka.” Da ya faɗi haka kuwa, sai ya cika. 47 Sa'ad da jarumin ya ga abin da ya gudana, sai ya girmama Allah ya ce, “Hakika mutumin nan marar laifi ne!” 48 Sa'ad da duk taro masu yawa, waɗanda suka zo kallo suka ga abin da ya faru, suka koma, suna bugun ƙirjinsu. 49 Amma duk idon sani, da kuma matan da suka biyo shi, tun daga ƙasar Galili, suka tsaya daga nesa, suna duban waɗannan abubuwa.

Jana'izar Yesu

50 To, akwai wani mutum mai suna Yusufu, mutumin Arimatiya, wani garin Yahudawa, shi ɗan majalisa ne, nagari ne, adali kuma. 51 Shi kuwa dā ma bai yarda da shawararsu, da kuma abin da suka yi ba, yana kuwa sauraron bayyanar Mulkin Allah. 52 Shi ne ya tafi wurin Bilatus, ya roƙa a ba shi jikin Yesu. 53 Sai ya sauko da shi, ya sa shi a likkafanin lilin, ya sa shi a wani kabari da aka fafe dutse aka yi, wanda ba a taɓa sa kowa ba. 54 Ran nan kuwa ranar shiri ce, Asabar kuma ta doso. 55 Matan nan kuwa da suka zo tare da shi daga ƙasar Galili, suka bi baya, suka duba kabarin da yadda kuma aka sa jikinsa. 56 Sai suka koma, suka shirya kayan ƙanshi da man shafawa. Ran Asabar kuwa, sai suka huta bisa ga umarni.

Luka 24

Tashin Yesu daga Matattu

1 A ranar farko ta mako kuwa, da asussuba, suka je wurin kabarin da kayan ƙanshi da suka shirya. 2 Sai suka tarar an mirgine dutsen daga kabarin. 3 Suka shiga ciki, amma ba su sami jikin Ubangiji ba. 4 Tun suna cikin damuwa da abin, sai kawai ga waɗansu mutum biyu a tsaye a kusa da su, saye da tufafi masu ƙyalƙyali. 5 Don tsoro, matan suka sunkuyar da kansu a ƙasa. Mutanen suka ce musu, “Don me kuke neman rayayye a cikin matattu? 6 Ai, ba ya nan, ya tashi. Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana Galili 7 cewa, ‘Lalle ne a ba da Ɗan Mutum ga mutane masu zunubi, a gicciye shi, a rana ta uku kuma ya tashi.’ ” 8 Sai suka tuna da maganarsa. 9 Da suka dawo daga kabarin suka shaida wa goma sha ɗayan nan, da kuma duk sauransu, dukan waɗannan abubuwa. 10 To, Maryamu Magadaliya, da Yuwana, da Maryamu uwar Yakubu, da kuma sauran matan da suke tare da su, su ne suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa. 11 Su kuwa sai maganar nan ta zama musu kamar zance ne kawai, suka ƙi gaskatawa. 12 Amma Bitrus ya tashi, ya doshi kabarin da gudu. Ya duƙa, ya leƙa a ciki, ya ga likkafanin lilin a ajiye a waje ɗaya. Sai ya koma gida yana al'ajabin abin da ya auku.

Almajirai Biyu a Hanyar Imuwasu

13 A ran nan kuma sai ga waɗansu biyu suna tafiya wani ƙauye, mai suna Imuwasu, nisansa daga Urushalima kuwa kusan mil bakwai ne. 14 Suna ta zance da juna a kan dukan al'amuran da suka faru. 15 Ya zamana tun suna magana, suna tunani tare, sai Yesu da kansa ya matso, suka tafi tare. 16 Amma idanunsu a rufe, har ba su gane shi ba. 17 Yesu ya ce musu, “Wace magana ce kuke yi da juna a tafe?” Sai suka tsaya cik, suna baƙin ciki. 18 Sai ɗayansu, mai suna Kiliyobas, ya amsa masa ya ce, “Ashe, kai kaɗai ne baƙo a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a 'yan kwanakin nan ba?” 19 Sai ya ce musu, “Waɗanne abubuwa?” Suka ce masa, “A game da Yesu Banazare ne, wanda yake annabi mai manyan ayyuka da ƙwaƙƙwarar magana a gaban Allah da dukan mutane, 20 da kuma yadda manyan firistoci da shugabanninmu suka ba da shi don a yi masa hukuncin kisa, suka kuwa gicciye shi. 21 Dā kuwa muna bege shi ne zai fanshi Isra'ila. Hakika kuma, bayan wannan duka, yau kwana uku ke nan da aukuwar wannan abu. 22 Har wa yau kuma, waɗansu mata na cikinmu, sun ba mu al'ajabi. Don sun je kabarin da sassafe, 23 da ba su sami jikinsa ba, suka komo, suka ce har ma an yi musu wahayi, sun ga mala'ikun da suka ce yana da rai. 24 Waɗansunsu da suke tare da mu kuma, suka je kabarin, suka tarar kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.” 25 Sai Yesu ya ce musu, “Ya ku mutane marasa fahimta, masu nauyin gaskata duk abin da annabawa suka faɗa! 26 Ashe, ba wajibi ne Almasihu ya sha wuyar waɗannan abubuwa ba, ya kuma shiga ɗaukakarsa?” 27 Sai ya fara ta kan littattafan Musa da na dukan annabawa, ya yi ta bayyana musu abubuwan da suka shafe shi a dukan Littattafai. 28 Sai suka kusato ƙauyen da za su. Ya yi kamar zai ci gaba, 29 suka matsa masa suka ce, “Sauka a wurinmu, ai, magariba ta doso, rana duk ta tafi.” Sai ya sauka a wurinsu. 30 Sa'ad da yake cin abinci tare da su, sai ya ɗauki gurasa, ya yi wa Allah godiya, ya gutsura, ya ba su. 31 Idonsu ya buɗe, suka kuma gane shi. Sai ya ɓace musu. 32 Suka ce wa juna, “Ashe, zuciyarmu ba ta yi annuri ba, sa'ad da yake a hanya, yana bayyana mana Littattafai?” 33 Anan take, suka tashi suka koma Urushalima, suka sami sha ɗayan nan tare gu ɗaya, da kuma waɗanda suke tare da su, 34 suna cewa, “Hakika Ubangiji ya tashi, har ya bayyana ga Bitrus!” 35 Su kuma suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane shi a wajen gutsura gurasa.

Yesu ya Bayyana ga Almajiransa

36 Suna a cikin faɗar waɗannan abubuwa, sai ga Yesu da kansa a tsaye a tsakiyarsu, ya ce musu, “Salama a gare ku!” 37 Amma suka firgita, tsoro ya kama su, suka zaci fatalwa suke gani. 38 Sai ya ce musu, “Don me kuka firgita, kuke kuma tantama a zuciyarku? 39 Ku dubi hannuwana da ƙafafuna, ai, ni ne da kaina. Ku taɓa ni, ku ji, don fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.” 40 Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa. 41 Amma tun suna da sauran shakka saboda tsananin farin ciki da mamaki, sai ya ce musu, “Kuna da wani abinci a nan?” 42 Sai suka ba shi wata tsokar gasasshen kifi. 43 Ya kuwa karɓa, ya ci a gabansu. 44 Ya kuma ce musu, “Wannan ita ce maganata da na gaya muku tun muna tare, cewa lalle ne a cika duk abin da yake a rubuce, a game da ni a Attaura ta Musa, da littattafan annabawa, da kuma Zabura.” 45 Sa'an nan ya wayar da hankalinsu su fahimci Littattafai, 46 ya kuma ce musu, “Haka yake a rubuce, cewa wajibi ne Almasihu ya sha wuya, a rana ta uku kuma ya tashi daga matattu, 47 a kuma yi wa dukan al'ummai wa'azi su tuba, a gafarta musu zunubansu saboda sunansa. Za a kuwa fara daga Urushalima. 48 Ku ne shaidun waɗannan abubuwa. 49 Ga shi, ni zan aiko muku da abin da Ubana ya alkawarta. Amma ku dakata a birni tukuna, har a yi muku baiwar iko daga Sama.”

An Ɗauke Yesu zuwa Sama

50 Sai ya kai su a waje har jikin Betanya. Ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka. 51 Yana sa musu albarka ke nan, sai ya rabu da su, aka ɗauke shi zuwa sama. 52 Su kuwa suka yi masa sujada, suka koma Urushalima, suna matuƙar farin ciki. 53 Ko yaushe kuma suna a Haikali suna yabon Allah.

Yahaya 1

Kalman ya Zama Mutum

1 Tun fil'azal akwai Kalma, Kalman nan kuwa tare da Allah yake, Kalman nan kuwa Allah ne. 2 Shi ne tun fil'azal yake tare da Allah. 3 Dukan abubuwa sun kasance ta gare shi ne, ba kuma abin da ya kasance na abubuwan da suka kasance, sai ta game da shi. 4 Shi ne tushen rai, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane. 5 Haske na haskakawa cikin duhu, duhun kuwa bai rinjaye shi ba. 6 Akwai wani mutum da Allah ya aiko, mai suna Yahaya. 7 Shi fa ya zo shaida ne, domin ya shaidi hasken, kowa yă ba da gaskiya ta hanyarsa. 8 Ba shi ne hasken ba, ya zo ne domin ya shaidi hasken. 9 Akwai hakikanin haske mai shigowa duniya da yake haskaka kowane mutum. 10 Dā yana duniyar ma ta wurinsa ta kasance, duk da haka duniya ba ta san shi ba. 11 Ya zo ga abin mulkinsa ne, jama'arsa kuwa ba ta karɓe shi ba. 12 Amma duk iyakar waɗanda suka karɓe shi, wato, masu gaskatawa da sunansa, ya ba su ikon zama 'ya'yan Allah, 13 wato, waɗanda aka haifa ba daga jini ba, ba daga nufin jiki ko nufin mutum ba, amma daga wurin Allah. 14 Kalman nan kuwa ya zama mutum, ya zauna a cikinmu, yana mai matuƙar alheri da gaskiya. Mun kuma dubi ɗaukakarsa, ɗaukaka ce ta makaɗaicin Ɗa daga wurin Ubansa. 15 Yahaya ya shaida shi, ya ɗaga murya ya ce, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya zama shugabana, domin dā ma yana nan tun ba ni.’ ” 16 Dukanmu kuwa daga falalarsa muka samu, alheri kan alheri. 17 Domin Shari'a, ta hannun Musa aka ba da ita, alheri da gaskiya kuwa ta wurin Yesu Almasihu suka kasance. 18 Ba mutumin da ya taɓa ganin Allah daɗai. Makaɗaicin Ɗa, wanda yake yadda Allah yake, wanda kuma yake a wurin Uba, shi ne ya bayyana shi.

Shaidar Yahaya Maibaftisma

19 Wannan kuwa ita ce shaidar Yahaya, wato, sa'ad da Yahudawa suka aiki firistoci da Lawiyawa daga Urushalima su tambaye shi, ko shi wane ne. 20 Sai ya faɗi gaskiya, bai yi m�su ba, gaskiya ya faɗa ya ce, “Ba ni ne Almasihu ba.” 21 Sai suka tambaye shi, “To, yaya, Iliya ne kai?” Ya ce, “A'a, ba shi ba ne.” Suka ce, “Kai ne annabin nan?” Ya ce, “A'a.” 22 Sai suka ce masa, “To, wane ne kai, domin mu sami amsar da za mu mayar wa waɗanda suka aiko mu? Me kake ce da kanka?” 23 Ya ce, “Ni murya ce ta mai kira a jeji, mai cewa, ‘Ku gyara wa Ubangiji tafarki,’ yadda Annabi Ishaya ya faɗa.” 24 Su kuwa, Farisiyawa ne suka aiko su. 25 Sai suka tambaye shi suka ce, “To, don me kake yin baftisma in kai ba Almasihu ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?” 26 Sai Yahaya ya amsa musu ya ce, “Ni kam, da ruwa nake baftisma, amma da wani nan tsaye a cikinku wanda ba ku sani ba, 27 shi ne mai zuwa bayana, wanda ko maɓallin takalminsa ma, ban isa in kwance ba.” 28 An yi wannan a Betanya ne, a hayin Kogin Urdun, inda Yahaya yake yin baftisma. 1 .29 “Ga Ɗan Rago na Allah” “Ga Ɗan Rago na Allah” 29 Kashegari Yahaya ya tsinkayo Yesu na nufo shi, sai ya ce, “Kun ga, ga Ɗan Rago na Allah, wanda zai ɗauke zunubin duniya! 30 Wannan shi ne wanda na ce, ‘Wani yana zuwa bayana, wanda ya zama shugabana, domin dā ma yana nan tun ba ni.’ 31 Dā kam, ban san shi ba, sai domin a bayyana shi ga Isra'ila na zo, nake baftisma da ruwa.” 32 Yahaya ya yi shaida ya ce, “Na ga Ruhu na saukowa kamar kurciya daga sama, ya kasance a kansa. 33 Dā kam, ban san shi ba, shi dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa, shi ne ya ce mini, ‘Wanda ka ga Ruhun na sauko masa, yana kuma kasance a kansa, shi ne mai yin baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’ 34 Na kuwa gani, na kuma yi shaida, cewa, wannan Ɗan Allah ne.”

Almajiran Yesu na Farko

35 Kashegari kuma Yahaya na tsaye da almajiransa biyu. 36 Yana duban Yesu na tafiya, sai ya ce, “Kun ga, ga Ɗan Rago na Allah!” 37 Almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suke bi Yesu. 38 Yesu ya waiwaya ya ga suna biye da shi, sai ya ce musu, “Me kuke nema?” Suka ce masa, “Ya Rabbi, wato, Malam ke nan, ina kake da zama?” 39 Sai ya ce musu, “Ku zo ku gani.” Sai suka je suka ga inda yake da zama, suka kuwa yini tare da shi. Wajen ƙarfe huɗu na yamma ne kuwa. 40 Ɗaya daga cikin biyun nan da suka ji maganar Yahaya suka kuma bi Yesu, Andarawas ne, ɗan'uwan Bitrus. 41 Sai ya fara nemo ɗan'uwansa Bitrus, ya ce masa, “Mun sami Almasihu,” wato, shafaffe. 42 Sai ya kai shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi, ya ce, “Wato, kai ne Saminu ɗan Yahaya? Za a kira ka Kefas,” wato, Bitrus.

Yesu ya Kira Filibus da Nata'ala

43 Kashegari Yesu ya yi niyyar zuwa ƙasar Galili. Sai ya sami Filibus, ya ce masa, “Bi ni.” 44 Filibus kuwa mutumin Betsaida ne, garin su Andarawas da Bitrus. 45 Filibus ya sami Nata'ala, ya ce masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta labarinsa a Attaura, annabawa kuma suka rubuta labarinsa, wato, Yesu Banazare, ɗan Yusufu.” 46 Nata'ala ya ce masa, “A iya samun wani abin kirki a Nazarat kuwa?” Sai Filibus ya ce masa, “Taho dai, ka gani.” 47 Yesu ya ga Nata'ala na nufo shi, sai ya yi zancensa ya ce, “Kun ga, ga Ba'isra'ile na gaske wanda ba shi da ha'inci!” 48 Nata'ala ya ce masa, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa masa ya ce, “Tun kafin Filibus ya kira ka, sa'ad da kake gindin ɓaure, na gan ka.” 49 Sai Nata'ala ya amsa masa ya ce, “Ya Shugaba, kai Ɗan Allah ne! Kai Sarkin Isra'ila ne!” 50 Yesu ya amsa ya ce, “Wato, domin na ce maka na gan ka a gindin ɓaure ne kake ba da gaskiya? Ai, za ka ga al'amuran da suka fi haka ma.” 51 Yesu kuma ya ce masa, “Lalle hakika, ina gaya muku, za ku ga sama ta dāre, mala'ikun Allah suna hawa da sauka ga Ɗan Mutum.”

Yahaya 2

Biki a Kana ta Galili

1 A rana ta uku sai aka yi bikin aure a Kana ta ƙasar Galili. Mahaifiyar Yesu kuwa tana nan, 2 aka kuma gayyaci Yesu da almajiransa. 3 Da ruwan inabi ya gaza, mahaifiyar Yesu ta ce masa, “Ba su da sauran ruwan inabi.” 4 Yesu ya ce mata, “Iya, ai, wannan magana ba taki ba ce. Lokacina bai yi ba tukuna.” 5 Sai mahaifiyar Yesu ta ce wa barorin, “Duk abin da ya ce ku yi, sai ku yi.” 6 A wurin kuwa akwai randuna shida na dutse a ajijjiye, bisa ga al'adar Yahudawa ta tsarkakewa, kowacce tana cin wajen tulu shida shida. 7 Sai Yesu ya ce musu, “Ku cika randunan nan da ruwa.” Suka ciccika su fal. 8 Sa'an nan ya ce musu, “To, yanzu ku ɗiba, ku kai wa uban bikin.” Sai suka kai. 9 Da uban bikin ya kurɓi ruwan da yanzu aka mayar ruwan inabi, bai kuwa san inda aka samo shi ba (amma barorin da suka ɗebo ruwan sun sani), ya yi magana da ango, 10 ya ce, “Kowa, ai, kyakkyawan ruwan inabi yakan fara bayarwa, bayan mutane sun shassha, sa'an nan kuma ya kawo wanda ya gaza na farin kyau. Amma kai ka ɓoye kyakkyawan ruwan inabin sai yanzu!” 11 Wannan ce mu'ujizar farko da Yesu ya yi, ya kuwa yi ta ne a Kana ta ƙasar Galili, ya bayyana ɗaukakarsa. Almajiransa kuma suka gaskata da shi. 12 Bayan haka sai ya tafi Kafarnahum, da shi da mahaifiyarsa, da 'yan'uwansa, da kuma almajiransa, suka zauna a can 'yan kwanaki.

Yesu ya Tsabtace Haikali

13 Idin Ƙetarewa na Yahudawa ya matso, sai Yesu ya tafi Urushalima. 14 A cikin Haikali ya sami waɗansu dillalan shanu, da na tumaki, da na tattabarai, da kuma 'yan canjin kuɗi zaune wurin aikinsu. 15 Sai ya tufka bulala mai harsuna ta igiya, ya kore su duka daga Haikalin, har da tumakin da shanun, ya kuma watsar da kuɗin 'yan canjin, ya birkice teburorinsu. 16 Ya ce da dillalan tattabarai, “Ku kwashe waɗannan daga nan, kada ku mai da Haikalin Ubana kasuwa.” 17 Sai almajiransa suka tuna a rubuce yake cewa, “Kishin Haikalinka ya ci raina matuƙa.” 18 Sai Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Wace mu'ujiza za ka nuna mana da kake haka?” 19 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ku rushe Haikalin nan, ni kuwa in ta da shi a cikin kwana uku.” 20 Yahudawa suka ce, “Sai fa da aka shekara arba'in da shida ana ginin Haikalin nan, kai kuwa a cikin kwana uku za ka ta da shi?” 21 Amma haikalin da Yesu ya ambata jikinsa ne. 22 Saboda haka bayan an tashe shi daga matattu, almajiransa suka tuna ya faɗi haka, suka kuma gaskata Nassi da maganar da Yesu ya faɗa.

Yesu ya San Zuciyar Kowa

23 To, sa'ad da yake Urushalima lokacin Idin Ƙetarewa, mutane da yawa suka gaskata da sunansa, saboda ganin mu'ujizan da ya yi. 24 Yesu bai amince da su ba, 25 domin ya san zuciyar kowa, ba kuma sai wani ya shaidi mutum a wurinsa ba, domin shi kansa ya san abin da yake zuciyar ɗan adam.

Yahaya 3

Yesu da Nikodimu

1 To, akwai wani Bafarisiye, sunansa Nikodimu, wani shugaban Yahudawa. 2 Wannan mutum ya zo wurin Yesu da dad dare, ya ce masa, “Ya Shugaba, mun sani kai malami ne da ka zo daga wurin Allah, domin ba mai iya yin waɗannan mu'ujizan da kake yi, sai ko Allah yana tare da shi.” 3 Yesu ya amsa masa ya ce, “Lalle hakika, ina gaya maka, in ba a sāke haifar mutum ba, ba zai iya ganin Mulkin Allah ba.” 4 Nikodimu ya ce masa, “Ƙaƙa za a haifi mutum bayan ya tsufa? Wato, ya iya komawa a cikin mahaifiyarsa ta sāke haifo shi?” 5 Yesu ya amsa masa ya ce, “Lalle hakika, ina gaya maka, in ba an haifi mutum ta wurin ruwa da kuma Ruhu ba, ba zai iya shiga Mulkin Allah ba. 6 Abin da mutum ya haifa mutum ne, abin kuma da Ruhu ya haifa ruhu ne. 7 Kada ka yi mamaki domin na ce maka, ‘Dole a sāke haifarku.’ 8 Iska tana busawa inda ta ga dama. Kakan ji motsinta, amma ba ka san inda ta fito da inda za ta ba. Haka fa yake ga duk wanda Ruhu ya haifa.” 9 Sai Nikodimu ya amsa masa ya ce, “Ƙaƙa wannan zai yiwu?” 10 Yesu ya amsa masa ya ce, “Ashe, kai ma da kake malamin Isra'ila, ba ka fahimci waɗannan al'amura ba? 11 Lalle hakika, ina gaya maka, abin da muka sani shi muke faɗa, muna kuma shaidar da abin da muka gani, amma kun ƙi yarda da shaidarmu. 12 In na yi muku zancen al'amuran duniya ba ku gaskata ba, yaya za ku gaskata in na yi muku zancen al'amuran sama? 13 Ba wanda ya taɓa hawa cikin Sama sai shi wanda ya sauko daga Sama, wato, Ɗan Mutum (da yake Sama). 14 Kamar yadda Musa ya ɗaga macijin nan a jeji, haka kuma dole ne a ɗaga Ɗan Mutum, 15 domin duk wanda ya gaskata da shi, ya sami rai madawwami. 16 “Saboda ƙaunar da Allah ya yi wa duniya har ya ba da makaɗaicin Ɗansa, domin duk wanda ya gaskata da shi kada ya hallaka, sai dai ya sami rai madawwami. 17 Gama Allah bai aiko Ɗansa duniya domin yă yanke mata hukunci ba, sai dai domin duniya ta sami ceto ta wurinsa. 18 Duk wanda ya gaskata da shi, ba za a yi masa hukunci ba. Wanda kuwa bai ba da gaskiya ba, an riga an yi masa hukunci, domin bai gaskata da sunan makaɗaicin Ɗan Allah ba. 19 Hukuncin kuwa shi ne, haske ya shigo duniya, amma mutane suka fi ƙaunar duhu da hasken, don ayyukansu mugaye ne. 20 Duk mai yin rashin gaskiya yakan ƙi hasken, ba ya kuma zuwa wajen hasken, don kada ayyukansa su tonu. 21 Mai aikata gaskiya kuwa yakan zo wajen hasken, domin a bayyana ayyukansa, cewa, da taimakon Allah ne aka yi su.”

Shi lalle ya Riƙa Ƙaruwa, ni kuwa Raguwa

22 Bayan haka, Yesu da almajiransa suka tafi ƙasar Yahudiya. A nan ya jima da su, yana yin baftisma. 23 Yahaya kuma yana yin baftisma a Ainon kusa da Salima, domin da ruwa da yawa a can. Mutane kuwa suka yi ta zuwa ana yi musu baftisma. 24 Domin a sa'an nan ba a sa Yahaya a kurkuku ba tukuna. 25 Sai fa almajiran Yahaya suka tasar wa wani Bayahude da muhawwara a kan maganar tsarkakewa. 26 Suka kuma zo wurin Yahaya, suka ce masa, “Ya shugaba, wanda dā kuke tare a hayin Kogin Urdun, wanda kai kanka ma ka shaida shi, to, ga shi, yana yin baftisma, har kowa da kowa yana zuwa wurinsa.” 27 Sai Yahaya ya amsa ya ce, “Ba mai iya samun kome sai ko an ba shi daga Sama. 28 Ku kanku ma shaiduna ne a kan na ce ba ni ne Almasihu ba, amma an aiko ni ne ni riga shi gaba. 29 Mai amarya shi ne ango. Abokin ango kuwa da yake tsaye, yake kuma sauraron maganarsa, yakan yi farin ciki ƙwarai da jin muryar angon. Saboda haka farin cikin nan nawa ya cika. 30 Shi kam, lalle ne ya riƙa ƙaruwa, ni kuwa in riƙa raguwa.

Wanda ya Zo daga Sama

31 “Mai zuwa daga Sama yana Sama da kowa. Wanda yake na ƙasa asalinsa kuwa na ƙasa ne, maganar ƙasa kuma yake yi. Mai zuwan nan daga Sama yana Sama da kowa. 32 Abin da ya ji, ya kuma gani, shi yake shaidarwa, duk da haka ba wanda yake yarda da shaidarsa. 33 Duk wanda ya yarda da shaidarsa, ya haƙƙaƙe, cewa, Allah mai gaskiya ne. 34 Domin wanda Allah ya aiko, zantuttukan Allah yake faɗa, gama Allah yana ba da Ruhu ba da iyakancewa ba. 35 Uban yana ƙaunar Ɗan, ya kuma sa kome a hannunsa. 36 Wanda ya gaskata da Ɗan, yana da rai madawwami. Wanda ya ƙi bin Ɗan kuwa, ba zai sami rai ba, sai dai fushin Allah ya tabbata a gare shi.”

Yahaya 4

Yesu da wata Basamariya

1 To, da Ubangiji Yesu ya sani dai Farisiyawa sun ji labari yana samun almajirai, yana kuma yi musu baftisma fiye da Yahaya 2 (ko da yake dai ba Yesu kansa yake yin baftisma ba, almajiransa ne), 3 sai ya bar ƙasar Yahudiya, ya koma ƙasar Galili. 4 Lalle ne kuwa yă ratsa ƙasar Samariya. 5 Sai ya zo wani gari na ƙasar Samariya, wanda ake kira Saikar, kusa da yankin ƙasar da Yakubu ya ba ɗansa Yusufu. 6 Rijiyar Yakubu kuwa a nan take. Saboda gajiyar tafiya fa, sai Yesu ya zauna haka nan a bakin rijiyar. Wajen tsakar rana ce kuwa. 7 Sai ga wata Basamariya ta zo ɗiban ruwa. Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.” 8 Almajiransa kuwa sun shiga gari sayen abinci. 9 Sai Basamariyar ta ce masa, “Ƙaƙa kai Bayahude za ka roƙe ni ruwan sha, ni da nake Basamariya?” (Don Yahudawa ba sa cuɗanya da Samariyawa). 10 Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda ya ce miki, ‘Ba ni ruwa in sha,’ ai, da kin roƙe shi, shi kuwa zai ba ki ruwan rai.” 11 Sai matar ta ce masa, “Ya Shugaba, ai, ba ka da guga, rijiyar kuwa da zurfi. To, ina ka sami ruwan nan na rai? 12 Ashe, ka fi ubanmu Yakubu ne, wanda ya bar mana rijiyar, har shi da kansa, da 'yayansa, da dabbobinsa, suka sha ruwanta?” 13 Yesu ya amsa mata ya ce, “Duk mai shan ruwan nan zai sāke jin ƙishirwa. 14 Amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba har abada. Ruwan da zan ba shi kuwa zai zama maɓuɓɓuga a gare shi, yana ɓuɓɓugowa har ya zuwa rai madawwami.” 15 Macen ta ce masa, “Ya Shugaba, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, kada kuma in riƙa zuwa har nan in ɗiba.” 16 Sai Yesu ya ce mata, “Je ki, ku zo da mijinki.” 17 Sai macen ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji, 18 don kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.” 19 Macen ta ce masa, “Ya Shugaba, na dai gane kai annabi ne. 20 Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan. Ku kuwa kun ce a Urushalima ne wurin da ya wajaba a yi sujada.” 21 Sai Yesu ya ce da ita, “Mace, ki gaskata ni, lokaci na zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ba, ko a kan dutsen nan, ko a Urushalima, 22 Ku kuna yi wa abin da ba ku sani ba sujada, mu kuwa muna yi wa abin da muka sani sujada, domin ceto ta hanyar Yahudawa yake. 23 Amma lokaci na zuwa, har ma ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a ruhu, da gaskiya kuma. Lalle kuwa irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema. 24 Allah Ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa lalle su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.” 25 Sai macen ta ce masa, “Na san Almasihu yana zuwa, (wanda ake kira Kristi). Sa'ad da ya zo kuwa, zai sanar da mu kome.” 26 Yesu ya ce mata, “Ni ne, ni mai maganar nan da ke.” 27 Ya gama magana ke nan sai almajiransa suka iso. Suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma kuwa ba wanda ya ce, “Me kike bukata?” ko, “Don me kake magana da ita?” 28 Sai matar ta bar tulunta, ta koma gari, ta ce wa mutane, 29 “Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi! Shin, ko wannan shi ne Almasihu?” 30 Sai suka fito daga garin suka nufo shi. 31 Ana cikin haka sai almajiran suka roƙe shi suka ce, “Malam, ci abinci.” 32 Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku sani ba.” 33 Almajiran suka ce wa juna, “Shin, wani ya kawo masa abinci ne?” 34 Sai Yesu ya ce musu, “Abincina shi ne in aikata nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa. 35 Ba kuna cewa, kaka saura wata huɗu ba? Ina gaya muku fa, ku duba gonaki, ku gani, sun nuna sun isa girbi. 36 Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. 37 A nan kam, wannan karin maganar gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani da girbi.’ 38 Na aike ku girbin abin da ba ku yi wahalarsa ba. Waɗansu sun yi wahala, ku kuwa kun mori wahalarsu.” 39 Samariyawa da yawa na wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen nan da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.” 40 Da samariyawa suka iso wurinsa, suka roƙe shi ya sauka a wurinsu. Ya kuwa kwana biyu a nan. 41 Saboda maganarsa kuma waɗansu da yawa suka gaskata. 42 Sa'an nan suka ce wa macen, “Yanzu kam, mun ba da gaskiya, ba don abin da kika faɗa kawai ba, domin mu ma mun ji da kanmu, mun kuma tabbata lalle wannan shi ne Mai Ceton duniya.”

Yesu ya Warkar da Ɗan Basarake

43 Bayan kwana biyun nan sai ya tashi daga nan ya tafi ƙasar Galili. 44 Domin Yesu kansa ya yi shaida cewa, annabi ba shi da girma a garinsu. 45 Da ya isa ƙasar Galili, sai Galilawa suka yi na'am da shi, domin sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin idi, domin su ma sun je idin. 46 Sai ya sāke zuwa Kana ta ƙasar Galili, inda ya mai da ruwa ruwan inabi. A Kafarnahum kuwa akwai wani basarake wanda ɗansa ba shi da lafiya. 47 Da jin cewa, Yesu ya fito ƙasar Yahudiya ya komo ƙasar Galili, sai ya tafi wurinsa, ya roƙe shi ya je ya warkar da ɗansa, don yana bakin mutuwa. 48 Yesu ya ce masa, “In ba mu'ujizai da abubuwan al'ajabi kuka gani ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.” 49 Sai basaraken nan ya ce masa, “Ya Shugaba, ka zo tun ƙaramin ɗana bai mutu ba.” 50 Yesu ya ce masa, “Yi tafiyarka, ɗanka a raye yake.” Mutumin kuwa ya gaskata maganar da Yesu ya faɗa masa, ya yi tafiyarsa. 51 Yana cikin tafiya sai ga barorinsa sun taryo shi, suka ce masa, “Ɗanka ya warke.” 52 Sai ya tambaye su ainihin lokacin da ya fara samun sauƙi. Suka ce masa, “Jiya da ƙarfe ɗaya da rana zazzaɓin ya sake shi.” 53 Sai uban ya gane, daidai lokacin nan ne, Yesu ya ce masa, “Ɗanka a raye yake.” Shi da kansa kuwa ya ba da gaskiya, da jama'ar gidansa duka. 54 Wannan kuwa ita ce mu'ujiza ta biyu da Yesu ya yi a Galili, bayan komowarsa daga Yahudiya.

Yahaya 5

Warkarwa a Tafkin Betasda

1 Bayan haka sai Yesu ya tafi Urushalima domin idin Yahudawa. 2 A Urushalima, kusa da Ƙofar Tumaki, akwai wani ruwa da ake ce da shi Betasda da Yahudanci, an kuwa kewaye shi da shirayi biyar. 3 A shirayin nan kuwa marasa lafiya da yawa sun saba kwanciya, makafi, da guragu, da shanyayyu.Suna jira a motsa ruwan. 4 Don lokaci lokaci wani mala'ika yakan sauko cikin ruwan ya motsa shi. Duk kuwa wanda ya fara shiga bayan an motsa ruwan, sai ya warke daga duk irin cutar da yake da ita. 5 A nan kuwa akwai wani mutum da ya shekara talatin da takwas da rashin lafiya. 6 Da Yesu ya gan shi kwance, ya kuma sani ya daɗe da wannan hali, sai ya ce masa, “Kana so a warkar da kai?” 7 Marar lafiyar ya amsa masa ya ce, “Ya Shugaba, ai, ba ni da wanda zai saka ni cikin ruwan lokacin da aka motsa shi. Lokacin da na doshi ruwan kuma sai wani ya riga ni shiga.” 8 Sai Yesu ya ce masa, “Tashi, ka ɗauki shimfiɗarka, ka tafi!” 9 Nan take mutumin ya warke, ya ɗauki shimfiɗarsa ya yi tafiyarsa. Ran nan kuwa Asabar ce. 10 Saboda haka Yahudawa suka ce da wanda aka warkar ɗin, “Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka ɗauki shimfiɗarka ba.” 11 Sai ya amsa musu ya ce, “Ai, wanda ya warkar da ni, shi ne ya ce in ɗauki shimfiɗata, in tafi.” 12 Suka tambaye shi, “Wanne mutum ne ya ce maka ka ɗauki shimfiɗarka ka tafi?” 13 Wanda aka warkar ɗin kuwa bai san ko wane ne ba, domin Yesu ya riga ya tashi saboda taron da suke wurin. 14 Bayan haka Yesu ya same shi a Haikali, ya ce masa, “Ka ga fa, ka warke! To, ka daina yin zunubi, don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka.” 15 Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahudawa, Yesu ne ya warkar da shi. 16 Saboda haka, Yahudawa suka fara tsananta wa Yesu, don yana yin irin waɗannan abubuwa ran Asabar. 17 Yesu kuwa ya amsa musu ya ce, “Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina yi.” 18 Don haka, Yahudawa suka ƙara nema su kashe shi, ba don ya keta Asabar kaɗai ba, har ma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato, yana daidaita kansa da Allah.

Ikon Ɗan

19 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku, Ɗan ba ya yin kome shi kaɗai, sai abin da ya ga Uba yana yi. Domin duk abin da Uban yake yi, haka shi Ɗan ma yake yi. 20 Domin Uban na ƙaunar Ɗan, yana kuma nuna masa duk abin da shi kansa yake yi, har ma zai nuna masa ayyukan da suka fi waɗannan, domin ku yi al'ajabi. 21 Yadda Uba yake ta da matattu ya kuma raya su, haka Ɗan ma yake rayar da wanda ya nufa. 22 Uba ba ya hukunta kowa, sai dai yā danƙa dukkan hukunci ga Ɗan, 23 domin kowa yă girmama Ɗan, kamar yadda ake girmama Uban. Wanda ba ya girmama Ɗan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi ke nan. 24 Lalle hakika, ina gaya muku, duk mai jin maganata, yake kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami. Ba za a yi masa hukunci ba, domin ya riga ya tsere wa mutuwa, ya kai ga rai. 25 “Lalle hakika, ina gaya muku, lokaci yana zuwa, har ma ya yi, da matattu za su ji muryar Ɗan Allah, masu ji kuwa su rayu. 26 Yadda Uba kansa yake tushen rai, haka ya sa Ɗan ya zama tushen rai. 27 Ya kuma ba shi ikon zartar da hukunci, saboda shi Ɗan Mutum ne. 28 Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci yana zuwa da duk waɗanda suke kaburbura za su ji muryarsa, 29 su kuma fito, waɗanda suka aikata nagarta su tashi, tashin rai, waɗanda suka yi rashin gaskiya kuwa su tashi, tashin hukunci.

Shaidun Yesu

30 “Ba na iya yin kome ni kaɗai. Yadda nake ji, haka nake yin hukunci. Hukuncina kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 31 In na shaida kaina, shaidata ba tabbatacciya ba ce. 32 Akwai wani mashaidina dabam, na kuwa san shaidar da yake yi a kaina tabbatacciya ce. 33 Kun aika wajen Yahaya, shi kuma ya shaidi gaskiya. 34 Duk da haka shaidar da na dogara da ita ba ta mutum ba ce. Na dai faɗi haka ne domin ku sami ceto. 35 Yahaya fitila ne mai ci, mai haske kuma, kun kuwa yarda ku yi farin ciki matuƙa da haskensa ɗan lokaci kaɗan. 36 Amma shaidar da ni nake da ita ta fi ta Yahaya ƙarfi. Domin ayyukan da Uba ya ba ni in gama, su ainihin ayyukan nan da nake yi, ai, su ne shaidata a kan cewa, Uba ne ya aiko ni. 37 Uban kuma da ya aiko ni, shi kansa ya shaide ni. Ba ku taɓa jin muryarsa ba, ko ganin kama tasa. 38 Maganarsa kuwa ba ta zauna a zuciyarku ba, domin ba ku gaskata wanda ya aiko ba. 39 Kuna ta nazarin Littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. 40 Duk da haka, kun ƙi zuwa wurina ku sami rai. 41 Ba na karɓar girma wurin mutane. 42 Amma fa na san ku, ba ku da ƙaunar Allah a zuci. 43 Ni na zo ne da sunan Ubana, ga shi, ba ku karɓe ni ba. In da wani zai zo da sunan kansa, shi za ku karɓa. 44 Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karɓar girma a junanku, girman da yake daga Allah Makaɗaici kuwa, ba kwa nemansa? 45 Kada ku zaci zan yi ƙararku wurin Uba. Akwai mai yin ƙararku, shi ne Musa, wanda kuke dogara da shi. 46 Da dai kun gaskata Musa, da kun gaskata ni, domin labarina ya rubuta. 47 In kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?”

Yahaya 6

Ciyar da Mutum Dubu Biyar

1 Bayan haka Yesu ya haye Tekun Galili, wato, Tekun Tibariya. 2 Sai taro mai yawa suka bi shi, don sun ga mu'ujizan da yake yi ga marasa lafiya. 3 Sai Yesu ya hau dutse ya zauna a can tare da almajiransa. 4 To, Idin Ƙetarewa wato, idin Yahudawa, ya gabato. 5 Da Yesu ya ɗaga kai ya hango babban taro yana doso shi, sai ya ce wa Filibus, “Ina za mu sayo gurasar da mutanen nan za su ci?” 6 Ya faɗi haka ne fa domin ya gwada shi, saboda shi kansa ya san abin da zai yi. 7 Filibus ya amsa ya ce, “Ai, ko gurasar dinari metan ma ba ta isa ko wannensu ya sami kaɗan ba.” 8 Sai Andarawas ɗan'uwan Bitrus ɗaya daga cikin almajiransa, ya ce masa, 9 “Ga wani ɗan yaro nan da gurasa biyar na sha'ir, da kuma kifi biyu. Amma me waɗannan za su yi wa mutane masu yawa haka?” 10 Yesu ya ce, “Ku ce wa mutane su zauna.” Wuri ne kuwa mai ciyawa. Sai mazaje suka zazzauna, su wajen dubu biyar. 11 Yesu ya ɗauki gurasar, bayan ya yi godiya ga Allah kuma, sai ya rarraba wa waɗanda suke zazzaune. Haka kuma ya yi da kifin, gwargwadon abin da ya ishe su. 12 Da suka ci suka ƙoshi, sai ya ce wa almajiransa, “Ku tattara gutsattsarin da suka saura, kada kome ya lalace.” 13 Sai suka tattara gutsattsarin gurasar nan biyar na sha'ir da suka saura bayan kowa ya ci, suka cika kwando goma sha biyu. 14 Da jama'a suka ga mu'ujizar da ya yi, suka ce, “Lalle, wannan shi ne annabin nan mai zuwa duniya!” 15 Da Yesu ya gane suna shirin zuwa su ɗauke shi ƙarfi da yayi su naɗa shi sarki, sai ya sāke komawa a kan dutsen shi kaɗai.

Yesu na Tafiya a kan Ruwan Teku

16 Da magariba ta yi, sai almajiransa suka gangara zuwa teku. 17 Suka shiga jirgi suka tasar wa haye tekun zuwa Kafarnahun. A sa'an nan duhu ya yi, Yesu kuwa bai zo wurinsu ba tukuna. 18 Sai tekun ta fara hauka saboda wata riƙaƙƙiyar iska da take busowa. 19 Bayan sun yi tuƙi wajen mil uku ko huɗu, sai suka hango Yesu yana tafiya a kan ruwan, ya kusato jirgin. Sai suka firgita. 20 Amma ya ce musu, “Ni ne, kada ku ji tsoro.” 21 Sa'an nan suka yarda suka karɓe shi a cikin jirgin. Nan da nan sai ga jirgin a gāɓar da za su.

Taro sun Nemi Yesu

22 Kashegari sauran taron da suka tsaya a hayin tekun suka lura ba wani jirgi a wurin, sai ɗan ƙarami, suka kuma lura Yesu bai shiga cikinsa tare da almajiransa ba, sai almajiran ne kaɗai suka tafi. 23 Akwai kuwa waɗansu ƙananan jirage daga Tibariya da suka iso kusa da wurin nan da taron suka ci gurasa bayan Ubangiji ya yi godiya. 24 Sa'ad da kuwa taron suka ga ba Yesu, ba almajiransa a nan, su ma suka shiga ƙananan jiragen, suka tafi Kafarnahum neman Yesu.

Yesu Gurasar Rai

25 Da suka same shi a hayin tekun, suka ce masa, “Ya Shugaba, yaushe ka zo nan?” 26 Yesu ya amsa musu ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku, kuna nemana ne ba don kun ga mu'ujizai ba, sai don kun ci gurasar nan kun ƙoshi. 27 Kada ku yi wahala a kan neman abinci mai lalacewa, sai dai a kan abinci mai dawwama har ya zuwa rai madawwami, wanda Ɗan Mutum zai ba ku. Domin shi ne wanda Uba, wato, Allah, ya tabbatar wa da ikon yin haka.” 28 Sai suka ce masa, “Me za mu yi mu aikata ayyukan da Allah yake so?” 29 Yesu ya amsa musu ya ce, “Wannan shi ne aikin da Allah yake so, wato, ku gaskata da wanda ya aiko.” 30 Sai suka ce masa, “To, wace mu'ujiza za ka yi mu gani mu gaskata ka? Me za ka yi? 31 Kakannin kakanninmu sun ci manna a jeji, yadda yake a rubuce cewa, ‘Ya ba su gurasa daga Sama su ci.’ ” 32 Sa'an nan Yesu ya ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, ba Musa ne ya ba ku gurasar nan daga Sama ba, Ubana ne yake ba ku hakikanin Gurasa daga Sama. 33 Ai, Gurasar Allah shi ne mai saukowa daga Sama, mai ba duniya rai.” 34 Sai suka ce masa, “Ya Ubangiji, ka riƙa ba mu irin wannan gurasa kullum!” 35 Yesu ya ce musu, “Ni ne gurasa mai ba da rai. Wanda ya zo gare ni ba zai ji yunwa ba har abada, wanda kuma ya gaskata da ni ba zai ƙara jin ƙishirwa ba har abada. 36 Na dai gaya muku, kun gan ni, duk da haka ba ku ba da gaskiya ba. 37 Duk wanda Uba ya ba ni zai zo gare ni, wanda kuwa ya zo gare ni ba zan kore shi ba ko kaɗan. 38 Domin na sauko daga Sama, ba domin in bi nufin kaina ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni. 39 Nufin wanda ya aiko ni kuwa, shi ne kada in yar da kowa daga cikin dukkan waɗanda ya ba ni, sai dai in tashe su a ranar ƙarshe. 40 Gama nufin Ubana, shi ne duk wanda yake duban Ɗan, yake kuma gaskatawa da shi, yă sami rai madawwani, ni kuma zan tashe shi a ranar ƙarshe.” 41 Sai fa Yahudawa suka yi masa gunaguni, domin ya ce, “Ni ne Gurasar da ya sauko daga Sama.” 42 Suka ce, “Ashe, wannan ba Yesu ba ne, ɗan Yusufu, wanda mahaifiyarsa da mahaifinsa duk mun san su? To, yaya yanzu zai ce, ‘Na sauko ne daga sama?’ ” 43 Yesu ya amsa musu ya ce, “Kada ku yi gunaguni a junanku. 44 Ba mai iya zuwa wurina, sai dai in Uba wanda ya aiko ni ne ya jawo shi, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe. 45 A rubuce yake cikin littafan annabawa cewa, ‘Dukkansu Allah ne zai koya musu.’ To, duk wanda ya ji, ya kuma koya wurin Uba, zai zo gare ni. 46 Ba wanda ya taɓa ganin Uban, sai shi wanda yake daga wurin Allah, shi ne ya ga Uban. 47 Lalle hakika ina gaya muku, wanda ya ba da gaskiya, yana da rai madawwami. 48 Ni ne Gurasa mai ba da rai. 49 Kakannin kakanninku sun ci manna a jeji, amma kuwa sun mutu. 50 Ga Gurasa mai saukowa daga Sama, domin kowa yă ci, kada ya mutu. 51 Ni ne Gurasar rai da ya sauko daga Sama. Kowa ya ci Gurasan nan, zai rayu har abada. Har ma gurasar da zan bayar naman jikina ne, domin duniya ta rayu.” 52 Sai Yahudawa suka ta da husuma a junansu, suna cewa, “Yaya mutumin nan zai iya ba mu naman jikinsa mu ci?” 53 Sai Yesu ya ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, in ba ku ci naman jikin Ɗan Mutum ba, kuka kuma sha jininsa, ba rai a gare ku. 54 Duk wanda yake cin naman jikina, yake kuma shan jinina, yana da rai madawwami, ni kuwa zan tashe shi a ranar ƙarshe. 55 Domin naman jikina abinci ne na hakika, jinina kuma abin sha ne na hakika. 56 Duk wanda yake cin naman jikina, yake shan jinina, a cikina yake zaune, ni kuma a cikinsa. 57 Kamar yadda rayayyen Uba ya aiko ni, nake kuma rayuwa saboda Uban, haka ma wanda yake ni ne abincinsa zai rayu saboda ni. 58 Wannan shi ne Gurasar da ya sauko daga Sama, ba irin wadda kakannin kakanninku suka ci ba, duk da haka suka mutu. Duk mai cin Gurasan nan zai rayu har abada.” 59 Wannan kuwa a majami'a ya faɗa, sa'ad da yake koyarwa a Kafarnahum.

Kalmomin Rai

60 Da jin haka, da yawa daga cikin almajiransa suka ce, “Wannan magana mai wuya ce, wa zai iya jinta?” 61 Yesu kuwa, da yake ya sani a ransa almajiransa suna gunagunin wannan, sai ya ce musu, “Wato, wannan ne ya zamar muku abin tuntuɓe? 62 Yaya ke nan in kuka ga Ɗan Mutum yana hawa inda yake dā? 63 Ai, Ruhu shi ne mai rayarwa, jiki kam ba ya amfana kome. Kalmomin da na faɗa muku ruhu ne, da kuma rai. 64 Amma fa akwai waɗansunku da ba su ba da gaskiya ba.” Domin tun farko Yesu ya san waɗanda ba su ba da gaskiya ba, da kuma wanda zai bāshe shi. 65 Sai ya ƙara da cewa, “Shi ya sa na gaya muku, ba mai iya zuwa gare ni, sai ko Uba ya yardar masa.” 66 Kan wannan da yawa daga cikin almajiransa suka koma da baya, ba su ƙara tafiya tare da shi ba. 67 Sai Yesu ya ce wa goma sha biyun, “Ku ma kuna so ku tafi ne?” 68 Bitrus ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangiji, gun wa za mu je? Kai kake da maganar rai madawwami. 69 Mu kuwa mun gaskata, mun kuma tabbata kai ne Mai Tsarkin nan na Allah.” 70 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba ni na zaɓe ku, ku goma sha biyu ba? To, ɗayanku Iblis ne.” 71 Wato, yana nufin Yahuza, ɗan Saminu Iskariyoti, don shi ne zai bāshe shi, ko da yake ɗaya daga cikin goma sha biyun nan ne.

Yahaya 7

'Yan'uwan Yesu ba su Gaskata da shi Ba

1 Bayan haka, Yesu ya riƙa zagawa a Ƙasar Galili, bai yarda ya zaga ta Yahudiya ba, don Yahudawa suna neman kashe shi. 2 Idin Bukkoki na Yahudawa kuwa ya gabato. 3 Sai 'yan'uwansa suka ce masa, “Tashi daga nan mana ka tafi ƙasar Yahudiya, almajiranka su ma su ga ayyukan da kake yi. 4 Ai, ba mai aiki a ɓoye in yana so ya shahara. Tun da yake kana yin waɗannan al'amura, to, sai ka bayyana kanka ga duniya.” 5 Domin ko dā ma 'yan'uwansa ba su gaskata da shi ba. 6 Sai Yesu ya ce musu, “Lokacina bai yi ba tukuna, amma ku, koyaushe lokacinku ne. 7 Ba dama duniya ta ƙi ku, amma ni take ƙi, don na shaide ta a kan ayyukanta mugaye ne. 8 Ku dai ku tafi idin. Ni ba za ni ba yanzu, don lokacina bai yi sosai ba tukuna.” 9 Da ya faɗa musu haka, ya dakata a ƙasar Galili.

Yesu a Idin Bukkoki

10 Bayan 'yan'uwansa sun tafi idin kuwa, shi ma ya tafi, amma a ɓoye, ba a fili ba. 11 Yahudawa suna ta nemansa a wurin idin suna cewa, “Ina yake ne?” 12 Taro kuma suka riƙa maganarsa a raɗe, waɗansu suna cewa, “Mutum ne nagari.” Waɗansu kuma suna cewa, “A'a, ai, ɓad da jama'a yake.” 13 Amma ba wanda ya yi maganarsa a fili don tsoron Yahudawa. 14 Wajen tsakiyar idin sai Yesu ya shiga Haikali ya koyar. 15 Yahudawa suka yi mamakin abin, suka ce, “Yaya mutumin nan yake da karatu haka, ga shi kuwa, bai taɓa koyo ba?” 16 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Koyarwata ba tawa ba ce, ta wanda ya aiko ni ce. 17 Duk mai son aikata nufin Allah zai san koyarwar nan ko ta Allah ce, ko domin kaina nake faɗa. 18 Mai magana don kansa, neman ɗaukakar kansa yake yi. Amma mai neman ɗaukakar wanda ya aiko shi, shi ne mai gaskiya, ba kuwa rashin gaskiya a gare shi. 19 Ashe, ba Musa ne ya ba ku Shari'a ba? Duk da haka ba mai kiyaye Shari'ar a cikinku. Don me kuke neman kashe ni?” 20 Taron suka amsa suka ce, “Kana da iska! Wa yake neman kashe ka?” 21 Yesu ya amsa musu ya ce, “Aiki ɗaya kawai na yi, dukanku kuwa kuna mamakinsa. 22 Musa ya bar muku kaciya, (ba ko shi ya fara ba, tun kakannin kakanni ne), ga shi kuma, kukan yi wa mutum kaciya ko a ran Asabar ma. 23 To, in ana yi wa mutum kaciya ran Asabar don gudun keta Shari'ar Musa, kwa yi fushi don na warkar da mutum sarai ran Asabar? 24 Kada ku yi hukunci da zato, amma ku yi hukunci da adalci.” 7 .25 Wannan Almasihu Ne? Wannan Almasihu Ne? 25 Sai waɗansu mutanen Urushalima suka ce, “Ashe, ba wannan ne mutumin da suke nema su kashe ba? 26 Ga shi nan kuwa, yana magana a fili, ba su ce masa kome ba! Ya yiwu kuma shugabanni sun san lalle wannan shi ne Almasihu? 27 Wannan kam, mun san daga inda yake, amma sa'ad da Almasihu ya zo ba wanda zai san daga inda yake.” 28 Yesu yana koyarwa a Haikalin ke nan, sai ya ɗaga murya ya ce, “Kun dai san ni, kun kuma san daga inda nake. Ban fa zo domin kaina ba. Wanda ya aiko ni mai gaskiya ne, shi kuwa ba ku san shi ba. 29 Ni na san shi, domin daga wurinsa na fito, shi ne kuwa ya aiko ni.” 30 Don haka suka nema su kama shi, amma ba wanda ya taɓa shi, domin lokacinsa bai yi ba tukuna. 31 Duk da haka mutane da yawa cikin taron sun gaskata da shi, suna cewa, “Sa'ad da Almasihu ya zo, zai yi mu'ujizai fiye da na mutumin nan?”

An Aiki Dogaran Haikalin su Kamo Yesu

32 Farisiyawa suka ji taro suna raɗeraɗinsa haka, sai manyan firistoci da Farisiyawa suka aiki dogaran Haikali su kamo shi. 33 Sai Yesu ya ce, “Saurana ɗan lokaci kaɗan tare da ku, sa'an nan zan koma wurin wanda ya aiko ni. 34 Za ku neme ni, amma ba za ku same ni ba. Inda nake kuwa ba za ku iya zuwa ba.” 35 Sai Yahudawa suka ce wa juna, “Ina za shi da har ba za mu same shi ba? Za shi wurin Yahudawan da suka warwatsu a cikin al'ummai ne, ya koya wa al'umman? 36 Me kuma yake nufi da cewa, ‘Za ku neme ni amma ba za ku same ni ba?’ da kuma cewa, ‘Inda nake ba za ku iya zuwa ba?’ ”

Kogunan Ruwan Rai

37 A ranar ƙarshe ta idin, wato, babbar ranar, sai Yesu ya tsaya, ya ɗaga murya ya ce, “Duk mai jin ƙishirwa yă zo gare ni yă sha. 38 Duk mai gaskatawa da ni, kamar yadda nassi ya ce, ‘Daga zuciyarsa ne kogunan ruwan rai za su gudana.’ ” 39 To, wannan shi ne ya faɗa game da Ruhu, wanda masu gaskatawa da shi za su karɓa, domin har yanzu ba a ba da Ruhu ba, saboda ba a ɗaukaka Yesu ba tukuna.

Rabuwa ta Shiga Tsakanin Mutane

40 Da jin maganar nan waɗansu daga cikin taron suka ce, “Hakika wannan annabin nan ne.” 41 Waɗansu kuwa suka ce, “Wannan Almasihu ne.” Amma waɗansu suka ce, “Me? Ashe, Almasihu daga ƙasar Galili zai fito? 42 Nassi ba cewa, ya yi Almasihu zuriyar Dawuda ne ba, daga kuma Baitalami yake, ƙauyen da Dawuda ya zauna?” 43 Sai kuma rabuwa ta shiga tsakaninsu a kansa. 44 Waɗansunsu suka so su kama shi, amma ba wanda ya taɓa shi.

Shugabanni ba su Gaskata da Yesu Ba

45 Daga nan dogaran Haikali suka koma wurin manyan firistoci da Farisiyawa, su kuwa suka ce musu, “Don me ba ku kawo shi ba?” 46 Sai dogaran suka amsa suka ce, “A'a, ba mutumin da ya taɓa magana kamar wannan!” 47 Sai Farisiyawa suka amsa musu suka ce, “Af! Har ku ma an ɓad da ku ne? 48 Ashe, akwai wani daga cikin shugabanni ko Farisiyawa da ya gaskata da shi? 49 Amma wannan taro da ba su san Attaura ba, ai, la'anannu ne.” 50 Nikodimu kuwa da ya je wurinsa dā, yana kuwa ɗaya daga cikinsu, ya ce musu, 51 “Ashe, shari'armu takan hukunta mutum tun ba a ji daga bakinsa ba, an kuma san abin da yake ciki?” 52 Suka amsa masa suka ce, “Kai ma Bagalile ne? Bincika mana ka gani, ai, ba wani annabi da zai bayyana a ƙasar Galili.”

Matar da aka Kama da Zina

53 Sai kowa ya tafi gida.

Yahaya 8

1 Yesu kuwa ya hau Dutsen Zaitun. 2 Da sassafe kuma ya sāke shiga Haikali. Duk mutane suka zo wurinsa, ya kuwa zauna yana koya musu. 3 Sai malaman Attaura da Farisiyawa suka kawo wata mace da aka kama da zina. Da suka tsai da ita a tsaka, 4 suka ce masa, “Malam, matar nan an kama ta ne, suna cikin yin zina. 5 To, a Attaura Musa ya umarce mu mu kashe irin waɗannan da jifa, kai kuwa me ka ce?” 6 Sun faɗi haka ne don su gwada shi, ko sa sami hanyar kai ƙararsa. Amma Yesu ya sunkuya, ya yi ta rubutu a ƙasa da yatsa. 7 Da suka dinga tambayarsa sai ya ɗaga, ya ce musu, “To, marar zunubi a cikinku ya fara jifanta da dutse.” 8 Sai ya sāke sunkuyawa, ya yi ta rubutu a ƙasa. 9 Su kuwa da suka ji haka suka fita da ɗaya ɗaya, tun daga babbansu har ya zuwa ƙaraminsu, aka bar Yesu shi kaɗai, da matar a tsaye a wurin. 10 Sai Yesu ya ɗaga, ya ce mata, “Uwargida, ina suke? Ba wanda ya hukunta ki?” 11 Ta ce, “Babu, ya Ubangiji.” Sai Yesu ya ce, “Ni ma ban hukunta ki ba. Yi tafiyarki. Daga yau kada ki ƙara yin zunubi.”

Yesu Hasken Duniya

12 Sai Yesu ya ƙara musu da cewa, “Ni ne Hasken duniya. Wanda yake bi na ba zai yi tafiya a duhu ba, amma zai sami hasken rai,” 13 Saboda haka Farisiyawa suka ce masa, “Kanka kake wa shaida, shaidarka kuwa ba tabbatacciya ba ce.” 14 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ko na shaidi kaina, ai, shaidata tabbatacciya ce, domin na san inda na fito, da kuma inda za ni. Amma ku ba ku san inda na fito ba, ko kuma inda za ni. 15 Ku kuna hukunci irin na duniya ne, ni kuwa ba na hukunta kowa. 16 Amma ko da zan yi hukunci, hukuncina na gaskiya ne, domin ba ni kaɗai nake ba, ni da Uba wanda ya aiko ni ne. 17 A Attaurarku ma a rubuce yake, cewa, shaidar mutum biyu tabbatacciya ce. 18 Ni ne nake shaidar kaina, Uba da ya aiko ni kuma yana shaidata.” 19 Saboda haka suka ce masa, “Ina Uban naka yake?” Yesu ya amsa ya ce, “Ko ni ko Ubana, ba wanda kuka sani. Da kun san ni, da kun san Ubana ma.” 20 Ya faɗi wannan magana ne a baitulmalin Haikali, lokacin da yake koyarwa a wurin. Duk da haka ba wanda ya kama shi, don lokacinsa bai yi ba tukuna.

Inda za ni ba ku iya Zuwa Ba

21 Sai ya ƙara ce musu, “Zan yi tafiya, za ku kuwa neme ni, amma za ku mutu da zunubinku. Inda za ni kuwa ba za ku iya zuwa ba.” 22 Saboda haka sai Yahudawa suka ce, “Wato, zai kashe kansa ke nan da ya ce, ‘Inda za ni ba za ku iya zuwa ba?’ ” 23 Sai ya ce musu, “Ku daga ƙasa kuke, ni kuwa daga sama nake. Ku na duniyar nan ne, ni kuwa ba na duniyar nan ba ne. 24 Shi ya sa na ce muku za ku mutu da zunubanku. Domin in ba ku gaskata ni ne shi ba, za ku mutu da zunubanku.” 25 Sai suka ce masa, “Kai wane ne?” Yesu ya ce musu, “Daidai yadda na gaya muku. 26 Akwai abubuwa da yawa da zan faɗa game da ku, in kuma hukunta. Amma shi wannan da ya aiko ni mai gaskiya ne. Abin da na jiyo daga gare shi kuwa, shi nake shaida wa duniya.” 27 Ba su gane maganar Uba yake yi musu ba. 28 Sai Yesu ya ce, “Sa'ad da kuka ɗaga Ɗan Mutum, a sa'an nan ne za ku gane ni ne shi, ba na yin kome kuma ni kaɗai, sai dai Uba ya koya mini, haka nake faɗa. 29 Wanda kuwa ya aiko ni yana tare da ni, bai bar ni ni kaɗai ba, domin koyaushe ina aikata abin da yake so.” 30 Sa'ad da Yesu yake faɗar haka, mutane da yawa suka gaskata da shi.

Gaskiya za ta 'Yanta Ku

31 Sai Yesu ya ce wa Yahudawan nan da suka gaskata shi, “In dai kun zauna kan maganata, hakika ku almajiraina ne. 32 Za ku san gaskiya, gaskiyar kuwa za ta 'yanta ku.” 33 Suka amsa masa suka ce, “Ai, mu zuriyar Ibrahim ne, ba mu taɓa bauta wa kowa ba. Yaya kuma za ka ce za a 'yanta mu?” 34 Sai Yesu ya amsa musu ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku, duk mai aikata zunubi bawan zunubi ne. 35 Ai, bawa ba ya ɗorewa a gida har abada, ɗa kuwa yana ɗorewa. 36 In kuwa Ɗan ya 'yanta ku, za ku 'yantu, 'yantuwar gaske. 37 Na san dai ku zuriyar Ibrahim ne, amma kuwa kuna neman kashe ni, don maganata ba ta shigarku. 38 Ina faɗar abin da na gani a wurin Ubana, ku kuma kuna yin abin da kuka ji daga wurin naku uban.”

Ubanku Iblis Ne

39 Suka amsa masa suka ce, “Ai, Ibrahim ne ubanmu.” Yesu ya ce musu, “Da ku 'ya'yan Ibrahim ne, da sai ku yi aikin da Ibrahim ya yi. 40 Ga shi yanzu, kuna neman kashe ni, ni mutumin da na gaya muku gaskiyar da na ji wurin Allah. Ba haka Ibrahim ya yi ba. 41 Ku kuna aikin da ubanku yake yi ne.” Suka ce masa, “Ba a haife mu daga fasikanci ba, ubanmu ɗaya ne, wato, Allah.” 42 Yesu ya ce musu, “Da Allah ne Ubanku da kun ƙaunace ni, domin daga wurin Allah na fito, ga ni nan kuwa. Ban zo domin kaina ba, shi ne ya aiko ni. 43 Don me ba kwa gane maganata? Don ba kwa iya jimirin jin maganata ne. 44 Ku na ubanku Iblis ne, niyyarku kuwa ku aikata burin ubanku. Shi dā ma tun farko mai kisankai ne, bai zauna kan gaskiya ba, don ba ruwansa da gaskiya. Duk sa'ad da yake ƙarya, cinikinsa yake yi, don shi maƙaryaci ne, uban ƙarairayi kuma. 45 Amma domin ina faɗar gaskiya, ba kwa gaskata ni. 46 A cikinku wa zai iya haƙƙaƙewa na taɓa yin zunubi? In kuwa gaskiya nake faɗa, to, don me ba kwa gaskata ni? 47 Na Allah yakan saurari Maganar Allah. Abin da ya sa ba kwa sauraronta ke nan, don ku ba na Allah ba ne.”

Kafin Ibrahim, Nake

48 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Ashe, gaskiyarmu da muka ce kai Basamariye ne, kana kuma da iska.” 49 Yesu ya amsa ya ce, “Ni ba mai iska ba ne. Ubana nake girmamawa, ku kuwa wulakanta ni kuke yi. 50 Ba ni nake nemar wa kaina girma ba, akwai mai nemar mini, shi ne kuma mai yin shari'a. 51 Lalle hakika, ina gaya muku, kowa ya kiyaye maganata ba zai mutu ba har abada.” 52 Sai Yahudawa suka ce masa, “To, yanzu kam, mun tabbata kana da iska. Ai, Ibrahim ya mutu, haka ma annabawa, kana kuwa cewa, kowa ya kiyaye maganarka ba zai mutu ba har abada. 53 Wato, ka fi ubanmu Ibrahim ne, ya kuwa mutu? Annabawa ma sun mutu! Wa ka mai da kanka ne?” 54 Yesu ya amsa ya ce, “In ma na ɗaukaka kaina, ɗaukakata ba a bakin kome take ba. Ubana shi ne mai ɗaukaka ni, wanda kuke cewa, shi ne Allahnku. 55 Ku ba ku san shi ba, amma ni na san shi. Da na ce ban san shi ba, da na zama maƙaryaci kamarku. Amma na san shi, ina kuma kiyaye maganarsa. 56 Ubanku Ibrahim ya yi farin ciki matuƙa ya sami ganin zamanina, ya kuwa gan shi, ya yi murna.” 57 Sai Yahudawa suka ce masa, “Har yanzu ma ba ka kai shekara hamsin ba, ashe ka ga Ibrahim!” 58 Sai Yesu ya ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, tun ba a haifi Ibrahim ba, ni ne.” 59 Don haka suka ɗebo duwatsu su jajjefe shi. Yesu kuwa ya ɓuya, ya fita daga Haikalin.

Yahaya 9

Warkar da wanda aka Haifa Makaho

1 Yesu yana wucewa sai ya ga wani mutum da aka haifa makaho. 2 Sai almajiransa suka tambaye shi suka ce, “Ya Shugaba, wa ya yi zunubi da aka haifi mutumin nan makaho, shi, ko iyayensa?” 3 Yesu ya amsa ya ce, “Ba domin mutumin nan ko iyayensa sun yi zunubi ba, sai domin a nuna aikin Allah ne a kansa. 4 Lalle ne mu yi aikin wanda ya aiko ni tun da sauran rana. Ai, dare zai yi sa'ad da ba mai iya aiki. 5 Muddin ina duniya ni ne hasken duniya.” 6 Da ya faɗi haka sai ya tofa yau a ƙasa, ya cuɗa ƙasa, ya shafa a idanun makahon, 7 ya ce masa, “Je ka, ka wanke ido a ruwan Siluwam,” (wato, aikakke). Shi ke nan sai ya je ya wanke ido, ya komo yana gani. 8 Maƙwabta da waɗanda suka saba ganinsa dā yana bara, suka ce, “Ashe, ba wannan ne yakan zauna yana bara ba?” 9 Waɗansu suka ce, “Shi ne mana.” Waɗansu kuwa suka ce, “A'a, kai dai, sun yi kama.” Shi kuwa ya ce, “Sosai ni ne!” 10 Sai suka ce masa, “To, ƙaƙa aka yi idanunka suka buɗe?” 11 Ya amsa ya ce, “Mutumin nan da ake kira Yesu ne ya cuɗa ƙasa ya shafa mini a idanu, ya ce mini, ‘Je ka Siluwam ka wanke ido.’ Na kuwa je na wanke, sai na sami gani.” 12 Suka ce masa, “Ina yake?” Ya ce, “Ban sani ba.”

Farisiyawa sun Bincika Labarin wanda aka Warkar

13 Sai suka kai wa Farisiyawa mutumin da yake makaho a dā. 14 To, ran Asabar ne Yesu ya cuɗa ƙasar ya buɗe masa ido. 15 Farisiyawa ma suka tambaye shi ta yadda aka yi ya sami gani. Ya ce musu, “Cuɗaɗɗiyar ƙasa ya shafa a idona, na wanke, ina gani.” 16 Saboda haka, waɗansu Farisiyawa suka ce, “Mutumin nan ba daga Allah yake ba, don ba ya kiyaye Asabar.” Waɗansu kuwa suka ce, “Yaya mutum mai zunubi zai iya yin mu'ujizai haka?” Sai rabuwa ta shiga tsakaninsu. 17 Sai suka sāke ce wa makahon, “To, kai fa, me ka gani game da shi, da yake kai ya buɗe wa ido?” Ya ce, “Ai, annabi ne.” 18 Yahudawa kam, ba su gaskata shi makaho ne a dā ba, ya kuma sami gani, har suka kira iyayen wanda ya sami ganin, 19 suka tambaye su suka ce, “Wannan ɗanku ne da kuke cewa, an haife shi makaho? To, ta yaya yake iya gani yanzu?” 20 Sai iyayen nasa suka amsa suka ce, “Mun dai san wannan ɗanmu ne, makaho ne aka haife shi. 21 Amma ta yadda aka yi yake gani yanzu ba mu sani ba, ba mu ma san wanda ya buɗe idon ba. Ku tambaye shi, ai, ba yaro ba ne, zai faɗa da bakinsa.” 22 Iyayensa sun faɗi haka ne don tsoron Yahudawa, don dā ma Yahudawa sun ƙulla, cewa, kowa ya amsa, cewa, shi ne Almasihu, za a fisshe shi daga jama'a. 23 Shi ya sa iyayensa suka ce, “Ai, ba yaro ba ne, ku tambaye shi.” 24 Sai suka sāke kiran mutumin nan da yake makaho a dā, suka ce masa, “Ka tsoraci Allah dai! Mu kam, mun san mutumin nan mai zunubi ne.” 25 Sai ya amsa ya ce, “Ko mai zunubi ne, ni ban sani ba. Abu ɗaya kam, na sani, dā ni makaho ne, yanzu kuwa ina gani.” 26 Sai suka ce masa, “Shin, me ya yi maka? Ta yaya ya buɗe maka ido?” 27 Ya amsa musu ya ce, “Na riga na faɗa muku, ba ku ji ba. Don me kuke so ku sāke ji? Ko ku ma kuna so ku zama almajiransa ne?” 28 Sai suka fāɗa shi da zagi, suna cewa, “Kai ne dai almajirin wannan ɗin, mu kam, almajiran Musa ne. 29 Mun dai sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan ba mu san ta inda ya fito ba.” 30 Sai mutumin ya amsa musu ya ce, “Yau ga abin mamaki! Ashe, ba ku san ta inda ya fito ba, ga shi kuwa, ya buɗe mini ido! 31 Mun sani Allah ba ya sauraron masu zunubi, amma duk wanda yake mai bautar Allah, yake kuma aikata nufinsa, Allah yakan saurare shi. 32 Tun da aka fara duniya ba a taɓa jin wani ya buɗe idon wanda aka haifa makaho ba. 33 Da mutumin nan ba daga Allah ya fito ba, da ba abin da zai iya yi.” 34 Suka amsa masa suka ce, “Kai da aka haifa a baƙin zunubi ne za ka koya mana?” Sai suka kore shi.

Makanta ta Ruhu

35 Yesu ya ji labari sun kore shi. Da ya same shi, ya ce, “Ka gaskata da Ɗan Mutum ko?” 36 Ya amsa ya ce, “Wane ne shi, ya Shugaba, da zan gaskata da shi?” 37 Yesu ya ce masa, “Ai, ka gan shi, shi ne ma mai magana da kai.” 38 Sai ya ce, “Ya Ubangiji, na ba da gaskiya,” ya kuma yi masa sujada. 39 Yesu ya ce, “Na shigo duniyar nan ne don rarrabewa, domin waɗanda ba sa gani su gani, waɗanda suke gani kuma su makance.” 40 Da Farisiyawan nan da suke tare da shi suka ji haka, suka ce masa, “Wato, mu ma makafi ne?” 41 Yesu ya ce musu, “Ai, da makafi ne ku, da ba ku da zunubi. Amma da yake kun ce kuna gani, to, zunubinku ya tabbata.

Yahaya 10

Misali na Garken Tumaki

1 “Lalle hakika, ina gaya muku, wanda bai shiga garken tumaki ta ƙofa ba, amma ya haura ta wani wuri, to, shi ɓarawo ne, ɗan fashi kuma. 2 Wanda kuwa ya shiga ta ƙofar, makiyayin tumakin ne. 3 Mai tsaron ƙofar yakan buɗe masa, tumakin kuma sukan saurari muryarsa, yakan kama sunan nasa tumakin, ya kai su waje. 4 Bayan ya fitar da dukan nasa waje, sai ya shige gabansu, tumakin suna biye da shi, domin sun san muryarsa. 5 Ba za su bi baƙo ba, sai dai su guje shi, don ba su san muryar baƙo ba.” 6 Yesu ya yi musu wannan misali, amma ba su gane abin da ya faɗa musu ba.

Yesu ne Makiyayi Mai Kyau

7 Don haka Yesu ya sāke ce musu, “Lalle hakika, ina gaya muku, ni ne ƙofar tumakin. 8 Duk waɗanda suka riga ni zuwa cewa, su ne ni, ɓarayi ne, 'yan fashi kuma, amma tumakin ba su kula da su ba. 9 Ni ne ƙofar. Kowa ya shiga ta wurina zai sami ceto, ya kai ya kawo, ya kuma yi kiwo. 10 Ɓarawo yakan zo ne kawai don sata da kisa da hallakarwa. Ni kuwa na zo ne domin su sami rai, su kuma same shi a yalwace. 11 Ni ne makiyayi mai kyau. Makiyayi mai kyau kuwa shi ne mai ba da ransa domin tumakin. 12 Wanda yake ɗan asako kuwa, ba makiyayin gaske ba, tumakin kuma ba nasa ba, da ganin kyarkeci ya doso, sai ya watsar da tumakin, ya yi ta kansa, kyarkeci kuwa ya sure waɗansu, ya fasa sauran. 13 Ya gudu ne fa, don shi ɗan asako ne, ba abin da ya dame shi da tumakin. 14 Ni ne Makiyayi mai kyau. Na san nawa, nawa kuma sun san ni, 15 kamar yadda Uba ya san ni, ni kuma na san Uban. Ina ba da raina maimakon tumakin. 16 Ina kuma da waɗansu tumaki da ba na wannan garke ba ne. Su ma lalle ne in kawo su, za su kuwa saurari muryata, su zama garke guda, makiyayi kuma guda. 17 Domin wannan uba yake ƙaunata, domin ina ba da raina in ɗauko shi kuma. 18 Ba mai karɓe mini rai, don kaina nake ba da shi. Ina da ikon ba da shi, ina da ikon ɗauko shi kuma. Na karɓo wannan umarni ne daga wurin Ubana.” 19 Saboda maganar nan fa, sai rabuwa ta sāke shiga tsakanin Yahudawa. 20 Da yawa daga cikinsu suka ce, “Ai, mai iska ne, haukansa kawai yake yi. Don me za ku saurare shi?” 21 Waɗansu kuwa suka ce, “A'a, wannan magana, ai, ba ta mai iska ba ce. Ashe, iska tana iya buɗe wa makaho ido?”

Yahudawa sun Ƙi Yesu

22 Lokacin idin tsarkakewa ne kuwa a Urushalima, 23 damuna ce kuma, Yesu kuwa yana zagawa a Shirayin Sulemanu cikin Haikali, 24 sai Yahudawa suka kewaye shi, suka ce masa, “Har yaushe za ka bar mu da shakka? In dai kai ne Almasihun, ka gaya mana a fili.” 25 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, na faɗa muku, ba ku gaskata ba. Ayyukan da nake yi da sunan Ubana, suke shaidata. 26 Amma ku ba ku gaskata ba, domin ba kwa cikin tumakina. 27 Tumakin nan nawa sukan saurari muryata, na san su, suna kuma bi na. 28 Ina ba su rai madawwami, ba kuwa za su hallaka ba har abada, ba kuma mai ƙwace su daga hannuna. 29 Ubana, wanda ya ba ni su, ya fi duka girma, ba kuwa mai iya ƙwace su daga ikon Uban. 30 Ni da Uba ɗaya muke.” 31 Sai Yahudawa suka sāke ɗebo duwatsu su jajjefe shi. 32 Yesu ya amsa musu ya ce, “Na nuna muku ayyuka nagari masu yawa daga wurin Uba, a kan wanne a cikinsu za ku jajjefe ni?” 33 Yahudawa suka amsa suka ce, “Ba don wani aiki nagari za mu jajjefe ka ba, sai don sāɓo, don kai, ga ka mutum, amma kana mai da kanka Allah.” 34 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ba a rubuce yake a Shari'arku ba cewa, ‘Na ce ku alloli ne?’ 35 To, in waɗanda Maganar Allah ta zo musu ya ce da su alloli (Nassi kuwa ba ya tashi), 36 kwa ce da wanda Uba ya keɓe, ya kuma aiko duniya, ‘Sāɓo kake,’ domin na ce, ‘Ni Ɗan Allah ne?’ 37 In ba ayyukan da Ubana yake yi nake yi ba, to, kada ku gaskata ni. 38 Amma in su nake yi, ko ba ku gaskata ni ba, to, ku gaskata ayyukan, don ku sani, ku kuma gane, Uban yana cikina, ni kuma ina cikin Uban.” 39 Sai suka sāke ƙoƙarin kama shi, amma ya fita daga hannunsu. 40 Sa'an nan ya sāke komawa hayin Kogin Urdun, wurin da Yahaya ya fara yin baftisma, ya zauna a can, 41 mutane kuwa da yawa suka zo wurinsa, sai suka riƙa cewa, “Hakika, Yahaya bai yi wata mu'ujiza ba, amma duk abin da ya faɗa game da mutumin nan gaskiya ne.” 42 Nan fa mutane da yawa suka gaskata da shi.

Yahaya 11

Mutuwar Li'azaru

1 Wani mutum ne ya yi rashin lafiya, sunansa Li'azaru na Betanya, ƙauyen su Maryamu da 'yar'uwarta Marta. 2 Maryamun nan kuwa, wadda ɗan'uwanta Li'azaru ba shi da lafiya, ita ce wadda ta shafa wa Ubangiji man ƙanshi, ta kuma shafe ƙafafunsa da gashinta. 3 To, 'yan'uwan nan mata suka aika masa, suka ce, “Ya Ubangiji, ga shi, wanda kake ƙaunar nan ba shi da lafiya.” 4 Da Yesu ya ji haka ya ce, “Wannan rashin lafiya, ƙarshensa ba mutuwa ba ne, domin a ɗaukaka Allah ne, a kuma ɗaukaka Ɗan Allah ta wurinsa.” 5 Yesu kuwa na ƙaunar Marta da 'yar'uwarta, da kuma Li'azaru. 6 To, da ya ji Li'azaru ba shi da lafiya, sai ya ƙara kwana biyu. 7 Bayan haka ya ce wa almajiran, “Mu koma ƙasar Yahudiya.” 8 Almajiran suka ce masa, “Ya Shugaba, kwana kwanan nan fa Yahudawa suke neman jifanka, za ka sāke komawa can?” 9 Yesu ya amsa ya ce, “Ba sa'a goma sha biyu ce yini ɗaya ba? Kowa yake tafiya da rana ba ya tuntuɓe, don yana ganin hasken duniyar nan. 10 Amma kowa yake tafiya da dare yakan yi tuntuɓe, don ba haske a gare shi!” 11 Ya faɗi haka, sa'an nan ya ƙara ce musu, “Amininmu Li'azaru ya yi barci, amma za ni in tashe shi.” 12 Sai almajiran suka ce masa, “Ya Ubangiji, in dai barci ne ya ɗauke shi, ai, zai warke.” 13 Alhali kuwa, Yesu zancen mutuwar Li'azaru yake, amma su sun ɗauka yana nufin barcin hutawa ne. 14 Sai Yesu ya gaya musu a fili, ya ce, “Li'azaru dai ya mutu. 15 Ina kuwa farin ciki da ba na nan, saboda ku domin ku ba da gaskiya. Amma mu dai je wurinsa.” 16 Sai Toma, wanda ake kira Ɗan Tagwai, ya ce wa 'yan'uwansa almajirai, “Mu ma mu tafi, mu mutu tare da shi.”

Yesu shi ne Tashin Matattu da Rai Kuma

17 Da Yesu ya isa, ya tarar Li'azaru, har ya kwana huɗu a kabari. 18 Betanya kuwa kusa da Urushalima take, misalin mil biyu. 19 Yahudawa da yawa sun zo su yi wa Marta da Maryamu ta'aziyyar ɗan'uwansu. 20 Da jin Yesu yana zuwa, sai Marta ta je taryensa, Maryamu kuwa ta zauna a gida. 21 Sai Marta ta ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, da kana nan da ɗan'uwana bai mutu ba. 22 Ko yanzu ma na sani kome ka roƙi Allah zai yi maka.” 23 Yesu ya ce mata, “Ɗan'uwanki zai tashi.” 24 Marta ta ce masa, “Na sani zai tashi a tashin matattu a ranar ƙarshe.” 25 Yesu ya ce mata, “Ai, ni ne tashin matattu, ni ne kuma rai. Wanda ya gaskata da ni, ko ya mutu zai rayu. 26 Wanda kuwa yake raye, yake kuma gaskatawa da ni, ba zai mutu ba har abada. Kin gaskata wannan?” 27 Ta ce masa, “I, ya Ubangiji. Na gaskata kai ne Almasihu, Ɗan Allah, wanda yake zuwa cikin duniya.”

Yesu ya yi Hawaye

28 Da ta faɗi haka, ta je ta kirawo 'yar'uwarta Maryamu, ta raɗa mata ta ce, “Ga Malam ya zo, yana kiranki.” 29 Ita kuwa da jin haka, ta yi maza ta tashi ta nufi wurinsa. 30 Yesu dai bai iso ƙauyen ba tukuna, har yanzu yana wurin da Marta ta tarye shi. 31 Da Yahudawan da suke tare da ita a cikin gida, suna yi mata ta'aziyya, suka ga Maryamu ta yi maza ta tashi ta fita, suka bi ta, suna zaton za ta kabarin ne, ta yi kuka a can. 32 Da Maryamu ta iso inda Yesu yake, ta gan shi, sai ta faɗi a gabansa ta ce masa, “Ya Ubangiji, da kana nan da dan'uwana bai mutu ba.” 33 Da Yesu ya ga tana kuka, Yahudawan da suka zo tare da ita su ma, suna kuka, sai ya nisa a ransa, ya yi juyayi gaya. 34 Ya kuma ce, “Ina kuka sa shi?” Suka ce masa, “Ya Ubangiji, zo ka gani.” 35 Sai Yesu ya yi kuka. 36 Don haka Yahudawa suka ce, “Dubi yadda yake ƙaunarsa!” 37 Amma waɗansunsu suka ce, “Ashe, wanda ya buɗe wa makahon nan ido, ba zai iya hana wannan mutum mutuwa ba?”

Yesu ya Ta da Li'azaru daga Matattu

38 Sai Yesu ya sāke nisawa a ransa, ya iso kabarin. Kabarin kuwa kogon dutse ne, da wani dutse kuma an rufe bakin. 39 Yesu ya ce, “Ku kawar da dutsen.” Sai Marta, 'yar'uwar mamacin, ta ce masa, “Ya Ubangiji, ai, yanzu ya yi ɗoyi, don yau kwanansa huɗu ke nan da mutuwa.” 40 Sai Yesu ya ce mata, “Ban gaya miki ba, in kin ba da gaskiya za ki ga ɗaukakar Allah?” 41 Sai suka kawar da dutsen. Yesu kuwa ya ɗaga kai sama ya ce, “Ya Uba, na gode maka da ka saurare ni. 42 Ko dā ma na sani koyaushe kana saurarona, amma na faɗi haka ne saboda jama'ar da suke nan tsaitsaye, domin su gaskata kai ne ka aiko ni.” 43 Da ya faɗi haka ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Li'azaru fito!” 44 Sai mamacin ya fito, ƙafa da hannu a ɗaure da likkafani, fuskarsa kuma a naɗe da mayani. Yesu ya ce musu, “Ku kwance masa, ya tafi.”

An Kulla Shawara gāba da Yesu

45 Saboda haka Yahudawa da yawa da suka zo wurin Maryamu, suka kuma ga abin da ya yi, suka gaskata da shi. 46 Amma waɗansunsu suka tafi wurin Farisiyawa, suka gaya musu abin da Yesu ya yi. 47 Don haka manyan firistoci da Farisiyawa suka tara 'yan majalisa, suka ce, “Shin, me muke yi ne, har mutumin nan yake ta yin mu'ujizai da yawa haka? 48 In fa muka ƙyale shi kan haka, kowa zai gaskata da shi, Romawa kuma za su zo su karɓe ƙasarmu su ɗebe jama'armu.” 49 Amma ɗayansu, mai suna Kayafa, wanda yake shi ne babban firist a shekarar nan, ya ce musu, “Ku dai ba ku san kome ba. 50 Ba kwa lura, ai, ya fiye muku mutum ɗaya ya mutu saboda jama'a, da duk al'umma ta hallaka.” 51 Ba da nufinsa ya faɗi haka ba, sai dai da yake shi ne babban firist a shekarar nan, ya yi annabci cewa, Yesu zai mutu saboda jama'a, 52 ba ma saboda al'umma kaɗai ba, har ma yă tattaro 'ya'yan Allah da suke warwatse ko'ina su zama ɗaya. 53 Daga ran nan fa sai suka ƙulla su kashe shi. 54 Saboda haka, Yesu bai ƙara tafiya a cikin Yahudawa a sarari ba, amma ya tashi daga wurin, ya tafi ƙasar da take a bakin jeji, ya shiga wani gari, mai suna Ifraimu. Nan ya zauna da almajiran. 55 Ana nan, Idin Ƙetarewa na Yahudawa ya gabato, mutane da yawa daga ƙauyuka suka tafi Urushalima su tsarkake kansa kafin idin. 56 Suka yi ta neman Yesu, suna tsaitsaye a Haikali, suna ce wa juna, “Me kuka gani? Zai zo idin kuwa?” 57 Don dā ma, manyan firistoci da Farisiyawa sun yi umarni, cewa, idan kowa ya san inda Yesu yake, ya zo ya faɗa, su kama shi.

Yahaya 12

An Shafi Yesu da Man Ƙanshi a Betanya

1 Idin Ƙetarewa sauran kwana shida, sai Yesu ya zo Betanya inda Li'azaru yake, wanda Yesu ya tasa daga matattu. 2 Nan aka yi masa abincin dare, Marta ce ta yi hidima, Li'azaru kuwa yana cikin masu ci tare da shi. 3 Sai Maryamu ta ɗauko awo guda na man ƙanshi na nardi tsantsa, mai tamanin gaske, ta shafa a ƙafafun Yesu, sa'an nan ta shafe su da gashinta. Duk gidan ya game da ƙanshin man. 4 Amma Yahuza Iskariyoti, ɗaya daga cikin almajiransa, wato, wanda zai bāshe shi, ya ce, 5 “Me ya hana a sayar da man nan a kan dinari ɗari uku, a ba talakawa kuɗin?” 6 Ya faɗi haka fa, ba don yana kula da talakawa ba, a'a, sai dai don shi ɓarawo ne, da yake kuma jakar kuɗinsu tana hannunsa, yakan riƙa taɓa abin da ke ciki. 7 Sai Yesu ya ce, “A ƙyale ta, dā ma ta ajiye shi domin tanadin ranar jana'izata. 8 Ai, kullum kuna tare da talakawa, amma ba kullum kuke tare da ni ba.”

An Ƙulla Shawara gāba da Li'azaru

9 Da taron Yahudawa mai yawa suka ji labari yana nan, sai suka zo, ba domin Yesu kaɗai ba, har ma don su ga Li'azaru wanda ya tasa daga matattu. 10 Sai manyan firistoci suka yi shawarar kashe Li'azaru, shi ma, 11 domin ta dalilinsa Yahudawa da yawa suke warewa, suna gaskatawa da Yesu.

Mutanen Urushalima sun Marabci Yesu

12 Kashegari babban taron da suka zo idi, da suka ji Yesu yana zuwa Urushalima, 13 suka ɗaɗɗauko gazarin dabino suka firfita taryensa, suna ta da murya suna cewa, “Hosanna! Albarka ta tabbata ga mai zuwa da sunan Ubangiji, Sarkin Isra'ila!” 14 Da Yesu ya sami wani aholaki sai ya hau, kamar yadda yake a rubuce cewa, 15 “Kada ki ji tsoro, yake 'yar Sihiyona, Ga sarkinki yana zuwa a kan aholakin jaki!” 16 Da fari almajiransa ba su gane abin nan ba, amma bayan an ɗaukaka Yesu, suka tuna abin nan a rubuce yake game da shi, har ma aka yi masa shi. 17 Taron da suke tare da shi sa'ad da ya kira Li'azaru yă fito daga kabari, ya tashe shi daga matattu, su suka riƙa shaidarwa da haka. 18 Shi ya sa taron suka fita taryensa, don sun ji ya yi mu'ujizan nan. 19 Sai Farisiyawa suka ce wa juna, “Duba! Ba abin da muka iya! Ai, duk duniya tana bayansa.”

Waɗansu Helenawa sun Nemi Yesu

20 To, a cikin waɗanda suka zo idin yin sujada akwai waɗansu Helenawa. 21 Sai suka zo wurin Filibus, mutumin Betsaida ta ƙasar Galili, suka roƙe shi suka ce, “Maigida, muna bukatar mu gana da Yesu.” 22 Sai Filibus ya je ya gaya wa Andarawas, Andarawas kuma ya zo da Filibus, suka gaya wa Yesu. 23 Yesu ya amsa musu ya ce, “Lokaci ya yi da za a ɗaukaka Ɗan Mutum. 24 Lalle hakika, ina gaya muku, in ba an binne ƙwayar alkama ta mutu ba, za ta zauna ita kaɗai. Amma in ta mutu sai ta hayayyafa. 25 Mai ƙaunar ransa zai rasa shi. Wanda kuwa ya ƙi ransa a duniyar nan, ya kiyaye shi ke nan, har ya zuwa rai madawwami. 26 Wanda duk zai bauta mini, ya bi ni. Inda nake kuma, nan bawana zai kasance shi ma. Kowa yake bauta mini, Uba zai girmama shi.”

Lalle a Ɗaga Ɗan Mutum Sama

27 “Yanzu ina jin nauyi a raina. Me zan ce kuwa? In ce, ‘Ya Uba ka ɗauke mini wannan lokaci?’ A'a, ai, dā ma na zo ne takanas domin wannan lokaci. 28 Ya Uba, ka ɗaukaka sunanka.” Sai aka ji wata murya daga Sama ta ce, “Na riga na ɗaukaka shi, zan kuma ƙara ɗaukaka shi,” 29 Da taron da suke tsaya a wurin suka ji muryar, suka ce, “An yi cida.” Waɗansu kuwa suka ce, “Wani mala'ika ne ya yi masa magana.” 30 Yesu ya amsa ya ce, “Ba saboda ni aka yi wannan murya ba, sai dominku. 31 Yanzu ne za a yi wa duniyar nan shari'a, yanzu ne kuma za a tuɓe mai mulkin duniyar nan. 32 Ni kuwa bayan an ɗaga ni daga ƙasa zan ja dukan mutane gare ni.” 33 Ta faɗar haka ya kwatanta irin mutuwar da zai yi. 34 Sai taron suka amsa masa suka ce, “Shari'armu ta gaya mana, cewa, Almasihu zai tabbata har abada. To, yaya za ka ce lalle ne a ɗaga Ɗan Mutum? Wane ne Ɗan Mutum ɗin?” 35 Yesu ya ce musu, “Haske yana tare da ku har ɗan lokaci kaɗan na gaba. Ku yi tafiya tun haske yana tare da ku, kada duhu ya ci muku. Mai tafiya a cikin duhu bai san inda yake tafiya ba. 36 Ku gaskata da hasken, tun kuna tare da shi, domin ku zama mutanen haske.” Yahudawa ba su Gaskata da shi Ba Yesu ya faɗi haka, sa'an nan ya tafi ya ɓuya musu. 37 Amma ko da yake ya sha yin mu'ujizai da yawa a gabansu, duk da haka, ba su gaskata shi ba, 38 domin a cika faɗar Annabi Ishaya cewa, “Ya Ubangiji, wa ya gaskata jawabinmu? Ga wa kuma aka bayyana ikon Ubangiji?” 39 Shi ya sa ba su iya ba da gaskiya ba. Domin Ishaya ya sāke cewa, 40 “Ya makantar da su, ya kuma taurarar da zuciyarsu, Kada su gani da idanunsu, su kuma gane a zuci, Har su juyo gare ni in warkar da su.” 41 Ishaya ya faɗi haka saboda ya ga ɗaukakar Almasihu, ya kuma ba da labarinsa. 42 Duk da haka, da yawa har daga cikin shugabanni ma suka gaskata da shi, amma saboda tsoron Farisiyawa, ba su bayyana ba, don kada a fisshe su daga jama'a. 43 Don sun fi ƙaunar girmamawar mutane da girmamawar Allah.

Maganar Yesu za ta yi Hukunci

44 Sai Yesu ya ɗaga murya ya ce, “Wanda yake gaskatawa da ni, ba ni yake gaskatawa ba, amma ga wanda ya aiko ni. 45 Wanda kuma yake dubana, yana duban wanda ya aiko ni ne. 46 Na zo duniya a kan ni haske ne, domin duk mai gaskatawa da ni kada ya yi zaman duhu. 47 Kowa ya ji maganata, bai kuwa kiyaye ta ba, ba ni nake hukunta shi ba. Gama ba don yi wa duniya hukunci na zo ba, sai dai domin in ceci duniya. 48 Wanda ya ƙi ni, bai kuma karɓi maganata ba, yana da mai hukunta shi, maganar da na faɗa, ita za ta hukunta shi a ranar ƙarshe. 49 Ba kuwa domin kaina na yi magana ba, Uban da ya aiko ni shi kansa ya ba ni umarni a kan abin da zan faɗa, da kuma maganar da zan yi. 50 Na kuma san umarnin nan nasa rai ne madawwami. Domin haka, abin da nake faɗa ina faɗa ne daidai yadda Uba ya faɗa mini.”

Yahaya 13

Yesu ya Wanke Ƙafafun Almajiransa

1 Ana nan tun kafin Idin Ƙetarewa, da Yesu ya san lokacinsa ya yi da zai bar wannan duniya ya koma wurin Uba, da yake ya ƙaunaci mutanensa da suke duniya, ya ƙaunace su har matuƙa. 2 Ana cikin cin abincin dare, Iblis kuwa ya riga ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti ɗan Saminu yă bāshe shi. 3 Yesu kuwa, da yake ya san Uba ya sa kome a hannunsa, ya kuma sani daga wurin Allah ya fito, wurin Allah kuma zai koma, 4 sai ya tashi daga cin abincin, ya ajiye mayafinsa, ya ɗauko mayani ya yi ɗamara da shi. 5 Sa'an nan ya zuba ruwa a daro, ya fara wanke ƙafafun almajiran, yana shafewa da mayanin. 6 Sai ya zo kan Bitrus, shi kuwa ya ce masa, “Ya Ubangiji, ashe, kai ne za ka wanke mini ƙafa?” 7 Yesu ya amsa ya ce, “Yanzu kam, ba ka san abin da nake yi ba, amma daga baya za ka fahimta.” 8 Bitrus ya ce masa, “Wane ni! Ai, ba za ka wanke mini ƙafa ba har abada!” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo a gare ni.” 9 Bitrus ya ce masa, “Ya Ubangiji, ba ma ƙafafuna kaɗai ba, har ma da hannuwana da kaina!” 10 Yesu ya ce masa, “Wanda ya yi wanka ba ya bukatar wanke kome, sai ƙafafunsa kawai, domin ya riga ya tsarkaka sarai. Ku ma tsarkakakku ne, amma ba dukanku ne ba.” 11 Don ya san wanda zai bāshe shi, shi ya sa ya ce, “Ba dukanku ne tsarkakakku ba.” 12 Bayan ya wanke ƙafafunsu, ya yafa mayafinsa, sai ya sāke kishingiɗa, ya ce musu, “Kun gane abin da na yi muku? 13 Kuna kirana Malam, da kuma Ubangiji. Daidai ne kuwa, don haka nake. 14 Tun da yake ni da nake Ubangijinku, kuma Malaminku, har na wanke muku ƙafa, ashe, kuma wajibi ne ku wanke wa juna. 15 Na yi muku ishara domin ku ma ku yi yadda na yi muku 16 Lalle hakika, ina gaya muku, bawa ba ya fin ubangijinsa, manzo kuma ba ya fin wanda ya aiko shi. 17 In dai kun san wannan, kuna kuma aikatawa, ku masu farin ciki ne. 18 Ba dukanku nake nufi ba. Na san waɗanda na zaɓa. Wannan kuwa duk domin a cika Nassi ne cewa, ‘Wanda muke ci tare ya tasar mini.’ 19 Tun yanzu zan sanar da ku abu tun bai faru ba, domin sa'ad da ya faru ku ba da gaskiya ni ne shi. 20 Lalle hakika, ina gaya muku, wanda ya yi na'am da duk wanda na aiko, ya yi na'am da ni ke nan. Wanda ya yi na'am da ni kuwa, to, ya yi na'am da wanda ya aiko ni.”

Yesu ya Ce za a Bāshe Shi

21 Bayan da Yesu ya faɗi haka, ya ji nauyi a ransa, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku, ɗayanku zai bāshe ni.” 22 Sai almajiran suka duddubi juna, suka rasa ko da wa yake. 23 Wani daga cikin almajiransa kuwa, wanda Yesu yake ƙauna, yana kishingiɗe gab da Yesu. 24 Sai Bitrus ya alamta masa ya ce, “Gaya mana, da wa yake?” 25 Shi kuwa da yake kishingiɗe haka gab da Yesu ya karkata, ya ce masa, “Ya Ubangiji, wane ne shi?” 26 Sai Yesu ya amsa ya ce, “Shi ne wanda zan tsoma 'yar lomar nan in ba shi.” Da ya tsoma 'yar lomar kuwa, sai ya ba Yahuza, Ɗan Saminu Iskariyoti. 27 Da karɓar 'yar lomar nan Shaiɗan ya shige shi. Yesu ya ce masa, “Yi abin da za ka yi, maza.” 28 Amma cikin waɗanda suke cin abinci, ba wanda ya san dalilin da ya sa Yesu ya faɗa masa haka. 29 Har waɗansu ma sun yi zaton Yesu ya ce masa ya yi musu sayayyar idi ne, ko kuwa ya ba talakawa wani abu, don Yahuza ne yake riƙe da jakar kuɗinsu. 30 Shi kuwa da karɓar 'yar lomar, sai ya fita, da dare ne kuwa.

Sabon Umarni

31 Bayan da ya fita kuma sai Yesu ya ce, “Yanzu ne aka ɗaukaka Ɗan Mutum, aka kuma ɗaukaka Allah ta wurinsa. 32 Allah kuma zai ɗaukaka shi zuwa ga zatinsa, nan da nan kuwa zai ɗaukaka shi. 33 Ya ku 'ya'yana ƙanana, saura ɗan lokaci kaɗan ina tare da ku. Za ku neme ni, amma kamar yadda na faɗa wa Yahudawa cewa, ‘Inda za ni ba za ku iya zuwa ba,’ haka nake faɗa muku yanzu. 34 Sabon umarni nake ba ku, shi ne ku ƙaunaci juna. Kamar yadda na ƙaunace ku, haka ku ma, ku ƙaunaci juna. 35 Ta haka, kowa zai gane ku almajiraina ne, in dai kuna ƙaunar juna.” 13 .36 Bitrus zai Yi M�sun Sanin Yesu Bitrus zai Yi M�sun Sanin Yesu 36 Bitrus ya ce masa, “Ya Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba za ka iya bina yanzu ba, amma daga baya za ka bi ni.” 37 Bitrus ya ce masa, “Ya Ubangiji, don me, ba zan iya binka a yanzu ba? Ai, zan ba da raina saboda kai.” 38 Yesu ya amsa ya ce, “Ashe, za ka ba da ranka saboda ni? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara, za ka yi m�sun sanina sau uku.”

Yahaya 14

Yesu ne Hanya zuwa wurin Uban

1 “Kada ku damu. Ku gaskata da Allah, ku kuma gaskata da ni. 2 A gidan Ubana akwai wurin zama da yawa. Da ba haka ba ne, da na faɗa muku, domin zan tafi in shirya muku wuri. 3 In kuwa na je na shirya muku wuri, sai in dawo in kai ku wurina, domin inda nake, ku ma ku zama kuna can. 4 Inda za ni kuwa kun san hanya.” 5 Sai Toma ya ce masa, “Ya Ubangiji, ba mu san inda za ka ba, ta yaya za mu san hanyar?” 6 Yesu ya ce masa, “Ni ne hanya, ni ne gaskiya, ni ne kuma rai. Ba mai zuwa wurin Uba sai ta wurina. 7 Da kun san ni, da kun san Ubana ma. Amma daga yanzu kun san shi, kun kuma gan shi.” 8 Sai Filibus ya ce masa, “Ya Ubangiji, ka nuna mana Uban, bukatarmu ta biya ke nan.” 9 Yesu ya ce masa, “Na daɗe tare da ku haka, amma har yanzu ba ka san ni ba, Filibus! Duk wanda ya gan ni, ai, ya ga Uban. Yaya za ka ce, ‘Nuna mana Uban?’ ” 10 Wato, ba ka gaskata cikin Uba nake ba, Uba kuma cikina? Maganar da nake faɗa muku, ba domin kaina nake faɗa ba, Uba ne da yake zaune a cikina yake yin ayyukansa. 11 Ku gaskata ni, a cikin Uba nake, Uba kuma a cikina, ko kuwa ku gaskata ni saboda ayyukan su kansu. 12 “Lalle hakika, ina gaya muku, duk wanda yake gaskatawa da ni ayyukan da nake yi shi ma haka zai yi. Har ma, zai yi ayyukan da suka fi waɗannan, domin zan tafi wurin Uba. 13 Duk abin da kuka roƙa da sunana kuma zan yi, domin a ɗaukaka Uban ta wurin Ɗan. 14 Kome kuke roƙo da sunana, zan yi shi.”

Alkawarin Zuwan Ruhu Mai Tsarki

15 “In dai kuna ƙaunata, za ku bi umarnina. 16 Ni ma zan roƙi Uba, zai kuwa ba ku wani Mai Taimako ya kasance tare da ku har abada. 17 Shi ne Ruhu na gaskiya, wanda duniya ba ta iya samunsa, domin ba ta ganinsa, ba ta kuma san shi ba. Ku kam, kun san shi, domin yana zaune tare da ku, zai kuma kasance a zuciyarku. 18 “Ba zan bar ku marayu ba, zan zo wurinku. 19 Saura ɗan lokaci kaɗan duniya ba za ta ƙara ganina ba, amma ku za ku gan ni. Saboda ni a raye nake, ku ma za ku rayu. 20 A ran nan ne fa za ku sani, ni a cikin Uba nake, ku kuma a cikina, ni kuma a cikinku. 21 Duk wanda ya san umarnaina, yake kuma binsu, shi ne mai ƙaunata. Mai ƙaunata kuwa, Ubana zai ƙaunace shi, ni kuma zan ƙaunace shi, in bayyana kaina gare shi.” 22 Sai Yahuza (ba Iskariyoti ba) ya ce masa, “Ya Ubangiji, me ya sa za ka bayyana kanka gare mu, ba ga duniya ba?” 23 Yesu ya amsa masa ya ce, “Kowa yake ƙaunata, zai kiyaye maganata, Ubana kuwa zai ƙaunace shi, za mu zo wurinsa mu zauna tare da shi. 24 Wanda ba ya ƙaunata, ba zai kiyaye maganata ba. Maganar da kuke ji kuwa ba tawa ba ce, ta Uba ce wanda ya aiko ni. 25 “Duk wannan na faɗa muku ne tun muna tare. 26 Amma Mai Taimako, wato, Ruhu Mai Tsarki, wanda Uba zai aiko cikin sunana, shi ne zai koya muku kome, ya kuma tuna muku duk abin da na faɗa muku. 27 Na bar ku da salama. Salamata nake ba ku. Ba kamar yadda duniya take bayarwa nake ba ku ba. Kada ku damu, kada ku ji tsoro. 28 Kun dai ji na ce muku zan tafi, in kuma dawo wurinku. Da kuna ƙaunata da kun yi murna saboda za ni wurin Uba, domin kuwa Uban ya fi ni. 29 To, yanzu na faɗa muku tun bai faru ba, domin sa'ad da ya faru, ku ba da gaskiya. 30 Ba zan ƙara yi muku magana mai yawa ba, domin mai mulkin duniyar nan yana zuwa, ba shi kuwa da wani hannu a kaina, 31 sai dai domin duniya tă sani ina ƙaunar Uban, ina kuma yin yadda Uba ya umarce ni, ku tashi mu tafi daga nan.”

Yahaya 15

Yesu ne Itacen Inabi na Hakika

1 “Ni ne itacen inabi na hakika, Ubana kuwa shi ne manomi. 2 Kowane reshe a cikina da ba ya 'ya'ya, sai ya datse shi. Kowane reshe mai yin 'ya'ya kuwa yakan tsarkake shi don ya ƙara haihuwa. 3 Koyanzu ma ku tsarkakku ne saboda maganar da na faɗa muku. 4 Ku zauna a cikina, ni kuma a cikinku. Kamar yadda reshen inabi, ba ya iya 'ya'ya shi kaɗai, sai ko yana haɗe da itacen inabin, haka ku ma ba za ku iya ba, sai kun zauna a cikina. 5 Ni ne itacen inabin, ku kuwa rassan. Wanda ya zauna a cikina, ni kuma a cikinsa, shi ne mai yin 'ya'ya da yawa. Domin in ba game da ni ba, ba za ku iya kome ba. 6 Duk wanda bai zauna a cikina ba, za a yar da shi can, kamar reshe, yă bushe, a kuma tattara irinsu a jefa wuta, a ƙone. 7 In kun zauna a cikina, maganata kuma ta zauna a cikinku, za ku roƙi duk abin da kuke so, za a kuwa yi muku. 8 Yadda ake ɗaukaka Ubana ke nan, in kuna 'ya'ya da yawa, ta haka, kuma zaku tabbata almajiraina. 9 Kamar yadda Uba ya ƙaunace ni, haka ni ma na ƙaunace ku. To, ku zauna cikin ƙaunar da nake muku. 10 In kun bi umarnina, za ku zauna cikin ƙaunar da nake muku, kamar yadda ni na bi umarnin Ubana, na kuma zauna cikin ƙaunar da yake mini. 11 Na gaya muku haka domin farin cikina ya kasance a cikinku, farin cikinku kuma ya zama cikakke. 12 “Wannan fa shi ne umarnina, cewa, ku ƙaunaci juna kamar yadda na ƙaunace ku. 13 Ba ƙaunar da ta fi haka ga mutane, wato, mutum yă ba da ransa saboda aminansa. 14 Ku aminaina ne in kuna yin abin da na umarce ku. 15 Nan gaba, ba sauran in ce da ku bayi, don bawa bai san abin da ubangijinsa yake yi ba. Sai dai in ce da ku aminai, domin na sanar da ku duk abin da na jiyo wurin Ubana. 16 Ba ku kuka zaɓe ni ba, ni ne na zaɓe ku, na sa ku ku je ku yi 'ya'ya, 'ya'yanku kuma su tabbata, domin kome kuka roƙi Uba da sunana yă ba ku. 17 Na umarce ku haka domin ku ƙaunaci juna.

Ƙiyayyar Duniya

18 “In duniya ta ƙi ku, ku sani sai da ta ƙi ni kafin ta ƙi ku. 19 Da ku na duniya ne da duniya ta so abinta, amma saboda ku ba na duniya ba ne, na kuma zaɓe ku daga duniya, shi ya sa duniya take ƙinku. 20 Ku tuna da maganar da na yi muku cewa, ‘Bawa ba ya fin ubangijinsa.’ In sun tsananta mini, ku ma za su tsananta muku. Da sun kiyaye maganata, da sai su kiyaye taku ma. 21 Duk wannan za su yi muku saboda sunana, don ba su san wanda ya aiko ni ba. 22 Da ba domin na zo na yi musu magana ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu kam, ba su da wani hanzari a kan zunubinsu. 23 Wanda ya ƙi ni ya ƙi Ubana ma. 24 Da ba domin na yi ayyuka a cikinsu, da ba wanda ya taɓa yi sai ni ba, da ba su da zunubi. Amma yanzu sun gani, sun kuma ƙi mu, ni da Ubana duka. 25 An yi wannan kuwa domin a cika maganar da take a rubuce a cikin Shari'arsu cewa, ‘Sun ƙi ni ba dalili.’ 26 Amma sa'ad da Mai Taimako ya zo, wanda zan aiko muku daga wurin Uba, wato, Ruhu na gaskiya, mai fitowa daga wurin Uba, shi ne zai shaida ni. 27 Ku ma shaida ne, domin tun farko kuke tare da ni.

Yahaya 16

1 “Na faɗa muku waɗannan ne domin in kawar muku da sanadin tuntuɓe. 2 Za su fisshe ku daga jama'a. Hakika, lokaci ma yana zuwa da kowa ya kashe ku, zai zaci bautar Allah yake yi. 3 Za su yi haka ne kuwa, domin ba su san Uba ko ni ba. 4 Na faɗa muku waɗannan abubuwa ne, domin in lokacinsu ya yi ku tuna na faɗa muku.”

Aikin Ruhu Mai Tsarki

“Ban faɗa muku abubuwan tun da farko ba, domin ina tare da ku. 5 Yanzu kuwa za ni wurin wanda ya aiko ni, duk da haka a cikinku, ba wanda ya tambaye ni, ‘Ina za ka?’ 6 Amma saboda na faɗa muku waɗannan abubuwa, ga shi baƙin ciki ya cika zuciyarku. 7 Duk da haka ina gaya muku gaskiya, zai fiye muku in tafi, domin in ban tafi ba, Mai Taimakon nan ba zai zo gare ku ba. In kuwa na tafi, zan aiko shi gare ku. 8 Sa'ad da kuwa ya zo zai kā da duniya a kan zunubi, da adalci, da kuma hukunci. 9 Wato, a kan zunubi, domin ba su gaskata da ni ba, 10 a kan adalci kuwa, don za ni wurin Uba, ba kuwa za ku ƙara ganina ba, 11 a kan hukunci kuma, domin an yanke wa mai mulkin duniyar nan hukunci. 12 “Ina da sauran abubuwa da yawa da zan gaya muku tukuna, amma ba za ku iya ɗaukarsu a yanzu ba. 13 Sa'ad da kuwa Ruhu na gaskiya ya zo, zai bishe ku a cikin dukan gaskiya, domin ba zai yi magana don kansa ba, sai dai duk abin da ya ji, shi zai faɗa, zai kuma sanar da ku al'amuran da za su auku. 14 Zai ɗaukaka ni, domin zai ɗauko daga cikin abin da yake nawa ya sanar da ku. 15 Duk abin da Uba yake da shi, nawa ne. Shi ya sa na ce zai ɗauko daga cikin abin da yake nawa ya sanar da ku.”

Baƙin Ciki zai Koma Farin Ciki

16 “Bayan ɗan lokaci kaɗan, ba za ku gan ni ba, bayan ɗan lokaci kaɗan kuma, za ku gan ni.” 17 Sai waɗansu almajiransa suka ce wa juna, “Me yake nufi da ce mana, ‘Bayan ɗan lokaci kaɗan ba za ku gan ni ba, bayan ɗan lokaci kaɗan kuma za ku gan ni?’ da kuma cewa, ‘Domin za ni wurin Uba?’ ” 18 Suka ce, “Me yake nufi da, ‘Bayan ɗan lokaci kaɗan’ ɗin? Ai, ba mu san abin da yake faɗi ba.” 19 Yesu kuwa ya sani suna so su tambaye shi, sai ya ce musu, “Wato, kuna tambayar juna ne abin da nake nufi da cewa, ‘Bayan ɗan lokaci kaɗan ba za ku gan ni ba, bayan ɗan lokaci kaɗan kuma za ku gan ni?’ 20 Lalle hakika, ina gaya muku, za ku yi kuka da kuma gunji, amma duniya za ta yi farin ciki. Za ku yi baƙin ciki, amma baƙin cikinku zai koma farin ciki. 21 Idan mace tana naƙuda takan sha wuya, don lokacin haihuwarta ya yi. Amma da zarar ta haifi jinjirin, ba ta ƙara tunawa da wahalar da ta sha, domin murnar an sami baƙon duniya. 22 Haka ku ma yanzu kuke tare da baƙin ciki, amma zan sāke ganinku, sa'an nan zuciyarku za ta yi fari, ba kuwa mai ɗauke muku farin cikinku. 23 A ran nan, ba za ku yi mini wata tambaya ba. Lalle hakika, ina gaya muku, kome kuka roƙi Uba zai ba ku saboda sunana. 24 Har yanzu dai, ba ku roƙi komi cikin sunana ba. Ku roƙa, za ku samu, domin farin cikinku ya zama cikakke.”

Na yi Nasara da Duniya

25 “Duk waɗannan na faɗa muku da misalai ne. Lokaci yana zuwa da ba zan ƙara faɗa muku kome da misalai ba, sai dai in ba ku labarin Uba a sarari. 26 A ran nan za ku yi roƙo a cikin sunana. Ban kuwa ce muku zan roƙar muku Uba ba, 27 domin shi Uban kansa na ƙaunarku, domin kun ƙaunace ni, kun kuma gaskata daga wurin Uban na fito. 28 Daga wurin Uban ne na fito, na shigo duniya, har wa yau kuma zan bar duniya in koma wurin Uba.” 29 Sai almajiransa suka ce, “Yauwa! Yanzu ne fa kake magana a sarari, ba da misali ba. 30 Yanzu ne muka tabbata ka san kome, ba sai wani ya tambaye ka ba. Ta haka muka gaskata daga wurin Allah ka fito.” 31 Yesu ya amsa musu ya ce, “Ashe, yanzu kun gaskata? 32 To, lokaci yana zuwa, har ma ya yi, da za a warwatsa ku, kowa yă koma gidansu, ku bar ni ni kaɗai. Duk da haka kuwa ba ni kaɗai nake ba, domin Uba yana tare da ni. 33 Na faɗa muku wannan ne domin a gare ni ku sami salama. A duniya kuna shan wuya, amma dai ku yi farin ciki, ai, na yi nasara da duniya.”

Yahaya 17

Addu'ar Yesu don Almajiransa

1 Da Yesu ya faɗi haka, sai ya ɗaga kai sama ya ce, “Ya Uba, lokaci ya yi. Ka ɗaukaka Ɗanka domin Ɗan ya ɗaukaka ka, 2 tun da ka ba shi iko a kan dukkan 'yan adam, yă ba da rai madawwami ga duk waɗanda ka ba shi. 3 Rai madawwami kuwa, shi ne su san ka, Allah Makaɗaici na gaskiya, da kuma Yesu Almasihu da ka aiko. 4 Na ɗaukaka ka a duniya da yake na cika aikin da ka ba ni in yi. 5 Yanzu kuma, ya Uba, ka ɗaukaka ni zuwa ga zatinka da ɗaukakar nan da nake da ita tare da kai tun kafin duniya ta kasance. 6 “Na bayyana sunanka ga mutanen da ka ba ni daga cikin duniya. Dā ma naka ne, ka kuwa ba ni su, sun kuma kiyaye maganarka. 7 Yanzu kuwa sun san duk iyakar abin da ka ba ni daga gare ka yake. 8 Domin kuwa maganar da ka faɗa mini na faɗa musu, sun kuwa karɓa, sun kuma san hakika na fito daga wurinka ne, sun kuma gaskata kai ne ka aiko ni. 9 Ni, roƙo nake yi dominsu. Ba duniya nake roƙar wa ba, sai dai su waɗanda ka ba ni, domin su naka ne. 10 Dukkan nawa naka ne, duk naka kuma nawa ne, an kuma ɗaukaka ni a zukatansu. 11 Yanzu kuma ba sauran zamana a duniya, amma waɗannan a duniya suke, ni kuwa ina zuwa wurinka. Ya Uba Mai tsarki, ka kiyaye su da ikon sunanka da ka ba ni, su zama ɗaya kamar yadda muke. 12 Duk sa'ad da nake tare da su, na kiyaye su da ikon sunanka da ka ba ni. Na kāre su, ba kuwa waninsu da ya hallaka, sai dai hallakakken nan, domin Nassi ya cika. 13 Amma a yanzu ina zuwa wurinka. Ina faɗar wannan magana tun ina duniya, domin farin cikina ya zama cikakke a zukatansu. 14 Na faɗa musu maganarka, duniya kuwa ta ƙi su, domin su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne. 15 Ba na roƙonka ka ɗauke su daga duniya, sai dai ka kāre su daga Mugun nan. 16 Su ba na duniya ba ne, kamar yadda ni ma ba na duniya ba ne. 17 Ka tsarkake su cikin gaskiya. Maganarka ita ce gaskiya. 18 Kamar yadda ka aiko ni duniya, haka ni ma na aike su duniya. 19 Saboda su ne nake miƙa kaina, domin su ma a tsarkake su cikin gaskiya. 20 “Ba kuwa waɗannan kaɗai nake roƙar wa ba, har ma masu gaskatawa da ni ta wurin maganarsu, 21 domin dukansu su zama ɗaya, kamar yadda kai, ya Uba, kake cikina, ni kuma nake cikinka, haka su ma su kasance cikinmu, domin duniya ta gaskata, cewa, kai ne ka aiko ni. 22 Ɗaukakar da ka yi mini, ita na yi musu, domin su zama ɗaya kamar yadda muke ɗaya, 23 ni a cikinsu, kai kuma a cikina, domin su zama ɗaya sosai, duniya ta gane kai ne ka aiko ni, ta kuma gane ka ƙaunace su kamar yadda ka kaunace ni. 24 Ya Uba, ina so waɗanda ka ba ni, su ma su kasance tare da ni inda nake, su dubi ɗaukakata da ka yi mini, domin ka ƙaunace ni tun ba a halicci duniya ba. 25 Ya Uba mai adalci, duniya kam, ba ta san ka ba, amma ni na san ka, waɗannan kuma sun sani kai ne ka aiko ni. 26 Na sanar da su sunanka, zan kuma ci gaba da sanar masu, domin ƙaunar da ka yi mini tă kasance a cikinsu, ni ma in kasance a cikinsu.”

Yahaya 18

An Ba da Yesu, an Kama Shi

1 Bayan da Yesu ya yi maganar nan, ya fita, shi da almajiransa zuwa hayin Rafin Kidron, inda wani lambu yake, ya kuma shiga da almajiransa. 2 Yahuza ma wanda ya bāshe shi ya san wurin, domin Yesu ya saba haɗuwa da almajiransa a can. 3 Yahuza kuwa bayan ya ɗauko ƙungiyar soja, da waɗansu dogaran Haikali daga manyan firistoci da Farisiyawa, suka zo wurin, riƙe da fitilu, da jinyoyi, da makamai, 4 Yesu kuwa da ya san duk abin da zai same shi, ya yiwo gaba, ya ce musu, “Wa kuke nema?” 5 Suka amsa masa suka ce, “Yesu Banazare.” Yesu ya ce musu, “Ni ne.” Yahuza kuwa da ya bāshe shi yana tsaye tare da su. 6 Da Yesu ya ce musu, “Ni ne,” suka ja da baya da baya, har suka fāɗi. 7 Sai ya sāke tambayarsu, “Wa kuke nema?” Suka ce, “Yesu Banazare.” 8 Yesu ya amsa ya ce, “Ai, na gaya muku, ni ne. In kuwa ni kuke nema, ku bar waɗannan su tafi.” 9 Wannan kuwa domin a cika maganar da ya yi ne cewa, “A cikin waɗanda ka ba ni ban yar da ko ɗaya ba.” 10 Bitrus kuwa da yake yana da takobi, ya zaro ya kai wa bawan babban firist sara, ya fille masa kunnensa na dama. Sunan bawan Malkus. 11 Sai Yesu ya ce wa Bitrus, “Mai da takobinka kube. Ba sai in sha ƙoƙon da Uba ya ba ni in sha ba?”

Yesu a gaban Babban Firist

12 Sai ƙungiyar soja da shugabansu, da dogaran nan na Yahudawa suka kama Yesu, suka ɗaure shi, 13 suka tafi da shi wurin Hanana da fari, don shi surukin Kayafa ne, wanda yake shi ne babban firist a shekarar nan. 14 Kayafa kuwa shi ne ya yi wa Yahudawa shawara, cewa, ya fiye musu mutum ɗaya ya mutu saboda jama'a. 18 .15 Bitrus ya Yi M�sun Sanin Yesu Bitrus ya Yi M�sun Sanin Yesu 15 Sai Bitrus ya bi bayan Yesu, haka kuma wani almajiri. Almajirin nan kuwa sananne ne ga babban firist, sai ya shiga har gidan firist ɗin tare da Yesu, 16 Bitrus kuwa ya tsaya a bakin ƙofa daga waje. Sai ɗaya almajirin da yake sananne ga babban firist ya fita, ya yi magana da wanda yake jiran ƙofa, sa'an nan ya shigo da Bitrus. 17 Baranyar da yake jiran ƙofar kuwa ta ce wa Bitrus, “Anya! Kai ma ba a cikin almajiran mutumin nan kake ba?” Ya ce, “A'a, ba na ciki.” 18 To, barori da dogaran Haikali kuwa sun hura wutar gawayi, don ana sanyi, suna tsaitsaye, suna jin wutar. Bitrus ma yana tsaye tare da su yana jin wutar.

Babban Firist ya Tuhumi Yesu

19 Sai babban firist ya tuhumi Yesu a kan almajiransa da kuma koyarwarsa. 20 Yesu ya amsa masa ya ce, “Ai, na yi wa duniya magana a bayyane, na kuma sha koyarwa a majami'u da Haikali inda Yahudawa duka sukan taru. Ban faɗi kome a ɓoye ba. 21 Don me kake tuhumata? Tuhumi waɗanda suka saurare ni a kan abin da na faɗa musu, ai, sun san abin da na faɗa.” 22 Da ya faɗi haka, wani daga cikin dogaran da suke tsaye kusa, ya mari Yesu, ya ce, “Haka za ka amsa wa babban firist?” 23 Yesu ya amsa masa ya ce, “In na faɗi mugun abu to, ka ba da shaida kan haka. In kuwa daidai na faɗa, to, don me za ka mare ni?” 24 Sai Hanana ya aika da shi a ɗaure wurin Kayafa, babban firist. 18 .25 Bitrus ya Sāke M�sun Sanin Yesu Bitrus ya Sāke M�sun Sanin Yesu 25 To, Bitrus kuwa yana tsaye yana jin wuta. Sai suka ce masa, “Anya! Kai ma ba a cikin almajiransa kake ba?” Sai ya yi m�su ya ce, “A'a, ba na ciki.” 26 Sai wani daga cikin bayin babban firist, wato, dangin wanda Bitrus ya fille wa kunne, ya ce, “Ashe, ban gan ka tare da shi a lambun ba?” 27 Sai Bitrus ya sāke yin m�su. Nan da nan kuwa zakara ya yi cara.

Yesu a gaban Bilatus

28 Daga wurin Kayafa kuma suka kai Yesu fādar mai mulki. Da asuba ne kuwa. Su kansu ba su shiga fādar ba, don kada su ƙazantu su kāsa cin jibin Ƙetarewa. 29 Saboda haka, Bilatus ya fito wajensu, ya ce, “Wace ƙara kuka kawo ta mutumin nan?” 30 Sai suka amsa masa suka ce, “Da wannan ba mai laifi ba ne, ai, da ba mu bāshe shi gare ka ba.” 31 Bilatus ya ce musu, “Ku tafi da shi da kanku mana, ku hukunta shi bisa ga shari'arku!” Sai Yahudawa suka ce masa, “Ai, ba mu da ikon zartar da hukuncin kisa a kan kowa.” 32 Wannan kuwa don a cika maganar da Yesu ya yi ne, wadda ta kwatanta irin mutuwar da zai yi. 33 Sai Bilatus ya koma cikin fāda, ya kira Yesu ya ce masa, “Ashe, kai ɗin nan, kai ne Sarkin Yahudawa?” 34 Yesu ya amsa ya ce, “Wato, wannan faɗarka ce, ko kuwa waɗansu ne suka ce da ni haka a wurinka?” 35 Bilatus ya amsa ya ce, “Ni Bayahude ne? Ai, jama'arku da manyan firistoci su ne suka bāshe ka gare ni. Me ka yi?” 36 Yesu ya amsa ya ce, “Mulkina ba na duniyar nan ba ne. Da mulkina na duniyar nan ne da barorina za su yi yaƙi kada a bāshe ni ga Yahudawa. Amma hakika, mulkina ba daga nan yake ba.” 37 Sai Bilatus ya ce masa, “Wato, ashe, sarki ne kai?” Yesu ya amsa ya ce, “Yadda ka faɗa, ni sarki ne. Domin haka musamman aka haife ni, don haka kuma musamman na shigo duniya, domin in shaidi gaskiya. Kowane mai ƙaunar gaskiya kuwa yakan saurari muryata.” 38 Bilatus ya ce masa, “Wane abu ne, shi gaskiya?”

An Hukunta wa Yesu Mutuwa

Bayan da ya faɗi haka, ya sāke fitowa wurin Yahudawa, ya ce musu, “Ni kam, ban same shi da wani laifi ba. 39 Amma dai kuna da wata al'ada, in Idin Ƙetarewa ya yi, nakan sakar muku mutum ɗaya. To, kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?” 40 Sai suka sāke ɗaukar kururuwa suna cewa, “A'a, ba wannan ba, sai dai Barabbas!” Barabbas ɗin nan kuwa ɗan fashi ne.

Yahaya 19

1 Sa'an nan Bilatus ya sa a tafi da Yesu, a yi masa bulala. 2 Sai soja suka yi wani kambi na ƙaya suka sa masa a kā, suka yafa masa wata alkyabba mai ruwan shunayya. 3 Suka yi ta zuwa wurinsa, suna cewa, “Ranka ya daɗe, Sarkin Yahudawa!” suna ta marinsa. 4 Sai Bilatus ya sāke fitowa, ya ce wa Yahudawa, “Ga shi, zan fito muku da shi, domin ku san ban same shi da wani laifi ba.” 5 Sa'an nan Yesu ya fito, sāye da kambin ƙayar, da alkyabba mai ruwan shunayya. Sai Bilatus ya ce musu, “To, ga mutumin!” 6 Da manyan firistoci da dogaran Haikali suka gan shi, suka ɗau kururuwa suna cewa, “A gicciye shi! A gicciye shi!” Bilatus ya ce musu, “Ku tafi da shi ku da kanku, ku gicciye shi, ni kam, ban same shi da wani laifi ba.” 7 Yahudawa suka amsa masa suka ce, “Ai, muna da Shari'a, bisa ga Shari'ar nan kuwa ya wajaba a kashe shi, saboda ya mai da kansa Ɗan Allah.” 8 Da Bilatus ya ji maganar nan sai ya ƙara tsorata. 9 Ya sāke shiga fāda, ya ce wa Yesu, “Daga ina kake?” Amma Yesu bai amsa masa ba. 10 Saboda haka Bilatus ya ce masa, “Ba za ka yi mini magana ba? Ba ka sani ba ni ne da ikon sakinka, ko gicciye ka?” 11 Yesu ya amsa masa ya ce, “Ba ka da wani iko a kaina in ba an ba ka daga Sama ba, saboda haka wanda ya bāshe ni gare ka ya fi ka zunubi.” 12 A kan wannan Bilatus ya nema ya sake shi, sai dai Yahudawa suka ɗau kururuwa suna cewa, “In dai ka saki wannan, kai ba masoyin Kaisar ba ne. Ai, kowa ya mai da kansa sarki, ya tayar wa Kaisar ke nan.” 13 Da Bilatus ya ji wannan magana, sai ya fito da Yesu, ya zauna a kan gadon shari'a, wurin da ake kira Daɓe, da Yahudanci kuwa, Gabbata. 14 Ran nan kuwa ranar shirin Idin Ƙetarewa ce, wajen tsakiyar rana. Sai ya ce wa Yahudawa, “Ga sarkinku!” 15 Sai suka ɗau kururuwa suna cewa, “A yi da shi! A yi da shi! A gicciye shi!” Bilatus ya ce musu, “A! In gicciye sarkinku?” Sai manyan firistoci suka amsa suka ce, “Mu ba mu da sarki sai Kaisar.” 16 Sa'an nan ya bāshe shi gare su su gicciye shi.

An Gicciye Yesu

17 Sai suka tafi da Yesu. Ya kuwa fita, shi kansa yake ɗauke da gicciyensa, har zuwa wurin da ake kira Wurin Ƙoƙon Kai, da Yahudanci kuwa, Golgota. 18 Nan suka gicciye shi, da kuma waɗansu mutum biyu tare da shi, ɗaya ta kowane gefe, Yesu kuwa a tsakiya. 19 Bilatus kuma ya rubuta wata sanarwa, ya kafa ta a kan gicciyen. Abin da aka rubuta ke nan, “Yesu Banazare Sarkin Yahudawa.” 20 Yahudawa da yawa kuwa sun karanta wannan sanarwa, domin wurin da aka gicciye Yesu kusa da birni ne. An kuwa rubuta ta da Yahudanci, da Romanci, da kuma Helenanci. 21 Sai manyan firistocin Yahudawa suka ce wa Bilatus, “Kada ka rubuta ‘Sarkin Yahudawa,’ sai dai ka rubuta, ‘A faɗarsa shi ne Sarkin Yahudawa.’ ” 22 Bilatus ya amsa ya ce, “Abin da na rubuta na rubuta ke nan.” 23 Bayan soja sun gicciye Yesu, suka ɗibi tufafinsa, suka kasa kashi huɗu, kowane soja ya ɗauki kashi guda. Suka kuma ɗauki taguwarsa, taguwar kuwa ba ɗinki, saƙa ɗaya ce gudanta. 24 Sai suka ce wa juna, “Kada mu tsaga ta, sai dai mu yi kuri'a a kanta, mu ga wanda zai ci.” Wannan kuwa domin a cika Nassi ne cewa, “Suka rarraba tufafina a tsakaninsu, suka jefa kuri'a akan rigata” 25 Haka fa sojan suka yi. To, kusa da gicciyen Yesu kuwa da mahaifiyarsa, da 'yar'uwarta, da Maryamu matar Kilofas, da kuma Maryamu Magadaliya, suna tsaye. 26 Da Yesu ya ga mahaifiyarsa, da almajirin nan da yake ƙauna suna tsaye kusa, ya ce wa mahaifiyarsa, “Iya, ga ɗanki nan!” 27 Sa'an nan ya ce wa almajirin, “Ga tsohuwarka nan!” Tun daga wannan lokaci fa almajirin nan ya kai ta gidansa.

Mutuwar Yesu

28 Bayan haka, Yesu da ya san duk an gama kome, domin a cika Nassi sai ya ce, “Ina jin ƙishirwa.” 29 To, akwai wani gora cike da ruwan tsami a ajiye a nan. Sai suka jiƙa soso da ruwan tsamin, suka soka a sandan izob suka kai bakinsa. 30 Da Yesu ya tsotsi ruwan tsamin nan ya ce, “An gama!” Sa'an nan ya sunkuyar da kansa ya ba da ransa.

An Soki Kwiɓin Yesu

31 Da yake ran nan ranar shiri ce, don kada a bar jikuna a gicciye ran Asabar (domin wannan Asabar ɗin babbar rana ce), sai Yahudawa suka roƙi Bilatus a karya ƙafafunsu, a kuma ɗauke jikunan. 32 Sai soja suka zo suka karya ƙafafun na farkon nan, da kuma na ɗayan da aka gicciye tare da shi. 33 Amma da suka zo wurin Yesu, suka kuma ga ya riga ya rasu, ba su karya ƙafafunsa ba. 34 Sai dai ɗaya daga cikin sojan nan ya soke shi da mashi a kwiɓi, nan da nan sai ga jini da ruwa suka gudano. 35 Wanda ya gani ɗin kuwa shi ya ba da shaida kan haka, shaidarsa kuwa gaskiya ce, ya kuma san gaskiya yake faɗa, domin ku ma ku ba da gaskiya. 36 Wannan kuwa don a cika Nassi ne cewa, “Ko ƙashinsa ɗaya ba za a karya ba.” 37 Wani Nassi kuma ya ce, “Za su dubi wanda suka soka.”

Jana'izar Yesu

38 Bayan haka Yusufu, mutumin Arimatiya, wanda yake almajirin Yesu ne amma a ɓoye domin tsoron Yahudawa, ya roƙi Bilatus izinin ɗauke Yesu. Bilatus kuwa ya ba shi izini, ya kuwa zo ya ɗauke jikin Yesu. 39 Nikodimu kuma, wanda zuwansa na farko wurin Yesu da dad dare ne, ya zo da mur da al'ul a gauraye, wajen awo ɗari. 40 Sai suka ɗauki jikin Yesu suka sa shi a likkafanin lilin game da kayan ƙanshin nan, bisa ga al'adar Yahudawa ta jana'iza. 41 A wurin da aka gicciye shi kuwa akwai wani lambu, a cikin lambun kuma da wani sabon kabari wanda ba a taɓa sa kowa a ciki ba. 42 Da yake ranar shiri ce ta Yahudawa, kabarin kuma yana kusa, sai suka sa Yesu a nan.

Yahaya 20

Tashin Yesu daga Matattu

1 To, a ranar farko ta mako, Maryamu Magadaliya ta je kabarin da asuba, tun da sauran duhu, ta ga an kawar da dutsen daga kabarin. 2 Sai ta yiwo gudu wurin Bitrus da kuma almajirin nan da Yesu yake ƙauna, ta ce musu, “An ɗauke Ubangiji daga kabarin, ba mu kuwa san inda aka sa shi ba.” 3 Sai Bitrus da almajirin nan suka fita suka doshi kabarin. 4 Duka biyu suka ruga a guje, amma almajirin nan ya tsere wa Bitrus, ya riga isa kabarin. 5 Yana duƙawa yana leƙa ciki, sai ya ga likkafanin lilin a ajiye, amma fa bai shiga ba. 6 Sa'an nan Bitrus ya zo a bayansa, ya kuwa shiga kabarin, ya ga likkafanin a ajiye, 7 mayanin kuma da yake kansa ba a ajiye tare da likkafanin yake ba, amma a naɗe shi kaɗai a waje ɗaya. 8 Sai almajirin nan da ya riga isa kabarin shi ma ya shiga, ya gani, ya kuma ba da gaskiya. 9 Don kafin lokacin nan ba su fahimci Nassin nan ba, cewa, lalle ne yă tashi daga matattu. 10 Sai almajiran suka koma gida.

Yesu ya Bayyana ga Maryamu Magadaliya

11 Maryamu kuwa tana tsaye a bakin kabarin daga waje, tana kuka. Tana cikin kuka sai ta duƙa, ta leƙa kabarin, 12 sai ta ga mala'iku biyu saye da fararen tufafi a zaune inda dā gawar Yesu take, ɗaga wajen kai, ɗaya kuwa wajen ƙafafu. 13 Suka ce mata, “Uwargida, don me kike kuka?” Ta ce musu, “Ai, an ɗauke Ubangijina, ban kuwa san inda aka sa shi ba.” 14 Da ta faɗi haka sai ta juya ta ga Yesu tsaye, amma ba ta gane Yesu ne ba. 15 Yesu ya ce mata, “Uwargida, don me kike kuka? Wa kuma kike nema?” Saboda kuma ta zaci shi ne mai aikin lambun, ta ce masa, “Maigida, in kai ne ka ɗauke shi, gaya mini inda ka sa shi mana, ni kuwa in ɗauke shi.” 16 Yesu ya ce mata, “Maryamu!” Sai ta juya ta ce masa da Yahudanci, “Rabboni!” wato, Malam. 17 Yesu ya ce mata, “Kada ki riƙe ni, domin har yanzu ban hau wurin Uba ba tukuna. Sai dai ki tafi wurin 'yan'uwana ki ce musu ina hawa wurin Ubana kuma Ubanku, Allahna kuma Allahnku.” 18 Sai Maryamu Magadaliya ta je ta ce wa almajiran, “Na ga Ubangiji!” Ta kuma ce shi ya faɗa mata waɗannan abubuwa.

Yesu ya Bayyana ga Almajiransa

19 A ran nan da magariba, ranar farko ta mako, ƙofofin ɗakin da almajiran suke ciki yana kulle sabo da tsoron Yahudawa, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsaka, ya ce musu, “Salama a gare ku!” 20 Da ya faɗi haka, ya nuna musu hannuwansa da kwiɓinsa. Sai almajiran suka yi farin ciki da ganin Ubangiji. 21 Sai Yesu ya sāke ce musu, “Salama a gare ku! Kamar yadda Uba ya aiko ni, haka ni ma na aike ku.” 22 Da ya faɗi haka ya busa musu numfashinsa, ya ce musu, “Ku karɓi Ruhu Mai Tsarki. 23 Duk waɗanda kuka gafarta wa zunubansu, an gafarta musu ke nan. Duk waɗanda ba ku gafarta wa ba kuwa, ba a gafarta ba ke nan.”

Rashin Bangaskiyar Toma

24 Toma kuwa, ɗaya daga cikin goma sha biyun nan, wanda ake kira Ɗan Tagwai, ba ya nan tare da su sa'ad da Yesu ya zo. 25 Sai sauran almajiran suka ce masa, “Mun ga Ubangiji.” Amma ya ce musu, “In ban ga gurbin ƙusoshi a hannuwansa ba, in sa yatsata a gurbin ƙusoshin, in kuma sa hannuna a kwiɓinsa ba, ba zan ba da gaskiya ba.” 26 Bayan kwana takwas har wa yau almajiransa na cikin gidan, Toma ma yana nan tare da su, ƙofofi suna kulle, sai ga Yesu ya zo ya tsaya a tsaka, ya ce, “Salama a gare ku.” 27 Sa'an nan ya ce wa Toma, “Sa yatsarka nan, ka ji hannuwana. Miƙo hannunka kuma ka sa a kwiɓina. Kada ka zama marar ba da gaskiya, sai dai mai ba da gaskiya.” 28 Toma ya amsa masa ya ce, “Ya Ubangijina da kuma Allahna!” 29 Sai Yesu ya ce masa, “Wato, saboda ka gan ni ka ba da gaskiya? Albarka tā tabbata ga waɗanda ba su gani ba, amma kuwa suka ba da gaskiya.”

Manufar Littafin Nan

30 Yesu ya yi waɗansu mu'ujizai da yawa dabam dabam a gaban almajiran, waɗanda ba a rubuta a littafin nan ba. 31 Amma an rubuta waɗannan ne, domin ku ba da gaskiya Yesu shi ne Almasihu, Ɗan Allah, ta wurin gaskatawa kuma ku sami rai a cikin sunansa.

Yahaya 21

Yesu ya Bayyana ga Almajirai Bakwai

1 Bayan haka Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiran a bakin Tekun Tibariya. Ga kuwa yadda ya bayyana kansa. 2 Bitrus, da Toma wanda ake kira Ɗan Tagwai, da Nata'ala na Kana ta ƙasar Galili, da 'ya'yan nan na Zabadi, da kuma waɗansu almajiransa biyu, duk suna nan tare, 3 Sai Bitrus ya ce musu, “Za ni s�.” Suka ce masa, “Mu ma mā tafi tare da kai.” Sai suka fita suka shiga jirgi. Amma a daren nan ba su kama kome ba. 4 Gari yana wayewa sai ga Yesu tsaye a bakin gaci, amma almajiran ba su gane Yesu ne ba. 5 Sai Yesu ya ce musu, “Samari, kuna da kifi?” Suka amsa masa suka ce, “A'a.” 6 Ya ce musu, “Ku jefa taru dama da jirgin za ku samu.” Suka jefa, har suka kāsa jawo shi don yawan kifin. 7 Sai almajirin nan da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ubangiji ne fa!” Da Bitrus ya ji, ashe, Ubangiji ne sai ya yi ɗamara da taguwarsa, don a tuɓe yake, ya fāɗa tekun. 8 Sauran almajirai kuwa suka zo a cikin ƙaramin jirgi, janye da tarun cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, kamar misalin kamu ɗari biyu ne. 9 Da fitowarsu gaci sai suka ga garwashi a wurin, da kifi, da kuma gurasa. 10 Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifi daga cikin waɗanda kuka kama yanzu.” 11 Sai Bitrus ya hau jirgin, ya jawo tarun gaci, cike da manyan kifaye dari da hamsin da uku. Amma duk da yawansu haka, tarun bai kece ba. 12 Sai Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Daga cikin almajiran kuwa ba wanda ya yi ƙarfin halin tambayarsa ko shi wane ne, domin sun sani Ubangiji ne. 13 Sai Yesu ya zo ya ɗauki gurasar, ya ba su, haka kuma kifin. 14 Wannan ne fa zuwa na uku da Yesu ya bayyana ga almajiran bayan an tashe shi daga matattu.

Yi Kiwon Tumakina

15 Da suka karya kumallo Yesu ya ce wa Bitrus, “Bitrus ɗan Yahaya, ka fi waɗannan ƙaunata?” Ya ce masa, “I, ya Ubangiji, ka dai sani ina sonka.” Yesu ya ce masa, “Ka yi kiwon 'ya'yan tumakina.” 16 Ya sāke faɗa masa, faɗa ta biyu, “Bitrus ɗan Yahaya, kana ƙaunata?” Ya ce masa, “I, ya Ubangiji, ka dai sani ina sonka.” Yesu ya ce masa, “Ka kiyaye tumakina.” 17 Yesu ya faɗa masa, faɗa ta uku, “Bitrus ɗan Yahaya, kana sona?” Sai Bitrus ya yi baƙin ciki don a faɗar nan ta uku ya ce masa, “Kana sona?” Shi kuwa ya ce masa, “Ya Ubangiji, ai, ka san kome duka, ka kuwa sani ina sonka.” Yesu ya ce masa, “Ka yi kiwon tumakina. 18 Lalle hakika, ina gaya maka, lokacin samartakarka kakan yi wa kanka ɗamara, ka tafi inda ka nufa, amma in ka tsufa, za ka miƙe hannuwanka, wani ya yi maka ɗamara, ya kai ka inda ba ka nufa ba.” 19 (Ya faɗi wannan ne yana kwatanta irin mutuwar da Bitrus zai yi ya ɗaukaka Allah.) Bayan ya faɗi haka, ya ce masa, “Bi ni.”

Almajirin da Yesu yake Ƙauna

20 Sai Bitrus ya waiwaya ya ga almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana biye da su, wato, wanda ya jingina gab da Yesu lokacin cin jibin nan da ya ce, “Ya Ubangiji, wane ne zai bāshe ka?” 21 Da Bitrus ya gan shi, ya ce wa Yesu, “Ya Ubangiji, wannan fa?” 22 Yesu ya ce masa, “In na nufe shi da wanzuwa har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai, bi ni!” 23 Saboda haka maganar nan ta bazu cikin 'yan'uwa, cewa, almajirin nan ba zai mutu ba. Alhali kuwa Yesu bai ce masa ba zai mutu ba, ya dai ce, “In na nufe shi da wanzuwa har in zo, mene ne naka a ciki?” 24 Wannan shi ne almajirin da yake ba da shaida a kan waɗannan al'amura, ya kuma rubuta su, mun kuwa sani shaidarsa tabbatacciya ce. 25 Akwai waɗansu ayyuka kuma masu yawa da Yesu ya aikata, in da za a rubuta ko wannensu ɗaya ɗaya da ɗaya ɗaya, ina tsammani ko duniya kanta ba za ta iya ɗaukar littattafan da za a rubuta ba.

Ayyukan Manzanni 1

Alkawarin Zuwan Ruhu Mai Tsarki

1 Ya Tiyofalas, tarihin nan na farko wanda na rubuta, ya shafi dukan abubuwan da Yesu ya fara yi, da kuma waɗanda ya fara koyarwa, 2 har ya zuwa ranar da aka ɗauke shi aka kai shi Sama, bayan da ya yi umarni ta wurin Ruhu Mai Tsarki ga manzannin da ya zaɓa. 3 Ya bayyana kansa gare su a raye bayan shan wuyarsa, tare da tabbatarwa masu yawa, masu ƙarfi kuma, yana bayyana a gare su a kai a kai har kwana arba'in, yana zancen al'amuran Mulkin Allah. 4 Sa'ad da yake tare da su, ya umarce su kada su tashi daga Urushalima, amma su jira cikar alkawarin nan da Uba ya yi, “Wanda kuka ji daga bakina, 5 domin Yahaya kam, da ruwa ya yi baftisma, amma kafin 'yan kwanaki da Ruhu Mai Tsarki za a yi muku baftisma.”

An Ɗauke Almasihu zuwa Sama

6 Saboda haka da suka taru, suka tambaye shi suka ce, “Ya Ubangiji, yanzu ne za ka sāke kafa wa Isra'ila mulki?” 7 Ya ce musu, “Sanin lokatai da zamanai, da Uba ya sa cikin ikonsa, ba naku ba ne. 8 Amma za ku sami iko sa'ad da Ruhu Mai Tsarki ya sauko muku, za ku kuma zama shaiduna a Urushalima, da duk ƙasar Yahudiya, da ta Samariya, har ya zuwa iyakar duniya.” 9 Da ya faɗi haka, suna cikin dubawa, sai aka ɗauke shi Sama, wani gajimare ya tafi da shi, ba su ƙara ganinsa ba. 10 Suna cikin zuba ido a sama, shi kuma yana tafiya, sai ga mutum biyu tsaye kusa da su, saye da fararen tufafi. 11 Sai suka ce, “Ya ku mutanen Galili, don me kuke tsaye kuna duban sama? Yesun nan da aka ɗauke daga gare ku aka kai shi zuwa Sama, zai komo ne ta yadda kuka ga tafiyarsa zuwa Sama.”

Wanda ya Karɓi Matsayin Yahuza

12 Sai suka koma Urushalima daga dutsen nan da ake kira Dutsen Zaitun, wanda yake kusa da Urushalima, wajen mil ɗaya. 13 Da suka shiga birnin, suka hau soro inda suke zama, wato Bitrus, da Yahaya, da Yakubu, da Andarawas, da Filibus, da Toma, da Bartalamawas, da Matiyu, da Yakubu na Halfa, da Saminu Zaloti, da kuma Yahuza na Yakubu. 14 Duk waɗannan da nufi ɗaya suka nace da addu'a, tare da mata, da Maryamu uwar Yesu, da kuma 'yan'uwansa. 15 To, a kwanakin nan Bitrus ya miƙe tsaye cikin 'yan'uwa, (wajen mutum ɗari da ashirin ne a taron), ya ce, 16 “Ya ku 'yan'uwana, lalle ne a cika Nassin nan da Ruhu Mai Tsarki ya faɗa a dā ta bakin Dawuda a game da Yahuza, wanda ya yi wa masu kama Yesu jagaba. 17 Don an lasafta shi cikinmu dā, an kuma ba shi tasa hidima cikin aikin nan. 18 (To, shi mutumin nan, da ladan mugun aikinsa ya sayi wani fili, sai ya fāɗi da kā, cikinsa ya fashe, kayan cikinsa duk suka zubo. 19 Wannan abu fa ya zama sananne ga dukan mazaunan Urushalima, har ake kiran filin Akaldama harshensu, wato filin jini.) 20 Domin a rubuce yake a Zabura cewa, ‘Gidansa yă zama yasasshe, Kada kowa ya zauna a ciki.’ Da kuma, ‘Matsayinsa wani yă gada.’ 21 Don haka, lalle wani daga cikin mutanen nan da suke tare da mu, duk lokacin da Ubangiji Yesu yake cuɗanya da mu, 22 tun daga baftismar da Yahaya ya yi, har ya zuwa ranar da aka ɗauke shi daga wurinmu aka kai shi zuwa Sama, wato ɗaya daga cikin mutanen nan ya zama shaidar tashinsa daga matattu, tare da mu.” 23 Sai suka nuna mutum biyu, Yusufu mai suna Barsaba, wanda aka yi wa laƙabi da Yustus, da kuma Matiyas. 24 Sai suka yi addu'a, suka ce, “Ya Ubangiji, masanin zuciyar kowa, a cikin waɗannan mutum biyu ka nuna wanda ka zaɓa, 25 yă karɓi matsayi cikin aikin nan da manzancin nan da Yahuza ya bauɗe wa, don yă cike gurbinsa.” 26 Sai suka yi musu kuri'a, Matiyas ya ci, aka kuma sa shi a cikin manzannin nan goma sha ɗaya.

Ayyukan Manzanni 2

Zuwan Ruhu Mai Tsarki

1 Da ranar Fentikos ta yi, duk suna tare a wuri ɗaya, 2 farat ɗaya, sai aka ji wani amo daga sama, kamar na busowar gawurtacciyar iska, ya cika duk gidan da suke zaune. 3 Sai waɗansu harsuna kamar na wuta suka bayyana a gare su, suna rarrabuwa, suna sassauka a kan ko wannensu. 4 Sai duk, aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka kuma fara magana da waɗansu harsuna dabam dabam, gwargwadon yadda Ruhun ya yi musu baiwar yin magana. 5 To, a Urushalima a lokacin, akwai waɗansu Yahudawa masu bautar Allah daga ko'ina cikin ƙasashen duniya. 6 Da jin dirin nan kuwa, taron ya haɗe, ya ruɗe, domin ko wannensu ya ji suna magana da harshen garinsu. 7 Sai suka yi al'ajabi suka yi mamaki, suna cewa, “Ashe, duk masu maganar nan ba Galilawa ba ne? 8 Ƙaƙa kuwa ko wannenmu yake ji da harshen garinsu ake magana? 9 Ga mu kuwa, Fartiyawa, da Madayanawa, da Elamawa, da mutanen ƙasar Bagadaza, da ne Yahudiya, da na Kafadokiya, da na Fantas, da na Asiya, 10 da na Firijiya, da na Bamfiliya, da na Masar, da kuma na kewayen Kurane ta ƙasar Libiya, har ma da baƙi daga Roma, wato Yahudawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, 11 da kuma Karitawa, da Larabawa, duk muna ji suna maganar manyan al'amuran Allah da harshen garuruwanmu.” 12 Duk kuwa suka yi mamaki, suka ruɗe, suna ce wa juna, “Me ke nan kuma?” 13 Amma waɗansu suka yi ba'a suka ce, “Ruwan inabi suka sha suka yi tatil!”

Jawabin Bitrus a Ranar Fentikos

14 Amma Bitrus ya miƙe tare da sha ɗayan nan, ya ɗaga murya ya yi musu jawabi, ya ce, “Ya ku 'yan'uwana Yahudawa da dukan mazaunan Urushalima, ku kula da wannan, ku kuma saurari maganata. 15 Ai, mutanen nan ba bugaggu ba ne yadda kuke zato, tun da ya ke yanzu ƙarfe tare na safe ne kawai. 16 Wannan, ai, shi ne abin da Annabi Yowel ya faɗa cewa, 17 ‘Allah ya ce, A zamanin karshe zai zamanto zan zubo wa dukan 'yan adam Ruhuna. 'Ya'yanku mata da maza za su yi annabci, Wahayi zai zo wa samarinku, Dattawanku kuma za su yi mafarkai. 18 Hakika, har ma a kwanakin nan zan zubo Ruhuna a kan bayina mata da maza, Za su kuma yi annabci. 19 Zan nuna abubuwan al'ajabi a sararin sama, Da mu'ujizai a nan ƙasa, Wato jini, da wuta, da kuma, hauhawan hayaƙi. 20 Za a mai da rana duhu, Wata kuma jini, Kafin Ranar Ubangiji ta zo, Babbar ranar nan mai girma. 21 A sa'an nan ne zai zamanto kowa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.’ 22 “Ya ku 'yan'uwa, Isra'ilawa, ku ji wannan magana. Yesu Banazare, mutumin da Allah ya tabbatar muku cewa shi yardajjensa ne, ta mu'ujizai, da abubuwan al'ajabi, da alamu waɗanda ya yi ta wurinsa a cikinku, kamar yadda ku kanku kuka sani, 23 shi Yesun nan fa, an ba da shi bisa ƙaddarar Allah da rigyasaninsa, ku kuwa kuka gicciye shi, kuka kashe shi, ta hannun masu zunubi. 24 Amma Allah ya tashe shi bayan ya ɓalle masa ƙangin mutuwa, domin ba shi yiwuwa mutuwa ta riƙe shi. 25 Dawuda kuma ya yi faɗi a game da shi ya ce, ‘Kullum hankalina yana kan Ubangiji, Yana damana, domin kada in jijjigu. 26 Saboda haka, zuciyata ta yi fari, ina farin ciki matuƙa. Ko da yake kuma ni jiki ne, zan zauna ina sa zuciya, 27 Domin ba za ka yar da raina a Hades ba, Ba kuwa za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba. 28 Kā sanar da ni hanyoyin rai. Za ka cika ni da farin ciki ta zamana a zatinka.’ 29 Ya 'yan'uwa, na iya yi muku magana da amincewa a game da kakanmu Dawuda, cewa ya mutu, an binne shi, kabarinsa kuma yana nan gare mu har ya zuwa yau. 30 To, da ya ke shi annabi ne, ya kuma san Allah ya rantse masa, cewa zai ɗora wani daga cikin zuriyarsa kan kursiyinsa, 31 sai ya hango, ya kuma yi faɗi a kan tashin Almasihu daga matattu, cewa ba za a yashe shi a Hades ba, jikinsa kuwa ba zai ruɓa ba. 32 Yesun nan kam, Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa duk shaidu ne ga haka. 33 Da yake an ɗaukaka shi a dama ga Allah, ya kuma sami cikar alkawarin nan na baiwar Ruhu Mai Tsarki daga wurin Uba, sai ya zubo da wannan da kuke gani, kuke kuma ji. 34 Ai, ba Dawuda ne ya hau Sama ba, amma shi kansa ya ce, ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina, Zauna a damana, 35 Sai na sa ka tāke maƙiyanka.’ 36 “Don haka sai duk jama'ar Isra'ila su sakankance, cewa shi Yesun na da kuka gicciye, Allah ya mai da shi Ubangiji, da kuma Almasihu.” 37 To, da suka ji haka, maganar ta soke su a zuci, suka ce wa Bitrus da sauran manzannin, “'Yan'uwa, me za mu yi?” 38 Sai Bitrus ya ce musu, “Sai ku tuba, a yi wa ko wannenku baftisma, a kan kun yarda da sunan Yesu Almasihu, domin a gafarta zunubanku, za ku kuwa sami baiwar Ruhu Mai Tsarki, 39 domin alkawarin nan ku aka yi wa, ku da 'ya'yanku, da kuma dukan manisanta, wato duk waɗanda Ubangiji Allahnmu ya kira.” 40 Sai ya yi ta tabbatar musu da maganganu masu yawa, yana ta yi musu gargaɗi, yana cewa, “Ku tserar da kanku daga wannan karkataccen zamani.” 41 Waɗanda suka ya na'am da maganarsa kuwa aka yi musu baftisma. A ran nan kuma suka ƙaru da mutum wajen dubu uku. 42 Sai suka himmantu ga koyarwar manzanni da tarayya da juna, da gutsuttsura gurasa, da kuma yin addu'a.

Yadda Zaman Masu Bi Yake

43 Sai tsoro ya kama kowa, aka kuma yi abubuwan al'ajabi da mu'ujizai da yawa ta wurin manzannin. 44 Dukan masu ba da gaskiya suna tare, suna mallakar kome nasu gaba ɗaya. 45 Suka sayar da mallakarsu da kayansu, suka rarraba wa kowa kuɗin, gwargwadon bukatarsa. 46 Kowace rana kuma sukan riƙa zuwa Haikali da nufi ɗaya, suna gutsuttsura gurasa a gidajensu, suna cin abinci da farin ciki ƙwarai, rai kwance, 47 suna yabon Allah, suna da farin jini a wurin dukan mutane. Kowace rana kuma Ubangiji yana ƙara masu waɗanda ake ceta.

Ayyukan Manzanni 3

An Warkar da Gurgu a Ƙofar Haikali

1 To, Bitrus da Yahaya suna tafiya Haikali a lokacin addu'a, da ƙarfe uku na yamma, 2 sai ga wani mutum da aka haifa gurgu, ana ɗauke da shi. Kowace rana kuwa akan ajiye shi a ƙofar Haikali, wadda ake kira Ƙawatacciyar Ƙofa, don ya roƙi sadaka ga masu shiga Haikali. 3 Da ganin Bitrus da Yahaya suna shiga Haikalin, ya roƙe su sadaka. 4 Bitrus kuwa ya zuba masu ido, tare da Yahaya, ya ce, “Dube mu.” 5 Sai kuwa duk hankalinsa ya koma a kansu, da tsammanin samun wani abu a gunsu. 6 Amma Bitrus ya ce, “Kuɗi kam, ba ni da su, amma abin da nake da shi, shi zan ba ka. Da sunan Yesu Almasihu Banazare, yi tafiya.” 7 Sai Bitrus ya kama hannunsa na dama, ya tashe shi. Nan tāke ƙafafunsa da wuyan sawunsa suka yi ƙarfi. 8 Wuf, sai ya zabura, ya miƙe tsaye, ya fara tafiya, ya shiga Haikalin tare da su, yana tafe, yana tsalle, yana kuma yabon Allah. 9 Duk mutane suka gan shi yana tafe yana yabon Allah. 10 Suka kuwa gane shi ne mai zama a bakin Ƙawatacciyar Ƙofa ta Haikali yana bara. Sai mamaki ya kama su, suna al'ajabi ƙwarai a kan abin da aka yi masa.

Jawabin Bitrus a Shirayin Sulemanu

11 Tun yana riƙe da Bitrus da Yahaya, duk jama'a suka sheƙa a guje zuwa wurinsu a cikin shirayin da ake kira Shirayin Sulemanu, suka ruɗe don mamaki. 12 Da Bitrus ya ga haka, sai ya yi wa jama'a jawabi, ya ce, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, don me kuke mamakin wannan? Don me kuma kuke ta dubanmu, sai ka ce da ikon kanmu ne, ko kuwa don ibadarmu muka sa shi tafiya? 13 Allahn Ibrahim, da Ishaku, da Yakubu, Allahn kakanninmu, shi ya ɗaukaka Baransa Yesu, wanda kuka bashe shi, kuka kuma ƙi shi, a gaban Bilatus, sa'ad da ya ƙudura zai sake shi. 14 Amma ku kuka ƙi Mai Tsarkin nan, mai adalci kuka roƙa a saukar muku da mai kisankai, 15 kuka kuwa kashe Tushen Rai, amma Allah ya tashe shi daga matattu, mu kuwa shaidu na ga haka. 16 To, sunansa ne, wato ta wurin bangaskiya ga sunansa, shi ne ya ba mutumin nan da kuke gani, kuka kuma sani, ƙarfi. Hakika, bangaskiyar da take ta wurin Yesu ita ta ba mutumin nan cikakkiyar lafiya, a gaban idonku duka. 17 “To, yanzu 'yan'uwa, na sani da jahilci kuka yi haka, kamar yadda shugabanninku ma suka yi. 18 Amma ta haka Allah ya cika faɗar da ya riga ya yi ta bakin annabawa duka, cewa Almasihunsa zai sha wuya. 19 Saboda haka sai ku tuba, ku juyo, domin a shafe zunubanku, Ubangiji kuma kansa ya riƙa wartsakar da ku, 20 ya kuma aiko da Almasihun da aka ƙaddara muku tun dā, wato Yesu, 21 wanda lalle ne ya zauna a Sama, har kafin lokacin nan na sabunta dukkan abubuwa da Allah ya faɗa tun zamanin dā ta bakin annabawansa tsarkaka. 22 Musa ma ya ce, ‘Ubangiji Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni. Lalle ne ku saurari duk abin da ya faɗa muku. 23 Zai zamana kuma duk wanda ya ƙi sauraron annabin nan, za a hallaka shi daga cikin jama'a.’ 24 Hakika dukan annabawa da suka yi annabci, wato tun daga kan Sama'ila da waɗanda suka zo daga baya, duk sun yi faɗi a kan waɗannan kwanakin. 25 Ku ne tsatson annabawa, ku ne kuma magadan alkawarin da Allah ya yi wa kakanninku, da ya ce wa Ibrahim, ‘Ta zuriyarka ne za a yi wa dukkan kabilan duniya albarka.’ 26 Da Allah ya taso da Baransa, gare ku ne ya fara aiko shi, don yă yi muku albarka ta juyo da ko wannenku ga barin muguntarsa.”

Ayyukan Manzanni 4

Bitrus da Yahaya a gaban 'Yan Majalisa

1 Suna cikin yin magana da jama'a sai firistoci da shugaban dogaran Haikali da Sadukiyawa suka ji haushi ƙwarai, suka aukar musu, 2 don suna koya wa jama'a, suna tabbatar da tashi daga matattu, suna misali da Yesu. 3 Sai suka kama su, suka sa su a gidan waƙafi kafin gobe, don magariba ta riga ta yi. 4 Amma da yawa daga cikin waɗanda suka ji wa'azin sun ba da gaskiya, har jimillarsu ta kai wajen mutum dubu biyar. 5 Kashegari shugabanninsu da dattawansu da malamansu na Attaura suka taru a Urushalima, 6 tare da Hanana, babban firist, da Kayafa, da Yahaya, da Iskandari, da kuma duk waɗanda suke dangin babban firist. 7 Da suka tsai da su a tsakiya, suka tuhume su, suka ce, “Da wane iko ne, ko kuwa da wane suna ne, kuka yi haka?” 8 Sai Bitrus, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya ce musu, “Ya ku shugabannin jama'a, da dattawa, 9 in dai ana tuhumarmu ne yau a kan alherin da aka yi wa gajiyayyen mutumin nan, ta yadda aka warkar da shi, 10 to, sai ku sani, ku duka, da kuma duk jama'ar Isra'ila, da sunan Yesu Almasihu Banazare, wanda ku kuka gicciye, wanda kuma Allah ya tashi shi daga matattu, albarkacinsa ne mutumin nan yake tsaye a gabanku lafiyayye. 11 Wannan shi ne dutsen nan da ku magina kuka raina, shi ne kuwa ya zama mafificin dutsen gini. 12 Ba kuma samun ceto ga wani, domin ba wani suna duk duniyar nan da aka bayar cikin mutane, wanda lalle ta wurinsa ne za mu sami ceto.” 13 To, da suka ga ƙarfin halin Bitrus da Yahaya, suka kuma gane marasa ilimi ne, talakawa kuma, suka yi mamaki, suka kuwa shaida su, a kan dā suna tare da Yesu. 14 Amma da suka ga mutumin nan da aka warkar ɗin yana tsaye tare da su, suka rasa hanyar yin m�su. 15 Bayan sun umarce su, su fita daga majalisa, suka yi shawara da juna, 16 suka ce, “Yaya za mu yi da mutanen nan? Don hakika sanannen abu ne ga dukan mazauna Urushalima, cewa an yi wata tabbatacciyar mu'ujiza ta wurinsu, ba mu kuwa da halin yin m�su. 17 Amma don kada abin ya ƙara bazuwa a cikin mutane, sai mu yi musu kashedi, kada su kuskura su ƙara yi wa kowa magana, suna kama wannan suna.” 18 Sai suka kirawo manzannin, suka kwaɓe su, kada su kuskura su yi wa kowa magana, ko su ƙara koyarwa suna kama sunan Yesu. 19 Amma Bitrus da Yahaya suka mayar musu da jawabi suka ce, “To, in daidai ne a gun Allah mu fi jin taku da ta Allah, sai ku duba ku gani. 20 Domin mu kam, ba yadda za a yi sai mun faɗi abin da muka ji, muka kuma gani.” 21 Da kuma suka daɗa yi musu kashedi, suka sake su, don sun rasa yadda za su hore su saboda jama'a, domin dukan mutane suna ɗaukaka Allah saboda abin da ya auku. 22 Mutumin nan da aka yi wa mu'ujizar nan ta warkarwa kuwa ya ba shekara arba'in baya.

Masu Bi sun yi Addu'a su yi Magana Gabagaɗi

23 Da aka săke su, suka tafi wurin mutanensu, suka ba su labarin duk abin da manyan firistoci da shugabanni suka faɗa musu. 24 Su kuwa da jin haka, sai suka ɗaga muryarsu ga Allah da nufi ɗaya, suka ce, “Ya Mamallaki, Mahaliccin sama, da ƙasa, da teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu, 25 wanda ta Ruhu Mai Tsarki, ta bakin kakanmu Dawuda baranka, ka ce, ‘Don me al'ummai suka husata? Kabilai kuma suka yi makidar al'amuran wofi? 26 Sarakunan duniya sun kafa dāga, Mahukunta kuma sun haɗa kai, Suna gāba da Ubangiji, da kuma Almasihunsa.’ 27 Gama hakika Hirudus da Buntus Bilatus sun haɗa kai a birnin nan tare da al'ummai da jama'ar Isra'ila gāba da Yesu Baranka mai tsarki, wanda ka maishe shi Almasihu. 28 Sun haɗa kai domin su yi dukan abin da ka ƙaddara zai auku, bisa ga ikonka da nufinka. 29 Yanzu kuma ya Ubangiji, dubi wannan kashedinsu, ka yi wa bayinka baiwar yin maganarka da iyakar ƙarfin hali, 30 kana kuma miƙo hannunka kana warkarwa, ana kuma yin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi albarkacin sunan Baranka mai tsarki Yesu.” 31 Bayan sun yi addu'a, wurin da suke a tattare ya raurawa. Sai duk aka cika su da Ruhu Mai Tsarki, suka yi ta faɗar maganar Allah gabagaɗi.

Kome na 'Yan Ikilisiya Ɗaya Ne

32 To, duk taron da suka ba da gaskiya kuwa nufinsu ɗaya ne, ra'ayinsu ɗaya, ba kuma waninsu da ya ce abin da ya mallaka nasa ne, sai dai kome nasu ne baki ɗaya. 33 Manzanni kuma suka yi shaida da tabbatarwa mai ƙarfi a kan tashin Ubangiji Yesu daga matattu. Alheri mai yawa yana tare da kowannensu, 34 har ba wanda yake da rashi a cikinsu ko ɗaya, don duk masu gonaki ko gidaje sun sayar da su, 35 sun kawo kuɗin, sun ajiye gaban manzanni, an kuwa rarraba wa kowa gwargwadon bukatarsa. 36 Ana cikin haka sai Yusufu, wani Balawiye, asalinsa mutumin tsibirin Kubrus, wanda manzannin suke kira Barnaba, (wato ɗan ƙarfafa zuciya), 37 ya sayar da wata gonarsa, ya kawo kuɗin ya ajiye a gaban manzannin.

Ayyukan Manzanni 5

Hananiya da Safiratu

1 Amma wani mutum mai suna Hananiya, da matarsa Safiratu, ya sayar da wata mallakarsa, 2 sai ya ɓoye wani abu daga cikin kuɗin, da sanin matarsa, ya kawo sashin kuɗin kurum ya ajiye a gaban manzanni. 3 Sai Bitrus ya ce, “Kai, Hananiya, ta ƙaƙa Shaiɗan ya cika zuciyarka, har ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya, ka kuma ɓoye wani abu daga kuɗin gonar? 4 Kafin ka sayar, ba taka ba ce? Bayan ka sayar kuma, kuɗin ba halalinka ba ne? Ta ƙaƙa ka riya wannan aiki a zuciyarka? Ai, ba mutum ka yi wa ƙarya ba, Allah ka yi wa.” 5 Da jin wannan magana Hananiya ya fāɗi ya mutu. Duk waɗanda suka ji kuwa, matsanancin tsoro ya kama su. 6 Samari suka taso, suka sa shi a likkafani, suka ɗauke shi suka fitar da shi, suka je suka binne shi. 7 Bayan misalin sa'a uku matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba. 8 Sai Bitrus ya ce mata, “Gaya mini, shin, haka kuka sayar da gonar nan?” Sai ta ce, “I, haka ne.” 9 Amma Bitrus ya ce mata, “Ƙaƙa kuka gama baki ku gwada Ruhun Ubangiji? Kin ji tafiyar waɗanda suka binne mijinki, har sun iso bakin ƙofa ma, za su kuwa ɗauke ki, su fitar da ke.” 10 Nan tāke, ta fāɗi a gabansa, ta mutu. Da dai samarin suka shigo, suka iske ta matacciya, suka ɗauke ta suka fitar da ita, suka binne ta a jikin mijinta. 11 Sai matsanancin tsoro ya kama dukan ikilisiyar, da kuma dukan waɗanda suka ji labarin waɗannan abubuwa.

An Yi Mu'ujizai da Abubuwan Al'ajabi masu Yawa

12 To, an yi mu'ujizai da abubuwan al'ajabi masu yawa a cikin mutane ta hannun manzanni. Dukansu kuwa da nufi ɗaya sukan taru a Shirayin Sulemanu. 13 Amma a cikin sauran mutane ba wanda ya yi ƙarfin halin shiga cikinsu, duk da haka kuwa jama'a suna girmama su. 14 Masu ba da gaskiya sai ƙaruwa suke ta yi ga Ubangiji fiye da dā, jama'a masu yawan gaske mata da maza. 15 Har ma ya kai ga fitowa da marasa lafiya tafarku, suna shimfiɗa su a kan gadaje da tabarmi, don in Bitrus ya zo wucewa, ko da inuwarsa ma ta bi ta kan waɗansunsu. 16 Mutane kuwa suka yi ta taruwa daga garuruwan da suke kewayen Urushalima, suna ta kawo marasa lafiya da waɗanda baƙaƙen aljannu suke wahalshe su, dukansu kuwa aka warkar da su.

An Tsananta wa Manzanni

17 Amma babban firist ya taso, da duk waɗanda suke tare da shi, wato 'yan ɗariƙa Sadukiyawa, suna kishi gaya, 18 suka kama manzannin, suka sa su kurkuku. 19 Amma da daddare sai wani mala'ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun, ya fito da su, ya ce, 20 “Ku tafi, ku tsaya a cikin Haikali, ku sanar da jama'a duk maganar wannan rai.” 21 Da suka ji haka, suka shiga Haikalin da sassafe, suna koyarwa. To, babban firist ya fito, shi da waɗanda suke tare da shi, suka kira majalisa, da dukan shugabannin Isra'ilawa, suka aika zuwa kurkuku a kawo su. 22 Amma da dogaran Haikali suka je, ba su same su a kurkukun ba, suka dawo suka ba da labari, suka ce, 23 “Mun iske kurkukun a kulle sosai, masu tsaro kuma suna tsaro a bakin ƙofofin, amma da muka buɗe, sai muka tarar ba kowa a ciki.” 24 To, da shugaban dogaran Haikali da manyan firistocin suka ji haka, suka ruɗe ƙwarai a game da su, suka rasa inda abin zai kai. 25 Sai wani ya zo ya ce musu, “Ai, ga shi, mutanen nan da kuka sa a kurkuku suna nan a tsaye a Haikali, suna koya wa jama'a.” 26 Sai shugaban dogaran Haikali da dogaran suka je suka kawo manzannin, amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada jama'a su jejjefe su da duwatsu. 27 Da suka kawo su, suka tsai da su a gaban majalisar. Sai babban firist ya tambaye su, 28 ya ce, “Mun fa kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa da sunan nan, amma ga shi, kun gama Urushalima da koyarwarku, har ma kuna nema ku ɗafa mana alhakin jinin mutumin nan.” 29 Amma Bitrus da manzannin suka amsa suka ce, “Wajibi ne mu yi wa Allah biyayya fiye da mutum. 30 Allahn kakanninmu ya ta da Yesu, wanda kuka kashe ta wurin kafe shi a jikin gungume. 31 Shi ne Allah ya ɗaukaka ga damansa, Shugaba da kuma Mai Ceto, domin ya buɗe wa Isra'ila hanyar tuba, su kuma sami gafarar zunubansu. 32 Mu kuwa shaidu ne ga waɗannan al'amura, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya bai wa masu yi masa biyayya.” 33 Da suka ji haka, sai suka husata ƙwarai da gaske, suna so su kashe su. 34 Amma wani Bafarisiye, mai suna Gamaliyal, masanin Attaura, wanda duk jama'a suke girmamawa, ya miƙe a cikin majalisa, ya yi umarni a fitar da mutanen nan a waje tukuna. 35 Sa'an nan ya ce musu, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, ku kula fa da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan. 36 A shekarun baya wani mutum ya ɓullo, mai suna Tudas, wanda ya mai da kansa wani abu, wajen mutum arbaminya kuma suka bi shi, amma aka kashe ƙi, mabiyansa kuwa aka watsa su, suka lalace. 37 A bayansa kuma, a lokacin ƙirgen mutane, wani mai sunan Yahuza Bagalile ya ɓullo, ya zuga waɗansu suka yi tawaye, suka bi shi. Shi ma ya hallaka, duk mabiyansa ma aka warwatsa su. 38 To, a yanzu ma, ina gaya muku, ku fita daga sha'anin mutanen nan, ku ƙyale su. Idan dai niyyarsu ko aikinsu na mutum ne, ai, zai rushe, 39 amma in na Allah ne, ba dama ku rushe su. Kada fa a same ku kuna gāba da Allah.” 40 Sai suka bi shawararsa, suka kuma kirawo manzannin, suka yi musu d�ka, suka kwaɓe su kada su ƙara magana da sunan Yesu, sa'an nan suka sake su. 41 To, sai suka tashi daga gaban majalisar, suna farin ciki a kan an ga sun isa su sha wulakanci saboda sunan Yesu. 42 Kowace rana kuwa, ko a Haikali ko a gida, ba su daina koyarwa da yin bishara, cewa Yesu shi ne Almasihu ba.

Ayyukan Manzanni 6

Zaɓen Mutum Bakwai Masu Hidima

1 To, a kwanakin nan da yawan masu bi yake Ƙaruwa, sai Yahudawa masu jin Helenanci suka yi wa Ibraniyawa gunaguni domin ba a kula da matansu gwauraye ba, a wajen rabon gudunmawa a kowace rana. 2 Sai goma sha biyun nan suka kirawo duk jama'ar masu bi, suka ce, “Ai, bai kyautu ba mu mu bar wa'azin Maganar Allah, mu shagala a kan sha'anin abinci. 3 Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku, waɗanda ake yabawa, cike da Ruhu da kuma hikima, waɗanda za mu danƙa wa wannan aiki. 4 Mu kuwa sai mu nace da yin addu'a da kuma koyar da Maganar.” 5 Abin da suka faɗa kuwa ya ƙayatar da jama'a duka. Sai suka zaɓi Istifanas, mutumin da yake cike da bangaskiya da Ruhu Mai Tsarki, da Filibus, da Burokoras, da Nikanar, da Timan, da Barminas, da Nikolas mutumin Antakiya wanda dā ya shiga Yahudanci. 6 Waɗannan ne aka gabatar a gaban manzannin. Bayan sun yi addu'a kuma, suka ɗora musu hannu. 7 Maganar Allah kuwa sai ƙara haɓaka take yi, yawan masu bi kuma a birnin Urushalima sai ta ƙaruwa yake yi ƙwarai da gaske, firistoci masu yawan gaske kuma suka yi na'am da bangaskiyar nan.

An Kama Istifanas

8 To, Istifanas, a cike da alheri da iko, ya yi ta yin manyan al'ajabai da mu'ujizai a cikin jama'a. 9 Sa'an nan waɗansu na majami'ar da ake kira majami'ar Libartinawa, wato Kuraniyawa da Iskandariyawa, da kuma waɗansu daga ƙasar Kilikiya da ta Asiya, suka tasar wa Istifanas da muhawwara. 10 Amma ko kaɗan ba dama su yi masa m�su, domin ya yi magana da hikima, Ruhu yana iza shi. 11 Sai suka zuga mutane a asirce, su kuwa suka ce, “Mun ji shi yana zagin Musa, yana saɓon Allah.” 12 Ta haka suka ta da hankalin jama'a, da shugabanni, da malaman Attaura, su kuma suka aukar masa, suka kama shi, suka kawo shi a gaban majalisa. 13 Sai suka gabatar da masu shaidar zur, suka ce, “Mutumin nan ba ya rabuwa da kushe tsattsarkan wurin nan, da kuma Attaura, 14 don mun ji shi yana cewa, wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan, yă kuma sauya al'adun da Musa ya bar mana.” 15 Da duk waɗanda suke zaune a majalisar suka zura masa ido, suka ga fuskarsa kamar fuskar mala'ika take.

Ayyukan Manzanni 7

Hanzarin Istifanas

1 Sai babban firist ya ce, “Ashe, haka ne?” 2 Sai Istifanas ya ce, “Ya ku 'yan'uwa da shugabanni, ku saurare ni. Allah Maɗaukaki ya bayyana ga kakanmu Ibrahim, sa'ad da yake ƙasar Bagadaza, tun bai zauna a Haran ba, 3 ya ce masa, ‘Tashi daga ƙasarku, kuma daga cikin 'yan'uwanka, ka je ƙasar da zan nuna maka.’ 4 Sai ya tashi daga ƙasar Kaldiyawa, ya zauna a Haran. Daga can kuma, bayan mutuwar mahaifinsa, Allah ya kawo shi ƙasar nan da yanzu kuke zaune. 5 Amma kuwa shi da kansa, bai ba shi gādonta ba, ko da tăki ɗaya, sai dai ya yi masa alkawari zai mallakar masa ita, shi da zuriyar bayansa, ko da yake ba shi da ɗa a lokacin. 6 Abin da Allah ya faɗa kuwa shi ne zuriyar Ibrahim za su yi baƙunci a wata ƙasa, mutanen ƙasar kuwa za su bautar da su, su kuma gwada musu azaba har shekara arbaminya. 7 ‘Har wa yau kuma,’ Allah ya ce, ‘Al'ummar da za su bauta wa, ni zan hukunta ta, bayan haka kuma za su fito su bauta mini a wannan wuri.’ 8 Ya kuma yi masa alkawari a game da kaciya. Ta haka, da Ibrahim ya haifi Ishaku, ya yi masa kaciya a rana ta takwas. Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi kakanninmu goma sha biyun nan. 9 “Kakannin nan namu kuwa, da yake suna kishin Yusufu, suka sayar da shi, aka kai shi Masar. Amma Allah yana tare da shi, 10 ya kuma tsamo shi daga dukan wahalarsa, ya ba shi farin jini da hikima a gun Fir'auna, Sarkin Masar, shi kuwa ya naɗa shi mai mulkin Masar, ya kuma danƙa masa jama'ar gidansa duka. 11 To, sai wata yunwa ta auku a dukan ƙasar Masar da ta Kan'ana, a game da matsananciyar wahala, har kakanninmu suka rasa abinci. 12 Amma da Yakubu ya ji akwai alkama a Masar, ya aiki kakanninmu tafiyar farko. 13 A tafiyarsu ta biyu Yusufu ya sanar da kansa ga 'yan'uwansa, asalinsa kuma ya sanu ga Fir'auna. 14 Sai Yusufu ya aika wa mahaifinsa Yakubu yă zo, da kuma dukan 'yan'uwansa, mutum saba'in da biyar. 15 Sai Yakubu ya tafi Masar. A can ma ya mutu, shi da kakanninmu. 16 Sai aka ɗebo su aka mai da su Shekem, aka sa su a kabarin da Ibrahim ya saya da kuɗi azurfa a wurin 'ya'yan Hamor a nan Shekem. 17 “Amma da lokacin cikar alkawarin da Allah ya yi wa Ibrahim ya gabato, jama'ar suka ƙaru, suka yawaita ƙwarai a ƙasar Masar, 18 har aka yi wani sarki a Masar, wanda bai san ko wane ne Yusufu ba. 19 Wannan sarki kuwa ya cuci kabilarmu, yana gwada wa kakanninmu azaba, yana sawa a yar da jariransu, don kada su rayu. 20 A lokacin nan ne aka haifi Musa, yaro kyakkyawan gaske. Sai aka rene shi wata uku a gidan mahaifinsa. 21 Da aka fitar da shi waje, 'yar Fir'auna ta ɗauke shi tallafinta, ta goya shi kamar ɗanta. 22 Sai aka karantar da Musa a cikin dukan ilimin Masarawa, shi kuwa mutum mai iko ne a cikin magana da ayyukansa. 23 “Yana gab da cika shekara arba'in ke nan, sai ya faɗo masa a rai yă ziyarci 'yan'uwansa Isra'ilawa. 24 Da ya ga ana cutar ɗayansu, sai ya tăre wanda ake wulakantawa, ya rama masa, ya buge Bamasaren, ya mutu. 25 Ya zaci 'yan'uwansa sun gane ta hannunsa ne Allah zai cece su. Amma ba su gane ba. 26 Kashegari kuma waɗansu suna faɗa, sai ya nemi shirya su, ya ce, ‘Ku jama'a, ku 'yan'uwa ne fa, don me kuke cutar juna?’ 27 Amma mai cutar ɗan'uwa nasa sai ya ture Musa, ya ce, ‘Wa ya sa ka shugaba da alƙali a kanmu? 28 Wato kana so ne ka kashe ni kamar yadda ka kashe Bamasaren nan na jiya?’ 29 Da jin wannan magana, sai Musa ya gudu ya yi baƙunci a ƙasar Madayana, a inda ya haifi 'ya'ya biyu maza. 30 “To, bayan shekara arba'in, sai mala'ika ya bayyana a gare shi a cikin harshen wuta, a wani kurmi a jejin Dutsen Sina'i. 31 Da Musa ya ga haka, ya yi mamakin abin da ya gani. Da ya matso domin ya duba, sai ya ji muryar Ubangiji tana cewa, 32 ‘Ni ne Allahn kakanninka, Allahn Ibrahim da Ishaku da Yakubu.’ Sai jikin Musa ya ɗauki rawa, bai kuma iya ƙarfin halin dubawa ba. 33 Sai Ubangiji ya ce masa, ‘Tuɓe takalminka, domin wurin da kake tsayen nan, tsattsarka ne. 34 Hakika, na ga wulakancin da ake yi wa mutanena da suke Masar, na ji nishinsu, na kuma sauko don in cece su. To, a yanzu sai ka zo in aike ka Masar.’ 35 “To, shi Musan nan da suka ƙi, suna cewa, ‘Wa ya sa ka shugaba da kuma alƙali?’ Shi ne Allah ya aiko ya zama shugaba, da mai ceto, ta taimakon mala'ikan nan da ya bayyana a gare shi a cikin kurmin nan. 36 Shi ne kuwa ya fito da su, bayan ya yi abubuwan al'ajabi da mu'ujizai a ƙasar Masar, da Bahar Maliya, da kuma a cikin jeji, har shekara arba'in. 37 Wannan shi ne Musan da ya ce wa Isra'ilawa, ‘Allah zai tasar muku da wani annabi daga cikin 'yan'uwanku, kamar yadda ya tashe ni.’ 38 Shi ne kuma wanda yake a cikin ikilisiyar nan a jeji tare da mala'ikan da ya yi masa magana a Dutsen Sinai, tare da kakanninmu kuma. Shi ne kuma ya karɓo rayayyiyar magana domin ya kawo mana. 39 Amma kakanninmu suka ƙi yi masa biyayya, suka ture shi, zuciyarsu ta koma ƙasar Masar. 40 Suka ce wa Haruna, ‘Ka yi mana gumakan da za su yi mana jagaba, don Musan nan kam, da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya auku a gare shi ba.’ 41 A lokacin nan suka ƙera ɗan maraƙi, suka yanka wa gunkin nan hadaya, suka riƙa farin ciki da aikin da suka yi da hannunsu. 42 Saboda haka Allah ya juya musu baya, ya sallame su ga bautar taurari, yadda yake a rubuce a littafin annabawa cewa, ‘Ya ku jama'ar Isra'ila, Ni ne kuka yanka wa dabbobi, kuka miƙa wa hadaya, Har shekara arba'in a cikin jeji? 43 Ai, yawo kuka yi da alfarwar Molek, Da surar tauraron gunki Ramfan, Wato surorin nan da kuka ƙera don ku yi musu sujada. Ni kuwa zan kawar da ku a can bayan Babila.’ 44 “Dā kakanninmu suna da alfarwar shaida a jeji, irin wadda mai maganar nan da Musa ya umarta a yi, daidai fasalin da ya gani. 45 Alfarwar nan ita ce kakanninmu suka gāda, suka kuma kawo ƙasar nan a zamanin Joshuwa, bayan sun mallake ƙasar al'umman da Allah ya kora a gaban idonsu. Alfarwar nan kuwa tana nan har ya zuwa zamanin Dawuda, 46 wanda ya sami tagomashi wurin Allah, har ya nemi alfarmar yi wa Allahn Yakubu masujada. 47 Amma Sulemanu ne ya yi wa Allah gini. 48 Duk da haka Maɗaukaki ba ya zama a gidaje, ginin mutum. Yadda Annabi Ishaya ya ce, 49 ‘Allah ya ce, Sama ita ce kursiyina, Ƙasa kuwa matashin ƙafata. Wane wuri kuma za ku gina mini? Ko kuwa wane wuri ne wurin hutuna? 50 Ba da ikona na halicci dukan waɗannan abubuwa ba?’ 51 “Ku kangararru, masu ɓatan basira, masu kunnen ƙashi, kullum kuna yi wa Ruhu Mai Tsarki tsayayya. Yadda kakanninku suka yi, haka ku ma kuke yi. 52 A cikin annabawa wane ne kakanninku ba su tsananta wa ba? Sun kuma kashe waɗanda suka yi făɗi a kan zuwan Mai Adalcin nan, wanda a yanzu kuka zama maciya amanarsa, da kuma makasansa, 53 ku ne kuwa kuka karɓi Shari'a ta wurin mala'iku, amma ba ku kiyaye ta ba!”

An Kashe Istifanas da Jifa

54 Da suka ji haka, suka husata ƙwarai da gaske, har suka ciji leɓe don jin haushinsa. 55 Amma Istifanas, a cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya zuba ido sama, ya ga ɗaukakar Allah, da kuma Yesu yana tsaye a dama ga Allah. 56 Sai ya ce, “Ga shi, ina ganin sama a buɗe, da kuma Ɗan Mutum a tsaye a dama ga Allah.” 57 Amma suka ɗauki ihu ƙwarai, suka tattoshe kunnuwansu, suka aukar masa da nufi ɗaya, 58 suka fitar da shi a bayan gari ya ta jifansa da dutse. Shaidu kuwa suka ajiye tufafinsu wurin wani saurayi, mai suna Shawulu. 59 Suna ta jifan Istifanas, shi kuwa yana ta addu'a, yana cewa, “Ya Ubangiji Yesu, ka karɓi ruhuna.” 60 Sa'an nan ya durƙusa, ya ɗaga murya da ƙarfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka ɗora musu wannan zunubi.” Da faɗar haka sai ya yi barci.

Ayyukan Manzanni 8

1 Shawulu kuwa yana goyon bayan kisan Istifanas. Shawulu ya Yi wa Ikilisiya Ɓarna Ƙwarai A ran nan kuwa wani babban tsanani ya auko wa ikilisiyar da take Urushalima. Duk aka warwatsa su a lardin Yahudiya da na Samariya, sai dai manzannin kawai. 2 Sai waɗansu mutane masu bautar Allah suka binne Istifanas, suka yi masa kuka ƙwarai. 3 Amma Shawulu ya yi ta yi wa Ikilisiya ɓarna ƙwarai da gaske, yana shiga gida gida, yana jan mata da maza, yana jefa su a kurkuku.

An yi Wa'azin Bishara a Samariya

4 To, waɗanda aka warwatsar ɗin kuwa, suka yi ta zazzagawa suna yin bishara. 5 Filibus ya tafi birnin Samariya, yana ta yi musu wa'azin Almasihu. 6 Da taron suka ji, suka kuma ga mu'ujizan da Filibus yake yi, da nufi ɗaya suka mai da hankali ga abin da ya faɗa. 7 Domin da yawa masu baƙaƙen aljannu suka rabu da su, aljannun kuwa suna ta ihu. Shanyayyu da guragu da yawa kuma an warkar da su. 8 Saboda haka aka yi ta farin ciki a garin ƙwarai da gaske. 9 Akwai wani mutum kuwa, mai suna Saminu, wanda dā yake sihiri a birnin, har yana ba Samariyawa mamaki, yana cewa shi wani muhimmi ne. 10 Duk jama'a kuwa mai da hankali a gare shi, babba da yaro, suna cewa, “Mutumin nan, ai, ikon nan ne na Allah, da ake kira mai girma.” 11 Sai suka mai da hankali a gare shi, don ya daɗe yana ta ba su al'ajabi da sihirinsa. 12 Amma da suka gaskata bisharar da Filibus ya yi a kan Mulkin Allah, da kuma sunan Yesu Almasihu, duka aka yi musu baftisma mata da maza. 13 Har Saminu da kansa ma ya ba da gaskiya, bayan an yi masa baftisma kuma ya manne wa Filibus. Ganin kuma ana yin mu'ujizai da manyan al'ajibai, ya yi mamaki ƙwarai. 14 To, da manzannin da suke Urushalima suka ji Samariyawa sun yi na'am da Maganar Allah, suka aika musu da Bitrus da Yahaya. 15 Su kuwa sa suka iso, suka yi musu addu'a don su sami Ruhu Mai Tsarki, 16 domin bai sauko wa ko wannensu ba tukuna, sai dai kawai an yi musu baftisma ne da sunan Ubangiji Yesu. 17 Sai suka ɗora musu hannu, suka kuwa sami Ruhu Mai Tsarki. 18 To, da Saminu ya ga, ashe, ta ɗora hannun manzanni ne ake ba da Ruhun, sai ya miƙa musu kuɗi, 19 ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iko, don kowa na ɗora wa hannu, yă sami Ruhu Mai Tsarki.” 20 Amma Bitrus ya ce masa, “Ku hallaka, kai da kuɗinka, don ka zaci da kuɗi ne za ka sami baiwar Allah! 21 Ba ruwanka da wannan al'amari sam, don zuciyarka ba ɗaya take ba a gaban Allah. 22 Saboda haka sai ka tuba da wannan mugun aiki naka, ka roƙi Ubangiji ko a gafarta maka abin da ka riya a zuciyarka. 23 Domin na ga kai tushen ɗaci ne, kana kulle a cikin mugunta.” 24 Sai saminu ya amsa ya ce, “Ku roƙar mini Ubangiji kada ko ɗaya daga cikin abin da kuka faɗa ya aukar mini.” 25 To, bayan manzannin sun tabbatar da Maganar Ubangiji, sun faɗe ta, suka koma Urushalima, suna yin bishara a ƙauyukan Samariyawa da yawa.

Filibus da Mutumin Habasha

26 Sai mala'ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Tashi, ka yi kudu, ka bi hanyar da ta fito daga Urushalima zuwa Gaza,” wato hanyar hamada. 27 Sai ya tashi ya tafi. Ga wani mutumin Habasha, wani bābā, mai babban matsayi a mulkin Kandakatu, sarauniyar Habasha, shi ne kuwa ma'ajinta, ya zo Urushalima ne yin sujada, 28 yana komawa gida a zaune a cikin keken dokinsa, yana karatun littafin Annabi Ishaya. 29 Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa ka yi kusa da keken dokin nan.” 30 Sai Filibus ya yi gudu zuwa wurinsa, ya ji shi yana karatun littafin Annabi Ishaya. Ya ce, “Kana kuwa fahimtar abin da kake karantawa?” 31 Sai ya ce, “Ina fa? Sai ko wani ya fassara mini.” Sai ya roƙi Filibus ya hau su zauna tare. 32 Wannan kuwa shi ne nassin da yake karantawa, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka. Kamar yadda ɗan rago yake shiru a hannun mai sausayarsa, Haka, ko bakinsa bai buɗe ba. 33 An yi masa ƙasƙanci har an hana masa gaskiyarsa. Wa yake iya ba da labarin zamaninsa? Domin an katse ransa daga duniya.” 34 Sai bābān ya ce wa Filibus, “Shin kam, annabin nan, maganar wa yake yi? Tasa ko ta wani?” 35 Sai Filibus ya buɗe baki ya fara da wannan Nassi, yana yi masa bisharar Yesu. 36 Suna cikin tafiya, suka iso wani ruwa, sai bābān ya ce, “Ka ga ruwa! Me zai hana a yi mini baftisma?” 37 Filibus ya ce, “In dai ka ba da gaskiya da zuciya ɗaya, ai, sai a yi maka.” Bābān ya amsa ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu ɗan Allah ne.” 38 Sai ya yi umarni a tsai da keken dokin. Sai dukansu biyu suka gangara zuwa cikin ruwan, Filibus da bābān, ya yi masa baftisma. 39 Da suka fito daga ruwan, Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuma bai ƙara ganinsa ba. Sai ya yi ta tafiya yana farin ciki. 40 Amma aka ga Filibus a Azotus. Sai ya zaga dukan garuruwa, yana yin bishara, har ya isa Kaisariya.

Ayyukan Manzanni 9

Juyowar Shawulu

1 Shawulu kuwa yana kan tsananta yin kashedi da gāba da masu bin Ubangiji, cewa zai kashe su, sai ya je wurin babban firist, 2 ya roƙe shi ya yi masa wasiƙu zuwa majami'un Dimashƙu, don in ya sami musu bin wannan hanya, mata ko maza, yă zo da su birnin Urushalima a ɗaure. 3 Yana tafiya ke nan, ya yi kusa da Dimashƙu, ba zato sai ga wani haske daga sama ya haskaka kewaye da shi. 4 Sai ya fāɗi, ya kuma ji wata murya tana ce masa, “Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?” 5 Shi kuma ya ce, “Wane ne kai, ya Ubangiji?” Sai ya ce, “Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa. 6 Amma ka tashi ka shiga gari, a can za a faɗa maka abin da za ka yi.” 7 Abokan tafiyarsa kuwa suka rasa bakin magana, suna jin muryar, amma ba su ga kowa ba. 8 Sai Shawulu ya tashi, amma da ya buɗe ido sai ya kasa gani. Sai da aka yi masa jagora, aka kai shi Dimashƙu. 9 Kwanansa uku ba ya gani, ba ya kuma ci, ba ya sha. 10 To, akwai wani mai bi a Dimashƙu, mai suna Hananiya. Ubangiji ya yi masa magana a cikin wahayi ya ce, “Hananiya.” Shi kuwa ya ce, “Na'am, ya Ubangiji.” 11 Sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka tafi hanyar nan da ake kira Miƙaƙƙiya, ka yi tambaya a gidan Yahuza, ko akwai wani mutumin Tarsus, mai suna Shawulu, ga shi nan, yana addu'a, 12 har ma a cikin wahayi ya ga wani mutum, mai suna Hananiya, ya shigo ya ɗora masa hannu, don ya sāke samun ganin gari.” 13 Amma Hananiya ya amsa ya ce, “Ya Ubangiji, na sha jin labarin mutumin nan a gun mutane da yawa, a kan yawan muguntar da ya yi wa tsarkakanka a Urushalima. 14 Ga shi kuma manyan firistoci sun ba shi izini ya ɗaure duk mai yin addu'a da sunanka har a nan ma.” 15 Amma Ubangiji ya ce masa, “Kai dai, je ka, domin shi ma'aikacina ne zaɓaɓɓe, domin yă sanar da sunana ga al'ummai, da sarakuna, da kuma Isra'ilawa. 16 Domin zan sanar da shi yawan wuyar da lalle zai sha saboda sunana.” 17 Sai Hananiya ya tafi, ya shiga gidan. Da ya ɗora masa hannu, sai ya ce, “Ya ɗan'uwana Shawulu, Ubangiji ne ya aiko ni, wato Yesu, wanda ya bayyana a gare ka a kan hanyar da ka biyo, domin ka sāke gani, a kuma cika ka da Ruhu Mai Tsarki.” 18 A nan take sai wani abu kamar ɓawo ya faɗo daga idanunsa, sai ya sāke gani. Sa'an nan ya tashi, aka yi masa baftisma. 19 Sai ya ci abinci, ƙarfinsa kuma ya komo.

Shawulu ya yi Wa'azi a Dimashƙu

Shawulu kuwa ya yi 'yan kwanaki tare da masu bi da suke Dimashƙu. 20 Nan da nan ya fara wa'azin Yesu a majami'unsu, cewa shi ne Ɗan Allah. 21 Duk waɗanda suka ji shi, suka yi ta al'ajabi, suka ce, “Ashe, ba wannan ne ya watsa masu yin addu'a da sunan nan a Urushalima ba? Ya zo nan ne ma da niyyar ya kai su a gaban manyan firistoci a ɗaure.” 22 Sai Shawulu ya ƙara ƙarfafa, yana ta dama hankalin Yahudawan da suke zaune a Dimashƙu, yana tabbatarwa, cewa Yesu shi ne Almasihu.

Shawulu ya Kuɓuce wa Yahudawa

23 Bayan an ɗan daɗe Yahudawa suka ƙulla shawara su kashe shi. 24 Amma Shawulu ya sami labarin makircinsu. Dare da rana suna fako a ƙofofin gari don su kashe shi, 25 amma da daddare almajiransa suka tafi da shi, suka zura shi ta wata taga a jikin garu cikin babban kwando.

Shawulu a Urushalima

26 Da ya zo Urushalima ya yi ƙoƙarin shiga a cikin masu bi, amma duk suka ji tsoronsa, don ba su gaskata shi mai bi ba ne. 27 Amma Barnaba ya kama hannunsa ya kai shi wurin manzannin, ya gaya musu yadda Shawulu ya ga Ubangiji a hanya, da yadda Ubangiji ya yi masa magana, da kuma yadda ya yi wa'azi gabagaɗi da sunan Yesu a Dimashƙu. 28 A daga nan ya yi ta cuɗanya da su a Urushalima, 29 yana wa'azi gabagaɗi da sunan Ubangiji. Ya kuma riƙa yin magana da Yahudawa masu jin Helenanci, yana muhawwara da su, amma suka yi ta neman hanyar kashe shi. 30 Da 'yan'uwa suka fahimci haka, suka kawo shi Kaisariya, suka aika da shi Tarsus. 31 Sa'an nan ne Ikilisiyar duk ƙasar Yahudiya, da ta Galili, da ta Samariya ta sami lafiya, ta ingantu sosai, suna tafiyar da al'amuransu da tsoron Ubangiji, Ruhu Mai Tsarki yana taimakonsu, har suka yawaita.

An Warkar da Iniyasu

32 To, da Bitrus ya zazzaga lardi duka, sai kuma ya je wurin tsarkakan nan da suke zaune a Lidda. 33 A nan ya tarar da wani mutum, mai suna Iniyasu, wanda yake kwance a kan gado shekara takwas, yana shanyayye. 34 Sai Bitrus ya ce masa, “Iniyasu, Yesu Almasihu ya warkar da kai. Tashi ka kintsa gadonka.” A nan tāke ya tashi. 35 Duk mutanen Lidda da na ƙasar Sarona kuwa suka gan shi, suka juyo ga Ubangiji.

Bitrus ya Ta da Tabita daga Matattu

36 A Yafa kuwa akwai wata mai bi, mai suna Tabita, wato Dokas ke nan. Matar nan kuwa lazimar aiki nagari ce, da kuma gudunmawa. 37 A lokacin nan ta yi rashin lafiya, ta mutu. Da suka yi mata wanka, suka shimfiɗe ta a kan bene. 38 Da yake Lidda kusa da yafa take, da masu bi suka ji Bitrus yana can, suka aiki mutum biyu wurinsa, su roƙe shi ya zo wurinsu ba da jinkiri ba. 39 Sai Bitrus ya tashi ya tafi tare da su. Da ya iso suka kai shi benen. Dukan mata gwauraye suka tsaya kusa da shi, suna kuka, suna nunnuna riguna da tufafi da Dokas ta yi musu tun suna tare. 40 Amma Bitrus ya fitar da su duka waje, ya durƙusa, ya yi addu'a. Ya juya wajen gawar, ya ce, “Tabita, tashi.” Ta buɗe ido, da ta ga Bitrus, sai ta tashi zaune. 41 Ya kuwa miƙa mata hannu ya tashe ta. Sai ya kira tsarkaka da mata gwauraye, ya miƙa musu ita rayayyiya. 42 Labari ya bazu a dukan Yafa, mutane da yawa kuwa suka gaskata da Ubangiji. 43 To, ya zauna kwanaki da yawa a Yafa a gidan wani majemi mai suna Saminu.

Ayyukan Manzanni 10

Bitrus da Karniliyas

1 An yi wani mutum a Kaisariya, mai suna Karniliyas, wani jarumi ne na ƙungiyar soja da ake kira Ƙungiyar Italiya. 2 Shi kuwa mutum ne mai ibada, yana tsoron Allah shi da iyalinsa duka, yana yi wa Yahudawa gudunmawa hannu sake, yana kuma addu'a ga Allah a kai a kai. 3 Wata rana wajen ƙarfe uku na yamma, ya ga wani mala'ikan Allah a fili cikin wahayi, ya shigo, ya ce masa, “Ya Karniliyas.” 4 Shi kuwa ya zura masa ido a tsorace, ya ce, “Ya Ubangiji, mene ne?” Mala'ikan kuma ya ce masa, “Addu'arka da sadakarka sun kai har a gaban Allah, abubuwan tunawa ne kuma a gare shi. 5 To, a yanzu, sai ka aiki mutane Yafa su kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, 6 ya sauka a gun Saminu majemi, wanda gidansa yake a bakin bahar.” 7 Da mala'ikan da ya yi masa magana ya tafi, ya kira barorinsa biyu, da kuma wani soja mai ibada daga cikin waɗanda suke yi masa hidima kullum. 8 Da ya ba su labarin kome, ya aike su Yafa. 9 Kashegari suna cikin tafiya, sun zo kusa da gari ke nan, sai Bitrus ya hau kan soro yin addu'a, wajen rana tsaka. 10 Yunwa ta kama shi, har ya so ya ci wani abu. Ana cikin shirya abincin, sai wahayi ya zo masa, 11 ya ga sama ta dare, wani abu kuma yana saukowa kamar babban mayafi, ana zuro shi ƙasa ta kusurwoyinsa huɗu. 12 A cikinsa akwai kowace irin dabba, da masu jan ciki, da tsuntsaye. 13 Sai ya ji wata murya ta ce masa, “Bitrus, tashi, ka yanka ka ci.” 14 Amma Bitrus ya ce, “A'a, ya Ubangiji, don ban taɓa cin wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta ba.” 15 Sai ya sāke jin murya, ji na biyu, ta ce, “Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.” 16 Da aka yi wannan sau uku, nan da nan aka yi sama da abin. 17 Bitrus na a cikin damuwa ƙwarai a kan ko mece ce ma'anar wahayin da aka yi masa, sai ga mutanen da Karniliyas ya aiko a tsaye a ƙofar zaure, sun riga sun tambayi gidan Saminu, 18 suna sallama, suna tambaya ko Saminu da ake kira Bitrus a nan ya sauka. 19 Tun Bitrus yana bibiya wahayin nan, Ruhu ya ce masa, “Ga mutum uku nan suna nemanka. 20 Tashi, ka sauka, ku tafi tare, ba da wata shakka ba, domin ni ne na aiko su.” 21 Sai Bitrus ya sauka a wurin mutanen, ya ce musu, “Ga ni, ni ne kuke nema. Wace magana take tafe da ku?” 22 Sai suka ce, “Wani jarumi ne, mai suna Karniliyas, mutumin kirki, mai tsoron Allah, wanda duk jama'ar Yahudawa suke yabo, shi ne wani tsattsarkan mala'ika ya umarce shi, ya aiko ka je gidansa, ya ji maganarka.” 23 Sai Bitrus ya shigo da su, ya sauke su. Kashegari ya tashi suka tafi tare, waɗansu 'yan'uwa kuma daga Yafa suka raka shi. 24 Kashegari kuma suka shiga Kaisariya. Dā ma Karniliyas yana tsammaninsu, har ya gayyato 'yan'uwansa da aminansa. 25 Bitrus yana shiga gidan ke nan sai Karniliyas ya tarye shi, ya fāɗi a gabansa, ya yi masa sujada. 26 Amma Bitrus ya tashe shi, ya ce, “Tashi, ai, ni ma ɗan adam ne.” 27 Bitrus yana zance da shi, ya shiga ya tarar mutane da yawa sun taru. 28 Ya ce musu, “Ku da kanku kun sani, bai halatta Bayahude ya yi cuɗanya, ko ya ziyarci wani na wata kabila dabam ba. Amma Allah ya nuna mini kada in ce da kowa marar tsarki, ko mai ƙazanta. 29 Saboda haka da aka neme ni, na zo, ban ce a'a ba. To, a yanzu ina so in ji abin da ya sa kuka kira ni.” 30 Sai Karniliyas ya ce, “Yau kwana uku ke nan, a wajen war haka, ina addu'ar ƙarfe uku na yamma a gidana, sai wani mutum a tsaye a gabana, yana saye da tufafi masu ɗaukar ido, 31 ya ce, ‘Ya Karniliyas, an amsa addu'arka sadakarka kuma ta zama abar tunawa ga Allah. 32 Saboda haka sai ka aika Yafa a kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, yă sauka a gidan Saminu majemi a bakin bahar.’ 33 Nan da nan kuwa na aika maka, ka kuma kyauta da ka zo. To, a yanzu ga mu duk mun hallara a gaban Allah, domin mu ji duk irin abin da Ubangiji ya umarce ka.”

Bitrus ya yi Jawabi a Gidan Karniliyas

34 Sai Bitrus ya kāda baki ya ce, “Hakika na gane lalle Allah ba ya tara, 35 amma a kowace al'umma duk mai tsoronsa, mai kuma aikata adalci, abin karɓuwa ne a gare shi. 36 Allah ya aiko wa Isra'ilawa, ana yi musu bisharar salama ta wurin Yesu Almasihu, shi ne kuwa Ubangijin kowa. 37 Kun dai san labarin nan da ya bazu a duk ƙasar Yahudiya, an fara tun daga ƙasar Galili, bayan baftismar da Yahaya ya yi wa'azi, 38 wato labarin Yesu Banazare, yadda Allah ya shafe shi da Ruhu Mai Tsarki da kuma iko, da yadda ya riƙa zagawa yana aikin alheri, yana warkar da duk waɗanda Iblis ya matsa wa, domin Allah yana tare da shi. 39 Mu kuwa shaidu ne ga duk abin da ya yi a ƙasar Yahudawa da Urushalima. Shi ne kuma suka kashe ta wurin kafa shi a jikin gungume. 40 Shi ne Allah ya tashe shi a rana ta uku, ya kuma yarda ya bayyana, 41 ba ga dukan jama'a ba, sai dai ga shaidun nan da Allah ya zaɓa tun dā, wato mu ke nan, da muka ci muka sha tare da shi, bayan ya tashi daga matattu. 42 Ya kuma umarce mu mu yi wa mutane wa'azi, mu kuma tabbatar cewa shi ne wanda Allah ya sa mai hukunta rayayyu da matattu. 43 Shi ne duk annabawa suka yi wa shaida, cewa albarkacin sunansa duk mai gaskatawa da shi zai sami gafarar zunubai.”

An Ba Al'ummai Ruhu Mai Tsarki

44 Bitrus yana a cikin wannan magana, sai Ruhu Mai Tsarki ya sauko wa dukan masu jinta. 45 Sai Yahudawa masu bi, ɗaukacin waɗanda suka zo tare da Bitrus, suka yi mamakin ganin har al'ummai ma an zubo musu baiwar Ruhu Mai Tsarki. 46 Domin sun ji suna magana da waɗansu harsuna, suna ta ɗaukaka Allah. Sa'an nan Bitrus ya ce, 47 “Akwai mai iya hana ruwan da za a yi wa mutanen nan baftisma, waɗanda suka sami Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda mu ma muka samu?” 48 Sai ya yi umarni a yi musu baftisma da sunan Yesu Almasihu. Sa'an nan suka roƙe shi ya ƙara 'yan kwanaki a gunsu.

Ayyukan Manzanni 11

Bitrus ya Yi wa Ikilisiyar Urushalima Bayani

1 To, manzanni da 'yan'uwa da suke a ƙasar Yahudiya suka ji, cewa al'ummai ma sun yi na'am da Maganar Allah. 2 Da Bitrus ya zo Urushalima, 'yan ɗariƙar masu kaciyar nan suka yi masa s�ka, 3 suka ce, “Ga shi, ka shiga wurin marasa kaciya, har ka ci abinci tare da su!” 4 Sai Bitrus ya fara, yana yi musu bayani bi da bi cewa, 5 “Ni dai, ina birnin Yafa ina addu'a, sai wahayi ya zo mini, na ga wani abu yana saukowa kamar babban mayafi, an zuro shi daga sama ta kusurwoyinsa huɗu, har ya zo wurina. 6 Da na zuba masa ido, na duba na ga dabbobi, da namomin jeji, da masu jan ciki, da kuma tsuntsaye a ciki. 7 Sai kuma na ji wata murya ta ce mini, ‘Bitrus, ka tashi, ka yanka, ka ci.’ 8 Amma na ce, ‘A'a, ya Ubangiji, don ba wani abu marar tsarki ko mai ƙazanta da ya taɓa shiga bakina.’ 9 Sai muryar ta amsa daga Sama ta yi magana ta biyu, ta ce, ‘Abin da Allah ya tsarkake, kada ka ce da shi marar tsarki.’ 10 An yi wannan sau uku, sa'an nan aka janye abin sama. 11 Ba zato sai ga mutum uku a tsaye a ƙofar gidan da muke, an aiko su wurina ne daga Kaisariya. 12 Sai Ruhu ya ce mini in tafi tare da su, ba tare da wata shakka ba. 'Yan'uwan nan shida kuma suka rako ni, har muka shiga gidan mutumin nan. 13 Sai ya gaya mana yadda ya ga mala'ika a tsaye a gidansa, yana cewa, ‘Ka aika Yafa a kirawo Saminu, wanda ake kira Bitrus, 14 shi zai faɗa maka maganar da za ka sami ceto a game da ita, kai da jama'ar gidanka duka.’ 15 Da fara maganata, Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu, a daidai yadda ya sauko mana tun da farko. 16 Sai na tuna da Maganar Ubangiji, yadda ya ce, ‘Yahaya kam, da ruwa ya yi baftisma, amma ku da Ruhu Mai Tsarki za a yi muku baftisma.’ 17 Tun da yake Allah ya yi musu baiwa daidai da wadda ya yi mana, sa'ad da muka gaskata da Ubangiji Yesu Almasihu, wane ni da zan dage wa Allah!” 18 Da suka ji haka, suka rasa ta cewa, suka kuma ɗaukaka Allah suka ce, “Ashe, har al'ummai ma Allah ya ba su tuba zuwa rai.”

Ikilisiya a Antakiya ta Suriya

19 To, waɗanda suka warwatsu saboda tsananin nan da ya tashi a kan sha'anin Istifanas, sun yi tafiya har ƙasar Finikiya, da tsibirin Kubrus, da birnin Antakiya, ba su yin wa'azin Maganar Allah ga kowa sai ga Yahudawa kaɗai. 20 Amma akwai waɗansu mutanen Kubrus da na Kurane a cikinsu waɗanda da isowarsu Antakiya suka yi wa al'ummai magana, suna yi musu bisharar Ubangiji Yesu. 21 Ikon Ubangiji kuwa na tare da su, har mutane da yawa da suka ba da gaskiya suka juyo ga Ubangiji. 22 Sai labarin nan ya kai kunnen ikilisiyar da take Urushalima, Ikilisiyar kuma ta aiki Barnaba zuwa can Antakiya. 23 Da ya iso ya kuma ga alherin da Allah ya yi musu, ya yi farin ciki, ya gargaɗe su duka su tsaya ga Ubangiji da dukan zuciyarsu, 24 domin shi mutum ne nagari a cike da Ruhu Mai Tsarki da bangaskiya. Sai mutane masu yawan gaske suka ƙaru ga Ubangiji. 25 Sai Barnaba ya tafi Tarsus neman Shawulu, 26 bayan da ya same shi kuwa, sai ya kawo shi Antakiya. Shekara gaba ɗaya cur suna taruwa da Ikilisiya, suna koya wa mutane masu yawan gaske. A Antakiya ne aka fara kiran masu bi da suna Kirista. 27 To, a kwanakin nan waɗansu annabawa suka zo Antakiya daga Urushalima. 28 Sai ɗaya daga cikinsu, mai suna Agabas, ya miƙe a tsaye, ya yi faɗi da ikon Ruhu, cewa za a yi wata babbar yunwa, a duniya duka, an yi ta kuwa a zamanin Kalaudiyas. 29 Sai masu bi suka ɗaura niyya, kowa gwargwadon ƙarfinsa, su aika wa yan'uwan da suke ƙasar Yahudiya gudunmawa. 30 Haka kuwa suka yi, suka aika wa dattawan Ikilisiya ta hannun Barnaba da Shawulu.

Ayyukan Manzanni 12

An Kashe Yakubu, an Kulle Bitrus

1 A lokacin nan kuwa sarki Hirudus ya fara gwada wa waɗansu 'yan Ikilisiya azaba, 2 har ma ya sare Yakubu ɗan'uwan Yahaya da takobi. 3 Da ya ga abin ya ƙayatar da Yahudawa, har wa yau kuma ya kama Bitrus, shi ma. A kwanakin idin abinci marar yisti ne kuwa. 4 Da ya kama shi, ya sa shi a kurkuku, ya danƙa shi a hannun soja hurhuɗu kashi huɗu, don su yi tsaronsa, da niyyar kawo shi a gaban jama'a bayan idin. 5 Sai aka tsare Bitrus a kurkuku, Ikilisiya kuwa ta himmantu ga roƙon Allah saboda shi.

An Ceci Bitrus daga Kurkuku

6 A daren da in gari ya waye Hirudus yake da niyyar fito da shi a yi masa hukunci, Bitrus kuwa yana barci a tsakanin soja biyu, ɗaure da sarƙa biyu, masu tsaronsa kuma suna bakin ƙofa suna tsaron kurkukun, 7 sai ga mala'ikan Ubangiji a tsaye a kusa da shi, wani haske kuma ya haskaka ɗakin, sa'an nan mala'ikan ya bugi Bitrus a kwiɓi, ya tashe shi, ya ce, “Maza, ka tashi.” Sai kuwa sarƙar ta zube daga hannunsa. 8 Mala'ikan ya ce masa, “Yi ɗamara, ka sa takalminka.” Sai ya yi. Sai ya ce masa, “Yafa mayafinka, ka biyo ni.” 9 Sai ya fito ya bi shi, bai san abin da mala'ikan nan ya yi hakika ne ba, cewa yake wahayi ake yi masa. 10 Da suka wuce masu tsaron farko da na biyu, suka isa ƙyauren ƙarfe na ƙofar shiga gari, ƙyauren kuwa ya buɗe musu don kansa. Sai suka fita. Sun ƙure wani hanya ke nan, nan da nan sai mala'ikan ya bar shi. 11 Da Bitrus ya koma a cikin hankalinsa, ya ce, “Yanzu kam na tabbata, Ubangiji ne ya aiko mala'ikansa, ya cece ni daga hannun Hirudus, da kuma dukan mugun fatan Yahudawa.” 12 Da ya gane haka, ya je gidan Maryamu, mahaifiyar Yahaya wanda ake kira Markus, a inda aka taru da yawa, ana addu'a. 13 Da ya ƙwanƙwasa ƙofar zauren, wata baranya mai suna Roda ta zo ji ko wane ne. 14 Da ta shaida muryar Bitrus, ba ta buɗe ƙofar ba don murna, sai ta koma ciki a guje, ta ce Bitrus yana tsaye a ƙofar zaure. 15 Sai suka ce mata, “Ke dai akwai ruɗaɗɗiya.” Ita kuwa ta nace a kan shi ne. Su kuwa suka ce, “To, mala'ikansa ne!” 16 Bitrus dai ya ta ƙwanƙwasawa, da suka buɗe suka gan shi, suka yi ta al'ajabi. 17 Shi kuwa ya ɗaga musu hannu su yi shiru, ya kuma bayyana musu yadda Ubangiji ya fito da shi daga kurkuku. Ya kuma ce, “Ku faɗa wa Yakubu da 'yan'uwa waɗannan abubuwa.” Sa'an nan ya tashi ya tafi wani wuri. 18 Da gari ya waye kuwa ba ƙaramar rigima ce ta tashi a tsakanin sojan nan ba, a kan abin da ya sami Bitrus. 19 Da Hirudus ya neme shi bai same shi ba, ya yi tuhumar masu tsaron, ya kuma yi umarni a kashe su. Sa'an nan ya tashi daga ƙasar Yahudiya ya tafi Kaisariya, ya yi 'yan kwanaki a can.

Mutuwar Hirudus

20 To, sai Hirudus ya yi fushi ƙwarai da mutanen Taya da na Sidon. Suka zo wurinsa da nufi ɗaya. Bayan da suka rinjayi Bilastasa, sarkin fāda, suka nemi zaman lafiya, domin ga ƙasar sarkin nan suka dogara saboda abincinsu. 21 Ana nan a wata rana da aka shirya, Hirudus ya yi shigar sarauta, ya zauna a gadon sarauta, ya yi musu jawabi. 22 Taron mutane kuwa suka ɗauki sowa, suna cewa, “Kai! ka ji muryar wani Allah, ba ta mutum ba!” 23 Nan tāke sai mala'ikan Ubangiji ya buge shi don bai ɗaukaka Allah ba. Sai tsutsotsi suka yi ta cinsa har ya mutu.

Barnaba da Shawulu

24 Maganar Allah kuwa sai ƙara haɓaka take yi, tana yaɗuwa. 25 Sai Barnaba da Shawulu suka komo daga Urushalima, bayan sun cika aikin da aka yi musu, suka kuma zo da Yahaya wanda ake kira Markus.

Ayyukan Manzanni 13

1 To, a Ikilisiyar da ke Antakiya akwai waɗansu annabawa, da masu koyarwa, wato Barnaba, da Saminu wanda ake kira Băƙi, da Lukiyas Bakurane, da Manayan wanda aka goya tare da sarki Hirudus, da kuma Shawulu. 2 Sa'ad da suke yi wa Ubangiji ibada, suna kuma yin azumi, sai Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Sai ku kuɓe mini Barnaba da Shawulu domin aikin da na kira su a kai.” 3 Bayan kuma sun yi azumi, sun kuma yi addu'a, sai suka ɗora musu hannu, suka sallame su.

Manzanni sun yi Wa'azi a Kubrus

4 Su kuwa, da Ruhu Mai Tsarki ya aike su, suka tafi Salukiya, daga can kuma suka shiga jirgin ruwa, sai tsibirin Kubrus. 5 Da suka kai Salamis, suka sanar da Maganar Allah a majami'un Yahudawa, ga kuma Yahaya yana taimakonsu. 6 Bayan sun zazzaga tsibirin duka har Bafusa, suka iske wani mai sihiri, annabin ƙarya, Bayahude, mai suna Bar-yashu'a, 7 Wanda yake tare da muƙaddas Sarjiyas Bulus, mutum ne mai basira. Sai muƙaddashin ya kira Barnaba da Shawulu ya nemi jin Maganar Allah. 8 Amma Alimas mai sihirin nan, (don wannan ita ce ma'anar sunansa), ya m�sa musu, yana neman bauɗar da muƙaddashin nan daga bangaskiya. 9 Shawulu kuwa, wanda kuma ake kira Bulus, a cike da Ruhu Mai Tsarki, ya zuba masa ido, 10 ya ce, “Kai babban maha'inci, munafiƙi, ɗan Iblis, magabcin adalci duka, ba za ka daina karkata miƙaƙƙun hanyoyin Ubangiji ba? 11 To, ga shi, hannun Ubangiji yana kanka, za ka makance, ba za ka ga rana ba har wani lokaci.” A nan take kuwa sai wani hazo da duhu suka rufe shi, ya yi ta neman wanda zai yi masa jagora. 12 Da muƙaddashin ya ga abin da ya faru, sai ya ba da gaskiya, yana mamaki da koyarwar Ubangiji.

Bulus da Barnaba a Antakiya ta Bisidiya

13 Sai Bulus da abokan tafiyarsa suka tashi daga Bafusa a jirgin ruwa, suka isa Bariyata ta ƙasar Bamfiliya. Yahaya kuwa ya bar su, ya koma Urushalima. 14 Amma suka wuce gaba daga Bariyata, suka tafi Antakiya ta ƙasar Bisidiya. A ran Asabar kuma sai suka shiga majami'a suka zauna. 15 Bayan da aka yi karatun Attaura da littattafan annabawa, shugabannin majami'ar suka aika musu, suka ce, “'Yan'uwa, in kuna da wata maganar gargaɗi da za ku yi wa jama'a, sai ku yi.” 16 Sai Bulus ya miƙe, ya ɗaga hannu a yi shiru, ya ce, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, da sauran masu tsoron Allah, ku saurara! 17 Allahn jama'ar nan Isra'ila ya zaɓi kakanninmu, ya ɗaukaka jama'ar sa'ad da suke baƙunci a ƙasar Masar, da maɗaukakin iko kuma ya fito da su daga cikinta. 18 Har wajen shekara arba'in yake haƙuri da su a cikin jeji. 19 Ya kuma hallaka al'umma bakwai a ƙasar Kan'ana, sai ya raba musu ƙasar tasu gādo, suka zauna har shekara arbaminya da hamsin. 20 Bayan haka kuma, sai ya naɗa musu mahukunta har ya zuwa zamanin Annabi Sama'ila. 21 Sa'an nan suka roƙa a naɗa musu sarki, sai Allah ya ba su Saul ɗan Kish, mutumin kabilar Biliyaminu, har shekara arba'in. 22 Bayan da ya kawar da shi sai ya gabatar da Dawuda ya zama sarkinsu, ya kuma shaide shi da cewa, ‘Na sami Dawuda ɗan Yesse, mutum ne da nake ƙauna ƙwarai, wanda zai aikata dukan nufina.’ 23 Daga zuriyar mutumin nan ne Allah ya kawo wa Isra'ila Mai Ceto, Yesu kamar yadda ya yi alkawari. 24 Kafin ya bayyana a fili kuwa, Yahaya ya yi wa duk jama'ar Isra'ila wa'azi cewa, su tuba a kuma yi musu baftisma. 25 Yayin da Yahaya ya kusa gama nasa zamani, sai ya ce, ‘Wa kuke tsammani nake? Ba fa ni ne shi ɗin nan ba. Amma ga shi akwai wani mai zuwa a bayana, wanda ko takalmansa ma ban isa in ƙwance ba.’ 26 “Ya ku 'yan'uwa, zuriyar Ibrahim, da kuma sauran masu tsoron Allah a cikinku, mu fa aka aiko wa kalmar ceton nan. 27 Ga shi, mazaunan Urushalima da shugabanninsu ba su gane shi ba, sa'an nan kuma ba su fahimci maganar annabawa da ake karantawa a kowace Asabar ba, har suka cika maganar nan ta annabawa, a yayin da suka hukunta shi. 28 Ko da yake ba su same shi da wani laifin kisa ba, duk da haka suka roƙi Bilatus don a kashe shi. 29 Da suka cikasa dukkan abin da aka rubuta a game da shi, suka sauko da shi daga kan gungumen, suka sa shi a kabari. 30 Amma Allah ya tashe shi daga matattu. 31 Kwanaki da yawa kuwa yana bayyana ga waɗanda suka zo tare da shi Urushalima daga Galili, waɗanda a yanzu su ne shaidunsa ga jama'a. 32 Mu ma mun kawo muku albishir, cewa, alkawarin nan da Allah ya yi wa kakanninmu, 33 ya cika mana shi, mu zuriyarsu, da ya ta da Yesu daga matattu, yadda yake a rubuce a cikin Zabura ta biyu cewa, ‘Kai Ɗana ne, Ni Ubanka ne yau.’ 34 A game da ta da shi daga matattu da Allah ya yi, a kan cewa ba zai sāke komawa cikin halin ruɓa ba kuwa, ga abin da ya ce, ‘Zan yi muku tsattsarkar albarkar nan da na tabbatar wa Dawuda.’ 35 Domin a wata Zabura ma ya ce, ‘Ba za ka yarda Mai Tsarkinka ya ruɓa ba.’ 36 Dawuda kam, bayan da ya bauta wa mutanen zamaninsa bisa ga nufin Allah, ya yi barci, aka binne shi tare da kakanninsa, ya kuwa ruɓe. 37 Amma shi wannan da Allah ya tashe shi, bai ruɓa ba. 38 Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku sani albarkacin mutumin nan ne ake sanar da ku gafarar zunubanku. 39 Ta gare shi kuma, duk masu ba da gaskiya suka kuɓuta daga dukan abubuwan da ba dama Shari'ar Musa ta kuɓutar da ku. 40 Saboda haka sai ku mai da hankali, kada abin nan da littattafan annabawa ke faɗa ya aukar muku, wato 41 ‘Ga shi, ku masu rainako, Za ku ruɗe don mamaki, ku shuɗe! Domin zan yi wani aiki a zamaninku, Aikin da ba yadda za a yi ku gaskata, Ko da wani ya gaya muku.’ ” 42 Suna fita daga majami'a ke nan, sai mutane suka roƙe su, don su ƙara yi musu wannan magana a ran Asabar mai zuwa. 43 Da jama'a suka watse, Yahudawa da yawa, da kuma waɗanda suka shiga Yahudanci, masu ibada, suka bi Bulus da Barnaba. Su kuma suka yi musu magana, suna yi musu gargaɗi cewa su zauna a cikin alherin Allah. 44 Da Asabar ta kewayo, kusan duk birnin, suka hallara don su ji Maganar Allah. 45 Amma da Yahudawa suka ga taro masu yawa, suka yi kishi gaya, suka yi ta musun abubuwan da Bulus ya faɗa, suna zaginsa. 46 Sai Bulus da Barnaba suka yi magana gabagaɗi, suka ce, “Ku, ya wajaba a fara yi wa Maganar Allah, amma da yake kun ture ta, kun nuna ba ku cancanci samun rai madawwami ba, to, za mu juya ga al'ummai. 47 Domin haka ubangiji ya umarce mu, ya ce, ‘Na sa ka haske ga al'ummai, Don ka zama sanadin ceto, har ya zuwa iyakar duniya.’ ” 48 Da al'ummai suka ji haka, suka yi farin ciki, suka ɗaukaka Maganar Ubangiji, ɗaukacin kuma waɗanda aka ƙaddara wa samun rai madawwami suka ba da gaskiya. 49 Maganar Ubangiji kuwa, sai ta yi ta yaɗuwa a duk ƙasar. 50 Amma Yahudawa suka zuga waɗansu mata masu ibada, masu daraja, da kuma waɗansu manyan gari, suka haddasa tsanani ga Bulus da Barnaba, suka kore su daga ƙasarsu. 51 Su kuwa suka karkaɗe ƙurar ƙafafunsu don shaida a kansu, suka tafi Ikoniya. 52 Amma kuwa masu bi suna ta farin ciki matuƙa, suna kuma a cike da Ruhu Mai Tsarki.

Ayyukan Manzanni 14

Bulus da Barnaba a Ikoniya

1 To, a Ikoniya suka shiga majami'ar Yahudawa tare, suka yi wa'azi, har mutane masu yawa, Yahudawa da al'ummai, suka ba da gaskiya. 2 Amma Yahudawa da suka ƙi bi, suka zuga al'ummai, suka ɓata tsakaninsu da 'yan'uwa. 3 Sai Bulus da Barnaba suka daɗe a nan ƙwarai, suna wa'azi gabagaɗi bisa ga ikon Ubangiji, shi da ya shaida maganar alherinsa ta yarjin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi ta hannunsu. 4 Amma mutanen birni suka rarrabu, waɗansu suka koma bayan Yahudawa, waɗansu kuma bayan manzannin. 5 Sa'ad da al'ummai da Yahudawa tare da shugabanninsu suka tasar wa manzannin, su wulakanta su, su jejjefe su da duwatsu, 6 suka sami labari, suka gudu zuwa biranen Likoniya wato Listira da Darba, da kuma kewayensu. 7 A nan suka yi ta yin bisharar.

An Jejjefi Bulus a Listira

8 To, a Listira akwai wani mutum a zaune, wanda ƙafafunsa ba su da ƙarfi, gurgu ne tun da aka haife shi, bai ma taɓa tafiya ba. 9 Yana sauraron wa'azin Bulus, sai Bulus ya zuba masa ido, da ya ga bangaskiyarsa ta isa a warkar da shi, 10 sai ya ɗaga murya ya ce, “Tashi, ka tsaya cir.” Sai wuf ya zabura, har ya yi tafiya. 11 Da taron suka ga abin da Bulus ya yi, suka ɗaga murya gaba ɗaya suna cewa da Likoniyanci, “Lalle, alloli sun sauko mana da siffar mutane!” 12 Sai suka ce Barnaba shi ne Zafsa, Bulus kuwa don shi ne shugaban magana, shi ne Hamisa. 13 Sai sarkin tsafin Zafsa, wanda ɗakin gunkinsa yake a ƙofar gari, ya kawo bajimai da tutocin furanni a ƙofar gari, yana son yin hadaya tare da jama'a. 14 Amma da manzannin nan, Barnaba da Bulus, suka ji haka, suka kyakketa tufafinsu, suka ruga zuwa cikin taron, suna ɗaga murya suna cewa, 15 “Don me kuke yin haka? Ai, mu ma 'yan adam ne kamarku, mun dai kawo muku bishara ne, domin ku juya wa abubuwan banzan nan baya, ku juyo ga Allah Rayayye, wanda ya halicci sama, da ƙasa, teku, da kuma dukkan abin da yake a cikinsu. 16 Shi ne a zamanin dā, ya bar dukan al'ummai su yi yadda suka ga dama. 17 Duk da haka kuwa bai taɓa barin kansa, ba shaida ba, domin yana yin alheri, shi da yake yi muku ruwan sama, da damuna mai albarka, yana ƙosar da ku da abinci, yana kuma faranta muku rai.” 18 Duk da waɗannan maganganu da ƙyar suka hana jama'ar nan yin hadaya saboda su. 19 Amma waɗansu Yahudawa suka zo daga Antakiya da Ikoniya, da suka rarrashi taron, suka jejjefe Bulus suka ja shi zuwa bayan gari, suna zato ya mutu. 20 Amma da masu bi suka taru a kansa, sai ya tashi ya koma garin. Kashegari kuma ta tafi Darba tare da Barnaba. 21 Bayan sun yi bishara a wannan gari, sun kuma sami masu bi da yawa, suka koma Listira da Ikoniya, da kuma Antakiya, 22 suna ƙarfafa masu bi, suna yi musu gargaɗi su tsaya ga bangaskiya, suna cewa, sai da shan wuya mai yawa za mu shiga Mulkin Allah. 23 Bayan kuma sun zaɓar musu dattawa a kowace Ikilisiya, a game da addu'a da azumi, suka danƙa su ga Ubangiji, wanda dā ma suka gaskata da shi.

Komawa Antakiya ta Suriya

24 Da suka zazzaga ƙasar Bisidiya, suka isa ƙasar Bamfiliya. 25 Da kuma suka faɗi Maganar a Bariyata, suka tafi Ataliya. 26 Daga nan kuma suka shiga jirgin ruwa sai Antakiya, a inda tun dā aka yi musu addu'a alherin Allah ya kiyaye su a cikin aikin nan da a yanzu suka gama. 27 Da suka iso, suka tara jama'ar Ikilisiya suka ba da labarin dukan abin da Allah ya aikata ta wurinsu, da kuma yadda ya buɗe wa al'ummai ƙofar bangaskiya. 28 Sun kuwa jima a can tare da masu bi.

Ayyukan Manzanni 15

Majalisar Ikilisiyar Urushalima

1 Sai kuma waɗansu mutane suka zo daga Yahudiya suna koya wa 'yan'uwa, suna cewa, “In ba an yi muku kaciya kamar yadda al'adar Musa take ba, ba dama ku sami ceto.” 2 A kan wannan magana kuwa ba ƙaramar gardama da muhawwara Bulus da Barnaba suka sha yi da mutanen ba. Sai aka sa Bulus da Barnaba da kuma waɗansunsu, su je Urushalima a gun manzanni da dattawan ikilisiya a kan wannan magana kuwa. 3 To, da Ikilisiya ta raka su, sai suka zazzaga ƙasar Finikiya da ta Samariya, suna ba da labarin tubar al'ummai, sun kuwa ƙayatar da dukan 'yan'uwa ƙwarai. 4 Da suka isa Urushalima, Ikilisiya, da manzanni, da dattawan Ikilisiya suka yi musu maraba, su kuma suka gaggaya musu dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. 5 Amma waɗansu masu ba da gaskiya, 'yan ɗariƙar Farisiyawa, suka miƙe, suka ce, “Wajibi ne a yi musu kaciya, a kuma umarce su, su bi Shari'ar Musa.” 6 Sai manzannin da dattawan Ikilisiya suka taru don su duba maganar. 7 Bayan da aka yi ta muhawwara da gaske, Bitrus ya miƙe a tsaye, ya ce musu, “Ya 'yan'uwa, kun sani tun farkon al'amari, Allah ya yi zaɓe a cikinku, cewa dai ta bakina ne al'ummai za su ji maganar bishara, su ba da gaskiya. 8 Allah kuwa, masanin zuciyar kowa, ya yi musu shaida da ya ba su Ruhu Mai Tsarki, kamar yadda ya ba mu. 9 Bai kuma nuna wani bambanci a tsakaninmu da su ba, tun da yake ya tsarkake zukatansu saboda bangaskiyarsu. 10 Saboda haka, don me kuke gwada Allah, ta ɗora wa almajiran nan kayan da mu, duk da kakanninmu, muka kasa ɗauka? 11 Amma mun gaskata, cewa, albarkacin alherin Ubangiji Yesu ne muka sami ceto, kamar yadda su ma suka samu.” 12 Sai duk taron mutane suka yi tsit, suka saurari Barnaba da Bulus, sa'ad da suke ba da labarin mu'ujizai da abubuwan al'ajabi, da Allah ya yi ga al'ummai ta wurinsu. 13 Bayan da suka gama jawabi, sai Yakubu ya amsa ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku saurare ni. 14 Bitrus ya ba da labari yadda Allah ya fara kula da al'ummai, domin ya keɓe wata jama'a daga cikinsu ta zama tasa. 15 Wannan kuwa daidai yake da maganar annabawa, yadda yake a rubuce cewa, 16 ‘Bayan haka kuma zan komo, In sāke gina gidan Dawuda da ya rushe, In sāke ta da kangonsa, In tsai da shi, 17 Domin sauran mutane su nemi Ubangiji, Wato al'umman da suke nawa.’ 18 Haka Ubangiji ya ce, shi da ya bayyana waɗannan abubuwa tun zamanin dā. 19 Saboda haka, a ganina, kada mu matsa wa al'ummai waɗanda suke juyowa ga Allah, 20 sai dai mu rubuta musu wasiƙa, su guji abubuwan ƙazanta na game da gumaka, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini. 21 Domin tun a zamanin dā, a kowane gari akwai masu yin wa'azi da littattafan Musa, ana kuma karanta su a majami'u kowace Asabar.”

Amsar Majalisar Ikilisiya

22 Sai manzanni da dattawan Ikilisiya, tare da dukan 'yan Ikilisiya, suka ga ya kyautu su zaɓi waɗansu daga cikinsu, su aike su Antakiya tare da Bulus da Barnaba. Sai suka aiki Yahuza, wanda ake kira Barsaba, da kuma Sila, shugabanni ne a cikin 'yan'uwa, 23 da wannan takarda cewa, “Daga 'yan'uwanku, manzanni da dattawan Ikilisiya, zuwa ga 'yan'uwanmu na al'ummai a Antakiya da ƙasar Suriya da ta Kilikiya. Gaisuwa mai yawa. 24 Tun da muka sami labari, cewa waɗansu daga cikinmu sun ta da hankalinku da maganganu, suna ruɗa ku, ko da yake ba mu umarce su da haka ba, 25 sai muka ga ya kyautu, da yake bakinmu ya zo ɗaya, mu aiko muku da waɗansu zaɓaɓɓun mutane, tare da ƙaunatattunmu Barnaba da Bulus, 26 waɗanda suka sayar da ransu saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu. 27 Don haka, ga shi, mun aiko muku Yahuza da Sila, su ma za su gaya muku waɗannan abubuwa da bakinsu. 28 Domin Ruhu Mai Tsarki ya ga ya kyautu, mu ma mun gani, kada a ɗora muku wani nauyi fiye da na waɗannan abubuwa da suke wajibi, wato 29 ku guji abin da aka yanka wa gunki, da cin nama tare da jini, da cin abin da aka maƙure, da kuma fasikanci. In kun tsare kanku daga waɗannan, za ku zauna lafiya. Wassalam.” 30 Su kuma da aka sallame su, suka tafi Antakiya, da suka tara jama'ar, suka ba da wasiƙar. 31 Da suka karanta ta, suka yi farin ciki saboda gargaɗin. 32 Yahuza da Sila kuma, da yake su annabawa ne, suka gargaɗi 'yan'uwa da maganganu masu yawa, suka kuma ƙarfafa su. 33 Bayan da suka yi 'yan kwanaki a wurin, sai 'yan'uwa suka sallame su lafiya, suka koma wurin waɗanda suka aiko su. 34 Amma Sila ya ga ya kyautu shi ya zauna a nan. 35 Bulus da Barnaba kuwa suka dakata a Antakiya, suna koyarwa suna kuma yin bisharar Maganar Ubangiji, tare da waɗansu ma da yawa.

Bulus ya Rabu da Barnaba

36 Da aka jima, sai Bulus ya ce wa Barnaba, “Bari yanzu mu koma mu dubo 'yan'uwa a kowane gari da muka sanar da Maganar Ubangiji, mu ga yadda suke.” 37 Barnaba kuwa ya so su tafi da Yahaya, wanda ake kira Markus. 38 Amma Bulus bai ga ya kyautu su tafi da wanda ya rabu da su a ƙasar Bamfiliya, ya ƙi tafiya aiki tare da su ba. 39 Sai matsanancin saɓanin ra'ayi ya auku, har ya kai su ga rabuwa. Barnaba ya ɗauki Markus, suka shiga jirgin ruwa zuwa tsibirin Kubrus, 40 amma Bulus ya zaɓi Sila, bayan da 'yan'uwa suka yi masa addu'a alherin Allah ya kiyaye shi, ya tafi. 41 Bulus ya zazzaga ƙasar Suriya da ta Kilikiya, yana ta ƙarfafa Ikilisiyoyi.

Ayyukan Manzanni 16

Timoti ya Bi Bulus da Sila

1 Sai kuma Bulus ya zo Darba da Listira. Akwai wani almajiri a Listira, mai suna Timoti, ɗan wata Bayahudiya mai bi, mahaifinsa kuwa Bahelene ne. 2 Shi kuwa 'yan'uwa da suke Listira da Ikoniya na yabonsa. 3 Sai Bulus ya so Timoti ya rako shi, har ya yi masa kaciya saboda Yahudawan da suke waɗannan wurare, don duk sun san mahaifinsa Bahelene ne. 4 Lokacin da suke tafiya suna bin gari gari, suka riƙa gaya wa jama'a ka'idodin da manzanni da dattawan ikilisiya suka ƙulla a Urushalima, don su kiyaye su. 5 Ta haka ikilisiyoyi suka ƙarfafa a cikin bangaskiya, a kowace rana suna ƙara yawa.

Wahayin Bulus na Mutumin Makidoniya

6 Sai suka zazzaga ƙasar Firijiya da ta Galatiya, saboda Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin Maganar Ubangiji a ƙasar Asiya. 7 Da suka zo kan iyakar ƙasar Misiya, sai suka yi ƙoƙarin zuwa ƙasar Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yardar musu ba. 8 Suka kuwa ratsa ƙasar Misiya, suka gangara zuwa Taruwasa. 9 Wata rana da daddare aka yi wa Bulus wahayi, ya ga wani mutumin ƙasar Makidoniya yana tsaye, yana roƙonsa yana cewa, “Ka ƙetaro Makidoniya, ka taimake mu mana.” 10 Da kuwa ya ga wahayin, nan tāke sai muka nemi tafiya Makidoniya, muka tabbata cewa Allah ne ya kira mu mu yi musu bishara.

Lidiya ta Ba da Gaskiya

11 Shi ke nan fa, sai muka tashi a jirgin ruwa daga Taruwasa, muka miƙe sosai har zuwa tsibirin Samutaraki, kashegari kuma sai Niyabolis, 12 daga nan kuma sai Filibi ta ƙasar Makidoniya, wadda take babbar alkarya ce a wannan waje, birnin Romawa ne kuma. A nan birnin muka yi 'yan kwanaki. 13 A ran Asabar muka fita ƙofar gari, muka je bakin kogi, a inda muke tsammani akwai wurin addu'a. A nan muka zauna, muka yi wa matan da suka taru magana. 14 Ɗaya daga cikin masu sauraronmu wata mace ce, mai suna Lidiya, mai sayar da jar hajja, mutuniyar Tayatira, mai ibada ce kuma. Ubangiji ya buɗe zuciyarta, har ta mai da hankali ga abin da Bulus ya faɗa. 15 Da aka yi mata baftisma tare da jama'ar gidanta, ta roƙe mu ta ce, “Da yake kun amince ni mai ba da gaskiya ga Ubangiji ce, to, sai ku zo gidana ku sauka.” Sai ta rinjaye mu.

Kulle Manzanni a Kurkukun Filibi

16 Wata rana muna tafiya wurin yin addu'a, sai muka gamu da wata yarinya mai aljani mai duba, tana kuwa samo wa iyayengijinta amfani mai yawa ta wurin dubar. 17 Sai ta riƙa binmu, mu da Bulus, tana ihu tana cewa, “Mutanen nan fa bayin Allah Maɗaukaki ne, suna kuwa sanar da ku hanyar ceto!” 18 Haka ta dinga yi kwana da kwanaki, har Bulus ya ji haushi ƙwarai, ya juya ya ce wa aljanin, “Na umarce ka da sunan Yesu Almasihu, ka rabu da ita.” A nan tāke kuwa ya rabu da ita. 19 Da iyayengijinta suka ga hanyar samunsu ta toshe, suka danƙe Bulus da Sila, suka ja su har zuwa bakin kasuwa gaban mahukunta. 20 Da suka kai su a gaban alƙalai suka ce, “Mutanen nan suna birkita garinmu ƙwarai da gaske, Yahudawa ne kuwa. 21 Suna kuma koyar da al'adun da ba su halatta mu karɓa ko mu bi ba, da yake mu Romawa ne.” 22 Sai jama'a suka ɗungumo musu gaba ɗaya, alƙalan kuma suka yi kaca-kaca da tufafinsu, suka tuttuɓe su, suka yi umarni a bulale su da tsumagu. 23 Da aka bulale su da gaske, aka jefa su a kurkuku, aka umarci yari ya tsare su da kyau. 24 Shi kuwa da ya karɓi wannan umarni, sai ya jefa su a can ciki cikin kurkuku, ya sa su a turu. 25 A wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu'a suna waƙoƙin yabon Allah, 'yan sarka kuwa suna sauraronsu, 26 farat ɗaya, sai aka yi wata babbar rawar ƙasa, har harsashin ginin kurkuku ya raurawa. Nan da nan ƙofofin suka bubbuɗe, mărin kowa kuma ya ɓalle. 27 Da yari ya farka daga barci ya ga ƙofofin kurkuku a buɗe, ya zaro takobinsa, yana shirin kashe kansa, cewa yake 'yan sarƙa sun gudu. 28 Amma Bulus ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Kada ka cuci kanka, ai duk muna nan!” 29 Sai yari ya ce a kawo fitilu, ya yi wuf ya ruga ciki, ya fāɗi gaban Bulus da Sila, yana rawar jiki don tsoro. 30 Sa'an nan ya fito da su waje, ya ce, “Ya shugabanni, me zan yi in sami ceto?” 31 Su kuwa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.” 32 Sa'an nan suka gaya masa Maganar Ubangiji, shi da iyalinsa duka. 33 A nan tāke da daddaren nan ya ɗebe su, ya wanke musu raunukansu. Nan da nan kuwa aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa. 34 Sa'an nan ya kawo su gidansa, ya kawo musu abinci, ya yi ta farin ciki matuƙa, domin shi da iyalinsa duka sun gaskata da Allah. 35 Amma da gari ya waye, sai alƙalan suka aiko dogari, suka ce, “Suka ce a sāke mutanen nan.” 36 Yari kuwa ya shaida wa Bulus maganar, ya ce, “Alƙalai sun aiko a sake ku, saboda haka yanzu sai ku fito, ku tafi lafiya.” 37 Amma Bulus ya ce musu, a “Ai, a fili suka daddoke mu, ba ko bin ba'asi, mu ma da muke Romawa bisa ga 'yangaranci, suka jefa mu a kurkuku, a yanzu kuma sā fitar da mu a ɓoye? Sai dai su zo da kansu su fito da mu.” 38 Sai dogarai suka shaida wa alƙalan wannan magana. Su kuwa da suka ji Bulus da Sila Romawa ne suka tsorata. 39 A sa'an nan sai suka zo suka tubar musu, bayan kuma sun fito da su, suka roƙe su su bar garin. 40 To, da suka fita daga kurkukun, suka tafi wurin Lidiya. Bayan da sun ga 'yan'uwa, suka kuma ƙarfafa musu zuciya, suka tashi.

Ayyukan Manzanni 17

Hargitsi a Tasalonika

1 To, da suka bi ta Amfibolis da Aboloniya, suka isa Tasalonika, a inda wata majami'ar Yahudawa tāke. 2 Sai Bulus ya shiga a wurinsu kamar yadda ya saba, Asabar uku a jere yana muhawwara da su daga cikin Littattafai, 3 yana yi musu bayani, yana kuma tabbatarwa, cewa lalle ne, Almasihu yă sha wuya, ya kuma tashi daga matattu. Ya kuma ce, “Yesun nan da nake sanar muku, shi ne Almasihu.” 4 Sai waɗansunsu suka amince, suka koma wajen Bulus da Sila, haka kuma babban taron Helenawa masu ibada, da manyan mata ba kaɗan ba. 5 Amma Yahudawa, saboda kishi, suka ɗibi waɗansu ashararai, 'yan iska, suka tara jama'a suka hargitsa garin kaf, suka fāɗa wa gidan Yason, suna nemansu don su fito da su a gaban taron jama'a. 6 Da ba su same su ba, sai suka jawo Yason da waɗansu 'yan'uwa, har gaban mahukuntan garin, suna ihu suna cewa, “Mutanen nan masu ta da duniya a tsaye, ga su sun zo nan ma, 7 har ma Yason ya sauke su! Dukansu kuwa suna saɓa dokokin Kaisar, suna cewa wani ne sarki, cewa shi Yesu ne.” 8 Da mutanen gari da mahukunta suka ji wannan, hankalinsu ya tashi. 9 Ba su sake su ba, sai da suka karɓi kuɗin lamuni a hannun Yason da sauransu.

Manzanni a Biriya

10 Nan da nan kuwa da dare ya yi, 'yan'uwa suka sallami Bulus da Sila su tafi biriya. Da suka isa can kuma suka shiga majami'ar Yahudawa. 11 To, waɗannan Yahudawa kam, sun fi na Tasalonika dattaku, domin sun karɓi Maganar hannu biyu biyu, suna ta nazarin Littattafai a kowace rana, su ga ko abin haka yake. 12 Saboda haka da yawa daga cikinsu suka ba da gaskiya, har waɗansu Helenawa ba kaɗan ba, mata masu daraja, da kuma maza. 13 Amma da Yahudawan Tasalonika suka ji labari Bulus yana sanar da Maganar Allah a Biriya ma, suka je suka zuga taro masu yawa a can ma, suna ta da hankalinsu. 14 Nan da nan kuwa 'yan'uwa suka tura Bulus a bakin bahar, amma Sila da Timoti suka dakata a nan. 15 Waɗanda suka rako Bulus kuwa, sai da suka kai shi har Atina. Bayan da Bulus ya yi musu saƙon umarni zuwa wurin Sila da Timoti, cewa su zo wurinsa da gaggawa, suka tafi.

Bulus a Atina

16 To, sa'ad da Bulus yake dākonsu a Atina, ya ji haushi ƙwarai da ya ga a ko'ina gumaka ne a birnin. 17 A kowace rana ya yi ta muhawwara a cikin majami'a da Yahudawa, da waɗansu masu ibada, da kuma waɗanda yake tararwa a bakin kasuwa. 18 Har wa yau kuma waɗansu Abikuriyawa da Sitokiyawa masu ilimi suka ci karo da shi. Waɗansu suka ce, “Me wannan mai surutu yake nufi?” Waɗansu kuwa suka ce “Ga alama, mai yin wa'azin bāƙin alloli ne”�domin kawai yana yin bisharar Yesu, da kuma tashi daga matattu. 19 Sai suka riƙe shi suka kai shi Tudun Arasa, suka ce, “Ko ka faɗa mana wace irin baƙuwar koyarwa ce wannan da kake yi? 20 Domin ka kawo mana abin da yake baƙo a gare mu, muna kuwa so mu san ma'anarsa.” 21 Alhali kuwa duk Atinawa da baƙinsu ba abin da suke yi, sai kashe zarafinsu a wajen jin baƙon abu, ko kuma ɗorar da shi. 22 Sai Bulus ya miƙe a tsaye Tudun Arasa, ya ce, “Ya ku mutanen Atina, na dai lura, ku masoyan ibada ne ƙwarai, ta kowane fanni. 23 Don sa'ad da nake zagawa, na duba abubuwan da kuke yi wa ibada, har ma na tarar da wani bagadin hadaya da wannan rubutu a sama da shi cewa, ‘Saboda Allahn da ba a sani ba.’ To, shi wanda kuke yi wa sujada ba a tare da kun san shi ba, shi ina sanar muku. 24 Allahn da ya halicci duniya da dukkan abin da yake cikinta, shi da yake Ubangijin sama da ƙasa, ba ya zama a haikalin ginin mutum. 25 Haka kuma ba ya neman wani taimako daga gun mutum, sai ka ce wani abu yake bukata, tun da yake shi da kansa ne yake ba dukkan mutane rai, da numfashi, da dukkan abubuwa. 26 Shi ne kuma ya halicci dukkan al'umma daga tsatso ɗaya, domin su zauna a dukan sararin duniya, ya kuma ƙayyade zamanansu da iyakokin ƙasashensu, 27 wato nufinsa shi ne su neme shi, ko watakila sā laluba su same shi, alhali kuwa ba ya nesa da kowane ɗayanmu. 28 Domin ‘Ta gare shi ne muke rayuwa, muke motsi, muka kuma kasance,’ kamar yadda waɗansu mawaƙanku ma suka ce, ‘Hakika, mu ma zuriyarsa ce.’ 29 To, da yake mu zuriyar Allah ne, ai, bai kamata mu tsammaci Allah yana kama da wata surar zinariya, ko ta azurfa, ko ta dutse ba, wadda mutum ya ƙago ta dabararsa. 30 A dā kam, Allah ya kawar da kai ga zamanin jahilci, amma a yanzu yana umartar dukkan mutane a ko'ina su tuba, 31 tun da yake ya tsai da ranar da zai yi wa duniya shari'a, shari'a adalci, ta wurin mutumin nan da ya sa, wannan kuwa ya tabbatar wa dukan mutane, da ya tashe shi daga matattu.” 32 Da dai suka ji maganar tashin matattu, sai waɗansu suka yi ba'a, amma waɗansu suka ce, “A game da wannan magana kam, mā sāke jin abin da za ka faɗa.” 33 Sai Bulus ya fita daga cikinsu. 34 Amma waɗansu mutane suka koma wajensa suka ba da gaskiya, a cikinsu har Diyonisiyas, ɗan majalisar Tudun Arasa, da wata mace mai suna Damarisa, da waɗansu dai haka.

Ayyukan Manzanni 18

Bulus a Koranti

1 Bayan haka Bulus ya tashi daga Atina ya tafi Koranti. 2 A can ya tarar da wani Bayahude mai suna Akila, asalinsa kuwa mutumin Fantas ne, bai daɗe da zuwa daga ƙasar Italiya ba, tare da matarsa Bilkisu, don Kalaudiyas ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya je wurinsu. 3 Da yake kuma sana'arsu ɗaya ce, maɗinkan tanti ne, ya sauka a wurinsu, suka yi ta aiki tare. 4 Ya kuma yi ta yin muhawwara a majami'a a kowace Asabar, yana ta rinjayar Yahudawa da al'ummai. 5 Sa'ad da Sila da Timoti suka zo daga Makidoniya, Bulus ya dukufa a kan yin wa'azi, yana tabbatar wa Yahudawa, cewa Almasihu dai Yesu ne. 6 Da suka m�sa masa, suna ta zaginsa, ya karkaɗe tufafinsa ya ce musu, “Alhakinku yana a wuyanku! Ni kam na fita. Daga yau wurin al'ummai zan je.” 7 Sai ya tashi daga nan ya je gidan wani mutum mai suna Titus Yustus mai ibada, gidansa kuwa gab da majami'a yake. 8 Sai Kirisbus, shugaban majami'ar ya ba da gaskiya ga Ubangiji, shi da jama'ar gidansa duka. Korantiyawa kuma da yawa da suka ji maganar Bulus suka ba da gaskiya, aka yi musu baftisma. 9 Wata rana da daddare, Ubangiji ya yi wa Bulus wahayi, ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, sai dai ka yi ta wa'azi, kada ka yi shiru, 10 domin ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa ka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.” 11 Sai Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da wata shida, yana ta koyar da Maganar Allah a cikinsu. 12 Amma sa'ad da Galiyo yake muƙaddashin ƙasar Akaya, Yahudawa suka tasar wa Bulus da nufi ɗaya suka kawo shi a gaban shari'a, 13 suka ce, “Mutumin nan yana rarrashin mutane, don su bauta wa Allah ta hanyar da Shari'ar ta hana.” 14 Bulus yana shirin yin magana ke nen sai Galiyo ya ce wa Yahudawan, “Ku Yahudawa! Da ma wani laifi ya yi, ko munafunci, da sai in iya sauraronku. 15 Amma tun da yake gardama ce kawai a kan kalmomi, da sunaye, da kuma shari'arku, ai, sai ku ji da ita, ku da kanku. Ni kam, ba ni da niyyar yin shari'a irin waɗannan abubuwa.” 16 Sai ya kore su daga ɗakin shari'a. 17 Sai duk suka kama Sastanisu, shugaban majami'a, suka yi masa d�ka a gaban gadon shari'a. Amma Galiyo ko yă kula.

Bulus ya Koma Antakiya ta Suriya

18 Bulus kuwa da ya ƙara kwanaki da yawa, bayan da ya sausaye kansa a Kankiriya don ya cika wa'adin da ya ɗauka, ya yi bankwana da 'yan'uwa, ya shiga jirgin ruwa zuwa ƙasar Suriya, tare da Bilikisu da Akila. 19 Sai suka isa Afisa, a can ne kuma ya bar su, shi kuwa ya shiga majami'a ya yi muhawwara da Yahudawa. 20 Sai suka roƙe shi ya ƙara jimawa a wurinsu, amma bai yarda ba. 21 Sai dai ya yi bankwana da su, ya ce, “Zan dawo wurinku in Allah ya so.” Sa'an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa. 22 Da ya sauka a Kaisariya, sai ya je Urushalima, don ya gaisa da ikilisiya, sa'an nan ya tafi Antakiya. 23 Bayan da ya ɗan jima a nan, ya tashi ya zazzaga ƙasar Galatiya da ta Firijiya, yana bin gari gari, yana ƙarfafa dukan masu bi.

Afolos ya Yi Wa'azi a Afisa

24 To, wani Bayahude mai suna Afolos ya zo Afisa. Shi kuwa asalinsa mutumin Iskandariya ne, masani ne kuwa, ya san Littattafai ƙwarai da gaske. 25 An karantar da shi a tafarkin Ubangiji, da yake kuma muhimmanci ne ƙwarai, yakan yi ta magana a kan al'amuran Yesu, yana kuma koyar da su sosai, amma fa baftismar Yahaya kaɗai ya sani. 26 Sai ya fara wa'azi gabagaɗi a majami'a, amma da Bilkisu da Akila suka ji maganarsa, suka ja shi a jika, suka ƙara bayyana masa tafarkin Allah sosai da sosai. 27 Da ya so hayewa zuwa ƙasar Akaya, 'yan'uwa suka taimake shi, suka rubuta wa masu bi wasiƙa su karɓe shi hannu biyu biyu. Da kuwa ya isa, ya yi matuƙar taimako ga waɗanda suka ba da gaskiya ta wurin alherin Ubangiji, 28 don yā kayar da Yahudawa ƙwarai a gaban jama'a, yana tabbatar musu ta wurin Littattafai cewa Almasihu dai Yesu ne.

Ayyukan Manzanni 19

Bulus a Afisa

1 To, a lokacin da Afolos yake a Koranti, Bulus ya zazzaga ƙasar ta kan tudu, ya gangara zuwa Afisa. A can ya tarar da waɗansu masu bi, 2 sai ya ce musu, “Kun sami Ruhu Mai Tsarki sa'ad da kuka ba da gaskiya?” Suka ce masa, “Ba mu ma ji zuwan Ruhu Mai Tsarki ba.” 3 Sai ya ce, “To, wace baftisma ke nan aka yi muku?” Suka ce, “Irin ta Yahaya ce.” 4 Bulus ya ce, “Ai, Yahaya baftisma ya yi a tuba, yana faɗa wa mutane su gaskata da mai zuwa bayansa, wato Yesu.” 5 Da suka ji haka, aka yi musu baftisma da sunan Ubangiji Yesu. 6 Da Bulus ya ɗora musu hannu, Ruhu Mai Tsarki ya sauko musu, suka kuwa yi magana da waɗansu harsuna, suna annabci. 7 Su wajen goma sha biyu ne duka duka. 8 Sai ya shiga majami'a yana wa'azi gabagaɗi, ya kuma yi wata uku yana muhawwara da su, yana kuma rinjayarsu a kan al'amarin Mulkin Allah. 9 Amma da waɗansu suka taurare, suka ƙi ba da gaskiya, suna kushen wannan hanya a gaban jama'a, sai ya rabu da su, ya keɓe masu bi, yana ta muhawwara da su a kowace rana a makarantar Tiranas. 10 Shekara biyu ana wannan, har dukan mazaunan ƙasar Asiya suka ji Maganar Ubangiji, Yahudawa da al'ummai duka.

'Ya'yan Siba

11 Ta hannun Bulus kuma Allah ya yi waɗansu mu'ujizai da ba a saba gani ba, 12 har akan wa marasa lafiya adikansa, ko tufafinsa da yake sawa yana aiki, sun kuwa warke daga cuce-cucensu, baƙaƙen aljannu kuma sun rabu da su. 13 Sai waɗansu Yahudawa masu yawo gari gari, matsubbata, suka yi ƙoƙarin kama sunan Ubangiji Yesu ga masu baƙaƙen aljannu, suna cewa, “Mun umarce ku da sunan Yesun nan da Bulus yake wa'azi.” 14 To, akwai 'ya'ya bakwai maza, na wani babban firist na Yahudawa, mai suna Siba, duk suna yin wannan abu. 15 Amma aljanin ya amsa musu ya ce, “Yesu dai na san shi, na kuma san Bulus, to, ku kuma su wane ne?” 16 Mutumin nan mai aljanin sai ya daka tsalle, ya fāɗa musu, ya fi ƙarfinsu dukkansu, ya ci ɗunguminsu, har suka fita daga gidan a guje, a tuɓe, suna masu rauni. 17 Wannan abu fa ya sanu ga dukan mazaunan Afisa, Yahudawa da al'ummai duka, duka kuma tsoro ya kama su, aka kuwa ɗaukaka sunan Ubangiji Yesu. 18 Da yawa kuma daga cikin waɗanda suka ba da gaskiya suka zo, suna bayyana ayyukansu a fili. 19 Mutane da yawa kuwa masu yin sihiri, suka tattaro littattafansu suka ƙone a gaban jama'a duka. Da suka yi wa littattafan nan kima, sai suka ga sun kai kuɗi azurfa dubu hamsin. 20 Sai kuma Maganar Ubangiji ta ƙara haɓaka, ta kuma fifita ƙwarai.

Hargitsi a Afisa

21 Bayan waɗannan al'amura Bulus ya ƙudura a ransa, cewa in ya zazzaga ƙasar Makidoniya da ta Akaya, za shi Urushalima, ya kuma ce, “Bayan da na je can, lalle ne kuma in je in ga birnin Roma.” 22 Da ya aiki mataimakansa biyu Makidoniya, wato Timoti da Arastas, shi kuwa ya ɗan dakata a ƙasar Asiya. 23 A lokacin nan kuwa ba ƙaramin hargitsi aka yi a game da wannan hanya ba. 24 Domin akwai wani maƙerin farfaru, mai suna Dimitiriyas, mai ƙera surorin haikalin Artimas da azurfa, ba kuwa ƙaramar riba yake jawo wa masu yin wannan sana'a ba. 25 Sai ya tara su da duk ma'aikatan irin wannan sana'a, ya ce, “Ya ku jama'a, kun sani fa da sana'ar nan muke arziki. 26 Kuna kuwa ji, kuna gani, ba a nan Afisa kawai ba, kusan ma a duk ƙasar Asiya, Bulus ɗin nan ya rinjayi mutane masu yawan gaske, ya juyar da su, yana cewa, allolin da mutum ya ƙera ba alloli ba ne. 27 Ga shi kuma, akwai hatsari, ba cewa cinikinmu kawai ne zai zama wulakantacce ba, har ma haikalin nan na uwargijiya Artimas mai girma zai zama ba a bakin kome ba, har kuma a raba ta da darajarta, ita da duk ƙasar Asiya, kai, har duniya ma duka suke bauta wa.” 28 Da suka ji haka suka hasala ƙwarai, suka kuma ɗaga murya gaba ɗaya suna cewa, “Girma yā tabbata ga Artimas ta Afisawa!” 29 Sai garin duk ya ruɗe, jama'a suka ruga zuwa dandali da nufi ɗaya, suna Gayus da Aristarkus, mutanen Makidoniya, abokan tafiyar Bulus. 30 Bulus ya so shiga taron nan, amma masu bi suka hana shi. 31 Waɗansu zaɓaɓɓun mutanen ƙasar Asiya, waɗanda suke abokansa, su ma suka aika masa, suka roƙe shi kada ya kuskura ya shiga dandalin nan. 32 Taron kuwa, waɗansu suka ta da murya suka ce kaza, waɗansu suka ce kaza, don duk taron a ruɗe yake, yawancinsu ma ba su san dalilin da ya sa suka taru ba. 33 Da Yahudawa suka gabatar da Iskandari, waɗansu suka ɗauka a kan shi ne sanadin abin. Iskandari kuwa ya ɗaga hannu a yi shiru, don ya kawo musu hanzari, 34 amma da suka fahimci, cewa shi Bayahude ne, suka ɗaga murya gaba ɗaya har wajen sa'a biyu, suna ta cewa, “Girma yā tabbata ga Artimas ta Afisawa!” 35 To, da marubucin garin ya kwantar da hankalin jama'a, ya ce, “Ku mutanen Afisa! Wane mutum ne bai san cewa musamman birnin Afisawa ne yake kula da haikalin mai girma Artimas ba, da kuma dutsen nan da ya faɗo daga sama? 36 To, da yake ba dama a yi musun waɗannan abubuwa, ai, ya kamata ku natsu, kada ku yi kome da garaje. 37 Ga shi, kun kawo mutanen nan, su kuwa ba su yi sata a ɗakin uwargijiya ba, ba su kuma saɓi uwargijiyarmu ba. 38 To, in Dimitiriyas da abokan sana'arsa suna da wata magana a game da wani, ai, ga ɗakin shari'a a buɗe, ga kuma mahukunta, sai su kai ƙara. 39 Amma in wani abu kuke nema dabam, to, ai, sai a daidaita a majalisa ke ke nan. 40 Hakika muna a cikin hatsarin amsa ƙara a kan tawaye saboda al'amarin nan na yau, tun da yake ba za mu iya ba da wani hanzari a game da taron hargitsin nan ba.” 41 Da ya faɗi haka ya sallami taron.

Ayyukan Manzanni 20

Bulus ya Koma Makidoniya da Hellas

1 Bayan hargowar nan ta kwanta, Bulus ya kira masu bi, bayar da ya ƙarfafa musu zuciya, ya yi bankwana da su, ya tafi ƙasar Makidoniya. 2 Da ya zazzaga lardin nan, ya kuma ƙarfafa masu zuciya ƙwarai, ya zo ƙasar Hellas, 3 ya yi wata uku a nan. Da Yahudawa suka ƙulla masa makirci, a sa'ad da zai tashi a jirgin ruwa zuwa ƙasar Suriya, ya yi niyyar komawa ta ƙasar Makidoniya. 4 Subataras Babiriye, ɗan Burus, shi ya raka shi, tare da Aristarkus da Sakundas, mutanen Tasalonika, da Gayus Badarbe, da Timoti, har ma da Tikikus da Tarofimas, mutanen Asiya, 5 waɗanda suka riga tafiya suka jira mu a Taruwasa. 6 Mu kuwa muka tashi daga Filibi a jirgin ruwa, bayan idin abinci marar yisti, muka iske su a Taruwasa bayan kwana biyar. A nan muka zauna har kwana bakwai.

Taruwar Bankwana a Taruwasa

7 A ranar farko ta mako kuma, da muka taru don gutsuttsura gurasa, Bulus ya yi masu jawabi, don ya yi niyyar rashi kashegari, sai ya yi ta jan jawabin nasa har tsakar dare. 8 Akwai kuwa fitilu da yawa a benen da muka taru. 9 Da wani saurayi a zaune a kan taga, mai suna Aftikos, sai barci ya ci ƙarfinsa sa'ad da Bulus yake ta tsawaita jawabi, da barci mai nauyi ya kwashe shi, sai ya faɗo daga can hawa na uku, aka ɗauke shi matacce. 10 Amma Bulus ya sauka ƙasa, ya miƙe a kansa, ya rungume shi, ya ce, “Kada ku damu, ai, yana da rai.” 11 Da Bulus ya koma sama, ya gutsuttsura gurasa ya ci, ya daɗe yana magana da su, har gari ya waye, sa'an nan ya tashi. 12 Sai suka tafi da saurayin nan a raye, daɗin da suka ji kuwa ba kaɗan ba ne.

Tafiya a Teku daga Taruwasa zuwa Militas

13 Mu kuwa muka yi gaba zuwa jirgin, muka miƙa sai Asus da nufin ɗaukar Bulus daga can, don dā ma haka ya shirya, shi kuwa ya yi niyyar bi ta ƙasa. 14 Da ya same mu a Asus, muka ɗauke shi a jirgin, muka zo Mitilini. 15 Daga nan kuma muna tafe a jirgin ruwan dai, kashegari kuma sai ga mu daura da tsibirin Kiyos. Kashegari kuma, ga mu a tsibirin Samas, wani kashegari kuma sai Militas. 16 Dā ma kuwa Bulus ya ƙudura zai wuce Afisa a cikin jirgin, don kada ya yi jinkiri a Asiya, domin yana sauri, ni mai yiwuwa ne ma, ya kai Urushalima a ranar Fentikos.

Bulus ya Yi wa Dattawan Ikilisiyar Afisa Jawabi

17 Daga Militas ne ya aika Afisa a kira masa dattawan ikilisiya. 18 Da suka zo wurinsa sai ya ce musu, “Ku da kanku kun san irin zaman da na yi a cikinku, tun ran da na sa ƙafata a ƙasar Asiya, 19 ina bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali'u, har da hawaye, da gwaggwarmaya iri iri da na sha a game da makircin Yahudawa. 20 Kun kuma san yadda ban ji nauyin sanar da ku kowane abu mai amfani ba, ina koya muku a sarari, da kuma gida gida, 21 ina tabbatar wa Yahudawa da al'ummai duka sosai wajibcin tuba ga Allah, da kuma gaskatawa da Ubangijinmu Yesu. 22 To, ga shi kuma, a yanzu zan tafi Urushalima, Ruhu yana iza ni, ban kuwa san abin da zai same ni a can ba, 23 sai dai Ruhu Mai Tsarki yakan riƙa tabbatar mini a kowane gari, cewa ɗauri da shan wuya na dākona. 24 Amma ni ban mai da raina a bakin kome ba, bai kuma dame ni ba, muddin zan iya cikasa tserena da kuma hidimar da na karɓa daga gun Ubangiji Yesu, in shaidar da bisharar alherin Allah. 25 To, ga shi, a yanzu na san dukanku ba za ku ƙara ganina ba, ku da na zazzaga a cikinku ina yi muku bisharar Mulkin Allah. 26 Saboda haka ina dai tabbatar muku a yau, cewa na kuɓuta daga hakkin kowa, 27 domin kuwa ban ji nauyin sanar da ku dukan nufin Allah ba. 28 Ku kula da kanku, da kuma duk garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi, kuna kiwon Ikilisiyar Allah wadda ya sama wa kansa da jininsa. 29 Na sani bayan tashina waɗansu mugayen kyarketai za su shigo a cikinku, ba kuwa za su ji tausayin garken ba. 30 Har ma a cikinku waɗansu mutane za su taso, suna maganganun da ba sa kan hanya, don su jawo masu bi a gare su. 31 Saboda haka sai ku zauna a faɗake, ku tuna, shekara uku ke nan ba dare ba rana, ban fasa yi wa kowa gargaɗi ba, har da hawaye. 32 To, a yanzu na danƙa ku ga Ubangiji, maganar alherinsa kuma tă kiyaye ku, wadda ita take da ikon inganta ku, ta kuma ba ku gādo tare da dukan tsarkaka. 33 Ban yi ƙyashin kuɗin kowa ba, ko kuwa tufafin wani. 34 Ku da kanku kun sani hannuwan nan nawa su suka biya mini bukace-bukacena, da na waɗanda suke tare da ni. 35 Na zamar muku abin misali ta kowace hanya, cewa ta wahalar aiki haka lalle ne a taimaki masu ƙaramin ƙarfi, kuna kuma tunawa da Maganar Ubangiji Yesu da ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’ ” 36 Da Bulus ya faɗi haka, ya durƙusa, duka suka yi addu'a tare. 37 Sai duk suka fashe da kuka, suka rungume Bulus, suna ta sumbantarsa, 38 suna baƙin ciki tun ba ma saboda maganar da ya faɗa ba, cewa ba za su ƙara ganinsa ba. Daga nan suka rako shi har bakin jirgi.

Ayyukan Manzanni 21

Tafiyar Bulus zuwa Urushalima

1 Sa'ad da muka rabu da su da ƙyar, muka shiga jirgi muka miƙa sosai zuwa tsibirin Kos, kashegari kuma sai Rodusa, daga nan kuma sai Batara. 2 Da muka sami jirgi mai hayewa zuwa ƙasar Finikiya, muka shiga muka tafi. 3 Da muka tsinkayo tsibirin Kubrus, muka mai da shi hagun, muka ci gaba zuwa ƙasar Suriya, muka sauka a Taya, don a nan ne jirgin zai sauke kayansa. 4 Da muka sami inda masu bi suke, muka zauna a nan kwana bakwai. Sai Ruhu ya iza su suka gaya wa Bulus kada ya je Urushalima. 5 Amma da lokacin tashinmu ya yi, muka tashi muka ci gaba da tafiyarmu, dukansu kuma har da matansu da 'ya'yansu, suka raka mu har bayan gari, sa'an nan muka durƙusa a kan gaci, muka yi addu'a, muka yi bankwana da juna. 6 Sai muka shiga jirgi, su kuma suka koma gida. 7 Da muka gama tafiyarmu daga Taya, muka isa Talamayas, sai muka gaisa da 'yan'uwa, muka kuma kwana ɗaya a wurinsu. 8 Kashegari muka tashi muka zo Kaisariya, muka shiga gidan Filibus mai yin bishara, wanda yake ɗaya daga cikin bakwai ɗin nan, muka sauka a wurinsa. 9 Shi kuwa yana da 'ya'ya huɗu 'yan mata, masu yin annabci. 10 To, muna nan a zaune 'yan kwanaki, sai wani annabi, mai suna Agabas, ya zo daga Yahudiya. 11 Da ya zo gare mu, ya ɗauki ɗamarar Bulus ya ɗaure kansa sawu da hannu, ya ce, “Ga abin da Ruhu Mai Tsarki ya ce, ‘Haka Yahudawan Urushalima za su ɗaure mai wannan ɗamara, su kuma bashe shi ga al'ummai.’ ” 12 Da muka ji haka, mu da waɗanda suke a wurin muka roƙi Bulus kada ya je Urushalima. 13 Sai Bulus ya amsa ya ce, “Me ke nan kuke yi, kuna kuka kuna baƙanta mini rai? Ai, ni a shirye nake, ba ma a ɗaure ni kawai ba, har ma a kashe ni a Urushalima saboda sunan Ubangiji Yesu.” 14 Da dai ya ƙi rarrasuwa, muka yi shiru, muka ce, “Ubangiji ya yi yadda ya so.” 15 Bayan 'yan kwanakin nan muka shirya muka tafi Urushalima. 16 Waɗansu masu bi daga Kaisariya suka rako mu, suka kawo mu wurin Manason, mutumin Kubrus, wani daɗaɗɗen mai bi, wanda za mu sauka a gunsa.

Bulus ya Ziyarci Yakubu

17 Da muka zo Urushalima, 'yan'uwa suka karɓe mu da murna. 18 Kashegari Bulus ya tafi tare da mu a wurin Yakubu, dattawan ikilisiya kuwa duk suna nan. 19 Bayan da ya gaisa da su, sai ya shiga bayyana musu filla abubuwan da Allah ya yi a cikin al'ummai ta wurin hidimarsa. 20 Su kuwa da suka ji haka, suka ɗaukaka Allah. Suka ce wa Bulus, “To, kā gani ɗan'uwa, dubban mutane sun ba da gaskiya a cikin Yahudawa, dukansu kuwa masu himma ne a wajen bin Shari'a. 21 An kuwa sha gaya musu labarinka, cewa kai ne kake koya wa dukan Yahudawan da suke a cikin al'ummai su yar da Shari'ar Musa. Kuma kana ce musu kada su yi wa 'ya'yansu kaciya, ko kuwa su bi al'adu. 22 To, ƙaƙa ke nan? Lalle za su ji labarin zuwanka. 23 Saboda haka sai ka yi abin da za mu faɗa maka. Muna da mutum huɗu da suka ɗauki wa'adi. 24 Sai ka tafi da su ku tsarkaka gaba ɗaya, ka kuma biya musu kome don su samu su yi aski. Ta haka, kowa zai sani duk abin da aka gaya musu a game da kai, ba wata gaskiya a ciki, kai kuma kana kiyaye Shari'a. 25 Amma a game da al'ummai da suka ba da gaskiya, mun aika da wasiƙa a kan mun hukunta, cewa su guji cin abin da aka yanka wa gunki, da fasikanci, da cin abin da aka maƙure, da kuma cin nama tare da jini.” 26 Sa'an nan Bulus ya ɗibi mutanen nan, kashegari kuma da suka tsarkaka tare, sai ya shiga Haikali domin ya sanar da ranar cikar tsarkakewar tasu, wato ranar da za a ba da sadaka saboda kowannensu.

An Kama Bulus a cikin Haikali

27 Da kwana bakwai ɗin suka yi kusan cika, Yahudawan ƙasar Asiya suka gan shi a Haikalin, sai suka zuga taron duka, suka danƙe shi, 28 suna ta ihu suna cewa, “Ya ku 'yan'uwa Isra'ilawa, ku taimaka! Ga mutumin da yake bi ko'ina yana koya wa mutane su raina jama'armu da Shari'a, da kuma wannan wuri. Banda haka kuma har ma ya kawo al'ummai a cikin Haikalin, ya ƙazantar da wurin nan tsattsarka.” 29 Don dā ma can sun ga Tarofimas Ba'afise tare da shi a cikin gari, sun kuma zaci Bulus ya kawo shi a cikin Haikalin. 30 Sai duk garin ya ruɗe, jama'a suka ɗungumo a guje suka danƙe Bulus, suka ja shi a waje daga Haikalin, nan da nan kuma aka rufe ƙofofi. 31 Suna neman kashe shi ke nan, sai labari ya kai ga shugaban ƙungiyar yaƙi, Urushalima duk ta hargitse. 32 A nan tāke ya ɗibi soja da jarumawa, suka ruga zuwa wajensu. Su kuwa da ganin shugaban da soja suka daina d�kan Bulus. 33 Sai shugaban ya matsa kusa ya kama Bulus, ya yi umarni a ɗaure shi da sarƙa biyu, sa'an nan ya tambaya ko shi wane ne, da abin da kuma ya yi. 34 Taron kuwa suka ɗau kururuwa, waɗansu suka ce kaza, waɗansu suka ce kaza. Don tsananin hargowa ma har ya kasa samun ainihin tushen maganar, ya yi umarni a kai shi kagarar sojoji. 35 Da Bulus ya zo ga bakin matakala, sai da soja suka kinkime shi saboda haukan taron, 36 don taron jama'a suna dannowa a bayansu, suna ihu suna cewa, “A yi da shi!”

Hanzarin Bulus

37 An yi kusan shigar da Bulus a kagarar sojoji ke nan, sai ya ce wa shugaban, “Ko ka yarda in yi magana da kai?” Sai shugaban ya ce, “Ashe, ka iya Helenanci? 38 Shin, ba kai ne Bamasaren nan da shekarun baya ya haddasa tawaye ba, har ya ja mutanen nan dubu huɗu masu kisankai zuwa jeji?” 39 Sai Bulus ya amsa ya ce, “Ai, ni Bayahude ne na Tarsus ta ƙasar Kilikiya, ɗan shahararren birni, ina roƙonka ka bar ni in yi wa mutane jawabi.” 40 Da ya ba shi izini, sai Bulus ya tsaya a kan matakala, ya ɗaga wa jama'a hannu su yi shiru. Da suka yi tsit, sai ya yi musu magana da Yahudanci.

Ayyukan Manzanni 22

1 “Ya ku 'yan'uwa da shugabanni, ku ji hanzarin da zan kawo muku a yanzu.” 2 Da suka ji ya yi musu magana da Yahudanci, sai suka ƙara natsuwa. Sa'an nan ya ce, 3 “Ni bayahude ne, haifaffen Tarsus, ta ƙasar Kilikiya, amma a nan garin na yi girma, aka kuma karantar da ni a wurin Gamaliyal, bisa ga tsarin tsanantacciyar hanyar nan ta Shari'ar kakanninmu. Ina mai himmar bauta wa Allah, kamar yadda kuke a yau, 4 har na tsananta wa masu bin wannan hanya, ina karkashe su, ina ɗaure mutane maza da mata, ina jefa su a kurkuku. 5 Babban firist ma da dukan majalisar shugabannin jama'a za su iya shaidata, daga gunsu ne kuma na karɓi wasiƙu zuwa ga 'yan'uwanmu Yahudawa, na tafi Dimashƙu, don in ɗebo waɗanda suke can ma, in zo da su Urushalima a ɗaure, a azabta su.”

Bulus ya Ba da Labarin Juyowarsa

6 “Ina a cikin tafiya, da na yi kusa da Dimashƙu, a wajen rana tsaka, kwamfa sai wani matsanancin haske ya bayyano daga sama, ya haskaka kewaye da ni. 7 Sai na fāɗi, na kuma ji wata murya tana ce mini, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini?’ 8 Ni kuma na amsa na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ Sai ya ce mini, ‘Ni ne Yesu Banazare wanda kake tsananta wa.’ 9 To, waɗanda suke tare da ni suka ga hasken, amma ba su ji kalmomin mai yi mini maganar nan ba. 10 Sai na ce, ‘To, me zan yi, ya Ubangiji?’ Sai ubangiji ya ce mini, ‘Tashi, ka shiga Dimashƙu, a can ne za a faɗa maka duk abin da aka ɗora maka ka yi.’ 11 Da na kāsa gani saboda tsananin hasken nan, sai waɗanda suke tare da ni suka yi mini jagora, har na isa Dimashƙu. 12 “Sai kuma wani mai suna Hananiya, mai bautar Allah ne a wajen bin Shari'a, wanda duk Yahudawan da suke zaune a can suke yabo, 13 ya zo ya tsaya a kusa da ni, ya ce mini, ‘Ya ɗan'uwana Shawulu, ganinka yă komo maka.’ A nan tāke, sai ganina ya komo, na kuwa gan shi. 14 Sai ya ce, ‘Allahn kakanninmu ya zaɓe ka don kă san nufinsa, ka ga Mai Adalcin nan, ka kuma ji jawabi daga bakinsa. 15 Don za ka zama mashaidinsa ga dukan mutane a game da abin da ka gani, ka kuma ji. 16 To, a yanzu me kake jira? Tashi, a yi maka baftisma a wanke zunubanka ta wurin kira bisa sunansa.’ ”

Kiran Bulus zuwa ga Al'ummai

17 “Da na komo Urushalima, ina addu'a a Haikali, sai wahayi ya zo mini. 18 Na gan shi, yana ce mini, ‘Yi sauri maza ka fita daga Urushalima, don ba za su yarda da shaidarka a kaina ba.’ 19 Ni kuma na ce, ‘Ya Ubangiji, ai, su ma kansu sun sani a kowace majami'a nakan ɗaɗɗaure waɗanda suka gaskata da kai, nakan kuma daddoke su. 20 Sa'ad da kuma aka zub da jinin Istifanas, mashaidin nan naka, ni ma ina a tsaye a gun, ina goyon bayan abin da aka yi, har ma ina tsaron tufafin masu kisansa.’ 21 Sai ya ce mini, ‘Tashi ka tafi, zan aike ka can nesa a wurin al'ummai.’ ”

Shugaba ya Tsare Bulus

22 Suna ta sauraronsa har ya iso kalmar nan, sai suka ɗau ihu suka ce, “A kashe shi! A raba irin mutumin nan da duniya, bai kyautu ya rayu ba!” 23 Da suka dinga ihu suna kaɗa mayafansu suna ta ature da ƙura, 24 sai shugaba ya yi umarni a kai Bulus kagarar soja a tuhume shi da bulala, don yă san abin da ya sa suke masa ihu haka. 25 Bayan da suka ɗaɗɗaure shi da tsirkiya, Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye kusa, “Ashe, ya halatta a gare ka ka yi wa mutumin da yake da 'yancin Roma bulala, ba ko bin ba'asi?” 26 Da jarumin ya ji haka, sai ya je ya shaida wa shugaban, ya ce, “Me kake shirin yi ne? Mutumin nan fa Barome ne.” 27 Sai shugaban ya zo ya ce wa Bulus, “Faɗa mini gaskiya, kai kuwa Barome ne?” Sai ya ce, “I.” 28 Sai shugaban ya amsa ya ce, “Ni fa da kuɗi masu yawa na sami 'yancin nan.” Bulus ya ce, “Ka ga ni kuwa da shi aka haife ni.” 29 Saboda haka, waɗanda suke shirin tuhumarsa, suka rabu da shi nan da nan. Shi ma shugaban da ya fahimci cewa, Bulus Barome ne, sai ya tsorata, ga shi kuwa, ya ɗaure shi.

Bulus a gaban 'Yan Majalisa

30 Kashegari kuma da shugaban ya so sanin ainihin ƙarar da Yahudawa suke yi a kan Bulus, sai ya kwance shi, ya yi umarni domin manyan firistoci da dukan majalisa su taru, sa'an nan ya sauko da Bulus ya tsai da shi a gabansu.

Ayyukan Manzanni 23

1 Sai Bulus ya zuba wa majalisar ido ya ce, “Ya ku 'yan'uwa, ku sani, bautar Allah nake yi da lamiri mai kyau har ya zuwa yau.” 2 Sai Hananiya babban firist ya umarci waɗanda suke tsaye kusa da Bulus su buge bakinsa. 3 Sai Bulus ya ce masa, “Kai munafiƙi, kai ma Allah zai buge ka! Ashe, wato kana zaune kana hukunta ni bisa ga Shari'a ne, ga shi kuwa kana yin umarni a doke ni, a saɓanin Shari'a?” 4 Sai waɗanda ke tsaye a wurin suka ce masa, “Babban firist na Allah za ka zaga?” 5 Sai Bulus ya ce, “Ai, ban sani shi ne babban firist ba, 'yan'uwa, don a rubuce yake cewa, ‘Kada ka munana shugaban jama'a.’ ” 6 Amma da Bulus ya ga sashe ɗaya Sadukiyawa ne, ɗayan kuma Farisiyawa, ya ɗaga murya a majalisar ya ce, “Ya 'yan'uwa, ni ma Bafarisiye ne, ɗan Farisiyawa. Ga shi kuwa, saboda na sa zuciya ga tashin matattu ne ake yi mini shari'a.” 7 Da ya faɗi haka sai gardama ta tashi a tsakanin Farisiyawa da Sadukiyawa, har taron ya rabu biyu. 8 Sadukiyawa sun ce, suna cewa ba tashin matattu, ba kuma mala'iku, ko ruhu. Farisiyawa kuwa sun tsaya a kan cewa duk akwai. 9 Sai ƙasaitacciyar hargowa ta tashi, waɗansu malamai kuma na cikin ɗariƙar Farisiyawa suka miƙe a tsaye, suka yi ta yin matsananciyar jayayya, suna cewa, “Mu ba mu ga laifin mutumin nan ba. In wani ruhu ne ko mala'ika ya yi masa magana fa?” 10 Da gardamar ta yi tsanani, don gudun kada su yi kaca-kaca da Bulus, shugaban ya umarci sojan su sauka su ƙwato shi daga wurinsu ƙarfi da yaji, su kawo shi a kagarar soja. 11 Da daddare sai Ubangiji ya tsaya a kusa da Bulus, ya ce, “Ka yi ƙarfin hali, don kamar yadda ka shaide ni a Urushalima, haka kuma lalle ne ka shaide ni a Roma.”

Ƙulla Shawara a Kashe Bulus

12 Da gari ya waye, Yahudawa suka gama baki suka yi rantsuwa, cewa ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe Bulus. 13 Waɗanda suka ƙulla wannan makirci kuwa sun fi mutum arba'in. 14 Sai suka je wurin manyan firistoci da shugabanni, suka ce, “Mun yi wata babbar rantsuwa, cewa za mu zauna ba ci ba sha sai mun kashe Bulus. 15 Saboda haka, a yanzu ku da majalisa ku shaida wa shugaban soja ya kawo muku shi, kamar kuna so ne ku ƙara bincika maganarsa sosai, mu kuwa a shirye muke mu kashe shi kafin ya iso.” 16 To, ɗan 'yar'uwar Bulus ya ji labarin farkon da za su yi, ya kuma je ya shiga kagarar soja ya gaya wa Bulus. 17 Bulus kuwa ya kira wani jarumi ya ce, “Ka kai saurayin nan wurin shugaba, yana da wata magana da zai faɗa masa.” 18 Sai jarumin ya ɗauki saurayin ya kai shi gun shugaba, ya ce, “Ɗan sarƙan nan, Bulus, ya kira ni, ya roƙe ni in kawo saurayin nan a wurinka, don yana da wata maganar da zai gaya maka.” 19 Sai shugaban ya kama hannun saurayin, ya ja shi a waje ɗaya, ya tambaye shi a keɓance, “Wace magana za ka gaya mini?” 20 Yaron ya ce, “Yahudawa sun ƙulla za su roƙe ka ka kai musu Bulus majalisa gobe, kamar suna so su ƙara bincika maganarsa sosai. 21 Amma kada ka yardar musu, don fiye da mutum arba'in daga cikinsu suna fakonsa, sun kuma yi rantsuwa a kan ba za su ci ba, ba za su sha ba, sai sun kashe shi. A yanzu kuwa a shirye suke, yardarka kawai suka jira.” 22 Sai shugaban ya sallami saurayin ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa cewa ka sanar da ni maganar nan.”

An Aika da Bulus zuwa ga Mai Mulki Filikus

23 Sa'an nan ya kira jarumi biyu ya ce, “Ku shirya soja metan, da barade saba'in, da 'yan māsu metan, su tafi Kaisariya da ƙarfe tara na daren nan.” 24 Ya kuma yi umarni su shirya wa Bulus dabbobin da zai hau, don su kai shi wurin mai mulki Filikus lafiya. 25 Ya kuma rubuta wasiƙa kamar haka: 26 “Daga Kalaudiyas Lisiyas zuwa ga mafifici mai mulki Filikus. Gaisuwa mai yawa. 27 Bayan haka mutumin nan, Yahudawa sun kama shi, suna kuma gab da kashe shi, sai na yi farat na je da soja na ƙwato shi, saboda na ji cewa shi Barome ne. 28 Da nake so in jin laifin da suke zarginsa a kai, sai na kai shi majalisarsu. 29 Na kuwa tarar suna zarginsa a kan maganar Shari'arsu, amma laifin da suka ɗora masa bai kisa ko ɗauri ba. 30 Da aka buɗa mini cewa akwai wani makircin da aka ƙulla masa, nan da nan na aika da shi a gare ka, na kuma umarci masu ƙararsa su faɗi ƙararsu a gabanka. Wassalam.” 31 Saboda haka, sojan suka ɗauki Bulus, kamar yadda aka umarce su, suka kai shi Antibatiris da daddare. 32 Kashegari kuma suka bar barade su ci gaba da shi, su kuwa suka koma kagarar soja. 33 Da baraden suka isa Kaisariya, suka ba mai mulkin wasiƙar, suka kai Bulus a gabansa. 34 Da ya karanta wasiƙar, ya tambayi Bulus ko shi mutumin wane lardi ne? Da ya ji daga Kilikiya yake, 35 sai ya ce, “Zan saurari maganarka duka, in masu ƙararka sun zo.” Sai kuma ya yi umarni a tsare shi a fadar Hirudus.

Ayyukan Manzanni 24

An Kai Ƙarar Bulus

1 Bayan kwana biyar sai babban firist, Hananiya, ya zo tare da waɗansu shugabanni, da kuma wani lauya, mai suna Tartulus, suka yi ƙarar Bulus a gaban mai mulki. 2 Da aka kirawo Tartulus, ya shiga kai ƙarar Bulus, ya ce, “Ya mafifici Filikus, tun da yake ta gare ka ne muke zaman lafiya ƙwarai, ta tsinkayarka ne kuma ake kyautata zaman jama'armu, 3 kullum muna yarda da haka ƙwarai a ko'ina, tare da godiya ba iyaka. 4 Amma don kada in gajiyad da kai, ina roƙonka a cikin nasiharka, ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu. 5 Mun tarar da mutumin nan fitinanne ne, yana ta da hargitsi a tsakanin Yahudawa ko'ina a duniya, shi kuma ne turun ɗariƙar Nazarawa. 6 Har ma yana nema ya tozarta Haikali, amma muka kama shi.Niyyarmu ce mu hukunta shi bisa ga shari'armu. 7 Amma shugaba Lisiyas ya zo ya ƙwace shi daga hannunmu ƙarfi da yaji, 8 ya yi umarni masu ƙararsa su zo a gabanka. In kuwa ka tuhume shi da kanka, za ka iya tabbatarwa daga bakinsa duk ƙarar da muke tāsarwa.” 9 Yahudawa ma suka goyi bayan haka, suna tabbatarwa haka abin yake.

Hanzarin Bulus a gaban Filikus

10 Da mai mulki ya alamta wa Bulus ya yi magana, sai ya amsa ya ce, “Tun da na sani ka yi shekaru da yawa kana yi wa jama'ar nan shari'a, da farin ciki zan kawo hanzarina. 11 Ai, ka iya tabbatarwa, bai fi kwana goma sha biyu ba tun da na tafi Urushalima yin sujada. 12 Ba su kuwa taɓa samuna ina muhawwara da kowa ba, ko kuwa ta da husuma har mutane su taru a Haikali, ko a majami'u, ko kuwa a cikin birni ba. 13 Ba kuma za su iya tabbatar maka abin da yanzu suke ƙarata a kai ba. 14 Amma na yarda da cewa, bisa ga hanyar nan da suke kira ‘Ɗariƙa’ nake bauta wa Allahn kakanninmu, nake kuma gaskata duk abin da yake a rubuce a cikin Attaura da kuma littattafan annabawa. 15 Ina sa zuciya ga Allah, yadda su waɗannan ma suke sawa, wato za a ta da matattu, masu adalci da marasa adalci duka. 16 Saboda haka, a kullum nake himma in kasance da lamiri marar abin zargi a wurin Allah da wurin mutane. 17 To, bayan 'yan shekaru sai na je domin in kai gudunmawa ga jama'armu, in kuma yi sadaka. 18 Ina cikin yin haka sai suka same ni a tsarkake a Haikali, ba kuwa da wani taro ba, balle hargowa. Amma akwai waɗansu Yahudawa daga ƙasar Asiya� 19 su ne kuwa ya kamata su zo nan a gabanka su yi ƙarata, in suna da wata magana a game da ni. 20 Ko kuwa waɗannan mutane da kansu su faɗi laifina da suka samu, sa'ad da na tsaya a gaban majalisa, 21 sai ko maganar nan ɗaya tak, da na ɗaga murya na faɗa, sa'ad da nake a tsaye a cikinsu, cewa, ‘A game da maganar tashin matattu ake yi mini shari'a a gabanku yau.’ ”

An Tsare Bulus

22 Filikus kuwa da yake yana da sahihin ilimi a game da wannan hanya ya dakatar da su, ya ce, “In shugaba Lisiyas ya iso, zan yanke muku shari'a.” 23 Ya kuma ba jarumi umarni ya tsare Bulus, amma ya sassauta masa, kada kuwa ya hana mutanensa zuwa wurinsa su kula da shi. 24 Bayan 'yan kwanaki Filikus ya zo tare da matarsa, Durusila, wata Bayahudiya. Sai ya aika a zo da Bulus, ya kuwa saurare shi a kan maganar gaskatawa da Almasihu Yesu. 25 Bulus yana ba da bayani a kan adalci, da kamunkai, da kuma hukuncin nan mai zuwa, Filikus ya kaɗu, ya kāda baki ya ce, “Yanzu kam, sai ka koma. In na sami zarafi nā kira ka.” 26 Don yana sa rai Bulus zai ba shi kuɗi, shi ya sa ya yi ta kiransa a kai a kai, yana zance da shi. 27 Amma bayan shekara biyu sai Borkiyas Festas ya gāji Filikus. Filikus kuwa don neman farin jini a wurin Yahudawa, ya bar Bulus a ɗaure.

Ayyukan Manzanni 25

Bulus ya Ɗaukaka Ƙara zuwa ga Kaisar

1 To, da Festas ya iso lardinsa, bayan kwana uku sai ya tashi daga Kaisariya ya tafi Urushalima. 2 Sai manyan firistoci da manyan Yahudawa suka kai ƙarar Bulus a gunsa, suka roƙe shi 3 ya kyauta musu, ya aika a zo da shi Urushalima, alhali kuwa sun shirya 'yan kwanto su kashe shi a hanya. 4 Amma Festas ya amsa ya ce, “Bulus yana a tsare a Kaisariya, ni ma kuwa da kaina ina niyyar zuwa a can a kwanan nan.” 5 Ya kuma ce, “Saboda haka, sai waɗansu manya a cikinku su taho tare da ni, in kuwa mutumin nan yana da wani laifi, su yi ƙararsa.” 6 Bai fi kwana takwas ko gama a wurinsu ba, sai ya tafi Kaisariya. Kashegari kuma ya zauna a kan gadon shari'a, ya yi umarni a zo da Bulus. 7 Da ya zo, Yahudawan da suka zo daga Urushalima suka kewaye shi a tsaitsaye, suna ta kawo ƙararraki masu yawa masu tsanani a game da shi, waɗanda ma suka kasa tabbatarwa. 8 Amma Bulus ya kawo hanzarinsa ya ce, “Ni ban yi wani laifi a game da shari'ar Yahudawa, ko Haikali, ko a game da Kaisar ba, ko kaɗan.” 9 Festas kuwa don neman farin jini a wurin Yahudawa, ya amsa ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari'a a can a kan waɗannan abubuwa a gabana?” 10 Amma Bulus ya ce, “Ai, a tsaye nake a majalisar Kaisar, a inda ya kamata a yi mini shari'a. Ban yi wa Yahudawa wani laifi ba, kai kanka kuwa ka san da haka sarai. 11 To, in ni mai laifi ne, har na aikata abin da ya isa kisa, ai, ba zan guji a kashe ni ba, amma in ba wata gaskiya a cikin ƙarata da suke yi, to, ba mai iya bashe ni a gare su don a faranta musu rai. Na nema a ɗaukaka ƙarata a gaban Kaisar.” 12 Bayan da Festas ya yi shawara da majalisa, sai ya amsa ya ce, “To, ka nema a ɗaukaka ƙararka a gaban Kaisar! A gun Kaisar kuwa za ka tafi.”

Bulus a gaban Agaribas da Barniki

13 Bayan 'yan kwanaki sai sarki Agaribas da Barniki, suka zo Kaisariya don su yi wa Festas maraba. 14 Da yake kuma sun yi kwanaki da dama a can, sai Festas ya rattaba wa sarki labarin Bulus, ya ce, “Akwai wani mutumin da Filikus ya bari a ɗaure, 15 wanda sa'ad da nake Urushalima manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka kawo mini ƙararsa, suka roƙe ni in yi masa hukunci. 16 Ni kuwa na amsa musu na ce, ba al'adar Romawa a yi wa wani hukunci, don a faranta wa wani rai, ba tare da masu ƙarar, da wanda aka kai ƙara, sun gurfana a gaban shari'a ba, ya kuma sami damar kawo hanzarinsa game da ƙarar da aka tāsar. 17 Saboda haka, da suka zo nan tare, ban yi wani jinkiri ba, sai kawai na hau akan gadon shari'a kashegari, na kuma yi umarni a kawo mutumin. 18 Da masu ƙarar suka tashi a tsaye, ba su kawo wata mummunar ƙara yadda na zata a game da shi ba, 19 sai dai waɗansu maganganu da suka ɗora masa a game da addininsu, da kuma wani, shi Yesu, wanda ya mutu, amma Bulus ya tsaya a kan, cewa lallai yana da rai. 20 Ni kuwa da na rasa yadda zan bincika waɗannan abubuwa, sai na tambayi Bulus ko ya yarda ya je Urushalima a yi masa shari'a a can a kan waɗannan abubuwa. 21 Amma da Bulus ya nema a dakatar da maganarsa sai Augustas ya duba ta, sai na yi umarni a tsare shi har kafin in aika da shi zuwa a gun Kaisar.” 22 Sai Agaribas ya ce wa Festas, “Ni ma dai na so in saurari mutumin nan da kaina.” Festas ya ce, “Kā kuwa ji shi gobe.” 23 To kashegari sai Agaribas da Barniki suka zo a cikin alfarma, suka shiga ɗakin majalisa tare da shugabannin yaƙi da kuma jigajigan garin. Sai aka shigo da Bulus sai da umarnin Festas. 24 Sai Festas ya ce, “Ya sarki Agaribas, da dukan mutanen da suke a tare da mu, kun ga mutumin nan da duk jama'ar Yahudawa suka kawo mini ƙararsa a Urushalima, da kuma nan, suna ihu, cewa bai kamata a bar shi da rai ba. 25 Amma ni ban ga abin da ya yi wanda ya isa kisa ba. Tun da kuma shi kansa ya nema a mai da shari'arsa a gaban Augustas, na ƙudura in aika da shi zuwa wurinsa. 26 Amma ba ni da wata tabbatacciyar magana da zan rubuta wa ubangidana a game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku, musamman kuwa a gabanka, ya sarki Agaribas, don bayan an yi bincike, ko na abin da zan rubuta. 27 Don ni, a ganina, wauta ce a aika da ɗan sarƙa, ba tare da an nuna laifofin da ya yi ba.”

Ayyukan Manzanni 26

Hanzarin Bulus a gaban Agaribas

1 Daga nan, sai Agaribas ya ce wa Bulus, “An ba ka izinin yin magana.” Sa'an nan fa Bulus ya ɗaga hannu, ya fara kawo hanzarinsa ya ce, 2 “Lalle na yi arziki, ya sarki Agaribas, da yake a gabanka ne zan kawo hanzarina yau a game da duk ƙarata da Yahudawa suka yi, 3 musamman da yake gwani ne kai ga sanin al'adun Yahudawa da maganganunsu. Saboda haka, ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri. 4 “Irin zaman da na yi tun daga ƙuruciyata, wato tun da farko, a cikin jama'armu da kuma a Urushalima har ya zuwa yau, sananne ne ga dukan Yahudawa. 5 Sun sani tun ainihi, in dai za su yarda su yi shaida, cewa lalle ni Bafarisiye ne bisa ga ɗariƙar nan da ta fi tsanani a cikin addinin nan namu. 6 Ai, saboda na sa zuciya ga cikar alkawarin nan ne da Allah ya yi wa kakanninmu nake nan a tsaye a yi mini shari'a. 7 Alkwarin nan kuwa, shi ne wanda kabilanmu goma sha biyu suke himmantuwa ga bauta wa Allah dare da rana, suna sa zuciya su ga cikarsa. Saboda sa zuciyar nan kuma fa Yahudawa suke ƙarata, ya sarki! 8 Yaya cewa Allah yana ta da matattu sa'an nan, ya ƙi gaskatuwa a gare ku? 9 “To, ni kaina ma a dā na ga kamar wajibi ne in yi abubuwa da yawa, na gāba da sunan Yesu Banazare. 10 Na kuwa yi haka a Urushalima, har na sami izinin daga manyan firstoci, na kulle tsarkaka da yawa a kurkuku. Har ma a lokacin da ake kashe su ina goyon bayan yin haka ɗin. 11 Na kuma sha gwada musu azaba a dukan majami'u, ina ƙoƙarin sa su yin saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.”

Labarin Juyowar Bulus

12 “A cikin hali haka ne, ina tafiya Dimashƙu da izinin manyan firistoci da kuma saƙonsu, 13 da rana a tsaka a hanya, ya sarki, na ga wani haske ya bayyana daga sama, fiye da hasken rana, duk ya haskaka kewaye da ni da abokan tafiyata. 14 Da duk muka fāɗi, sai na ji wata murya tana ce mini da yahudanci, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Da wuya a gare ka ka yi ta shuri bisa a kan tsini.’ 15 Ni kuwa sai na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ Sai Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa. 16 Amma tashi ka miƙe a tsaye, gama na bayyana a gare ka ne da wannan maƙasudi, wato in sa ka mai hidima, mashaidi kuma na abubuwan da ka gani a game da ni, da kuma abubuwa waɗanda zan bayyana maka a nan gaba. 17 Zan tsirar da kai daga jama'ar nan da kuma al'ummai, waɗanda zan aike ka a gare su, 18 domin ka buɗe musu ido, su juyo daga duhu zuwa haske, daga kuma mulkin Shaiɗan zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai, da kuma gādo tare da dukan tsarkaka saboda sun gaskata da ni.’ ”

Shaidar Bulus a gaban Yahudawa da Al'ummai

19 “Saboda haka, ya sarki Agaribas, ban ƙi biyayya ga wahayin nan da ya zo mini daga Sama ba. 20 Da fari, na yi wa mutanen Dimashƙu wa'azi, sa'an nan na yi a Urushalima da dukan kewayen ƙasar Yahudiya, sa'an nan kuma na yi wa al'ummai, cewa su tuba su juyo ga Allah, su kuma yi aikin da zai nuna tubarsu. 21 Saboda wannan dalili ne Yahudawa suka kama ni a Haikali, har suna neman kashe ni. 22 Da na sami taimakon Allah kuwa, ga ni a nan har yanzu, ina shaida wa babba da yaro, ba na faɗar kome sai abin da annabawa da Musa suka ce zai auku, 23 cewa dai lalle ne Almasihu yă sha wuya, shi ne kuma zai fara tashi daga matattu, ya sanar da jama'ar nan da al'ummai haske.”

Bulus yana Fata Agaribas ya Gaskata

24 Bulus yana cikin kawo hanzarinsa, sai Festas ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Bulus, kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.” 25 Amma Bulus ya ce, “Ya mafifici Festas, ai, ban ruɗe ba, gaskiya nake faɗa, a cikin natsuwa kuwa. 26 Ai, al'amarin nan sananne ne ga sarki, ina kuma masa magana gabagaɗi ne, gama na tabbata ba abin da ya kuɓuce wa hankalinsa a cikin al'amarin nan, don wannan abu ba a ɓoye aka yi shi ba. 27 Ya sarki Agaribas, ka gaskata annabawa? Na dai sani ka gaskata.” 28 Sai Agaribas ya ce wa Bulus, “Wato a ɗan wannan taƙaitaccen lokaci kake nufin mai da ni Kirista?” 29 Bulus kuwa ya ce, “Ko a ɗan wannan, ko a mai yawa, ina fata ga Allah, ba kai kaɗai ba, har ma duk waɗanda suke saurarona a yau, su zama kamar yadda nake, sai dai banda sarƙar nan.” 30 Sai sarki ya tashi, haka kuma mai mulki da Barniki, da waɗanda suke a zaune tare da su. 31 Bayan sun keɓe a waje ɗaya, suka yi shawara, suka ce, “Ai, mutumin nan bai yi wani abin da ya isa kisa ko ɗauri ba.” 32 Agaribas kuma ya ce wa Festas, “Ba don dai mutumin nan ya riga ya nemi ɗaukaka ƙararsa a gaban Kaisar ba, da sai a sake shi.”

Ayyukan Manzanni 27

Bulus ya Shiga Jirgi zuwa Roma

1 Da aka shirya mu tashi a jirgin ruwa zuwa ƙasar Italiya, sai suka danƙa Bulus da waɗansu 'yan sarƙa a hannun wani jarumi, mai suna Yuliyas, na ƙungiyar Augustas. 2 Da muka shiga wani jirgi na Adaramitiya, mai shirin tashi zuwa waɗansu garuruwan da suke gaɓar Asiya, muka fara tafiya. Aristarkus kuwa, wani mutumin Tasalonika ta ƙasar Makidoniya, yana tare da mu. 3 Kashegari ga mu a Sidon. Yuliyas kuwa ya yi wa Bulus alheri, ya ba shi izini ya je ya gano abokansa, su yi masa taimako. 4 Da muka tashi daga nan a jirgin ruwa sai muka zaga ta bayan tsibirin Kubrus, saboda iska tana gāba da mu. 5 Bayan da muka haye bahar ɗin da yake kusa da kasar Kilikiya da ta Bamfiliya, muka isa Mira ta ƙasar Likiya. 6 A nan jarumin ya sami wani jirgin Iskandariya mai zuwa ƙasar Italiya, ya sa mu a ciki. 7 Muka yi kwana da kwanaki muna tafiya kaɗan kaɗan, har da ƙyar muka kai kusa da Kinidas. Da dai iska ta hana mu ci gaba, muka zaga ta bayan tsibirin Karita kusa da Salmoni. 8 Muna bin gefen gaɓarsa da ƙyar, har muka isa wani wuri mai suna Amintacciyar Mafaka, wadda take a kusa da birnin Lasiya. 9 Da yake an ɓata lokaci mai yawa, tafiyar ma ta riga ta zama mai hatsari, lokacin azumi kuwa ya wuce, sai Bulus ya gargaɗe su, 10 ya ce musu, “Ya ku jama'a, na dai ga tafiyar nan za ta zamanto da masifa da hasara mai yawa, ba ta kaya da jirgi kawai ba, har ma ta rayukanmu.” 11 Amma jarumin soja, ya fi mai da hankali ga maganar mai tuƙin jirgin da kuma ta mai jirgin, a kan abin da Bulus ya faɗa. 12 Da yake mafakar nan ba ta kamaci jirage su ci damuna a ciki ba, sai yawanci suka kawo shawara a tashi daga nan, ko ta ƙaƙa su iya kaiwa Finikiya, wata mafakar tsibirin Karita, mai duban gabas maso arewa da kuma gabas maso kudu, su ci damuna a can.

Hadiri a Teku

13 Da iska ta buso daga kudu sannu sannu, a tsammaninsu muradinsu ya biya ke nan, sai suka janye anka suka bi ta gefen tsibirin Karita gab da gaci. 14 Ba da jimawa ba, kuwa dai ga wata gawurtacciyar iska da ake kira Yurokilidon ta bugo daga tsibirin. 15 Da iskar ta bugo jirgin, har ya kasa fuskantarta, sai muka sallama mata, ta yi ta kora mu. 16 Da muka bi ta jikin wani ɗan tsibiri mai suna Kauda muka samu muka yi iko da ƙaramin jirginmu da ƙyar. 17 Bayan da suka jawo ƙaramin jirgi zuwa cikin babban jirgi, sai suka yi dabara suka ɗaɗɗaura igiyoyi ta gindin babban jirgin, suka rage shi. Don kuma gudun kada a fyaɗa su a yashin nan na Sirtis mai haɗiye kome, suka sauke filafilai, aka kora jirgin haka. 18 Saboda hadiri yana sa mu tangaɗi ƙwarai da gaske, kashegari sai suka fara watsar da kayan da jirgin ya ɗauko, a ruwa. 19 A rana ta uku kuma, su da kansu suka jefar da kayan aikin jirgin. 20 Da dai muka yi kwana da kwanaki ba mu ga rana ko taurari ba, gawurtacciyar iskar hadiri kuma ta yi ta bugunmu, sai muka fid da zuciya daga tsira. 21 Da yake an daɗe ba cin abinci, sai Bulus ya miƙe a tsaye a tsakiyarsu, ya ce, “Ya ku jama'a, da kun ji maganata, da ba ku taso daga tsibirin Karita kun fāɗa wannan masifa da hasara ba. 22 To, a yanzu, ina yi muku gargaɗi ku yi ƙarfin hali, don ba wanda zai yi hasarar ransa a cikinku, sai dai a yi hasarar jirgin. 23 Don a daren jiya mala'ikan Allah wanda ni nasa ne, nake kuma bauta masa, ya tsaya kusa da ni, 24 ya ce, ‘Kada ka ji tsoro Bulus, lalle za ka tsaya a gaban Kaisar, ga shi kuma, Allah ya amsa ya yardar maka duk abokan tafiyarka su tsira.’ 25 Saboda haka, sai ku yi ƙarfin hali, ya ku jama'a, domin na gaskata Allah a kan cewa, yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka za a yi. 26 Amma fa lalle ne a fyaɗa mu a wani tsibirin.” 27 A dare na goma sha huɗu, ana ta kora mu sakaka a bahar Adariya, wajen tsakar dare sai masu tuƙi suka zaci mun yi kusa da ƙasa. 28 Sai suka gwada zurfin ruwan, suka sami gaba ashirin, da muka ci gaba kaɗan, sai suka sāke gwadawa, suka sami gaba goma sha biyar. 29 Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki anka guda huɗu na bayan jirgin, suka ƙagauta gari ya waye. 30 Masu tuƙi suna neman gudu daga jirgin ke nan, har sun zura ƙaramin jirgi a cikin ruwa, don a ga kamar za su ja su anka ɗin ne daga goshin jirgin su sake su, 31 sai Bulus ya ce da jarumin yaki da kuma sojan. “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba yadda za a yi ku tsira.” 32 Sai sojan suka yayyanke igiyoyin ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa. 33 Da gari ya yi kusan wayewa sai Bulus ya roƙe su su taɓa ɗan abinci, ya ce, “Yau fa kwana goma sha huɗu ke nan kuke zaman jira, ba wani abin da kuka ci. 34 Saboda haka, ina roƙonku ku ci abinci, don lafiyarku, tun da yake ba wanda ko gashin kansa zai yi ciwo a cikinku.” 35 Da ya faɗi haka, ya ɗauki curin gurasa, ya yi godiya ga Allah a gabansu duka, sa'an nan ya gutsuttsura ya fara ci. 36 Sai duk suka farfado, su ma kansu suka ci abinci. 37 Mu duka a cikin jirgin kuwa mutum metan da saba'in da shida ne. 38 Da suka ci suka ƙoshi, sai suka riƙa rage wa jirgin nauyi, suka yi ta zub da alkama a cikin ruwa.

Ragargajewar Jirgi

39 Da gari ya waye ba su shaida ƙasar ba, amma dai sun lura da wani lungu da gaci mai yashi, sai kuma suka yi shawara cewa in mai yiwuwa ne su kai jirgin kan yashin. 40 Sai suka daddatse su anka duka, suka bar su a ruwa, suna kuma ɓalle maɗaurin abin juyar da jirgin a lokacin, sa'an nan kuma suka ta da filafilan goshin jirgin daidai iska, suka doshi gaci. 41 Amma da muka isa wata mahaɗar ruwa, sai suka tura jirgin ya dunguri yashi, har goshinsa ya cije ya kasa motsi, ƙarshensa kuma ya fara ragargejewa saboda haukan raƙuman ruwa. 42 Sai sojan suka yi niyya su kashe 'yan sarka, don kada wani ya yi ninƙaya ya tsira. 43 Amma jarumin da ya so ya ceci Bulus, ya hana i da nufinsu, ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci, 44 sauran kuwa waɗansu suka hau katako, waɗansu kuma suka hau tarkacen jirgin. Da haka duk suka kai gaci lafiya.

Ayyukan Manzanni 28

Bulus a Tsibirin Malita

1 Bayan da muka tsira, sai muka ji, ashe, sunan tsibirin nan Malita ne. 2 Mutanen garin kuwa sun yi mana alheri matuƙar alheri, don sun hura wuta sun karɓe mu, mu duka, saboda ana ruwa, ga kuma sanyi. 3 Sa'ad da Bulus ya tattaro waɗansu ƙirare rungume guda ya sa a wutar, sai ga wani maciji ya bullo saboda zafi, ya ɗafe masa a hannu. 4 Da mutanen garin suka ga mugum ƙwaron nan a makale a hannun Bulus, suka ce wa juna, “Lalle mutumin nan mai kisankai ne, kun ga ko da yake ya tsira daga bahar, duk da haka alhaki yana binsa sai ya mutu.” 5 Bulus kuwa ya karkaɗe ƙwaron a cikin wutar, bai kuwa ji wani ciwo ba. 6 Su kuwa suna zaton wurin zai kumbura, ko kuwa farat ɗaya ya fāɗi matacce. Amma da aka daɗe suka ga ba abin da ya same shi, suka sāke magana suka ce lalle shi wani Allah ne. 7 A nan kusa kuwa akwai wani fili, mallakar shugaban tsibirin nan, mai suna Babiliyas. Shi ne ya karɓe mu, ya sauke mu a cikin martaba har kwana uku. 8 Ashe, mahaifin Babiliyas yana a kwance, yana fama da zazzaɓi da ciwon atuni. Sai Bulus ya shiga wurinsa ya yi addu'a, ya ɗora masa hannu ya warkar da shi. 9 Da aka yi haka sai duk sauran marasa lafiya a tsibirin suka riƙa zuwa ana warkar da su. 10 Suka yi mana kyauta mai yawa, da za mu tashi a jirgin ruwa kuma, suka yi ta tara mana duk irin abubuwan da muke bukata.

Bulus ya Isa Roma

11 Bayan wata uku muka tashi a cikin wani jirgin Iskandariya, wanda ya ci damuna a nan tsibirin. An kuwa yi masa alama da surar Tagwaye Maza. 12 Da muka zo Sirakusa muka kwana uku a nan. 13 Daga nan kuma muka zaga sai ga mu a Rigiyum. Da muka kwana, iska ta taso daga kudu, kashegari kuma muka kai Butiyoli. 14 A nan muka tarar da waɗansu 'yan'uwa, suka roƙe mu mu kwana bakwai tare da su. Da haka dai har muka isa Roma. 15 Da 'yan'uwa na can suka ji labarinmu, sai da suka zo don su tarye mu har Kasuwar Abiyus, da kuma wurin nan da ake kira Maciya Uku. Da kuwa Bulus ya sadu da su, ya yi godiya ga Allah, jikinsa kuma ya yi ƙarfi. 16 Da muka shiga Roma aka yardar wa Bulus ya je ya sauka abinsa tare da sojan da yake tsaronsa.

Wa'azin Bulus a Roma

17 Bayan kwana uku ya kira manyan Yahudawan birnin. Da suka taru sai ya ce musu, “Ya ku 'yan'uwa, ko da yake ban yi wa jama'armu wani laifi ba, ko laifi a game da al'adun kakanninmu, duk da haka an bashe ni ɗaurarre ga Romawa tun daga Urushalima. 18 Su kuwa da suka tuhume ni, suna so su sāke ni, don ban yi wani laifi da ya isa kisa ba. 19 Amma da Yahudawa suka ƙi yarda, sai ya zamar mini dole in nema a ɗaukaka ƙarata gaban Kaisar, ba don ina ƙarar jama'armu ba ne. 20 Shi ya sa na nema in gana da ku, tun da yake dai saboda sa zuciyar nan da Isra'ila take yi ne nake ɗaure da sarƙan nan.” 21 Sai suka ce masa, “Mu kam, ba mu sami wata wasiƙa daga Yahudiya a game da kai ba, ba kuwa wani ɗan'uwanmu da ya zo nan ya kawo labarinka, ko ya faɗi wata mummunar magana a game da kai. 22 Amma muna so mu ji daga bakinka abin da yake ra'ayinka, don in dai ta ɗariƙar nan ne, mun sani ko'ina ana kushenta.” 23 Da suka sa masa rana, sai suka zo masaukinsa, su da yawa. Sa'an nan ya yi ta yi musu bayani, yana ta shaidar musu Mulkin Allah, tun daga safe har magariba, yana ƙoƙarin rinjayarsu a kan Yesu, ta hanyar Attaurar Musa da littattafan annabawa. 24 Waɗansu sun rinjayu da maganarsa, amma waɗansu sun ƙi gaskatawa. 25 Da suka kasa yarda a junansu, kafin su watse sai Bulus ya yi musu magana ɗaya ya ce, “Ashe kuwa, Ruhu Mai Tsarki ya faɗa, da ya yi wa kakanninku magana ta bakin Annabi Ishaya cewa, 26 ‘Je ka wurin jama'ar nan, ka ce, Za ku ji kam, amma ba za ku fahimta ba faufau, Za ku gani kuma, amma ba za ku gane faufau. 27 Don zuciyar jama'ar nan ta yi kanta, Sun toshe kunnuwansu, Sun kuma runtse idanunsu, don kada su gani da idanunsu, Su kuma ji da kunnuwansu, Su kuma fahimta a zuciyarsu, Har su juyo gare ni in warkar da su.’ 28 To, sai ku sani, wannan ceto na Allah, an aiko da shi har ga al'ummai, su kam za su saurara.” 29 (Da ya faɗi haka, sai Yahudawa suka tashi suna ta muhawwara da juna.) 30 Sai Bulus ya zauna a nan a gidan da yake haya, har shekara biyu cikakku, yana maraba da duk wanda ya je wurinsa, 31 yana ta wa'azin Mulkin Allah, da koyar da al'amarin Ubangiji Yesu Almasihu gabagaɗi, ba tare da wani hani ba.

Romawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, bawan Yesu Almasihu, manzo kirayayye, keɓaɓɓe domin yin bisharar Allah, 2 wadda Allah ya yi alkawari tun dā, ta bakin annabawansa a cikin Littattafai masu tsarki. 3 Bishara ɗin nan a kan Ɗansa ce, Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ga jiki shi zuriyar Dawuda ne, 4 amma ga tsarkinsa na ruhu shi Ɗan Allah ne, da iko aka ayyana shi haka ta wurin tashinsa daga matattu. 5 Ta wurinsa ne muka sami alheri da kuma manzanci, saboda sunansa dukan al'ummai su gaskata su yi biyayya, 6 a cikinsu kuma har da ku da kuke kirayayyun Yesu Almasihu. 7 Daga Bulus zuwa ga dukan ƙaunatattun Allah da kuke a Roma, tsarkaka kirayayyu. Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Nufin Bulus ya Ziyarci Roma

8 Da farko dai ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Almasihu saboda ku duka, domin ana baza labarin bangaskiyarku a ko'ina a duniya. 9 Domin kuwa Allah, wanda nake bauta wa a ruhuna ta yin bisharar Ɗansa, shi ne mashaidina a kan yadda kullum ba na fasa ambatonku a cikin addu'ata, 10 ina addu'a, ko ta ƙaƙa, da yardar Allah, a yanzu kam, in sami arzikin zuwa wurinku. 11 Domin ina ɗokin ganinku, in ni'imta ku da wata baiwa ta ruhu, domin ku ƙarfafa. 12 Wato ni da ku, mu ƙarfafa juna ta bangaskiyarmu, tawa da taku. 13 Ina so ku sani 'yan'uwa, na sha ɗaura niyyar zuwa wurinku, ko da yake har yanzu ba a yardar mini ba, domin ku ma in sami amfani a gare ku, kamar yadda na samu a cikin al'ummai. 14 Akwai hakkin Helenawa, da na bare, da na masu ilimi, da na jahilai duka a kaina. 15 Saboda haka a gwargwadon iyawata, ina da himma ku ma in yi muku bisharar, ku da kuke a Roma.

Ikon Bishara

16 Gama ba na jin kunyar bishara, domin ita ce ikon Allah mai kai kowane mai ba da gaskiya ga samun ceto, Yahudawa da fari, sa'an nan kuma al'ummai. 17 Gama bishara ɗin ta bayyana wata hanyar samun adalci a gaban Allah, hanyar nan kuwa ta bangaskiya ce, tun daga farko har zuwa ƙarshe, yadda yake a rubuce cewa, “Wanda yake da adalci ta wurin bangaskiya zai rayu.”

Laifin 'Yan Adam

18 Gama ana bayyana fushin Allah daga Sama, a kan dukan rashin bin Allah, da aikin mugunta na mutanen da suke danne gaskiya, ta aikin muguntarsu, 19 Domin abin da za a iya sani a game da Allah a bayyane yake a gare su, gama Allah ne ya bayyana musu shi. 20 Gama tun daga halittar duniya al'amuran Allah marasa gănuwa, wato ikonsa madawwami, da allahntakarsa, sun fahimtu sarai, ta hanyar abubuwan da aka halitta kuma ake gane su. Saboda haka mutane sun rasa hanzari. 21 Domin kuwa ko da yake sun san da Allah, duk da haka ba su ɗaukaka shi a kan shi Allah ne ba, ba su kuma gode masa ba. Sai tunaninsu ya wofince, zuciyarsu marar fahimta kuma ta duhunta. 22 Suna da'awa cewa, su masu hikima ne, sai suka zama wawaye. 23 Sun sauya ɗaukakar Allah marar mutuwa da misalin siffar mutum mai mutuwa, da ta tsuntsaye, da ta dabbobi, da kuma ta masu jan ciki. 24 Saboda haka Allah ya sallama su ga rashin tsarkaka ta mugayen sha'awace-sha'awacensu, har su wulakanta jikinsu a junansu, 25 saboda sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, har yi wa halitta ibada, sun kuma bauta mata, sun ƙi su yi wa Mahalicci, shi wanda yabo ya tabbata a gare shi har abada. Amin. 26 Don haka Allah ya sallama su ga mugayen sha'awace-sha'awace masu banƙyama, har matansu suka sauya ɗabi'arsu ta halal, da wadda take ta haram. 27 Haka kuma maza suka bar ma'amalarsu ta halal da mata, jarabar juna ta ɗebe su, maza da maza suna aikata rashin kunya, suna jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu. 28 Tun da yake sun ƙi su yarda su san Allah, Allah ya sallama su ga halin banza, su aikata abin kunya. 29 Su masu aikata rashin adalci ne ƙwarai, da mugunta, da kwaɗayi, da ƙeta. Masu hassada ne, da kisankai, da jayayya, da ha'inci, da kuma nukura gaya matuƙa. Macizan ƙaiƙayi ne, 30 da masu yanke, da maƙiyan Allah, da masu cin mutunci, da masu girmankai, da masu ruba, da masu haddasa mugunta, da marasa bin iyaye, 31 da marasa fahimta, da masu ta da alkawari, da marasa ƙauna, da marasa tausayi. 32 Waɗannan kuwa ko da yake sun san shari'ar Allah cewa masu yin irin waɗannan abubuwa, sun cancanci mutuwa, duk da haka, ba aikata su kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon masu yinsu.

Romawa 2

Hukuncin Allah daidai Ne

1 Saboda haka ba ka da wata hujja, kai mutum, ko kai wane ne da kake ganin laifin wani. A yayin da kake ganin laifin wani, ai, kanka kake hukunta wa, don ga shi, kai mai ganin laifin wani, kai ma haka kake yi. 2 Mun dai san hukuncin Allah a kan masu yin haka daidai ne. 3 Ya kai mutum, kai da kake ganin laifin masu yin haka, alhali kuwa kai kanka, kana yinsu, kana tsammani za ka tsere wa hukuncin Allah ne? 4 Ko kuwa kana raina yalwar alherinsa, da jimirinsa, da kuma haƙurinsa ne? Ashe, ba ka sani ba alherin Allah yana jawo ka zuwa ga tuba? 5 Amma ga shi, saboda ƙeƙasasshiyar zuciyarka marar tuba, kana nema wa kanka fushin Allah a ranar fushi, sa'ad da za a bayyana hukuncin Allah macancani. 6 Allah ne zai saka wa kowa gwargwadon aikinsa. 7 Waɗanda suke neman daraja da ɗaukaka da kuma dawwama ta wurin naciyarsu ga aikata nagarta, zai saka musu da rai madawwami. 8 Waɗanda suke masu sonkai, da waɗanda ke ƙin bin gaskiya, da masu bin rashin adalci, zai saka musu da fushi da hasala. 9 Duk waɗanda suke aikata mugunta za su sha wahala da masifa, da fari Yahudawa, sa'an nan kuma al'ummai. 10 Amma Allah zai ba da daraja, da ɗaukaka, da salama ga dukan waɗanda suke aikata nagarta, da fari ga Yahudawa, sa'an nan ga al'ummai. 11 Domin kuwa, Allah ba ya nuna tara. 12 Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a rashin sanin Shari'a, za su hallaka na ba tare da Shari'a ba. Ɗaukacin waɗanda suka yi zunubi a ƙarƙashin Shari'a kuwa, za a hukunta su ta hanyar Shari'a. 13 Don ba ta jin shari'ar kawai mutum yake samun kuɓuta ga Allah ba, sai dai masu aikata ta, su ne za su kuɓuta. 14 In al'ummai, su da ba su da Shari'a, jikinsu ya ba su suka bi umarnin Shari'a, ko da yake ba su da Shari'ar, ashe kuwa, suna da shari'a ke nan. 15 Ayyukansu sun nuna, cewa abin da Shari'a ta umarta a rubuce yake a cikin zukatansu, lamirinsu kuwa yana shaidawa, tunaninsu kuwa yana zarginsu, ko kuma yana kāre su. 16 A wannan rana Allah zai yi wa 'yan adam shari'a a kan asiransu, ta wurin Yesu Almasihu, bisa ga bishara da nake wa'azinta.

Yahudawa da Shari'a

17 To, in ka ce kai Bayahude ne, cewa ka dogara da Shari'a, har kana taƙama da Allah, 18 ka san abin da yake so, da ya ke kuma ka karantu da Shari'a, ka iya bambancewa da abubuwa mafifita, 19 har ka amince kai kanka jagoran makafi ne, haske ga waɗanda suke a cikin duhu, 20 mai horon marasa azanci, mai koya wa sababbin shiga, don a cikin Shari'ar kana da ainihin sani da ainihin gaskiya, 21 to, kai mai koya wa wani, ba ka koya wa kanka? Kai mai wa'azin kada a yi sata, shin, kai ba ka yi ne? 22 Kai mai cewa kada a yi zina, kai ba ka yi ne? Kai mai ƙyamar gumaka, ba ka sata a ɗakin gunki ne? 23 Kai mai taƙama da Shari'a, ashe, ba wulakanta Allah kake yi ba ta keta Shari'ar? 24 Yadda yake a rubuce cewa, “A sanadinku ne al'ummai suke saɓon sunan Allah.” 25 Lalle yin kaciya yana da amfani, in dai kana bin Shari'ar. Amma in kai mai keta shari'ar ne, kaciyarka ba a bakin kome take ba. 26 In kuwa marar kaciya yana kiyaye farillan Shari'a, ashe, ba sai a lasafta rashin kaciyarsa a kan kaciya ba? 27 Ashe, wanda rashin kaciya al'adarsa ce, ga shi kuwa, yana bin Shari'ar daidai, ba sai ya kāshe ka ba, kai da kake da Shari'a a rubuce da kuma kaciya, amma kana keta Shari'ar? 28 Gama Bayahude na ainihi ba mutum ne wanda yake Bayahude bisa siffar jikinsa na fili ba, kaciya ta ainihi kuwa ba kaciya ce ta fili ta fatar jiki ba. 29 Wanda yake Bayahude a zuci, ai, shi ne Bayahude. Kaciyar ainihi kuwa a zuci take, wato ta ruhu, ba ta zahiri ba. Irin wannan mutum, Allah ne yake yaba masa, ba ɗan adam ba.

Romawa 3

1 To, ina fifikon Bayahude? Ko kuma ina fa'idar kaciya? 2 Ai kuwa, akwai ƙwarai, ta kowace hanya. Da farko dai, Yahudawa su ne aka amince wa a game da zantuttukan Allah. 3 To, ƙaƙa ke nan in waɗansu sun ci amanar nan? Sai cin amanarsu ya shafe cikar alkawarin Allah? 4 A'a, ko kusa! A dai tabbata Allah mai gaskiya ne, ko da yake kowane mutum maƙaryaci ne, yadda yake a rubuce cewa, “Don maganarka tă tabbatar da adalcinka, Ka kuma yi rinjaye in an binciki al'amarinka.” 5 In kuwa rashin adalcinmu shi ne yake nuna adalcin Allah a fili, me za mu ce? In Allah ya hore mu, ya yi rashin adalci ke nan? (Misali nake yi kawai.) 6 A'a, ko kusa! To, in da haka ne, ta ƙaƙa Allah zai yi wa duniya shari'a? 7 In kuwa, a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka kara ɗaukaka shi, to, don me har yanzu ake hukunta ni a kan ni mai zunubi ne? 8 In haka ne, ba sai mu yi ta yin mugun aiki don ya zama sanadin nagarta ba? Kamar yadda dai waɗansu suke mana yanke, cewa haka muke faɗa. Hukuncin da za a yi wa irin waɗannan kuwa daidai ne.

Babu Mai Adalci

9 To, ƙaƙa? Mu Yahudawa mun fi sauran ne? A'a, ko kaɗan! Don dā ma mun ɗora wa Yahudawa da al'ummai laifi, cewa dukkansu zunubi yana iko da su. 10 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Babu wani mai adalci, babu, ko ɗaya, 11 Babu wani mai fahimta, babu wani mai neman Allah. 12 Duk sun bauɗe, sun zama marasa amfani baki ɗaya, Babu wani mai aiki nagari, babu kam, ko da guda ɗaya.” 13 “Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗen kabari ne, Maganarsu ta yaudara ce.” “Masu ciwon baki ne.” 14 “Yawan zage-zage da ɗacin baki gare su.” 15 “Masu hanzarin zub da jini ne, 16 Ta ko'ina suka bi sai hallaka da baƙin ciki, 17 Ba su kuma san hanyar salama ba.” 18 “Babu tsoron Allah a cikin sha'aninsu sam.” 19 To, mun sani duk abin da Shari'a ta ce, ya shafi waɗanda suke ƙarƙashinta ne, don a tuƙe hanzarin kowa, duk duniya kuma tă sani ƙarƙashin hukuncin Allah take. 20 Ai, ba wani ɗan adam da zai sami kuɓuta ga Allah ta kiyaye ayyukan Shari'a, tun da yake ta Shari'a ne mutum yake ganin laifinsa.

Adalci ta wurin Bangaskiya

21 A yanzu, ba kuwa a game da shari'a ba, an bayyana wata hanyar samun adalcin Allah, wadda ma Attaura da littattafan annabawa suke yi wa shaida. 22 Adalcin nan na Allah, wanda yake samuwa ta wurin bangaskiya ga Yesu Almasihu, na masu ba da gaskiya ne dukka, ba kuwa wani bambamci, 23 gama 'yan adam duka sun yi zunubi, sun kasa kuma ga ɗaukakar Allah. 24 Amma ta wurin alherin da Allah ya yi musu kyauta, sun sami kuɓuta ta wurin fansar da Almasihu Yesu ya yi. 25 Allah kuwa ya ayyana Yesu Almasihu ya zama hadayar sulhu, ta wurin ba da gaskiya ga jininsa. Allah kuwa ya yi haka domin ya nuna adalcinsa ne, domin dā saboda haƙurinsa ya jingine zunuban da aka gabatar, 26 domin a nuna adalcinsa a wannan zamani, wato a bayyana shi kansa mai adalci ne, mai kuɓutar da duk mai gaskatawa da Yesu kuma. 27 To, ina kuma fariyarmu ta shiga? Ina kuwa! Ta wace hanya aka kawar da ita? Ta aikin lada? A'a, sai dai ta hanyar bangaskiya. 28 Domin mun amince, cewa ta bangaskiya ne mutum yake kuɓuta, ba ta kiyaye ayyukan Shari'a ba. 29 Wato Allah, Allahn Yahudawa ne kurum? Ashe, ba na al'ummai ba ne kuma? Hakika na al'ummai ne ma, 30 tun da yake Allah ɗaya ne, zai kuwa kuɓutar da masu kaciya ta wurin bangaskiya, marasa kaciya ma ta wannan bangaskiya. 31 Wato mun soke Shari'a ke nan ta bangaskiyar nan? A'a, ko kusa! Sai tabbatar da ita muka yi.

Romawa 4

Misali na Ibrahim

1 To, me ke nan za mu ce a game da Ibrahim, kakan kakanninmu? 2 Gama in da Ibrahim ya sami kuɓuta ta aikinsa na lada, ashe kuwa, yana da abin yin taƙama ke nan, amma fa ba a gaban Allah ba. 3 To, me Nassin ya ce? “Ibrahim ya gaskata Allah, bangaskiyar nan tasa kuma aka lasafta ta adalci ce a gare shi.” 4 Wanda yake aikin lada, ladarsa ba kyauta ba ce, sakamakon aikinsa ce. 5 Wanda ba ya aikin lada, amma yana dogararsa ga Allah, wanda yake kuɓutar da masu laifi, akan lasafta bangaskiyar nan tasa adalci ce. 6 Haka kuma Dawuda ya yi maganar albarkar da aka yi wa mutumin da Allah yake lasafta adalci a gare shi, ba don ya yi aikin lada ba, 7 da ya ce, “Albarka tā tabbata ga waɗanda aka yafe wa laifofinsu, Waɗanda kuma aka shafe zunubansu, 8 Albarka tā tabbata ga wanda faufau Ubangiji ba zai lasafta zunubansa ba.” 9 To, wannan albarka, masu kaciya ne kawai ake yi wa, ko kuwa har da marasa kaciya ma? Gama abin da muke cewa shi ne, “Aka lasafta bangaskiyar Ibrahim adalci ce a gare shi.” 10 To, a cikin wane hali aka lasafta masa ita? Bayan da aka yi masa kaciya ne, ko kuwa tun ba a yi ba? Ai, tun ba a yi ba ne, ba bayan da aka yi ba. 11 Kaciyar da aka yi masa alama ce, wato tabbatacciyar shaida ce ta samun adalci, albarkacin bangaskiyar da yake da ita tun ba a yi masa kaciya ba. Wannan kuwa, domin yă zama uban dukkan masu ba da gaskiya ne, domin su ma a lasafta su masu adalci ne, ba tare da an yi musu kaciya ba, 12 haka kuma yă zama uban masu kaciya, waɗanda ba kaciya kaɗai suke da ita ba, har ma suna bin hanyar bangaskiyar nan ta kakanmu Ibrahim, wadda shi ma ya bi, tun ba a yi masa kaciya ba.

Tabbatar da Alkawari ta wurin Bangaskiya

13 Alkawarin nan da aka yi wa Ibrahim da zuriyarsa, cewa zai zama magājin duniya, ba ta Shari'a aka yi masa ba, amma domin ya ba da gaskiya ne, shi ya sa Allah ya karɓe shi mai adalci ne. 14 In dai masu bin Shari'a su ne magāda, ashe, bangaskiya ta zama banza ke nan, alkawarin nan kuma ya wofinta, 15 don Shari'a tana jawo fushin Allah. A inda ba Shari'a kuwa, ba keta umarni ke nan. 16 Saboda haka al'amarin ya dogara ga bangaskiya, domin ya zama bisa ga alheri, don kuma a tabbatar da alkawarin nan ga dukkan zuriyar Ibrahim, ba ga masu bin Shari'a kaɗai a cikinsu ba, har ma ga waɗanda suke da bangaskiya irin Ibrahim, shi da yake ubanmu duka. 17 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Na sa ka uban al'ummai da yawa.” Shi ne kuwa ubanmu a gaban Allah, wannan da ya gaskata, wato mai raya matattu, shi ne kuma mai kiran marasa kasancewa kamar sun kasance. 18 Ibrahim kuwa ko da yake ba halin sa zuciya a gare shi, sai ya yi ta sawa, ya gaskata zai zama uban al'ummai da yawa, kamar yadda aka faɗa masa cewa, “Haka zuriyarka za ta yawaita.” 19 Bangaskiyarsa kuwa ba ta raunana ba, bai dubi gajiyawar jikinsa ba, don yana da shekara wajen ɗari a lokacin, ko kuma cewa Saratu ta wuce haihuwa. 20 Ba kuwa wata rashin bangaskiyar da ta sa shi shakkar cikar alkawarin Allah, sai ma ƙara ƙarfafa ga bangaskiyarsa ya yi, yana ɗaukaka Allah, 21 yana haƙƙaƙewa, cewa Allah na da ikon yin abin da ya yi alkawari. 22 Shi ya sa aka lasafta bangaskiyarsa adalci ce a gare shi. 23 To, “Lasafta masa” ɗin nan da aka rubuta kuwa, ba saboda Ibrahim kaɗai aka rubuta ba, 24 har saboda mu ma, za a lasafta mana, wato mu da muke gaskatawa da wannan da ya ta da Yesu Ubangijinmu daga matattu, 25 wanda aka bayar a kashe saboda laifofinmu, aka kuma tashe shi, domin mu sami kuɓuta ga Allah.

Romawa 5

Abubuwan da Kuɓutarwa take Kawowa

1 To, da yake mu kuɓutattu ne ta wurin bangaskiya, muna da salama ke nan a gun Allah, ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu. 2 Ta wurinsa kuma muka sami shiga alherin nan da muke a ciki, saboda bangaskiyarmu, muna kuma taƙama da sa zuciyarmu ga samun ɗaukakar nan ta Allah. 3 Banda haka ma, har muna taƙama da shan wuyarmu, da yake mun sani shan wuya take sa jimiri, 4 jimiri kuma yake sa ingataccen hali, ingataccen hali kuma yake sa sa zuciya, 5 ita sa zuciyar nan kuwa ba ta sāce iska faufau, domin Allah ya kwarara ƙaunarsa a zukatanmu, ta wurin Ruhu Mai Tsarki da aka ba mu. 6 Tun muna raunana tukuna, Almasihu ya mutu a daidaitaccen lokaci, domin marasa bin Allah. 7 Da ƙyar za a sami wanda zai ba da ransa, saboda mutum mai adalci, ko da yake watakila saboda mutum mai nagarta wani ma sai ya yi kasai da ransa. 8 Amma kuwa Allah yana tabbatar mana da ƙaunar da yake yi mana, wato tun muna masu zunubi, Almasihu ya mutu dominmu. 9 To, tun da yake a yanzu an kuɓutar da mu ta wurin jininsa, ashe kuwa, ta wurinsa za mu fi samun kārewa daga fushin Allah ke nan. 10 In kuwa tun muna maƙiyan Allah aka sulhunta mu da shi ta mutuwar Ɗansa, to, da yake an sulhunta mu, ashe kuwa, za a fi kāre mu ta wurin rayuwarsa ke nan. 11 Banda haka ma, har muna fariya da Allah ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurinsa ne muka sami sulhun nan a yanzu.

Adamu da Almasihu

12 To, kamar yadda zunubi ya shigo duniya ta dalilin mutum ɗaya, zunubi kuwa shi ya jawo mutuwa, ta haka mutuwa ta zama gādo ga kowa, don kowa ya yi zunubi. 13 Lalle fa zunubi yana nan a duniya tun ba a ba da Shari'a ba, sai dai inda ba shari'a, ba a lasafta zunubi. 14 Duk da haka kuwa mutuwa ta mallaka tun daga Adamu har ya zuwa Musa, har ma a kan waɗanda ba su yi zunubi irin na keta umarnin da adamu ya yi ba, wanda yake shi ne kwatancin mai zuwan nan. 15 Amma fa baiwar nan dabam take ƙwarai da laifin nan. Ai, in laifin mutum ɗayan nan ya jawo wa masu ɗumbun yawa mutuwa, ashe ma, alherin Allah, da kuma baiwar nan, albarkacin alherin Mutum ɗaya, Yesu Almasihu, sai su yalwata ga masu ɗumbun yawa fin haka ƙwarai. 16 Baiwar nan kuwa dabam take ƙwarai da hakkokin zunubin mutum ɗayan nan. Don kuwa hukuncin da aka yi a kan laifin mutum ɗayan nan, shi ya jawo hukuncin hallaka. Amma baiwar nan da aka yi a sanadin laifofi da yawa, ita take sa kuɓuta ga Allah. 17 In kuwa saboda laifin mutum ɗayan nan ne mutuwa ta yi mallaka ta wurinsa, ashe kuwa, waɗanda suke samun alherin nan mayalwaci, da kuma baiwar nan ta adalcin Allah, sai su yi mallaka fin haka ƙwarai a cikin rai, ta wurin ɗayan nan, wato Yesu Almasihu. 18 To, kamar yadda laifin mutum ɗayan nan ya jawo wa dukan mutane hukunci, haka kuma aikin adalci na Mutum ɗayan nan ya zama wa dukan mutane sanadin kuɓuta zuwa rai. 19 Kamar yadda masu ɗumbun yawa suka zama masu zunubi ta wurin rashin biyayyar mutum ɗaya, haka kuma ta wurin biyayyar Mutum ɗaya za a mai da masu ɗumbun yawa masu adalci. 20 Shari'a fa, an shigo da ita ne, don laifi yă haɓaka. Amma a inda zunubi ya haɓaka, alherin Allah ma ya fi haɓaka ƙwarai da gaske. 21 Wato kamar yadda mallakar zunubi mutuwa ce, haka mallakar Allah ta wurin alheri adalci ce, da ke bi da mu zuwa rai madawwami ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu.

Romawa 6

Mutuwa ga Zunubi, Rayuwa ga Almasihu

1 To, me kuma za mu ce? Ma ci gaba da yin zunubi ne domin alherin Allah yă haɓaka? 2 A'a, ko kusa! Mu da muka mutu ga zunubi, ƙaƙa za mu ƙara rayuwa a cikinsa har yanzu? 3 Ashe, ba ku sani ba duk ɗaukacinmu da aka yi wa baftisma a cikin Almasihu Yesu, a cikin mutuwarsa aka yi mana baftismar ba? 4 Saboda haka, an binne mu da shi ke nan, ta wurin baftisma cikin mutuwarsa, domin kamar yadda aka ta da Almasihu daga matattu ta wurin ɗaukakar Uba, haka mu ma mu yi zaman sabuwar rayuwa. 5 Tun da yake mun zama ɗaya da shi wajen kwatancin mutuwarsa, ashe kuwa, za mu zama ɗaya ma a wajen tashinsa. 6 Wato, mun sani an gicciye halayenmu na dā tare da shi, domin a hallakar da ikon nan namu mai zunnubi, kada mu ƙara bauta wa zunubi. 7 Wanda ya yi irin wannan mutuwa kuwa, an kuɓutar da shi daga zunubi ke nan. 8 Amma idan muka mutu tare da Almasihu, mun gaskata za mu rayu tare da shi kuma. 9 Mun sani tun da yake an ta da Almasihu daga matattu, ba zai sāke mutuwa ba ke nan, mutuwa ba ta da sauran wani iko a kansa. 10 Mutuwar nan da ya yi kuwa, ya mutu ne sau ɗaya tak ba ƙari, saboda shafe zunubanmu, amma rayuwar da yake yi, yana rayuwa ne, rayuwa ga Allah. 11 Haka ku ma sai ku lasafta kanku kamar ku matattu ne ga zunubi, amma kuna a raye rayuwa ga Allah, ta wurin Almasihu Yesu. 12 Saboda haka, kada ku yarda zunubi ya mallaki jikin nan naku mai mutuwa har da za ku biye wa muguwar sha'awarsa. 13 Kada kuma ku miƙa gaɓoɓinku su zama kayan aikin mugunta, don yin zunubi. Amma ku miƙa kanku ga Allah, kamar waɗanda aka raya bayan mutuwa, kuna miƙa gaɓoɓinku ga Allah kayan aikin adalci. 14 Domin zunubi ba zai mallake ku ba, tun da yake ba shari'a take iko da ku ba alherin Allah ne.

Bayin Adalci

15 To, ƙaƙa? Wato, sai mu yi zunubi don shari'a ba ta iko da mu, sai alherin Allah? A'a, ko kusa! 16 Ba ku sani ba, shi wanda kuke miƙa kanku a gare shi domin yi wa biyayya, lalle ku bayi ne na wanda kuke yi wa biyayya ɗin (ko bautar zunubi wanda ƙarshensa mutuwa ne, ko bautar biyayya wadda ƙarshenta adalci ce)? 17 Amma godiya tā tabbata ga Allah, ko da yake dā can ku bayin zunubi ne, a yanzu kam kuna biyayya da zuciya ɗaya ga irin koyarwar nan da aka yi muku. 18 Da aka 'yanta ku kuma daga bautar zunubi, kun zama bayin aikin adalci. 19 Mai da magana nake yi irin ta yau da kullum, saboda rarraunar ɗabi'arku. Wato, kamar yadda dā can kuka miƙa gaɓoɓinku ga bautar rashin tsarki, da mugun aiki a kan mugun aiki, haka kuma a yanzu sai ku miƙa gaɓoɓinku ga bautar aikin adalci, domin aikata tsarkakan ayyuka. 20 Sa'ad da kuke bayin zunubi, ba ruwanku da aikin adalci. 21 To, wace fa'ida kuka samu a lokacin nan, a game da aikin da kuke jin kunya a yanzu? Lalle ƙarshen irin wannan aiki mutuwa ne. 22 Amma a yanzu da aka 'yanta ku daga bautar zunubi, kun zama bayin Allah, sakamakonku shi ne tsarkakewa, ƙarshenta kuwa rai madawwami ne. 23 Gama sakamakon zunubi mutuwa ne, amma baiwar Allah ita ce rai madawwami a cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu.

Romawa 7

Ƙiyasi da Aure

1 Ya 'yan'uwa, ko ba ku sani ba, shari'a tana da iko da mutum, muddin yana raye ne kawai? Da waɗanda suke san shari'a fa nake. 2 Misali, mace mai aure, shari'a ta ɗaure ta ga mijinta muddin yana da rai. Amma in mijinta ya mutu, ta kuɓuta daga igiyar auren ke nan. 3 Don haka, muddin mijinta yana da rai, in ta auri wani, sai a kira ta mazinaciya. Amma in mijinta ya mutu, ta kuɓuta daga igiyar wannan aure, ko da ta auri wani kuwa, ita ba mazinaciya ba ce. 4 Haka kuma 'yan'uwana, kun zama matattu ga Shari'a, ta wurin jikin Almasihu, domin ku zama mallakar wani, wato, wanda aka tashe shi daga matattu, domin mu ba da amfani ga Allah. 5 Ai, dā sa'ad da muke zaman halin mutuntaka, muguwar sha'awa wadda faɗakarwar Shari'a ke sa a yi, ita take aiki a gaɓoɓinmu, tă wurin haddasa mutuwa. 6 Amma a yanzu mun 'yantu daga Shari'a, mun mutu daga abin da dā ya ɗaure mu ke nan, har muna iya bauta wa Allah da sabon rai da Ruhu, ba da tsofaffin rubutattun ka'idodi ba.

Damuwa wadda Zunubin da yake a cikinmu take Haddasawa

7 To, me kuma za mu ce? Shari'a zunubi ce? A'a, ko kusa! Amma kuwa duk da haka, da ba domin Shari'a ba, da ban san zunubi ba. Da ba domin Shari'a ta ce, “Kada ka yi ƙyashi” ba, da ban san ƙyashi ba. 8 Amma zunubi, da ya sami ƙofa ta hanyar umarni, sai ya haddasa ƙyashi iri iri a zuciyata. Gama da ba domin shari'a ba, da zunubi ba shi da wani tasiri. 9 Dā kam, sa'ad da ban san shari'a ba, ni rayayye ne, amma da na san umarnin, sai zunubi ya rayu, ni kuma sai na mutu. 10 Umarnin nan kuwa, wanda manufarsa a gare ni rai ne, sai ya jawo mini mutuwa. 11 Don kuwa zunubi ya sami ƙofa ta hanyar umarni, sai ya yaudare ni, ta wurinsa kuwa ya kashe ni. 12 Domin haka Shari'a da kanta mai tsarki ce, umarnin kuma mai tsarki ne, daidai ne, negari ne. 13 Wato, abar nan da take tagari ta jawo mini mutuwa ke nan? A'a, ko kusa! Zunubi ne ya jawo, domin ya bayyana kansa shi zunubi ne, gama ta wurin abar nan tagari ya jawo mini mutuwa, ta dalilin umarnin nan kuma, zunubi ya bayyana matuƙar muninsa. 14 Mun dai san Shari'a aba ce ta ruhu, ni kuwa mai halin mutuntaka ne, bautar zunubi kawai nake yi. 15 Ban ma fahimci abin da nake yi ba. Don ba abin da nake niyya yi, ba shi nake aikatawa ba, abin da nake ƙi, shi nake yi. 16 To, idan abin da ba na niyya, shi nake yi, na yarda ke nan Shari'a aba ce mai kyau. 17 Ashe kuwa, ba ni nake yinsa ba ke nan, zunubin da ya zaune mini ne. 18 Don na sani ba wani abin kirki da ya zaune mini, wato a jikina. Niyyar yin abin da yake daidai kam, ina da ita, sai dai ikon zartarwar ne babu. 19 Nagarin abin da nake niyya yi kuwa, ba shi nake yi ba, sai dai mugun abin da ba na niyya, shi nake aikatawa. 20 To, idan abin da ba na niyya shi nake yi, ashe kuwa, ba ni nake yinsa ba ke nan, zunubin da ya zaune mini ne. 21 Sai na ga, ashe, ya zama mini ka'ida, in na so yin abin da yake daidai, sai in ga mugunta a tare da ni. 22 Ni kam, a birnin zuciyata, na amince da shari'ar Allah. 23 Amma ina ganin wata ka'ida dabam a gaɓoɓina, wadda take yaƙi da ka'idar da hankalina ya ɗauka, har tana mai da ni bawan ƙa'idar nan ta zunubi wadda take zaune a gaɓoɓina. 24 Kaitona! Wa zai cece ni daga jikin nan, wanda yake kai ni ga mutuwa? 25 Godiya tā tabbata ga Allah, akwai, ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu! Ashe kuwa, ni a kaina, da hankalina, hakika Shari'ar Allah nake bauta wa, amma da jikina ka'idar zunubi nake bauta wa.

Romawa 8

Rayuwa a cikin Ruhu

1 Saboda haka a yanzu, ba sauran kayarwa ga waɗanda suke na Almasihu Yesu. 2 Ka'idar nan ta Ruhu mai ba da rai da yake ga Almasihu, Yesu ta 'yanta ni daga ka'idar zunubi da ta mutuwa. 3 Abin da ba shi yiwuwa Shari'a ta yi domin ta kasa saboda halin ɗan adam, Allah ya yi shi, wato ya ka da zunubi a cikin jiki, da ya aiko da Ɗansa da kamannin jikin nan namu mai zunubi, domin kawar da zunubi. 4 Wannan kuwa domin a cika hakkokin Shari'a ne a gare mu, mu da ba zaman halin mutuntaka muke yi ba, sai dai na Ruhu. 5 Masu zaman halin mutuntaka, ai, ƙwallafa ransu ga al'amuran halin mutuntaka suke yi, masu zaman Ruhu kuwa ga al'amuran Ruhu. 6 Ƙwallafa rai ga al'amuran halin mutuntaka ƙarshensa mutuwa ne, ƙwallafa rai ga ala'muran Ruhu kuwa rai ne da salama. 7 Don ƙwallafa rai ga al'amuran halin mutuntake gāba ne da Allah, gama ba ya bin Shari'ar Allah, ba kuwa zai iya ba. 8 Masu zaman halin mutuntaka, ba dama su faranta wa Allah rai. 9 Amma ku kam, ba masu zaman halin mutuntaka ba ne, masu zaman Ruhu ne, in dai har Ruhun Allah yana zauna a zuciyarku. Duk wanda ba shi da Ruhun Almasihu kuwa, ba na Almasihu ba ne. 10 In kuwa Almasihu yana a zuciyarku, ba ruwan jikinku da zunubi ke nan, Ruhu kuwa rai ne a gare ku saboda kun sami adalcin Allah. 11 In kuwa Ruhun wannan da ya ta da Yesu daga matattu yana zaune a zuciyarku, to, shi da ya ta da Almasihu Yesu daga matattu zai kuma raya jikin nan naku mai mutuwa, ta wurin Ruhunsa da yake a zaune a zuciyarku. 12 Domin haka, 'yan'uwa, kun ga halin mutuntaka ba shi da wani hakki a kanmu har da za mu yi zamansa. 13 In kuna zaman halin mutuntaka, za ku mutu ke nan, amma in da ikon Ruhu kuka kashe ayyukan nan na halin mutuntaka, sai ku rayu. 14 Duk waɗanda Ruhun Allah yake bishe su, su ne 'ya'yan Allah. 15 Ai, ruhun da kuka samu ba na bauta ba ne, har da za ku koma zaman tsoro. A'a, na zaman 'ya'ya ne, har muna kira, “Ya Abba! Uba!” 16 Ruhu da Kansa ma, tare da namu ruhu suna yin shaida, cewa mu 'ya'yan Allah ne. 17 In kuwa 'ya'ya muke, ashe, magāda ne kuma, magādan Allah, abokan gādo kuma da Almasihu, in dai har muna shan wuya tare da shi, a kuwa ɗaukaka mu tare da shi. 18 Ai, a ganina, wuyar da muke sha a wannan zamani, ba ta isa a kwatanta ta da ɗaukakar da za a bayyana mana ba. 19 Ga shi, duk halitta tana marmari, tana ɗokin ganin bayyanar 'ya'yan Allah. 20 An sarayar da halitta ta zama banza, ba da nufinta ba, amma da nufin wanda ya sarayar da ita. Duk da haka, akwai sa zuciya, 21 gama za a 'yantar da halitta da kanta ma, daga bautar ruɓewa, domin ta sami 'yancin nan, na ɗaukaka na 'ya'yan Allah. 22 Mun dai san dukan halitta tana nishi, na shan azaba kuma irin ta mai naƙuda, har ya zuwa yanzu. 23 Banda haka ma, har mu kanmu da muka riga muka sami Ruhu Mai Tsarki, wanda yake shi ne nunan fari, a cikin abubuwan da za mu samu, muna nishi a ranmu, muna ɗokin cikar zamanmu na 'ya'yan Allah, wato, fansar jikin nan namu ke nan. 24 Sa'ad da aka cece mu ne muka yi wannan sa zuciya. Amma kuwa, ai, sa zuciya ga abin da aka samu, ba sa zuciya ba ce. Wa yake sa zuciya ga abin da ya samu? 25 In kuwa muna sa zuciya ga abin da ba mu samu ba, da jimiri mukan yi sauraronsa. 26 Haka kuma Ruhu yake yi mana taimako a kan gajiyawarmu, domin ba mu ma san abin da ya kamata mu roƙa ba, amma Ruhu da kansa yana yi mana roƙo da nishe-nishen da ba su hurtuwa. 27 Amma shi mai fayyace zukatanmu ya san abin da Ruhu yake niyya, domin bisa ga nufin Allah ne Ruhu yake yi wa tsarkaka roƙo.

Mun Zarce A ce da Mu Masu Nasara ne

28 Mun kuma sani al'amura duka suna aikatawa tare, zuwa alheri ga waɗanda suke ƙaunar Allah, wato, waɗanda suke kirayayyu bisa ga nufinsa. 29 Waɗanda Allah ya riga ya zaɓa tun tuni, su ne ya ƙaddara su ɗauki kamannin Ɗansa, domin shi Ɗan yă zama na farko a cikin 'yan'uwa masu yawa. 30 Waɗanda ya ƙaddarar nan kuwa, su ne ya kira. Waɗanda ya kira kuwa, su ne ya kuɓutar. Waɗanda ya kuɓutar ɗin kuwa, su ne ya ɗaukaka. 31 To, me kuma za mu ce a game da haka? Da yake Allah yana goyon bayanmu, wa kuwa zai iya gāba da mu? 32 Shi da bai hana Ɗansa ba, sai ma ya ba da shi saboda mu duka, ashe, ba zai ba mu kome tare da shi hannu sake ba? 33 Wa zai ɗora wa zaɓaɓɓun Allah laifi? Allah ne yake kuɓutar da su! 34 Wa zai hukunta su? Almasihu Yesu wanda ya mutu, ka kuwa a ce wanda ya tashi daga matattu, shi ne wanda yake zaune dama ga Allah, shi ne kuwa wanda yake roƙo saboda mu! 35 Wa zai iya raba mu da ƙaunar da Almasihu yake yi mana? Ƙunci ne? ko masifa? ko tsanani? ko yunwa? ko huntanci? ko hatsari? ko takobi? 36 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Saboda kai ne ake kashe mu yini zubur, An lasafta mu kamar tumakin yanka.” 37 Duk da haka kuwa a cikin wannan hali duka, har mun zarce ma a ce mana masu nasara, ta wurin wannan da ya ƙaunace mu. 38 Domin na tabbata, ko mutuwa ce, ko rai, ko mala'iku, ko manyan mala'iku, ko al'amuran yanzu, ko al'amura masu zuwa, ko masu iko, 39 ko tsawo, ko zurfi, kai, ko kowace irin halitta ma, ba za su iya raba mu da ƙaunar da Allah yake yi mana ta wurin Almasihu Yesu Ubangijinmu ba.

Romawa 9

Allah ya Zaɓi Isra'ila

1 Gaskiya nake faɗa, ni na Almasihu ne, ba ƙarya nake yi ba. Lamirina, ta wurin Ruhu Mai Tsarki, yana ba da shaida, 2 cewa ina da matuƙar baƙin ciki da kuma takaici marar yankewa a zuciyata. 3 Da ma a la'ance ni, a raba ni da Almasihu saboda dangina, 'yan'uwana na kabila! 4 Su ne Isra'ilawa. Da zama 'ya'yan Allah, da ganin ɗaukakarsa, da alkawaran nan, da baiwar Shari'a, da ibada, da kuma sauran alkawarai, duk nasu ne. 5 Kakannin kakannin nan kuma nasu ne, Almasihu kuma, ta wurin zamansa mutum, na kabilarsu ne. Yabo yā tabbata ga Allah har abada, shi da yake bisa kome. Amin. 6 Ba cewa Maganar Allah ta fādi ba, don ba duk zuriyar Isra'ila ne suke Isra'ilawa na gaske ba. 7 Ba kuwa duk su ne 'ya'yan Ibrahim ba, wai don suna zuriyarsa. Amma an ce, “Ta wurin Ishaku ne za a lasafta zuriyarka.” 8 Wato, zaman zuriyar Ibrahim, ba shi ne zama 'ya'yan Allah ba, a'a, zuriya ta alkawarin nan su ne ake lasaftawa zuriyar Ibrahim. 9 Alkawarin kuwa shi ne, “Baɗi war haka zan dawo, Saratu kuma za ta haifi ɗa.” 10 Banda haka ma, sa'ad da Rifkatu ta yi ciki da mutumin nan ɗaya, wato, kakanmu Ishaku, 11 tun ba ta haifi 'ya'yan ba, balle su yi wani abu mai kyau ko marar kyau�don nufin Allah bisa ga zaɓensa ya tabbata, ba ga aikin lada ba, sai dai ga kiransa� 12 aka ce mata, “Wan zai bauta wa ƙanen.” 13 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yakubu na so, Isuwa na ƙi.” 14 To, me kuma za mu ce? Allah ya yi rashin adalci ke nan? A'a, ko kusa! 15 Domin ya ce wa Musa, “Wanda zan yi wa jinƙai, zan yi masa jinƙan, wanda zan nuna wa tausayi kuwa, zan nuna masa tausayin.” 16 Ashe kuwa, abin bai danganta ga nufin mutum ko himma tasa ba, sai dai ga jinƙan Allah. 17 Don a Nassi an ce da Fir'auna, “Na girmama ka ne musamman, domin in nuna ikona a kanka, domin kuna a sanar da sunana a duniya duka.” 18 Wato, yana nuna jinƙai ga wanda ya so, yana kuma taurara zuciyar wanda ya so. 19 Kila ka ce mini, “To, don me har yanzu yake ganin laifi? Wa zai iya tsayayya da nufinsa?” 20 Ya kai ɗan adam! Wane ne kai har da za ka yi jayayya da Allah? Ashe, abin da aka gina zai iya ce wa magininsa, “Don me ka yi ni haka?” 21 Ashe, maginin tukwane ba ya iko da yumɓu, ya gina wata domin aiki mai martaba, wata kuma don kasasshen aiki, duk daga curi ɗaya? 22 To, ƙaƙa fa? Allah da yake yana so ya nuna fushinsa, ya kuma bayyana ikonsa, sai ya haƙura matuƙar haƙuri da waɗanda suka cancanci fushinsa, suka kuma isa hallaka, 23 Nufinsa ne ya bayyana yalwar ɗaukakarsa ga waɗanda ya yi wa jinƙai, wato, waɗanda dā ma ya yi wa tanadin ɗaukaka? 24 Wato, mu ke nan da ya kira, ba kuwa daga cikin Yahudawa kaɗai ba, har ma daga cikin al'ummai. 25 Kamar dai yadda ya faɗa a Littafin Yusha'u cewa, “Waɗanda dā ba jama'ata ba, Zan ce da su ‘jama'ata,’ Wadda dā ba abar ƙaunata ba kuma, Zan ce da ita ‘abar ƙaunata.’ ” 26 “A daidai wurin da aka ce da su, ‘Ku ba jama'ata ba ne,’ A nan ne za a kira su ‘'ya'yan Allah Rayayye,’ ” 27 A game da Isra'ila Ishaya ma ya ɗaga murya ya ce, “Ko da yake yawan Isra'ilawa ya kai kamar yashin teku, duk da haka kaɗan ne za su sami ceto. 28 Domin Ubangiji zai zartar da hukuncinsa a duniya, ya gama shi tashi ɗaya.” 29 Kamar yadda Ishaya ya yi faɗa cewa, “Da ba domin Ubangijin Runduna ya bar mana zuriya ba, Da mun zama kamar Saduma, An kuma maishe mu kamar Gwamrata.”

Isra'ila da Bishara

30 To, me kuma za mu ce? Ga shi, al'ummai da ba su nace da neman adalcin Allah ba, sun samu, wato, sun sami adalcin da yake daga bangaskiya. 31 Isra'ila kuwa da suka nace da neman hanyar adalcin Allah, suka kasa samunta. 32 Me ya sa? Don ba su neme ta ta hanyar bangaskiya ba, sai dai ta hanyar aikata aikin lada. Sai suka yi tuntuɓe da dutsen tuntuɓe, 33 kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ga shi, na sa dutsen sa tuntuɓe a Sihiyona, Da fā na sa faɗuwa. Duk mai gaskatawa da shi, ba zai kunyata ba.”

Romawa 10

1 Ya 'yan'uwa, muradin zuciyata da kuma roƙona ga Allah saboda su, shi ne su sami ceto. 2 Na dai shaida su a kan suna da himmar bauta wa Allah, amma ba da cikakken sani ba. 3 Don saboda rashin fahimtar hanyar samun adalci, wadda Allah ya tanadar, da kuma neman kafa tāsu hanya, sai suka ƙi bin ita wannan hanya ta samun adalci wadda Allah ya tanadar. 4 Domin Almasihu shi ne cikamakin Shari'a, domin kowane mai ba da gaskiya ya sami adalcin Allah. 5 Gama Musa ya rubuta zancen adalcin da yake samuwa ta wurin bin Shari'a, cewa mai iya aikata ta zai rayu ta wurinta. 6 Amma, a game da samun adalcin Allah wanda yake ta wurin bangaskiya ya ce, Kada ka ce a ranka, “Wa zai hau zuwa sama?” Wato, yă sauko da Almasihu. 7 Ko kuwa, “Wa zai gangara can ƙasa?” Wato yă ta da Almasihu daga matattu. 8 Amma me Nassi ya ce? “Maganar, ai, tana kusa da kai, tana ma a bakinka, da kuma a cikin zuciyarka.” Ita ce maganar bangaskiya da muke wa'azi. 9 Wato, in kai da bakinka ka bayyana yarda, cewa Yesu Ubangiji ne, ka kuma gaskata a zuciyarka Allah ya tashe shi daga matattu, za ka sami ceto. 10 Domin da zuci mutum yake gaskatawa yă sami adalcin Allah, da baki yake shaidawa ya sami ceto. 11 Gama Nassi ya ce, “Duk mai gaskatawa da shi ba zai kunyata ba.” 12 Ai, ba wani bambanci a tsakanin Bayahude da Ba'al'umme. Ubangijin nan ɗaya shi ne Ubangijin kowa, mayalwacin baiwa ne kuma ga dukkan masu addu'a a gare shi. 13 “Duk wanda kuwa ya yi addu'a da sunan Ubangiji zai sami ceto.” 14 Amma ta ƙaƙa za su yi addu'a ga wanda ba su gaskata da shi ba? Ta ƙaƙa kuma za su gaskata da wanda ba su taɓa ji ba? Ta ƙaƙa kuma za su ji, in ba mai wa'azi? 15 Ta ƙaƙa kuma za su yi wa'azi, in ba aikarsu aka yi ba? Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Yaya zai kasance a isowar masu kawo bishara!” 16 Amma ba duka ne suka yi na'am da bisharar ba. Ishaya ma ya ce, “Ya Ubangiji, wa ya gaskata jawabinmu?” 17 Ashe, bangaskiya ta wurin jawabin da ake ji take samuwa, jawabin da ake ji kuma ta Maganar Almasihu yake. 18 Amma ina tambaya. Ba su ji jawabin ba ne? Hakika sun ji. “Muryarsu ta gama duniya duka, Maganarsu kuma ta kai har bangon duniya.” 19 Har wa yau, ina tambaya. Shin, Isra'ila kam, ba su fahimta ba ne? Da farko dai Musa ya ce, “Zan sa ku kishin waɗanda ba al'umma ba ne, Zan kuma sa ku fushi da wata al'ummar marar fahimta.” 20 Ishayan kuma ya fito gabagaɗi ƙwarai ya ce, “Waɗanda ba su neme ni ba, su suka same ni. Na bayyana kuma ga waɗanda ba su taɓa neman sanina ba.” 21 Amma a game da isra'ila, sai ya ce, “Yini zubur ina miƙa hannuwana ga jama'a marasa biyayya, masu tsayayya.”

Romawa 11

Sauran Isra'ila

1 To, ina tambaya. Wato, Allah ya juya wa jama'arsa baya ke nan? A'a, ko kusa! Ai, ni ma da kaina Ba'isra'ile ne, zuriyar Ibrahim, na kabilar Biliyaminu. 2 Ko kaɗan, Allah bai juya wa jama'arsa da ya zaɓa tun dā baya ba. Ko ba ku san abin da Nassi ya faɗa ba ne, a game da Iliya? Yadda ya kai kuka ga Allah, a kan isra'ila, ya ce, 3 “Ya Ubangiji, sun karkashe annabawanka, sun rurrushe bagadanka na hadaya. Ni kaɗai ne na ragu, suna kuwa neman raina.” 4 Amma me Allah ya amsa masa? Cewa ya yi, “Na keɓe wa kaina mutum dubu bakwai waɗanda ba su taɓa durƙusa wa Ba'al ba.” 5 Haka ma a wannan zamani akwai ragowa, waɗanda aka zaɓa saboda alherinsa. 6 In kuwa na alheri ne, ba sauran cewa ya dogara ga aikin lada ke nan. In ba haka ba, ashe, alheri ba alheri ba ne kuma. 7 To, yaya ke nan? Ashe, abin da Isra'ila take nema, ba su samu ba ke nan, amma zaɓaɓɓun nan sun samu, sauran kuwa sun taurare. 8 Yadda yake a rubuce cewa, “Allah ya toshe musu basira, Ya ba su ido, ba na gani ba, Da kuma kunne, ba na ji ba, Har ya zuwa yau.” 9 Dawuda kuma ya ce, “Dā ma shagalinsu ya zama musu tarko, abin shammatarsu, Sanadin faɗuwarsu kuma, har aniyarsu ta koma kansu. 10 Idonsu kuma yă shiga duhu, har su kasa gani, Ka kuma tanƙwara bayansu har abada.”

Ceton Al'ummai

11 Ina kuma tambaya. Faɗuwar da suka yi, sun faɗi ba tashi ke nan? A'a, ko kusa! Sai ma faɗuwarsu ta zama sanadin ceto ga al'ummai, don a sa Isra'ila kishi. 12 To, in kuwa duniya ta arzuta da hasararsu, wa zai kimanta yawan albarka, in adadinsu masu ɗungumawa ga Allah ya cika? 13 Da ku al'ummai fa nake. Tun da yake ni manzo ne ga al'ummai, ina taƙama da aikina, 14 ko ta wane hali in sa kabilata kishin zuci, har in ceci waɗansunsu. 15 Domin in an sulhunta duniya ga Allah, saboda yar da su da aka yi, to, in an karɓe su fa, ba sai rai daga matattu ba? 16 In curin farko tsattsarka ne, haka sauran gurasar ma. In kuma saiwa tsattsarka ce, haka rassan ma. 17 Amma in an sassare waɗansu rassan zaitun na gida, kai kuma da kake zaitun na jeji aka ɗaura aure da kai a gurbinsu, kana kuma shan ni'imar saiwar zaitun ɗin nan tare da sauran rassan, 18 kada ka yi wa sauran rassan alwashi. In kuwa ka yi, ka tuna fa, ba kai kake ɗauke da saiwar ba, saiwar ce take ɗauke da kai. 19 Kila za ka ce, “Ai, an sare rassan nan ne, don a ɗaura aure da ni.” 20 Hakika haka ne, amma saboda rashin bangaskiyarsu ne aka sare su, kai kuwa saboda bangaskiyarka ne kake kafe. Kada fa ka nuna alfarma, sai dai ka ji tsoron Allah. 21 Da yake Allah bai bar rassan asalin ba, kai ma ba zai bar ka ba. 22 Dubi fa alherin Allah da kuma tsananinsa, wato, tsanani ga waɗanda suka fāɗi, alherinsa kuwa a gare ka, muddin ka ɗore a cikin alherin. In ba haka ba, kai ma sai a datse ka. 23 Ko su ma, in dai ba su nace wa rashin bangaskiyarsu ba, sai a ɗaura aure da su, domin Allah yana da ikon sāke mai da su. 24 Kai ma da aka saro daga zaitun ɗin da asalinsa yake na jeji, aka ɗaura aure da kai a jikin zaitun ɗin na gida, saɓanin yadda aka saba, balle waɗannan rassa na asali, da za a ɗaura aure da su a jikin zaitun ɗin nan nasu na asali?

Komar da Isra'ila ga Matsayinsa

25 'Yan'uwa, ga wata asirtacciyar gaskiya da nake so ku sani, domin kada ku zaci ku masu hikima ne, taurarewar nan�wadda ba mai tabbata ba ce�ta sami Isra'ilawa ne, har adadin al'ummai masu ɗungumawa zuwa ga Allah ya cika. 26 Ta haka nan ne Isra'ila duka za su sami ceto, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai Ceto zai zo daga Sihiyona, Zai kuma kawar da rashin bin Allah daga zuriyar Yakubu,” 27 “Cikar alkawarina a gare su ke nan, Sa'ad da na ɗauke musu zunubansu.” 28 A game da bishara kuma, maƙiyan Allah ne su, domin amfaninku ne kuwa. Amma a game da zaɓen Allah, su ƙaunatattunsa ne, albarkacin kakannin kakanninsu. 29 Domin baiwar Allah da kiransa ba sa tashi. 30 Kamar yadda kuka ƙi bin Allah a dā, amma a yanzu aka yi muku jinƙai saboda rashin biyayyarsu, 31 haka su ma da suke marasa biyayya a yanzu, yanzu a yi musu jinƙai kamar yadda aka yi muku. 32 Don Allah ya kulle kowa a cikin rashin biyayya, domin ya nuna jinƙai ga kowa. 33 Zurfin hikimar Allah da na saninsa da rashin iyaka suke! Hukunce-hukuncensa sun fi gaban bincikewa, hanyoyinsa kuma sun fi gaban bin diddigi! 34 “Wa ya taɓa sanin zuciyar Ubangiji? Ko kuwa wa ya taɓa ba shi wata shawara?” 35 “Wa kyauta ta shiga tsakaninsu da Allah, ya fara bayarwa, Har da za a sāka masa?” 36 Ai, daga gare shi ne, ta wurinsa kuma, dukkan abubuwa suke, shi ne kuma makomarsu. Ɗaukaka tă tabbata a gare shi har abada. Amin.

Romawa 12

Hadaya Mai Rai

1 Don haka ina roƙonku 'yan'uwa, saboda yawan jinƙai na Allah, ku miƙa jikinku hadaya rayayyiya, tsattsarka, abar karɓa ga Allah. Domin wannan ita ce ibadarku ta ainihi. 2 Kada ku biye wa zamanin nan, amma ku bar halinku ya sāke, ta wurin sabunta hankalinku ɗungum, don ku tabbatar da abin da Allah yake so, wato nufinsa kyakkyawa, abin karɓa, cikakke kuma. 3 Albarkacin alherin da aka yi mini ina yi wa kowannenku gargaɗi kada ya ɗauki kansa fiye da yadda ya kamata, sai dai ya san kansa, gwargwadon bangaskiyar da Allah ya ba shi. 4 Wato kamar yadda gaɓoɓi da yawa suke harhaɗe a jiki ɗaya, gaɓoɓin nan kuwa ba aiki iri ɗaya suke yi ba, 5 haka mu ma, ko da yake muna da yawa, jiki ɗaya muke haɗe da Almasihu, kowannenmu kuma gaɓar ɗan'uwansa ne. 6 Da yake muna da baiwa iri iri, gwargwadon alherin da aka yi mana, to, sai mu yi amfani da su. In ta annabci ce, sai mu yi amfani da ita gwargwadon bangaskiyarmu, 7 in ta hidima ce, wajen hidimarmu, mai koyar da Maganar Allah kuwa, wajen koyarwarsa, 8 mai ƙarfafa zuciya kuwa, wajen ƙarfafawarsa, mai yin gudunmawa kuwa, ya bayar hannu sake, shugaba ya yi shugabancinsa da himma, mai yin aikin tausayi, ya yi shi da fara'a.

Gargaɗi a kan Zaman Kirista

9 Ƙauna ta kasance sahihiya. Ku yi ƙyamar abin da yake mugu, ku lazamci abin da yake nagari. 10 A game da ƙaunar 'yan'uwa kuwa, ku ƙaunaci juna gaya. A wajen ba da girma, kowa ya riga ba ɗan'uwansa. 11 Kada ku sassauta a wajen himma, ku himmantu a ruhu, kuna bauta wa Ubangiji. 12 Sa zuciyar nan taku ta sa ku farin ciki, ku jure wa wahala, ku nace wa yin addu'a. 13 Ku agaji tsarkaka, ku himmantu ga yi wa baƙi alheri. 14 Ku sa wa masu tsananta muku albarka. Ku sa musu albarka, kada ku la'ance su. 15 Ku taya masu farin ciki farin ciki, masu kuka kuwa ku taya su kuka. 16 Ku yi zaman lafiya da juna. Kada ku nuna alfarma, sai dai ku miƙa kanku ga aikata ayyukan tawali'u. Kada ku aza kanku masu hikima ne. 17 Kada ku rama muguntar kowa da mugunta. Ku yi ta lura al'amuranku su zama daidai a gaban kowa. 18 In mai yiwuwa ne, a gare ku, ku yi zaman lafiya da kowa. 19 Ya ku ƙaunatattuna, kada ku ku yi ramuwa, sai dai ku bar wa fushin Allah. Domin a rubuce yake cewa, “Ramuwa tawa ce, ni zan saka, in ji Ubangiji.” 20 Har ma “In maƙiyinka yana jin yunwa, sai ka ci da shi. In yana jin ƙishirwa, ka shayar da shi. Don ta haka ne za ka tula garwashin wuta a kansa.” 21 Kada mugunta ta rinjaye ku, amma ku rinjayi mugunta da nagarta.

Romawa 13

1 Bari kowa ya yi biyayya ga mahukunta. Gama ba wani iko sai da yardar Allah. Mahukuntan da suke nan kuwa naɗin Allah ne. 2 Saboda haka duk wanda ya yi wa mahukunta tsayayya, ya yi wa umarnin Allah ke nan, masu yin tsayayyar nan kuwa za a yi musu hukunci. 3 Don kuwa mahukunta ba abin tsoro ba ne ga masu aiki nagari, sai dai ga masu mugun aiki. Kana so kada ka ji tsoron mahukunci? To, sai ka yi nagarta, sai kuwa ya yaba maka. 4 Domin shi bawan Allah ne, don kyautata zamanka. Amma in kai mai mugun aiki ne, to, ka ji tsoro, don ba a banza yake riƙe da takobi ba. Ai, shi bawa ne na Allah, mai sāka wa mugu da fushi. 5 Saboda haka wajibi ne ka yi biyayya, ba domin gudun fushi kaɗai ba, amma domin lamiri kuma. 6 Shi ne ma ya sa kuke biyan haraji, don su mahukunta ma'aikata ne na Allah, suna kuma yin wannan aiki a koyaushe. 7 Ku ba kowa hakkinsa, masu haraji, harajinsu, masu kuɗin fito, kuɗinsu na fito, waɗanda suka cancanci ladabi, ladabi, waɗanda suka cancanci girmamawa, girmamawa. 8 Kada hakkin kowa ya zauna a kanku, sai dai na ƙaunar juna, don mai ƙaunar maƙwabcinsa ya cika Shari'a ke nan. 9 Umarnan nan cewa, “Kada ka yi zina, kada ka yi kisankai, kada ka yi sata, kada ka yi ƙyashi,” da dai duk sauran umarnai an ƙunshe su ne a wannan kalma cewa, “Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.” 10 Ƙauna ba ta cutar maƙwabci saboda haka ƙauna cika Shari'a ce. 11 Ga shi kuma, kun dai san irin zamanin da muke a ciki, ai, lokaci ya riga ya yi da za ku farka daga barci. Gama yanzu mun fi kusa da ceton nan namu a kan sa'ad da muka fara ba da gaskiya. 12 Dare fa ya ƙure, gari ya kusa wayewa. Sai mu watsar da ayyukan duhu, mu yi ɗamara da kayan ɗamara na haske. 13 Mu tafiyar da al'amuranmu yadda ya dace a yi da rana, ba a cikin shashanci da buguwa, ko fasikanci da fajirci, ko jayayya da kishi ba. 14 Amma ku ɗauki halin Ubangiji Yesu Almasihu, kada kuwa ku tanadi halin mutuntaka, don biye wa muguwar sha'awarsa.

Romawa 14

Kada ka Ɗora wa Ɗan'uwanka Laifi

1 A game da wanda bangaskiya tasa rarrauna ce kuwa, ku karɓe shi hannu biyu biyu, amma ba a game da sukan ra'ayinsa ba. 2 Ga wani, bangaskiyarsa ta yardar masa cin kome, wanda bangaskiyarsa rarrauna ce kuwa, sai kayan gona kawai yake ci. 3 To, kada fa mai cin kome ɗin nan ya raina wanda ya ƙi ci, kada kuma wanda ya ƙi cin nan, ya ga laifin mai ci, domin Allah ya riga ya karɓe shi hannu biyu biyu. 4 Kai wane ne har da za ka ga laifin baran wani? Ko dai ya tsaya, ko ya faɗi, ai, ruwan maigidansa ne. Za a ma tsai da shi, domin Ubangiji yana da ikon tsai da shi. 5 Wani yakan ɗaukaka wata rana fiye da sauran ranaku, wani kuwa duk ɗaya ne a wurinsa. Kowa dai yă zauna a cikin haƙƙaƙewa, a kan ra'ayinsa. 6 Mai kiyaye wata rana musamman, yana kiyaye ta ne saboda Ubangiji. Mai cin nan kuma, yana ci ne saboda Ubangiji, da yake yana gode wa Allah. Marar cin nan kuma yana ƙin ci ne saboda Ubangiji, shi ma kuwa yana gode wa Allah. 7 Duk a cikinmu ba wanda ya isar wa kansa a sha'anin rayuwarsa ko mutuwarsa. 8 Ko muna a raye, zaman Ubangiji muke yi, ko mun mutu ma, zaman Ubangiji muke yi. Ashe, ko muna a raye, ko kuma a mace, na Ubangiji ne mu. 9 Saboda haka ne musamman Almasihu ya mutu, ya sāke rayuwa, wato, domin ya zama shi ne Ubangijin matattu da na rayayyu duka. 10 To, kai, me ya sa kake ganin laifin ɗan'uwanka? Kai kuma, me ya sa kake raina ɗan'uwanka? Ai, dukkanmu za mu tsaya a gaban kursiyin shari'ar Allah. 11 Domin a rubuce yake, “Na rantse da zatina, in ji Ubangiji, kowace gwiwa sai ta rusuna mini, Kowane harshe kuwa sai ya yabi Allah.” 12 Don haka kowannenmu zai faɗi abin da shi da kansa ya yi, a gaban Allah.

Kada ka Sa Ɗan'uwanka Yin Tuntuɓe

13 Saboda haka kada mu ƙara ganin laifin juna, gara mu ƙudura, don kada kowannenmu ya zama sanadin tuntuɓe ko faɗuwa ga ɗan'uwansa, 14 Na sani, na kuma tabbata, a tsakani na da Ubangiji Yesu, ba abin da yake marar tsarki ga asalinsa, sai dai ga wanda ya ɗauke shi marar tsarki ne yake marar tsarki. 15 In kuwa cimarka tana cutar ɗan'uwanka, ashe, ba zaman ƙauna kake yi ba. Kada fa cimarka ta hallaka wannan da Almasihu ya mutu dominsa. 16 Saboda haka kada abin da ka ɗauka kyakkyawa ya zama abin zargi ga waɗansu. 17 Ai, Mulkin Allah ba ga al'amarin ci da sha yake ba, sai dai ga adalci, da salama da farin ciki ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 18 Wanda duk yake bauta wa Almasihu ta haka, abin harɓa ne ga Allah, yardajje na kuma ga mutane. 19 Don haka sai mu himmantu ga yin abubuwan da suke kawo salama, suke kuma kawo inganta juna. 20 Kada ka rushe aikin Allah saboda abinci kawai. Hakika dukan abu mai tsarki ne, amma mugun abu ne mutum ya zama sanadin tuntuɓe ga wani, ta wurin abin da yake ci. 21 Ya kyauta kada ma ka ci nama, ko ka sha ruwan inabi, ko kuwa ka yi kowane irin abu, wanda zai sa ɗan'uwanku yin tuntuɓe. 22 Kana da bangaskiya? To, ka riƙe ta tsakaninka da Allah. Albarka tā tabbata ga wanda zuciyarsa ba ta ba shi laifi ba, a game da abin da hankalinsa ya ga daidai ne. 23 Wanda yake shakka, amma kuwa ya ci, ya sani ya yi laifi ke nan, domin ba da bangaskiya ya ci ba. Duk abin da ba na bangaskiya ba ne, zunubi ne.

Romawa 15

Faranta wa Ɗan'uwanka Rai, ba kanka Ba

1 To, mu da muke ƙarfafa, ya kamata mu ɗauki nauyin raunana, kada mu yi sonkai. 2 Kowannenmu yă faranta wa maƙwabcinsa rai, don kyautata zamansa da kuma inganta shi. 3 Gama ko Almasihu ma bai yi sonkai ba, amma kamar yadda yake a rubuce cewa, “Zagin da waɗansu suka yi maka duk yā komo kaina.” 4 Ai, duk abin da aka rubuta tun dā, an rubuta shi ne domin a koya mana, domin mu ɗore a cikin sa zuciyar nan tamu ta wurin haƙuri da ta'aziyyar da Littattafai suke yi mana. 5 Allah mai ba da haƙuri da ta'aziyya, yă ba ku zaman lafiya da juna bisa halin Almasihu Yesu, 6 domin ku ɗaukaka Allah, Ubangijinmu Yesu Almasihu, da kuma Ubansa, nufinku ɗaya, bakinku ɗaya.

Bishara ga Al'ummai

7 Saboda haka ku karɓi juna da hannu biyu biyu, kamar yadda Almasihu ya karɓe ku hannu biyu biyu, domin a ɗaukaka Allah. 8 Ina dai gaya muku, Almasihu ya zama bara ga Isra'ila, domin nuna gaskiyar Allah, domin kuma tabbatar da alkawaran nan, da Allah ya yi wa kakannin kakanninmu, 9 al'ummai kuma su ɗaukaka Allah saboda jinƙansa. Yadda yake a rubuce, “Domin haka zan yabe ka a cikin al'ummai, In kuma yi waƙar yabon sunanka.” 10 Har wa yau kuma an ce, “Ya ku al'ummai, ku yi ta farin ciki tare da jama'arsa.” 11 Da kuma, “Ku yabi Ubangiji, ya ku al'ummai duka, Dukkan kabilai kuma su yabe shi.” 12 Ishaya kuma ya ce, “Tsatson Yesse zai bayyana, Wanda zai tashi ya mallaki al'ummai, A gare shi ne al'ummai za su sa zuciya.” 13 Allah mai kawo sa zuciya, yă cika ku da matuƙar farin ciki da salama saboda bangaskiyarku, domin ku yi matuƙar sa zuciya ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki. 14 Ya 'yan'uwana, ni ma da kaina na amince da ku, cewa ku da kanku masu nagarta ne ƙwarai da gaske, masu cikakken sani, kun kuma isa ku gargaɗi juna. 15 Duk da haka, a kan waɗansu batatuwan da na rubuto muku, na ƙara ƙarfafawa ƙwarai, domin tuni, saboda alherin da Allah ya yi mini 16 da ya sa ni bawan Almasihu Yesu ga al'ummai, ina hidimar bisharar Allah, domin al'ummai su zama hadaya mai karɓuwa a gare shi, tsattsarka ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 17 Ashe kuwa, ina da dalilin yin alfarma da Almasihu Yesu a game da al'amarin Allah. 18 Ba zan kuskura in faɗi kome ba, sai abin da Almasihu ya aikata ta wurina, a wajen sa al'ummai biyayya ta wurin maganata da aikina, 19 ta wurin ikon mu'ujizai, da abubuwan al'ajabai, da kuma ta wurin ikon Ruhun, har dai daga Urushalima da kewayenta, har zuwa Ilirikun, na yi bisharar Almasihu a ko'ina. 20 Har ya zama mini abin buri in sanar da bishara, a inda ba a taɓa sanar da sunan Almasihu ba, don kada in ɗora ginina a kan harsashin wani, 21 sai dai kamar yadda yake a rubuce, “Waɗanda ba a taɓa faɗa wa labarinsa ba, za su gane, Waɗanda ba su taɓa jin labarinsa ba ma, za su fahimta.”

Bulus ya Shirya ya Ziyarci Roma

22 Shi ya sa sau da yawa ban sami sukunin zuwa wurinku ba. 23 A yanzu kuwa tun da yake ba sauran wani wuri da ya rage mini a lardin nan, shekaru da yawa kuma ina ɗokin zuwa wurinku, 24 ina sa zuciya in gan ku, in zan wuce zuwa ƙasar Asbaniya, har ma ku raka ni zuwa can, bayan da na ɗan ɗebe kewa da ganinku. 25 Amma a yanzu kam, za ni Urushalima, don in kai wa tsarkaka gudunmawa. 26 Mutanen Makidoniya da na Akaya, sun ji daɗin yin gudunmawar daidai gwargwado ga matalauta, a cikin tsarkakan da suke a Urushalima. 27 Sun kuwa ji daɗin yin haka, domin hakika kamar bashi ne a kansu. Domin tun da yake al'ummai sun yi tarayya da su a kan ni'imarsu ta ruhu, ashe kuwa, ya kamata su ma su taimake su da ni'imarsu ta duniya. 28 In kuwa na gama wannan, na kuma danƙa musu wannan taimako lafiya, sai in bi ta kanku zuwa ƙasar Asbaniya. 29 Na kuma sani, in na zo wurinku, zan zo ne a cikin falalar albarkar Almasihu 30 Amma ina roƙonku 'yan'uwa, saboda Ubangijinmu Yesu Almasihu, da kuma ƙaunar nan da Ruhu yake bayarwa, ku taya ni yin addu'a da naciya ga Allah saboda kaina, 31 domin in tsira daga maƙiyan bangaskiya a Yahudiya, don kuma gudunmawar da nake kaiwa Urushalima, ta zama abar karɓa ga tsarkaka, 32 har in Allah ya yarda in iso wurinku da farin ciki, mu wartsake tare. 33 Allah mai ba da salama ya kasance tare da ku duka. Amin.

Romawa 16

Gaisuwa

1 Ga 'yar'uwarmu Fibi ina sada ku da ita, ita ma kuwa mai hidimar ikilisiya ce a Kankiriya. 2 Ku karɓe ta da hannu biyu biyu saboda Ubangiji, ta halin da ya dace da tsarkaka. Ku kuma taimake ta da duk irin abin da ta nemi taimako a gare ku, domin ita ma tā taimaki mutane da yawa, har ma da ni kaina. 3 Ku gai da Bilkisu da Akila, abokan aikina a cikin Almasihu Yesu, 4 waɗanda suka kasai da ransu saboda ni, ba kuwa ni kaɗai nake gode musu ba, har ma da dukkan ikilisiyoyin al'ummai. 5 Ku kuma gai da ikilisiyar da take taruwa a gidansu. Ku gai da ƙaunataccena Abainitas, wanda yake shi ne ya fara bin Almasihu a ƙasar Asiya. 6 Ku gai da Maryamu, wadda ta yi muku aiki ƙwarai da gaske. 7 Ku gai da Andaranikas da Yuniyas, 'yan'uwana, abokan ɗaurina, waɗanda suke shahararru a cikin manzanni, har ma sun riga ni bin Almasihu. 8 Ku gai da Amfiliyas, ƙaunataccena a cikin Ubangiji. 9 Ku gai da Urbanas abokin aikinmu a cikin Almasihu, da kuma ƙaunataccena Istakis. 10 Ku kuma gai da Abalis, amintaccen nan a cikin Almasihu. Ku gai da jama'ar Aristobulus. 11 Ku gai da 'dan'uwana Hirudiyan. Ku gai da waɗanda suke na Ubangiji a cikin jama'ar Narkisas. 12 Ku gai da Tarafina da Tarafusa, masu Ubangiji. Ku gai da Barsisa, ƙaunatacciya, wadda ta yi aikin Ubangiji ƙwarai da gaske. 13 Ku gai da Rufas, fitaccen mai bin Ubangiji, da kuma mahaifiyarsa, tawa kuma. 14 Ku gai da Asinkiritas, da Filiguna, da Hamisa, da Baturobas, da Hamasa, da kuma 'yan'uwan da suke tare da su. 15 Ku gai da Filulugusa, da Yuliya, da Niriyas, da 'yar'uwarsa, da Ulumfas da kuma dukan tsarkakan da suke tare da su. 16 Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba. Dukan ikilisiyoyin Almasihu suna gaishe ku. 17 Ina roƙonku, 'yan'uwa, ku yi hankali fa da masu raba tsakani, saɓanin koyarwar da kuka koya, suna sa tuntuɓe. Ku yi nesa da su. 18 Ai, irin waɗannan mutane ba sa bauta wa Ubangijinmu Almasihu, sai dai cikinsu. Ta romon kunne da daɗin baki suke yaudarar masu sauƙin kai. 19 Amma ku kam, ai, kowa ya san biyayyarku, shi ya sa nake farin ciki da ku. Sai dai ina so ku gwanance da abin da yake nagari, amma ya zama ba ruwanku da mugunta. 20 Allah mai ba da salama kuwa, zai sa ku tattake Shaiɗan da hanzari. Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku. 21 Timoti, abokin aikina, yana gaishe ku, haka kuma Lukiyas da Yason da kuma Susibataras, 'yan'uwana. 22 Ni Tartiyas, mai rubuta wasiƙar nan, ina gaishe ku saboda Ubangiji. 23 Gayus, mai masaukina, mai kuma saukar da dukan 'yan ikilisiya, yana gaishe ku. Arastas, ma'ajin gari, da kuma ɗan'uwanmu Kawartas, suna gaishe ku. 24 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku duka. Amin, Amin.

Ƙarasawa da Yabo

25 Ɗaukaka tă tabbata ga mai ikon ƙarfafa ku bisa ga bisharata, bisa ga wa'azin Yesu Almasihu, wadda ta gare ta ne aka bayyana asirin nan da yake ɓoye tun fil'azal. 26 Asirin nan kuwa sanar da shi ga dukan al'ummai, ta wurin littattafan annabawa, bisa ga umarnin Allah Madawwami, domin a jawo su, su gaskata, su yi biyayya. 27 Ɗaukaka tă tabbata har abada ga Allah Makaɗaicin hikima ta wurin Yesu Almasihu! Amin, Amin.

1 Korantiyawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzo kirayayye na Almasihu Yesu da yardar Allah, da kuma ɗan'uwanmu Sastanisu, 2 zuwa ga ikilisiyar Allah da take a Koranti, wato, su waɗanda aka keɓe a cikin Almasihu Yesu, tsarkaka kirayayyu, tare da dukan waɗanda a ko'ina suke addu'a, da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangijinsu da namu duka. 3 Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Godiya saboda Bayebaye na Ruhu

4 Kullum nakan gode wa Allah dominku, saboda alherin Allah da aka yi muku baiwa ta hanyar Almasihu Yesu, 5 har ta kowace hanya aka wadata ku a cikinsa, a wajen yin magana duka da ilimi duka� 6 domin kuwa an tabbatar da shaida a kan Almasihu a cikinku. 7 Har ma ku ba kāsassu ba ne a wajen samun kowace baiwar Allah, kuna zuba ido ga bayyanar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 8 Wanda zai tabbatar da ku har ya zuwa ƙarshe, ku kasance marasa abin zargi a ranar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 9 Allah mai alkawari ne, shi ne kuma ya kira ku ga tarayya da Ɗansa Yesu Almasihu Ubangijinmu.

Tsattsaguwa a Ikilisiya

10 Na roƙe ku 'yan'uwa, saboda sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, cewa dukanku bakinku yă zama ɗaya, kada wata tsaguwa ta shiga a tsakaninku, sai dai ku haɗa kai, kuna da nufi ɗaya, ra'ayinku ɗaya. 11 Don kuwa, ya 'yan'uwana, mutanen gidan Kuluwi sun ba ni labari, cewa akwai jayayya a tsakaninku. 12 Abin da nake nufi, shi ne kowannenku yana faɗar abu dabam, “Ni na Bulus ne,” wani kuwa, “Ni na Afolos ne,” wani kuwa, “Ni na Kefas ne,” ko kuwa, “Ni na Almasihu ne.” 13 Ashe, Almasihu a rarrabe yake? Ko Bulus ne aka gicciye dominku? Ko kuwa an yi muku baftisma ne da sunan Bulus? 14 Na gode Allah da ban yi wa waninku baftisma ba, banda Kirisbus da Gayus, 15 kada wani ya ce da sunana ne aka yi muku baftisma. 16 Ai, kuwa lalle na yi wa jama'ar gidan Istifanas ma. Amma banda waɗannan ban san ko na yi wa wani baftisma ba. 17 Ai, ba don in yi baftisma Almasihu ya aiko ni ba, sai dai in sanar da bishara, ba kuwa da gwanintar iya magana ba, domin kada a wofinta ƙarfin gicciyen Almasihu.

Almasihu Ikon Allah Ne, da Hikimarsa

18 Maganar gicciye, maganar wauta ce ga waɗanda suke hallaka, amma ƙarfin Allah ce a gare mu, mu da ake ceto. 19 Domin a rubuce yake cewa, “Zan rushe hikimar mai hikima, Zan kuma shafe haziƙancin haziƙi.” 20 To, ina masu hikima suke? Ina kuma masana? Ina masu muhawwarar zamanin nan? Ashe, Allah bai fallashi hikimar duniyar nan a kan wauta ce ba? 21 Da yake bisa ga hikimar Allah, duniya ba ta san Allah ta wurin hikimarta ba, sai Allah ya ji daɗin ceton masu ba da gaskiya, ta wurin wautar shelar bishara. 22 Yahudawa kam, mu'ujiza suke nema su gani, Helenawa kuwa hikima suka nema su samu, 23 mu kuwa muna wa'azin Almasihu gicciyeyye, abin sa yin tuntuɓe ga Yahudawa, wauta kuma ga al'ummai, 24 amma ga waɗanda suke kirayayyu, ko Yahudawa ko al'ummai duka biyu, Almasihu ikon Allah ne, da hikimar Allah. 25 Domin abin da aka zata wauta ce ta Allah, ya fi hikimar ɗan adam, abin da kuma aka zata rauni ne na Allah, ya fi duk ƙarfin ɗan adam. 26 Ku dubi kiranku da aka yi, ya ku 'yan'uwa, a cikinku, ai, ba a kira masu hikima irin ta duniya da yawa ba, masu iko kuma ba su da yawa, haka ma masu asali ma ba yawa. 27 Amma Allah ya zaɓi abin da yake wauta a duniya, domin ya kunyata masu hikima. Allah ya zaɓi abin da ke rarrauna a duniya, domin ya kunyata ƙaƙƙarfa. 28 Allah ya zaɓi abin da yake ƙasƙantacce, wulakantacce a duniya, har ma abubuwan da ba su, domin ya shafe abubuwan da suke akwai. 29 Wannan kuwa duk don kada wani ɗan adam ya yi fariya a gaban Allah ne. 30 Gama Allah ne ya sa kuka zama na Almasihu Yesu, Allah ne kuma ya sa Almasihu ya zama hikima a gare mu. Ta wurin Almasihu ne kuma muka sami adalci, da tsarkakewa da fansa. 31 Saboda haka, “Duk mai yin alfarma, yă yi da Ubangiji” (abin da yake a rubuce ke nan).

1 Korantiyawa 2

Shelar Almasihu Gicciyeyye

1 Sa'ad da na zo wurinku, 'yan'uwa, ban zo ina sanar da ku asiran Allah ta wurin iya magana ko gwada hikima ba. 2 Don na ƙudura a raina, sa'ad da nake zaune da ku, ba zan so sanin kome ba, sai dai Yesu Almasihu, shi ma kuwa gicciyeyye. 3 Ina kuma tare da ku ne da rauni, da tsoro, da rawar jiki ƙwarai. 4 Jawabina da wa'azina, ba su danganta ga maganar rarrashi ko ta wayo ba, sai dai ga rinjaye na ikon Ruhu, 5 kada bangaskiyarku ta dogara ga hikimar mutane, sai ga ƙarfin Allah.

Bayani daga Ruhun Allah

6 Duk da haka dai muna sanar da hikima ga waɗanda suka kammala, sai dai ba hikimar wannan zamani ba, ba kuwa ta masu mulkin zamanin nan, waɗanda suke shuɗewa ba. 7 Amma muna maganar asirtacciyar hikima ta Allah, wadda dā ɓoyayyiya ce, wato, hikimar da Allah ya ƙaddara tun gaban farkon zamanai, domin ɗaukakarmu. 8 A cikin masu mulkin zamanin nan, ba wanda ya gane hikimar nan, don da sun gane ta, da ba su gicciye Ubangiji Maɗaukaki ba. 9 Amma kuwa yadda yake a rubuce ke nan cewa, “Abubuwan da ido bai taɓa gani ba, Kunne bai taɓa ji ba, Zuciyar mutum kuma ba ta ko riya ba, Waɗanda Allah ya tanadar wa masu ƙaunarsa,” 10 mu ne Allah ya bayyana wa, ta wurin Ruhu, domin Ruhu shi yake fayyace kome, har ma zurfafan al'amuran Allah. 11 Wane ne a cikin mutane ya san tunanin wani mutum, in ba ruhun shi mutumin ba? Haka kuma ba wanda ya san tunanin Allah, sai dai Ruhun Allah. 12 Mu kuwa ba ruhun duniya muka samu ba, sai dai Ruhu wanda yake daga wurin Allah, domin mu fahimci abubuwan da Allah ya yi mana baiwa hannu sake. 13 Su ne kuwa muke sanarwa ta maganar da ba hikimar ɗan adam ce ta koyar ba, sai dai wadda Ruhu ya koyar, muna bayyana al'amura masu ruhu ga waɗanda suke na ruhu. 14 Mutumin da ba shi da Ruhu yakan ƙi yin na'am da al'amuran Ruhun Allah, don wauta ne a gare shi, ba kuwa zai iya fahimtarsu ba, domin ta wurin ruhu ne ake rarrabewa da su. 15 Mutumin da yake na ruhu kuwa yakan rarrabe da kome, shi kansa kuma ba mai jarraba shi. 16 “Wa ya taɓa sanin tunanin Ubangiji, har da zai koya masa?” Mu kuwa tunaninmu na Almasihu ne.

1 Korantiyawa 3

Abokan Aiki na Allah

1 Amma ni, 'yan'uwa, ban iya yi muku jawabi ba, kamar yadda nake yi wa mutanen da suke na ruhu, sai dai kamar yadda nake yi wa masu halin matuntaka, kamar jarirai a cikin bin Almasihu. 2 Nono ne na shayar da ku, ba abinci mai tauri na ba ku ba, don ba ku isa ci ba a lokacin, ko a yanzu ma ba ku isa ba, 3 don har a yanzu ku masu halin mutuntaka ne. Muddin akwai kishi da jayayya a tsakaninku, ashe, ku ba masu halin mutuntaka ba ne, kuna kuma aikata halin mutuntaka? 4 Don in wani ya ce, “Ni na Bulus ne,” wani kuma ya ce, “Ni na Afolos ne,” ashe, ba aikata halin mutuntaka kuke yi ba? 5 To, wane ne Afolos? Wane ne Bulus kuma? Ashe, ba bayi ne kawai ba, waɗanda kuka ba da gaskiya ta wurinsu, ko wannensu kuwa gwargwadon abin da Ubangiji ya ba shi? 6 Ni na yi shuka, Afolos ya yi banruwa, amma Allah ne ya girmar. 7 Don haka da mai shukar, da mai banruwan, ba a bakin kome suke ba, sai dai Allah kaɗai, shi da ya girmar. 8 Da mai shukar, da mai banruwan, duk daidai suke, sai dai ko wanne zai sami tasa ladar gwargwadon wahalarsa, 9 gama mu abokan aiki ne na Allah, ku kuwa gona ce ta Allah, ginin Allah kuma. 10 Kamar gwanin magini, haka na sa harsashin gini, gwargwadon baiwar alherin da Allah ya yi mini, wani kuma yana ɗora gini a kai. Sai dai kowane mutum, ya lura da irin ginin da yake ɗorawa a kai. 11 Harsashin kam, ba wanda yake iya sa wani dabam da wanda aka riga aka sa, wato, Yesu Almasihu. 12 To, kowa ya yi ɗori da zinariya a kan harsashin nan, ko da azurfa, ko da duwatsun alfarma, ko da itace, ko da shuci, ko da kara, 13 ai, aikin kowane mutum zai bayyana, domin ranar nan za ta tona shi, gama za a bayyana ta da wuta, wutar kuwa za ta gwada aikin kowa a san irinsa. 14 In aikin da kowane mutum ya ɗora a kan harsashin nan ya tsira, to, zai sami sakamako. 15 In kuwa aikin wani ya ƙone, to, sai ya yi hasara, ko da yake shi da kansa zai tsira, amma kamar ya bi ta wuta ne. 16 Ashe, ba ku sani ku Haikalin Allah ne ba, Ruhun Allah kuma yana zaune a zuciyarku? 17 In wani ya ɓāta Haikalin Allah, Allah zai ɓāta shi. Gama Haikalin Allah tsattsarka ne, ku kanku Haikalinsa ne. 18 Kada kowa ya ruɗi kansa. In waninku ya zaci shi mai hikima ne, yadda duniya ta ɗauki hikima, sai ya mai da kansa marar hikima, domin ya sami zama mai hikima. 19 Gama hikimar duniyar nan wauta ce a gun Allah, domin a rubuce yake, “Yakan kama masu hikima da makircinsu.” 20 Har wa yau, “Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne.” 21 Saboda haka kada kowa ya yi fariya da 'yan adam. Don kuwa kome naku ne, 22 ko Bulus, ko Afolos, ko Kefas, ko duniya, ko rai, ko mutuwa, ko abubuwan yanzu, ko da na gaba, ai, duk naku ne. 23 Ku kuwa na Almasihu ne, Almasihu kuma na Allah ne.

1 Korantiyawa 4

Aikin Manzanni

1 Ta haka ya kamata a san mu da zama ma'aikatan Almasihu, masu riƙon amanar asirtattun al'amuran Allah. 2 Har wa yau dai, abin da ake bukata ga mai riƙon amana, a same shi amintacce. 3 A gare ni kam, sassauƙan abu ne a ce ku ne za ku gwada ni, ko kuwa a gwada ni a gaban kowace mahukunta ta mutane. Ni ma ba na gwada kaina. 4 Ban sani ina da wani laifi ba, amma ba don wannan na kuɓuta ba, ai, Ubangiji shi ne mai gwada ni. 5 Don haka, kada ku yanke wani hukunci tun lokaci bai yi ba, kafin komowar Ubangiji, wanda zai tone al'amuran da suke ɓoye a duhu, ya kuma bayyana nufin zukata. A sa'an nan ne, Allah zai yaɓa wa kowa daidai gwargwado. 6 To, 'yan'uwa, ga zancen waɗannan abubuwa, na misalta su ne ga kaina, da kuma Afolos saboda ku, don ku yi koyi da mu, cewa, kada ku zarce abin da yake a rubuce, kada kuma waninku ya yi fahariya da wani a kan wani. 7 Wa ya fifita ka da sauran? Me kuma kake da shi, wanda ba karɓa ka yi ba? Da yake karɓa ka yi, don me kake fahariya, kamar ba karɓa ka yi ba? 8 Mhm, wato, har kun riga kun yi hamdala! Har kun wadata! Har ma kun yi sarauta ba tare da mu ba ma! Da ma a ce kun yi mulki mana, har mu ma mu yi tare da ku! 9 Don a ganina, Allah ya bayyana mu, mu manzanni, koma bayan duka ne, kamar waɗanda mutuwa ke jewa a kansu, don mun zama abin nuni ga duniya, da mala'iku duk da mutane. 10 An ɗauke mu marasa azanci saboda Almasihu, wato, ku kuwa masu azanci cikin Almasihu! Wato, mu raunana ne, ku kuwa ƙarfafa! Ku kam, ana ganinku da martaba, mu kuwa a wulakance! 11 Har a yanzu haka, yunwa muke ji, da ƙishirwa, muna huntanci, ana bugunmu, kuma yawo muke yi haka, ba mu da gida. 12 Guminmu muke ci. In an zage mu, mukan sa albarka. In an tsananta mana, mukan daure. 13 In an ci mutuncinmu, mukan ba da haƙuri. Mun zama, har a yanzu ma, mu ne kamar jujin duniya, abin ƙyamar kowa. 14 Ba don in kunyata ku na rubuta wannan ba, sai dai don in gargaɗe ku a kan cewa, ku 'ya'yana ne, ƙaunatattu. 15 Ko da kuna da malamai masu ɗumbun yawa, amma ba ku da ubanni da yawa, don ni ne ubanku a cikin Almasihu ta wurin bishara. 16 Don haka, ina roƙon ku, ku yi koyi da ni. 17 Saboda haka, na aika muku da Timoti, wanda yake shi ne ɗana ƙaunatacce, amintacce kuma a cikin Ubangiji, zai kuwa tuna muku da ka'idodina na bin Almasihu, kamar yadda nake koyarwa a ko'ina, a kowace ikilisiya. 18 Waɗansu har suna ɗaga kai, kamar ba zan zo wurinku ba. 19 Amma kuwa zan zo gare ku ba da daɗewa ba, in Ubangiji ya yarda, zan kuma bincika, in ga ƙarfin mutane masu ɗaga kan nan, ba maganganunsu ba. 20 Domin Mulkin Allah ba ga maganar baka yake ba, sai dai ga ƙarfi. 21 To, me kuka zaɓa, in zo muku da sanda, ko kuwa da fuskar ƙauna da lumana?

1 Korantiyawa 5

Hukunci a kan Fasikanci

1 Ana ta cewa akwai fasikanci a tsakaninku, irin wanda ba a yi ko a cikin al'ummai, har wani yana zama da matar ubansa. 2 A! Har kuwa alfarma kuke yi! Ashe, ba gwamma ku yi baƙin ciki ba, har a fitar da wanda ya yi wannan mugun aiki daga cikin jama'arku? 3 Ko da yake a jiki ba na nan, ai, ruhuna yana nan, kamar ma ina nan ne, har ma na riga na yanke wa mutumin da ya yi abin nan hukunci da sunan Ubangijinmu Yesu. 4 Sa'ad da kuka hallara, ruhuna kuma yana nan, da kuma ikon Ubangijinmu Yesu, 5 sai ku miƙa irin wannan mutum ga Shaiɗan, don ya hallaka jikinsa, ruhunsa kuma ya tsira a ranar Ubangiji Yesu. 6 Fāriyarku ba da kyau. Ashe, ba ku sani ba, ɗan yisti kaɗan yake game dukkan curin gurasa? 7 Ku fitar da tsohon yistin nan, don ku zama sabon curi, domin hakika an raba ku da yistin, da yake an riga an yanka Ɗan Ragonmu na Idin Ƙetarewa, wato, Almasihu. 8 Saboda haka, sai mu riƙa yin idinmu, ba da gurasa mai tsohon yisti ba, ba kuwa gauraye da yisti na ƙeta da na mugunta ba, sai dai da gurasa marar yisti ta sahihanci da ta gaskiya. 9 Na rubuta muku a cikin wasiƙata, cewa kada ku yi cuɗanya da fasikai. 10 Ko kusa, ba na nufin fasikai marasa bi, ko makwaɗaita, da mazambata, ko matsafa, don in haka ne, sai ya zama dole ku fita daga duniya. 11 Sai dai na rubuta muku ne, don kada ku yi cuɗanya da duk wanda ake kira ɗan'uwa, mai bi, in yana fasiki, ko makwaɗaici, ko matsafi, ko mai zage-zage, ko mashayi, ko mazambaci, kada ku ko ci abinci da irin waɗannan. 12 Ina ruwana da hukunta waɗanda ba namu ba? Ba waɗanda suke a cikin Ikilisiya za ku hukunta ba? 13 Allah ne yake hukunta waɗanda ba namu ba. Ku kori mugun nan daga cikinku.

1 Korantiyawa 6

Kada a Kai Ƙara gaban Marasa Bi

1 In waninku yana da wata ƙara a game da ɗan'uwansa, ashe, zai yi ƙurun kai maganar a gaban marasa adalci, ba a gaban tsarkaka ba? 2 Ashe, ba ku sani ba, tsarkaka ne za su yi wa duniya shari'a? In kuwa ku ne za ku yi wa duniya shari'a, ashe, ba za ku iya shari'ar ƙananan al'amura ba? 3 Ba ku sani ba, za mu yi wa mala'iku shari'a, balle al'amuran da suka shafi zaman duniyar nan? 4 In kuwa kuna da irin waɗannan ƙararraki, don me kuma kuke kai su gaban waɗanda su ba kome ba ne, a game da Ikilisiya? 5 Na faɗi wannan ne don ku kunyata. Ashe, wato, ba ko mutum ɗaya mai hikima a cikinku, da zai iya sasanta tsakanin 'yan'uwa? 6 Amma ɗan'uwa yakan kai ƙarar ɗan'uwa, gaban marasa ba da gaskiya kuma? 7 Ku yi ƙarar juna ma, ai, hasara ce a gare ku. Ba gara ku haƙura a cuce ku ba? Ku kuma haƙura a zambace ku? 8 Amma, ga shi, ku da kanku kuna cuta, kuna zamba, har ma 'yan'uwanku kuke yi wa! 9 Ashe, ba ku sani ba, marasa adalci ba za su sami gādo a cikin Mulkin Allah ba? Kada fa a yaudare ku! Ba fasikai, ko matsafa, ko mazinata, ko masu luɗu da maɗugo, 10 ko ɓarayi, ko makwaɗaita, ko mashaya, ko masu zage-zage, ko mazambata, da za su sami gādo a cikin Mulkin Allah. 11 Waɗansunku ma dā haka suke, amma an wanke ku, an tsarkake ku, an kuma kuɓutar da ku, da sunan Ubangiji Yesu Almasihu, da kuma Ruhun Allahnmu.

Ku Ɗaukaka Allah da Jikinku

12 “Dukan abubuwa halal ne a gare ni,” amma ba dukan abubuwa ne masu amfani ba. “Abu duka halal na a gare ni,” amma ba zan zama bawan kome ba. 13 “Abinci don ciki aka yi shi, ciki kuma don abinci”�Allah kuma zai hallaka duka biyu, wannan da wancan. Jiki kam, ba don fasikanci yake ba, sai dai domin Ubangiji, Ubangiji kuma domin jiki. 14 Allah ya ta da Ubangiji daga matattu, haka mu ma zai ta da mu da ikonsa. 15 Ashe, ba ku sani ba jikinku gaɓoɓin Almasihu ne? Ashe kuma, sai in ɗauki gaɓoɓin Almasihu in mai da su gaɓoɓin karuwa? Faufau! 16 Ashe, ba ku sani ba, duk wanda ya tara da karuwa, sun zama jiki ɗaya ke nan? Domin a rubuce yake cewa, “Su biyun za su zama jiki ɗaya.” 17 Duk wanda kuwa yake haɗe da Ubangiji, sun zama ɗaya a ruhu ke nan. 18 Ku guji fasikanci. Duk sauran zunubin da mutum yake yi bai shafi jikinsa ba, amma mai yin fasikanci, yana ɗaukar alhalin jikinsa ne. 19 Ashe, ba ku sani ba, jikinku Haikali ne na Ruhu Mai Tsarki wanda yake a zuciyarku, wanda kuka kuma samu a gun Allah? Ai, ku ba mallakar kanku ba ne. 20 Sayenku aka yi da tamani. To, sai ku ɗaukaka Allah da jikinku.

1 Korantiyawa 7

Damuwar da take a cikin Aure

1 To, a yanzu, a game da abin da kuka rubuto, yana da kyau mutum ya zauna ba aure. 2 Amma don gudun fasikanci sai kowane mutum ya kasance da matarsa, kowace mace kuma da mijinta. 3 Miji yă ba matarsa hakkinta na aure, haka kuma matar ga mijinta. 4 Matar kuwa ba ta da iko da jikinta, sai dai mijin, haka kuma mijin ba shi da iko da jikinsa, sai dai matar. 5 Kada ɗayanku ya ƙaurace wa ɗaya, sai ko da yardar juna zuwa wani ɗan lokaci kaza, don ku himmantu ga addu'a, sa'an nan ku sāke haɗuwa, kada Shaiɗan ya zuga ku ta wajen rashin kamewa. 6 Na fadi wannan ne bisa ga shawara, ba bisa ga umarni ba. 7 Da ma a ce kowa kamar ni yake mana! Sai dai kowa da irin baiwar da Allah ya yi masa, wani iri kaza, wani kuma iri kaza. 8 Abin da na gani ga waɗanda ba su yi aure ba, da kuma mata gwauraye, ya kyautu a gare su su zauna ba aure kamar yadda nake. 9 In kuwa ba za su iya kamewa ba, to, sai su yi aure. Ai, gwamma dai a yi aure da sha'awa ta ci rai. 10 Masu aure kuwa ina yi musu umarni, ba kuwa ni ba, Ubangiji ne, cewa kada mace ta rabu da mijinta 11 (in kuwa ta rabu da shi, sai ta zauna haka ba aure, ko kuwa ta sāke shiryawa da mijinta), miji kuma kada ya saki matarsa. 12 Ga sauran, ni nake faɗa, ba Ubangiji ba, in wani ɗan'uwa yana da mace marar ba da gaskiya, ta kuma yarda su zauna tare, to, kada ya rabu da ita. 13 Mace kuma mai miji marar ba da gaskiya, ya kuwa yarda su zauna tare, to, kada ta rabu da shi. 14 Don miji marar ba da gaskiya, a tsarkake yake a wajen matarsa. Mace marar ba da gaskiya kuma, a tsarkake take a wajen mijinta. In ba haka ba, zai zamana 'ya'yanku ba masu tsarki ba ne, amma ga hakika masu tsarki ne. 15 In kuwa shi, ko ita, marar ba da gaskiya ɗin yana son rabuwa, to, sai su rabu. A wannan hali, ɗan'uwa ko 'yar'uwa mai bi, ba tilas a kansu, domin Allah ya kira mu ga zaman lafiya. 16 Ke mace, ina kika sani ko za ki ceci mijinki? Kai miji, ina ka sani ko za ka ceci matarka?

Zaman da Ubangiji ya Nufa

17 Sai dai kowa ya yi zaman da Ubangiji ya sa masa, wanda kuma Allah ya kira shi a kai. Haka nake umarni a dukan Ikilisiyoyi. 18 Duk wanda Allah ya kira, wanda dā ma yake da kaciya, to, kada ya nemi zama marar kaciya. Wanda kuwa ya kira yana marar kaciya, to, kada ya nema a yi masa kaciya. 19 Don kaciya da rashin kaciya ba sa hassala kome, sai dai kiyaye umarnin Allah. 20 Kowa yă zauna a maƙamin da Allah ya kiraye shi. 21 In ya kira ka kana bawa, kada ka damu. In kuwa kana iya samun 'yanci, ai, sai ka samu. 22 Wanda aka kiraye shi ga tafarkin Ubangiji yana bawa, ai, 'yantacce ne na Ubangiji ne. Kuma, wanda aka kira shi yana ɗa, bawa ne na Almasihu. 23 Da tamani aka saye ku. Kada fa ku zama bayin mutane. 24 To, 'yan'uwa, duk halin da aka kira mutum a ciki, sai ya zauna a kai, yana zama tare da Allah.

Marasa Aure da Mata Gwauraye

25 A game da matan da ba su yi aure ba kuwa, ba ni da wani umarnin Ubangiji, amma ina ba da ra'ayina ne a kan ni amintacce ne, bisa ga jinƙan Ubangiji. 26 Na dai ga ya yi kyau mutum ya zauna yadda yake, saboda ƙuncin nan da yake gabatowa. 27 In da igiyar aure a wuyanka, to, kada ka nemi tsinkewa. In kuwa ba igiyar aure a wuyanka, to, kada ka nemi aure. 28 Amma kuwa in ka yi aure, ba ka yi zunubi ba, ko budurwa ma ta yi aure, ba ta yi zunubi ba. Duk da haka dai, duk masu yin aure za su ji jiki, niyyata kuwa in sawwaƙe muku. 29 Abin da nake nufi 'yan'uwa, lokacin da aka ƙayyade ya ƙure. A nan gaba masu mata su zauna kamar ba su da su, 30 masu kuka kamar ba kuka suke yi ba, masu farin ciki ma kamar ba farin ciki suke yi ba, masu saye kuma kamar ba su riƙe da kome, 31 masu moron duniya kuma, kada su ba da ƙarfi ga moronta. Don yayin duniyar nan mai shuɗewa ne. 32 Ina so ku 'yantu daga damuwa. Mutum marar aure yakan tsananta kula da sha'anin Ubangiji, yadda zai faranta wa Ubangiji rai. 33 Mutum mai aure kuwa, yakan tsananta kula da sha'anin duniya, yadda zai faranta wa matarsa rai. 34 Hankalinsa ya rabu biyu ke nan. Mace marar aure, ko budurwa, takan tsananta kula da sha'anin Ubangiji, yadda za ta kasance tsattsarka a jiki, da kuma a rai. Mace mai aure kuwa takan tsananta kula da sha'anin duniya, yadda za ta faranta wa mijinta rai. 35 Na faɗi haka ne, don in taimake ku, ba don in ƙuntata muku ba, sai dai don in kyautata zamanku, da nufin ku himmantu ga bautar Ubangiji ba da raba hankali ba. 36 Ga zancen 'ya budurwa, wadda ta zarce lokacin aure, idan mahaifinta ya ga bai kyauta mata ba, in kuwa hali ya yi, sai ya yi abin da ya nufa, wato, a yi mata aure, bai yi zunubi ba. 37 In kuwa ya zamana ba lalle ne ya yi wa 'yar tasa budurwa aure ba, amma ya tsai da shawara bisa ga yadda ya nufa, ya kuma ƙudura sosai a ransa, a kan tsare ta, to, haka daidai ne. 38 Wato, wanda ya yi wa 'yar tasa budurwa aure, ya yi daidai, amma wanda bai aurar da ita ba, ya fi shi. 39 Igiyar aure tana wuyan mace, muddin mijinta yana da rai. In kuwa mijinta ya mutu, to, tana da dama ta auri wanda take so, amma fa, sai mai bin Ubangiji. 40 Amma a nawa ra'ayi, za ta fi farin ciki, in ta zauna a yadda take. A ganina kuwa ina da Ruhun Allah.

1 Korantiyawa 8

Abincin da aka Miƙa wa Gumaka

1 To, yanzu a game da abubuwan da aka yanka wa gumaka, mun sani dukanmu muna da ilimi. Ilimi yakan kumbura mutum, ƙauna kuwa takan inganta shi. 2 Duk mai gani ya san wani abu, ai, har a yanzu, bai san yadda ya kamata ya sani ba. 3 In kuwa wani na ƙaunar Allah, to, Allah ya san shi. 4 A game da cin abin da aka yanka wa gumaka kuwa, mun sani, duk duniyar nan gunki yana a matsayin abin da babu ne, da kuma, babu wani Allah sai ɗaya. 5 Ko da yake, akwai waɗanda ake kira alloli a sama ko a ƙasa, don kuwa akwai “alloli” da “iyayengiji” da yawa, 6 duk da haka dai, a gare mu kam, Allah ɗaya ne, wato Uba, wanda dukkan abubuwa suke daga gare shi, wanda mu kuma zamansa muke yi, Ubangiji kuma ɗaya ta gare shi muka kasance. 7 Amma dai ba kowa ne yake da wannan sani ba. Amma waɗansu ta wurin sabawarsu da al'amuran gunki har yanzu, sukan ci naman da suka ɗauka kamar an yanka wa gunki ne. Saboda haka lamirinsu, da yake rarrauna ne, ya ƙazantu. 8 Abinci ba zai ƙare mu a game da Allah ba. In mun ci, ba mu ƙaru ba, in kuma ba mu ci ba, ba mu ragu ba. 9 Sai dai ku lura, kada 'yancin nan naku ya zama abin sa tuntuɓe ga waɗanda ba su tsai da zuciyarsu ba. 10 Amma in wani mutum, wanda yake da rarraunan lamiri, ya gan ka, kai da kake da sani, kana ci a ɗakin gunki, ashe, wannan ba zai ƙarfafa lamirinsa har ya ci abincin da aka miƙa wa gunki ba? 11 Wato, ta sanin nan naka, sai a rushe rarraunan nan, ɗan'uwa ne kuwa wanda Almasihu ya mutu dominsa! 12 Ta haka ne kuke yi wa Almasihu laifi, wato ta wurin yi wa 'yan'uwanku laifi, kuna rushe rarraunan lamirinsu. 13 Saboda haka in dai cin nama ya sa ɗan'uwana tuntuɓe, har abada ba zan ƙara cin nama ba, don haka in sa ɗan'uwana tuntuɓe.

1 Korantiyawa 9

Hakkokin Manzo

1 Ni ba ɗa ba ne? Ba kuma manzo ba ne? Ban ga Yesu Ubangijinmu ba ne? Ku ba aikina ba ne a cikin Ubangiji? 2 Ai, ko waɗansu ba su ɗauke ni a kan manzo ba, lalle ku kam, ni manzo ne a gare ku, domin kuwa ku ne tabbatar manzancina a gaban Ubangiji. 3 Wannan ita ce kariyata ga masu son tuhumata. 4 Ashe, ba mu da iko a ba mu ci da sha? 5 Ba mu da ikon tafiya da matarmu ta aure mai bi, kamar yadda sauran manzanni, da 'yan'uwan Ubangiji, da kuma Kefas suke yi? 6 Ko kuwa dai ni da Barnaba ne kawai, ba mu da iko a ɗauke mana aikin ci da kai? 7 Wa yake yin aikin soja, sa'an nan ya ci da kansa? Wa zai shuka garkar inabi, ya kasa cin 'ya'yan? Wa zai yi kiwon garke, ya kasa shan nonon? 8 Wato, ina faɗar haka bisa ga ra'ayin mutum kawai ne? Ba haka ma Attaura ta faɗa ba? 9 Ai, haka yake a rubuce a Shari'ar Musa cewa, “Kada ka sa wa takarkari takunkumi a sa'ad da yake sussuka.” Da shanu ne kawai Allah yake kula? 10 Ba saboda mu musamman yake magana ba? Hakika saboda mu ne aka rubuta. Ai, ya kamata mai noma ya yi noma da sa zuciya, mai sussuka kuma ya yi sussuka da sa zuciya ga samun rabo daga amfanin gonar. 11 Da yake mun shuka iri na ruhu a zuciyarku, to, wani ƙasaitaccen abu ne, in mun mori amfaninku irin na duniya? 12 Da yake waɗansu sun mori halaliyarsu a game da ku, ashe ba mu muka fi cancanta ba? Duk da haka ba mu mori wannan halaliya ba, sai dai muna jure wa kome, don ta ko ƙaƙa kada mu hana bisharar Almasihu yaɗuwa. 13 Ashe, ba ku sani ba, masu hidima a Haikali daga nan suke samun abincinsu? Masu hidimar bagadi kuma, a nan suke samun rabo daga hadayar da aka yanka? 14 Haka nan kuma Ubangiji ya yi umarni, cewa, ya kamata masu sanar da bishara, a cishe su albarkacin bishara. 15 Amma ni kam, ban mori ko ɗaya daga cikin halaliyan nan ba, ba kuma ina rubuta wannan ne, don a yi mini haka ba. Ai, gara in mutu a kan wani ya banzanta mini fahariyata. 16 Don ko da yake ina yin bishara, ba na fahariya da haka, gama tilas ne a gare ni. Kaitona in ba na yin bishara! 17 Da da ra'ina nake yi, da sai a biya ni. Amma da yake ba ni da ra'ina ba ne, an danƙa mini amana ke nan. 18 Ina kuma hakkina? To, ga shi. A duk lokacin da nake yin bishara, sona in yi ta a kyauta, kada in ƙurashe halaliyata a game da bishara. 19 Ko da yake ni ba bawan kowa ba ne, na mai da kaina bawan kowa, domin in rinjayi mutane masu yawa. 20 Ga Yahudawa, sai na zama kamar Bayahude, domin in rinjayi Yahudawa. Ga waɗanda Shari'a take iko da su, sai na zama kamar wanda Shari'a take iko da shi, ko da yake ba Shari'a take iko da ni ba, domin in rinjayi waɗanda Shari'a take iko da su ne. 21 Ga marasa Shari'a kuwa, sai na zama kamar marar Shari'a, ba cewa ba wata shari'ar Allah da take iko da ni ba, a'a, shari'ar Almasihu na iko da ni, domin in rinjayi marasa Shari'a ne. 22 Ga raunana, sai na zama kamar rarrauna domin in rinjayi raunana. Na zama kowane irin abu ga kowaɗanne irin mutane, domin ta ko ƙaƙa in ceci waɗansu. 23 Na yi wannan ne duk saboda bishara, domin in sami rabo a cikin albarkarta. 24 Ashe, ba ku sani ba, a wajen tsere dukan masu gudu suna ƙoƙarin tsere wa juna, amma ɗaya ne kaɗai yake samun kyautar ci? To, sai ku yi ta gudu haka nan, don ku ci. 25 Duk masu wasan gasa, sukan hori kansu ta kowane hali. Su kam, suna yin haka ne, don su sami lada mai lalacewa, mu kuwa marar lalacewa. 26 To, ni ba gudu nake yi ba wurin zuwa ba, dambena kuwa ba naushin iska nake yi ba. 27 Amma ina azabta jikina ne, don in bautar da shi, kada bayan da na yi wa waɗansu wa'azi, ni da kaina a yar da ni.

1 Korantiyawa 10

Kashedi kan Bautar Gumaka

1 To, ina so ku sani, 'yan'uwa, dukan kakanninmu an kara su ne a ƙarƙashin gajimare, dukansu kuma sun ratsa ta cikin bahar. 2 Dukansu kuwa an yi musu baftisma ga bin Musa a cikin gajimaren, da kuma bahar ɗin. 3 Duka kuwa sun ci abincin nan na ruhu, 4 duk kuma sun sha ruwan nan na ruhu. Domin sun sha ruwa daga Dutsen nan na ruhu, wanda ya yi tafiya tare da su. Dutsen nan kuwa Almasihu ne. 5 Duk da haka Allah bai yi murna da yawancinsu ba, har aka karkashe su a jeji. 6 To, ai, waɗannan abubuwa gargaɗi ne a gare mu, kada mu yi marmarin mugayen abubuwa, kamar yadda suka yi. 7 Kada fa ku zama matsafa kamar yadda waɗansunsu suke. A rubuce yake cewa, “Jama'a sun zauna garin ci da sha, suka kuma tashi suka yi ta rawa.” 8 Kada fa mu yi fasikanci yadda waɗansunsu suka yi, har mutum dubu ashirin da uku suka zuba a rana ɗaya tak. 9 Kada kuma mu gwada Ubangiji yadda waɗansu suka yi, har macizai suka hallaka su. 10 Kada kuma mu yi gunaguni yadda waɗansu suka yi, har mai hallakarwa ya hallaka su. 11 To, duk wannan ya same su ne a kan misali, an kuma rubuta shi ne don a gargaɗe mu, mu da ƙarshen zamani ya zo mana. 12 Don haka duk wanda yake tsammani ya kahu, ya mai da hankali kada ya fāɗi. 13 Ba wani gwajin da ya taɓa samunku, wanda ba a saba yi wa ɗan adam ba. Allah mai alkawari ne, ba zai kuwa yarda a gwada ku fin ƙarfinku ba, amma a game da gwajin sai ya ba da mafita, yadda za ku iya jure shi. 14 Saboda haka, ya ƙaunatattuna, ku guji bautar gumaka. 15 Ina magana da ku a kan ku mahankalta ne fa, ku duba da kanku ku ga abin da make faɗa. 16 Ƙoƙon nan na yin godiya, wanda muke gode wa Allah saboda shi, ashe, ba tarayya ne ga jinin Almasihu ba? Gurasar nan da muke gutsuttsurawa kuma, ashe, ba tarayya ce ga jikin Almasihu ba? 17 Da yake gurasar nan ɗaya ce, ashe kuwa, mu da muke da yawa jiki ɗaya ne, gama mu duk gurasa ɗaya muke ci. 18 Ku dubi ɗabi'ar Isra'ila. Ashe, waɗanda suke ci daga hadayu, ba tarayya suke yi da bagadin hadaya ba? 19 Me nake nufi ke nan? Abin da aka yanka wa gumakan ne ainihin wani abu, ko kuwa gunkun ne ainihin wani abu? 20 A'a! Na nuna ne kawai cewa abin da al'ummai suke yankawa, ga aljannu suke yanka wa, ba Allah ba. Ba na fa so ku zama abokan tarayya da aljannu. 21 Ba dama ku sha a ƙoƙon Ubangiji, ku kuma sha a na aljannu. Ba dama ku ci abinci a teburin Ubangiji, ku kuma ci a na aljannu. 22 Ashe, har mā tsokani Ubangiji ya yi kishi? Mun fi shi ƙarfi ne?

Yi Kome saboda Ɗaukakar Allah

23 “Dukan abubuwa halal ne,” amma ba dukan abubuwa ne masu amfani ba. “Dukan abubuwa halal ne,” amma ba dukan abubuwa ne suke ingantawa ba. 24 Kada kowa ya nemi ya kyautata wa kansa, sai dai ya kyautata wa ɗan'uwansa. 25 Ku ci kowane irin abu da ake sayarwa a mahauta, ba tare da tambaya ba saboda lamiri. 26 Don an rubuta, “Duniya ta Ubangiji ce, da duk abin da ke cikinta.” 27 In wani a cikin marasa ba da gaskiya ya kira ku cin abinci, kuka kuwa yarda ku tafi, sai ku ci duk irin da aka sa a gabanku, ba tare da tambaya ba saboda lamiri. 28 In kuwa wani ya ce muku, “An yanka wannan saboda gunki ne fa,” to, kada ku ci, saboda duban mutuncin wannan mai gaya muku, da kuma saboda lamiri, 29 nasa lamiri fa na ce, ba naka ba. Don me fa lamirin wani zai soki 'yancina? 30 In na yi godiya ga Allah a kan abincina, saboda me za a zarge ni a kan abin da na ci da godiya ga Allah? 31 To, duk abin da kuke yi, ko ci, ko sha, ku yi kome saboda ɗaukakar Allah. 32 Kada ku zama abin tuntuɓe ga Yahudawa ko al'ummai ko ikilisiyar Allah, 33 kamar dai yadda nake ƙoƙarin kyautata wa dukan mutane a cikin duk abin da nake yi, ba nema wa kaina amfani nake yi ba, sai dai in amfani mutane da yawa, don su sami ceto.

1 Korantiyawa 11

1 Ku yi koyi da ni kamar yadda nake koyi da Almasihu.

Mata su Rufe Kansu

2 Ina yaba muku ne don kuna tunawa da ni a cikin kowace harka, kuna kuma riƙe ka'idodin nan da kyau, daidai yadda na ba ku. 3 Amma fa ina so ku fahimci cewa, shugaban kowane mutum Almasihu ne, shugaban kowace mace kuwa mijinta ne, shugaban Almasihu kuma Allah ne. 4 Duk mutumin da ya yi addu'a ko ya yi annabci kansa a rufe, ya wulakanta shugabansa ke nan. 5 Amma duk matar da ta yi addu'a, ko ta yi annabci da kanta a buɗe, ta wulakanta shugabanta ke nan, duk ɗaya ne da an aske kanta ma. 6 In mace ta ƙi rufe kanta, to, sai ta sausaye gashinta. In kuwa abin kunya ne a yi wa mace sausaye ko kundumi, to, sai ta rufe kanta. 7 Namiji kam, bai kamata ya rufe kansa ba, tun da yake shi kamannin Allah ne, abin alfahari ga Allah kuma. Amma mace abar taƙamar namiji ce. 8 (Don kuwa namiji ba daga jikin mace yake ba, amma matar daga jikin namiji take. 9 Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.) 10 Shi ya sa ya kamata mace ta rufe kanta, wato, alamar ikon namiji, saboda mala'iku. 11 Duk da haka, a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, haka kuma namiji ba a rabe yake da mace ba. 12 Wato kamar yadda mace take daga namiji, haka namiji kuma haihuwar mace ne. Amma dukkan abubuwa daga Allah suke. 13 Ku kanku ku duba fa ku gani. Ya dace da mace ke nan ta yi addu'a ga Allah da kanta a buɗe? 14 Ashe, ko ɗabi'a ma ba ta nuna muku cewa namiji ya yi gizo, abin kunya ne ba? 15 In kuwa mace tana da gashi, ba alfarmarta ce ba? Gama don rufin kai ne aka yi mata gashin. 16 In kuwa wani yana da niyyar gardama, to, mu dai ba mu san wata al'ada ba, ikilisiyoyin Allah kuma haka.

Ƙasƙantar da Cin Jibin Ubangiji

17 A game da umarnin nan kuwa, ban yaba muku ba, taruwarku ba ta kirki ba ce, ta rashin kirki ce. 18 To, da farko dai sa'ad da kuka taru, taron ikilisiya, na ji har akwai rarrabuwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen. 19 Don lalle ne a sami tsattsaguwa a tsakaninku, don a iya rarrabewa da waɗanda suke amintattu a cikinku. 20 Ashe kuwa, in kun taru gu ɗaya, ba jibin Ubangiji kuke ci ba! 21 Domin a wajen cin abinci, kowa yakan dukufa a kan akushinsa, ga wani yana jin yunwa, ga wani kuwa ya sha ya bugu. 22 A! Ba ku da gidajen da za ku ci ku sha a ciki ne? Ko kuwa kuna raina Ikilisiyar Allah ne, kuna kuma muzanta waɗanda ba su da kome? To, me zan ce muku? Yaba muku zan yi a kan wannan matsala? A'a, ba zan yaba muku ba.

Cin Jibin Ubangiji

23 Abin nan kuwa da na karɓa a gun Ubangiji, shi ne na ba ku, cewa Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki gurasa, 24 bayan da ya yi godiya ga Allah kuma, sai ya gutsuttsura, ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake saboda ku. Ku riƙa yin haka tunawa da ni.” 25 Haka kuma bayan jibin, sai ya ɗauki ƙoƙo, ya ce, “Ƙoƙon nan na Sabon Alkawari ne, da aka tabbatar da shi da jinina. Ku yi haka duk a sa'ad da kuke sha, domin tunawa da ni.” 26 Wato, duk sa'ad da kuke cin gurasar nan, kuke kuma sha a ƙoƙon nan, kuma ayyana mutuwar Ubangiji ke nan, har sai ya dawo.

Cin Jibin Ubangiji da Rashin Cancanta

27 Saboda haka duk wanda ya ci gurasar nan, ko ya sha a ƙoƙon nan na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulakanta jikin Ubangiji da jininsa ke nan. 28 Sai dai kowa ya auna kansa, sa'an nan ya ci gurasar, ya kuma sha a ƙoƙon. 29 Kowa ya ci, ya kuma sha, ba tare da faɗaka da jikin Ubangiji ba, ya jawo wa kansa hukunci ke nan, ta wurin ci da sha da ya yi. 30 Shi ya sa da yawa daga cikinku suke da rashin lafiya da rashin ƙarfi, har ma waɗansu da dama suka yi barci. 31 Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za a hukunta mu ba. 32 In kuwa Ubangiji ne yake hukunta mu, to, muna horuwa ke nan, don kada a yanke mana hukunci tare da sauran duniya. 33 Saboda haka, ya 'yan'uwana, in kuka taru don cin abinci, sai ku jiraci juna. 34 In kuwa wani yana jin yunwa, sai ya ci a gida, kada ya zamana taronku ya jawo muku hukunci. Batun sauran abubuwa kuwa, zan ba da umarni a kai sa'ad da na zo.

1 Korantiyawa 12

Bayebaye na Ruhu

1 A yanzu kuma 'yan'uwa, a game da baye-baye na ruhu, ba na so ku rasa sani. 2 Kun sani fa a sa'ad da kuke bin al'ummai, an juyar da ku ga bin gumakan nan marasa baki yadda aka ga dama. 3 Don haka nake sanar da ku, cewa ba mai magana ta wurin ikon Ruhun Allah sa'an nan ya ce, “Yesu la'ananne ne!” Haka kuma ba mai iya cewa, “Yesu Ubangiji ne,” sai ta wurin ikon Ruhu Mai Tsarki. 4 To, akwai baiwa iri iri, amma Ruhu ɗaya ne. 5 Akwai fanni iri iri na ibada, amma Ubangiji ɗaya ne. 6 Akwai kuma aiki iri iri, amma Allah ɗaya yake iza kowa ga yin kowannensu. 7 An yi wa kowanne baiwa da wani buɗi na Ruhu, don kyautata wa duka. 8 Wani an yi masa baiwa da koyar da hikima ta wurin Ruhu, wani kuma da koyar da sani ta wurin wannan Ruhu. 9 Wani kuwa an yi masa baiwa da bangaskiya ta wurin Ruhun nan, wani kuma baiwar warkarwa ta wurin Ruhun nan, 10 wani kuma yin mu'ujizai, wani kuma annabci, wani kuma baiwar rarrabe ruhu da aljani, wani kuma iya harshe iri iri, wani kuma fassara harsuna. 11 Dukan waɗannan Ruhu ɗaya ne da yake iza su, yake kuma rarraba wa ko wannensu yadda ya nufa.

Dukkanmu Gaɓoɓin Jiki guda Ne

12 Wato kamar yadda jiki yake guda, yake kuma da gaɓoɓi da yawa su gaɓoɓin kuwa ko da yake suna da yawa, jiki guda ne, to, haka ga Almasihu. 13 Dukanmu an yi mana baftisma ta wurin Ruhu guda, mu zama jiki guda, Yahudawa ko al'ummai, bayi ko 'ya'ya, dukanmu kuwa an shayar da mu Ruhu guda. 14 Jiki ba gaba ɗaya ba ne, gaɓoɓi ne da yawa. 15 Da ƙafa za ta ce, “Da yake ni ba hannu ba ce, ai, ni ba gaɓar jiki ba ce,” faɗar haka ba za ta raba ta da zama gaɓar jikin ba. 16 Da kuma kunne zai ce, “Da yake ni ba ido ba ne, ai, ni ba gaɓar jiki ba ne,” faɗar haka ba za ta raba shi da zama gaɓar jikin ba. 17 Da dukan jiki ido ne, da me za a ji? Da dukan jiki kunne ne, da me za a sansana? 18 Amma ga shi, Allah ya shirya gaɓoɓin jiki, kowaccensu yadda ya nufa. 19 Da dukan jikin gaɓa ɗaya ne, da ina sauran jikin? 20 Amma ga shi, akwai gaɓoɓi da yawa, jiki kuwa ɗaya. 21 Ba dama ido ya ce wa hannu, “Ba ruwana da kai,” ko kuwa kai ya ce wa ƙafafu, “Ba ruwana da ku.” 22 Ba haka yake ba, sai ma gaɓoɓin da ake gani kamar raunana, su ne wajibi, 23 gaɓoɓin jiki kuma da ake gani kamar sun kasa sauran daraja, mukan fi ba su martaba. Ta haka gaɓoɓinmu marasa kyan gani, akan ƙara kyautata ganinsu. 24 Gaɓoɓinmu masu kyan gani kuwa ba sai an yi musu kome ba. Amma Allah ya harhaɗa jiki, yana ba da mafificiyar martaba ga ƙasƙantacciyar gaɓa, 25 kada rashin haɗa kai ya kasance ga jiki, sai dai gaɓoɓin su kula da juna, kula iri ɗaya. 26 Ta haka, in wata gaɓa ta ji ciwo, duk sai su ji ciwo tare, in kuwa an yabi wata, duk sai su yi farin ciki tare. 27 To, ku jikin Almasihu ne, kowannenku kuwa gaɓarsa ne. 28 A cikin ikilisiya, Allah ya sa waɗansu su zama, na farko manzanni, na biyu annabawa, na uku masu koyarwa, sa'an nan sai masu yin mu'ujizai, sai masu baiwar warkarwa, da mataimaka, da masu tafiyar da Ikilisiya, da kuma masu magana da harsuna iri iri. 29 Shin, duka manzanni ne? Ko duka annabawa ne? Ko duk masu koyarwa ne? Su duka masu yin mu'ujizai ne? 30 Duka ne suke da baiwar warkarwa? Duka ne ke magana da waɗansu harsuna? Ko kuwa duka ne suke fassara? 31 Sai dai ku himmantu ga neman mafafitan baye-baye. Har ma zan nuna muku wata hanya mafificiya nesa.

1 Korantiyawa 13

Ƙauna

1 Ko da zan yi magana da harsunan mutane, har da na mala'iku, amma ya zamana ba ni da ƙauna, na zama ƙararrawa mai yawan ƙara ke nan, ko kuwa kuge mai amo. 2 Ko da zan yi annabci, ina kuma fahimtar dukkan asiri, da dukkan ilimi, ko da kuma ina da matuƙar bangaskiya, har yadda zan iya kawar da duwatsu, muddin ba ni da ƙauna, to, ni ba kome ba ne. 3 Ko da zan sadaukar da duk abin da na mallaka, in kuma ba da jikina a ƙone, in har ba ni da ƙauna, to, ban amfana da kome ba. 4 Ƙauna tana sa haƙuri da kirki. Ƙauna ba ta sa kishi, ba ta yin kumbura. 5 Ƙauna ba ta sa ɗaga kai ko rashin kārā, ƙauna ba ta sa sonkai, ba ta jin tsokana, ba ta riƙo. 6 Ƙauna ba ta sa yin farin ciki da mugunta, sai dai da gaskiya. 7 Ƙauna tana sa daurewa a cikin kowane hali, da bangaskiya a cikin kowane hali, haka kuma sa zuciya a cikin kowane hali, da jimiri a cikin kowane hali. 8 Ƙauna ba ta ƙarewa har abada. Annabci zai shuɗe, harsuna za su ɓace, ilimi kuma zai bushe. 9 Ai, hakika iliminmu ba cikakke ba ne, annabcinmu kuma ba cikakke ba ne. 10 Sa'ad da kuwa cikakken ya zo, sai ɗan kiman nan ya shuɗe. 11 Sa'ad da nake yaro, nakan yi magana irin ta ƙuruciya, nakan yi tunani irin na ƙuruciya, nakan ba da hujjojina irin na ƙuruciya. Da na isa mutum kuwa, sai na bar halin ƙuruciya. 12 Gama yanzu kamar a madubi muke gani duhu duhu, a ranar nan kuwa za mu gani ido da ido. A yanzu sanina sama sama ne, a ranar nan kuwa zan fahimta sosai, kamar yadda aka fahimce ni sosai. 13 To, a yanzu abubuwan nan uku sun tabbata, bangaskiya, da bege, da kuma ƙauna, amma duk mafi girma a cikinsu ita ce ƙauna.

1 Korantiyawa 14

Harsuna da Annabci

1 Ku nace wa ƙauna, ku kuma himmantu ga neman bayebaye na ruhu, tun ba ma na yin annabci ba. 2 Duk wanda yake magana da wani harshe, ba da mutane yake magana ba, da Allah yake yi, ba kuwa wanda yake fahimtarsa, domin asirtattun a al'amura yake ambato ta wurin Ruhu. 3 Wanda kuwa yake yin annabci, mutane yake yi wa magana domin ya inganta su, ya ƙarfafa su, ya ta'azantar da su. 4 Duk wanda yake magana da wani harshe, kansa yake ingantawa. Mai yin annabci kuwa, ikilisiya yake ingantawa. 5 To, ina so dukanku ku yi magana da waɗansu harsuna dabam, amma na fi so ku yi annabci. Wanda yake yin annabci, ya fi mai magana da waɗansu harsuna, sai ko in wani ya yi masa fassara, domin a inganta ikilisiya. 6 To, 'yan'uwa, in na zo muku ina magana da waɗansu harsuna, amfanin me zan yi muku in ban zo muku da wani bayani, ko ilimi, ko annabci, ko koyar da Maganar Allah ba? 7 In abubuwan nan marasa rai, kamar su sarewa da molo, muryarsu ba ta fita sosai ba, yaya wani zai san abin da ake busawa ko kaɗawa? 8 In ba a busa ƙaho sosai ba, wa zai yi shirin yaƙi? 9 Haka ma yake a gare ku. In kun yi magana da wani harshe, wanda ba a fahimta ba, yaya wani zai san abin da ake faɗa? Kun yi magana a banza ke nan! 10 Hakika akwai harsuna iri iri a duniya, ba kuwa wanda ba shi da ma'ana. 11 In kuwa ba na jin harshen, sai in zama bare ga mai maganar, mai maganar kuma ya zama bare a gare ni. 12 Haka ma yake a gare ku. Tun da ya ke kun ɗokanta da samun bayebaye na Ruhu, sai ku himmantu ku ba da ƙarfinku ga inganta ikilisiya. 13 Saboda haka duk mai magana da wani harshe, sai ya yi addu'a a yi masa baiwar fassara. 14 In na yi addu'a da wani harshe, ruhuna ne yake addu'a, amma tunanina bai amfana kowa ba. 15 To, ƙaƙa ke nan? Zan yi addu'a da ruhuna, zan kuma yi a game da tunanina. Zan yi waƙar yabon Allah da ruhuna, zan yi a game da tunanina. 16 In ba haka ba, in ka gode wa Allah da ruhu kawai, ta yaya wanda ke jahili zai ce, “Amin,” a kan godiyar da kake yi, in bai san abin da kake faɗa ba? 17 Ko da yake ka gode wa Allah sosai, ai, ɗan'uwanka bai ƙaru da kome ba. 18 Na gode Allah ina magana da waɗansu harsuna fiye da ku duka. 19 Duk da haka dai a taron ikilisiya na gwammace in faɗi kalmomi biyar a game da tunanina, domin in karantar da waɗansu, da in faɗi kalmomi dubu goma da wani harshe. 20 Ya ku 'yan'uwa, kada ku yi hankali irin na yara, sai dai a wajen mugunta, ku yi halin jarirai, amma a wajen hankali ku yi dattako. 21 A rubuce yake a cikin littattafai masu tsarki cewa, “Zan yi magana da jama'an nan ta wurin mutane masu baƙin harsuna, da kuma ta harshen baƙi, duk da haka kuwa ba za su saurare ni ba, in ji Ubangiji.” 22 Wato, ashe, harsuna a kan alamu suke, ba ga masu ba da gaskiya ba, sai dai ga marasa ba da gaskiya. Annabci kuwa domin masu ba da gaskiya ne, ba don marasa ba da gaskiya ba. 23 Saboda haka, in dukan ikilisiya ta taru, kowa kuma yana magana da wani harshe dabam, waɗansu jahilai kuma ko marasa ba da gaskiya suka shigo, ashe, ba sai su ce kun ruɗe ba? 24 In kuwa kowa yana yin annabci, wani kuma marar ba da gaskiya ko jahili ya shigo, sai maganar kowa ta ratsa shi, ya kamu a ransa ta maganar kowa, 25 asiran zuciyarsa kuma su tonu. Ta haka sai ya fāɗi ya yi wa Allah sujada, yana cewa lalle Allah na cikinku.

A Yi Kome yadda ya Dace, a Shirye

26 To, ƙaƙa abin yake ne, 'yan'uwa? Duk sa'ad da kuka taru, wani yakan yi waƙar yabon Allah, wani kuma koyar da Maganar Allah, wani bayani, wani yin magana da wani harshe, wani kuma fassara. Sai dai a yi kome don ingantawa. 27 In kuwa waɗansu za su yi magana da wani harshe, kada su fi mutum biyu, matuƙa uku, su ma kuwa bi da bi, wani kuma ya yi fassara. 28 In kuwa ba mai fassara, sai kowannensu ya yi shiru a cikin taron Ikilisiya, ya yi wa Allah magana a zuci. 29 Masu yin annabci kuma, sai dai biyu ko uku su yi magana, saura kuwa su auna maganar. 30 In kuwa an yi wa wani wanda yake zaune wani bayani, sai na farkon nan mai magana ya yi shiru. 31 Dukanku kuna iya yin annabci da ɗaya ɗaya, har kowa ya koya, ya kuma sami ƙarfafawa. 32 Annabawa suna sarrafa ruhohinsu na annabci, 33 domin Allah ba Allahn ruɗu ba ne, na salama ne. Haka yake kuwa a duk ikilisyoyin tsarkaka. 34 Sai mata su yi shiru a cikin taron ikilisiya, don ba a ba su izinin yin magana ba, sai dai su bi, kamar dai yadda Attaura ma ta ce. 35 In akwai wani abin da suke so su sani, to, sai su tambayi mazansu a gida, don abin kunya ne mace ta yi magana a cikin taron ikilisiya. 36 A kanku ne maganar Allah ta fara, ko kuwa a gare ku kaɗai ta isa? 37 In wani yana zato shi annabi ne, ko kuwa mai wata baiwa ta ruhu, to, sai ya fahimta, abin nan da nake rubuto muku umarni ne na Ubangiji. 38 In kuwa wani ya ƙi kula da wannan, shi ma sai a ƙi kula da shi. 39 Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku himmantu ga samun baiwar yin annabci, kada kuma ku hana yin magana da waɗansu harsuna. 40 Sai dai a yi kome ta hanyar da ta dace, ya zauna a natse kuma.

1 Korantiyawa 15

Tashin Almasihu daga Matattu

1 A yanzu kuma, 'yan'uwa, zan tuna muku da bisharar da na sanar da ku, wadda kuka karɓa, wadda kuke bi, 2 wadda kuma ake cetonku da ita, muddin kun riƙe maganar da na sanar da ku da kyau, in ba sama sama ne kuka gaskata ba. 3 Jawabi mafi muhimmanci da na sanar da ku, shi ne wanda na karɓo, cewa, Almasihu ya mutu domin zunubanmu, kamar yadda Littattafai suka faɗa, 4 cewa an binne shi, an ta da shi a rana ta uku, kamar yadda Littattafai suka faɗa, 5 ya kuma bayyana ga Kefas, sa'an nan ga sha biyun. 6 Sa'an nan ya bayyana ga 'yan'uwa fiye da ɗari biyar a lokaci guda, yawancinsu kuwa suna nan har zuwa yanzu, amma waɗansu sun yi barci. 7 Sa'an nan ya bayyana ga Yakubu, sa'an nan ga dukan manzanni. 8 Daga ƙarshen duka ya bayyana a gare ni, ni ma da nake kasasshe, marar cancanta. 9 Don ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban ma isa a ce da ni manzo ba, saboda na tsananta wa Ikilisiyar Allah. 10 Amma saboda alherin Allah na zama yadda nake, alherin da ya yi mini kuwa ba a banza yake ba. Har ma na fi kowannensu aiki, ba kuwa ni ba, alherin Allah ne da yake zuciyata. 11 To, ko ni ne dai, ko kuma su ne, haka muke wa'azi, ta haka kuma kuka gaskata.

Tashin Matattu

12 To, da yake ana wa'azin Almasihu a kan an tashe shi daga matattu, ƙaƙa waɗansunku suke cewa, babu tashin matattu? 13 In dai babu tashin matattu, ashe, ba a ta da Almasihu ba ke nan. 14 In kuwa ba a ta da Almasihu ba, to, ashe, wa'azinmu a banza ne, bangaskiyarku kuma banza ce. 15 Sai ma ya zamana mun yi wa Allah shaidar zur ke nan, domin mun shaida Allah, cewa ya ta da Almasihu, wanda kuwa bai tasar ba, in da gaskiya ne ba a ta da matattu. 16 Don kuwa in ba a ta da matattu, ashe, Almasihu ma ba a ta da shi ba ke nan. 17 In kuwa ba a ta da Almasihu ba, ashe, bangaskiyarku banza ce, har yanzu kuma kuna tare da zunubanku. 18 Ashe, waɗanda suka yi barci a kan su na Almasihu, sun hallaka ke nan. 19 Da begenmu ga Almasihu domin wannan rai ne kaɗai, ai, da mun fi kowa zama abin tausayi. 20 Amma ga hakika an ta da Almasihu daga matattu, shi ne ma nunan fari na waɗanda suka yi barci. 21 Tun da yake mutuwa ta warin mutum ta faru, haka kuma tashin matattu ta wurin Mutum yake. 22 Kamar yadda duk ake mutuwa saboda Adamu, haka duk za a rayar da su saboda Almasihu. 23 Amma kowanne bi da bi, Almasihu ne nunan fari, sa'an nan a ranar komowarsa, waɗanda suke na Almasihu. 24 Sa'an nan sai ƙarshen, sa'ad da zai mayar wa Allah Uba mulki, bayan ya shafe dukkan sarauta da mulki da iko. 25 Domin kuwa lalle ne ya yi mulki, har ya take dukkan maƙiyansa. 26 Magabciyar ƙarshe da za a shafe, ita ce mutuwa. 27 “Gama Allah ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa.” Amma da aka ce, “An sarayar da kome karƙashin ikonsa” a fili yake shi wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, a keɓe yake. 28 Sa'ad da kuma aka sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa ɗin, sa'an nan ne Ɗan da kansa shi ma zai sarayar da kansa ga wannan da ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa, domin Allah yă tabbata shi ne kome da kome. 29 In ba haka ba, mene ne nufin waɗanda ake yi wa baftisma saboda matattu? In ba a ta da matattu sam, don me ake yi wa waɗansu baftisma saboda su? 30 Don me kuma nake a cikin hatsari a kowane lokaci? 31 Na hakikance 'yan'uwa, saboda taƙama da ku da nake yi a cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu, a kowace rana sai na sallama raina ga mutuwa! 32 Idan bisa ga ra'ayin mutum ne, na yi kokawa da namomin jeji a Afisa, mece ce ribata in dai har ba a ta da matattu? “Ba sai mu yi ta ci da sha ba, da yake gobe za mu mutu?” 33 Kada fa a yaudare ku! “Zama da mugaye yakan ɓata halayen kirki.” 34 Ku farka daga magagi, ku kama aikin adalci, ku daina yin zunubi. Waɗansu kam, ba su da sanin Allah. Na faɗi wannan ne don ku kunyata.

Tashin Jiki

35 Watakila wani zai yi tambaya, “Ta yaya ake ta da matattu? Da wace irin kama kuma suke fitowa?” 36 Kai, marar azanci! Abin da ka shuka, ai, ba zai tsiro ba sai ya mutu. 37 Abin da ka shuka kuma, ba shi ne ainihin abin da zai kasance ba, ƙawai, ko ta alkama ce, ko kuma, wata iri dabam. 38 Amma Allah yakan ba ta kama, yadda ya nufa, kowace ƙwaya da irin tata kama. 39 Don ba dukan tsoka ce iri ɗaya ba, mutane da irin tasu, dabbobi ma da irin tasu, tsuntsaye da irin tasu, kifaye kuma da irin tasu. 40 Akwai halitta irin ta Sama, akwai kuma irin ta ƙasa. Amma ɗaukakar irin ta Sama dabam, ɗaukakar irin ta ƙasa kuma dabam. 41 Ɗaukakar rana dabam, ta wata dabam, ta taurari kuma dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen ɗaukaka. 42 Haka kuma yake ga tashin matattu. Akan shuka su da halin ruɓa, akan kuma ta da su da halin rashin ruɓa. 43 Akan shuka da wulakanci, akan tasa da ɗaukaka, akan shuka da rashin ƙarfi, akan tasa da ƙarfi. 44 Akan shuka da jikin mutuntaka, akan tasa da jiki na ruhu. Da yake akwai jiki na mutuntaka, lalle kuma akwai jiki na ruhu. 45 Haka kuma yake a rubuce, “Mutumin farko, Adamu, ya zama rayayyen taliki,” Adamun ƙarshe kuwa Ruhu ne mai rayarwa. 46 Amma ba shi na Ruhun nan ne ya fara bayyana ba, na mutuntaka ne, daga baya kuma sai na Ruhu. 47 Mutumin farko daga ƙasa yake, na turɓaya ne. Na biyun kuwa daga Sama yake. 48 Kamar yadda shi na turɓayar nan yake, haka kuma waɗanda suke na turɓaya suke. Kamar yadda shi na Saman nan yake, haka kuma waɗanda suke na Sama suke. 49 Kamar yadda muka ɗauki siffar na turɓayar nan, haka kuma za mu ɗauki siffar na Saman nan. 50 Ina dai gaya muku wannan 'yan'uwa, ba shi yiwuwa jiki mai tsoka da jini ya sami gādo a Mulkin Allah, haka kuma mai ruɓa ba ya gādon marar ruɓa. 51 Ga shi, zan sanar da ku wani asiri! Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, amma dukanmu za a sauya kamanninmu, 52 farat ɗaya da ƙyiftawar ido, da jin busar ƙaho na ƙarshe, domin za a busa ƙaho, za a kuma ta da matattu da halin rashin ruɓa, za a kuma sauya kamanninmu. 53 Domin lalle ne, marar ruɓa ya maye mai ruɓar nan, marar mutuwa kuma ya maye mai mutuwar nan. 54 Sa'ad da kuma marar ruɓa ya maye mai ruɓar nan, marar mutuwa kuma ya maye mai mutuwar nan, a sa'an nan ne fa maganar nan da take a rubuce za a cika ta, cewa, “An shafe mutuwa da aka ci nasararta da ita.” 55 “Ke mutuwa, ina nasararki? Ke mutuwa, ina ƙarinki?” 56 Ai, zunubi shi ne ƙarin mutuwa, Shari'a kuwa ita ce sanadin ƙarfin zunubi. 57 Godiya tā tabbata ga Allah wanda take ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu. 58 Don haka, ya 'yan'uwana, ƙaunatattu, ku tsaya a kafe, kullum kuna himmantuwa ga aikin Ubangiji, domin kuwa kun san famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.

1 Korantiyawa 16

Gudunmawa ga Tsarkaka

1 To, a yanzu kuma ga zancen ba da gudunmawa ga tsarkaka, kamar yadda na umarci ikilisiyoyin Galatiya, haka ku ma za ku yi. 2 A kowace ranar farko ta mako, kowannenku ya riƙa tanada wani abu, yana ajiyewa gwargwadon samunsa, kada sai na zo tukuna, a tara gudunmawa. 3 Sa'ad da na iso, sai in aiki waɗanda kuka amince da su da wasiƙa, su kai taimakonku Urushalima. 4 In ya kyautu ni ma in tafi, to, sai su raka ni.

Shirye-shiryen Tafiya

5 Zan zo gare ku bayan na zazzaga ƙasar Makidoniya, don kuwa ta Makidoniya zan bi. 6 Watakila zan jima a wurinku, ko ma in ci damina, don ku yi mini rakiya duk da za ni. 7 Ba sona ne in gan ku a yanzu in wuce kawai ba, a'a, ina sa zuciya ma in yi kwanaki a wurinku, in Ubangiji ya yarda. 8 Amma zan dakata a Afisa har ranar Fentikos. 9 Don kuwa, an buɗe mini wata hanya mai fāɗi ta yin aiki mai amfani, akwai kuma magabta da yawa. 10 In Timoti ya zo, ku tabbata ya sami sakewa a cikinku, domin aikin Ubangiji yake yi kamar yadda nake yi. 11 Kada fa kowa ya raina shi. Ku raka shi lafiya, ya komo a gare ni, domin ina duban hanyarsa tare da 'yan'uwa. 12 Ga zancen ɗan'uwanmu Afolos kuwa, na roƙe shi ƙwarai, don ya zo wurinku, tare da saurar 'yan'uwa, amma ko kusa bai yi nufin zuwa a yanzu ba. Zai zo dai sa'ad da ya ga ya dace.

Gargaɗi da Gaisuwa

13 Ku zauna a faɗake, ku dāge ga bangaskiyarku, ku yi ƙwazo, ku yi ƙarfi. 14 Duk abin da za ku yi, ku yi shi da ƙauna. 15 To, 'yan'uwa, kun sani fa jama'ar gidan Istifanas su ne nunan fari a ƙasar Akaya, sun kuwa ba da kansu ga yi wa tsarkaka hidima. 16 Ina roƙonku ku yi wa irin waɗannan mutane biyayya, har ma ga duk waɗanda suke abokan aikinmu da wahalarmu. 17 Na yi farin ciki da zuwan Istifanas, da Fartunatas, da Akaikas, domin sun ɗebe mini kewarku. 18 Sun dai wartsakar da ni da kuma ku. Sai ku kula da irin waɗannan mutane. 19 Ikilisiyoyin ƙasar Asiya suna gaishe ku. Akila da Bilkisu, tare da ikilisiyar da ke taruwa a gidansu, suna gaishe ku da kyau da kyau saboda Ubangiji. 20 Dukan 'yan'uwa suna gaishe ku. Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba. 21 Ni Bulus, ni nake rubuta gaisuwar nan da hannuna. 22 Duk wanda ba ya ƙaunar Ubangiji yă zama la'ananne. Ubangijinmu fa suna zuwa! 23 Alherin Ubangijinmu Yesu yă tabbata a gare ku. 24 Ina gaishe ku duka, gaisuwar ƙauna, albarkar Almasihu Yesu.

2 Korantiyawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzon Almasihu Yesu da yardar Allah, da kuma ɗan'uwanmu Timoti, zuwa ga ikilisiyar Allah da take a Koranti, tare da dukan tsarkaka na duk ƙasar Akaya. 2 Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu tabbata a gare ku.

Godiyar Bulus bayan Shan Wuya

3 Godiya ta tabbata a gare shi, shi wanda yake Allah, da Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uba mai yawan jinƙai, Allah na dukan ta'aziyya, 4 shi da yake yi mana ta'aziyya a dukan wahalarmu, domin mu kuma mu iya ta'azantar da masu shan kowace irin wahala, da ta'aziyyar nan da mu ma muka samu a gun Allah. 5 Domin kuwa kamar yadda muke shan wuya ƙwarai, irin wadda Almasihu ya sha, haka kuma ake yi mana ta'aziyya ƙwarai, ta wurin Almasihu. 6 Ko ana wahalshe mu ma, ai, saboda ta'azantuwarku ce, da kuma lafiyarku. Ko ana ta'azantar da mu, ai, saboda ta'azantuwarku ce, wadda take sa ku, ku jure wa irin wuyan nan, da muke sha. 7 Sa zuciyarmu a kanku ƙaƙƙarfa ce, domin mun sani, kamar yadda kuka yi tarayya da mu a cikin shan wuya, haka kuma, za ku yi tarayya a cikin ta'aziyyar. 8 'Yan'uwa, ba ma so ku jahilta da wahalar da muka sha a ƙasar Asiya, domin kuwa mun ji jiki ƙwarai da gaske, har abin ya fi ƙarfinmu, har ma muka fid da tsammanin rayuwa. 9 Har ma muka ji kamar hukuncin kisa aka yi mana, wannan kuwa don kada mu dogara ga kanmu ne, sai dai ga Allah, mai ta da matattu. 10 Shi ne ya kuɓutar da mu daga muguwar mutuwa a fili, zai kuwa kuɓutar da mu, ga shi kuma muke dogara ya kuɓutar da mu har ila yau. 11 Ku ma sai ku taimake mu da addu'a, domin mutane da yawa su gode wa Allah, ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu'o'i masu yawa.

Bulus ya Dakatar da Ziyararsa

12 Fariyarmu ke nan, lamirinmu yana ba da shaida, cewa mun yi zaman tsarki a duniya da zuciya ɗaya, tsakani da Allah, tun ba mu a gare ku ba, ba bisa ga wayo irin na ɗan adam ba, sai dai bisa ga alherin Allah. 13 Domin wasiƙarmu zuwa gare ku, ba ta ƙunshi wani abu dabam ba, sai dai ainihin abin da kuka karanta kuka kuma fahimta, ina kuwa fata ku fahimta sosai da sosai, 14 kamar yadda kuka riga kuka ɗan fahimce mu, cewa kwa iya yin fāriya da mu, kamar yadda mu ma za mu iya yi da ku, a ranar Ubangijinmu Yesu. 15 Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu. 16 Wato niyyata in bi a kanku in zai ni Makidoniya, in kuma komo wurinku daga Makidoniya, sa'an nan ku yi mini rakiya in zan tafi Yahudiya. 17 Ashe, a lokacin da na yi niyyar yin haka, wato na nuna rashin tsai da zuciya ke nan? Ko kuwa shiririta nake yi kawai irin ta halin mutuntaka, in ce, “I” in koma in ce, “A'a?” 18 Yadda ba shakka Allah yake mai alkawari, haka ma maganar da muka yi muku, ba shiririta a ciki. 19 Domin kuwa, Ɗan Allah, Yesu Almasihu, wanda ni, da Sila, da Timoti muka yi muku wa'azi, ai, ba shiririta a game da shi, har kullum a kan gaskiya yake. 20 Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi take, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin,” domin a ɗaukaka Allah. 21 Domin kuwa, Allah shi ne mai tabbatar da mu da ku gaba ɗaya ga Almasihu, shi ne wanda ya shafe mu kuma. 22 Ya buga mana hatiminsa cewa mu nasa ne, ya kuma yi mana baiwa da Ruhunsa a zukatanmu, domin tabbatar da abin da zai yi a nan gaba. 23 Labudda, Allah shi ne mashaidina a kan cewa, musamman don sawwaƙe muku ne, na fāsa zuwa Koranti. 24 Ba cewa muna nuna muku iko a kan bangaskiyarku ba ne, a'a, sai dai muna aiki tare ne, domin ku yi farin ciki, domin a game da bangaskiyarmu kam, kuna tsaye kankan.

2 Korantiyawa 2

1 Na ƙudura a raina ba zan sāke zuwa wurinku in sa ku baƙin ciki ba. 2 To, in na sa ku baƙin ciki, wa zai faranta mini rai, in ba wanda na sa baƙin cikin ba? 3 Na rubuto muku haka ne, don kada in na zo, waɗanda ya kamata su faranta mini rai, ya zamana sun sa ni baƙin ciki. Domin na amince da ku duka, cewa farin cikina naku ne ku duka. 4 Na rubuto muku ne ina a cikin wahala da baƙin ciki gaya, har da hawaye mai yawa, ba don in sa ku baƙin ciki ba, sai dai domin ku san irin tsananin ƙaunar da nake yi muku.

Gafarta wa Mai Laifi

5 Amma in wani ya jawo baƙin ciki, ba ni kaɗai ya jawo wa ba, amma ga wani fanni, sai in ce dukanku ne ya jawo wa, ba tsanantawa nake yi ba. 6 Irin mutumin nan, horon nan da galibin jama'a suka yi masa, ai, ya isa haka. 7 Gara dai ku yafe masa, ku kuma ƙarfafa masa zuciya, don kada gayar baƙin ciki ya sha kansa. 8 Saboda haka, ina roƙonku ku tabbatar masa da ƙaunarku. 9 Na rubuto muku wannan takanas, domin in jarraba ku, in ga ko kuna yin biyayya ta kowace hanya. 10 Wanda kuka yafe wa kome, ni ma na yafe masa. Abin da na yafe kuwa, in dai har ma akwai abin yafewa, saboda ku ne na yafe masa, albarkacin Almasihu, 11 don kada Shaiɗan ya ribace mu, gama mu ba jahilan makidodinsa ba ne.

Alhinin Bulus a Taruwasa

12 To, sa'ad da na zo Taruwasa in yi bisharar Almasihu, ko da yake an buɗe mini hanya a cikin Ubangiji, 13 duk da haka dai hankalina bai kwanta ba, domin ban tarar da ɗan'uwana Titus a can ba, saboda haka, sai na yi bankwana da su, na zarce na tafi Makidoniya.

Nasara a cikin Almasihu

14 Amma godiya ta tabbata ga Allah, shi da kullum yake yi mana jagaba mu ci nasara, albarkacin Almasihu, ta wurinmu kuma yake baza ƙanshin nan, na sanin Almasihu a ko'ina. 15 Don kuwa, a gun Allah mu ne ƙanshin Almasihu a cikin waɗanda ake ceto, da waɗanda suke a hanyar hallaka. 16 Ga na ƙarshe ɗin, ƙanshin nan warin mutuwa ne, mai kaiwa ga hallaka, ga na farkon kuwa, ƙanshin rai ne mai kaiwa ga rai. To, wa zai iya ɗaukar nauyin waɗannan abubuwa? 17 Domin mu ba kamar mutane da yawa muke ba, masu yi wa Maganar Allah algus, mu kaifi ɗaya ne, kamar yadda Allah ya umarce mu, haka muke magana a gaban Allah, muna na Almasihu.

2 Korantiyawa 3

Masu Hidimar Sabon Alkawari

1 Wato, har ila yau, yabon kanmu za fara yi kuma? Ko kuwa muna bukatar wasiƙun yabo ne zuwa gare ku, ko daga gare ku, kamar yadda waɗansu suke yi? 2 Ai, ku kanku ku ne wasiƙarmu ta yabo, wadda aka rubuta a zukatanku, domin kowa yă san ta, ya kuma karanta ta. 3 A fili yake, ku wasiƙa ce ta Almasihu, ta hannunmu, ba kuwa rubutun tawada ba ne, amma na Ruhun Allah Rayayye ne, ba kuwa a kan allunan dutse aka rubuta ta ba, sai dai a zuci. 4 Wannan ita ce irin amincewarmu ga Allah ta wurin Almasihu. 5 Ba domin mun isar wa kanmu ba ne, har da za mu ce mu ne muke gudanar da wani abu, a'a, iyawarmu daga Allah take, 6 domin shi ne ya iyar mana muka zama masu hidima na Sabon Alkawari, ba alkawarin rubutacciyar ka'ida ba, sai dai na Ruhu. Don kuwa rubutacciyar ka'ida, kisa take yi, Ruhu kuwa, rayarwa yake yi. 7 Aka zana hidimar Shari'ar Musa, wadda ƙarshenta mutuwa ce, a allunan duwatsu. An bayyana hidimar nan da babbar ɗaukaka, har Isra'ilawa suka kasa duban fuskar Musa saboda tsananin haskenta (ga ta kuwa mai shuɗewa ce). 8 Ina misalin fifikon hidimar Ruhu mafi ɗaukaka? 9 Gama idan hidimar da take jawo hukunci abar ɗaukakawa ce, to lalle hidimar da take jawo samun adalcin Allah ta fi ta ɗaukaka nesa. 10 Hakika a wannan hali, abin da dā take da ɗaukaka ya rasa ɗaukaka sam, saboda mafificiyar ɗaukakar da ta jice ta. 11 Domin in aba mai shuɗewa an bayyana ta da ɗaukaka, ashe, abin da yake dawwamamme, lalle ne ya kasance da ɗaukakar da ta fi haka nesa. 12 Tun da yake muna da sa zuciya irin wannan, to, muna magana ne gabanmu gaɗi ƙwarai. 13 Ba kamar Musa muke ba, wanda ya rufe fuskarsa da mayafi, don kada Isr'ailawa su ga ƙarewar ɗaukakar nan mai shuɗewa. 14 Amma hankalinsu ya dushe, domin har ya zuwa yau, in ana karatun Tsohon Alkawari, mayafin nan har yanzu ba a yaye yake ba, domin ba ya yayuwa sai ta wurin Almasihu kaɗai. 15 Hakika har ya zuwa yau, duk lokacin da ake karatun littattafin Musa, sai mayafin nan yakan rufe zukatansu. 16 Amma da zarar mutum ya juyo ga Ubangiji, akan yaye masa mayafin. 17 To, Ubangiji fa shi ne Ruhu, a inda Ruhun Ubangiji yake kuma, a nan 'yanci yake. 18 Mu dukanmu kuma, fuskokinmu ba lulluɓi, muna nuna ɗaukakar Ubangiji, kamar madubi, ana sauya mu mu ɗauki kamanninsa cikin ɗaukaka mai hauhawa. Ubangiji kuwa wanda yake ruhu, yana zartar da haka.

2 Korantiyawa 4

Arziki a cikin Kasake

1 Saboda haka, da yake muna da wannan hidima bisa ga jinƙan Allah, ba za mu karai ba. 2 Ba ruwanmu ba ɓoye-ɓoye ne munafunci, ko makirci, ko yi wa Maganar Allah algus, amma ta wurin bayyana gaskiya a fili, sai kowane mutum ya shaidi gaskiyarmu a lamirinsa a gaban Allah. 3 Ko da bishararmu a rufe take, ai, ga waɗanda suke hanyar hallaka kaɗai take a rufe. 4 Su ne marasa ba da gaskiya, waɗanda sarkin zamanin nan ya makantar da hankalinsu, don kada hasken bisharar ɗaukakar Almasihu, shi da yake surar Allah, ya haskaka su. 5 Domin ba wa'azin kanmu muke yi ba, sai dai na Yesu Almasihu a kan shi ne Ubangiji, mu kuwa bayinku ne saboda Yesu. 6 Domin shi Allah wanda ya ce, “Haske yă ɓullo daga duhu ya haskaka,” shi ne ya haskaka zukatanmu domin a haskaka mutane su san ɗaukakarsa a fuskar Yesu Almasihu. 7 Wannan wadata da muke da ita kuwa, a cikin kasake take, wato, jikunanmu, don a nuna mafificin ikon nan na Allah ne, ba namu ba. 8 Ana wahalshe mu ta kowace hanya, duk da haka, ba a ci ɗunguminmu ba. Ana ruɗa mu, duk da haka ba mu karai ba. 9 Ana tsananta mana, duk da haka ba mu zama yasassu ba. Ana ta fyaɗa mu a ƙasa, duk da haka ba a hallaka mu ba. 10 Kullum muna a cikin hatsarin kisa, irin kisan da aka yi wa Yesu, domin a bayyana rayuwar Yesu ta gare mu. 11 Wato, muddin muna a raye, kullum zaman mutuwa muke yi saboda Yesu, domin a bayyana ran Yesu ta wurin jikin nan namu mai mutuwa. 12 Ta haka mutuwa take aikatawa a cikinmu, ku kuwa rai a cikinku. 13 Tun da yake muna da ruhun bangaskiya iri ɗaya da na wanda ya rubuta wannan, “Na gaskata, saboda haka na yi magana,” to, mu ma mun gaskata, saboda haka kuma muke magana. 14 Mun sani shi wannan da ya ta da Ubangiji Yesu daga matattu, mu ma zai tashe mu albarkacin Yesu, yă kuma kawo mu a gabansa tare da ku. 15 Duk wannan fa don amfaninku ne, domin alherin Allah ya yaɗu ga mutane masu yawa, ta haka ya zama sanadin yawaita godiya ga Allah, domin a ɗaukaka Allah.

Rayuwa ta wurin Bangaskiya

16 Saboda haka ba mu karai ba, ko da yake jikinmu na mutuntaka yana ta lalacewa, duk da haka, ruhunmu a kowace rana sabunta shi ake yi. 17 Don wannan 'yar wahalar tamu, mai saurin wucewa ita take tanadar mana madawwamiyar ɗaukaka mai yawa, fiye da kwatanci. 18 Domin ba abubuwan da ido yake gani muke dubawa ba, sai dai marasa ganuwa, gama abubuwan da ake gani, masu saurin wucewa ne, marasa ganuwa kuwa, madawwama na.

2 Korantiyawa 5

1 Gama mun sani in an rushe jikinmu na wannan duniya, Allah ya tanadar mana jiki a Sama, wato, wanda shi kansa ya yi, wanda zai dawwama. 2 A jikin nan muna ajiyar zuciya, mun ƙosa mu samu a suturta mu da jiki namu na Sama, 3 gama in aka suturta mu da shi, ba za a same mu tsirara ba. 4 Sa'ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, amma don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa. 5 Allah kuwa shi ya tanadar mana wannan sākewar, shi da ya ba mu Ruhunsa, domin tabbatar da abin da zai yi a nan gaba. 6 Saboda haka, kullum muke da ƙarfin zuciya, mun kuma sani, muddin muna tare da wannan jiki, a rabe muke da Ubangiji, 7 domin zaman bangaskiya muke yi, ba na ganin ido ba. 8 Hakika muna da ƙarfin zuciya, mun kuma gwammace mu rabu da jikin nan, mu zauna a gun Ubangiji. 9 Saboda haka, ko muna gunsa, ko muna a rabe da shi, burinmu shi ne mu faranta masa zuciya. 10 Don lalle ne a gabatar da mu duka, a gaban kursiyin shari'a na Almasihu, domin kowa ya sami sakamakon abin da ya yi tun yana tare da wannan jiki, ko mai kyau ne, ko kuma marar kyau.

Aikin Sulhuntawa

11 Da yake muna tsoron Ubangiji, shi ya sa muke ƙoƙarin rinjayar mutane. Yadda muke kuwa, ai, sananne ne ga Allah, muna fata ku ma haka abin yake a lamirinku. 12 Har wa yau kuma, ba yabon kanmu muke yi a gare ku ba, sai dai muna ba ku hanyar yin taƙama da mu, don ku sami yadda za ku mai da jawabi ga waɗanda suke fariya da maƙaminsu, ba da halinsu ba. 13 In hankalinmu ya fita, ai, saboda Allah ne, in kuwa a cikin hankalinmu muke, ai, ribarku ce. 14 Ƙaunar Almasihu a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu. 15 Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin waɗanda suke a raye, kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su. 16 Saboda haka, a nan gaba ba mā ƙara duban kowane mutum bisa ga ɗabi'ar jiki kawai, domin ko da yake mun taɓa duban Almasihu bisa ga ɗabi'ar jiki, yanzu ba ma ƙara dubansa haka. 17 Saboda haka, duk wanda yake na Almasihu sabuwar halitta ne, tsohon al'amari duk ya shuɗe, ga shi, kome ya zama sabo. 18 Duk wannan kuwa yin Allah ne, shi da ya sulhunta mu da kansa ta wurin Almasihu, ya kuma ba mu aikin shelar sulhuntawar, 19 wato, Allah ne, ta wurin Almasihu, yake sulhunta 'yan adam da shi kansa, ba ya kuwa lasafta laifofinsu a kansu ba, ya kuma danƙa mana maganar nan ta sulhuntawa. 20 Saboda haka, mu jakadu ne na Almasihu, wato, Allah na neman mutane ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Almasihu, ku sulhuntu da Allah. 21 Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi zunubi saboda mu, domin mu mu sami adalcin Allah ta wurinsa.

2 Korantiyawa 6

1 Da yake kuma muna aiki tare da Allah, muna roƙonku kada ku yi na'am da alherin Allah a banza. 2 Domin ya ce, “Na saurare ka a lokacin samun karɓuwa, Na kuma taimake ka a ranan ceto.” Ga shi, yanzu ne lokacin samun karɓuwa! Ga shi kuma, yau ce ranar ceto! 3 Ba ma zamar wa kowa sanadin tuntuɓe, don kada a aibata aikinmu, 4 Amma ta kowace hanya muna bayyana gaskiyarmu, a kan bayin Allah muke, ta matuƙar jurewa, da shan wahala, da ƙuntata, da masifu, 5 da shan d�ka, da shan ɗauri, da yawan hargitsi, da yawan fama, da rasa barci, da kuma rasa abinci. 6 Muna kuma bayyana gaskiyarmu ta halin tsarkaka, da sani, da haƙuri, da kirki, da Ruhu Mai Tsarki, da sahihiyar ƙauna, 7 da maganar gaskiya, da kuma ikon Allah. Muna riƙe da makaman adalci dama da hagu. 8 Ana ɗaukaka mu, ana kuma wulakanta mu, ana yabonmu, ana kuma kushenmu. An ɗauke mu kamar mayaudara, mu kuwa masu gaskiya ne. 9 Kamar ma ba a san mu ba, an kuwa san mu sarai, kamar a bakin mutuwa muke, ga shi kuwa, muna a raye, ana ta horonmu, duk da haka ba a kashe mu ba, 10 kamar muna baƙin ciki, kullum kuwa farin ciki muke yi, kamar matalauta muke, duk da haka kuwa muna arzuta mutane da yawa, kamar ba mu da kome, alhali kuwa kome namu ne. 11 Ya ku Korantiyawa, ba mu ɓoye muku kome ba, mun saki zuciya da ku ƙwarai. 12 Ai, ba wata rashin yarda a zuciyarmu, sai dai a taku. 13 Ina roƙonku kamar 'ya'yana, ku ma ku saki zuciya da mu.

Ku Haikalin Allah Ne

14 Kada ku yi cuɗanya marar dacewa da marasa ba da gaskiya. To, me ya haɗa aikin adalci da na mugunta? Ko kuwa me ya haɗa haske da duhu? 15 Ina kuma jiyayyar Almasihu da iblis? Me kuma ya haɗa mai ba da gaskiya da marar ba da gaskiya? 16 Wace yarjejeniya ce take a tsakanin Haikalin Allah da gumaka? Domin mu haikali ne na Allah Rayayye. Yadda Allah ya ce, “Zan zauna tare da su, in yi yawo a tsakaninsu, Zan kuma kasance Allahnsu, Su kuma su kasance jama'ata. 17 Saboda haka, sai ku fito daga cikinsu, Ku keɓe, in ji Ubangiji, Kada ku ko taɓa wani abu marar tsarki, Ni kuwa in yi na'am da ku, 18 In kasance Uba a gare ku, Ku kuma ku kasance 'ya'yana, maza da mata, In ji Ubangiji Maɗaukaki.”

2 Korantiyawa 7

1 Ya ku ƙaunatattu, tun da aka yi mana waɗannan alkawarai, sai mu tsarkake kanmu daga kowace irin ƙazanta ta jiki ko ta zuci, da bangirma ga Allah mu kamalta a cikin tsarki.

Bulus ya Yi Farin Ciki saboda Tubar Ikilisiya

2 Ku saki zuciya da mu, ai, ba mu cuci kowa ba, ba mu ɓata kowa ba, ba mu zambaci kowa ba. 3 Ba don in sa muku laifi na faɗi haka ba, don dā ma na gaya muku, abin ƙauna kuke a gare mu ƙwarai, ko a mace ko a raye, ba mu rabuwa. 4 Na amince da ku ƙwarai, ina kuma taƙama da ku gaya. Zuciyata ta ƙarfafa ƙwarai. Duk da wahalce-wahalcenmu dai ina farin ciki ƙwarai da gaske. 5 Ko a lokacin da muka zo ƙasar Makidoniya ma, ba mu sami shaƙatawa ba, ana ta wahalshe mu ta kowace hanya, a waje ga husuma, a zukatanmu kuma ga fargaba. 6 Amma Allah, shi da yake ƙarfafa wa ƙasƙantattu zuciya, sai ya ƙarfafa mana zuciya da zuwan Titus, 7 ba kuwa da zuwan Titus kawai ba, har ma a game da ƙarfafa zuciyar nan da ya samu a wurinku, a yayin da ya gaya mana yadda kuke begena, kuna nadama, kuna kuma himmantuwa ga goyan bayana, har ma na ƙara farin ciki ƙwarai. 8 Ko da na ɓata muku rai a game da wasiƙar da dā na rubuto muku, ba na baƙin ciki da haka, ko da yake dā kam na yi baƙin ciki, don na lura wasiƙar nan ta ɓata muku rai, ko da yake dai zuwa ɗan lokaci kaɗan ne. 9 Amma a yanzu kam, ina farin ciki, ba don kun yi baƙin ciki ba, sai dai don baƙin cikinmu ya sa ku tuba, don kun yi baƙin ciki irin wanda Allah yake so. Saboda haka, ba ku yi hasarar kome a sanadinmu ba. 10 Don baƙin ciki irin wanda Allah yake sawa, shi ne yake biyarwa zuwa ga tuba, da kuma samun ceto, ba ya kuma sa “da na sani.” Amma baƙin ciki a kan al'amarin duniya, yakan jawo mutuwa. 11 Ku dubi fa irin himmar da baƙin cikin nan, da Allah yake so ya sa a zukatanku, da irin ɗokin da kuka yi na gyara al'amuranku, da irin haushin da kuka ji, da irin tsoron da kuka ji, da irin begen da kuka yi, da irin himmar kuka yi, da kuma irin niyyarku ta horo. A game da wannan sha'ani kam, lalle ta kowace hanya kun nuna cewa ba ku da laifi. 12 To, ko da yake na rubuto muku wasiƙa, ba musamman a kan wanda ya yi laifin ba ne, ba kuwa a kan wanda aka cutar ba, sai dai domin a bayyana muku a gaban Allah tsananin kula da kuke yi mana. 13 Saboda haka ne zukatanmu suka ƙarfafa. Banda ƙarfafa zukatanmu kuma, har wa yau mun ƙara farin ciki ƙwarai, saboda farin cikin Titus, don dukanku kun wartsakar da shi. 14 Don ko da na gaya masa cewa, ina 'yar taƙama da ku, ban kunyata ba. Kamar yadda duk abin da muka gaya muku gaskiya ne, haka kuma taƙamarmu da ku a idon Titus ma ta zama gaskiya. 15 Ransa kuma yana a gare ku fiye da dā ƙwarai, duk sa'ad da yake tunawa da biyayyarku, ku duka, da kuma yadda kuka yi na'am da shi a cikin halin bangirma tare da matsananciyar kula. 16 Ina farin ciki ne don na amince da ku ƙwarai da gaske.

2 Korantiyawa 8

Bayarwa bisa ga Ra'ayi

1 To, 'yan'uwa, muna so mu sanar da ku alherin Allah da ya bayar a cikin ikilisiyoyin Makidoniya, 2 wato, ko da yake an gwada su da matsananciyar wahala, suna kuma a cikin baƙin talauci, duk da haka, yawan farin cikinsu, har ya kai su ga yin alheri ƙwarai da gaske. 3 Domin na tabbata daidai ƙarfinsu suka bayar, har ma fiye da ƙarfinsu ne, da ra'insu kuma. 4 Sun roƙe mu ƙwarai da gaske mu yi musu alheri su ma, a sa su a cikin masu yi wa tsarkaka gudunmawa, 5 har ma suka bayar fiye da yadda muka zata, amma sai da suka fara miƙa kansu ga Ubangiji da a gare mu kuma, bisa ga nufin Allah. 6 Ganin haka sai muka roƙi Titus, da yake shi ne ya riga ya tsiro da wannan aikin alheri a cikinku, sai yă ƙarasa shi. 7 To, da yake kun fifita a kowane abu, wato, a cikin bangaskiya, da magana, da sani, da matuƙar himma, da kuma ƙaunar da kuke yi mana, to, sai ku fifita a wannan aikin alheri ma. 8 Ba kallafa muku wannan nake yi ba, sai dai ta nuna himmar waɗansu, in tabbata ƙaunarku ma sahihiya ce. 9 Domin kun san alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu, ko da yake shi mawadaci ne, sai ya zama matalauci sabili da ku, domin ta wurin talaucinsa ku wadata. 10 A wannan al'amari, ga shawarata. Ai, ya fiye muku a yanzu ku ƙarasa abin da kuka fara yi a bara, har kuka yi da ra'inku. 11 To, sai ku ƙarasa aikin da irin ra'in da kuka fara, gwargwadon ikonku. 12 Domin mutum yana da niyyar bayarwa, bayarwarsa za ta zama abar karɓa ce, bisa ga yawan abin da yake da shi, ba bisa ga abin da ba shi da shi ba. 13 Ba nufi nake yi a sawwaƙe wa waɗansu, ku kuwa a jibga muku nauyin ba. 14 Amma don a raba daidai wa daida, sai ku taimake su a yanzu da yalwarku saboda rashinsu, don wata rana su ma su taimake ku da yalwarsu saboda rashinku, don a daidaita al'amari. 15 Yadda yake a rubuce cewa, “Wanda ya tara mai yawa, bai fi bukatarsa ba, wanda ya tara kaɗan kuwa, ba abin da ya gaza masa.”

Titus da Abokansa

16 Godiya tā tabbata ga Allah wanda ya sa tsananin kula da ku a zuciyar Titus, kamar yadda nake yi. 17 Ba kuwa na'am da roƙonmu kaɗai ya yi ba, har ma saboda tsananin himma tasa yana zuwa wurinku da ra'in kansa. 18 Ga shi, mun aiko ɗan'uwan nan tare da shi, wanda ya yi suna wajen yin bishara a dukan ikilisiyoyi, 19 ba kuwa haka kaɗai ba, har ma ikilisiyoyi sun zaɓe shi ya riƙa tafiya tare da mu kan wannan aikin alheri da muke yi saboda ɗaukakar Ubangiji, da kuma nuna kyakkyawar niyyarmu. 20 Wato muna gudun kada kowa ya zarge mu a kan kyautan nan da ake yi hannu sake, wadda muke kasaftawa. 21 Niyyarmu ce mu yi abubuwan da ke daidai, ba wai a gaban Ubangiji kaɗai ba, har ma a gaban mutane. 22 Muna kuma aiko da ɗan'uwanmu tare da su, wanda sau da yawa muka tabbatar da himma tasa ta hanya iri iri, yanzu kuma ya fi koyaushe himma, domin amincewa da ku da yake yi ƙwarai da gaske. 23 Titus kuwa, ai, abokin tarayyata ne, abokin aikina kuma game da al'amuranku. 'Yan'uwan nan namu kuwa, ai, manzanni ne na ikilisiyoyi, masu ɗaukaka Almasihu. 24 Saboda haka sai ku tabbatar wa waɗannan mutane a gaban ikilisiyoyi irin ƙaunarku, da kuma cewa taƙama da ku da muke yi gaskiya ce.

2 Korantiyawa 9

Gudunmawa ga Tsarkaka

1 Ba sai lalle na rubuto muku zancen gudunmawa ga tsarkaka ba, 2 domin na san niyyarku, har ma ina taƙama da ku gun mutanen Makidoniya a kan haka, ina ce musu Ikilisiyar Akaya ta yi shiri tun bara, ƙwazonku kuwa ya ta da yawancinsu. 3 Amma ma aiko da 'yan'uwan nan, don kada gadarar da muke yi da ku a wannan al'amari ta zama banza, domin ku zauna a kan shiri, kamar yadda dā na ce za ku zauna. 4 Don kada ya zamana in waɗansu mutanen Makidoniya sun zo tare da ni, suka tarar ba ku shirya ba, kunya ta ishe mu, balle fa ku, saboda amincewa da muke yi da ku. 5 Saboda haka, na dai ga lalle ne in roƙi 'yan'uwan nan su riga ni zuwa a gare ku, su tanada baiwar nan da kuka yi alkawari kafin in zo, domin a same ta a shirye, ba tare da matsawa ba, sai dai kyautar sa kai. 6 Abin la'akari fa, shi ne wanda ya yi ƙwauron yafa iri, gonarsa za ta yi masa ƙwauron amfani, wanda kuwa ya yafa a yalwace, sai ya girba a yalwace. 7 Sai kowa yă bayar yadda ya yi niyya, ba tare da ɓacin rai ko tilastawa ba, domin Allah yana son mai bayarwa da daɗin rai. 8 Allah kuwa yana da iko ya ba ku fiye da bukatarku, domin kullum ku wadata da kome ta kowace hanya, kuna ta bayarwa hannu sake, kowane irin kyakkyawan aiki. 9 Kamar yadda yake a rubuce cewa, “Ya ba gajiyayyu hannu sake, ayyukansa na alheri madawwama ne.” 10 Shi da yake ba mai shuka iri, yake kuma ba da abinci a ci, shi ne zai ba ku irin shukawa, ya riɓanya shi, ya kuma yawaita albarkar ayyukanku na alheri. 11 Za a wadata ku ta kowace hanya, domin ku riƙa bayarwa a yalwace, bayarwar nan kuwa da za ku yi, za ta zama sanadin godiya ga Allah ta wurinmu. 12 Domin aikin nan na alheri, ba biyan bukatar tsarkaka kaɗai yake yi ba, har ma yana ƙara yawaita godiya ga Allah ƙwarai da gaske. 13 Aikin nan naku alheri tabbatar bangaskiyarku ne, za a kuwa ɗaukaka Allah saboda kun bayyana yarda, cewa kun yi na'am da bisharar Almasihu, saboda kuma gudunmawa da kuka yi musu da saura duka, hannu sake. 14 Su kuwa za su yi muku addu'a, su yi ɗokin ganinku saboda alherin Allah marar misaltuwa da ya yi muku. 15 Godiya tā tabbata ga Allah saboda baiwarsa da ta fi gaban a faɗa.

2 Korantiyawa 10

Bulus ya Ƙare Aikinsa

1 Ni Bulus da kaina, ina roƙonku albarkacin tawali'u da sanyin hali na Almasihu, ni da ake yi wa kirari “marar tsanani” ne a cikinku, amma “mai matsawa” ne sa'ad da nake rabe da ku, 2 ina roƙonku kada ku tilasta ni in matsa muku sa'ad da na zo, gama na tabbata zan iya tsaya wa waɗanda suka ce abin da muke yi sha'anin duniya ne. 3 Ko da yake a cikin jiki muke tafiya, famarmu ba irin na mutuntaka ba ne. 4 Don kuwa makamanmu na fama ba na mutuntaka ba ne, na ikon Allah ne, masu rushe maƙamai masu ƙarfi. 5 Muna ka da masu hujjoji a cikin zace-zacensu, muna rushe kowace ganuwar alfarma mai tare sanin Allah, muna kuma jan hankalin kowa ga bautar Almasihu. 6 A shirye muke kuma mu hori kowane marar biyayya, muddin biyayyarku ta tabbata. 7 Ku dubi abin da yake bayyane mana! In dai wani ya amince na Almasihu ne, to, ya ƙara tunawa, wato kamar yadda yake shi na Almasihu ne, mu ma haka muke. 8 Ko da zan gadara fiye da kima a game da izinin nan namu, wanda Ubangiji ya bayar saboda inganta ku, ba don rushe ku ba, ba zan kunyata ba. 9 Kada fa a ga kamar ina tsorata ku da wasiƙu ne. 10 Don waɗansu suna cewa, “Wasiƙunsa masu ratsa jiki ne, masu ƙarfi, amma kuwa in ka gan shi ba shi da kwarjini, maganarsa kuma ba wata magana ba ce.” 11 Irin mutanen nan dai su fahimci yadda abin da muke faɗa a cikin wasiƙa sa'ad da ba ma nan, shi muke aikatawa sa'ad da muke nan. 12 Wane mu mu daidaita kanmu, ko mu gwada kanmu da waɗansu masu yabon kansu! Ashe, waɗannan mutane masu auna kansu da juna, suna kuma neman bambanci a tsakaninsu da juna, ba su da basira. 13 Amma dai ba za mu yi alfarma fiye da yadda ya kamata ba, sai dai mu tsaya a kan iyakar da Allah ya yanke mana, wadda ta game har da ku. 14 Ai, ba mu wuce gona da iri ba, kamar ba a hannunmu kuke ba, domin mu ne muka fara shan nisa, muka je a gare ku da bisharar Almasihu. 15 Fahariyarmu ba fiye da yadda ya kamata take ba, ba ta kuma shafi aikin waɗansu ba. Amma muna sa zuciya bangaskiyarku ta riƙa ƙaruwa, ta haka kuma fagan aikinmu a cikinku ya riƙa ƙaruwa ƙwarai da gaske, 16 har ma mu samu mu yi bishara a ƙasashen da suke a gaba da ku, ba tare da wata fahariya da aikin da wani ya riga ya yi a fagensa ba. 17 Amma, “Duk mai yin fahariya, ya yi fahariya da Ubangiji.” 18 Ai, ba mai yabon kansa ake yarda da shi ba, sai dai wanda Ubangiji ya yaba wa.

2 Korantiyawa 11

Bulus da Manzannin Ƙarya

1 Da ma a ce ku jure 'yar wautata. Ku dai yi haƙuri da ni! 2 Ina kishi a kanku saboda Allah. Gama na bashe ku ga Almasihu, domin in miƙa ku kamar amarya tsattsarka ga makaɗaicin mijinta. 3 Amma ina tsoro kada ya zamana, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa'u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Almasihu. 4 Don in wani ya zo yana wa'azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa'azi, ko kuma in kun sami wani ruhu dabam da Ruhun da kuka samu, ko wata bishara dabam da wadda kuka yi na'am da ita, ashe, har kuna saurin yin na'am da irinsu ke nan! 5 A ganina ban kasa mafifitan manzannin nan da kome ba. 6 Ko da yake ni bami ne a wajen yin magana, a wajen sani kam, ba haka ba ne, mun kuwa bayyana wannan sarai ta kowace hanya a cikin dukan sha'aninmu da ku. 7 Ashe, laifi na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaukaka ku, wato saboda na yi muku bisharar Allah a kyauta? 8 Waɗansu ikilisiyoyi na biyan hakkina, sai ka ce ina yi musu ƙwace domin in yi muku hidima. 9 Sa'ad da nake a wurinku kuma nake zaman rashi, ban nauyaya wa kowa ba, domin 'yan'uwan da suka zo daga Makidoniya su ne suka biya mini bukata. Saboda haka, na ƙi nauyaya muku ta kowace hanya, ba kuwa zan nauyaya muku ba. 10 Albarkacin gaskiyar Almasihu da yake tare da ni, ba mai hana ni fahariyar nan tawa a lardin Akaya. 11 To, don me? Domin ba na ƙaunarku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku. 12 Abin da nake yi kuwa, shi zan riƙa yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su. 13 Irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, mayaudaran ma'aikata, suna mai da kansu kamar su manzannin Almasihu ne. 14 Ba abin mamaki ba ne kuwa, domin ko Shaiɗan ma da kansa, yakan mai da kansa kamar shi mala'ikan haske ne. 15 Don haka, ba abin mamaki ba ne in bayinsa ma sun mai da kansu kamar su bayi ne na aikin adalci. A ƙarshe za a saka musu gwargwadon ayyukansu.

Wahalar Bulus saboda Manzanci

16 Ina sāke faɗa, kada wani ya zaci ni wawa ne. In kuwa kun zaci haka nake, to, ku ji ni wawa ne, don ni ma in samu in taɓa 'yar taƙama kaɗan. 17 Abin nan da nake faɗa fa, ba bisa ga umarnin Ubangiji nake faɗa ba, sai dai magana ce irin ta wawa, wadda yake yi gabagaɗi, yana fariya, 18 da yake mutane da yawa suna fariya irin ta 'yan adam kawai, ni ma zan yi. 19 Ai, ku kam, hikimarku har ta kai ga jure wa wawaye da murna! 20 Don in wani ya sa ku bauta, kukan jure masa, ko ya yi muku ƙwace, ko ya more ku, ko ya nuna muka isa, ko kuwa ya mare ku. 21 Mu kam, saboda rauninmu, wane mu da yin haka! Amma ta ko yaya wani yake ƙarfin halin yin fariya, ina magana a kan ni wawa ne fa! To, ni ma sai in yi. 22 In su Ibraniyawa ne, ni me haka. In su Isra'ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka. 23 In su bayin Almasihu ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan ɗauri, na sha d�ka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri iri. 24 Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba'in ɗaya babu. 25 Sau uku aka bulale ni da tsumagu, sau ɗaya har aka jejjefe ni da dutse. Sau uku jirgi ya ragargaje ina ciki, na kwana na yini ruwan bahar yana tafiya da ni. 26 Na yi tafifiya da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin 'yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al'ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a bahar, na kuma sha hatsarin 'yan'uwa na ƙarya. 27 Na sha fama, na sha wuya, na sha rashin barci, na sha yunwa da ƙishirwa, sau da yawa na rasa abinci, na sha sanyi da huntanci. 28 Banda waɗansu abubuwa dabam kuma, kowace rana ina a matse da matsananciyar kula saboda dukan ikilisiyoyi. 29 Wane ne ya raunana da ban raunana ba? Wane ne aka sa tuntuɓe, ban ji zafin ba? 30 In ma lalle ne in yi gadara, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suke nuna raunanata. 31 Allahn Ubangiji Yesu, wato Ubansa, wanda ya yabo ya tabbata a gare shi har abada, ya sani ba ƙarya nake yi ba. 32 A Dimashƙu gwamnan da yake ƙarƙashin sarki Aretis ya tsare ƙofofin birnin Dimashƙu don ya kama ni, 33 amma sai aka zura ni a cikin babban kwando ta tagar garu, na kuɓuce masa.

2 Korantiyawa 12

Wahayan Bulus da Bayani Iri Iri

1 An tilasta mini ne in gadara, ko da yake ba ta amfane ni da kome ba. Amma zan ci gaba da zancen ruya da wahayi da Ubangiji ya yi mini. 2 Na san wani mutum wanda yau shekara goma sha huɗu ke nan, aka ɗauke shi zuwa Sama ta uku bisa ga ikon Almasihu, ko yana a cikin jiki ne, ko ba a cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ne masani. 3 Na kuma san mutumin na, an ɗauke shi zuwa Firdausi, ko yana a cikin jiki ne, ko ba a cikin jiki ba, ban sani ba, Allah ne masani, 4 ya kuma ji waɗansu maganganu, waɗanda ba dama a faɗa, irin ma waɗanda ɗan adam ba shi da izinin faɗa. 5 Zan yi gadara da mutumin nan kam, amma ba zan yi gadara da kaina ba, sai dai ko da raunanata. 6 Ko da zan so yin gadara ma, ba zan zama wawa ba, gama gaskiya zan faɗa. Amma na bar zancen haka, don kada wani ya ɗauke ni fiye da yadda yake ganina, ko yadda yake jin maganata. 7 Don kada kaina ya kumbura kuma saboda mafifitan wahayan da aka yi mini, sai aka saka mini wata cuta, wadda ta zama mini ƙaya, jakadan Shaiɗan, don yă riƙa wahalshe ni, don kada kaina ya kumbura. 8 Sau uku nake roƙon Ubangiji a kan wannan abu ya rabu da ni, 9 amma ya ce mini, “Alherina yā isa, domin ta wajen rashin ƙarfi ake ganin cikar ikona.” Saboda haka sai ma in ƙara yin alfarma da raunanata da farinciki fiye da na da, domin ikon Almasihu ya zauna a tare da ni. 10 Saboda haka, ina murna da raunanata, da cin mutuncin da ake yi mini, da shan wuya, da shan tsanani, da masifu saboda Almasihu, don sa'ad da nake rarrauna, a sa'an nan ne nake da ƙarfi.

Alhinin Bulus a kan Ikilisiyar Koranti

11 Na yi wauta kam, amma ku ne kuke tilasta mini, ku ne kuwa ya kamata ku yaba mini, domin ba a inda na kasa waɗannan mafifitan manzanni, ko da yake ni ba kome ba ne. 12 An gudanar da tabbatattun alamun manzo a cikinku ta matuƙar jimiri, da alamu da abubuwan al'ajabi da mu'ujizai. 13 Ta wace hanya ce kuka kasa sauran ikilisiyoyi? Ko kuwa domin dai ni ban nauyaya muku ba? To, ku yafe mini wannan laifi! 14 Ga shi, na yi shirin zuwa wurinku, zuwa na uku, ba kuwa zan nauyaya muku ba, don ba abinku nake nema ba, ku nake nema, domin ba yara ne da ɗaukar nauyin iyayensu ba, sai dai iyaye ne da ɗaukar nauyin yaran. 15 Ni kam, zan kashe dukan abin hannuna da dukan zarafina da matuƙar farin ciki saboda ranku. In na ƙara ƙaunarku, ashe, sai a rage ƙaunata? 16 To, a ce ban nauyaya muku ba ɗin, ashe, sai ku ce dabara na yi muku, na shawo kanku ta hanyar yaudara! 17 Na cuce ku ne ta wurin wani daga cikin waɗanda na aiko a gare ku? 18 Na roƙi Titus ya je, na kuma aiko ɗan'uwan nan tare da shi. To, Titus ya cuce ku ne? Ashe, ba Ruhu ɗaya yake bi da mu ba, ni da shi? Ba kuma hanya ɗaya muke bi ba? 19 Ashe, tun dā tsammani kuke yi muna kawo hanzarinmu a gare ku ne? A'a, a gaban Allah muke magana, muna na Almasihu, wannan kuwa duk domin inganta ku ne, ya ku ƙaunatattu. 20 Ina tsoro kada watakila in na zo in same ku ba a yadda nake so ba, ku kuma ku gan ni ba a yadda kuke so ba, ko ma a tarar da jayayya, da kishi, da fushi, da sonkai, da yanke, da tsegunguma, da girmankai, da tashin hankali. 21 Ina tsoro kada in na sāke zuwa, Allahna ya ƙasƙanta ni a gabanku, in kuma yi baƙin ciki saboda waɗansu da yawa da suka yi zunubi a dā, ba su kuwa tuba da aikinsu na lalata ba, da fasikancinsu, da fajircinsu da suka aikata.

2 Korantiyawa 13

Kashedi da Gaisuwa

1 Wannan shi ne zai zama zuwana na uku a gare ku. Lalle ne kuwa a tabbatar da kowace magana a bakin shaidu biyu ko uku. 2 Na gargaɗi waɗanda suka yi zunubi a dā, da kuma saura duka, a yanzu kuma da ba na nan ina yi musu gargaɗi, kamar yadda na yi sa'ad da nake nan a zuwana na biyu, cewa in na sāke zuwa ba zan sawwaƙe musu ba. 3 In dai nema kuke yi ku tabbata, cewa da izinin Almasihu nake magana, to, ai, shi ba rarrauna ba ne a gare ku, amma ƙaƙƙarfa ne a cikinku. 4 Ko da yake an gicciye shi ne da rashin ƙarfi, duk da haka a raye yake ta ikon Allah. Mu ma marasa ƙarfi ne kamarsa, amma a game da al'amuranku da za mu zartar, a raye muke tare da shi, ta ikon Allah. 5 Ku jarraba kanku ku gani, ko har yanzu kuna a raye da bangaskiya. Ku riƙa auna kanku. Ashe, ba ku tabbata Almasihu yana a cikinku ba? Sai ko in kun kasa ga gwajin! 6 Muna fata ku gane, mu ba mu kāsa ba. 7 Amma muna roƙon Allah kada ku yi wani mugun abu, ba don mu mu zama kamar mun ci gwajin kawai ba, sai dai domin ku yi abin da yake daidai, ko da yake za ku ga kamar mun kāsa. 8 Domin ba dama mu sāɓa wa gaskiya, sai dai mu bi bayan gaskiyar. 9 Gama farin ciki muke yi in muna raunana, ku kuna ƙarfafa. Addu'armu ita ce ku kammala. 10 Ina rubuta wannan ne sa'ad da ba na tare da ku, domin sa'ad da na zo, kada ya zama mini tilas in yi muku tsanani a game da nuna ikon nan da Ubangiji ya ba ni saboda ingantawa, ba saboda rushewa. 11 Daga ƙarshe kuma, 'yan'uwa, sai wata rana. Ku kammala halinku. Ku kula da roƙona, ku yi zaman lafiya da juna, ku yi zaman salama, Allah mai zartar da ƙauna da salama kuwa zai kasance a tare da ku. 12 Ku gaggai da juna da tsattsarkar sumba. 13 Dukan tsarkaka suna gaishe ku. 14 Alherin Ubangiji Yesu Almasihu, da ƙaunar Allah, da zumuntar Ruhu Mai Tsarki su tabbata a gare ku duka.

Galatiyawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzo, ba kuwa manzon mutum ba, ba kuma ta wurin wani mutum ba, sai dai ta wurin Yesu Almasihu, da Allah Uba, wanda ya tashe shi daga matattu, 2 da kuma dukan 'yan'uwa da suke tare da ni, zuwa ga ikilisiyoyin ƙasar Galatiya. 3 Alheri da salama na Allah Uba su tabbata a gare ku, da na Ubangijinmu Yesu Almasihu, 4 wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu, domin ya cece mu daga mugun zamanin nan, bisa ga nufin Allahnmu, wato Ubanmu. 5 Ɗaukaka tă tabbata a gare shi har abada abadin. Amin.

Ba wata Bishara

6 Na yi mamaki yadda nan da nan kuke ƙaurace wa wanda ya kira ku, bisa ga alherin Almasihu, har kuna koma wa wata baƙuwar bishara, 7 alhali kuwa ba wata bishara dabam, sai dai akwai waɗansu da suke ta da hankalinku, suna son jirkitar da bisharar Almasihu. 8 Amma ko mu, ko kuma wani mala'ika daga sama, in waninmu zai yi muku wata bishara dabam da wadda muka yi muku, to, yă zama la'ananne! 9 Kamar yadda muka faɗa a dā, haka yanzu ma nake sāke faɗa, cewa kowa ya yi muku wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, to, yă zama la'ananne! 10 To, wato ni son mutane nake nema ne, ko kuwa na Allah? Ko kuwa ƙoƙari nake yi in faranta wa mutane zuciya? Da har yanzu mutane nake faranta wa zuciya, ai, da ban zama bawan Almasihu ba.

Shigar Bulus Manzanci

11 Ina so in sanar da ku, 'yan'uwa, bisharar nan da na sanar ba ta ɗan adam ba ce, 12 domin ba daga wurin mutum na samo ta ba, ba kuma koya mini ita aka yi ba, sai dai ta wurin bayyanar Yesu Almasihu a gare ni ne na same ta. 13 Kun dai ji irin zamana na dā a cikin addinin yahudanci, yadda na riƙa tsananta wa Ikilisiyar Allah ƙwarai da gaske, har ina ta watsa ta, 14 yadda kuma a cikin addinin Yahudanci har na tsere wa yawancin tsararrakina a cikin mutanenmu, na himmantu ƙwarai da gaske ga bin al'adun kakanninmu. 15 Amma sa'ad da shi wannan da ya keɓe ni tun kafin a haife ni, ya kuma kira ni bisa ga alherinsa, ya ji daɗin 16 bayyana Ɗansa a gare ni, domin in sanar da shi ga al'ummai, ban yi shawara da ɗan adam ba, 17 ban kuma je Urushalima wurin waɗanda suka riga ni zama manzanni ba, sai nan da nan na je ƙasar Larabawa, sa'an nan na komo Dimashƙu. 18 Bayan shekara uku kuma sai na tafi Urushalima ganin Kefas, na kuwa kwana goma sha biyar a gunsa. 19 Amma ban ga ko ɗaya a cikin sauran manzanni ba, sai dai Yakubu ɗan'uwan Ubangiji. 20 Abin nan da nake rubuto muku fa, ba ƙarya nake yi ba, a gaban Allah nake faɗa. 21 Daga baya kuma, na tafi ƙasar Suriya da ta Kilikiya. 22 Amma kuwa ikilisiyoyin Almasihu da suke a ƙasar Yahudiya, ba su san ni ido da ido ba tukuna. 23 Sai dai kawai sun ji an ce, “Wanda dā yake tsananta mana, ga shi, a yanzu yana sanar da bangaskiyar nan da dā yake ta rusawa!” 24 Sai suka ɗaukaka Allah saboda ni.

Galatiyawa 2

Sauran Manzanni sun Karɓi Bulus

1 Bayan shekara goma sha huɗu na sāke komawa Urushalima tare da Barnaba, na kuma ɗauki Titus. 2 Da umarnin wahayi ne na tafi, har na rattaba musu bisharar da nake yi a cikin al'ummai, amma a keɓance a gaban waɗansu shugabannin ikilisiya, kada himmar da nake yi, ko wadda na riga na yi, ta zamana ta banza ce. 3 Kai, ko Titus ma da yake a tare da ni, ba a tilasta masa yin kaciya ba, ko da yake shi Bahelene ne. 4 Maganar nan ta tashi saboda 'yan'uwan ƙaryar nan ne, da aka shigo da su a asirce, waɗanda suka saɗaɗo su yi ganganen 'yancinmu da muke da shi ta wurin Almasihu Yesu, don dai su sa mu bauta. 5 Amma ko kaɗan ba mu sakar musu ba, ko da taƙi, domin gaskiyar bishara tă zaune muku. 6 Waɗanda kuma aka ɗauka a dā a kan su wani abu ne (ko su wane ne, ai, duk ɗaya ne a guna, domin Allah ba ya tāra), ina dai gaya muku waɗannan da suke wani abu ne a dā, ba su ƙare ni da kome ba. 7 Amma da suka ga an amince mini in yi wa marasa kaciya bishara, kamar yadda aka amince wa Bitrus ya yi wa masu kaciya bishara, 8 (domin shi da ya yi aiki a zuciyar Bitrus ya sa shi manzo ga masu kaciya, shi ne kuma ya yi aiki a zuciyata, ya sa ni manzo ga al'ummai), 9 sai Yakubu da Kefas da Yahaya, su da suke shahararrun ginshiƙan ikilisiya, da suka ga alherin da Allah ya yi mini, sai suka karɓe mu, ni da Barnaba, hannu biyu biyu, domin mu mu je wurin al'ummai, su kuwa gun masu kaciya. 10 Sai dai kuma suna so mu tuna matalauta, wannan kuwa ko dā ma ina da himmar yi ƙwarai.

Bulus ya Tsawata wa Bitrus a Antakiya

11 Amma da Kefas ya zo Antakiya, sai na tsaya masa fuska da fuska don laifinsa a fili yake. 12 Don kafin waɗansu su zo daga wurin Yakubu, yakan ci abinci da al'ummai. Amma da suka zo, ya janye jiki ya ware kansa, yana tsoron ɗariƙar masu kaciyar nan. 13 Haka ma sauran Yahudawa masu bi suka nuna fuska biyu kamarsa, ko da Barnaba ma sai da suka ciwo kansa da munafuncinsu. 14 Amma da na ga dai ba sa bin gaskiyar bishara sosai, na ce wa Kefas a gaban idon kowa, “Kai da kake Bayahude, in ka bi al'adar al'ummai ba ta Yahudawa ba, yaya kake tilasta wa al'ummai su bi al'adar Yahudawa?

Ceton Yahudawa duk da Al'ummai ta wurin Bangaskiya

15 “Mu da aka haifa Yahudawa, ba al'ummai masu zunubi ba, 16 da yake mun sani mutum ba ya samun kuɓuta ga Allah ta wurin bin Shari'a, sai dai ta wurin gaskatawa ga Yesu Almasihu kaɗai, mu ma mun gaskata da Almasihu Yesu, domin mu sami kuɓuta ga Allah ta wurin bangaskiya ga Almasihu, ba ta wurin bin Shari'a ba, don ba ɗan adam ɗin da zai sami kuɓuta ga Allah ta hanyar bin Shari'a. 17 In kuwa ya zamana, sa'ad da muke neman kuɓuta ga Allah ta wurin Almasihu, an tarar har mu kanmu ma masu zunubi ne, ashe, Almasihu yana hidimar zunubi ne? A'a, ko kusa! 18 Amma in na sāke ginin abin da dā na rushe, na tabbata mai laifi ke nan. 19 Gama ni ta wurin Shari'a matacce ne ga Shari'a domin in rayu ga Allah. 20 An gicciye ni tare da Almasihu. Yanzu ba ni ne kuma nake a raye ba, Almasihu ne yake a raye a cikina. Rayuwar nan kuma da nake yi ta jiki, rayuwa ce ta wurin bangaskiya ga Ɗan Allah, wanda ya ƙaunace ni, har ya ba da kansa domina. 21 Ba na tozarta alherin Allah. Don da ta wurin bin Shari'a ake samun adalcin Allah, ashe, da Almasihu ya mutu a banza ke nan.”

Galatiyawa 3

Shari'a ko Bangaskiya

1 Ya ku Galatiyawa marasa azanci! Wa ya ɗauke hankalinku? Ku da aka bayyana muku Yesu Almasihu gicciyeyye sosai. 2 Abu ɗaya kaɗai zan tambaye ku. Kun sami Ruhu saboda bin Shari'a ne, ko kuwa saboda gaskatawa ga maganar da kuka ji? 3 Ashe, rashin azancinku har ya kai ga haka? Da kuka fara da Ruhu, ashe, a yanzu kuma da halin mutuntaka za ku ƙarasa? 4 Ashe, a banza kuka sha wuya iri iri? In dai har a banzan ne! 5 Wato, shi da yake yi muku baiwar Ruhu, yake kuma yin mu'ujizai a cikinku, saboda kuna bin Shari'a ne yake yin haka, ko kuwa saboda gaskatawa da maganar da kuka ji? 6 Haka ma Ibrahim “Ya gaskata Allah, bangaskiyan nan tasa kuma, aka lasafta ta adalci ce a gare shi.” 7 Wato kun ga ashe, masu bangaskiya su ne 'ya'yan Ibrahim. 8 A cikin Nassi kuwa an hango, cewa Allah zai kuɓutar da al'ummai ta wurin bangaskiya, wato, dā ma can an yi wa Ibrahim bishara cewa, “Ta wurinka za a yi wa dukkan al'ummai albarka.” 9 To, ashe, masu bangaskiya su ne aka yi wa albarka a game da Ibrahim mai bangaskiyar nan. 10 Gama duk waɗanda suke dogara da bin Shari'a la'anannu ne, don a rubuce yake cewa, “Duk wanda bai tsaya ga aikata duk abin da yake rubuce a littafin Shari'a ba, la'ananne ne.” 11 To, a fili yake, ba mai samun kuɓuta ga Allah ta wurin bin Shari'a, domin “Wanda yake da adalci ta wurin bangaskiya zai rayu.” 12 Shari'a kuwa ba ta dangana ga bangaskiya ba, domin ta ce, “Wanda ya aikata ta, ta gare ta ne zai rayu.” 13 Almasihu ya fanso mu daga la'anar nan ta Shari'a, da ya zama abin la'ana saboda mu, domin a rubuce yake cewa, “Duk wanda aka kafa a jikin itace, la'ananne ne.” 14 An yi wannan kuwa domin albarkar nan da aka yi wa Ibrahim ta saukar wa al'ummai ta wurin Almasihu Yesu, mu kuma ta hanyar bangaskiya mu sami Ruhun nan da aka yi alkawari.

Shari'a da Alkawari

15 To, 'yan'uwa, bari in yi muku misali. Ko alkawari na mutum ne kawai, in dai an riga an tabbatar da shi, ba mai soke shi, ba kuma mai ƙara wani abu a kai. 16 To, alkawaran nan, an yi wa Ibrahim ne, da kuma wani a zuriyarsa. Ba a ce, “Da zuriya” ba, kamar suna da yawa. A'a, sai dai ɗaya kawai, aka ce, “Wani a zuriyarka,” wato Almasihu. 17 Ga abin da nake nufi. Shari'ar nan, wadda ta zo shekara arbaminya da talatin daga baya, ba ta shafe alkawarin nan da Allah ya tabbatar tun tuni ba, har da za ta wofinta shi. 18 Don da gādon nan ta hanyar Shari'a yake samuwa, ashe, da ba zai zama na alkawarin ke nan ba. Amma Allah ya bai wa Ibrahim ta wurin alkawari ne. 19 To, mece ce manufar Shari'a? Ƙari aka yi da ita don fitowa da laifi fili, har kafin na zuriyar nan ya zo, wanda aka yi wa alkawarin, an kuma ba da ita ta wurin mala'iku ne, ta hannun matsakanci. 20 Matsakanci fa ba domin ɗaya ba ne. Amma Allah ɗaya yake.

Manufar Shari'a

21 Wato, Shari'a ta zama saɓanin alkawaran Allah ke nan? A'a, ko kusa! Domin da an ba da wata shari'a mai iya ba da rai, da sai a sami adalcin Allah ta hanyar bin Shari'ar nan. 22 Amma Nassi ya kulle kowa a cikin zunubi, don albarkar da aka yi alkawari saboda gaskatawa da Yesu Almasihu, a ba da ita ga masu ba da gaskiya. 23 Tun kafin bangaskiya ta zo, a cikin ƙangin Shari'a muke a kulle, sai a lokacin da bangaskiya ta bayyana. 24 Ashe kuwa, Shari'a ta zama uwargijiyarmu da ta kai mu ga Almasihu, domin mu sami kuɓuta ga Allah ta wurin bangaskiya. 25 A yanzu kuwa da bangaskiya ta zo, ba sauran zamanmu a hannun wata uwargijiya. 26 Domin dukanku 'ya'yan Allah ne, ta wurin bangaskiya ga Almasihu Yesu. 27 Duk ɗaukacinku da aka yi wa baftisma ga bin Almasihu, kun ɗauki halin Almasihu ke nan. 28 Ba sauran cewa Bayahude ko Ba'al'umme, ko ɗa, ko bawa, ko namiji ko mace. Ai, dukkanku ɗaya kuke, na Almasihu Yesu. 29 In kuwa ku na Almasihu ne, ashe, ku zuriyar Ibrahim ne, magāda ne kuma bisa ga alkawarin nan.

Galatiyawa 4

1 Ana nufin, magaji, muddin yana yaro bai fi bawa ba, ko da yake yana da mallakar dukkan kome. 2 A hannun iyayen goyo da wakilai yake har zuwa ranar da mahaifinsa ya sa. 3 Haka yake a gare mu, wato sa'ad da muke kamar yara, a cikin ƙangin bautar al'adun duniya muke. 4 Amma da lokaci ya yi sosai, sai Allah ya aiko Ɗansa, haifaffen mace, haifaffe kuma a ƙarƙashin Shari'a, 5 domin ya fanso waɗanda suke a ƙarƙashin Shari'a, a mai da mu a matsayin 'ya'yan Allah. 6 Tun da yake ku 'ya'ya ne, sai Allah ya aiko da Ruhun Ɗansa a cikin zukatanmu, yana kira, “Ya Abba! Uba!” 7 Don haka, kai ba bawa ba ne kuma, amma ɗa ne. Da yake ɗa ne kuma, to, magāji ne bisa ga ikon Allah.

Alhinin Bulus a kan Masu Bangaskiya

8 Dā da ba ku san Allah ba, kuna bauta wa waɗansu gumaka, waɗanda ga ainihi ba a bakin kome suke ba. 9 Amma a yanzu da kuka san Allah, ko ma dai a ce Allah ya san ku, ta yaya za ku sāke komawa a kan raunanan al'adu marasa biyan bukata, har kuna neman komawa ga bautarsu? 10 Ga shi, al'adun ranaku, da na watanni, da na lokatai, da na shekaru ba sa wuce ku! 11 Amma kun ba ni tsoro, kada ya zamana na yi wahala a kanku a banza! 12 Ina roƙonku, ya ku 'yan'uwana, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma in zama kamar yadda kuke. Ba ku taɓa yi mini wani laifi ba. 13 Kun dai sani a dalilin rashin lafiyata ne na yi muku bishara a zuwana na fari. 14 Ko da yake rashin lafiyata ta hana ku sukuni, duk da haka ba ku nuna mini raini ko ƙyama ba, sai dai kuka yi na'am da ni kamar wani mala'ikan Allah, ko ma Almasihu Yesu kansa. 15 To, ina daɗin nan da kuka ji a game da ni? Don na shaide ku a kan lalle da mai yiwuwa ne da kun ƙwaƙule idanunku kun ba ni! 16 Ashe, wato na zama abokin gābarku ne don na gaya muku gaskiya? 17 Waɗannan suna habahaba da ku, amma ba da kyakkyawar niyya ba. Niyyarsu su raba ku da mu, don su ma ku yi habahaba da su. 18 Ai, in da kyakkyawar niyya, abu ne mai kyau koyaushe a yi habahaba da mutum, ba sai ina tare da ku kaɗai ba. 19 Ya ku 'ya'yana ƙanana, ina sāke shan wahalar naƙudarku, har Almasihu ya siffatu a zuciyarku! 20 Da ma a ce ina tare da ku a yanzu in sauya muryata! Gama na ruɗe a kan sha'aninku.

Ishara da Hajaratu da Saratu

21 Ku gaya mini, ku da kuke son Shari'a ta yi iko da ku, ba kwa sauraron Sharia ne? 22 Domin a rubuce yake, Ibrahim yana da 'ya'ya biyu maza, ɗaya ɗan kuyanga, ɗaya kuma ɗan 'ya. 23 Ɗan kuyangar nan, an haife shi ne bisa ga ɗabi'a, ɗan 'yar kuwa ta cikar alkawarin ne. 24 Wannan kuwa duk don ishara ne, wato matan nan a kan alkawari biyu suke. Ɗaya tushensa Dutsen Sina'i, mai haihuwar bayi, wato Hajaratu ke nan. 25 To, ai, Hajaratu Dutsen Sina'i ce a ƙasar Larabawa. Ita ce kwatancin Urushalima ta yanzu, don ita da 'ya'yanta duk a bauta suke. 26 Amma Urushalima ta sama, ai 'ya ce, ita ce kuma uwarmu. 27 Domin a rubuce yake cewa, “Ki yi farin ciki, ya ke bakarariya da ba kya haihuwa, Ki ɗauki sowa, ke da ba kya naƙuda, Don yasasshiya ta fi mai miji yawan 'ya'ya.” 28 To, 'yan'uwa, mu ma 'ya'yan alkawari ne kamar Ishaku. 29 Kamar yadda dā, shi da aka haifa bisa ga ɗabi'a ya tsananta wa wanda aka haifa bisa ga ikon Ruhun, haka a yanzu ma yake. 30 Amma me Nassin ya ce? “Ka kori kuyangar da ɗanta, don ko kaɗan ɗan kuyangar ba zai ci gādo tare da ɗan 'ya ba.” 31 Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan kuyanga ba ne, na 'ya ne.

Galatiyawa 5

Ku Dāge a cikin 'Yanci

1 Almasihu ya 'yanta mu, 'yantawar gaske. Don haka sai ku dāge, kada ku sāke sarƙafewa a cikin ƙangin bauta. 2 To, ni Bulus, ina gaya muku, in kuna yarda a yi muku kaciya, Almasihu ba zai amfane ku kome ba ke nan. 3 Ina sāke tabbatar wa duk wanda ya yarda a yi masa kaciya, cewa wajibi ne ya bi dukkan Shari'a. 4 Ku da kuke neman kuɓuta ga Allah ta wurin bin Shari'a, kun katse daga Almasihu ke nan, kun noƙe daga alherin Allah. 5 Gama mu, ta wurin ikon Ruhu, muke ɗokin cikar begen nan namu na samun adalcin Allah saboda bangaskiya. 6 In muna a cikin Almasihu Yesu, kaciya da rashin kaciya ba a bakin kome suke ba. Bangaskiya mai aikata ƙauna ita ce wani abu. 7 Dā, ai, kuna ci gaba sosai. Wane ne ya hana ku bin gaskiya? 8 Wannan rarrashin da ake muku ba daga wanda ya kira ku ba ne. 9 Ai, ɗan yisti kaɗan, yake game dukkan curin gurasa. 10 Na dai amince da ku a cikin Ubangiji, ba za ku bi wani ra'ayi dabam da nawa ba. Wannan da yake ta da hankalinku kuwa zai sha hukunci, ko shi wane ne. 11 Amma 'yan'uwa, in da har yanzu wa'azin yin kaciya nake yi, to, don me har yanzu ake tsananta mini? In da haka ne, ashe, an kawar da hamayyar da gicciyen Almasihu yake sawa ke nan! 12 Da ma a ce masu ta da hankalinku ɗin nan su mai da kansu babanni! 13 Ya ku 'yan'uwa, don 'yanci musamman aka kira ku, amma kada ku mai da 'yancin nan naku hujjar biye wa halin mutuntaka, sai dai ku bauta wa juna da ƙauna. 14 Don duk Shari'a an ƙunshe ta ne a kalma guda, wato, “Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.” 15 Amma in kuna cin naman juna, ku mai da hankali fa, hanyar hallaka juna ke nan.

Albarkar Ruhu da Halin Mutuntaka

16 Maganata ita ce, ku yi zaman Ruhu, ba kuwa za ku biye wa halin mutuntaka ba. 17 Don halin mutuntaka gāba yake yi da Ruhu, Ruhu kuma yana gāba da halin mutuntaka. Waɗannan biyu gāba suke yi da juna, har ba kwa iya yin abin da kuke so. 18 In Ruhu ne yake bi da ku, ashe, Shari'a ba ta da iko da ku, ke nan. 19 Aikin halin mutuntaka a fili yake, wato, fasikanci, da aikin lalata, da fajirci, 20 da bautar gumaka, da sihiri, da gāba, da jayayya, da kishi, da fushi, da sonkai, da tsaguwa, da hamayya, 21 da hassada, da buguwa, da shashanci, da kuma sauran irinsu. Ina faɗakar da ku kamar yadda na faɗakar da ku a dā, cewa masu yin irin waɗannan abubuwa, ba za su sami gādo a Mulkin Allah ba. 22 Albarkar Ruhu kuwa ita ce ƙauna, da farin ciki, da salama, da haƙuri, da kirki, da nagarta, da aminci, 23 da tawali'u da kuma kamunkai. Masu yin irin waɗannan abubuwa, ba dama shari'a ta kama su. 24 Waɗanda kuwa suke su na Almasihu Yesu ne, sun gicciye halin mutuntaka da mugayen sha'awace-sha'awace iri iri. 25 In dai rayuwar tamu ta Ruhu ce, to, sai mu tafiyar da al'amuranmu ta wurin ikon Ruhu. 26 Kada mu zama masu homa, muna tsokanar juna, muna yi wa juna hassada.

Galatiyawa 6

Ku Ɗauki Wahalar Juna

1 Ya ku 'yan'uwa, in an kama mutum yana a cikin yin laifi, ku da kuke na ruhu, sai ku komo da shi a kan hanya da tawali'u, kowa yana kula da kansa kada shi ma ya burmu. 2 Ku ɗauki wahalar juna, ta haka za ku cika shari'ar Almasihu. 3 Kowa ya zaci shi wani abu ne, alhali kuwa shi ba kome ba ne, ya ruɗi kansa ke nan. 4 Kowa yă auna aikinsa ya gani, sa'an nan ne zai iya gadara da maƙaminsa shi da kansa, ba sai ya gwada kansa da wani ba. 5 Lalle kowa yă ji da kayansa. 6 Duk wanda aka koya wa Maganar, yă ci moriyar abubuwansa na alheri tare da mai koyarwa. 7 Kada fa a yaudare ku, ai, ba a iya zambatar Allah. Duk abin da mutum ya shuka, shi zai girba. 8 Wanda ya yi shuka a kwaɗayin son zuciyarsa, ta wurin son zuciya zai girbi ruɓa. Wanda ya yi shuka a Ruhu, ta wurin Ruhu zai girbi rai madawwami. 9 Kada mu yi sanyi da yin aiki nagari, don za mu yi girbi a kan kari, in ba mu karai ba. 10 To, saboda haka, in hali ya yi, sai mu kyautata wa kowa, tun ba ma waɗanda suke jama'ar masu ba da gaskiya ba.

Kashedi da kuma Gaisuwa

11 Ku dubi irin rubutu gwada-gwada da nake muku da hannuna! 12 To, mutanen nan masu son nuna bijinta cikin jiki, su ne masu son tilasta muku yin kaciya, don gudun shan wuya saboda gicciyen Almasihu. 13 Ai, ko waɗanda aka yi wa kaciya ma ba sa kiyaye Shari'a. Sonsu ne a yi muku kaciya, don su yi fāriya da ku a kan an yi muku kaciya. 14 Amma ni ko kusa ba zan yi fariya ba, sai dai a game da gicciyen Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta albarkacin mutuwarsa a kan gicciye ne na yar da sha'anin duniya, duniya kuma ta yar da sha'anina. 15 Kaciya da rashin kaciya ba a bakin kome suke ba, sai dai sabuwar halitta ita ce wani abu. 16 Salama da jinƙai su tabbata ga duk masu bin ka'idar nan, wato Isra'ilar gaske ta Allah. 17 Daga nan gaba kada kowa ya ƙara damuna, domin a jikina ina da tabbai masu nuna ni bawan Ubangiji Yesu ne. 18 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku, 'yan'uwa. Amin.

Afisawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzon Almasihu Yesu da yardar Allah, zuwa ga mutanensa tsarkaka da suke a Afisa, amintattu a cikin Almasihu Yesu. 2 Alheri da salama na Allah ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Albarku na Ruhu a cikin Almasihu

3 Yabo yā tabbata ga Allahn Ubangijinmu Yesu Almasihu, da Ubansa kuma, wanda ya yi mana albarka da kowace albarka ta Ruhu, basamaniya, a cikin Almasihu, 4 domin kuwa ya zaɓe mu a cikin Almasihu tun ba a halicci duniya ba, mu zama tsarkaka, marasa aibu a gabansa. 5 Ya ƙaddara mu mu zama 'ya'yansa ta wurin Yesu Almasihu, bisa ga nufinsa na alheri, 6 domin mu yabi ɗaukakar alherinsa wanda ya ba mu kyauta hannu sake saboda Ƙaunataccensa. 7 Ta gare shi ne muka sami fansa albarkacin jininsa, wato yafewar laifofinmu, bisa ga yalwar alherin Allah, 8 wanda ya falala mana. Da matuƙar hikima da basira 9 ya sanasshe mu asirin nufinsa, bisa ga kyakkyawan nufinsa da ya nufa ya cika ta wurin Almasihu. 10 Duk wannan kuwa shiri ne, domin a cikar lokaci a harhaɗa dukkan abubuwa ta wurin Almasihu, wato abubuwan da suke sama, da abubuwan da suke a ƙasa. 11 A cikinsa ne aka maishe mu abin gādo na Allah, an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukkan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi, 12 domin mu da muka fara kafa bege ga Almasihu mu yi zaman yabon ɗaukakarsa. 13 A cikinsa ne ku kuma da kuka ji maganar gaskiya, wato, bisharar cetonku, a cikinsa, sa'ad da kuka ba da gaskiya kuma, aka hatimce ku da Ruhu Mai Tsarki wanda aka alkawarta. 14 Shi ne kuwa tabbatawar gādonmu har kafin mu kai ga samunsa, wannan kuma domin yabon ɗaukakarsa ne.

Addu'a don Hikima da Sani

15 Saboda haka da yake na ji labarin bangaskiyarku ga Ubangiji Yesu, da kuma ƙaunarku ga dukan tsarkaka, 16 ban fāsa gode wa Allah saboda ku ba, duk sa'ad da nake yi muku addu'a, 17 da nufin cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Almasihu, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhu mai ba da hikima da bayani ga sanin Allah, 18 a kuma sa ku ku waye ta idon zuci, domin ku san ko mene ne begen nan da ya kira ku a kai, da kuma ko mene ne yalwar gādonsa mai ɗaukaka a game da tsarkaka, 19 da kuma ko mene ne girman ikonsa marar misaltuwa da yake zartarwa a gare mu, mu masu ba da gaskiya, wato zartarwar ƙarfin ikon nan nasa, 20 wanda ya zartar ga Almasihu sa'ad da ya tashe shi daga matattu, ya kuma ba shi wurin zama a damansa a samaniya, 21 a can a birbishin dukkan sarauta da iko, da ƙarfi, da mulki, a birbishin kowane suna da za a sa, ba ma a duniyar nan kawai ba, har ma a lahira ma. 22 Allah kuma ya sarayar da kome a ƙarƙashin ikon Almasihu, ya kuma ba da shi ga Ikilisiya ya zama Kai mai mallakar abu duka. 23 Ikilisiya ita ce jikin Almasihu, cikar mai cika dukkan abu.

Afisawa 2

Daga Mutuwa zuwa Rai

1 Ku kuma zai raya ku sa'ad da kuke matattu ta wurin laifofinku da zunubanku, 2 waɗanda dā kuke a ciki, kuna biye wa al'amarin duniyar nan, kuna bin sarkin masu iko a sararin sama, wato iskar nan da take zuga zuciyar kangararru a yanzu. 3 Dukkanmu dā mun zauna a cikinsu, muna biye wa sha'awoyin halin mutuntaka, muna aikata abin da jiki da zuciya suke buri, har ma ga ɗabi'a wajibi ne fushin Allah ya bayyana a kanmu, kamar sauran 'yan adam. 4 Amma Allah da yake mai yalwar jinƙai ne, saboda matsananciyar ƙaunar da yake yi mana, 5 ko a sa'ad da muke matattu ma ta wurin laifofinmu, sai ya rayar da mu tare da Almasihu (ta wurin alheri an cece ku), 6 a cikin Almasihu Yesu kuma ya tashe mu tare, har ya ba mu wurin zama tare a samaniya. 7 Allah ya yi wannan kuwa domin a zamani mai zuwa ya bayyana yalwar alherinsa marar misaltuwa, ta wajen nuna mana alheri ta wurin Almasihu Yesu. 8 Domin ta wurin alheri ne aka cece ku saboda bangaskiya, wannan kuwa ba ƙoƙarin kanku ba ne, baiwa ce ta Allah, 9 ba kuwa saboda da aikin lada ba, kada wani ya yi fariya. 10 Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Almasihu Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.

Zama Ɗaya da Almasihu

11 Saboda haka, ku tuna dā ku al'ummai ne bisa ɗabi'a, ga waɗanda ake kira masu kaciyar nan kuwa, sukan kira ku marasa kaciya (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu). 12 Ku kuma tuna a lokacin nan a rabe kuke da Almasihu, bare ne ga jama'ar Isra'ila, bāƙi ne ga alkawaran nan da Allah ya yi, marasa bege, marasa Allah kuma a duniya. 13 Amma a yanzu, a cikin Almasihu, ku da dā kuke can nesa, an kawo ku kusa ta wurin jinin Almasihu. 14 Domin Almasihu shi ne salamarmu, shi wanda ya mai da Yahudawa da al'ummai ɗaya, wato ya rushe katangar nan da ta raba su a kan gāba. 15 Har ya soke Shari'ar nan mai umarni da dokoki, ta wurin ba da jikinsa, domin ta gare shi yă halicci sabon mutum guda daga mutanen nan biyu, ta haka yă kawo salama, 16 yă kuma sulhunta su duka biyu ga Allah, su zama jiki ɗaya ta wurin gicciye, ta haka yă kashe gābar. 17 Ya kuwa zo ya yi muku albishirin salama, ku da kuke nesa, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa. 18 Domin ta gare shi ne dukanmu biyu muka sami isa gun Uba ta hanyar Ruhu guda. 19 Wato ashe, ku ba baƙi ba ne kuma, ko kuwa bāre, ai, ku abokan 'yanci ne na tsarkaka, iyalin Allah kuma, 20 waɗanda aka gina bisa tushen manzanni da annabawa, Almasihu Yesu kansa kuwa shi ne mafificin dutsen ginin, 21 dukan wanda aka haɗa tsarin ginin a cikinsa, yana kuma tashi ya zama haikali tsattsarka na Ubangiji. 22 A cikinsa ne ku kuma aka gina ku, ku zama mazaunin Allah ta wurin Ruhu.

Afisawa 3

Hidimar Bulus ga Al'ummai

1 Domin haka, ni Bulus, ɗan sarƙa saboda Almasihu Yesu domin amfanin ku al'ummai, 2 in dai kun ji labarin mai da ni mai hidimar alherin Allah wanda aka yi mini baiwa saboda ku, 3 wato yadda aka sanar da ni asirin Ubangiji ta wahayi, kamar yadda na riga na rubuta a taƙaice. 4 A yayin da kuka karanta wannan, za ku iya gane basirata saboda asirin Almasihu, 5 wanda a zamanin dā ba a sanar da 'yan adam ba, kamar yadda a yanzu aka bayyana wa manzanninsa tsarkaka da annabawa, ta wurin Ruhu, 6 wato, yadda ta wurin bishara al'ummai da suke abokan gādo da mu, gaɓoɓin jiki guda, abokan tarayya kuma ga alkawaran nan a cikin Almasihu Yesu. 7 An kuwa sa ni mai hidimar wannan bishara, a bisa ga baiwar alherin Allah da aka yi mini ta ƙarfin ikonsa. 8 Ko da yake ni ne mafi ƙanƙantar tsarkaka duka, ni aka ba wannan alheri in yi wa al'ummai bishara a kan yalwar Almasihu marar ƙididdiguwa, 9 in kuma bayyana wa dukan mutane shirin asirin nan wanda shekara da shekaru yake a ɓoye a gun Allah, wanda ya halicci dukkan abubuwa. 10 An yi wannan ne kuwa domin a yanzu a sanar da hikimar Allah iri iri ga manyan mala'iku da masa iko a samaniya, ta hanyar Ikilisiya. 11 Wannan kuwa bisa ga dawwamammen nufin nan ne da Allah ya zartar a cikin Almasihu Yesu Ubangijinmu. 12 A cikinsa muke da gabagaɗin isa ga Allah, da amincewa, ta wurin bangaskiyarmu a gare shi. 13 Saboda haka, ina roƙonku kada ku karai da ganin wahalar da nake sha dominku, wannan kuwa ɗaukakarku ce.

A San Ƙaunar Almasihu

14 Saboda haka, nake durƙusawa a gaban Uban, 15 shi da yake sa wa kowace kabila ta sama da ta ƙasa suna, 16 ina addu'a ya yi muku baiwa bisa ga yalwar ɗaukakarsa, ku ƙarfafa matuƙa a birnin zuciyarku ta wurin Ruhunsa, 17 har ma Almasihu yă zauna a zukatanku ta wurin bangaskiyarku, domin ƙauna ta kahu da gindinta sosai a zukatanku, 18 har ku sami kaifin basira tare da dukan tsarkaka, ku fahimci ko mene ne fāɗin ƙaunar Almasihu, da tsawonta da zacinta, da kuma zurfinta, 19 ku kuma san ƙaunar da Almasihu yake yi mana, wadda ta fi gaban sani, domin a cika ku da dukan falala ta Allah. 20 Ɗaukaka tă tabbata ga wannan da yake da ikon aikatawa fiye da dukkan abin da za mu roƙa, ko za mu zata nesa, wato, aikatawa ta ƙarfin ikonsa da yake aiki a zuciyarmu. 21 Ɗaukaka tă tabbata a gare shi a cikin Ikilisiya ta wurin Almasihu Yesu, har ya zuwa dukkan zamanai har abada abadin. Amin.

Afisawa 4

Ɗayantuwar Ruhu

1 Don haka, ni ɗan sarƙa saboda Ubangiji, ina roƙonku ku yi zaman da ya cancanci kiran da aka yi muku, 2 da matuƙar tawali'u, da salihanci, da haƙuri, kuna jure wa juna saboda ƙauna. 3 Da ƙwazo ku kiyaye ɗayantuwar da Ruhu yake zartarwa, kuna a haɗe a cikin salama. 4 Jiki guda ne, Ruhu kuma guda, kamar yadda aka kira ku a kan begen nan guda, wanda yake game da kiran nan. 5 Ubangiji guda ne, bangaskiya guda, da kuma baftisma guda. 6 Allah ɗaya ne, Ubanmu duka, wanda yake bisa duka, ta wurin duka, a cikin duka kuma. 7 Amma an ba kowannenmu alheri gwargwadon baiwar Almasihu. 8 Saboda haka, Nassi ya ce, “Sa'ad da ya hau Sama ya bi da rundunar kamammu, Ya kuma yi wa 'yan adam baye-baye.” 9 (Wato, da aka ce “Ya hau” ɗin, me aka fahimta, in ba cewa dā ya sauka a can ƙasa ba? 10 Shi wanda ya sauka ɗin, shi ne kuma ya hau a can birbishin dukkan sammai, domin ya cika kome.) 11 Ya kuma yi wa waɗansu baiwa su zama manzanni, waɗansu annabawa, waɗansu masu yin bishara, waɗansu makiyaya masu koyarwa, 12 domin tsarkaka su samu, su iya aikin hidimar Ikilisiya, domin a inganta jikin Almasihu, 13 har mu duka mu riski haɗa kan nan na bangaskiya ga Ɗan Allah, da kuma saninsa, mu kai maƙamin cikakken mutum, mu kuma kai ga matsayin nan na falalar Almasihu. 14 An yi wannan kuwa don kada mu sāke zama kamar yara, waɗanda suke jujjuyawa, iskar kowace koyarwa tana ɗaukar hankalinsu, bisa ga wayon mutane da makircinsu da kissoshinsu. 15 A maimakon haka, sai mu faɗi gaskiya game da ƙauna, muna girma a cikinsa ta kowace hanya, wato Almasihu, shi da yake shugabanmu. 16 Domin ta gare shi ne dukkan jiki yake a game, yake kuma a haɗe, ta wurin gudunmawar kowace gaɓa, ta wurin kuma aikin kowace gaɓa daidai jikin yake ƙara girma, yana kuma ingantuwa da halin ƙauna.

Sabon Rai a cikin Almasihu

17 To, ina dai faɗa muku, ina kuma nace faɗa muku a cikin Ubangiji, cewa kada ku sāke yin zama irin na al'ummai, masu azancin banza da wofi. 18 Duhun zuciya yake a gare su, bare suke ga rai wanda Allah yake bayarwa, sabili da jahilcin da yake a gare su, saboda taurin kansu. 19 Zuciyarsu ta yi kanta, sun dulmiya a cikin fajirci, sun ɗokanta ido a rufe ga yin kowane irin aikin lalata. 20 Ba haka kuka koyi al'amarin Almasihu ba, 21 in da a ce kun saurare shi, an kuma koya muku ta gare shi ne, wato yadda gaskiya ta Yesu take. 22 Ku yar da halinku na dā, wanda dā kuke a ciki, wanda yake lalacewa saboda sha'awoyinsa na yaudara, 23 ku kuma sabunta ra'ayin hankalinku, 24 ku ɗauki sabon halin nan da aka halitta bisa ga kamannin Allah da hakikanin adalci da tsarki. 25 Saboda haka, sai ku watsar da ƙarya, kowa yă riƙa faɗar gaskiya ga maƙwabcinsa, gama mu gaɓoɓin juna ne. 26 In kun husata, kada ku yi zunubi, kada ma fushinku ya kai faɗuwar rana, 27 kada kuma ku bar wa Iblis wata ƙofa. 28 Kada ɓarawo ya ƙara yin sata, a maimakon haka sai ya motsa jiki yana aikin gaskiya da hannunsa, har da zai sami abin da zai ba matalauta. 29 Kada wata alfasha ta fita daga bakinku, sai dai irin maganar da ta kyautu domin ingantawa, a kuma yi ta a kan kari, domin ta sa alheri ga masu jinta. 30 Ku kuma kula, kada fa ku ɓata wa Ruhu Mai Tsarki na Allah rai, wanda aka hatimce ku da shi, cewa ku nasa ne a ranar fansa. 31 Ku rabu da kowane irin ɗacin rai, da hasala, da fushi, da tankiya, da yanke, da kowace irin ƙeta. 32 Ku yi wa juna kirki, kuna tausayi, kuna yafe wa juna kamar yadda Allah ya yafe muku ta wurin Almasihu.

Afisawa 5

Ku Yi Zaman Haske

1 Saboda haka sai ku zama masu koyi da Allah, in ku ƙaunatattun 'ya'yansa ne. 2 Ku yi zaman ƙauna kamar yadda Almasihu ya ƙaunace mu, ya kuma ba da kansa dominmu, sadaka mai ƙanshi, hadaya kuma ga Allah. 3 Kada ma a ko ambaci fasikanci, da kowane irin aikin lalata ko kwaɗayi a tsakaninku, domin kuwa bai dace da tsarkaka ba. 4 Haka ma alfasha, da zancen banza da wauta, don bai kamata ba, sai dai a maimakon haka ku riƙa gode wa Allah. 5 Kun dai tabbata, ba wani fasiki, ko mai aikin lalata, ko mai kwaɗayi (wanda shi da mai bautar gumaka duk ɗaya ne), da yake da gādo a mulkin Almasihu da na Allah. 6 Kada wani ya hilace ku da maganar wofi, gama sabili da waɗannan zunubai ne fushin Allah yake aukawa a kan kangararru. 7 Saboda haka, kada ku yi cuɗanya da su, 8 domin dā ku duhu ne, amma a yanzu ku haske ne a cikin Ubangiji. Ku yi zaman mutanen haske, 9 domin haske shi ne yake haifar duk abin da yake nagari, na adalci, da na gaskiya. 10 Ku dai tabbata abin zai gamshi Ubangiji. 11 Ku yi nesa da ayyukan duhu na banza da wofi, sai dai ku tona su. 12 Gama abin kunya ne a ma faɗi abubuwan da suke yi a asirce. 13 Duk abin da aka kawo a gaban haske a san ainihinsa, gama duk abin da aka san ainihinsa ya haskaka. 14 Saboda haka aka ce, “Farka, ya kai mai barci, ka tashi daga matattu. Almasihu kuwa zai haskaka ka.” 15 Saboda haka, sai ku mai da hankali ƙwarai ga zamanku, kada ku zama kamar marasa hikima, sai dai masu hikima. 16 Ku yi matuƙar amfani da lokaci don kwanaki mugaye ne. 17 Don haka kada ku zama marasa azanci, sai dai ku fahimci abin da yake nufin Ubangiji. 18 Kada kuma ku bugu da giya, hanyar masha'a ke nan. Sai dai ku cika da Ruhu, 19 kuna zance da junanku da kalmomin zabura, da waƙoƙin yabo, da waƙoƙi na ruhu, kuna raira waƙoƙi da zabura ga Ubangiji da yabo a zukatanku. 20 Kullum ku riƙa gode wa Allah Uba da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu a kan ko mene ne.

Maza da Mata

21 Ku bi juna saboda ganin girman Almasihu. 22 Ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, Ubangiji ke nan kuke yi wa. 23 Don miji shi ne shugaban matarsa, kamar yadda Almasihu ke shugaban Ikilisiya, wato, jikinsa, shi kansa kuma shi ne Mai Ceton jikin. 24 Kamar yadda Ikilisiya take bin Almasihu, haka kuma mata su bi mazansu ta kowane hali. 25 Ku maza, ku ƙaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya ƙaunaci ikilisiya, har ya ba da kansa dominta, 26 domin ya miƙa ta ga Allah, tsarkakakkiya bayan da ya wanke ta da ruwa ta wurin Kalma, 27 domin shi kansa yă ba kansa Ikilisiya da ɗaukakarta, ba tare da tabo ko tamoji ba, ko wani irin abu haka, tă dai zamo tsattsarka marar aibu. 28 Ta haka ya wajaba maza su ƙaunaci matansu, jikinsu ke nan suke yi wa. Ai, wanda ya ƙaunaci matarsa, ya ƙaunaci kansa ke nan. 29 Domin ba wanda ya taɓa ƙin jikinsa, sai dai ya rene shi, ya yi tattalinsa, kamar yadda Almasihu yake yi wa Ikilisiya, 30 domin mu gaɓoɓin jikinsa ne. 31 “Saboda haka ne, mutum sai ya bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, ya manne wa matarsa, su biyu su zama jiki guda.” 32 Wannan asiri muhimmi ne, ni kuwa ina nufin Almasihu ne da ikilisiya. 33 Duk da haka dai, sai kowane ɗayanku ya ƙaunaci matarsa kamar kansa, ita matar kuwa ta yi wa mijinta ladabi.

Afisawa 6

Biyayya da Ƙauna

1 Ku 'ya'ya, ku yi wa iyayenku biyayya tsakani da Ubangiji, domin wannan shi ne daidai. 2 Wannan shi ne umarnin farko mai alkawari, cewa, “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka, 3 don al'amarinka ya kyautatu, ka kuma yi tsawon rai a duniya.” 4 Ku ubanni, kada ku sa 'ya'yanku su yi fushi, sai dai ku goye su da tarbiyya, da kuma gargaɗi ta hanyar Ubangiji. 5 Ku bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya, da hali bangirma tare da matsananciyar kula da zuciya ɗaya, Almasihu ku ke yi wa ke nan, 6 ba aikin ganin ido ba, kamar masu son faranta wa mutane rai, sai dai kamar bayin Almasihu masu aikata abin da Allah yake so, da zuciya ɗaya, 7 kuna bauta da kyakkyawar niyya domin Ubangiji kuke yi wa, ba mutane ba. 8 Kun sani, kowane alherin da mutum ya yi, ko shi ɗa ne ko bawa, Ubangiji zai sāka masa shi. 9 Ku iyayengiji, ku ma ku yi musu haka, ku bar tsorata su, ku sani, shi wanda yake Ubangijinsu da ku duka, yana Sama, shi kuwa ba ya zaɓe.

Makaman Allah Duka

10 A ƙarshe kuma, ku ƙarfafa ga Ubangiji, ga ƙarfin ikonsa. 11 Ku yi ɗamara da dukan makamai na Allah, don ku iya dagewa gāba da kissoshin Iblis. 12 Ai, famarmu ba da 'yan adam muke yi ba, amma da mugayen ruhohi ne na sararin sama, masarauta, masu iko, da waɗanda ragamar mulkin zamanin nan mai duhu take hannunsu. 13 Saboda haka, sai ku ɗauki dukan makamai na Allah, domin ku iya dagewa a muguwar ranar nan, bayan kuma kun gama kome duka, ku dage. 14 Saboda haka fa ku dage, gaskiya ta zama ɗamararku, adalci ya zama sulkenku, 15 shirin kai bisharar salama ya zama kamar takalmi a ƙafafunku. 16 Banda waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kiban wutar Mugun nan da ita. 17 Ku kuma ɗauki kwalkwalin ceto, da takobin Ruhu, wato Maganar Allah, 18 a koyaushe kuna addu'a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fāsawa. A kan wannan manufa ku tsaya da kaifinku da matuƙar naci, kuna yi wa dukan tsarkaka addu'a. 19 Ni ma ku yi mini, domin in sami baiwar yin hurci, in yi magana gabagaɗi, in sanar da asirin bishara, 20 wadda ni jakadanta ne, ɗaurarre. Ku dai yi mini addu'a, duk sa'ad da nake yin bisharar, in bayyana ta gabagaɗi, kamar yadda ya kamata in yi.

Gaisuwa

21 A yanzu kuwa, don ku ma ku san lafiyata, da kuma halin da nake a ciki, ga Tikikus, ƙaunataccen ɗan'uwa, amintaccen mai hidimar Ubangiji, zai sanar da ku kome. 22 Na aiko shi gare ku musamman domin ku san yadda muke, ya kuma ƙarfafa muku zuciya. 23 Salamar Allah Uba da ta Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata ga 'yan'uwa, tare da ƙauna game da bangaskiya. 24 Alheri yă tabbata ga dukkan masu ƙaunar Ubangijinmu Yesu Almasihu da ƙauna marar ƙarewa.

Filibiyawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus da Timoti, bayin Almasihu Yesu, zuwa ga dukan tsarkaka a cikin Almasihu Yesu waɗanda suke a Filibi, tare da masu kula da ikilisiya da kuma masu hidimarta. 2 Alheri da salama na Allah ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu, su tabbata a gare ku.

Addu'ar Bulus domin Filibiyawa Masu Bin Almasihu

3 Ina gode Allahna duk sa'ad da nake tunawa da ku, 4 a kullum kuwa a kowace addu'a da nake muku duka, da farin ciki nake yi. 5 Ina godiya saboda tarayyarku da ni wajen yaɗa bishara, tun daga ranar farko har ya zuwa yanzu. 6 Na tabbata shi wanda ya fara kyakkyawan aiki a gare ku, zai ƙarasa shi, har ya zuwa ranar Yesu Almasihu. 7 Daidai ne kuwa a gare ni in riƙa tunaninku haka, ku duka, domin kuna a cikin zuciyata, domin dukanku abokan tarayya ne da ni da alherin Allah, ta wajen ɗaure ni da aka yi, da kuma ta yin kāriyar bishara da tabbatar da ita. 8 Domin Allah shi ne mashaidina a kan yadda nake begenku duka, da irin ƙaunar da Almasihu Yesu yake yi. 9 Addu'ata ita ce, ƙaunarku ta riƙa haɓaka da sani da matuƙar ganewa, 10 domin ku zaɓi abubuwa mafifita, ku zama sahihai, marasa abin zargi, har ya zuwa ranar Almasihu, 11 kuna da cikakken sakamakon aikin adalci da yake samuwa ta wurin Yesu Almasihu, wannan kuwa duk domin ɗaukakar Allah ne, da yabonsa.

Manufar Rayuwata, Almasihu Ne

12 'Yan'uwa, ina so ku sani, al'amuran nan da suka auku a gare ni, har ma sun yi amfani wajen yaɗa bishara, 13 har dai ya zama sananne ga dukan sojan fāda da sauran jama'a, cewa ɗaurina saboda Almasihu ne. 14 Har ma galibin 'yan'uwa cikin Ubangiji suka ƙarfafa saboda ɗaurina, sun kuma ƙara fitowa gabagaɗi, su faɗi Maganar Allah ba tare da tsoro ba. 15 Lalle waɗansu suna wa'azin Almasihu saboda hassada da husuma, amma waɗansu kam, saboda kyakkyawar niyya ne. 16 Waɗannan suna yi ne a kan ƙauna, sun sani, an sa ni nan ne domin kāriyar bishara. 17 Waɗancan kuwa suna shelar Almasihu saboda sonkai ne, ba da zuciya ɗaya ba, a sonsu, su wahalar da ni a cikin ɗaurina. 18 Me kuma? Ta ko yaya dai, ko da gangan, ko da gaske, ana shelar Almasihu, na kuma yi farin ciki da haka. I, zan yi farin ciki kuwa. 19 Domin na san duk wannan zai zama sanadin lafiyata, ta wurin addu'arku da taimakon Ruhun Yesu Almasihu. 20 Don kuwa ina ɗoki, ina kuma sa zuciya, ko kaɗan ba zan kunyata ba, sai dai zan yi ƙarfin hali matuƙa a yanzu kamar koyaushe, a girmama Almasihu a jikina, ko ta wurin rayuwata, ko ta wurin mutuwata. 21 Domin ni, a gare ni, rai Almasihu ne, mutuwa kuwa riba ce. 22 In ya zamanto rayuwa zan yi a cikin jiki, to, zan yi aiki mai amfani ke nan. Amma na rasa abin da zan zaɓa. 23 Duka biyu suna jan hankalina ƙwarai. Burina in ƙaura in zauna tare da Almasihu, domin wannan shi ne ya fi kyau nesa. 24 Amma in wanzu a cikin jiki, shi ya fi wajabta saboda ku. 25 Na tabbata haka ne, na kuwa sani zan wanzu in zauna tare da ku duka, domin ku ci gaba, bangaskiyarku tana sa ku yin farin ciki, 26 ku kuma sami ƙwaƙƙwaran dalilin yin taƙama da Almasihu ta wurina, saboda sāke komowata gare ku. 27 Sai dai ku yi zaman da ya cancanci bisharar Almasihu, domin ko na zo na gan ku, ko kuwa ba na nan, in ji labarinku, cewa kun dage, nufinku ɗaya, ra'ayinku ɗaya, kuna fama tare saboda bangaskiyar da bishara take sawa, 28 ba kwa kuwa jin tsoron magabtanku sam. Wannan kuwa ishara ce a gare su ta hallakarsu, ku kuwa ta cetonku, isharar kuwa daga Allah take. 29 Gama an yi muku alheri, cewa ba gaskatawa da Almasihu kawai za ku yi ba, har ma za ku sha wuya dominsa, 30 kuna shan fama irin nawa wanda kuka gani, wanda kuke ji nake sha har yanzu.

Filibiyawa 2

Ƙasƙantar Almasihu da kuma Ɗaukakarsa

1 In akwai ƙarfafawa a cikin Almasihu, in dai da ƙarfin rinjaye na ƙauna, in har da tarayyarku ga Ruhu, da soyayyarku da kuma tausayinku, 2 to, albarkacinsu ku cikasa farin cikina da zamanku lafiya da juna, kuna ƙaunar juna, nufinku ɗaya, ra'ayinku ɗaya. 3 Kada ku yi kome da sonkai ko girmankai, sai dai da tawali'u, kowa yana mai da ɗan'uwansa ya fi shi. 4 Kowannenku kada ya kula da harkar kansa kawai, sai dai ya kula har da ta ɗan'uwansa ma. 5 Ku ɗauki halin Almasihu Yesu, 6 wanda, ko da yake a cikin surar Allah yake, bai mai da daidaitakar nan tasa da Allah abar da zai riƙe kankan ce ba, 7 sai ma ya mai da kansa baya matuƙa ta ɗaukar surar bawa, da kuma kasancewa da kamannin ɗan adam. 8 Da ya bayyana da siffar mutum, sai ya ƙasƙantar da kansa ta wurin yin biyayya, har wadda ta kai shi ga mutuwa, mutuwar ma ta gicciye. 9 Saboda haka ne kuma Allah ya ɗaukaka shi mafificiyar ɗaukaka, ya kuma yi masa baiwa da sunan nan da yake birbishin kowane suna, 10 domin dai kowace gwiwa sai ta rusuna wa sunan nan na Yesu, a Sama da ƙasa, da kuma can ƙarƙashin ƙasa, 11 kowane harshe kuma yă shaida Yesu Almasihu Ubangiji ne, domin ɗaukaka Allah Uba.

Haskakawa kamar Fitilu a Duniya

12 Saboda haka, ya ƙaunatattuna, kamar yadda a kullum kuke biyayya, haka kuma yanzu, ku yi ta yin aikin ceton nan naku da halin bangirma tare da matsananciyar kula, ba ma sai ina nan kawai ba, har ma fiye da haka in ba na nan. 13 Domin Allah shi ne mai aiki a zukatanku, ku nufi abin da yake kyakkyawan nufinsa, ku kuma aikata shi. 14 Kome za ka yi, kada ku yi da gunaguni, ko gardama, 15 don ku zama marasa abin zargi, sahihai, 'ya'yan Allah marasa aibu, a zamanin mutane karkatattu, kangararru, waɗanda kuke haskakawa a cikinsu kamar fitilu a duniya, 16 kuna riƙe da maganar rai kankan, har a ranar bayyanar Almasihu in yi taƙama, cewa himmata da famana ba a banza suke ba. 17 Ko da za a tsiyaye jinina a kan hadaya da hidima na bangaskiyarku, sai in yi farin ciki, in kuma taya ku farin ciki, ku duka. 18 Haka ku ma, ya kamata ku yi farin ciki, ku kuma taya ni farin ciki.

Timoti da Abafaroditas

19 Ina sa zuciya ga Ubangiji Yesu in aika muku da Timoti da wuri, don ni ma in ƙarfafa da samun labarinku. 20 Ba ni da wani kamarsa, wanda da sahihanci zai tsananta kula da zamanku lafiya. 21 Dukansu sha'anin gabansu kawai suke yi, ba na Yesu Almasihu ba. 22 Amma, ai, kun san darajar Timoti yadda muka yi bautar bishara tare, kamar ɗa da mahaifinsa. 23 Shi ne nake fata in aiko, da zarar na ga yadda al'amarina yake gudana. 24 Na kuma amince har ga Ubangiji, ni ma da kaina ina zuwa ba da daɗewa ba. 25 Amma na ga lalle ne in aiko muku da Abafaroditas ɗan'uwana, abokin aikina, abokin famana kuma, wanda kuka aiko ya yi mini ɗawainiya. 26 Yana begenku ku duka, har ma ya damu ƙwarai don kun ji ba shi da lafiya. 27 Lalle ya yi rashin lafiya, har ya yi kusan mutuwa. Amma Allah ya ji tausayinsa, ba kuwa shi kaɗai ba, har ni ma, don kada in yi baƙin ciki a kan baƙin ciki. 28 Saboda haka na ɗokanta ƙwarai in turo shi domin ku yi farin cikin sāke ganinsa, ni kuma in rage baƙin cikina. 29 Don haka sai ku karɓe shi da matuƙar farin ciki saboda Ubangiji, ku kuma girmama irin waɗannan mutane, 30 domin ya kusa ya mutu saboda aikin Almasihu, yana sai da ransa domin ya cikasa ɗawainiyarku gare ni.

Filibiyawa 3

Adalci Mai Gaskiya

1 A ƙarshe kuma 'yan'uwa, ku yi farin ciki da Ubangiji. Sāke rubuto muku waɗannan abubuwa bai gundure ni ba, ga shi kuwa, domin lafiyarku ne. 2 Ku yi hankali da karnukan nan! Ku yi hankali da mugayen ma'aikatan nan! Ku yi hankali da masu yankan jikin nan! 3 Don mu ne masu kaciyar ainihi, masu bauta wa Allah ta wurin Ruhu, masu taƙama da Almasihu Yesu, ba mu kuma dogara da al'amuran ganin ido, 4 ko da yake ni ina iya dogara da al'amuran ganin ido, in dai nake so. In kuma akwai wanda yake tsammani yana iya dogara ga al'amuran ganin ido, to, ni na fi shi. 5 An yi mini kaciya a rana ta takwas, asalina Isra'ila ne, na kabilar Biliyaminu, Ba'ibrane ɗan Ibraniyawa, bisa ga Shari'a kuwa ni Bafarisiye ne, 6 a wajen himma kuwa mai tsananta wa Ikilisiya ne ni, wajen aikin adalci kuwa bisa ga tafarkin Shari'a, marar abin zargi nake. 7 Amma dai kowace irin riba na taɓa ci, na ɗauka hasara ce saboda Almasihu. 8 Dahir na ɗauki dukkan abubuwa hasara ne, a kan mafificiyar darajar sanin da nake yi na Almasihu Yesu Ubangijina. Saboda shi ne na zaɓi yin hasarar dukkan abubuwa, har ma na mai da su tozari domin Almasihu yă zama nawa, 9 a kuma same ni a cikinsa, ba da wani adalcin kaina ba, wanda ya danganta da bin Shari'a, sai dai da adalcin nan wanda yake tsirowa daga bangaskiya ga Almasihu, wato, da adalcin nan wanda yake samuwa daga Allah ta wurin bangaskiya. 10 Muradina ke nan, in san Almasihu, in san ikon tashinsa daga matattu, in yi tarayya da shi a shan wuyarsa, in kuma zama kamarsa a wajen mutuwarsa, 11 domin ta ko ƙaƙa in kai ga tashin nan daga matattu.

Nacewa gaba gaba zuwa Manufar

12 Ba cewa, na riga na kai ga waɗannan ba ne, ko kuwa na zama kammalalle, a'a, sai dai ina nacewa ne, in riƙi abin nan da Almasihu Yesu ma ya riƙe ni saboda shi. 13 Ya 'yan'uwa, ban ɗauka a kan cewa na riga na riƙi abin ba, amma abu guda kam ina yi, ina mantawa da abin da yake baya, ina kutsawa zuwa ga abin da yake gaba. 14 Ina nacewa gaba gaba zuwa manufar nan, domin in sami ladar kiran nan zuwa sama, da Allah ya yi mini ta wurin Almasihu Yesu. 15 Saboda haka ɗaukacin waɗanda suka kammala a cikinmu, sai su bi wannan ra'ayi. In kuwa a game da wani abu ra'ayinku ya sha bambam, to, Allah zai bayyana muku wannan kuma. 16 Sai dai a duk inda muka kai, mu ci gaba da haka. 17 Ya ku 'yan'uwa, ku yi koyi da ni dukanku baki ɗaya, ku kuma dubi waɗanda zamansu yake daidai da gurbin da muka bar muku. 18 Domin da yawa waɗanda na sha gaya muku, yanzu kuma nake gaya muku, har da kawaye, suna bin Yesu, in ji su, amma su magabtan gicciyen Almasihu ne. 19 Ƙarshensu hallaka ne, Allahnsu ciki ne, rashin kunyarsu ita ce abar taƙamarsu, sun ƙwallafa ransu a kan al'amuran duniya. 20 Mu kuwa 'yan Mulkin Sama ne, daga can ne kuma muke ɗokin zuwan Mai Ceto, Ubangiji Yesu Almasihu, 21 wanda zai sāke jikin nan namu na ƙasƙanci, ya mai da shi kamar jikin nan nasa na ɗaukaka, da ikon nan nasa na sarayar da dukkan abubuwa a gare shi.

Filibiyawa 4

Ku Yi Farin Ciki da Ubangiji

1 Saboda haka ya 'yan'uwana, ƙaunatattuna, waɗanda nake bege, ku da kuke abin farin cikina da abin taƙamata kuma, ku dage ga Ubangiji, ya ku ƙaunatattuna. 2 Na gargaɗi Afodiya, na kuma gargaɗi Sintiki, su yi zaman lafiya da juna saboda su na Ubangiji ne. 3 Ya kai abokin bautata na hakika, ina roƙonka, ka taimaki matan nan, don sun yi fama tare da ni a al'amarin bishara, haka ma Kilemas da sauran abokan aikina, waɗanda sunayensu suke a rubuce a cikin Littafin Rai. 4 A kullum ku yi farin ciki da Ubangiji, har wa yau ina dai ƙara gaya muku, ku yi farin ciki. 5 Bari kowa ya san jimirinku. Ubangiji ya yi kusan zuwa. 6 Kada ku damu da kome, sai dai a kowane hali ku sanar da Allah bukatunku, ta wurin yin addu'a da roƙo, tare da gode wa Allah. 7 Ta haka salamar Allah, wadda ta fi gaban dukkan fahimta, za ta tsai da zukatanku da tunaninku ga Almasihu Yesu.

Ku Yi Tunanin Waɗannan Abubuwa

8 Daga ƙarshe kuma, 'yan'uwa, ko mene ne yake na gaskiya, ko mene ne abin girmamawa, ko mene ne daidai, ko mene ne tsattsarka, ko mene ne abin ƙauna, ko mene ne daɗɗaɗar magana, in ma da wani abu mafifici, ko abin da ya cancanci yabo, a kan waɗannan abubuwa za ku yi tunani. 9 Abin da kuka koya, kuka yi na'am da shi, abin kuma da kuka ji kuka gani a gare ni, sai ku aikata. Ta haka Allah mai zartar da salama zai kasance tare da ku.

Tabbatarwa da Kyautar da Filibiyawa suka Aika

10 Na yi farin ciki da Ubangiji ƙwarai da yake a yanzu kam, kularku gare ni ta farfaɗo, ko dā ma kuna kula da ni, dama ce ba ku samu ba. 11 Ba cewa, ina kukan rashi ba ne, domin na koyi yadda zan zauna da wadar zuci a cikin kowane irin hali da nake. 12 Na san yadda zan yi in yi zaman ƙunci, na kuma san yadda zan yi in yi zaman yalwa. A kowane irin hali duka na horu da ƙoshi da yunwa, yalwa da rashi. 13 Zan iya yin kome albarkacin wannan da yake ƙarfafa ni. 14 Amma kuwa kun kyauta da kuka taya ni cikin ƙuntatata. 15 Ku kuma Filibiyawa, ku kanku kun sani tun da aka fara yin bishara, sa'ad da na bar ƙasar Makidoniya, ba wata ikilisiyar da ta yi tarayya da ni wajen hidimar bayarwa da karɓa, sai dai ku kaɗai. 16 Ko sa'ad da nake Tasalonika ma, kun aiko mini da taimako ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba. 17 Ba cewa, don ina neman kyautarku ba ne, a'a, nemar muku amfani nake yi, a ƙara a kan ribarku. 18 An biya ni sarai, har fi. Bukatata ta biya, da na karɓi kyautar da kuka aiko mini ta hannun Abafaroditas, baiwa mai ƙanshi, hadaya abar karɓa, mai faranta wa Allah rai. 19 Allahna kuma zai biya muku kowace bukatarku daga cikin yalwar ɗaukakarsa da take ga Almasihu Yesu. 20 Ɗaukaka tă tabbata ga Allahnmu, Ubanmu, har abada abadin. Amin! Amin!

Gaisuwa

21 Ku gai da kowane tsattsarka cikin Almasihu Yesu. 'Yan'uwan da suke tare da ni suna gai da ku. 22 Dukan tsarkaka suna gai da ku, tun ba ma na fadar Kaisar ba. 23 Alherin Ubangiji Yesu Almasihu yă tabbata a zukatanku.

Kolosiyawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzon Almasihu Yesu da yardar Allah, tare da Timoti, ɗan'uwanmu, 2 zuwa ga tsarkaka da amintattun 'yan'uwa cikin Almasihu da suke a Kolosi. Alheri da salamar Allah Ubanmu su tabbata a gare ku.

Addu'ar Bulus domin Kolosiyawa Masu Bin Almasihu

3 A kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Almasihu, duk sa'ad da muke yi muku addu'a, 4 saboda mun ji labarin bangaskiyarku ga Almasihu Yesu, da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan tsarkaka, 5 saboda bege ga abin da aka tanadar muku a sama. Kun riga kun ji labarin wannan a maganar gaskiya, 6 wato, bisharar da ta zo muku, kamar yadda ta zo wa duniya duka, tana hayayyafa, tana kuma ƙara yaɗuwa, kamar yadda take yi a tsakaninku tun daga ranar da kuka ji, kuka kuma fahimci alherin Allah na hakika. 7 Haka ma kuka koya wurin Abafaras, ƙaunataccen abokin bautarmu. Shi amintaccen mai hidima ne na Almasihu a madadinmu, 8 ya kuma sanasshe mu ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu. 9 Shi ya sa tun a ran da muka ji labarin, ba mu fāsa yi muku addu'a ba, muna roƙo a cika ku da sanin nufin Allah da matuƙar hikima da fahimta na ruhu, 10 domin ku yi zaman da ya cancanci bautar Ubangiji, kuna faranta masa ta kowane fanni, kuna ba da amfani a kowane aiki nagari, kuna ƙaruwa da sanin Allah. 11 Allah yă dai ƙarfafa ku da matuƙar ƙarfi bisa ga ƙarfin ɗaukakarsa, domin ku jure matuƙa a game da haƙuri da farin ciki, 12 kuna gode wa Uba, wanda ya maishe mu mu isa samun rabo cikin gādon tsarkakan da suke a cikin haske. 13 Ya tsamo mu daga mulkin duhu, ya maishe mu ga mulkin ƙaunataccen Ɗansa, 14 wanda ta gare shi ne muka sami fansa, wato, gafarar zunubanmu.

Cikar Allah

15 Shi ne surar Allah marar ganuwa, magāji ne tun ba a halicci kome ba, 16 don ta gare shi ne aka halicci dukkan kome, abubuwan da suke a sama da abubuwan da suke a ƙasa, masu ganuwa da marasa ganuwa, ko kursiyai, ko masu mulki, ko masarauta, ko masu iko, wato, dukkan abubuwa an halicce su ne ta wurinsa, shi ne kuma makomarsu. 17 Shi ne a gaba da dukkan abubuwa, dukkan abubuwa kuma shi ne yake riƙe da su. 18 Shi ne kai ga jikin nan, wato Ikilisiya. Shi ne tushe, na farko a cikin masu tashi daga matattu, domin ta wurin kowane abu ya zama shi ne mafifici. 19 A gare shi dukkan cikar Allah ta tabbata, domin Allah yana farin ciki da haka, 20 da nufin ta wurinsa, Allah yă sulhunta dukkan abubuwa da shi kansa, na ƙasa ko na sama, yana ƙulla zumunci ta wurin jininsa na gicciye. 21 Ku kuma dā a rabe kuke da Allah, maƙiyansa a zuci, masu mugun aiki. 22 Amma a yanzu ya sulhunta ku ta hanyar jikinsa na mutuntaka, wato, ta wurin mutuwarsa, domin ya miƙa ku tsarkakakku, marasa aibu, marasa abin zargi kuma a gabansa. 23 Sai dai fa ku nace wa bangaskiya, zaunannu, kafaffu, ba tare da wata ƙaura daga begen nan na bishara wadda kuka ji ba, wadda aka yi wa dukkan talikan da suke a duniya, wadda kuma ni Bulus na zama mai hidimarta.

Hidimar Bulus zuwa ga Ikilisiya

24 To, a yanzu ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, a jikina kuma ina cikasa abin da ya saura ga wahalar Almasihu, da aka aza mini saboda jikinsa, wato Ikilisiya, 25 wadda na zama mai hidimarta bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da Maganar Allah sosai, 26 wato, asirin nan da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, amma a yanzu an bayyana shi ga tsarkakansa. 27 Su ne Allah ya so ya sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al'ummai, asirin nan kuwa shi ne Almasihu a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana. 28 Shi ne kuwa muke sanarwa, muna yi wa kowane mutum gargaɗi, muna kuma koya wa kowane mutum da matuƙar hikima, da nufin mu miƙa kowane mutum cikakke a cikin Almasihu. 29 Saboda wannan nake shan wahala, nake fama da matuƙar himma, wadda yake sa mini ta ƙarfin ikonsa.

Kolosiyawa 2

1 To, ina so ku san irin yawan shan faman da nake yi dominku, da waɗanda suke a Lawudikiya, da kuma duk waɗanda ba su taɓa ganina ba. 2 Sona a ƙarfafa musu zuciya, ƙauna tana haɗa su, har su sami dukkan mayalwaciyar fahimta tabbatacciya, da sanin asirin nan na Allah, wato Almasihu, 3 wanda shi ne taska, wato maɓoyar dukkan mafifitan hikima da sani. 4 Na faɗi wannan ne don kada kowa ya hilace ku da maganar yaudara. 5 Don ko da yake a jiki ba na nan, ai, ruhuna yana nan tare da ku, ina kuwa farin cikin ganin kyakkyawan tsarinku, da dagewarku a kan bangaskiyarku ga Almasihu. 6 Da yake kun yi na'am da Almasihu Yesu Ubangiji, to, sai ku tsaya a gare shi, 7 kuna kafaffu, kuna ginuwa a cikinsa, kuna tsayawa da bangaskiya gaba gaba, daidai yadda aka koya muku, kuna gode wa Allah a koyaushe.

Dukkan Cikar Rai ga Almasihu Take

8 Ku lura fa, kada kowa ya ribace ku ta hanyar iliminsa na yaudarar wofi, bisa ga al'adar mutane kawai, wato, bisa ga al'adun duniyar nan, ba bisa ga koyarwar Almasihu ba. 9 Domin a cikinsa ne cikin jiki dukkan cikar Allahntaka take tabbata. 10 A gare shi ne aka kammala ku, wanda yake shi ne shugaban dukkan sarauta da iko. 11 A cikinsa ne kuma aka yi muku kaciya, ba kuwa yin mutum ba, amma wadda Almasihu ya yi muku ce, ta wurin tuɓe halinku na mutuntaka. 12 An kuma binne ku tare da shi a wajen baftisma, inda kuma aka tashe ku tare da shi saboda bangaskiyarku ga ikon Allah, wanda ya tashe shi daga matattu. 13 Ku kuma da kuke matattu saboda laifofinku, marasa kaciya ta jiki, Allah ya raya ku tare da Almasihu, ya yafe mana dukkan laifofinmu, 14 ya kuma yanke igiyar nan ta Shari'a da ta ɗaure mu da dokokinta, ya ɗauke ta, ya kafe ta da ƙusa a jikin gicciyensa. 15 Ya ƙwace makaman masarauta da na masu iko, ya kunyata su a fili, da ya yi nasara a kansu a kan gicciyen.

Ku Ƙwallafa Ranku a kan Abubuwan da suke a Sama

16 Saboda haka, kada ku damu in wani ya zarge ku a kan abin da kuke ci, ko abin da kuke sha, ko kuwa kan rashin kiyayewar wani idi, ko tsayawar wata, ko Asabar. 17 Waɗannan kam, isharori ne kawai na abin da zai auku, amma Almasihu shi ne ainihinsu. 18 Kada ku yarda kowane mutum ya ɓata ku, da cewa shi wani abu ne saboda, ya ga wahayi, ya kuma lazamta da yin tawali'un ƙarya, in ji shi kuma yana yi wa mala'iku sujada. Irin wannan mutum kumbura kansa yake yi ba dalili, sai ta son zuciya irin na halin mutuntaka, 19 bai kuwa manne wa kan ba, wanda ta gare shi ne dukkan jiki yake amfana, yake kuma a haɗe, ta wurin gaɓoɓi da jijiyoyi, yake kuma girma da girman da Allah yake sawa. 20 Idan mutuwarku tare da Almasihu ta 'yanta ku daga al'adun duniyar nan, me ya sa kuke zama har yanzu kamar ku na duniya ne? Don me kuke bin dokokin da aka yi bisa ga umarnin 'yan adam da koyarwarsu, 21 kamar su, “Kada ka kama, kada ka ɗanɗana, kada ka taɓa?” 22 (Wato, ana nufin abubuwan da, in an ci su sukan ruɓa duka.) 23 Irin waɗannan dokoki kam, lalle suna da'awar hikima ta wajen yin ibadar da aka ƙago, ta wurin yin tawali'un ƙarya da kuma wahalar da jiki, amma ko ɗaya ba su da wata daraja ga sarrafar halin mutuntaka.

Kolosiyawa 3

1 To, da yake an tashe ku tare da Almasihu, sai ku nemi abubuwan da suke a Sama, inda Almasihu yake, a zaune a dama ga Allah. 2 Ku ƙwallafa ranku a kan abubuwan da suke Sama, ba a kan abubuwan da suke a ƙasa ba. 3 Gama kun mutu, ranku kuwa a ɓoye yake a gun Almasihu cikin Allah. 4 Sa'ad da Almasihu wanda yake shi ne ranmu ya bayyana, sai ku ma ku bayyana tare da shi a cikin ɗaukaka.

Tsohon Rai da Sabon Rai

5 Saboda haka, sai ku kashe zukatanku ga sha'awace-sha'wacen duniya, wato fasikanci, da aikin lalata, da muguwar sha'awa, da mummunan buri, da kuma kwaɗayi, wanda shi ma bautar gumaka ne. 6 Saboda waɗannan abubuwa ne fushin Allah yake sauka a kan kangararru. 7 A dā kuna bin waɗannan sa'ad da suke jiki a gare ku. 8 Amma yanzu sai ku yar da duk waɗannan ma, wato fushi, da hasala, da ƙeta, da yanke, da alfasha. 9 Kada ku yi wa juna ƙarya, da yake kun yar da halinku na dā, da ayyukansa, 10 kun ɗauki sabon halin nan da ake sabuntawa ga sani, bisa ga kamannin Mahaliccinsa. 11 A nan kam, ba hanyar nuna bambanci a tsakanin Ba'al'umme da Bayahude, ko mai kaciya da marar kaciya, ko bare da baubawa, ko ɗa da bawa, sai dai Almasihu shi ne kome, shi kuma yake cikinmu duka. 12 Saboda haka, sai ku ɗauki halin tausayi, da kirki, da tawali'u, da salihanci, da haƙuri, idan ku zaɓaɓɓu ne na Allah, tsarkaka, ƙaunatattu, 13 kuna jure wa juna, in kuma wani yana da ƙara game da wani, sai su yafe wa juna. Kamar yadda Ubangiji ya yafe muku, ku kuma sai ku yafe. 14 Fiye da waɗannan duka, ku ɗau halin ƙauna, wadda dukkan kammala take ƙulluwa a cikinta. 15 Salamar Almasihu kuma tă mallaki zuciyarku, domin lalle ga haka aka kira ku in kuna jiki guda, ku kuma kasance masu gode wa Allah. 16 Maganar Almasihu tă kahu a cikin zuciyarku a yalwace, kuna koya wa juna, kuna yi wa juna gargaɗi da matuƙar hikima ta wurin rairar waƙoƙin Zabura da na yabon Allah, kuna kuma raira waƙa ga Allah, kuna gode masa tun daga zuci. 17 Kome kuke yi, a game da magana ko aikatawa, ku yi duka da sunan Ubangiji Yesu, kuna gode wa Allah Uba ta wurinsa.

Zaman Dacewa na Sabon Rai

18 Ku matan aure, ku bi mazanku yadda ya dace a cikin Ubangiji. 19 Ku maza, ku ƙaunaci matanku, kada kuma ku yi musu kaushin hali. 20 Ku 'ya'ya, ku yi wa iyayenku biyayya ta kowane hali, domin haka Ubangiji yake so. 21 Ku ubanni, kada ku ƙuntata wa 'ya'yanku, domin kada su karai. 22 Ku bayi, ku yi biyayya ga waɗanda suke iyayengijinku na duniya ta kowace hanya, ba da aikin ganin ido ba, kamar masu son faranta wa mutane rai, sai dai da zuciya ɗaya, kuna tsoron Ubangiji. 23 Kome za ku yi, ku yi shi da himma kuna bauta wa Ubangiji ne, ba mutum ba, 24 da yake kun sani Ubangiji zai ba ku gādo sakamakonku. Ubangiji Almasihu fa kuke bauta wa! 25 Mai mugun aiki kuwa za a sāka masa da mugun aikin da ya yi, babu kuma tāra.

Kolosiyawa 4

1 Ku iyayengiji kuma, riƙi bayinku da gaskiya da daidaita, da yake kun sani ku ma kuna da Ubangiji a Sama. 2 Ku lazamci yin addu'a, kuna zaune a faɗake a kanta sosai, tare da gode wa Allah, 3 mu ma ku yi mana addu'a Allah ya buɗe mana hanyar yin Maganarsa, mu sanar da asirin Almasihu, wanda saboda shi ne nake a ɗaure, 4 domin in bayyana shi sosai, kamar yadda ya kamata in faɗa. 5 Ku tafiyar da al'amuranku da hikima a cikin zamanku tare da marasa bi, kuna matuƙar amfani da lokaci. 6 A kullum maganarku ta zama mai ƙayatarwa, mai daɗin ji, domin ku san irin amsar da ta dace ku ba kowa.

Gaisuwa

7 Tikikus zai sanar da ku duk abin da nake ciki. Shi ƙaunataccen ɗan'uwa ne, amintaccen mai hidima, abokin bautarmu kuma a cikin Ubangiji. 8 Na aiko shi a gare ku musamman, domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa muku zuciya. 9 Ga kuma Unisimas a nan tare da shi, amintaccen ɗan'uwa ƙaunatacce, wanda shi ma a cikinku yake. Su za su gaya muku duk abin da ya faru a nan. 10 Aristarkus, abokin ɗaurina, yana gaishe ku, haka kuma Markus, wanda kakansu ɗaya ne da Barnaba. Shi ne aka riga aka yi muku umarni a game da shi. In dai ya zo wurinku, ku karɓe shi. 11 Yasuwa kuma da ake kira Yustus yana gaishe ku. Wato, cikin abokan aikina ga Mulkin Allah, waɗannan su kaɗai ne daga cikin Yahudawa masu bi, sun kuwa sanyaya mini zuciya. 12 Abafaras wanda yake ɗaya daga cikinku, bawan Almasihu Yesu, yana gaishe ku, a kullum yana yi muku addu'a da himma, ku dage, kuna cikakku, masu haƙƙaƙewa cikin dukkan nufin Allah. 13 Na shaide shi, lalle ya yi muku aiki ƙwarai da gaske, da kuma waɗanda suke na Lawudikiya da na Hirafolis. 14 Luka, ƙaunataccen likitan nan, da Dimas suna gaishe ku. 15 A gayar mini da 'yan'uwa na Lawudikiya, da kuma Nimfa da ikilisiyar da take taruwa a gidanta. 16 Sa'ad da aka karanta wasiƙar nan a gabanku, ku sa a karanta ta kuma a gaban ikilisiyar da take a Lawudikiya, ku kuma ku karanta tasu, wato ta Lawudikiyawa. 17 Ku kuma faɗa wa Arkibus ya mai da hankali ya cika hidimar da Ubangiji ya sa shi. 18 Ni Bulus, ni nake rubuta gaisuwar nan da hannuna. Ku tuna da ɗaurina. Alheri yă tabbata a gare ku.

1 Tasalonikawa

1 Tasalonikawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, da Sila, da Timoti, zuwa ga Ikilisiyar Tasalonikawa, wadda take ta Allah uba da Ubangiji Yesu Almasihu. Alheri da salama su tabbata a gare ku.

Bangaskiyar Tasalonikawa da irin Zamansu

2 A kullum muna gode wa Allah saboda ku duka, koyaushe muna ambatonku a cikin addu'armu, 3 ba ma fāsa tunawa da aikinku na bangaskiya a gaban Allahnmu, Ubanmu, da famar da kuke yi domin ƙauna, da kuma begen ku mara gushewa ga Ubangijinmu Yesu Almasihu. 4 Domin mun sani, 'yan'uwa, ƙaunatattu na Allah, shi ya zaɓe ku, 5 domin bishararmu ba da magana kawai ta zo muku ba, amma da iko, da Ruhu Mai Tsarki, da kuma matuƙar tabbatarwa. Kun dai san irin zaman da muka yi a cikinku domin ku amfana, 6 har kuka zama masu koyi da mu, da kuma Ubangiji, kuka kuma karɓi Maganar Allah game da farin cikin da Ruhu Mai Tsarki yake sawa, ko da yake ta jawo muku tsananin wahala. 7 Ku ma har kuka zama abin koyi ga dukan masu ba da gaskiya a ƙasar Makidoniya da ta Akaya. 8 Domin daga gare ku ne aka baza Maganar Ubangiji, ba ma a ƙasar Makidoniya da ta Akaya kaɗai ba, har ma a ko'ina bangaskiyarku ga Allah ta shahara, har ma ya zamana, ba sai lalle mun faɗa ba. 9 Domin su da kansu suke ba da labarin irin ziyartarku da muka yi, da kuma yadda kuka rabu da gumaka, kuka juyo ga Allah, domin ku bauta wa Allah Rayayye na gaskiya, 10 ku kuma saurari komowar Ɗansa daga Sama, wanda ya tasa daga matattu, wato Yesu, mai kuɓutar da mu daga fushin nan mai zuwa.

1 Tasalonikawa 2

Hidimar Bulus a Tasalonika

1 Ai, ku da kanku kun sani, 'yan'uwa, ziyartarku da muka yi, ba a banza take ba. 2 Amma ko da yake dā ma can mun sha wuya, an kuma wulakanta mu a Filibi, kamar yadda kuka sani, duk da haka da taimakon Allahnmu muka sanar da ku bisharar Allah gabagaɗi, amma sai da matsanancin fama. 3 Ai, gargaɗin da muke yi muku babu bauɗewa ko munafunci a ciki, balle yaudara, 4 sai dai kamar yadda Allah ya yarda da mu, ya damƙa mana amanar bishara, haka muke sanar da ita, ba domin mu faranta wa mutane rai ba, sai dai domin mu faranta wa Allah, shi da yake jarraba zukatanmu. 5 Yadda kuka sani, ba mu taɓa yin daɗin baki ko kwaɗayi ba. Allah kuwa shi ne shaida. 6 Ba mu kuwa taɓa neman girma ga mutane ba, ko a gare ku, ko ga waɗansu, ko da yake da muna so, da mun mori ikon nan namu na manzannin Almasihu. 7 Amma mun nuna taushin hali a cikinku, kamar yadda mai goyo ku kula da goyonta. 8 Saboda kuma muna Kaunarku ƙwarai da gaske ne shi ya sa muke jin daɗin ba da har rayukanmu ma saboda ku, ba yi muku bisharar Allah kaɗai ba, don kun shiga ranmu da gaske. 9 Ya ku 'yan'uwa, kuna iya tunawa da wahala da famar da muka sha, har muna aiki dare da rana, don kada mu nauyaya wa kowane ɗayanku, duk sa'ad da muke yi muku bisharar Allah. 10 Ku shaidu ne, haka kuma Allah, game da irin halin da muka nuna muku, ku masu ba da gaskiya, wato halin tsarki da na adalci da na rashin aibu. 11 Domin kun san yadda muka yi wa kowannenku gargaɗi kamar uba da 'ya'yansa ne, muna ta'azantar da ku, muna kuma ƙarfafa muku umarnin, cewa 12 ku yi zaman da ya cancanci bautar Allah, wanda yake kiranku ga mulkinsa da ɗaukakarsa. 13 Saboda wannan ne kuma muke gode wa Allah ba fasawa, domin sa'ad da kuka karɓi Maganar Allah ta bakinmu, ba ku karɓe ta kamar maganar mutum ce ba, sai dai ainihin yadda take, Maganar Allah, wadda take aiki a cikin zuciyarku, ku masu ba da gasikya. 14 'Yan'uwa, ku ne kuka zama masu koyi da ikilisiyoyin Allah da suke na Almasihu Yesu, waɗanda suke a ƙasar Yahudiya, don ku ma kun sha wuya a hannun mutanen ƙasarku, kamar yadda ikilisiyoyin nan ma suka sha a hannun Yahudawa, 15 waɗanda suka kashe Ubangiji Yesu da annabawa, suka kuma kore mu, ba sa yin aikin da Allah yake so, masu gāba ne kuma da dukan mutane, 16 suna hana mu yi wa al'ummai wa'azi, don kada su sami ceto. Ta haka a kullum suke cika mudun zunubansu. Amma fa fushin Allah ya aukar musu.

Nufin Bulus ya sāke Ziyartar Ikilisiya

17 Ya ku 'yan'uwa, ko da yake mun yi kewarku saboda an raba mu a ɗan lokaci kaɗan, duk da haka kuna cikin zukatanmu, mun kuwa ƙara ɗokanta mu gan ku ido da ido, matuƙar ɗoki. 18 Mun dai yi niyyar zuwa wurinku, ni Bulus, ba sau ɗaya ba, ba sau biyu ba, amma Shaidan ya hana. 19 Su wane ne abin sa zuciyarmu, da abin farin cikinmu, da kuma abin taƙamarmu a gaban Ubangiji Yesu a ranar komowarsa, in ba ku ba? 20 Ai, ku ne abin taƙamarmu, da abin farin cikinmu.

1 Tasalonikawa 3

1 Saboda haka, da muka kasa daurewa, sai muka ga ya kyautu a bar mu a Atina mu kaɗai, 2 muka kuma aiki Timoti ɗan'uwanmu, bawan Allah kuma na al'amarin bisharar Almasihu, ya kafa ku, ya kuma ƙarfafa ku a kan al'amarin bangaskiyarku, 3 don kada kowa ya raurawa a cikin tsananin wahalar nan. Ai, ku kanku kun sani an nufe mu da haka ne. 4 Domin dā ma sa'ad da muke tare, mun gaya muku tun da wuri, cewa za mu sha wahala. Haka kuwa ya auku, kamar yadda kuka sani. 5 Saboda haka, ni ma da na kasa daurewa, sai na aika in sami labarin bangaskiyarku, da fatan kada ya zamana mai ruɗin nan ya riga ya ruɗe ku, famarmu kuma yă zama banza. 6 Amma ga shi, a yanzu da Timoti ya dawo daga wurinku, ya yi mana albishir a kan bangaskiyarku da ƙaunarku, da kuma yadda kuke tunawa da mu da alheri a koyaushe, har kuna begen ganinmu, kamar yadda mu ma muke yi. 7 Saboda haka 'yan'uwa, cikin dukan wahala da ƙuncin da muka sha, an sanyaya mana zuciya a game da ku, albarkacin bangaskiyarku. 8 A yanzu kam a raye muke, in dai kun tsaya ga Ubangiji. 9 Wace irin godiya za mu yi wa Allah saboda ku, a kan matuƙar farin cikin da muke yi a gaban Allahnmu ta dalilinku! 10 Dare da rana muna nacin addu'a ƙwarai mu sami ganinku ido da ido, mu kuma cikasa abin da ya gaza wajen bangaskiyarku. 11 Muna fata dai Allahnmu, ubanmu, shi kansa, da kuma Ubangijinmu Yesu, ya kai mu gare ku. 12 Ku kuma, Ubangiji ya sa ku ƙaru, ku kuma yalwata da ƙaunar juna da dukan mutane, kamar yadda muke yi muku, 13 har ya tsai da zukatanku ku zama marasa abin zargi cikin tsarki a gaban Allahnmu, Ubanmu, a ranar komowar Ubangijinmu Yesu, tare da dukan tsarkakansa.

1 Tasalonikawa 4

Zaman da ya Dace a Gaban Allah

1 Daga ƙarshe kuma 'yan'uwa, muna roƙonku, muna kuma yi muku gargaɗi saboda Ubangiji Yesu, cewa kamar yadda kuka koya a wurinmu, irin zaman da ya dace da ku, ku faranta wa Allah rai, kamar yadda yanzu ma kuke yi, to, sai ku ƙara yin haka ƙwarai da gaske, 2 domin kun san umarnin nan da muka yi muku da iznin Ubangiji Yesu. 3 Gama wannan shi ne nufin Allah, wato ku yi zaman tsarki, ku guje wa fasikanci, 4 kowannenku kuma ya san yadda zai auro matarsa da tsarki da mutunci, 5 ba ta muguwar sha'awa ba, yadda al'ummai suke yi, waɗanda ba su san Allah ba. 6 A cikin wannan al'amari kuwa kada kowa ya keta haddi, har ya cuci ɗan'uwansa, domin Ubangiji mai sakamako ne a kan dukkan waɗannan abubuwa, kamar yadda muka gargaɗe ku, muka tabbatar muku tun da wuri. 7 Ai, ba a zaman ƙazanta ne Allah ya kira mu ba, amma ga zaman tsarki ne. 8 Saboda haka, kowa ya ƙi yarda da wannan, ba mutum ya ƙi ba, amma Allah ya ƙi, shi da ke ba ku Ruhunsa Mai Tsarki. 9 A game da ƙaunar 'yan'uwa kuma, ba lalle sai wani ya rubuto muku ba. Ai, ku kanku ma, Allah ya koya muku ku ƙaunaci juna. 10 Hakika kuwa kuna ƙaunar dukan 'yan'uwa a duk ƙasar Makidoniya. Sai dai muna muku gargaɗi, 'yan'uwa, ku ƙara yin haka ƙwarai da gaske, 11 kuna himmantuwa ga zaman lafiya, kuna kula da sha'anin gabanku kawai, kuna kuma aiki da hannunku, kamar yadda muka umarce ku, 12 domin ku zama masu mutunci ga waɗanda ba masu bi ba, kada kuma ku rataya a jikin kowa.

Matattu da Waɗanda suke a Raye a Zuwan Ubangiji

13 Amma 'yan'uwa, ba mu so ku jahilta game da waɗanda suka yi barci, don kada ku yi baƙin ciki kamar yadda sauran suke yi, marasa bege. 14 Tun da muka gaskata Yesu ya mutu, ya kuwa tashi, haka kuma albarkacin Yesu, Allah zai kawo waɗanda suka yi barci su zo tare da shi. 15 Muna kuwa shaida muku bisa ga faɗar Ubangiji, cewa mu da muka wanzu, muke kuma a raye har ya zuwa komowar Ubangiji ko kaɗan ba za mu riga waɗanda suka yi barci tashi ba, 16 domin Ubangiji kansa ma zai sauko daga Sama, da kira mai ƙarfi, da muryar babban mala'ika, da kuma busar ƙahon Allah. Waɗanda suka mutu suna na Almasihu, su ne za fara tashi, 17 sa'an nan sai mu da muka wanzu, muke a raye, za a ɗauke mu tare da su ta cikin gajimare, mu sadu da Ubangiji a sararin sama, sai kuma kullum mu kasance tare da Ubangiji. 18 Saboda haka, sai ku yi wa juna ta'aziyya da wannan magana.

1 Tasalonikawa 5

Ku Zauna a Faɗake don Zuwan Ubangiji

1 Amma ga zancen ainihin lokaci ko rana, ba lalle sai an rubuto muku kome ba. 2 Domin ku da kanku kun sani sarai, ranar Ubangiji za ta zo ne kamar ɓarawo da dare. 3 Lokacin da mutane suke cewa, “Muna zaman salama da zaman lafiya,” wuf; sai halaka ta auko musu, kamar yadda naƙuda take kama mace mai ciki, ba kuwa hanyar tsira. 4 Amma, ai, ba a cikin duhu kuke ba, 'yan'uwa, har da ranar nan za ta mamaye ku kamar ɓarawo. 5 Domin duk mutanen haske kuke, na rana kuma. Mu ba na dare ko na duhu ba ne. 6 Ashe, saboda haka kada mu yi barci yadda waɗansu suke yi, sai dai mu zauna a faɗake, da natsuwa. 7 Don masu barci da daddare suke barci, masu sha su bugu ma da daddare suke sha su bugu. 8 Amma da yake mu na rana ne, sai mu natsu, muna saye da sulken bangaskiya da ƙauna, muna begen samun ceto, shi ne kuma kwalkwakinmu. 9 Allah bai ƙaddara mu ga fushinsa ba, sai dai ga samun ceto ta wurin Ubangijinmu Yesu Almasihu, 10 wanda ya mutu saboda mu, domin ko muna a raye, ko muna barci, mu zama muna tare da shi. 11 Saboda haka, sai ku ƙarfafa wa juna zuciya, kuna riƙa inganta juna, kamar dai yadda kuke yi.

Gargaɗi da kuma Gaisuwa

12 Amma muna roƙonku 'yan'uwa, ku girmama masu fama da aiki a cikinku, wato waɗanda suke shugabanninku cikin Ubangiji, suke kuma yi muku gargaɗi. 13 Ku riƙe su da mutunci ƙwarai game da ƙauna saboda aikinsu. Ku yi zaman lafiya da juna. 14 Muna kuma yi muku gargaɗi, 'yan'uwa, ku tsawata wa malalata, ku ƙarfafa masu rarraunar zuciya, ku taimaki marasa tsayayyiyar zuciya, ku yi haƙuri da kowa da kowa. 15 Ku lura fa, kada kowa ya rama mugunta da mugunta. Sai dai kullum ku nace yi wa juna aiki nagari, da kuma dukkan mutane. 16 Ku riƙa yin farin ciki a kullum. 17 Ku riƙa yin addu'a ba fāsawa. 18 Ku godiya ga Allah a kowane hali, domin shi ne nufin Allah a game da ku ta wurin Almasihu Yesu. 19 Kada ku danne maganar Ruhu. 20 Kada ku raina annabci, 21 sai dai ku jarraba kome, ku riƙi abin da yake nagari kankan. 22 Ku yi nesa da kowace irin mugunta. 23 Allah kansa, mai zartar da salama, yă tsarkake ku sarai, ya kuma kiyaye ruhunku da ranku da jikinku ƙalau, ku kasance marasa abin zargi a ranar komowar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 24 Wanda yake kiranku ɗin nan mai alkawari ne, zai kuwa zartar. 25 Ya ku 'yan'uwa, ku yi mana addu'a. 26 Ku gai da dukkan 'yan'uwa da tsattsarkar sumba. 27 Na gama ku da Ubangiji, a karanta wa dukkan 'yan'uwa wasiƙar nan. 28 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku.

2 Tasalonikawa 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, da Sila, da Timoti, zuwa ga Ikilisiyar Tasalonikawa, wadda take ta Allah ubanmu da Ubangiji Yesu Almasihu. 2 Alheri da salama na Allah Uba, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Bayyanar Almasihu don Yin Hukunci

3 Lalle ne a kullum mu gode wa Allah saboda ku, 'yan'uwa, haka kuwa ya kyautu, da yake bangaskiyarku haɓaka take yi ƙwarai da gaske, har ma ƙaunar kowane ɗayanku ga juna ƙaruwa take yi. 4 Saboda haka, mu kanmu ma taƙama muke yi da ku a cikin ikilisiyoyin Allah, saboda jimirinku, da bangaskiyarku a cikin yawan tsananin da kuke sha, da ƙuncin da kuke a ciki. 5 Wannan kuwa ita ce tabbatar hukunci mai adalci na Allah, domin a lasafta ku a cikin waɗanda suke cancanci zama a Mulkin Allah, wanda kuke shan wuya dominsa, 6 domin kuwa Allah ya ga adalci ne, ya yi sakamakon ƙunci ga waɗanda suke ƙuntata muku, 7 yă kuma ba ku hutu har da mu ma, ku da ake ƙuntata wa ɗin, a ranar bayyanar Ubangiji Yesu daga Sama tare da manyan mala'ikunsa, a cikin wuta mai ruruwa, 8 yana ta sāka wa waɗanda suke ƙi sanin Allah, da kuma waɗanda suke ƙi bin bisharar Ubangijinmu Yesu. 9 Za su sha hukuncin madawwamiyar hallaka, suna a ware da zatin Ubangiji, da kuma, maɗaukakin ikonsa, 10 wato, a lokacin da ya dawo, tsarkakansa su ɗaukaka shi, duk masu ba da gaskiya kuma su yi al'ajabinsa a ranar nan, don kun gaskata shaidar da muka yi muku. 11 Da wannan maƙasudi, a kullum muke yi muku addu'a, Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ya biya muku duk muradinku na yin nagarta, da aikin bangaskiya ta wurin ƙarfin ikonsa, 12 don a ɗaukaka sunan Ubangijinmu Yesu a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu.

2 Tasalonikawa 2

Sarkin Tawaye

1 To, a game da komowar Ubangijinmu Yesu Almasihu, da kuma taruwarmu mu sadu da shi, muna roƙonku 'yan'uwa, 2 kada ku yi saurin jijiguwa a zukatanku, ku kuwa hankalinku ya tashi, saboda faɗar wani ruhu, ko wani jawabi, ko wata wasiƙa a kan cewa daga gare mu suke, cewa ranar Ubangiji ta zo. 3 Kada ku yarda kowa ya yaudare ku ko ta halin ƙaƙa, domin wannan rana ba za ta zo ba, sai an yi fanɗarewar nan, sarkin tawaye kuma ya bayyana, wato, hallakakken nan. 4 Shi ne magabci, mai ɗaukaka kansa, yana gāba da duk abin da ya shafi sunan Allah, ko kuma wanda ake yi wa ibada. Har ma yakan zauna a Haikalin Allah, yana cewa, shi ne Allah. 5 Ashe, ba ku tuna ba, nakan gaya muku haka tun muna tare? 6 To, a yanzu dai kun san abin da yake tare shi, don kada ya bayyana kafin lokacinsa. 7 Ko a yanzu ma tawayen nan, wanda ba shi fahimtuwa, an fara shi, amma farawar abin da zai faru, sai an ɗauke wanda yake hana shi tukuna. 8 A sa'an nan ne fa sarkin tawayen zai bayyana, Ubangiji Yesu kuwa zai hallaka shi da hucin bakinsa, ya kuma shafe shi da bayyanarsa a ranar komowarsa. 9 Mai tawayen nan kuwa, zai zo ne bisa ga ikon Shaiɗan, yana aikata abubuwan al'ajabi, da alamu, da aikin dabo na ƙarya iri iri, 10 yana kuma yaudarar waɗanda suke a hanyar hallaka, muguwar yaudara, domin sun ƙi ƙaunar gaskiya har yadda za su sami ceto. 11 Saboda haka, Allah zai auko masu da wata babbar ɓatan basira don su gaskata ƙarya, 12 don duk a hukunta waɗanda suke ƙi gaskata gaskiya, suke kuma jin daɗin mugunta.

Ya Zaɓe ku ku Sami Ceto

13 Ya ku 'yan'uwa, ƙaunatattun Ubangiji, lalle ne kullum mu gode wa Allah saboda ku, domin Allah ya zaɓe ku, don ku fara samun ceto ta wurin tsarkakewar Ruhu, da kuma amincewarku da gasikya. 14 Domin wannan maƙasudi ya kira ku, ta wurin bishararmu, domin ku sami ɗaukakar Ubangijinmu Yesu Almasihu. 15 Saboda haka, 'yan'uwa, sai ku dage, ku kuma riƙi ka'idodin da muka koya muku kankan, ko da baka ko ta wurin wasiƙa. 16 To, Ubangijinmu Yesu Almasihu kansa, da kuma Allah Ubanmu, wanda ya ƙaunace mu, ya kuma ba mu madawwamiyar ta'aziyya da kyakkyawan bege ta wurin alherinsa, 17 yă ta'azantar da ku, ya kuma ƙarfafa ku ga yin kowane kyakkyawan aiki da magana.

2 Tasalonikawa 3

Addu'a Dominmu

1 Daga ƙarshe kuma 'yan'uwa, ku yi mana addu'a, Maganar Ubangiji ta yi saurin yaɗuwa, ta sami ɗaukaka, kamar yadda ta samu a gare ku, 2 a kuma cece mu daga fanɗararrun mutane, mugaye. Don ba duka ne suke da bangaskiya ba. 3 Amma Ubangiji mai alkawari ne, zai kuwa kafa ku, ya tsare ku daga Mugun nan. 4 Mun kuma amince da ku a game da Ubangiji, cewa kuna bin umarnin da muka yi muku, za ku kuma riƙa bi. 5 Ubangiji yă tattaro hankalinku a kan ƙaunar nan ta Allah, da kuma jimirin nan na Almasihu.

Wajibi ne a Yi Aiki

6 To, 'yan'uwa, muna yi muku umarni da sunan Ubangijinmu Yesu Almasihu, ku fita daga sha'anin kowane ɗan'uwa malalaci, wanda ba ya bin ka'idodin da kuka samu a wurinmu. 7 Ai, ku kanku kun san yadda ya kamata ku yi koyi da mu, domin sa'ad da muke a tare, ba mu nuna muku lalaci ba, 8 ba mu kuwa ci abincin kowa a banza ba, sai dai mun sha wahala da fama, muna aiki dare da rana, don kada mu nawaita wa kowane ɗayanku. 9 Ba don ba mu da halaliya a wurinku ba ne, a'a, sai dai don mu zama abin misali a gare ku kawai, don ku yi koyi da mu. 10 Ai, ko dā ma, sa'ad da muke a tare, mun yi muku wannan umarni, cewa duk wanda ya ƙi yin aiki, kada a ba shi abinci. 11 Gama mun ji labari cewa waɗansunku malalata ne kawai, ba sa aikin kome, masu shisshigi ne kurum. 12 To, irin waɗannan mutane muna yi musu umarni, muna kuma gargaɗinsu da izinin Ubangiji Yesu Almasihu, su riƙa aiki da natsuwa, suna ci da kansu. 13 Amma ku 'yan'uwa, kada ku gaji da yin nagari. 14 In wani ya ƙi bin abin da muka faɗa a wasiƙar nan, sai fa ku lura da shi, kada ma ku yi cuɗanya da shi, don yă kunyata. 15 Amma kada ku ɗauke shi a kan abokin gāba, sai dai ku gargaɗe shi a kan shi ɗan'uwa ne.

Sa Albarka

16 To, Ubangiji kansa, mai zartar da salama, yă ba ku salama a koyaushe a kowane hali. Ubangiji ya kasance tare da ku duka. 17 Ni Bulus, ni nake rubuto wannan Gaisuwa da hannuna. Ita ce kuwa shaidar kowace wasiƙata. Rubutun hannuna ke nan. 18 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a gare ku daka.

1 Timoti 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzon Almasihu Yesu bisa ga umarnin Allah Mai Cetonmu, da kuma na Almasihu Yesu abin begenmu, 2 zuwa ga Timoti, ɗana na hakika, ta wajen bangaskiya. Alheri, da jinƙai, da salama na Allah Uba, da na Almasihu Yesu Ubangijinmu su tabbata a gare ka.

Faɗaka a kan wata Koyarwa Dabam

3 Kamar yadda na roƙe ka, ka dakata a Afisa sa'ad da za ni ƙasar Makidoniya, ka gargaɗi waɗansu mutane kada su koyar da wata koyarwa dabam, 4 kada kuma su ɓata zarafinsu a wajen almara da yawan ƙididdigar asali marar iyaka, waɗanda sukan haddasa gardandami, a maimakon riƙon amanar al'amuran Allah da bangaskiya. 5 Alhali kuwa manufar gargaɗinmu ƙauna ce, wadda take bulbulowa daga tsarkakakkiyar zuciya, da lamiri mai kyau, da kuma sahihiyar bangaskiya. 6 Waɗansu sun kauce wa waɗannan al'amura, har sun bauɗe, sun shiga zancen banza. 7 Suna burin zama masanan Attaura, ba tare da fahimtar abin da suke faɗa ba, balle matsalar da suke taƙamar haƙiƙicewa a kai. 8 To, mun san Shari'a aba ce mai kyau, in mutum ya yi aiki da ita yadda ya wajaba, 9 yana kuma tunawa, cewa ita Shari'a ba a kafa ta domin masu adalci ba, sai dai kangararru, da marasa biyayya, da marasa bin Allah, da masu zunubi, da marasa tsarkaka, da masu saɓon Allah, da masu kashe iyaye maza da mata, da masu kisankai, 10 da fasikai, da masu luɗu, da masu sace mutane, da maƙaryata, da masu shaidar zur, da kuma duk sauran abin da ya sāɓa sahihiyar koyarwar nan, 11 bisa ga bishara mai daraja ta Allah abar yabo, wadda aka danƙa mini.

Godiyar Bulus domin Jinƙai

12 Ina gode wa Almasihu Yesu Ubangijinmu, wanda ya ƙarfafa ni, saboda ya amince da ni, har ya sa ni aikinsa, 13 ko da yake dā can sāɓo nake yi, ina tsanantarwa, ina wulakantarwa, duk da haka, sai dai aka yi mini jinƙai, domin na yi haka ne da jahilci saboda rashin bangaskiya. 14 Alherin Ubangijinmu kuma ya kwararo mini ƙwarai da gaske, a game da bangaskiya, da kuma ƙaunar da take ga Almasihu Yesu. 15 Maganar nan tabbatacciya ce, ta kuma cancanci a karɓe ta ɗungum cewa, “Almasihu Yesu ya shigo duniya ne domin ceton masu zunubi,” ni ne kuwa babbansu. 16 Duk da haka an yi mini jinƙai musamman, don ta kaina, ni babbansu, Yesu Almasihu yă nuna cikakken haƙurinsa, in zama gurbi ga waɗanda a nan gaba za su gaskata da shi su sami rai madawwami. 17 Girma da ɗaukaka su tabbata ga Sarkin zamanai, marar mutuwa, marar ganuwa, Allah Makaɗaici, har abada abadin. Amin, amin. 18 Na danƙa maka wannan umarni, ya ɗana Timoti, bisa ga annabce-annabcen da dā aka faɗa a kanka, domin ka ƙarfafu ta wurinsu, ka yi yaƙi mai kyau, 19 kana riƙe da bangaskiya da lamiri mai kyau. Gama waɗansu mutane, saboda ƙin kasa kunna ga lamirinsu, suka lalatar da bangaskiyarsu. 20 Cikinsu har da Himinayas da Askandari, waɗanda na miƙa wa Shaiɗan, don su horo su yin sāɓo.

1 Timoti 2

Gargaɗi a kan Addu'a

1 Da farko dai ina gargaɗi, cewa a yi ta roƙon Allah, ana addu'a, ana godo, ana gode wa Allah saboda dukkan mutane, 2 da sarakuna da kuma duk waɗanda suke a manyan maƙamai, don mu zauna lafiya, rai a kwance, muna bin Allah sosai a cikin natsuwa. 3 Wannan kyakkyawan abu ne, kuma abin karɓa ne a gun Allah Mai Cetonmu, 4 wanda yake son dukkan mutane su sami ceto, su kuma kai ga sanin gaskiya. 5 Domin Allah ɗaya ne, matsakanci kuma ɗaya ne, a tsakanin Allah da mutane, Almasihu Yesu, mutum, 6 wanda ya ba da kansa fansa saboda kowa da kowa. An kuwa yi shaidar wannan a daidai lokacinsa. 7 Don haka ne aka sa ni mai wa'azi, da manzo kuma (gasikya nake faɗa, ba ƙarya ba), mai koya wa al'ummai al'amarin bangaskiya da kuma na gaskiya. 8 Saboda haka, a kowane wuri ina so maza su yi addu'a, suna ɗaga hannuwa tsarkakakku, ba tare da fushi ko jayayya ba. 9 Mata kuma su riƙa sa tufafin da suka dace da su saboda kunya da kamunkai, ba adon kitso, ko kayan zinariya, ko lu'ulu'u, ko tufafi masu tsada ba, 10 sai dai su yi aiki nagari, yadda ya dace da mata masu bayyana shaidar ibadarsu. 11 Mace ta riƙa koyo da kawaici da matuƙar biyayya. 12 Ban yarda mace ta koyar, ko kuma ta yi iko da maza ba, sai dai ta zama shiru. 13 Ai, Adamu aka fara halitta, sa'an nan Hawwa'u. 14 Ba kuma Adamu aka yaudara ba, amma matar ce aka yaudara, har ta keta umarni. 15 Duk da haka kuwa, ta wurin haifar 'ya'ya sai ta kai ga kammala, muddin ta nace wa bangaskiya, da ƙauna, da zama a tsarkake, da kuma kamunkai.

1 Timoti 3

Sharuɗan Zama Shugabannin Ikilisiya

1 Maganar nan tabbatacciya ce, cewa duk mai burin aikin kula da ikilisiya, yana burin yin aiki mai kyau ke nan. 2 To, lalle ne mai kula da ikilisiya yă zama marar abin zargi, ya zama mai mace ɗaya, mai kamunkai, natsattse, kintsattse, mai yi wa baƙi alheri, gwanin koyarwa kuma. 3 Ba mashayi ba, ba mai saurin d�ka ba, amma salihi, ba kuma mai husuma ba, ba kuwa mai son kuɗi ba. 4 Lalle ne yă iya sarrafa iyalinsa da kyau, yana kuma kula da 'ya'yansa, su yi biyayya da matuƙar ladabi. 5 Don kuwa in mutum bai san yadda zai sarrafa iyalinsa ba, ta ƙaƙa zai iya kula da ikilisiyar Allah? 6 Lalle ne kuma, kada ya zama sabon tuba, don kada ya daga kai ya burmu a cikin hukuncin da aka yi wa Iblis. 7 Banda haka kuma, lalle ne ya zama mai mutunci ga waɗanda ba su a cikinmu, don kada ya zama abin zargi, ya faɗa a cikin tarkon Iblis.

Sharuɗan Zama Mai Hidimar Ikilisiya

8 Haka kuma masu hidimar ikilisiya, lalle ne su zama natsattsu, ba masu baki biyu ba, ko mashaya, ko masu kwaɗayin ƙazamar riba. 9 Lalle ne su riƙi asirin bangaskiya da lamiri mai tsabta. 10 Sai an gwada su tukuna, in kuma an tabbata ba su da wani abin zargi, to, sai su kama aikin hidimar. 11 Haka kuma matan, lalle su zama natsattsu, ba masu yanke ba, amma masu kamunkai, masu amince ta kowace hanya. 12 Masu hidima kuma su zama masu mata ɗaya ɗaya, masu sarrafa 'ya'yansu da sauran iyalinsu da kyau. 13 Masu hidimar da suke aikinsu sosai, suna samar wa kansu kyakkyawan suna, da kuma ƙaƙƙarfar amincewa ga bangaskiyarsu ga Almasihu Yesu.

Asirin Addininmu

14 Ina sa zuciya in zo a wurinka ba da daɗewa ba, amma ina rubuto maka waɗannan abubuwa. 15 Don in ya zamana na yi jinkiri, za ka san irin zaman da ya kamata a yi a jama'ar Allah, wadda take ita ce Ikilisiyar Allah Rayayye, jigon gaskiya da kuma ginshiƙinta. 16 Ba shakka, asirin addininmu muhimmi ne ƙwarai, An bayyana shi da jiki, Ruhu ya nuna shi adali ne, Mala'iku sun gan shi, An yi wa al'ummai wa'azinsa, An gaskata da shi a duniya, An ɗauke shi Sama wurin ɗaukaka.

1 Timoti 4

Faɗi a kan Malaman Ƙarya

1 To, Ruhu musamman ya ce, a can wani zamani waɗansu za su fanɗare wa bangaskiya, su mai da hankali ga aljannu masu ruɗi, da kuma koyarwar aljannu, 2 ta wurin makircin waɗansu maƙaryata, waɗanda aka yi wa lamirinsu lalas. 3 Su ne masu hana aure da cin abinci iri iri, waɗanda Allah ya halitta don waɗanda suka ba da gaskiya, suka kuma san gaskiya, su karɓa da godiya. 4 Domin duk abin da Allah ya halitta kyakkyawa ne, kada kuma a ƙi kome muddin an karɓe shi da godiya, 5 gama an tsarkake shi ta wurin Maganar Allah da addu'a

Amintaccen Bawan Almasihu

6 In kana tuna wa 'yan'uwa wadannan abubuwa, za ka zama amintaccen bawan Almasihu Yesu, wanda aka goya da maganar bangaskiya, da kuma sahihiyar koyarwar nan wadda ka bi har ya zuwa yau. 7 Ka ƙi tatsuniyoyin saɓo da na banza da wofi. Ka hori kanka ga bin Allah. 8 Horon jiki yana da ɗan amfaninsa, amma bin Allah yana da amfani ta kowace hanya, da yake shi ne da alkawarin rai na a yanzu da na nan gaba. 9 Maganar nan tabbatacciya ce, ta kuma cancanci a karɓe ta ɗungum. 10 Saboda wannan maƙasudi muke wahala, muke ta fama, domin mun dogara ne ga Allah Rayayye, wanda yake Mai Ceton dukan mutane, musamman masu ba da gaskiya. 11 Ka yi umarni da waɗannan abubuwa, ka kuma koyar da su. 12 Kada ka yarda kowa ya raina ƙuruciyarka, sai dai ka zama gurbi ga masu ba da gaskiya ta wurin magana, da hali, da ƙauna, da bangaskiya, da kuma tsarkaka. 13 Kafin in zo, ka lazamci karanta wa mutane Littattafai, da yin gargaɗi, da kuma koyarwa. 14 Kada ka shagala da baiwar da aka yi maka, wadda aka ba ka ta wurin annabci, sa'ad da dattawan ikilisiya suka ɗora maka hannu. 15 Ka himmantu ga waɗannan abubuwa, ka kuma lazamce su ƙwarai, don kowa yă ga ci gaban da kake yi. 16 Ka kula da kanka da kuma koyarwarka. Ka nace da haka, domin ta yin haka za ka ceci kanka da masu sauraronka.

1 Timoti 5

Wajibi ga Juna

1 Kada ka tsauta wa dattijo, sai dai ka roƙe shi kamar mahaifinka. Samari kuma ka ɗauke su kamar 'yan'uwanka, 2 tsofaffi mata kuma kamar uwayenka, 'yan mata kuwa kamar 'yan'uwanka, da matuƙar tsarkaka. 3 Ka girmama gwauraye mata, waɗanda ba sa da mataimaka. 4 In wata gwauruwa tana da 'ya'ya ko jikoki, sai su koya, ya wajaba su fara nuna wa danginsu bautar Allah da suke yi, su kuma sāka wa iyayensu da alheri. Wannan abin karɓa ne a gun Allah. 5 Gwauruwa marar mataimaki kuwa, mai zaman kaɗaici, ta dogara ga Allah ke nan, tana nacewa ga roƙon Allah, tana addu'a dare da rana. 6 Amma wadda take zaman annashuwa kuwa, kamar matacciya take, ko da tana a raye. 7 Ka umarce su a game da waɗannan abubuwa, don su kasance marasa abin zargi. 8 Duk wanda bai kula da danginsa ba, tun ba ma iyalinsa ba, ya m�sa wa bangaskiya ke nan, ya kuma fi marar ba da gaskiya mugunta. 9 Kada a lasafta gwauruwa a cikin gwauraye, sai dai ta kai shekara sittin, ba ta yi aure fiye da ɗaya ba, 10 wadda ake yabo a kan kyawawan ayyukanta, wadda kuma ta goyi 'ya'ya sosai, ta yi wa baƙi karamci, ta wanke ƙafafun tsarkaka, ta taimaki ƙuntatattu, ta kuma nace wa yin kowane irin aiki nagari. 11 Amma kada ka lasafta gwauraye masu ƙuruciya waɗanda mazansu suka mutu, a cikin gwaurayen, don in zuciyarsu ta kasa daurewa a game da wa'adin da suka yi da Almasihu, sai su so yin aure, 12 hukunci yā kama su ke nan, tun da yake sun ta da wa'adinsu na farko. 13 Banda haka kuma sukan koyi zaman banza, suna zirga-zirga gida gida. Ba ma kawai masu zaman banza za su zama ba, har ma sai su zama matsegunta, masu shishigi, suna faɗar abin da bai kamata ba. 14 Saboda haka, ina so gwauraye masu ƙuruciya waɗanda mazansu suka mutu su yi aure, su haifu, su yi tafiyar da al'amuran gida, kada su ba magabci hanyar zarginmu. 15 Gama waɗansu ma har sun bauɗe, sun bi Shaiɗan. 16 Duk mace mai bi, da take da dangi gwauraye mata, sai ta taimake su, kada a nauwaita wa ikilisiya, don ikilisiyar ta samu ta taimaki gwauraye marasa mataimaka. 17 Dattawan ikilisiya da suke a riƙe da al'amura sosai, a girmama su ninkin ba ninkin, tun ba ma waɗanda suke fama da yin wa'azi da koyarwa ba. 18 Domin Nassi ya ce, “Kada ka sa wa takarkari takunkumi sa'ad da yake sussuka.” Ya kuma ce, “Ma'aikaci ya cancanci ladarsa.” 19 Kada ka yarda in an kawo ƙarar wani dattijon ikilisiya, sai dai da shaidu biyu ko uku. 20 Masu yin zunubi kuwa, sai ka tsawata musu a gaban dukkan jama'a, don saura su tsorata. 21 Na gama ka da Allah, da Almasihu Yesu, da kuma zaɓaɓɓun mala'iku, ka kiyaye waɗannan abubuwa ƙwarai da gaske, kada ka yi kome da tāra. 22 Kada ka yi garajen ɗora wa kowa hannu, kada kuwa zunuban waɗansu su shafe ka. Ka tsare kanku a tsarkake. 23 A nan gaba ba ruwa kaɗai za ka sha ba, sai dai ka sha ruwan inabi kaɗan saboda cikinka, da kuma yawan laulayinka. 24 Zunuban waɗansu mutane a fili suke, tun ba a kai gaban shari'a ba. Zunuban waɗansu kuwa, sai daga baya suke bayyana. 25 Haka kuma, kyawawan ayyukan waɗansu a fili suke, waɗanda ba haka suke ba, ba za su tabbata a ɓoye ba.

1 Timoti 6

1 Duk ɗaukacin masu igiyar bauta a wuyansu, su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci a girmama su matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwar nan. 2 Waɗanda suke da iyayengiji masu ba da gaskiya, kada su raina su, domin su 'yan'uwa ne a gare su. Sai ma su ƙara bauta musu, tun da yake waɗanda suke moron aikin nan nasu masu ba da gaskiya ne, ƙaunatattu kuma a gare su.

Bin Allah da Wadar Zuci

Ka koyar da waɗannan abubuwa, ka kuma yi gargaɗinsu. 3 Duk wanda yake wata koyarwa dabam, bai kuwa yarda da sahihiyar maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu, da kuma koyarwar da ta dace da bautar Allah ba, 4 girmankai ya ciccika shi ke nan, bai san kome ba, yana da muguwar jarabar gardama da jayayya a kan maganganu kawai, waɗanda suke jawo hassada, da husuma, da yanke, da mugayen zace-zace, 5 da kuma yawan tankiya a cikin mutane masu ɓataccen hankali, waɗanda har gaskiya ta ƙaurace musu, suna tsammani bin Allah hanya ce ta samu. 6 Bin Allah a game da wadar zuci kuwa riba ce mai yawa. 7 Don ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu iya fita da kome ba. 8 To, in muna da abinci da sutura, ai, sai mu dangana da su. 9 Masu ɗokin yin arziki kuwa, sukan zarme da jaraba, su fāɗa a cikin tarko, suna mugayen sha'awace-sha'awace iri iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka. 10 Ai, son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Don tsananin jarabar kuɗi kuwa waɗansu mutane, har sun bauɗe wa bangaskiya, sun jawo wa kansu baƙin ciki iri iri masu sukar rai.

Famar Gaske saboda Bangaskiya

11 Amma, ya kai, bawan Allah, ka guje wa waɗannan abubuwa, ka dimanci aikin adalci, da bin Allah, da bangaskiya, da ƙauna, da jimri, da kuma tawali'u. 12 Ka yi fama, famar gaske saboda bangaskiya, ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira ka saboda shi, sa'ad da ka bayyana yarda, kyakkyawar bayyana yarda, a gaban shaidu masu yawa. 13 Na gama ka da Allah mai raya kome, na kuma gama ka da Almasihu Yesu, wanda ya yi shaida, kyakkyawar shaidar nan, a gaban Buntus Bilatus, 14 ka bi umarninsa, ba tare da wani aibi ko zargi ba, har ya zuwa bayyanar Ubangijinmu Yesu Almasihu, 15 wannan kuwa makaɗaicin mamallaki, abin yabo, Sarkin sarakuna. Ubangijin iyayengiji zai bayyana shi a lokacinsa. 16 Shi ne kaɗai marar mutuwa, yake kuma zaune a cikin hasken da ba ya kusatuwa. Shi kuwa ba mutumin da ya taɓa ganinsa, ko kuwa zai iya ganinsa. Girma da madawwamin mulki su tabbata a gare shi. Amin, amin. 17 Masu dukiyar duniyar nan kuwa ka gargaɗe su kada su nuna alfarma, kada kuwa su dogara da dukiya marar tabbata, sai dai ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don mu ji daɗinsa. 18 Sai dai su yi nagarta da bijinta a wajen aiki nagari, su kasance masu hannu sake, suna alheri. 19 Ta haka suke kafa wa kansu kyakkyawan tushe don nan gaba, domin su riƙi rai wanda yake na hakika. 20 Ya Timoti, ka kiyaye abin da aka ba ka amana. Ka yi nesa da masu maganganun sāɓo na banza da wofi, da yawan musu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi. 21 Waɗansu kuwa, a garin taƙama, da haka har sun kauce wa bangaskiya. Alheri yă tabbata a gare ku.

2 Timoti 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, manzon Almasihu Yesu da yardar Allah, don sanar da alkawarin nan na rai wanda yake ga Almasihu Yesu, 2 zuwa ga Timoti ƙaunataccen ɗana. Alheri, da jinƙai, da salama na Allah Uba, da na Almasihu Yesu Ubangijinmu su tabbata a gare ka.

Kada ka Ji Kunya

3 Ina gode wa Allah, wanda nake bauta wa da lamiri mai tsabta, kamar yadda kakannina suka yi, duk sa'ad da nake tunawa da kai a cikin addu'ata ba fāsawa. 4 Sa'ad da nake tunawa da hawayenka, nakan yi began ganinka dare da rana, domin in yi farin ciki matuƙa. 5 Ina tunawa da sahihiyar bangaskiyarka, wadda da farko take tare da kakarka Loyis, da mahaifiyarka Afiniki, a yanzu kuma na tabbata tana tare da kai. 6 Saboda haka, ina so in faɗakar da kai, ka lura baiwar nan ta Allah, wadda take tare da kai ta wurin ɗora maka hannuwana. 7 Ai, Allah ba halin tsoro ya ba mu ba, hali mai ƙarfi ne, mai ƙauna, da kuma kamunkai. 8 Saboda haka, kada ka ji kunyar ba da shaidar Ubangijinmu, da kuma tawa, ni da nake ɗan sarƙa saboda shi, sai dai mu jure wa shan wuya tare, saboda bishara, bisa ga ikon Allah, 9 wanda ya cece mu, ya kuma kira mu da kira mai tsarki, ba don wani aikin lada da muka yi ba, sai dai domin nufinsa, da kuma alherinsa, da aka yi mana baiwa tun fil'azal, a cikin Almasihu Yesu, 10 wadda a yanzu aka bayyana ta bayyanar Mai Cetonmu Almasihu Yesu, wanda ya shafe mutuwa, ya kuma bayyana rai da rashin mutuwa, ta wurin bishara. 11 A wannan bishara an sa ni mai wa'azi, da kuma manzonta, da mai koyarwarta kuma. 12 Saboda haka, ne nake shan wuya haka. Duk da haka, ban kunyata ba, domin na san wanda na gaskata da shi, na kuma tabbata yana da iko ya kiyaye abin da na danƙa masa, har ya zuwa waccan rana. 13 Ke yi koyi da sahihiyar maganar da ka ji daga gare ni, da bangaskiya da ƙauna da take ga Almasihu Yesu. 14 Kyakkyawan abin nan da aka ba ka amana, ka kiyaye shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, wanda yake zaune a zuciyarmu. 15 Ka dai sani duk waɗanda suke ƙasar Asiya sun juya mini baya, a cikinsu kuwa har da Fijalas da kuma Harmajanas. 16 Ubangiji yă yi wa iyalin Onisifaras jinƙai, don sau da yawa yake sanyaya mini zuciya, bai kuwa ji kunyar ɗaurina da aka yi ba. 17 Har ma da ya zo Roma, sai ya neme ni ido a rufe, ya kuwa same ni. 18 Ubangiji ya yi masa jinƙai a waccan rana. Ka dai sani sarai yadda ya yi ɗawainiya mai yawa a Afisa.

2 Timoti 2

Amintaccen Sojan Almasihu

1 Saboda haka, ya kai ɗana, sai ka ƙarfafa da alherin da yake ga Almasihu Yesu. 2 Abin da ka ji a guna a gaban shaidu masu yawa kuwa, sai ka danƙa wa amintattun mutane, waɗanda su ma za su koya wa waɗansu. 3 Kai kuma ka jure wa shan wuya, kana amintaccen sojan Almasihu Yesu. 4 Ai, ba sojan da yake a bakin dāga da ransa zai sarƙafe da sha'anin duniya, tun da yake burinsa shi ne yă faranta wa wanda ya ɗauke shi soja. 5 Mai wasan guje-guje da tsalle-tsalle, ba zai sami ɗaukaka ba, sai ko ya bi dokokin wasan. 6 Ma'aikaci, ai, shi ya kamata ya fara cin amfanin gonar. 7 Ka yi tunani a kan abin da nake faɗa, Ubangiji kuwa zai ba ka fahimtar kome. 8 Ka tuna da Yesu Almasihu fa, shi da aka tashe shi daga matattu, na zuriyar Dawuda bisa ga bisharata, 9 wadda nake shan wuya saboda ita, har nake ɗaure kamar mai laifi. Amma Maganar Allah ba a ɗaure take ba. 10 Don haka nake jure kome saboda zaɓaɓɓu, domin su ma su sami ceton nan da yake samuwa ta wurin Almasihu, a game da madawwamiyar ɗaukaka. 11 Maganar nan tabbatacciya ce, “In mun mutu tare da shi, za mu rayu ma tare da shi, 12 In mun jure, za mu yi mulki ma tare da shi, In mun yi musun saninsa, shi ma zai yi musun saninmu, 13 In ba mu da aminci, shi kam ya tabbata mai aminci, Domin ba zai yi musun kansa ba.”

Yardajjen Ma'aikaci

14 Ka riƙa tuna masu da haka, ka kuma gama su da Ubangiji, kada su yi jayayya a kan maganganu, don ba ta da wani amfani, sai ɓad da masu ji kawai take yi. 15 Ka himmantu, ka miƙa kanka yardajje ga Allah, ma'aikaci wanda ba hanya ya kunyata, mai kuma fassara Maganar gaskiya daidai. 16 Ka yi nesa da masu maganganun banza na sāɓo. Sai daɗa jan mutane zuwa ga rashin bin Allah suke yi, 17 maganarsu takan haɓaka kamar gyambo. A cikinsu har da Himinayas da Filitas, 18 waɗanda suka bauɗe wa gaskiya suna cewa tashin matattu ya riga ya wuce, suna jirkitar da bangaskiyar waɗansu. 19 Duk da haka, ƙaƙƙarfan harsashin ginin nan na Allah ya tabbata, hatimin nan kuwa yana jikinsa cewa, “Ubangiji ya san nasa,” da kuma, “Duk wanda ya bayyana yarda ga sunan Ubangiji, to, yă yi nesa da aikata mugunta.” 20 Aa babban gida, ba kayan zinariya da na azurfa ne kawai ba, har ma da na itace da na yumɓu, waɗansu don aikin ɗaukaka, waɗansu kuwa don ƙasƙantaccen aiki. 21 Kowa ya tsarkake kansa daga ayyukan nan ƙasƙantattu, zai zama ma'aikaci mai daraja, tsarkakakke, mai amfani ga Ubangiji, shiryayye ga kowane kyakkyawan aiki. 22 Don haka, sai ka guje wa mugayen sha'awace-sha'awacen ƙuruciya, ka dimanci aikin adalci, da bangaskiya, da ƙauna, da kuma salama, tare da waɗanda suke roƙon Ubangiji da zuciya tsarkakakkiya. 23 Ka ƙi gardandamin banza marasa ma'ana, ka san lalle suna jawo husuma. 24 Bawan Ubangiji kuwa lalle ba zai zama mai husuma ba, sai dai ya zama salihi ga kowa, gwanin koyarwa, mai haƙuri, 25 mai sa abokan hamayyarsa a kan hanya da tawali'u, ko Allah zai sa su tuba, su kai ga sanin gaskiya, 26 su kuɓuce wa tarkon Iblis, su bi nufin Allah, bayan da Iblis ya tsare su.

2 Timoti 3

Halin Ƙarshen Zamani

1 Amma ka fahimta, a zamanin ƙarshe za a sha wuya ƙwarai. 2 Mutane za su zama masu sonkai, da masu son kuɗi, da masu ruba, da masu girmankai, da masu zagezage, da marasa bin iyayensu, da masu butulci, da marasa tsarkaka, 3 da marasa ƙauna, da masu riƙo a zuci, da masu yanke, da fajirai, da maƙetata, da maƙiyan nagarta, 4 da maciya amana, da masu taurinkai, da masu homa, da masu son annashuwa fiye da son Allah, 5 suna riƙe da siffofin ibada, amma suna sāɓa wa ikonta. Ka yi nesa da irin waɗannan mutane. 6 A cikinsu kuwa akwai masu saɗaɗawa su shiga gidajen mutane, suna rinjayar mata marasa wayo, waɗanda zunubi ya sha kansu, muguwar sha'awa iri iri kuma ta ɗauke musu hankali, 7 kullum suna koyo, amma kullum sai su kāsa kaiwa ga sanin gaskiya. 8 Kamar yadda Yanisu da Yambirisu saka tayar wa Musa, haka mutanen nan kuma suke tayar wa gaskiya, mutane ne masu ɓataccen hankali ƙwarai, bangaskiyarsu kuwa ta banza ce. 9 Amma ba za su yi nisa ba, don rashin hankalinsu zai bayyana ga kowa, kamar na mutanen nan biyu.

Gargaɗin Bulus ga Timoti na Ƙarshe

10 Kai kam, ka riga ka kiyaye koyarwata, da halina, da niyyata, da bangaskiyata, da haƙurina, da ƙaunata, da jimirina, 11 da kuma yawan tsanani, da wuyar da na sha, da suka same ni a Antakiya, da Ikoniya, da Listira, wato irin tsanance-tsanancen da na jure. Amma Ubangiji ya kuɓutar da ni daga cikinsu duka. 12 Labudda, duk masu niyyar zaman tsarkaka, suna ga Almasihu Yesu, za su sha tsanani. 13 Mugayen mutane da masu ruɗi kuwa, ƙara muni za su riƙa yi, suna yaudara, ana kuma yaudararsu. 14 Amma kai kuwa, ka zauna a kan abin da ka koya, ka kuma haƙƙaƙe, gama ka san wurin waɗanda ka koye su, 15 da kuma yadda tun kana ɗan ƙaramin yaro ka san Littattafai masu tsarki, waɗanda suke koya maka hanyar samun ceto ta dalilin bangaskiya ga Almasihu Yesu. 16 Kowane Nassi hurarre na Allah ne, mai amfani ne kuma wajen koyarwa, da tsawatarwa, da gyaran hali, da kuma tarbiyyar aikin adalci, 17 domin bawan Allah yă zama cikakke, shiryayye sosai ga kowane kyakkyawan aiki.

2 Timoti 4

1 Na gama ka da Allah, da kuma Almasihu Yesu, wanɗa zai yi wa rayayyu da matattu shari'a, na kuma gargaɗe ka saboda bayyanarsa da kuma mulkinsa, 2 ka yi wa'azin Maganar Allah, ka dimanta a kai ko da yaushe, kana shawo kan mutane, kana tsawatarwa, kana ƙarfafa zukata, a game da matuƙar haƙuri da kuma koyarwa. 3 Don lokaci zai zo da mutane ba za su jure sahihiyar koyarwa ba, amma saboda kunnensu yana ƙaiƙayi, sai su taro masu koyarwa da za su biya musu muradinsu. 4 Za su toshe kunnensu ga jin tatsuniyoyi. 5 Kai kuwa, sai ka natsu a cikin kowane hali, ka jure wa shan wuya, kana aikin mai bishara, ka cika hidimarka. 6 Ni fa tsiyaye ni ake yi kamar hadaya, lokacin ƙauracewata kuma ya gabato. 7 Na sha fama, famar gaske, na gama tseren, na riƙe bangaskiya. 8 Saura kuwa, sai sakamakon nan na aikin adalci, da aka tanadar mini, wanda Ubangiji, mahukunci mai adalci, zai ba ni a ranar nan, ba kuwa ni kaɗai ba, har da duk waɗanda suke ɗokin ganin bayyanarsa.

Waɗansu Umarnai

9 Ka yi matuƙar ƙoƙari ka zo wurina da hanzari, 10 domin Dimas, saboda ƙaunar duniyar nan, ya yashe ni, ya tafi Tasalonika. Karaska ya tafi ƙasar Galatiya, Titus kuma ya tafi ƙasar Dalmatiya. 11 Luka ne kaɗai yake tare da ni. Ka ɗauko Markus ku zo tare, gama yana da amfani a gare ni a wajen yi mini hidima. 12 Tikikus kuwa na aike shi Afisa. 13 Sa'ad da za ka taho, ka zo da alkyabbar nan da na bari a wurin Karbus a Taruwasa, da kuma littattafan nan, tun ba ma fatun nan masu rubutu ba. 14 Iskandari maƙerin farfarun nan ya yi mini mugunta ƙwarai, Ubangiji zai yi masa sakayyar aikinsa. 15 Kai ma, ka mai da hankali da shi, gama ya hauri maganarmu, mummunan hauri. 16 A lokacin da na ba da hanzarina na farko, ba wanda ya goyi bayana, sai duk suka yashe ni. Ina fata ba za a lasafta wannan laifi a kansu ba. 17 Amma Ubangiji ya tsaya tare da ni, ya ba ni ƙarfin sanar da bishara sosai da sosai, domin duk al'ummai su ji, aka kuwa cece ni daga bakin zaki. 18 Ubangiji zai cece ni daga kowane mugun abu, ya kuma kiyaye ni, ya kai ni ga Mulkinsa na Sama. Ɗaukaka tă tabbata a gare shi har abada abadin. Amin! Amin!

Gaisuwa

19 Ka gayar mini da Bilkisu da Akila, da mutanen gidan Onisifaras. 20 Aratas ya dakata a Koranti. Tarofimas kuwa na bar shi a Militas, ba shi da lafiya. 21 Ka yi matuƙar ƙoƙari ka zo kafin damuna. Aubulus yana gaishe ka, da Budis, da Linas, da Kalaudiya, da kuma dukkan 'yan'uwa. 22 Ubangiji yă kasance a zuciyarka, alheri yă tabbata a gare ku.

Titus 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, bawan Allah, kuma manzon Yesu Almasihu, saboda bangaskiyar zaɓaɓɓun Allah, da kuma inganta sanin gaskiyar ibadarmu, 2 duk wannan kuwa saboda begen nan ne ga rai madawwami da Allah ya yi alkawari tun fil'azal, shi wanda ƙarya ba ta a gare shi, 3 ya kuwa bayyana maganarsa a lokacin da ya ƙayyade, ta wa'azin da shi Allah Mai Cetonmu ya amince mini in yi, bisa ga umarninsa, 4 zuwa ga Titus, ɗana na hakika ta wajen bangaskiyarmu mu duka. Alheri da salama na Allah Uba, da na Almasihu Yesu Mai Cetonmu su tabbata a gare ka.

Aikin Titus a Karita

5 Wannan shi ya sa na bar ka a Karita, musamman domin ka ƙarasa daidaita al'amuran da suka saura, ka kuma kafa dattawan ikilisiya a kowane gari, kamar yadda na nushe maka, 6 sai wanda ya kasance marar abin zargi, mai mace ɗaya, wanda 'ya'yansa suke masu ba da gaskiya, waɗanda ba a zarginsu da aikin masha'a ko na kangara. 7 Lalle ne kuwa, kowane mai kula da ikilisiya, da ya ke shi riƙon amana saboda Allah ne, ya zama marar abin zargi, ba mai taurinkai ba, ko mai saurin fushi, ko mashayi, ko mai saurin d�ka, ko mai kwaɗayin ƙazamar riba. 8 Amma ya kasance mai yi wa baƙi alheri, mai son abu nagari, natsattse, mai kirki, tsarkakakke, mai kamunkai, 9 mai riƙe da tabbatacciyar maganar nan kankan, daidai yadda aka koya masa, domin ya iya ƙarfafa wa waɗansu zuciya da sahihiyar koyarwa, ya kuma ƙaryata waɗanda suka yi musunta. 10 Don kuwa akwai kangararrun mutane da yawa, da masu surutan banza, da masu ruɗi, tun ba ma ɗariƙar masu kaciyar nan ba. 11 Lalle ne a kwaɓe su, tun da yake suna jirkitar da jama'a gida gida, ta wurin koyar da abin da bai kamata ba, don neman ƙazamar riɓa. 12 Wani annabi na Karitawa ya ce, “Karitawa a kullum maƙaryata ne, mugayen dabbobi, ragwaye, haɗamammu.” 13 Shaidar nan tasa kuwa gaskiya ce. Saboda haka, dai ka tsawata musu da gaske, domin su zama sahihai a wajen bangaskiya, 14 a maimakon su mai da hankali ga almarar Yahudawa, ko kuwa dokokin mutane masu ƙin gaskiya. 15 Ga masu tsarkin rai duk al'amarinsu mai tsarki ne, marasa tsarkin rai kuwa marasa ba da gaskiya, ba wani al'amarinsu da yake mai tsarki, da zuciyarsu da lamirinsu duka marasa tsarki ne. 16 Suna cewa sun san Allah, amma suna sāɓa masa ta wurin aikinsu. Abin ƙyama ne su, kangararru, ko kaɗan ba su da wani amfani a wajen yin aiki nagari.

Titus 2

Koyar da Kyakkyawar Koyarwa

1 Amma kai kam, sai ka faɗi abin da ya dace da sahihiyar koyarwa. 2 Dattawa su kasance masu kamunkai, natsattsu, mahankalta, masu sahihiyar bangaskiya, da ƙauna, da kuma jimiri. 3 Haka kuma, manyan mata su kasance masu keɓaɓɓen hali, ba masu yanke, ko masu jarabar giya ba, su zamana masu koyar kyakkyawan abu, 4 ta haka su koya wa mata masu ƙuruciya su so mazansu da 'ya'yansu, 5 su kuma kasance natsattsu, masu tsarkin rai, masu kula da gida, masu alheri, masu biyayya ga mazansu, don kada a kushe Maganar Allah. 6 Haka kuma, ka gargaɗi samari su yi kamunkai. 7 Kai ma sai ka zama gurbi na aiki nagari ta kowace hanya, da koyarwarka kana nuna rashin jirkituwa, da natsuwa, 8 da kuma sahihiyar maganar da ba za a kushe mata ba, don a kunyata abokan hamayya, su rasa hanyar zarginmu. 9 Bayi su yi biyayya ga iyayengijinsu, su kuma gamsar da su ta kowane hali. Kada su yi tsayayya, 10 ko taɓe-taɓe, sai dai su riƙi amana sosai, don su ƙawatar da koyarwar Allah Mai Cetonmu ta kowane hali. 11 Alherin Allah ya bayyana saboda ceton dukkan mutane, 12 yana koya mana mu ƙi rashin bin Allah da mugayen sha'awace-sha'awacen duniya, mu kuma yi zamanmu a duniyar nan da natsuwa, da adalci, da kuma bin Allah, 13 muna sauraron cikar begen nan mai albarka, wato bayyanar ɗaukakar Allahnmu Mai Girma, Mai Cetonmu Yesu Almasihu, 14 wanda ya ba da kansa dominmu, domin ya fanso mu daga dukan mugun aiki, ya kuma tsarkake jama'a su zama abin mulkinsa, masu himmar yin kyakkyawan aiki. 15 Ka yi ta sanar da waɗannan abubuwa, kana gargaɗa su, kana tsawatarwa da ƙaƙƙarfan umarni. Kada ka yarda kowa ya raina ka.

Titus 3

Himmantuwa ga Aiki Nagari

1 Ka riƙa tuna musu yi wa mahukunta da shugabanni ladabi, suna yi musu biyayya, suna kuma zaune da shirinsu na yin kowane irin kyakkyawan aiki. 2 Kada su ci naman kowa, kada su yi husuma, sai dai su zama salihai, suna yi wa dukan mutane matuƙar tawali'u. 3 Mu kanmu ma dā can mun yi wauta, mun kangare, an ɓad da mu, mun jarabta da muguwar sha'awa da nishaɗi iri iri, mun yi zaman ƙeta da hassada, mun zama abin ƙi, mu kuma mun ƙi waɗansu. 4 Amma sa'ad da alherin Allah Mai Cetonmu da ƙaunarsa ga 'yan adam suka bayyana, 5 sai ya cece mu, ba don wani aikin adalci da mu muka yi ba, a'a, sai dai domin jinƙan nan nasa, albarkacin wankan nan na sāke haihuwa, da kuma sabuntawar nan ta Ruhu Mai Tsarki, 6 wanda ya zubo mana a yalwace ta wurin Yesu Almasihu Mai Cetonmu. 7 Wannan kuwa domin a kuɓutar da mu bisa ga alherinsa ne, mu kuma zama magāda masu bege ga rai madawwami. 8 Maganar nan tabbatacciya ce. Ina so ka ƙarfafa waɗannan abubuwa ƙwarai, don waɗanda suka ba da gaskiya ga Allah su himmantu ga aiki nagari, waɗannan abubuwa kuwa masu kyau ne, masu amfani kuma ga mutane. 9 Amma ka yi nesa da gardandamin banza, da ƙididdigar asali, da husuma, da jayayya a kan Shari'a, domin ba su da wata riba, aikin banza ne kuma. 10 Mutumin da yake sa tsattsaguwa kuwa, in ya ƙi kula da gargaɗinka na farko da na biyu, to, sai ka fita sha'aninsa. 11 Ka dai sani irinsa ɓatacce ne, mai yin zunubi, shi kansa ma ya sani haka yake.

Waɗansu Umarnai

12 Sa'ad da na aiko Artimas ko Tikikus zuwa wurinka, sai ka yi matuƙar, ƙoƙari ka zo wurina a Nikafolis, don na yi niyyar cin damuna a can. 13 Ka yi himmar taimakon Zinas, masanin shari'a, da Afolos, su kamo hanya, ka kuma tabbata ba abin da ya gaza musu. 14 Jama'armu su koyi himmantuwa ga aikin kirki don biyan bukatun matsattsu, kada su zama marasa amfani.

Sa Albarka

15 Duk waɗanda suke tare da ni suna gaishe ka. Ka gayar mini da masoyanmu, masu bangaskiya. Alheri yă tabbata a gare ku, ku duka.

Filiman 1

Gaisuwa

1 Daga Bulus, ɗan sarƙa saboda Almasihu Yesu, da kuma Timoti ɗan'uwanmu, zuwa ga Filiman ƙaunataccen abokin aikinmu, 2 da Aufiya 'yar'uwarmu, da Arkibus abokin famanmu, da kuma ikilisiyar da take taruwa a gidanka. 3 Alheri da salama na Allah Ubanmu, da na Ubangiji Yesu Almasihu su tabbata a gare ku.

Ƙaunar Filiman da Bangaskiyarsa

4 A kullum ina gode wa Allahna duk sa'ad da nake yi maka addu'a, 5 saboda nakan ji labarin ƙauna da bangaskiya da kake yi wa Ubangiji Yesu da dukkan tsarkaka. 6 Ina addu'a bangaskiyar nan da ta haɗa ku, tă kasance mai ƙwazo a wajen ciyar da sanin dukkan kyawawan abubuwan da suke namu, saboda Almasihu. 7 Na yi farin ciki ƙwarai, zuciyata kuma ta ƙarfafa saboda ƙaunar da kake yi, ya kai 'dan'uwana, domin zukatan tsarkaka sun wartsake ta dalilinka.

Bulus ya yi Roƙo domin Unisimas

8 Saboda haka, ko da yake saboda Almasihu ina iya umartarka gabagaɗi, ka yi abin da ya wajaba, 9 duk da haka saboda ƙauna, na fi so in roƙe ka, ni Bulus tsoho, a yanzu kuma ga ni ɗan sarƙa saboda Almasihu Yesu, 10 ina roƙonka saboda ɗana Unisimas, wanda na zama ubansa ina ɗaure. 11 Dā kam, ba shi da wani amfani a wurinka, amma a yanzu, hakika yana da amfani a gare mu, ni da kai. 12 Ga shi nan, na komo maka da shi kamar gudan zuciyata. 13 Dā kam sona in riƙe shi a wurina, ya riƙa yi mini hidima a madadinka, muddin ina ɗaure saboda bishara, 14 amma ba na so in yi kome ba tare da yardarka ba, don kada alherinka ya zamana na tilas ne, ba na ganin dama ba. 15 Watakila shi ya sa kuka ɗan rabu, don kă same shi har abada, 16 ba kuma a kan bawa ba, sai dai a kan abin da ya fi bawa, wato 'dan'uwa abin ƙauna, tun ba ma a gare ni ba, balle fa a gare ka, ta wajen al'amarin jiki da kuma wajen al'amarin Ubangiji. 17 Saboda haka in ka ɗauke ni a kan abokin tarayya, to, sai ka karɓe shi kamar yadda za ka karɓe ni. 18 Ko ma ya yi maka wani laifi, ko kuwa kana binsa wani abu, sai ka mai da shi a kaina. 19 Ni Bulus, ni nake rubuto wannan da hannuna, ni kuwa zan biya, kada ma a yi zancen ranka da na fanso maka! 20 Ya ɗan'uwana, ka yarda in sami wata fa'ida a gare ka saboda Ubangiji! Ka sanyaya mini zuciya saboda Almasihu. 21 Don na tabbatar da biyayyarka, shi ya sa na rubuto maka, don na sani za ka yi, har fiye da abin da na faɗa. 22 Har wa yau kuma, ka shirya mini masauki, domin ina sa zuciya a ba ni yarjin zuwa gare ku albarkacin addu'arku.

Gaisuwa

23 Abafaras, abokin ɗaurina saboda Almasihu Yesu, yana gaishe ka, 24 haka kuma Markus, da Aristarkus, da Dimas, da Luka, abokan aikina, suna gaishe ka. 25 Alherin Ubangijinmu Yesu Almasihu yă tabbata a zukatanku.

Ibraniyawa 1

Allah ya yi Magana ta wurin Ɗansa

1 A zamanin dā, Allah ya yi wa kakannin kakanninmu magana ta hanyoyi masu yawa iri iri, ta bakin annabawa, 2 amma a zamanin nan na ƙarshe, sai ya yi mana magana ta wurin Ɗansa, wanda ya sa magājin kome, wanda ta wurinsa ne kuma ya halicci duniya. 3 Shi ne hasken ɗaukakar Allah, ainihin kamannin zatinsa kuma, shi kuma yana a riƙe da dukan abubuwa ta ikon faɗarsa. Bayan da ya tsarkake zunubanmu, sai ya zauna a dama da Maɗaukaki a can Sama.

Fifikon Yesu a kan Mala'iku

4 Ta haka yake da fifiko a kan mala'iku, kamar yadda sunansa da ya gāda yake da fifiko nesa a kan nasu. 5 Domin kuwa wane ne a cikin mala'iku Allah ya taɓa ce wa, “Kai Ɗana ne, Ni Ubanka ne yau?” da kuma, “Zan kasance Uba a gare shi, Shi kuma, zai kasance Ɗa a gare ni?” 6 Amma da zai sāke shigo da magāji a duniya, sai ya ce, “Dukkan mala'ikun Allah su yi masa sujada.” 7 A game da mala'iku kuma sai ya ce, “Yakan mai da mala'ikunsa ruhohi, Masu hidimarsa kuma harsunan wuta.” 8 Amma a game da ɗan, sai ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, na har abada abadin ne, Sandar sarautarka sanda ce ta tsantsar gaskiya. 9 Kā ƙaunaci aikin adalci, kā ƙi aikin sāɓo. Saboda haka Allah, wato, Allahnka, ya shafe ka Da man farin ciki fiye da tsararrakinka.” 10 Da kuma, “Ya ubangiji, kai ne ka halicci duniya tun farko, Sammai kuma aikinka ne. 11 Su za su hallaka, amma kai madawwami ne. Duk za su tsufa kamar tufa, 12 Za ka naɗe su kamar mayafi, Za su kuma sauya, Amma kai kana nan ba sākewa, Har abada shekarunka ba za su ƙare ba.” 13 Amma wane ne a cikin mala'iku Allah ya taɓa ce wa, “Zauna a damana, Sai na sa ka take maƙiyanka?” 14 Ashe, dukan mala'iku ba ruhohi masu hidima ba ne, waɗanda Allah yakan aiki, don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?

Ibraniyawa 2

Maganar Ceto Mai Girma

1 Saboda haka, lalle ne mu ƙara mai da hankali musamman ga abubuwan da muka ji, don kada mu yi sakaci, su sulluɓe mana. 2 In kuwa maganar nan da aka faɗa ta bakin mala'iku ta zama tabbatacciya, har kowane keta umarni da rashin biyayya, suka gamu da sakamakonsu wanda ya kamace su, 3 to, ta ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi kula da ceto mai girma haka? Domin Ubangiji kansa, shi ne ya fara sanar da shi, waɗanda suka saurare shi kuma suka tabbatar mana da shi, 4 sa'an nan kuma Allah ya haɗa shaidarsa, da tasu a kan ceton, ta alamu da abubuwan al'ajabi da mu'ujizai iri iri, da kuma baiwar Ruhu Mai Tsarki dabam dabam da ya rarraba kamar yadda ya nufa.

Shugaban Ceto

5 Ai, ba ga mala'iku ba ne Allah ya sa mulkin duniyar da za a yi, wanda muke zance. 6 Amma wani ya tabbatar a wani wuri cewa, “Mutum ma mene ne, har da za ka tuna da shi? Ko ɗan mutum ma, har da za ka kula da shi? 7 Kā sa shi ya gaza mala'iku a ɗan lokaci kaɗan, Kā naɗa shi da ɗaukaka da girma, Kā ɗora shi a kan dukkan halittarka. 8 Kā sarayar da kome a ƙarƙashin ikonsa.” To, a wajen sarayar da dukkan abubuwa a ƙarƙashinsa ɗin nan, Allah bai bar kome a keɓe ba. Amma kuwa har a yanzu ba mu ga yana sarrafa dukkan abubuwa ba. 9 Amma muna ganin Yesu, wanda a ɗan lokaci aka sa shi ya gaza mala'iku, an naɗa shi a ɗaukaka da girma, saboda shan wuyarsa ta mutuwa. Wannan kuwa duk ta wurin alherin Allah ne Yesu ya mutu saboda kowa. 10 Saboda haka, ya dace da Allah, shi da dukkan abubuwa suka kasance dominsa, ta gare shi ne kuma dukkan abubuwa suka samu, yă kammala shugaban cetonsu ta wurin shan wuya, a wajen kawo 'ya'ya masu yawa ga samun ɗaukaka. 11 Domin da shi mai tsarkakewar da kuma waɗanda aka tsarkaken, duk tushensu ɗaya ne. Shi ya sa ba ya jin kunyar kiransu 'yan'uwansa, 12 da ya ce, “Zan sanar da sunanka ga 'yan'uwana, A tsakiyar ikilisiya zan yabe ka da waƙa.” 13 Har wa yau, ya ce, “Zan dogara a gare shi.” Da kuma, “Ga ni nan, ni da 'ya'yan da Allah ya ba ni.” 14 Wato tun da yake 'ya'yan duk suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamannin haka, domin ya hallakar da mai ikon mutuwa, wato iblis, ta wurin mutuwarsa, 15 yă kuma 'yanta duk waɗanda tun haihuwarsu suke zaman bauta saboda tsoron mutuwa. 16 Don hakika ba mala'iku yake taimako ba, a'a, zuriyar Ibrahim ne yake taimako. 17 Saboda haka, lalle ne ya zama kamar 'yan'uwansa ta kowane hali, domin ya zama Babban Firist, mai jinƙai, mai aminci kuma na al'amarin Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu ta gafarta zunuban jama'a. 18 Tun da yake shi ma ya sha wuya, sa'ad da aka gwada shi, ashe, zai taimaki waɗanda ake yi wa gwaji.

Ibraniyawa 3

Fifikon Almasihu a kan Musa

1 Saboda haka, ya ku 'yan'uwa tsarkaka, ku da kuke da rabo a kiran nan basamaniya, sai ku tsai da zuciya ga Yesu, Manzo, da kuma Babban Firist na bangaskiyar da muke shaidawa, 2 shi da yake mai aminci ga wannan da ya sa shi, kamar yadda Musa ya yi ga duk jama'ar Allah. 3 Amma kuwa an ga Yesu ya cancanci ɗaukaka fiye da ta Musa nesa, kamar yadda mai gina gida ya fi gidan martaba. 4 Kowane gida ai, da wanda ya gina shi, amma maginin dukkan abubuwa Allah ne. 5 To, shi Musa mai aminci ne ga dukkan jama'ar Allah a kan shi bara ne, saboda shaida a kan al'amuran da za a yi maganarsu a nan gaba, 6 amma Almasihu mai aminci ne, yana mulkin jama'ar Allah a kan shi Ɗa ne, mu ne kuwa jama'arsa, muddin mun tsaya gabanmu gaɗi, muna gadara da begenmu ƙwarai.

Shiga Inuwar Allah, Hutawar Mutanensa ke Nan

7 Saboda haka, kamar yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau in kun ji muryarsa, 8 Kada ku taurare zukatanku kamar a lokacin tawayen nan, Wato, ranar gwaji a jeji, 9 A inda kakanninku suka gwada ni, suka jarraba ni, Suna ganin ayyukana har shekara arba'in. 10 Saboda haka ne, na yi fushi da mutanen wannan zamani, Har na ce, ‘A kullum zuciyarsu a karkace take, Ba su kuwa san hanyoyina ba.’ 11 Sai na yi rantsuwa da fushina, na ce, ‘Ba za su shiga inuwata ba sam.’ ” 12 Ku kula fa, 'yan'uwa, kada wata muguwar zuciyar marar gaskatawa ta wakana ga waninku, wadda za ta bauɗar da ku daga wurin Allah Rayayye. 13 Sai dai kowace rana ku ƙarfafa wa juna zuciya muddin akwai “Yau,” don kada kowannenku ya taurare, ta yaudarar zunubi. 14 Don kuwa mun zama masu tarayya da Almasihu, muddin muna tsaye da ƙarfi a kan amincewar nan tamu ta fari, har zuwa ƙarshe. 15 Domin kuwa an ce, “Yau in kun ji muryarsa, Kada ku taurare zukatanku kamar a lokacin tawayen nan.” 16 To, su wane ne suka ji, duk da haka suka yi tawaye? Ashe, ba duk waɗanda suka fito daga ƙasar Masar ba ne, waɗanda Musa ya shugabantar? 17 Da su wa kuma ya yi fushi har shekara arba'in? Ashe, ba da waɗanda suka yi zunubi ba ne, waɗanda gawawwakinsu suka fādi a jeji? 18 Su wa kuma ya rantse wa, cewa ba za su shiga inuwarsa ba, in ba marasa biyayyar nan ba? 19 Sai muka ga, ashe, saboda rashin bangaskiyarsu ne suka kāsa shiga.

Ibraniyawa 4

1 Saboda haka tun alkawarin shiga inuwarsa tana nan, sai mu yi tsananin kula, kada ya zamana waninku ya kāsa shiga. 2 Ai kuwa, an yi mana albishir kamar yadda aka yi musu, sai dai maganar da aka yi musu ba ta amfane su da kome ba, don kuwa ba ta gamu da bangaskiya ga majiyanta ba. 3 Mu kuwa da muka ba da gaskiya, muna shiga inuwar, yadda ya ce, “Sai na yi rantsuwa da fushina, na ce, ‘ba za su shiga inuwata ba sam,’ ” ko da yake ayyukan Allah gamammu ne tun daga farkon duniya. 4 Domin a wani wuri ya yi maganar rana ta bakwai cewa, “A rana ta bakwai Allah ya huta daga ayyukansa duka.” 5 Amma a wannan wuri kuwa sai ya ce, “Ba za su shiga inuwata ba sam.” 6 Wato, tun da yake har yanzu dai da sauran dama waɗansu su shiga, su kuwa waɗanda aka fara yi wa albishirin nan sun kāsa shiga saboda rashin biyayya, 7 to, sai ya sāke sa wata rana, ya ce, “Yau,” yana magana ta bakin Dawuda bayan da aka daɗe, kamar an riga an faɗa cewa, “Yau in kun ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku.” 8 Da dai a ce Joshuwa ya kai su cikin inuwar Allah, da Allah bai yi maganar wata rana nan gaba ba, 9 wato, har yanzu dai akwai sauran wani hutun Asabar ga jama'ar Allah, 10 domin kuwa duk wanda ya shiga inuwar Allah, ya huta ke nan daga ayyukansa, kamar yadda Allah ya hutu daga nasa. 11 Saboda haka, sai mu yi himmar shiga inuwar nan, kada wani ya kāsa shiga, saboda irin wannan rashin biyayya. 12 Domin Maganar Allah rayayyiya ce, mai ƙarfin aiki, ta fi kowane irin takobi kaifi, har tana ratsa rai da ruhu, da kuma gaɓoɓi, har ya zuwa cikin ɓargo, tana kuma iya rarrabe tunanin zuciya da manufarta. 13 Ba wata halittar da za ta iya ɓuyar masa, amma kowane abu a fili yake, a shanye sosai a gaban idon wannan da za mu ba da lissafi a gabansa.

Yesu Babban Firist Mai Girma

14 To, tun da ya ke muna da Babban Firist mai girma, wanda ya ratsa sammai, wato Yesu Ɗan Allah, sai mu tsaya a kan abin da muka bayyana yarda a gare shi. 15 Gama Babban Firist da muke da shi ba marar juyayin kasawarmu ba ne, a'a, shi ne wanda aka jarabe shi ta kowace hanya da aka jarabce mu, amma bai yi zunubi ba. 16 Saboda haka, sai mu kusaci kursiyin Allah na alheri da amincewa, domin a yi mana jinƙai, a kuma yi mana alherin da zai taimake mu a kan kari.

Ibraniyawa 5

1 Kowane babban firist, da yake an zaɓe shi ne daga cikin mutane, akan sa shi ya wakilci mutane ga al'amarin Allah, don ya miƙa sadakoki da kuma hadayu domin kawar da zunubai. 2 Ya kuma zamana wanda zai iya tafiyar da jahilai da sangartattu a cikin salihanci, tun da yake rarrauna ne shi ta ko'ina. 3 Saboda haka, wajibi ne ya miƙa hadayu, ba saboda kawar da zunuban jama'a kaɗai ba, har ma don nasa. 4 Ba wanda zai kai kansa wannan matsayi mai girma, sai dai Allah ya yi kiransa ga haka, kamar yadda aka kirayi Haruna. 5 Haka kuma, Almasihu ba shi ya ɗaukaka kansa ya zama Babban Firist ba, sai dai wannan ne ya sa shi, wanda ya ce da shi, “Kai Ɗana ne, Ni Ubanka ne yau.” 6 Kamar dai yadda a wani wuri kuma ya ce, “Kai firist ne na har abada, Kwatancin ɗabi'ar Malkisadik.” 7 Almasihu, a lokacin zamansa a duniya, ya yi addu'o'i da roƙe-roƙe, tare da kuka mai tsanani, har da hawaye, ga wannan da yake da ikon cetonsa daga mutuwa, aka kuwa saurare shi saboda tsananin miƙa kansa. 8 Ko da yake shi Ɗa ne, ya koyi biyayya ta wurin wuyar da ya sha, 9 da ya kai ga kammala, sai ya zama tushen madawwamin ceto ga dukkan waɗanda suke masa biyayya, 10 gama Allah yana kiransa Babban Firist, kwatancin ɗabi'ar Malkisadik.

Faɗakarwa a kan wata Koyarwa Dabam

11 Muna da abu da yawa da za mu faɗa a game da shi kuwa, amma zai yi wuyar bayani, da yake basirarku ta dushe. 12 Ko da yake kamar a yanzu kam, ai, ya kamata ku zama masu koyarwa, duk da haka, ashe, ba ku wuce wani ya sāke koya muku jigajigan farko na Maganar Allah ba, har ya zamana sai an ba ku nono, ba abinci mai tauri ba. 13 Ai, duk wanda yake nono ne abincinsa, bai ƙware da maganar adalci ba, kamar jariri yake. 14 Amma abinci mai tauri, ai, na manya ne, wato waɗanda hankalinsu ya horu yau da kullum, su rarrabe nagarta da mugunta.

Ibraniyawa 6

1 Saboda haka, sai mu ci gaba a kan ka'idodin farko na al'amarin Almasihu, har ya zuwa kammala, ba wai mu sāke koyar da jigajigan nan na tuba da ibada marar tasiri ba, da na gaskatawa da Allah, 2 da kuma na koyarwa a kan wanke-wanke, da ɗora hannu, da tashin matattu, da dawwamammen hukunci. 3 Za mu kuwa ci gaba in Allah ya yarda. 4 Domin waɗanda aka haskaka zukatansu sarai, har suka ɗanɗana baiwar nan ta Basamaniya, suka kuma sami rabo na ruhu mai tsarki, 5 har suka ɗanɗana daɗin Maganar Allah, da ikon zamani mai zuwa, 6 sa'an nan kuma suka ridda, ba mai yiwuwa ba ne a sāke jawo su ga tuba, tun da yake sāke gicciye Ɗan Allah suke yi, su da kansu, suka kuma wulakanta shi a sarari. 7 Ƙasa ma da take shanye ruwan da ake yi mata a kai a kai, take kuma fid da tsire-tsire masu amfani ga waɗanda ake noma ta dominsu, Allah yakan sa mata albarka. 8 Amma tsire-tsirenta ƙaya ne da kashin yawo, ba ta da amfani ke nan, tana kuma gab da la'antarwa, ƙarshenta dai ƙonewa ne.

Tabbataccen Bege

9 Ko da yake mun faɗi haka, a game da ku kam, ya ƙaunatattu, mun tabbata kuna a kan abubuwa mafiya kyau na zancen ceto. 10 Gama Allah ba marar adalci ba ne, har da zai ƙi kula da aikinku, da kuma ƙaunar sunansa da kuka yi, wajen yi wa tsarkaka hidima, har yanzu ma kuna yi. 11 Muna dai bukata ƙwarai kowannenku ya nuna irin wannan himma ga yin cikkaken bege, tabbatacce, har ya zuwa ƙarshe, 12 don kada ku yi ragwanci, sai dai ku yi koyi da waɗanda suka karɓi cikar alkawaran nan, ta wurin bangaskiyarsu da haƙurinsu. 13 Sa'ad da Allah ya yi wa Ibrahim alkawari, da yake ba wani wanda ya fi shi girma da zai rantse da shi, sai ya rantse da kansa, 14 ya ce, “Hakika zan yi maka albarka, in kuma riɓanya zuriyarka.” 15 Ta haka Ibrahim, bayan da ya jure da haƙuri, ya karɓi cikar alkawarin. 16 Hakika mutane sukan rantse da abin da ya fi su, rantsuwa kuma ita ce abar da take tabbatarwa a duk lokacin gardama. 17 Don haka, sa'ad da Allah yake son ƙara tabbatar wa magādan alkawarin nan dahir, cewa nufinsa ba mai sākewa ba ne sam, sai ya haɗa da rantsuwa, 18 domin albarkacin abubuwa guda biyun nan marasa sākewa, masu nuna, cewa ba shi yiwuwa Allah ya yi ƙarya, mu da muka gudu muka sami mafaka, mu ƙarfafa ƙwarai mu riski abin da muka kafa bege a kai. 19 Begen nan kuwa da muke da shi, kamar anka yake ga rai, kafaffe, tabbatacce, shi ne kuma yake shiga har can ciki bayan labulen, 20 a inda saboda mu ne Yesu ya riga mu shiga, da yake ya zama Babban Firist na har abada, kwatancin ɗabi'ar Malkisadik.

Ibraniyawa 7

Firist Kwatancin Malkisadik

1 Shi wannan Malkisadik, Sarkin Urushalima, firist na Allah Maɗaukaki, ya gamu da Ibrahim a lokacin da Ibrahim yake dawowa daga kisan sarakuna, ya sa masa albarka. 2 Shi ne kuwa Ibrahim ya ba shi ushirin kome. Da farko dai, kamar yadda ma'anar sunansa take, shi sarkin adalci ne, sa'an nan kuma Sarkin Urushalima ne, wato, sarkin salama. 3 Shi ba shi da uwa ko uba, ba a kuma san asalinsa ba. Ba shi da ranar haihuwa balle ranar mutuwa, yana dai kama da Ɗan Allah, firist ne har abada. 4 Kai, ku dubi irin girmansa! Har kakanmu Ibrahim ma ya ba shi ushirin ganima! 5 Ga shi kuma, waɗansu na zuriyar Lawi, in sun sami matsayin firist, akan umarce su bisa ga Shari'a su karɓi ushiri a gun jama'a, wato a gun 'yan'uwansu, ko da yake su ma zuriyar Ibrahim ne. 6 Amma wannan, wanda ma ba a asalin Lawi yake ba, ya karɓi ushiri a gun Ibrahim, har ya sa masa albarka, shi ma da aka yi wa alkawarai. 7 Ai, ba abin musu ba ne, cewa na gaba shi yake sa wa na baya albarka. 8 Ga shi, a nan masu karɓar ushiri, mutane ne masu mutuwa, a can kuwa mai karɓar wanda aka shaida shi, rayayye ne. 9 A ma iya cewa ko Lawi ma da kansa, mai karɓar ushiri, ya ba da ushiri ta wurin Ibrahim, 10 don shi Lawi yana daga tsatson kakansa Ibrahim, sa'ad da Ibrahim ɗin ya gamu da Malkisadik. 11 Gama da a ce kammala tana samuwa ta wurin firistoci na zuriyar Lawi (don ta gare su ne jama'a suka karɓi shari'a), wace bukata kuma ake da ita ta wani firist dabam ya bayyana kwatancin ɗabi'ar Malkisadik, wanda za a ambata ba kwatancin ɗabi'ar Haruna ba? 12 Domin in an sauya matsayin firistoci, sai tilas a sauya Shari'a kuma. 13 Domin kuwa shi wannan da aka faɗi waɗannan abubuwa a game da shi, ai, na wata kabila ne dabam, wadda ba waninta da ya taɓa hidimar bagadin hadaya. 14 Tabbatacce ne, cewa Ubangijinmu ya fito daga zuriyar Yahuza ne, Musa kuwa bai ce kome ba a game da kabilar nan a kan zancen firistoci. 15 Wannan kuma ya ƙara fitowa fili sosai, sa'ad da wani firist dabam ya bayyana kamar Malkisadik, 16 wanda kuwa ya zama firist, ba bisa ga wata ka'ida ta al'adar 'yan adam ba, sai dai ta wurin ikon rai marar gushewa. 17 Domin an shaide shi shi da cewa, “Kai firist ne na har abada, Kwatancin ɗabi'ar Malkisadik.” 18 Ta wani hali an soke wani umarni ta dā saboda rauninsa da kuma rashin amfaninsa, 19 don Shari'a ba ta kammala kome ba, ta wani hali kuma an shigo da wani bege wanda yake mafi kyau, ta wurinsa kuwa muke kusatar Allah. 20 Ba kuwa da rashin rantsuwa aka yi haka ba. 21 Waɗancan sun zama firistoci, ba tare da an yi musu rantsuwa ba, amma wannan kam, sai da aka yi masa rantsuwa, da Allah ya ce masa, “Ubangiji ya rantse, Ba kuwa zai ta da maganarsa ba cewa, ‘Kai firist ne har abada.’ ” 22 A sanadin wannan ne Yesu ya zama lamunin alkawarin da ya fi wancan nesa. 23 Waɗancan firistoci, an yi su da yawa, domin mutuwa ta hana su tabbata a aikin. 24 Amma shi da yake madawwami ne, yana da matsayinsa na firist wanda ba ya komawa hannun wani. 25 Saboda haka, yana da ikon ceton masu kusatowa ga Allah ta wurinsa, matuƙar ceto, tun da yake kullum a raye yake saboda yi musu addu'a. 26 Irin babban firist wanda muke bukata ke nan, mai tsarki, marar aibu, marar cikas, keɓaɓɓe daga masu zunubi, ɗaukakke kuma birbishin sammai. 27 Ba zai miƙa hadaya kowace rana kumar waɗancan manyan firistocin ba, wato, da farko saboda zunubansa, sa'an nan kuma saboda na jama'a. Wannan ya yi ta ne sau ɗaya tak, lokacin da ya miƙa kansa hadaya. 28 Wato shari'a tana sa mutane su zama manyan firistoci duk da rauninsu, amma maganar nan ta rantsuwa da ta sauko bayan Shari'a, ta sa Ɗa wanda yake kammalalle har abada.

Ibraniyawa 8

Babban Firist na Sabon Alkawari

1 Wato, duk manufar maganarmu ita ce wannan. Shi ne irin babban firist wanda muke da shi, wato wanda ya zauna a dama da kursiyin Maɗaukaki a can sammai, 2 mai hidima a Wuri Mafi Tsarki, da kuma masujada ta gaskiya, wadda Ubangiji ya kafa, ba mutum ba. 3 Kowane babban firist akan sa shi domin ya miƙa sadakoki da hadayu, saboda haka wajibi ne wannan shi ma, ya zamanto yana da abin da zai miƙa. 4 To, ashe, da har yanzu yana duniya, da bai zama firist ba ke nan, tun da yake akwai firistocin da suke miƙa sadakoki bisa ga Shari'a. 5 Suna bauta wa makamantan abubuwan Sama da kuma ishararsu, kamar yadda Allah ya gargaɗi Musa sa'ad da yake shirin kafa alfarwar nan, da ya ce, “Ka lura fa, ka shirya kome da kome daidai yadda aka nuna maka a kan dutsen.” 6 Amma ga ainhi, Almasihu ya sami hidima wadda take mafificiya, kamar yadda alkawarin nan, wanda shi ne matsakancinsa, yake da fifiko nesa, tun da yake an kafa shi ne a kan mafifitan alkawarai. 7 Domin da wancan alkawari na farko bai gaza ba kome ba, da ba sai an sāke neman na biyu ba. 8 Gama da ya ga laifinsu da ya ce, “Lokaci yana zuwa, in ji Ubangiji, Da zan tsara sabon alkawari da jama'ar Isra'ila, Da kuma zuriyar Yahuza. 9 Ba irin alkawarin da na yi da kakanninsu ba, A ranar da na kama hannunsu Domin in fito da su daga ƙasar Masar. Saboda ba su tsaya ga alkawarina ba, Shi ya sa na ƙyale su, in ji Ubangiji. 10 Wannan shi ne alkawarin da zan yi da jama'ar Isra'ila, Bayan kwanakin nan, in ji Ubangiji, Wato, zan sa shari'una a birnin zuciyarsu, In kuma rubuta su a allon zuciyarsu. Zan kasance Allahnsu, Su kuma su kasance jama'ata. 11 Ba kuma sai sun koya wa ɗan garinsu ba, Balle wani ya ce ɗan'uwansa, ‘Kă san Ubangiji!’ Domin kowa zai san ni, Daga ƙaraminsu, har ya zuwa babbansu. 12 Domin zan yi musu jinƙai a kan muguntarsu, Ba kuwa zan ƙara tunawa da zunubansu ba.” 13 Da ya ce sabon alkawari, ashe kuwa, ya mai da na farkon tsoho ke nan. Abin da yake tsufa, yana kuwa daɗa tsofewa, lalle ya yi kusan shuɗewa ke nan.

Ibraniyawa 9

Wurare Tsarkaka na Duniya da na Sama

1 Alkawarin farko yana da ka'idodinsa na yin sujada, da kuma wurin yinta tsattsarka wanda mutane suka shirya. 2 Wato, an kafa alfarwa wadda sashinta na farko yake da fitila, da tebur, da kuma keɓaɓɓiyar gurasa. Ana kiran wannan sashi Wuri Mai Tsarki. 3 Bayan labule na biyu kuma, akwai sashin alfarwa da ake kira Wuri Mafi Tsarki. 4 A cikinsa kuwa da faranti na zinariya domin ƙona turare, da kuma akwatin alkawari da aka yi masa laffa da zinariya ta kowane gefe. A cikinsa kuwa akwai tasar zinariya da manna a ciki, da sandar Haruna wadda ta yi toho, da kuma allunan dutse na alkawarin nan. 5 A bisa akwatin alkawari kuma akwai kerubobin nan na ɗaukakar Allah, waɗanda suka yi wa murfin akwatin nan laima. Ba za mu iya yin maganar waɗannan abubuwa filla filla ba a yanzu. 6 In an gama waɗannan shirye-shirye haka, sai firistoci kullum su riƙa shiga sashin farko an alfarwar, suna hidimarsu ta ibada. 7 Amma na biyun, sai babban firist kaɗai yake shiga, shi ma kuwa sai sau ɗaya a shekara, sai kuma da jini wanda yakan miƙa saboda kansa, da kuma kurakuran jama'a. 8 Ta haka Ruhu Mai Tsarki yake yin ishara, cewa ba a buɗe hanyar shiga Wuri Mafi Tsarki ba tukuna, muddin alfarwa tana nan a tsaye, 9 wadda take ishara ce ga wannan zamani. Bisa ga wannan ishara akan yi miƙa sadaka da hadaya, amma ba sa iya kammala lamirin mai ibadar, 10 tun da yake ci da sha da wankewanke iri iri kaɗai suke shafa, ka'idodi ne a game da jiki kurum, waɗanda aka sa kafin a daidaita al'amari. 11 Amma Almasihu ya riga ya zo, yana babban firist na kyawawan abubuwan da suke akwai. Masujadar da yake hidima a ciki mafi ɗaukaka ce, mafi kammala kuwa (wadda ba yin mutum ba ce, wato, ba ta wannan halittacciyar duniya ba ce). 12 Almasihu ya shiga Wuri Mafi Tsarki sau ɗaya tak, ba ƙari, ba kuwa ta wurin jinin awaki ko na 'yan maruƙa ya shiga ba, sai dai ta wurin nasa jini, ya samo mana madawwamiyar fansa. 13 To, jinin awaki ne fa da na bijimai, da kuma tokar karsana da ake yayyafa wa waɗanda suka ƙazantu, suke tsarkake su da tsabtacewar jiki, 14 balle fa jinin Almasihu wanda ya miƙa kansa marar aibu ga Allah, ta wurin Madawwamin Ruhu, lalle zai tsarkake lamirinmu daga barin ibada marar tasiri, domin mu bauta wa Allah Rayayye. 15 Saboda haka, shi ne matsakancin sabon alkawari, domin waɗanda aka kira su karɓi dawwamammen gādon da aka yi musu alkawari, tun da yake an yi wata mutuwa mai fansar waɗanda suke keta umarni a game da alkawarin farko. 16 A game da al'amarin wasiyya, lalle ne a tabbatar da mutuwar wanda ya yi ta tukuna. 17 Domin ba a zartar da wasiyya sai bayan an mutu, tun da yake ba a yin aiki da ita muddin wanda ya yi ta yana a raye. 18 Ashe kuwa, mun ga alkawarin nan na farko, ba a tabbatar da shi ba, sai a game da jini. 19 Don bayan Musa ya sanar da kowane umarnin Shari'a ga dukan jama'a, sai ya ɗebi jinin 'yan maruƙa da na awaki, tare da ruwa, da jan ulu, da kuma ganyen izob, ya yayyafa wa Littafin kansa, da kuma duk jama'a, 20 yana cewa, “Wannan shi ne jini na tabbatar alkawarin nan, da Allah ya yi umarni a game da ku.” 21 Haka kuma, ya yayyafa jinin ga alfarwar nan, da dukan kayanta na yin hidima. 22 Hakika, bisa ga Shari'a, kusan kowane abu da jini ake tsarkake shi, in ba a game da zubar da jini ba kuwa, to, ba gafara.

Almasihu ya Miƙa Kansa domin Kawar da Zunubi

23 Da waɗannan abubuwa ne, ya wajaba a tsarkake makamantan abubuwan da ke a Sama, sai dai ainihin abubuwan Sama za a tsarkake su ne da hadayar da ta fi waɗannan kyau. 24 Domin Almasihu bai shiga wani wuri tsattsarka da mutum ya yi ba, wanda yake sura ne kawai na gaskataccen, a'a Sama kanta ya shiga, domin yă bayyana a gaban zatin Allah a yanzu saboda mu. 25 Ba kuwa domin ya riƙa miƙa kansa hadaya a kai a kai ba ne, kamar yadda babban firist yake shiga Wuri Mafi Tsarki a kowace shekara da jinin da ba nasa ba ne. 26 In da haka ne, ashe, da sai lalle ya yi ta shan wuya a kai a kai ke nan, tun daga farkon duniya. Amma a yanzu ya bayyana sau ɗaya tak, a ƙarshen zamanai, domin ya kawar da zunubi ta wurin miƙa kansa hadaya. 27 Tun da yake an ƙaddara wa ɗan adam ya mutu sau ɗaya ne, bayan haka kuma sai shari'a, 28 shi Almasihu ma, da aka miƙa shi hadaya sau ɗaya tak, domin ya ɗauke zunuban mutane da yawa, zai sāke bayyana, bayyana ta biyu, ba a kan maganar kawar da zunubi ba, sai dai domin yă ceci waɗanda suke ɗokin zuwansa.

Ibraniyawa 10

1 To, tun da yake Shari'a ishara ce kawai ta kyawawan abubuwan da suke a gaba, ba ainihin siffarsu ba, ashe, har abada ba za ta iya kammala waɗanda suke kusatar Allah ta wurin waɗannan hadayu ba, waɗanda ake yi a kai a kai kowace shekara. 2 In haka ne kuwa, ashe, ba sai a daina yin hadayar ba? Da an taɓa tsarkake masu ibadar nan sarai, ai, da ba su ƙara damuwa da zunubai ba. 3 Amma a game da irin waɗannan hadayu, akan tuna da zunubai a kowace shekara, 4 domin ba mai yiwuwa ba ne jinin bijimai da na awaki ya ɗauke zunubi. 5 Shi ya sa da Almasihu zai shigo duniya, sai ya ce, “Hadaya da sadaka kam, ba ka so, Amma kā tanadar mini jiki. 6 Ba ka farin ciki da hadayar ƙonewa, da kuma hadayar kawar da zunnbai. 7 Sa'an nan na ce, ‘Ga ni, na zo in aikata nufinka, ya Allah,’ Kamar yadda yake a rubuce a game da ni a Littafi.” 8 Sa'ad da ɗazu ya ce, “Ba ka son hadaya, da sadaka, da hadayar ƙonewa, sa hadayar kawar da zunubai, ba ka kuwa jin daɗinsu,” wato, irin waɗanda ake miƙawa ta hanyar Shari'a, 9 sai kuma ya ƙara da cewa, “Ga ni, na zo in aikata nufinka.” Ya kawar da na farkon ne, don yă kafa na biyun. 10 Ta nufin nan ne aka tsarkake mu, ta wurin miƙa jikin Yesu Almasihu hadaya sau ɗaya tak, ba ƙari. 11 Har wa yau kuma, kowane firist yakan tsaya a kan hidimarsa kowace rana, yana miƙa hadaya iri ɗaya a kai a kai, waɗanda har abada ba za su iya ɗauke zunubai ba. 12 Amma shi Almasihu da ya miƙa hadaya guda ta har abada domin kawar da zunubai, sai ya zauna a dama ga Allah, 13 tun daga lokacin nan yana jira, sai an sa ya take maƙiyansa. 14 Gama ya hadaya guda kawai ya kammala waɗanda aka tsarkake har abada. 15 Ruhu Mai Tsarki ma yana yi mana shaida haka, domin bayan ya ce, 16 “Wannan shi ne alkawarin da zan yi da su, Bayan kwanakin nan, in ji Ubangiji, Zan sa shari'una a birnin zuciyarsu, In kuma rubuta su a allon zuciyarsu,” 17 sai kuma ya ƙara cewa, “Ba kuma zan ƙara tunawa da zunubansu da laifofinsu ba.” 18 To, a inda aka sami gafarar waɗannan, ba sauran wata hadaya domin kawar da zunubi.

Mu Matsa kusa, mu Dage

19 Saboda haka, ya 'yan'uwa, tun da muke da amincewar shiga Wuri Mafi Tsarki, ta wurin jinin Yesu, 20 ta wurin sabuwar hanya, rayayyiya wadda ya buɗe mana ta labulen nan, wato jikinsa, 21 da yake kuma muna da Firist mai girma, mai mulkin jama'ar Allah, 22 sai mu matsa kusa, da zuciya ɗaya, da cikakkiyar bangaskiya tabbatacciya, da zukatunmu tsarkakakku daga mugun lamiri, jikinmu kuma wankakke da tsattsarkan ruwa. 23 Sai mu tsaya da ƙarfi a kan bayyana yarda ga begen nan namu, domin shi mai yin alkawarin nan amintacce ne, 24 mu kuma riƙa kula da juna, ta yarda za mu ta da juna a tsimi mu mu yi ƙauna da aika nagari. 25 Kada mu bar yin taronmu, yadda waɗansu suke yi, sai dai mu ƙarfafa wa juna zuciya, tun ba ma da kuka ga ranar nan tana kusatowa ba. 26 In kuwa mun ci gaba da yin zunubi da gangan, bayan mun yi na'am da sanin gaskiya, to, ba fa sauran wata hadaya domin kawar da zunubai, 27 sai dai matsananciyar fagabar hukunci, da kuma wuta mai tsananin zafi, wadda za ta cinye maƙiyan Allah. 28 Kowa ya yar da Shari'ar Musa, akan kashe shi ba tausayi, a kan shaidu biyu ko uku. 29 To mutumin da ya raina Ɗan Allah, ya kuma tozarta jinin nan na tabbatar alkawari, wanda aka tsarkake shi da shi, har ya wulakanta Ruhun alheri, wane irin hukunci mafi tsanani kuke tsammani ya cancanta fiye da wancan? 30 Domin mun san shi, shi wanda ya ce, “Ramuwa tawa ce, ni zan sāka.” Da kuma, “Ubangiji zai yi wa jama'arsa hukunci.” 31 Abu ne fa mai matuƙar bantsoro a fāɗa a cikin hukuncin Allah Rayayye. 32 Amma dai ku tuna, a shekarun baya, bayan da aka haskaka zukatanku, kun jure tsananin fama da shan wuya, 33 wata rana ana zaginku, ana ta wahalshe ku, ana wulakanta ku a gaban jama'a, wata rana kuma kuna mai da kanku ɗaya da waɗanda aka yi wa haka, 34 domin kun ji tausayin ɗaurarru, kun kuma yarda da daɗin rai da wason da aka yi muku, tun da yake kun sakankance kuna da mallaka mafi kyau, mai tabbata kuwa. 35 Saboda haka, kada ku yar da amincewar nan taku, domin tana da sakemako mai yawa. 36 Gama yin jimiri ya kama ku, domin bayan da kun aikata nufin Allah, ku sami abin da aka yi muku alkawari. 37 “Sauran lokaci kaɗan, Mai zuwan nan zai zo, ba kuwa zai yi jinkiri ba. 38 Amma adalina, ta wurin bangaskiya zai rayu. Amma in ya ja da baya, ba zan yi farin ciki da shi ba.” 39 Amma mu ba a cikin waɗanda suke ja da baya su hallaka muke ba, mu a cikin masu bangaskiya muke, mai kai mu ga ceton rayukanmu.

Ibraniyawa 11

Bangaskiya

1 To, bangaskiya kuwa ita ce haƙƙaƙewar abubuwan da ake bege, a kai, ita ce kuma tabbatawar abubuwan da ba a gani ba. 2 Domin ta gare ta ne shugabannin dā suka sami yardar Allah. 3 Ta wurin bangaskiya muka fahimta, cewa ta faɗar Allah ce aka tsara duniya, har ma abubuwan da ake gani, daga abubuwan da ba a gani ne, suka kasance. 4 Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadaya mafi kyau a kan Kayinu, ta wurin wannan bangaskiya ce ya kuma sami yardar Allah a kan shi mai adalci ne domin Allah ma ya shaide shi, da ya karɓi abubuwan da ya bayar. Ya mutu kam, amma ta wurin bangaskiyar nan tasa har ya zuwa yanzu yana magana. 5 Saboda bangaskiya ce aka ɗauke Anuhu, shi ya sa bai mutu ba, ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Tun kafin a ɗauke shi ma, an shaide shi a kan ya faranta wa Allah rai. 6 In ba a game da bangaskiya ba kuwa, ba shi yiwuwa a faranta masa rai. Domin duk wanda zai kusaci Allah, lalle ne ya gaskata cewa, akwai shi, yana kuma sakamako ga masu nemansa. 7 Ta wurin bangaskiya Nuhu, da Allah ya yi masa gargaɗi a kan al'amuran da ba a gani ba a lokacin, yana tsoron Allah, ya sassaƙa jirgi, don ceton iyalin gidansa, ta wurin bangaskiya kuma ya tabbatar wa duniya laifinta, har ya zama magājin adalcin Allah, wanda yake samuwa ta wurin bangaskiya. 8 Ta wurin bangaskiya Ibrahim ya yi biyayya, sa'ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasa da zai karɓa gādo. Ya kuwa fita, bai ma san inda za shi ba. 9 Ta wurin bangaskiya kuma ya yi baƙunci a ƙasar alkawari, kamar dai a ƙasar bare, suna zaune a cikin alfarwai, shi da Ishaku da Yakubu, abokan tarayya ga gādon alkawarin nan. 10 Yana ta jiran birnin nan mai tushe, wanda mai fasalta shi, mai gina shi kuma, Allah ne. 11 Ta wurin bangaskiya Saratu da kanta ta sami ikon yin ciki, ko da yake ta wuce lokacin haihuwa, tun da dai ta amince, cewa shi mai yin alkawarin nan amintacce ne. 12 Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, aka haifi zuriya masu yawa kamar taurari, kamar yashi kuma dangam a bakin teku. 13 Waɗannan duka sun mutu cikin bangaskiyarsu, ba su kuwa sami abubuwan da aka yi musu alkawari ba, amma da suka tsinkato su, sai suka yi ta murna da ganinsu, suna kuma yarda su baƙi ne, bare kuma a duniya. 14 Mutane masu irin wannan magana, ai, sun bayyana a fili, suna neman wata ƙasa ta kansu ne. 15 Da suna marmarin ƙasar nan da suka baro ne, da sun sami damar komawa. 16 Amma bisa ga hakika sun ɗokanta ne a kan wata ƙasa mafi kyau, wato ta Sama. Saboda haka ne, Allah ba ya jin kunya a ce da shi Allahnsu, don kuwa ya shirya musu birni. 17 Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa'ad da aka gwada shi, ya miƙa Ishaku hadaya, wato shi da ya yi na'am da alkawaran nan, ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa, 18 wanda a kansa aka yi faɗi cewa, “Ta wurin Ishaku ne za a lasafta zuriyarka.” 19 Ya amince da cewa, ko daga matattu Allah yana da iko ya ta da mutum. Ai kuwa, bisa ga misali, sai a ce daga matattu ne ya sāke samun Ishaku. 20 Ta wurin bangaskiya Ishaku ya sa wa Yakubu da Isuwa albarka a kan al'amuran da za su zo. 21 Ta wurin bangaskiya Yakubu, sa'ad da yake bakin mutuwa, ya sa wa 'ya'yan Yusufu albarka dukkansu biyu, ya kuma yi sujada, yana sunkuye a kan sandarsa. 22 Ta wurin bangaskiya Yusufu, da ajalinsa ya yi, ya yi maganar ƙaurar Isra'ilawa, har ya yi wasiyya a game da ƙasusuwansa. 23 Ta wurin bangaskiya ne, sa'ad da aka haifi Musa, iyayensa suka ɓoye shi har wata uku, domin sun ga yaron kyakkyawa ne, ba su kuma ji tsoron umarnin sarki ba. 24 Ta wurin bangaskiya Musa, sa'ad da ya girma, ya ƙi yarda a kira shi ɗan 'yar Fir'auna, 25 ya gwammaci ya jure shan wuya tare da jama'ar Allah, da ya mori romon zunubi, mai saurin wucewa. 26 Ya amince, cewa wulakanci saboda Almasihu wadata ce a gare shi, fiye da dukiyar ƙasar Masar, domin ya sa ido a kan sakamakon. 27 Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, bai ji tsoron fushin sarki ba, ya kuwa jure saboda yana ganin wannan da ba ya ganuwa. 28 Ta wurin bangaskiya ya ci Jibin Ƙetarewa, ya yayyafa jini, domin kada mai hallakar da 'ya'yan fari ya taɓa Isra'ilawa. 29 Ta wurin bangaskiya suka haye Bahar Maliya ta busasshiyar ƙasa, amma da Masarawa suka yi ƙoƙarin yin haka, sai aka dulmuyar da su. 30 Ta wurin bangaskiya garun Yariko ya rushe, bayan an yi ta kewaya shi har kwana bakwai. 31 Ta wurin bangaskiya Rahab karuwar nan ba ta hallaka tare da maƙiya biyayya ba, ta karɓi 'yan ganganimar nan kamar aminai. 32 Me kuma zan ƙara cewa? Ai, lokaci zai ƙure mini a wajen ba da labarin su Gidiyon, da Barak, da Samson, da Yefta, da Dawuda, da Sama'ila, da kuma sauran annabawa, 33 waɗanda ta wurin bangaskiya suka ci masarautai, suka aikata adalci, suka sami cikar alkawarai, suka rurrufe bakunan zakoki, 34 suka i, wa ikon wuta, suka tsere wa kaifin takobi, suna marasa ƙarfi sai suka zama masu ƙarfi, suka yi jaruntaka a wajen yaƙi, suka fatattaka rundunar waɗansu ƙasashe. 35 Aka mayar wa mata da matattunsa da aka tasar. Waɗansu mutane kuma an azabta su har suka mutu, amma sun ƙi yarda da irin 'yancin da za a ba su, domin a tashe su su rayu da rayuwa mafi kyau. 36 Har wa yau kuma, waɗansu suka sha ba'a da bulala, har ma da ɗauri da jefawa a cikin kurkuku. 37 Aka jejeffe su da duwatsu, an gwada su, aka raba su biyu da zarto, aka sare su da takobi. Sun yi yawo saye da buzun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, da ƙunci, da wukakanci. 38 Su kam, duniya ba ta ma cancanci su zama a cikinta ba. Sun yi yawo a jazza da a kan duwatsu, suna kwana a cikin kogwanni da ramummuka. 39 Waɗannan duka, ko da yake Allah ya shaide su saboda bangaskiyarsu, duk da haka, ba su sami cikar alkawarin ba, 40 tun da Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau, sai kuwa tare da mu ne za a kammala su.

Ibraniyawa 12

Horon Ubangiji

1 Saboda haka, tun da taron shaidu masu ɗumbun yawa suka kewaye mu haka, sai mu ma mu yar da dukkan abin da ya nauyaya mana, da kuma zunubin da ya ɗafe mana, mu kuma yi tseren nan da yake gabanmu tare da jimiri, 2 muna zuba ido ga Yesu, shi da yake shugaban bangaskiyarmu, da kuma mai kammala ta, wanda domin farin cikin da aka sa a gabansa ya daure wa gicciye, bai mai da shi wani abin kunya ba, a yanzu kuma a zaune yake a dama ga kursiyin Allah. 3 Ku fa, dubi wannan da ya jure irin a gābar nan da masu zunubi suka sha yi da shi, don kada ku gaji, ko kuwa ku karai. 4 Famarku da zunubi ba ta kai har yadda za a kashe ku ba. 5 Kun kuma mance da gargaɗin nan da Allah ya yi muku a kan ku 'ya'yansa ne, wato “Ya ɗana, kada ka raina horon Ubangiji, Kada kuma ka karai, in ya kwaɓe ka. 6 Domin Ubangiji, wanda yake ƙauna, shi yake horo, Yakan kuma hori duk ɗan da ya karɓa.” 7 Shan wuyar da kuke jurewa, ai, duk don horo ne. Allah ya riƙe ku, ku 'ya'yansa ne. To, wane ɗa ne mahaifinsa ba ya horonsa? 8 In kuwa ba ku da horo irin horon da ake yi wa kowa, to, ashe, kun zama shegu ke nan, ba 'yan halal ba. 9 Har wa yau kuma, ai, muna da ubanninmu na jiki da suke hore mu, mun kuwa yi musu ladabi. Ashe, ba za mu fi ya wa Uban ruhohinmu biyayya ƙwarai ba, mu rayu? 10 Su kam, sun hore mu a ɗan lokaci kaɗan don ganin damarsu, amma shi, don amfanin kanmu ne yake horonmu, domin mu zama abokan tarayya a cikin tsarkinsa. 11 Ai, kowane irin horo, a lokacin shansa, abu ne mai baƙin ciki, ba na farin ciki ba. Amma daga baya waɗanda suka horu ta haka sukan sami kwanciyar rai wadda aikin adalci yake bayarwa.

Faɗakarwa a kam Ƙin Alherin Allah

12 Domin wannan, ku miƙe hannuwanku da suke reto, da gwiwoyinku marasa ƙarfi. 13 Ku bi miƙaƙƙun hanyoyi ɗoɗar, don kada mai ɗingishi ya gulle, a maimakon ya warke. 14 Ku himmantu ga zaman lafiya da kowa, ku kuma zama a tsarkake, in banda shi kuwa, ba wanda zai ga Ubangiji. 15 Ku kula fa, kada kowa ya kāsa samun alherin Allah, kada kuma wani tushen ɗacin rai ya tabbata, ya haddasa ɓarna, har ya ɓata mutane masu yawa ta haka, 16 kada kuma wani ya zama fasiki, ko mai sāɓon Allah, kamar isuwa, wanda ya sayar da hakkinsa na ɗan fari a kan cimaka a ɗaya tak. 17 Kun dai sani daga baya, da ya so ya gāji albarkar nan, sai aka ƙi shi, domin bai sami hanyar tuba ba, ko da yake ya yi ta nemanta har da hawaye. 18 Ai, ba ga abin da za a taɓa ne, kuka iso ba, ko wuta mai ruruwa, ko baƙin duhu duhu ƙirin, ko hadiri, 19 ko ƙarar ƙaho, ko wata murya, wadda har masu jin maganarta suka yi roƙo kada su ƙara ji, 20 don ba su iya jure umarnin da aka yi musu ba cewa, “Ko da dabba ce ta taɓa dutsen, sai a kashe ta da jifa.” 21 Amma ganin wannan abu da matuƙar bantsoro yake! Har ma Musa ya ce, “Ina rawar jiki don matuƙar tsoro.” 22 Amma ku kan iso Ɗutsen Sihiyona ne, da birnin Allah Rayayye, Urushalima ta Sama, wurin dubban mala'iku. 23 Kun iso taron farin ciki na kirayayyun 'ya'yan fari na Allah, waɗanda sunayensu ke a rubuce a Sama. Kun iso wurin Allah, wanda yake shi ne mai yi wa kowa shari'a, da kuma wurin ruhohin mutane masu adalci, waɗanda aka kammala. 24 Kun iso wurin Yesu, matsakancin sabon alkawari, da kuma wurin jinin nan na tsarkakewa, wanda yake yin mafificiyar magana fiye da na Habila. 25 Ku kula fa, kada ku ƙi mai maganar nan. Domin in waɗanda suka ƙi jin mai yi musu gargaɗi a duniya ba su tsira ba, to, ƙaƙa mu za mu tsira, in mun ƙi jin wannan da yake yi mana gargaɗi ma daga Sama? 26 A lokacin nan muryarsa ta girgiza duniya, amma a yanzu ya yi alkawari cewa, “Har wa yau dai sau ɗaya tak, ba duniya kaɗai zan girgiza ba, amma har sama ma.” 27 To, wannan cewa, “Har wa yau dai sau ɗaya tak,” ya nuna kawar da abubuwan da aka girgiza, wato abubuwan da aka halitta, don abubuwan da ba sa girgizuwa su wanzu. 28 Saboda haka, sai mu yi godiya domin mun sami mulkin da ba ya girgizuwa, ta haka kuma mu yi wa Allah sujada abar karɓa, tare da tsoro da tsananin girmamawa, 29 domin Allahnmu wuta ne mai cinyewa.

Ibraniyawa 13

Gudunmawar da yake Faranta wa Allah Rai

1 Sai ku nace da ƙaunar 'yan'uwa. 2 Kada ku daina yi wa baƙi alheri, gama ta haka ne waɗansu suka sauki mala'iku ba da sani ba. 3 Ku riƙa tunawa da waɗanda ke kurkuku, kamar tare kuke a ɗaure, da kuma waɗanda ake gwada wa wuya, kamar ku ake yi wa. 4 Kowa yă girmama aure, Gădon aure kuwa yă zauna marar dauɗa, don fasikai da mazinata Allah zai hukunta su, 5 Kada halinku ya zama na son kuɗi. Ku dangana da abin da kuke da shi, gama Allah kansa ya ce, “Har abada ba zan bar ka ba. Har abada kuma ba zan yashe ka ba.” 6 Saboda haka, ma iya fitowa gabagaɗi, mu ce, “Ubangiji shi ne mataimakina, Ba zan ji tsoro ba. Me mutum zai iya yi mini?” 7 Ku tuna da shugabanninku na dā, waɗanda suka faɗa muku Maganar Allah. Ku dubi ƙarshensu, ku kuma yi koyi da bangaskiyarsu. 8 Yesu Almasihu ba ya sākewa, shi ne a jiya, da yau, hakika har abada ma. 9 Kada baƙuwar koyarwa iri iri ta bauɗar da ku, ai, abu ne mai kyau alherin Allah ya zamana shi yake ƙarfafa zuciya, ba abinci iri iri ba, waɗanda ba su amfani ga masu dogara da su. 10 Muna da bagadin hadaya, wanda masu ibada a alfarwar nan ba su da izini su ci abincin wurin, 11 domin naman dabbobin da babban firist ke ɗiban jininsu yă kai Wuri Mafi Tsarki domin kawar da zunubai, akan ƙone shi ne a bayan zango. 12 Haka ma, Yesu ya sha wuya a waje bayan birni, domin yă tsarkake jama'a da nasa jini. 13 Saboda haka, sai mu fita mu je a gare shi a bayan zango, muna shan irin wulakancin da aka yi masa. 14 Domin ba mu da wani dawwamammen birni a nan, birnin nan mai zuwa muke nema. 15 To, a koyaushe, sai mu yi ta yabon Allah ta wurinsa, sadakar da muke miƙawa ke nan, wato mu yabe shi, muna ta ɗaukaka sunansa. 16 Kada kuwa ku daina yin alheri da gudunmawa, domin irin waɗannan su ne suke faranta wa Allah rai. 17 Ku yi wa shugabanninku biyayya, ku bi umarnansu, don su ne masu kula da rayukanku, su ne kuma za su yi lissafin aikinsu, don su yi haka da farin ciki, ba da baƙin ciki ba, don in sun yi da baƙin ciki ba zai amfane ku ba. 18 Ku yi mana addu'a, gama mun tabbata muna da lamiri mai kyau, muna kuwa so mu tafiyar da al'amuranmu da halin kirki ne. 19 Musamman nake tsananta roƙonku ku yi haka, don a hanzarta a komo da ni a gare ku.

Sa Albarka da kuma Gaisuwa

20 Allah mai zartar da salama, wanda ya ta da Ubangijinmu Yesu, Makiyayin tumaki mai girma, daga matattu, albarkacin jinin nan na tabbatar madawwamin alkawari, 21 yă kamala ku da kowane irin kyakkyawan abu, domin ku aikata nufinsa, yă kuma aikata a cikinmu abin da yake faranta masa rai ta wurin Yesu Almasihu. Ɗaukaka tă tabbata a gare shi har abada abadin. Amin, Amin. 22 To, ina roƙonku, 'yan'uwa, ku yi haƙuri da gargaɗina, don taƙaice na rubuto muku. 23 Ku sani, an sāki ɗanuwanmu Timoti, da shi ma za mu gan ku, in ya zo da wuri. 24 Ku gai da dukan shugabanninku, da kuma dukan tsarkaka. Waɗanda suke daga ƙasar Italiya suna gaishe ku. 25 Alharin Ubangiji yă tabbata a gare ku, ku duka. Amin.

Yakubu 1

Gaisuwa

1 Daga Yakubu, bawan Allah, da kuma na Ubangiji Yesu Almasihu, zuwa ga kabilan nan goma sha biyu da suke a warwatse a duniya. Gaisuwa mai yawa.

Bangaskiya da Tawali'u

2 Ya ku 'yan'uwana, duk sa'ad da gwaje-gwaje iri iri suka same ku, ku mai da su abin farin ciki ƙwarai. 3 Domin kun san jarrabawar bangaskiyarku takan haifi jimiri. 4 Sai kuma jimiri ya yi cikakken aikinsa, domin ku zama kamilai cikakku kuma, ba ku gaza da kome ba. 5 In waninku ya rasa hikima, sai ya roƙi Allah, mai ba kowa hannu sake, ba tare da gori ba, sai kuwa a ba shi. 6 Amma fa sai ya roƙa da bangaskiya, ba tare da shakka ba. Don mai shakka kamar raƙuman ruwan teku yake, waɗanda iska take korawa tana tuttunkuɗawa. irin mutumin nan mai zuciya biyu, wanda bai tsai da zuciyarsa a gu ɗaya a dukan al'amuransa ba, ya sa rai da wani abu a gun Ubangiji. 9 Ƙasƙantaccen ɗan'uwa yă yi taƙama da ɗaukakarsa. 10 Mai arziki kuma yă yi alfarma da ƙasƙancinsa, gama zai shuɗe kamar hudar ciyawa. 11 In rana ta tāke da ƙunarta, sai ciyawa ta bushe, hudarta ta kaɗe, kyanta kuma ya gushe. Haka ma mai arziki zai gushe yana a cikin tsakiyar da harkarsa.

Gwaji da Jarrabawa

12 Albarka tā tabbata ga mai jimirin gwaji, domin in ya jure gwajin, sai ya sami kambin rai, wanda Ubangiji ya yi wa masu ƙaunarsa alkawari. 13 Duk wanda ake jarabta, kada ya ce Allah ne yake jarabtarsa, gama ba shi yiwuwa a jarabci Allah da mugunta, shi kansa kuwa ba ya jarabtar kowa. 14 Amma kowane mutum yakan jarabtu in mugun burinsa ya ruɗe shi, ya kuma yaudare shi. 15 Mugun buri kuma in ya yi ciki, yakan haifi zunubi. Zunubi kuma in ya balaga, yakan jawo mutuwa. 16 Kada fa a yaudare ku, ya 'yan'uwana ƙaunatattu. 17 Kowace kyakkyawar baiwa, da kowace cikakkiyar kyauta, daga Sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau. 18 Bisa ga nufinsa ya kawo mu ta maganar gaskiya, domin mu zama kamar nunan fari na halittarsa.

Jin Magana da Aikatawa

19 Ya 'yan'uwana ƙaunatattu, ku san wannan, wato, kowa yă yi hanzarin kasa kunne, da jinkirin yin magana, da kuma jinkirin yin fushi, 20 don fushin mutum ba ya aikata adalci. 21 Saboda haka, sai ku yar da kowane irin aikin ƙazanta da ƙeta iri iri, maganar nan da aka dasa a zuciyarku, ku yi na'am da ita a cikin halin tawali'u, domin ita ce mai ikon ceton rayukanku. 22 Amma ku zama masu aikata maganar, ba masu ji kawai, kuna yaudarar kanku ba. 23 Don duk wanda yake mai jin maganar ne kawai, ba mai aikatawa ba, kamar mutum yake mai duba fuskarsa a madubi, 24 don yakan dubi fuskarsa ne kawai ya tafi, nan da nan kuwa sai ya mance kamanninsa. 25 Amma duk mai duba cikakkiyar ka'idar nan ta 'yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai ya mance ba, sai dai mai aikatawa ne ya zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake aikatawa. 26 In wani yana zaton shi mai addini ne, amma bai kame bakinsa ba, sai dai ya yaudari kansa, to, addinin mutumin nan na banza ne. 27 Addini sahihi kuma marar aibu a gaban Allah Ubanmu, shi ne a kula da gwauraye mata, da marayu a cikin ƙuntatarsu, a kuma a keɓe kai marar aibi daga duniya.

Yakubu 2

Faɗaka a kan Tara

1 Ya ku 'yan'uwana, kada ku nuna bambanci muddin kuna riƙe da bangaskiyarku ga Ubangijinmu Yesu Almasihu, Ubangiji Maɗaukaki. 2 Misali, in mutum mai zobban zinariya da tufafi masu ƙawa ya halarci taronku, wani matalauci kuma ya shigo a saye da tsummoki, 3 sa'an nan kuka kula da mai tufafi masu ƙawar nan, har kuka ce masa, “Ga mazauni mai kyau a nan,” matalaucin nan kuwa kuka ce masa, “Tsaya daga can,” ko kuwa, “Zauna a nan ƙasa a gabana,” 4 ashe, ba ku nuna bambanci a tsakaninku ba ke nan, kuna zartar da hukunci da mugayen tunani? 5 Ku saurara, ya 'yan'uwana ƙaunatattu. Ashe, Allah bai zaɓi matalautan duniyar nan su wadata da bangaskiya, har su sami gado a cikin mulkin nan da ya yi wa masu ƙaunarsa alkawari ba? 6 Amma, kun wulakanta matalauta! Ashe, ba masu arzikin ne suke matsa muku ba? Ba su ne kuwa suke janku zuwa gaban shari'a ba? 7 Ba kuma su ne kuke saɓon sunan nan mai girma da ake kiranku da shi ba? 8 Idan lalle kun cika muhimmin umarni yadda Nassi ya ce, “Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka,” to, madalla. 9 Amma in kun nuna bambanci, kun yi zunubi ke nan, Shari'a kuma ta same ku da laifin keta umarni. 10 Duk wanda yake kiyaye dukkan Shari'a, amma ya saɓa a kan abu guda, ya saɓi Shari'a gaba ɗaya ke nan. 11 Domin shi wannan da ya ce, “Kada ka yi zina,” shi ne kuma ya ce, “Kada ka yi kisankai.” To, in ba ka yi zina ba amma ka yi kisankai, ai, ka zama mai keta Shari'a ke nan. 12 Saboda haka, maganarku da aikinku su kasance irin na mutanen da za a yi wa shari'a bisa ga ka'idar 'yanci. 13 Gama Shari'a marar jinƙai ce ga wanda ba ya nuna jinƙai. Amma jinƙai yana rinjayar hukunci.

Bangaskiya Ba tare da Ayyuka ba Banza Ce

14 Ya ku 'yan'uwana, ina amfani mutum ya ce yana da bangaskiya, alhali kuwa ba ya aikin da zai nuna ta? Anya, bangaskiyar nan tāsa ta iya cetonsa? 15 Misali, in wani ɗan'uwa ko 'yar'uwa suna zaman huntanci, kullum kuma abinci bai wadace su ba, 16 waninku kuma ya ce musu, “To, ku sauka lafiya, Allah ya ba ci, da sha, da tufatarwa” ba tare da kun biya musu bukata ba, ina amfanin haka? 17 Haka ma, bangaskiya ita kaɗai, ba tare da aikin da ya nuna ta ba, banza ce. 18 To, amma wani zai ce, “Ai, kai kana da bangaskiya, ni kuwa sai aikatawa.” To, nuna mini bangaskiya, taka ba tare da aikatawa ba, ni kuma in nuna maka aikatawata, tabbatar bangaskiyata. 19 Ka gaskata Allah ɗaya ne? To, madalla. Ai, ko aljannu ma sun gaskata, amma suna rawar jiki don tsoro. 20 Kai marar azanci! Wato sai an nuna maka, bangaskiya ba tare da aikatawa ba, wofiya ce? 21 Sa'ad da kakanmu Ibrahim ya miƙa ɗansa Ishaku a bagadin hadaya, ashe, ba ta wurin aikatawa ne ya barata ba? 22 Ka gani, ashe, bangaskiyarsa da aikatawarsa duka yi aiki tare, har ta wurin aikatawar nan bangaskiyarsa ta kammala. 23 Aka kuma cika Nassin nan da ya ce, “Ibrahim ya gaskata Allah, bangaskiyar nan tasa kuma aka lasafta ta adalci ce a gare shi,” aka kuma kira shi aminin Allah. 24 Kun ga, ashe, Allah yana kuɓutar da mutum saboda aikatawarsa ne, ba saboda bangaskiya ita kaɗai ba. 25 Ashe, ba haka kuma Rahab karuwar nan ta sami kuɓuta saboda aikatawarta ba? Wato, sa'ad da ta sauki jakadun nan, ta fitar da su ta wata hanya dabam? 26 To, kamar yadda jiki ba numfashi matacce ne, haka ma bangaskiya ba aikatawa matacciya ce.

Yakubu 3

Ɓarnar Harshe

1 Ya ku 'yan'uwana, kada yawancinku su zama masu koyarwa, domin kun sani, mu da muke koyarwa za a yi mana shari'a da ƙididdiga mafi tsanani. 2 Domin dukanmu muna yin kuskure da yawa. In kuwa mutum ba ya shirme a maganarsa, to, shi cikakken mutum ne, yana kuwa iya kame duk sauran gaɓoɓinsa ma. 3 Ga misali, idan mun sa linzami a bakin doki, don mu bi da shi, mukan sarrafa dukan jikinsa ma. 4 Ku dubi jiragen ruwa kuma, ko da yake suna da girma haka ƙaƙƙarfar iska kuma tana kora su, duk da haka, da ɗan ƙaramin ƙarfe ne matuƙi yake juya su duk inda ya nufa. 5 Haka ma harshe yake, ga shi, ɗan ƙaramin abu ne, sai manyan fariya! Ku dubi yadda ɗan ƙaramin ƙyastu yake kunna wa babban jeji wuta! 6 Harshe ma wuta ne fa! A cikin duk gaɓoɓinmu, harshe shi ne tushen kowace irin mugunta, mai ɓata dukan jiki, mai zuga zuciyar mutum ta tafasa, shi kuwa Gidan Wuta ne yake zuga shi. 7 Don kuwa ana iya sarrafa kowace irin dabba, da tsuntsu, da masu jan ciki, da halittar ruwa, ɗan adam har yā sarrafa su ma, 8 amma ba ɗan adam ɗin da zai iya sarrafa harshe, ai, mugunta ne da ba ta hanuwa, a cike yake da dafi mai kashewa. 9 Da shi muke yabon Ubangiji Uba, da shi kuma muke zagin mutane waɗanda aka halitta da kamannin Allah. 10 Da baki ɗaya ake yabo, ake kuma zagi. 'Yan'uwana, ai, wannan bai kamata ba! 11 Ashe, marmaro ɗaya ya iya ɓuɓɓugowa da ruwan daɗi da na zartsi ta ido guda? 12 Ya 'yan'uwana, ashe, ɓaure yana iya haifar zaitun? Ko kuwa inabi ya haifi ɓaure? Haka kuma, ba dama a sami ruwan daɗi a idon ruwan zartsi.

Hikima Mai Saukowa daga Sama

13 Ina mai hikima da fahimi a cikinku? To, ta kyakkyawan zamansa sai ya nuna aikinsa da halin tawali'u da hikima suke sawa. 14 Amma in kuna da matsanancin kishi da sonkai a zuciyarku, kada ku yi alwashi da haka, kuna saɓa wa gaskiya. 15 Wannan hikima ba irin wadda take saukowa daga Sama ba ce, ta duniya ce, ta son zuciya, ta Shaiɗan kuma. 16 A duk inda kishi da sonkai suke, a nan hargitsi da kowane irin mugun aiki ma suke. 17 Amma hikimar nan ta Sama, da farko dai tsattsarka ce, mai lumana ce, saliha ce, mai sauƙin kai, mai tsananin jinƙai, mai yawan alheri, mai kaifi ɗaya, sahihiya kuma. 18 Daga irin salama wanda masu sulhuntawa suke shukawa akan girbe adalci.

Yakubu 4

Abuta da Duniya

1 Me yake haddasa gāba da husuma a tsakaninku? Ashe, ba sha'awace-sha'awacenku ne suke yaƙi da juna a zukatanku ba? 2 Kukan yi marmarin abu ku rasa, sai ku yi kisankai. Kukan yi kwaɗayi, ku kasa samu, sai ku yi husuma da faɗa. Kukan rasa don ba kwa addu'a ne. 3 Kukan yi addu'a ku rasa, don kun yi ta da mugun nufi ne, don ku ɓatar a kan nishaɗinku. 4 Maciya amana! Ashe, ba ku sani abuta da duniya gāba ce da Allah ba? Saboda haka, duk mai son abuta da duniya, yā mai da kansa mai gāba da Allah ke nan. 5 Ko kuna tsammani a banza ne Nassi ya ce, “Wannan ruhu da Allah ya sa a cikinmu yana tsaronmu ƙwarai?” 6 Allah shi yake yin mayalwacin alheri. Domin haka Nassi ya ce, “Allah yana gāba da masu girmankai, amma yana yi wa masu tawali'u alheri.” 7 Saboda haka, ku miƙa kanku ga Allah, ku yi tsayayya da Iblis, lalle kuwa zai guje muku. 8 Ku kusaci Allah, shi ma zai kusace ku. Ku tsarkake al'amuranku, ya ku masu zunubi. Ku kuma tsarkake zukattanku, ya ku masu zuciya biyu. 9 Ku yi nadama, ku yi baƙin ciki, ku yi ta kuka. Dariyarku tă zama baƙin ciki, murnarku tă koma ɓacin zuciya. 10 Ku ƙasƙantar da kanku ga Ubangiji, shi kuwa zai ɗaukaka ku.

Ɗora wa Ɗan'uwa Laifi

11 Ya ku 'yan'uwana, kada ku kushe wa juna. Kowa ya kushe wa ɗan'uwansa, ko ya ɗora masa laifi, ya kushe wa shari'a ke nan, ya kuma ɗora mata laifi. In kuwa ka ɗora wa shari'a laifi, kai ba mai binta ba ne, mai ɗora mata laifi ne. 12 Mai ba da Shari'a ɗaya ne, shi ne kuma mai yinta, shi ne kuwa mai ikon ceto da hallakarwa. To, kai wane ne har da za ka ɗora wa ɗan'uwanka laifi?

Kada a yi Fariya Saboda Gobe

13 To, ina musu cewa, “Yau ko gobe za mu je gari kaza, mu shekara a can, mu yi ta ciniki, mu ci riba?” 14 Alhali kuwa ba ku san abin da gobe za ta kawo ba. Wane iri ne ranku? Ai, kamar hazo yake, jim kaɗan sai ya ɓace. 15 Sai dai ya kamata ku ce, “In Ubangiji ya nufa, ya kai rai, ma yi kaza da kaza.” 16 Amma ga shi, kuna fariya ta alfarmar banza da kuke yi. Duk irin wannan fariya kuwa muguwar aba ce. 17 Saboda haka, duk wanda ya san abin da ya kamata, ya kuwa kasa yi, ya yi zunubi ke nan.

Yakubu 5

Faɗaka ga Masu Arziki

1 To, ina masu arziki? Ku yi ta kuka da kururuwa saboda baƙin ciki iri iri da za su aukar muku. 2 Arzikinku mushe ne! Tufafinku kuma duk cin asu ne! 3 Zinariyarku da azurfarku sun ɓāci ƙwarai, ɓācin nan nasu kuwa zai zama shaida a kanku, yă ci naman jikinku kamar wuta! Kun dai jibge dukiya a zamanin ƙarshen nan! 4 Ga shi kuwa, zaluncin da kuka yi na hakkin masu girbi a gonakinku yana ta ƙara, kukan masu girbin kuwa ya kai ga kunnen Ubangijin Runduna. 5 Kun yi zaman duniya da annashuwa da almubazzaranci, ashe, kiwata kanku kuka yi saboda ranar yanka! 6 Kun hukunta mai adalci, kun kuma kashe shi, bai kuwa yi muku tsayayya ba.

Haƙuri da Addu'a

7 Domin haka, sai ku yi haƙuri, 'yan'uwana, har ya zuwa ranar komowar Ubangiji. Ga shi, manomi yana sa rai ga samun amfanin gona mai albarka, yana kuwa haƙuri da samunsa, har a yi ruwan shuka da na kaka. 8 Ku ma sai ku yi haƙuri, ku tsai da zukatanku, domin ranar komowar Ubangiji ta yi kusa. 9 'Yan'uwa, kada ku yi wa juna gunguni, don kada a hukunta ku. Ga mai shari'a a bakin ƙofa! 10 A kan misalin shan wuya da haƙuri kuma, 'yan'uwa, ku dubi annabawa ma da suka yi magana da sunan Ubangiji. 11 Ga shi, mukan yaba wa waɗanda suka jure. Kun dai ji irin jimirin da Ayuba ya yi, kun kuma ga irin ƙarshen da Ubangiji ya yi masa, yadda Ubangiji yake mai yawan tausayi, mai jinƙai kuma. 12 Amma fiye da kome, 'yan'uwana, kada ku rantse sam, ko da sama, ko da ƙasa, ko da kowace irin rantsuwa ma. Sai dai in kun ce “I,” ya tsaya a kan “I” ɗin kawai, in kuwa kun ce “A'a,” ya tsaya a kan “A'a” ɗin kawai, don kada a hukunta ku. 13 In waninku yana shan wuya, to, sai ya yi addu'a, in kuma waninku yana murna, to, sai ya yi waƙar yabon Allah. 14 In waninku yana rashin lafiya, to, sai ya kira dattawan ikilisiya su yi masa addu'a, suna shafa masa mai da sunan Ubangiji. 15 Addu'ar bangaskiya kuwa, za ta warkar da marar lafiya Ubangiji kuma zai tashe shi, in ma ya yi zunubi, za a gafarta masa. 16 Saboda haka, sai ku riƙa bayyana wa juna laifofinku, kuna yi wa juna addu'a, don a warkar da ku. Addu'ar mai adalci tana da ƙarfin aiki ƙwarai da gaske. 17 Iliya ɗan adam ne kamarmu, amma da ya nace da addu'a kada a yi ruwa, sai da aka shekara uku da wata shida ba a yi ruwa a ƙasar ba. 18 Da ya sāke yin addu'a kuwa, sai sama ta sako ruwa, ƙasa kuma ta ba da amfaninta. 19 Ya ku 'yan'uwana, in waninku ya bauɗe wa gaskiya, wani kuma ya komo da shi, 20 to, yă dai tabbata, kowa ya komo da mai zunubi a hanya daga bauɗewarsa, ya kuɓutar da ran mai zunubin nan ke nan daga mutuwa, ya kuma rufe ɗumbun zunubansa.

1 Bitrus 1

Gaisuwa

1 Daga Bitrus, manzon Yesu Almasihu, zuwa ga zaɓaɓɓun Allah da suke bare, a warwatse a Fantas, da Galatiya, da Kafadokiya, da Asiya, da kuma Bitiniya, 2 su da suke zaɓaɓɓu bisa ga rigyasanin Allah Uba, waɗanda Ruhu kuma ya tsarkake, domin su yi wa Yesu Almasihu biyayya, su kuma tsarkaka da jininsa. Alheri da salama su yawaita a gare ku.

Rayayyiyar Bege

3 Godiya ta tabbata a gare shi, shi wanda yake Allah da Uba na Ubangijinmu Yesu Almasihu, wanda ta wurin tsananin jinƙansa ya sāke haifuwarmu, domin mu yi rayayyen bege, ta wurin albarkacin tashin Yesu Almasihu daga matattu, 4 mu kuma sami gādo marar lalacewa, marar ɓāci, marar ƙarewa kuma, wanda aka keɓe muku a Sama, 5 wato, ku da ikon Allah yake kiyayewa ta wurin bangaskiyarku, domin samun ceton nan da aka shirya a bayyana a ƙarshen zamani. 6 A kan wannan ne kuke da matuƙar farin ciki, ko da yake da ɗan lokaci kwa yi baƙin ciki ta dalilin gwaje-gwaje iri iri. 7 Wannan kuwa domin a tabbatar da sahihancin bangaskiyarku ne (wadda ta fi zinariya daraja nesa, ita zinariya kuwa, ko da yake mai ƙarewa ce, akan jarraba ta da wuta), domin bangaskiyar nan taku tă jawo muku yabo da girma da ɗaukaka a bayyanar Yesu Almasihu. 8 Ko da yake ba ku taɓa ganinsa ba, kuna ƙaunarsa. Ko da yake ba kwa ganinsa a yanzu, duk da haka kuna gaskatawa da shi, kuna farin ciki matuƙa, wanda ya fi gaban ambato, 9 kuna samun ceton rayukanku, ta wurin sakamakon bangaskiyarku. 10 Annabawan da suka yi annabci a kan alherin da zai zama naku, sun tsananta bin diddigi a kan wannan ceto, 11 suna bincike ko wane ne, ko kuma wane lokaci ne, Ruhun Almasihu da yake a zuciyarsu yake ishara, sa'ad da ya yi faɗi a kan wuyar da Almasihu zai sha, da kuma ɗaukakar da take biye. 12 An dai bayyana musu, cewa ba kansu suke bauta wa ba, ku suke bauta wa, a game da abubuwan da masu yi muku bishara, ta ikon Ruhu Mai Tsarki, wanda aka aiko daga sama suka samar da ku a yanzu. Su ne kuwa abubuwan da mala'iku suke ɗokin gani.

Kira a yi Zaman Tsarki

13 Don haka, sai ku yi ɗamara, ku natsu, ku sa zuciyarku sosai a kan alherin da zai zo muku a bayyanan Yesu Almasihu. 14 Ku yi zaman 'ya'ya masu biyayya. Kada ku biye wa muguwar sha'awarku ta dā, ta lokacin jahilcinku. 15 Amma da yake wanda ya kira ku mai tsarki ne, ku ma kanku sai ku zama tsarkaka a cikin dukan al'amuranku. 16 Domin a rubuce yake cewa, “Sai ku zama tsarkaka domin ni mai tsarki ne.” 17 Da yake kuna kiransa Uba a wajen addu'a, shi da yake yi wa kowa shari'a gwargwadon aikinsa, ba zaɓe, sai ku ƙarasa lokacin baƙuncinku, kuna tsoronsa. 18 Domin kun sani an fanshe ku ne daga al'adunku na banza da wofi da kuka gāda, ba da abubuwa masu lalacewa kamar azurfa da zinariya ba, 19 sai dai da jinin nan mai daraja na Almasihu, kamar na ɗan rago marar naƙasa, marar tabo. 20 An rigyasaninsa a kan haka, tun ba a halicci duniya ba, amma saboda ku ne aka bayyana shi a zamanin ƙarshe. 21 To gare shi ne kuka gaskata da Allah, wanda ya ta da shi daga matattu, ya kuma ɗaukaka shi, domin bangaskiyarku da begenku su kasance ga Allah. 22 Da yake kun tsarkake ranku kuna yi wa gaskiya biyayya har kuna nuna sahihiyar ƙauna ga 'yan'uwa, sai ku himmantu ga ƙaunar juna da zuciya ɗaya. 23 Gama sāke haifuwarku aka yi, ba ta iri mai lalacewa ba, sai dai marar lalacewa, wato, ta Maganar Allah rayayyiya dawwamammiya. 24 Domin “Duk ɗan adam kamar ciyawa yake, Duk darajarsa kamar furen ciyawa take, Ciyawar takan bushe, furen yakan kaɗe, 25 Maganar Ubangiji kuwa dawwamammiya ce,” Ita ce maganar bishara da aka yi muku.

1 Bitrus 2

Rayayyen Dutse da Kabila Tsattsarka

1 Saboda haka, sai ku yar da kowace irin ƙeta, da ha'inci, da munafunci, da hassada, da kuma kowane irin kushe. 2 Kamar jariri sabon haihuwa, ku yi marmarin shan madara marar gami mai ruhu, domin ku girma da shi, har ya kai ku ga samun ceto, 3 in dai kun ɗanɗana alherin Ubangiji. 4 Ku zo a gare shi, rayayyen dutsen nan, hakika abin ƙi ne a gun mutane, amma zaɓaɓɓe, ɗaukakakke a gun Allah. 5 Ku kuma, kamar rayayyun duwatsu, bari a gina gida mai ruhu da ku, domin ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, da nufin ku miƙa hadayu na ruhu, abin karɓa ga Allah, ta wurin Yesu Almasihu, 6 Domin a tabbace yake a Nassi cewa, “Ga shi, na sa mafificin dutsen a gini a Sihiyona, zaɓaɓɓe, ɗaukakakke, Duk mai gaskatawa da shi kuwa, ba zai kunyata ba.” 7 A gare ku, ku da kuka ba da gaskiya kuwa, shi ɗaukakakke ne. Amma ga waɗanda suka ƙi gaskatawa, to, “Dutsen da magina suka ƙi, Shi ne ya zama mafificin dutsen gini,” 8 Da kuma, “Dutsen sa tuntuɓe, Da fā na sa faɗuwa.” Sun yi tuntuɓe ne da maganar, don sun ƙi biyayya da ita. Haka kuwa aka ƙaddaro musu. 9 Amma ku kabila ce zaɓaɓɓiya, ƙungiyar firistocin babban Sarki, tsattsarkar al'umma, jama'ar mallakar Allah, domin ku sanar da mafifitan al'amuran wannan da ya kirawo ku daga cikin duhu, kuka shiga maɗaukakin haskensa. 10 Dā ba jama'a ɗaya kuke ba, amma a yanzu, ku jama'ar Allah ce. Dā ba ku sadu da jinƙansa ba, amma a yanzu kun sadu da shi.

Ku yi Zaman Bayin Allah

11 Ya ƙaunatattuna, ina roƙonku don ku baƙi ne, bare kuma, ku guje wa mugayen sha'awace-sha'awace na halin mutuntaka waɗanda suke yaƙi da zuciyarku. 12 Ku yi halin yabo a cikin al'ummai, don duk sa'ad da suke kushenku, cewa ku mugaye ne, sai su ga kyawawan ayyukanku, har su ɗaukaka Allah a ran da alheri ya sauko musu. 13 Ku yi biyayya ga kowace hukumar mutane saboda Ubangiji, ko ga sarki, domin shi ne shugaba, 14 ko kuwa ga mahukunta, domin su ne ya a'aika su hori mugaye, su kuma yabi masu kirki. 15 Domin nufin Allah ne ku toshe jahilcin marasa azanci ta yin aiki nagari. 16 Ku yi zaman 'yanci, sai dai kada ku fake a bayan 'yancin nan naku, ku yi mugunta. Amma ku yi zaman bayin Allah. 17 Ku girmama kowa, ku ƙaunaci 'yan'uwa, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.

Koyi da Wahalar Almasihu

18 Ku barori, ku bi iyayen gidanku da matuƙar ladabi, ba sai na kirki da masu sanyin hali kaɗai ba, har ma da miskilai. 19 Ai, abin karɓa ne, in saboda mutum yana sane da nufin Allah, ya jure wa wuyar da yake sha, ba da alhakinsa ba. 20 To, ina abin taƙama don kun yi haƙuri in kun sha d�ka a kan laifin da kuka yi? Amma, in kun yi aiki nagari kuka sha wuya a kansa, kuka kuma haƙura, to shi ne abin karɓa ga Allah. 21 Domin a kan haka ne musamman aka kira ku. Gama Almasihu ma ya sha wuya dominku, ya bar muku gurbi ku bi hanyarsa. 22 Bai yaɓa yin laifi ba faufau, ba a kuwa taɓa jin yaudara a bakinsa ba. 23 Da aka zage shi bai rama ba, da ya sha wuya kuma bai yi kashedi ba, sai dai ya dogara ga mai shari'ar adalci. 24 Shi kansa zunubanmu a jikinsa a kan gungume, domin mu yi zamanmu matattu ga zunubi, rayayyu kuma ga adalci. Da raunukansa ne aka warkar da ku. 25 A dā kun ɓăce kamar tumaki, amma a yanzu kun dawo ga Makiyayi, wato mai kula da rayukanku.

1 Bitrus 3

Hakkin Aure

1 Haka kuma, ku matan aure, ku yi biyayya ga mazanku, don ko waɗansunsu ba su bi maganar Allah ba, halin matansu yă shawo kansu, ba tare da wata magana ba, 2 don ganin tsarkakakken halinku da kuma ladabinku. 3 Kada adonku ya zama na kwalliyar kitso, da kayan zinariya, ko tufafi masu ƙawa, 4 sai dai ya zama na hali, da kuma kyan nan marar dushewa na tawali'u da natsuwa. Wannan kuwa abu ne mai martaba ƙwarai a gun Allah. 5 Don dā ma haka tsarkakan mata masu dogara ga Allah suka yi ado, suka bi mazansu, 6 kamar yadda Saratu ta bi Ibrahim, tana kiransa ubangijinta. Ku kuma 'ya'yanta ne muddin kuna aiki nagari, ba kwa yarda wani abu ya tsorata ku. 7 Haka kuma, ku maza, ku yi zaman ɗa'a da matanku, kuna girmama su, da yake su ne raunana, gama ku abokan tarayya ne na Allah. Ku yi haka don kada wani abu ya hana ku yin addu'a tare.

Shan Wuya don Adalci

8 Daga ƙarshe kuma dukanku ku haɗa hankulanku, ku zama masu juyayi, masu ƙaunar 'yan'uwa, masu tausayi, da kuma masu tawali'u. 9 Kada ku rama mugunta da mugunta, ko zagi da zagi, a maimakon haka, sai ku sa albarka. Domin a kan haka ne musamman aka kira ku, ku kuma gaji albarka. 10 Domin, “Duk mai so ya more wa zamansa na duniya da alheri, Sai ya kame bakinsa daga ɓarna, Ya kuma hana shi maganar yaudara. 11 Ya rabu da mugunta, ya kama nagarta, Ya himmantu ga zaman lafiya, ya kuma dimance ta. 12 Gama Ubangiji yana lura da masu aikata adalci, Yana kuma sauraron roƙonsu. Amma Ubangiji yana gāba da masu aikata mugunta.” 13 To, wa zai cuce ku in kun himmantu a kan abin da yake nagari? 14 Amma ko da za ku sha wuya saboda aikata abin da yake daidai, ku masu albarka ne. Kada ku ji tsoronsu, kada kuma ku damu. 15 Sai dai ku girmama Almasihu a zukatanku da hakikancewa, shi Ubangiji ne. Kullum ku zauna a shirye ku ba da amsa ga duk wanda ya tambaye ku dalilin begen nan naku, amma fa da tawali'u da bangirma. 16 Ku kuma kasance da lamiri mai kyau, don in an zage ku, waɗanda suka kushe kyakkyawan halinku na bin Almasihu su kunyata. 17 Zai fi kyau a sha wuya ga yin abin da yake nagari, in haka nufin Allah ne, da a sha don yin abin da ba daidai ba. 18 Domin Almasihu ma ya mutu sau ɗaya tak ba ƙari, domin kawar da zunubanmu, mai adalci saboda marasa adalci, domin ya kai mu ga Allah. An kashe shi a jiki, amma an rayar da shi a ruhu. 19 Da ruhun ne kuma ya je ya yi wa ruhohin da suke a kurkuku shela, 20 wato, waɗanda dā ba su bi ba, sa'ad da Allah ya yi jira da haƙuri a zamanin Nuhu, a lokacin sassaƙar jirgin nan, wanda a cikinsa mutane kaɗan, wato takwas suka kuɓuta ta ruwa. 21 Baftisma kuwa, wadda ita ce kwatancin wannan, ta cece ku a yanzu, ba ta fitar da dauɗa daga jiki ba, sai dai ta wurin roƙon Allah da lamiri mai kyau, ta wurin tashin Yesu Almasihu daga matattu, 22 wanda ya tafi Sama, yake dama ga Allah kuma, mala'iku da manyan mala'iku da masu iko suna binsa.

1 Bitrus 4

Amintaccen Mai Riƙon Amanar Alherin Allah

1 Tun da yake Almasihu ya sha wuya a jiki dominmu, sai ku ma ku ɗauki irin wannan ra'ayi. Ai, duk wanda ya sha wuya a jiki, ya daina aikata zunubi ke nan, 2 domin a nan gaba yă ƙarasa sauran zamansa na jiki ba tare da biye wa muguwar sha'awar zuciya ba, sai dai nufin Allah. 3 Lalle zaman da kuka yi na dā, irin wanda al'ummai suke son yi, ya isa haka nan, wato zaman fajirci, da mugayen sha'awace-sha'awace, da buguwa, da shashanci, da shaye-shaye, da kuma bautar gumaka, abar ƙyama. 4 Suna mamaki da ba kwa haɗa kai da su a yanzu, kuna zarmewa, kuna aikata masha'a irin tasu, har suna zaginku. 5 Amma lalle su ba da hujjojinsu ga wannan da yake a shirye ya yi wa rayayyu da matattu shari'a. 6 Shi ya sa aka yi bishara har ga matattu ma, waɗanda ko da yake an yi musu hukunci a cikin jiki kamar mutane, su samu su rayu a ruhu kamar Allah. 7 Ƙarshen dukan abubuwa ya gabato. Saboda haka, sai ku kanku, ku natsu, domin ku yi addu'a. 8 Fiye da kome kuma, ku himmantu ga ƙaunar juna, domin ƙauna takan yafe laifofi masu ɗumbun yawa. 9 Ku riƙa yi wa juna baƙunta, ba tare da ƙunƙuni ba. 10 Duk baiwar da mutum ya samu, yă yi amfani da ita ga kyautata wa ɗan'uwansa, a kan amintaccen mai riƙon amanar alherin Allah iri iri ne. 11 Duk mai wa'azi yă dai san faɗar Allah yake yi. Duk mai yin hidima, yă yi da ƙarfin da Allah ya ba shi, domin a cikin al'amura duka a ɗaukaka Allah ta wurin Yesu Almasihu. Ɗaukaka da mulki sun tabbata a gare shi har abada abadin. Amin! Amin!

Shan Wuyar Kirista

12 Ya ƙaunatattuna, kada ku yi mamakin matsananciyar wahalar da ta same ku a kan gwaji, kamar wani baƙon abu ne yake faruwa a gare ku. 13 Amma, muddin kuna tarayya da Almasihu a wajen shan wuyarsa, sai ku yi farin ciki, domin sa'ad da aka bayyana ɗaukakarsa, ku yi farin ciki da murna matuƙa. 14 Albarka ta tabbata a gare ku in ana zaginku saboda sunan Almasihu, don Ruhun ɗaukaka, wato Ruhun Allah yā tabbata a gare ku. 15 Sai dai kada shan wuyar ko ɗaya daga cikinku ya zama na horon laifin kisankai ne, ko na sata, ko na mugun aiki, ko kuma na shisshigi. 16 Amma in wani ya sha wuya a kan shi Kirista ne, to, kada ya ji kunya, sai dai ya ɗankaka Allah saboda wannan suna. 17 Don lokaci ya yi da za a fara shari'a ta kan jama'ar Allah. In kuwa ta kanmu za a fara, to, me zai zama ƙarshen waɗanda ba su bi bisharar Allah ba? 18 “In adali da ƙyar ya kuɓuta, Me zai auku ga marar bin Allah da mai zunubi?” 19 Saboda haka, sai duk masu shan wuya bisa ga nufin Allah su danƙa ransu ga Mahalicci mai aminci suna aikata abin da yake daidai.

1 Bitrus 5

Ku yi Kiwon Garken Allah

1 Don haka, ku dattawan ikilisiya da suke cikinku, ni da nike dattijon ikilisiya, ɗan'uwanku, mashaidin shan wuyar Almasihu, mai samun rabo kuma a cikin ɗaukakar da za a bayyana, ina yi muku gargaɗi, 2 ku yi kiwon garken Allah da yake tare da ku, ba a kan tilas ba, sai dai a kan yarda, ba ma don neman ribar banza ba, sai dai da himma. 3 Kada ku nuna wa waɗanda ke hannunka iko, sai dai ku zama abin koyi ga garken nan. 4 Sa'ad da kuma Sarkin Makiyaya ya bayyana, za ku sami kambin ɗaukaka marar dusashewa. 5 Hakanan ku masu ƙuruciya, ku yi biyayya ga dattawan ikilisiya. Dukanku ku yi wa kanku ɗamara da tawali'u, kuna bauta wa juna, gama “Allah yana gāba da masu girmankai, amma yana wa masu tawali'u alheri.” 6 Don haka, sai dai ku ƙasƙantar da kanku ga maɗankakin ikon Allah, domin ya ɗaukakaku a kan kari. 7 Ku jibga masa dukan taraddadinku, domin yana kula da ku. 8 Ku natsu, ku kuma zauna a faɗake. Magabcinku Iblis yana zazzāgawa kamar zaki mai ruri, yana neman wanda zai lanƙwame. 9 Ku yi tsayayya da shi, kuna dagewa a kan bangaskiyarku, da yake kun san 'yan'uwanku a duniya duka an ɗora musu irin wannan shan wuya. 10 Bayan kun sha wuya kuma ta ɗan lokaci kaɗan, Allah mai alheri duka, wanda ya kira ku ga samun madawwamiyar ɗaukakarsa a cikin Almasihu, shi kansa zai kammala ku, ya kafa ku, ya kuma ƙarfafa ku. 11 Mulki yā tabbata a gare shi har abada abadin. Amin! Amin!

Gaisuwa

12 Na rubuto muku wasiƙar nan a taƙaice ta hannun Sila, ɗan'uwa mai aminci, a yadda na ɗauke shi, domin in yi muku gargaɗi, in kuma sanar da ku, cewa wannan shi ne alherin Allah na gaske, ku tsaya a gare shi da ƙarfi. 13 Ita da take a Babila, wadda ita ma zaɓaɓɓiya ce, ta aiko muku da gaisuwa. Haka kuma, ɗana, Markus. 14 Ku gai da juna da sumbar ƙauna. Salama tă tabbata a gare ku duka, ku na Almasihu.

2 Bitrus 1

Gaisuwa

1 Daga Saminu Bitrus, bawan Yesu Almasihu, manzonsa kuma, zuwa ga waɗanda aka yi wa baiwar bangaskiya mai daraja iri ɗaya da tamu, albarkacin adalcin Allahnmu da Mai Cetonmu Yesu Almasihu. 2 Alheri da salama su yawaita a gare ku, a wajen sanin Allah da Yesu Ubangijinmu

Kiranku da Zaɓenku

3 Allah da ikonsa yā yi mana baiwa da dukan abubuwan da suka wajaba ga rayuwa da kuma binsa, ta sanin wanda ya kira mu ga samun ɗaukakarsa da fifikonsa, 4 waɗanda kuma ta wurinsu ya yi mana baiwa da manyan alkawaransa masu ɗaukaka ƙwarai, domin ta wurin waɗannan ku zama masu tarayya da Allah a wajen ɗabi'arsa, da yake kun tsira daga ɓācin nan dake a duniya da muguwar sha'awa take haifa. 5 Saboda wannan dalili musamman, sai ku yi matuƙar himma, ku ƙara bangaskiyarku da halin kirki, halin kirki da sanin ya kamata, 6 sanin ya kamata da kamunkai, kamunkai da jimiri, jimiri da bin Allah, 7 bin Allah da son 'yan'uwa, son 'yan'uwa kuma da ƙauna. 8 In kuwa halayen nan sun zama naku ne, har suna yalwata, za su sa ku kada ku yi zaman banza, ko marasa amfani a wajen sanin Ubangijinmu Yesu Almasihu. 9 Domin duk wanda ya rasa halayen nan, to, makaho ne ko kuwa ganinsa dishi-dishi ne, ya kuma mance an tsarkake shi daga zunubansa na dā. 10 Saboda haka, ya ku 'yan'uwa, ku ƙara ba da himma ku tabbatar da kiranku da zaɓenku da aka yi. Domin in kun bi waɗannan halaye, ba za ku fādi ba har abada. 11 Ta haka kuma, za a ba ku cikakken 'yancin shiga madawwamin mulki na Ubangijinmu Mai Cetonmu Yesu Almasihu. 12 Don haka, lalle kullum ba zan fasa yi muku tunin waɗannan abubuwa ba, ko da yake kun san su, kun kuma kahu a kan gaskiyar nan da kuke da ita. 13 A ganina daidai ne, muddin ina raye a cikin jikin nan, in riƙa faɗakar da ku ta hanyar tuni, 14 da yake na sani na yi kusan rabuwa da jikin nan nawa, kamar yadda Ubangijinmu Yesu Almasihu ya yi mini ishara. 15 Aniyta ce, a kowane lokaci ku iya tunawa da waɗannan abubuwa bayan ƙauracewata.

Ganin Ɗaukakarsa Muraran

16 Ai, ba tatsuniyoyi da aka ƙaga da wayo muka bi ba, sa'ad da muka sanar da ku ikon Ubangijinmu Yesu Almasihu, da kuma bayyanarsa, ɗaukakarsa ce muka gani muraran. 17 Domin sa'ad da Allah Uba ya girmama shi, ya kuma ɗaukaka shi, sai murya ta zo masa daga mafificiyar ɗaukaka cewa, “Wannan shi ne Ɗana ƙaunataccena, wanda nake farin ciki da shi ƙwarai,” 18 mu ne muka ji muryar nan da aka saukar daga sama, don muna tare da shi a kan tsattsarkan Dutsen nan. 19 Har wa yau kuma, aka ƙara tabbatar mana da maganar annabcin nan, ya kuwa kyautu a gare ku, ku mai da hankali a gare ta, kamar fitila take mai haskakawa a wuri mai duhu har ya zuwa asubahin ranar nan, gamzaki kuma yă bayyana a zukatanku. 20 Da farko dai, lalle ne ku fahimci wannan cewa, ba wani annabci a Littattafai da za a iya fassarawa ta ra'ayin mutum. 21 Domin ba wani annabcin da ya taɓa samuwa ta nufin mutum, sai dai mutane ne Ruhu Mai Tsarki yake izawa, Allah yana magana ta bakinsu.

2 Bitrus 2

Annabawan Ƙarya da Malaman Ƙarya

1 Amma fa annabawan ƙarya sun bayyana a cikin jama'a, kamar yadda za a sami malaman ƙarya a cikinku, waɗanda za su saɗaɗo da maɓarnacciyar fanɗarewa, har mw su ƙi Mamallakin da ya fanso su, suna jawo wa kansu hallaka farat ɗaya. 2 Da yawa kuwa za su bi fajircinsu, har za a kushe hanyar gaskiya saboda su. 3 Mahaɗantan malaman nan na ƙarya za su ribace ku da tsararrun labarunsu. An riga an yanke hukuncinsu tun dā, wanda zai hallaka su a shirye yake sosai. 4 Da yake Allah bai rangwanta wa mala'iku ba sa'ad da suka yi zunubi, sai ya jefa su a Gidan Wuta, ya tura su a cikin ramummuka masu zurfi, masu baƙin duhu, a tsare su har ya zuwa ranar hukunci, 5 tun da yake bai ran gwanta wa mutanen tun can dā dā kuma ba, amma ya kiyaye Nuhu mai wa'azin adalci, da waɗansu mutum bakwai, sa'ad da ya aiko da Ruwan Tsufana zuwa a cikin duniyar nan ta marasa bin Allah, 6 da yake kuma ya mai da biranen Saduma da Gwamrata toka, ya yi musu hukuncin hallaka, ya mai da su abin ishara ga marasa bin Allah, 7 da yake kuma ya ceci Lutu adali, wanda fajircin kangararru ya baƙanta masa rai ƙwarai 8 (don kuwa abin da adalin nan ya yi, ya kuma gani, sa'ad da yake a cikinsu, sai kowace rana yakan ji ciwon aikinsu na kangara a zuciyarsa mai adalci), 9 ashe kuwa, Ubangiji ya san yadda zai kuɓutar da masu tsoronsa daga gwaje-gwaje, ya kuma tsare marasa adalci a kan jiran hukunci, har ya zuwa ranar shari'a, 10 tun ba waɗanda suka dulmuya a cikin muguwar sha'awa mai ƙazantarwa ba, suke kuma raina mulki. Masu tsaurin ido ne su, masu taurin kai kuma, ba sa jin tsoron zagin masu ɗaukaka. 11 Amma kuwa mala'iku, ko da yake sun fi su ƙarfi da iko, duk da haka, ba sa ɗora musu laifi da zage-zage a gaban Ubangiji. 12 Amma waɗannan mutane, kamar daddobi marasa hankali suke, masu bin abin da jikinsu ya ba su kawai, waɗanda aka haifa, don a kama a kashe, har suna kushen abubuwan da ba su fahinta ba, lalle kuwa za su hallaka a sanadin ɓacin nan nasu, 13 suna shan sakamakon muguntarsu. Sun ɗauka a kan jin daɗi ne a yi annashuwa da rana kata. Sun baƙanta, sun zama abin kunya. Sun dulmuya ga ciye-ciye da shaye-shaye, suna ta nishaɗi a cikinku. 14 Jarabar zina take a gare su, ba sa ƙoshi da yin zunubi. Suna yaudarar marasa kintsuwa. Sun ƙware da ƙwaɗayi. La'anannun iri! 15 Sun yar da miƙaƙƙiyar hanya, sun bauɗe, sun bi hanyar Bal'amu ɗan Beyor, wanda ya cika son samu ta hanyar mugunta. 16 Amma an tsawata masa a kan laifinsa, har dabba marar baki ma ta yi magana kamar mutum, ta kwaɓi haukan annabin nan. 17 Mutanen nan kamar mabubbugen ruwa wadanda suka kafe, ƙasashi ne da iska take kaɗawa. Su ne aka tanada wa matsanancin duhu. 18 Ta surutai barkatai marasa kan gado na ruba, da halinsu na fasikanci sukan shammaci waɗanda da ƙyar suke kuɓucewa daga masu zaman saɓo, 19 suna yi musu alkawarin 'yanci, ga shi kuwa, su da kansu bayin zamba ne. Don mutum bawa ne na duk abin da ya rinjaye shi. 20 In kuwa bayan da suka tsere wa ƙazantar duniyar albarkacin sanin Ubangijinmu, Mai Cetonmu Yesu Almasihu, suka kuma sāke sarƙafewa a ciki, har aka rinjaye su, ƙarshen zamansu ya fi na fari lalacewa ke nan. 21 Da ba su taɓa sanin hanyar adalci tun da fari ba, da ya fiye musu, bayan sun san ta, sa'an nan su juya ga barin umarnin nan mai tsarki. 22 Ai kuwa, karin maganar nan na gaskiya ya dace da su cewa, “Kare ya cinye amansa,” da kuma, “Gursunar da aka yi wa wanka ta kome ga birgima cikin laka.”

2 Bitrus 3

Alkawarin Zuwan Ubangiji

1 Ya ƙaunatattuna, wannan ita ce wasiƙa ta biyu da na rubuto muku, a kowaccensu kuwa na faɗakar da sahihan zukatanku ta hanyar tuni. 2 Ina so ku tuna da yin faɗin annabawa tsarkaka, da kuma umarnin Ubangiji Mai Ceto ta bakin manzannin da suka zo muku. 3 Da farko dai lalle ne ku fahimci wannan, cewa a can zamanin ƙarshe masu ba'a za su zo suna ba'a, suna biye wa muguwar sha'awarsu, 4 suna cewa, “To, ina alkawarin dawowarsa? Ai, tun a lokacin da kakannin kakanninmu suka ƙaura, dukan abubuwa suna tafe ne kamar dā, tun farkon halitta.” 5 Da gangan suke goce wa maganar nan, cewa tun dā dā ta wurin maganar Allah sammai suka kasance, aka kuma siffata ƙasa daga ruwa, tana kuma a tsakiyar ruwa. 6 Ta haka ne kuma, duniyar wancan zamani, ruwa ya sha kanta, ta hallaka. 7 Ta maganar Allah ne kuma sama da ƙasa da suke a nan a yanzu, aka tanada su ga wuta, ana ajiye su, har ya zuwa ranar nan da za a yi wa marasa bin Allah shari'a, a hallaka su. 8 Amma ya ku ƙaunatattuna kada ku goce wa magana gudar nan, cewa ga Ubangiji kwana ɗaya kamar shekara dubu ne, shekara dubu kuma kamar kwana ɗaya ne. 9 Ubangiji ba ya jinkirta alkawarinsa, yadda waɗansu suka ɗauki ma'anar jinkiri, amma mai haƙuri ne a gare ku, ba ya so kowa ya hallaka, sai dai kowa ya kai ga tuba. 10 Duk da haka, ranar Ubangiji za ta zo kamar ɓarawo, sa'an nan sammai za su shuɗe da ƙara mai tsanani, dukkan abin da yake a cikinsu za su ƙone, su hallaka, ƙasa kuma da abubuwan da suke a kanta, duk za su ɓăce. 11 Tun da yake duk abubuwan nan za a hallaka su haka, waɗanne irin mutane ya kamata ku zama? Ya kamata ku yi zaman tsarkaka masu ibada, 12 kuna sauraron ranar Allah, kuna gaggauta zuwanta! Da zuwanta kuwa za a kunna wa sammai wuta, su hallaka, dukkan abubuwa kuma da suke a cikinsu, wuta za ta narkar da su. 13 Amma bisa ga alkawarinsa muna jiran sababbin summai da sabuwar ƙasa a inda adalci zai yi zamansa. 14 Saboda haka, ya ƙaunatattuna, tun da kuke jiran waɗannan abubuwa, ku himmantu ya same ku marasa tabo, marasa aibu, masu zaman salama. 15 Ku ɗauki haƙurin Ubangijinmu, ceto ne. Haka ma, ƙaunataccen ɗan'uwanmu Bulus ya rubuto muku, bisa ga hikimar da aka ba shi, 16 yana magana a kan wannan, kamar yadda yake yi a dukan wasiƙunsa, akwai waɗansu abubuwa a cikin masu wuyar fahinta, waɗanda jahilai da marasa kintsuwa suke juya ma'anarsu, kamar yadda suke juya sauren Littattafai, ta haka suke jawo wa kansu hallaka. 17 Don haka, ya ku ƙaunatatuna, da yake kun riga kun san haka, ku kula kada bauɗewar kangararru ta tafi da ku, har ku fāɗi daga matsayinku. 18 Amma ku ƙaru da alherin Ubangijinmu, Mai Cetonmu Yesu Almasihu da kuma saninsa. Ɗaukaka tă tabbata a gare shi a yanzu, da kuma har abada. Amin! Amin!

1 Yahaya 1

Kalmar Rai

1 Shi da yake tun fil'azal yake nan, wanda muka ji, muka gani da idonmu, muka duba, hannuwanmu kuma suka taɓa, a game da Kalmar Rai, 2 wannan Rai kuwa an bayyana shi, mu kuwa mun gani, muna ba da shaida, muna kuma sanar da ku Rai madawwamin nan wanda tun dā yake tare da Uba, aka kuwa bayyana shi gare mu, 3 to, shi wannan da muka ji, muka kuma gani, shi ne dai muke sanar da ku, domin ku ma ku yi tarayya da mu. Hakika kuwa tarayyar nan tamu da Uba ne, da kuma Ɗansa Yesu Almasihu. 4 Muna kuma rubuto muku wannan ne domin farin cikinmu ya zama cikakke.

Allah Haske Ne

5 Wannan shi ne jawabin da muka ji a gunsa, muke sanar da ku cewa Allah haske ne, ba kuwa duhu gare shi ko kaɗan. 6 In mun ce muna tarayya da shi, alhali kuwa muna zaune a duhu, mun yi ƙarya ke nan, ba ma aikata gaskiya. 7 In kuwa muna zaune a haske, kamar yadda shi yake cikin haske, muna tarayya da juna ke nan, jinin Yesu Ɗansa kuma yana tsarkake mu daga dukkan zunubi. 8 In mun ce ba mu da zunubi, ruɗin kanmu muke yi, gaskiya kuwa ba ta tare da mu. 9 In kuwa muka bayyana zunubanmu, to, shi mai alkawari ne, mai adalci kuma, zai kuwa gafarta mana zunubanmu, ya tsarkake mu daga dukkan rashin adalci, 10 In mun ce ba mu yi zunubi ba, mun ƙaryata shi ke nan. Maganarsa kuma ba ta tare da mu.

1 Yahaya 2

Almasihu Mai Taimako gun Allah

1 Ya ku 'ya'yana ƙanana, ina rubuto muku wannan ne domin kada ku yi zunubi. In kuwa wani ya yi zunubi, muna da Mai Taimako a gun Uba, wato, Yesu Almasihu mai adalci. 2 Shi kansa kuwa shi ne hadayar sulhu saboda gafarta zunubanmu, ba kuwa namu kaɗai ba, har ma na duniya duka. 3 Ta haka za mu tabbata mun san shi, in dai muna bin umarninsa. 4 Kowa ya ce ya san shi, ba ya kuwa bin umarninsa, maƙaryaci ne, gaskiya kuma ba ta tare da shi. 5 Amma duk wanda yake kiyaye maganarsa, wannan kam, hakika yana ƙaunar Allah, cikakkiyar ƙauna. Ta haka muka tabbata muna cikinsa. 6 Kowa ya ce yana zaune a cikinsa, ya kamata shi kansa ma ya yi irin zaman da shi ya yi.

Sabon Umarni

7 Ya ku ƙaunatattuna, ba fa wani sabon umarni nake rubuto muku ba, a'a, daɗaɗɗen umarnin nan ne wanda kuke da shi tun farko. Daɗaɗɗen umarnin nan kuwa, ai, shi ne maganar da kuka ji. 8 Har wa yau sabon umarni nake rubuto muku, wanda yake tabbatacce ga Almasihu, da kuma gare ku, domin duhu yana shuɗewa, hakikanin haske kuma yana haskakawa. 9 Kowa ya ce yana a cikin haske, yana kuwa ƙin ɗan'uwansa, ashe, a duhu yake har yanzu. 10 Mai ƙaunar ɗan'uwansa, a haske yake zaune, ba kuma wani sanadin sa tuntuɓe a gare shi. 11 Mai ƙin ɗan'uwansa kuwa, a duhu yake, a cikin duhu yake tafiya, bai san ma inda yake sa ƙafa ba, domin duhun ya makantar da shi. 12 Ya ku 'ya'yana ƙanana, ina rubuto muku ne domin an gafarta muku zunubanku saboda sunansa. 13 Ya ku dattawa, ina rubuto muku ne domin kun san shi, shi wanda yake tun fil'azal. Ya ku samari, ina rubuto muku ne domin kun ci nasara a kan Mugun nan. Ya ku 'yan yara, ina rubuto muku ne domin kun san Uba. 14 Ya ku dattawa, na rubuto muku ne domin kun san shi, shi wanda yake tun fil'azal. Ya ku samari, na rubuto muku ne domin kuna da ƙarfi, Maganar Allah tana zauna a zuciyarku, kun kuma ci nasara a kan Mugun nan. 15 Kada ku ƙaunaci duniya, ko abin da yake a cikinta. Kowa ke ƙaunar duniya, ba ya ƙaunar Uba ke nan sam. 16 Don kuwa duk abin da yake duniya, kamar su sha'awa irin ta halin mutuntaka, da sha'awar ido, da kuma alfarmar banza, ba na Uba ba ne, na duniya ne. 17 Duniyar kuwa tana shuɗewa da mugayen burinta, amma mai aikata nufin Allah zai dawwama har abada.

Magabcin Almasihu

18 Ya ku 'yan yarana, zamanin ƙarshe ne fa. Kamar yadda kuka ji, magabcin Almasihu yana zuwa, ko a yanzu ma, magabtan Almasihu da yawa sun zo. Ta haka muka sani zamanin ƙarshe ne. 19 Sun dai fita daga cikinmu, amma dā ma can ba namu ba ne. Don in da namu ne, da har yanzu suna tare da mu. Amma sun fita ne domin a bayyana dukansu ba namu a ciki. 20 Ku kam, Mai Tsarkin nan ya shafe ku, dukanku kuma kun san gaskiya. 21 Ina rubuto muku, ba don ba ku san gaskiya ba ne, a'a, sai domin kun san ta, kun kuma sani gaskiya ba ta haifar ƙarya. 22 Wane ne maƙaryacin nan, in ba wanda ya m�sa Yesu shi ne Almasihu ba? Irin wannan shi ne magabcin Almasihu, shi wanda yake ƙin Uban da Ɗan. 23 Ba mai ƙin Ɗan ya sami Uban. Kowa ya bayyana yarda ga Ɗan, ya sami Uban ke nan. 24 Ku kam, abin da kuka ji tun da farko, sai ya zauna a zuciyarku. In abin da kuka ji tun farko ya zauna a zuciyarku, ku ma sai ku zauna cikin Ɗan, da kuma Uban. 25 Wannan shi ne alkawarin da ya yi mana, wato, rai madawwami. 26 Ina rubuto muku wannan ne a kan waɗanda suke ƙoƙarin ɓad da ku. 27 Ku kam, shafar nan da kuka samu daga Ruhu Mai Tsarki tā tabbata a zuciyarku, ba sai wani ya koya muku ba. Amma kamar yadda shafar nan tasa ke koya muku kome, ita kuwa gaskiya ce ba ƙarya ba, yadda dai ta koya muku, to, sai ku zauna a cikinsa. 28 To a yanzu, ya ku 'ya'yana ƙanana, sai ku zauna cikinsa, domin sa'ad da ya bayyana, mu kasance da amincewa, kada kunya ta rufe mu a gabansa a ranar komowarsa. 29 Da yake kun san shi mai adalci ne, ku dai tabbata duk mai aikata adalci haifaffensa ne.

1 Yahaya 3

'Ya'yan Allah

1 Ku dubi irin ƙaunar da Uba ya nuna mana, har yake ce da mu 'ya'yan Allah, haka kuwa muke. Abin da ya sa duniya ba ta san mu ba, don ba ta san shi ba ne. 2 Ya ku ƙaunatattuna, a yanzu mu 'ya'yan Allah ne, yadda za mu zama nan gaba kuwa, ba a bayyana ba tukuna, amma mun sani sa'ad da ya bayyana, za mu zama kamarsa, domin za mu gan shi kamar yadda yake. 3 Duk mai ƙwallafa sa zuciya gare shi haka, yana tsarkake kansa ke nan, kamar yadda shi yake Mai Tsarki. 4 Duk mai aikata zunubi ya yi tawaye ke nan. Zunubi tawaye ne. 5 Kun dai sani an bayyana shi domin yă ɗauke zunubai ne, a gare shi kuma ba zunubi. 6 Kowa da yake a zaune a cikinsa, ba ya aikata zunubi. Kowa da yake aikata zunubi, bai taɓa ganinsa ba, bai ma san shi ba. 7 Ya ku 'ya'yana ƙanana, kada fa kowa ya ɓad da ku. Shi wanda yake aikata adalci, mai adalci ne, kamar yadda Almasihu mai adalci ne. 8 Duk mai aikata zunubi, na Iblis ne, don tun farko Iblis mai aikata zunubi ne. Dalilin bayyanar Ɗan Allah shi ne domin yă rushe aikin Iblis. 9 Duk wanda yake haifaffen Allah, ba yakan aikata zunubi ba, domin irinsa yana a cikinsa a zaune, ba yakan aikata zunubi ba, da yake shi haifaffen Allah ne. 10 Ta haka sai a ga waɗanda suke 'ya'yan Allah, da kuma waɗanda suke 'ya'yan Iblis, wato duk wanda ba ya aikata adalci, ba na Allah ba ne, haka kuma wanda ba ya ƙaunar ɗan'uwansa.

Ku Ƙaunaci Juna

11 Wannan shi ne jawabin da kuka ji tun farko, cewa dai mu ƙaunaci juna, 12 kada mu zama kamar Kayinu, wanda yake na Mugun, har ma ya kashe ɗan'uwansa. To, don me ya kashe shi? Don ayyukansa mugaye ne, na ɗan'uwansa kuwa na kirki ne. 13 Kada ku yi mamaki, 'yan'uwa, idan duniya take ƙinku. 14 Mu kam, mun sani mun riga mun tsere wa mutuwa, mun kai ga rai saboda muna ƙaunar 'yan'uwa. Wanda ba shi da ƙauna, zaman mutuwa yake yi. 15 Kowa da yake ƙin dan'uwansa, mai kisankai ne. Ƙun kuwa sani ba mai kisankan da yake da rai madawwami a zauna tare da shi. 16 Yadda muka san ƙauna ke nan, wato, ta wurin ba da ransa da ya yi saboda mu. Mu kuma ya kamata mu ba da ranmu saboda 'yan'uwa. 17 Duk kuwa wanda yake da abin hannunsa, yake kuma ganin ɗan'uwansa da rashi, sa'an nan ya rufe ido gare shi, ƙaƙa ƙaunar Allah yake zaune a cikinsa? 18 Ya ku 'ya'yana ƙanana, kada mu nuna ƙauna da fatar baki kawai, sai dai da aikatawa da kuma gaskiya.

Amincewa gaban Allah

19 Ta haka za mu tabbata mu na gaskiya ne, har kuma mu amince wa kanmu gaban Allah, 20 duk sa'ad da zuciyarmu ta ba mu laifi, saboda Allah ya fi ta, ya kuma san kome. 21 Ya ku ƙaunatattuna, in zuciyarmu ba ta ba mu laifi ba, sai mu je gaban Allah amincewa. 22 Mukan kuma sami duk abin da muka roƙa a gare shi, domin muna bin umarninsa, muna kuma yin abin da yake so. 23 Umarninsa kuwa shi ne mu gaskata da sunan Ɗansa Yesu Almasihu, mu kuma ƙaunaci juna, kamar yadda ya umarce mu. 24 Duk mai bin umarnin Allah kuwa a dawwame yake cikinsa, Allah kuma a cikinsa. Ta haka muka tabbata ya dawwama a cikinmu, saboda Ruhun da ya ba mu.

1 Yahaya 4

Ruhun Allah da na Magabci

1 Ya ku ƙaunatattuna, ba kowane ruhu za ku gaskata ba, sai dai ku jarraba ku gani ko na Allah ne, don annabawan ƙarya da yawa sun fito duniya. 2 Ta haka za ku san Ruhun Allah, wato, duk ruhun da ya bayyana yarda, cewa Yesu Almasihu ya bayyana ne da jiki, shi ne na Allah. 3 Duk ruhun kuwa da bai bayyana yarda ga Yesu ba, ba na Allah ba ne, wannan shi ne ruhun magabcin nan na Almasihu wanda kuka ji zai zo, a yanzu ma har yana duniya. 4 Ya ku 'ya'yana ƙanana, ku kam na Allah ne, kun kuma ci nasara a kan waɗannan, domin shi wanda yake zuciyarku ya fi wanda yake duniya ƙarfi. 5 Su kuwa na duniya ne, shi ya sa suke zance irin na duniya, duniya kuwa tana sauraronsu. 6 Mu kam na Allah ne. Duk wanda ya san Allah yakan saurare mu, wanda yake ba na Allah ba kuwa, ba ya sauraronmu. Ta haka muka san Ruhu na gaskiya da ruhu na ƙarya.

Allah Ƙauna Ne

7 Ya ku ƙaunatattuna, sai mu ƙaunaci juna, domin ƙauna ta Allah ce. Duk mai ƙauna kuwa haifaffen Allah ne, ya kuma san Allah. 8 Wanda ba ya ƙauna, bai san Allah ba sam, domin Allah shi ne ƙauna. 9 Ta haka aka bayyana ƙaunar Allah gare mu, da Allah ya aiko da Ɗansa makaɗaici a duniya, domin mu sami rai madawwami ta wurinsa. 10 Ta haka ƙauna take, wato, ba mu ne muka ƙaunaci Allah ba, sai dai shi ne ya ƙaunace mu, ya aiko Ɗansa, hadayar sulhu saboda a gafarta zunubanmu. 11 Ya ku ƙaunatattuna, tun da ya ke Allah ya ƙaunace mu haka, ai, mu ma ya kamata mu ƙaunaci juna. 12 Ba mutumin da ya taɓa ganin Allah daɗai, amma kuwa in muna ƙaunar juna sai Allah ya dawwama cikinmu, ƙaunar nan tasa kuma tă cika a cikinmu. 13 Ta haka muka sani muna a zaune a cikinsa, shi kuma a cikinmu, saboda Ruhunsa da ya ba mu. 14 Mun duba, muna kuma ba da shaida, cewa Uba ya aiko Ɗan ya zama Mai Ceton duniya. 15 Kowa ya bayyana yarda, cewa Yesu Ɗan Allah ne, sai Allah yă dawwama a cikinsa, shi kuma a cikin Allah. 16 Mun sani, mun kuma gaskata ƙaunar da Allah yake yi mana. Allah shi ne ƙauna wanda yake a dawwame cikin kauna kuwa, ya dawwama a cikin Allah ke nan, Allah kuma a cikinsa. 17 Ta haka ne ƙauna ta cika a gare mu, har mu kasance da amincewa a ranar shari'a, domin kamar yadda yake, haka mu ma muke a duniyar nan. 18 Ba tsoro ga ƙauna, amma cikakkiyar ƙauna takan yaye tsoro. Tsoro kansa ma azaba ne, mai jin tsoro kuwa ba shi da cikakkiyar ƙauna, 19 Muna ƙauna, domin shi ne ya fara ƙaunarmu. 20 Kowa ya ce yana ƙaunar Allah, alhali kuwa yana ƙin dan'uwansa, to, maƙaryaci ne. Don wanda ba ya ƙaunar ɗan'uwansa da ya ke gani, ba dama ya ƙaunaci Allah wanda bai taɓa gani ba. 21 Wannan kuma shi ne umarnin da muka samu daga gare shi, cewa mai ƙaunar Allah, sai ya ƙaunaci ɗan'uwansa kuma.

1 Yahaya 5

Bangaskiya ta yi Nasara da Duniya

1 Kowa da yake gaskata Yesu shi ne Almasihu, haifaffen Allah ne. Kowa ke ƙaunar mahaifi kuwa, yana ƙaunar ɗa kuma. 2 Ta haka muku sani muna ƙaunar 'ya'yan Allah, wato, in muna ƙaunar Allah, muna kuma bin umarninsa. 3 Domin ƙaunar Allah ita ce mu bi umarninsa, umarninsa kuwa ba matsananta ba ne. 4 Domin duk wanda yake haifaffen Allah yana nasara da duniya. Bangaskiyarmu kuwa ita ce ta sa muka yi nasara da duniya. 5 Wane ne yake nasara da duniya, in ba wanda ya gaskata Yesu Ɗan Allah ba ne?

Shaida a kan Ɗansa

6 Shi ne wanda ya bayyana ta wurin ruwa da jini, Yesu Almasihu, ba fa ta wurin ruwa kaɗai ba, amma ta wurin ruwa da jini. 7 Ruhu kuma shi ne mai ba da shaida, domin Ruhun shi ne gaskiya. 8 Akwai shaidu uku, wato Ruhun, da ruwa, da kuma jini, waɗannan uku kuwa manufarsu ɗaya ce. 9 Tun da yake muna yarda da shaida mutane, ai, shaidar Allah ta fi ƙarfi. Wannan ita ce shaidar Allah, wato, ya shaidi Ɗansa. 10 Kowa ya gaskata da Ɗan Allah, shaidar tana nan gare shi. Wanda bai gaskata Allah ba, ya ƙaryata shi ke nan, domin bai gaskata shaidar da Allah ya yi Ɗansa ba. 11 Wannan kuma ita ce shaidar, cewa Allah yā ba mu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Ɗansa. 12 Duk wanda yake da Ɗan, yana da rai. Wanda ba shi da Ɗan Allah kuwa, ba shi da rai.

Tabbatar Samun Rai Madawwami

13 Na rubuto muku wannan ne, ku da kuka gaskata da sunan Ɗan Allah, domin ku tabbata kuna da rai madawwami. 14 Wannan ita ce amincewarmu a gabansa, wato, in mun roƙi kome bisa ga nufinsa, sai ya saurare mu. 15 In kuwa muka san kome muka roƙa yana sauraronmu, mun tabbata mun sami abin da muka roƙa a gare shi ke nan. 16 Kowa ya ga ɗan'uwansa yana yin zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai ya yi masa addu'a. Saboda mai addu'ar nan kuwa, Allah zai ba da rai ga waɗanda suka yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yake na mutuwa. Ban ce a yi addu'a domin wannan ba. 17 Duk rashin adalci zunubi ne. Akwai kuma zunubin da ba na mutuwa ba. 18 Mun sani kowane haifaffen Allah ba ya yin zunubi, kasancewarsa haifaffen Allah ita takan kare shi. Mugun nan kuwa ba ta taɓa shi. 19 Mun sani mu na Allah ne, duniya duka kuwa tana hannun Mugun. 20 Mun kuma sani Ɗan Allah ya zo, ya yi mana baiwar fahimta domin mu san shi wanda yake na gaskiya. Mu kuwa muna a cikinsa, shi da yake na gaskiya, wato Ɗansa Yesu Almasihu. Shi ne Allah na gasikya da kuma rai madawwami. 21 Ya ku 'ya'yana ƙanana, ku yi nesa da gumaka.

2 Yahaya 1

Gaisuwa

1 Daga dattijon nan na ikilisiya zuwa ga uwargida zaɓaɓɓiya, da 'ya'yanta waɗanda nake ƙauna da gaske, ba kuwa ni kaɗai ba, har ma dukan waɗanda suka san gaskiya, 2 wato, muna ƙaunarku saboda gaskiyar da take a dawwame a cikinmu, za ta kuwa kasance tare da mu har abada. 3 Alheri, da jinƙai, da salama na Allah Uban, da kuma na Yesu Almasihu Ɗan Uban, za su tabbata a gare mu, da gaskiya da ƙauna.

Ku Zauna cikin Koyarwar Almasihu

4 Na yi farin ciki ƙwarai da samun waɗansu 'ya'yanki suna bin gaskiya, kamar yadda Uba ya ba mu umarni. 5 Yanzu kuma ina roƙonki, uwargida, ba cewa wani sabon umarni nake rubuto miki ba, sai dai wanda muke da shi tun farko ne, cewa mu ƙaunaci juna. 6 Ƙauna kuwa ita ce mu bi umarninsa. Umarnin kuwa, shi ne kamar yadda kuka ji tun farko, cewa ku yi zaman ƙauna. 7 Gama masu ruɗi da yawa sun fito duniya, waɗanda ba sa bayyana yarda, cewa Yesu Almasihu ya bayyana da jiki, irin wannan shi ne mai ruɗi, magabcin Almasihu. 8 Ku kula da kanku don kada ku yar da aikin da muka yi, amma dai ku sami cikakken sakamako. 9 Kowa ya yi ƙari, bai tsaya a kan koyarwar Almasihu ba, Allah ba ya tare da shi ke nan. Wanda kuwa ya tsaya a kan koyarwar nan, yana da uba da Ɗan. 10 Kowa ya zo gare ku, bai kuwa zo da wannan koyarwa ba, kada ku karɓe shi a gidanku, ko maraba ma kada ku yi masa. 11 Don duk wanda ya yi masa maraba, mugun aikinsa, sai yă shafe shi.

Gaisuwa

12 Ko da yake ina da abin da zan faɗa muku da yawa, na gwammace ba a wasiƙa ba, amma na sa zuciya in ziyarce ku, mu yi magana baka da baka, don farin cikinmu ya zama cikakke. 13 'Ya'yan 'yar'uwarki zaɓaɓɓiya suna gaishe ki.

3 Yahaya 1

Gaisuwa

1 Daga dattijon nan na ikilisiya zuwa ga Gayus, ƙaunatacce, wanda nake ƙauna da gaske. 2 Ya ƙaunataccena, ina addu'a kă sami zaman lafiya ta kowace hanya da kuma lafiya jiki, kamar yadda ruhunka yake a zaune lafiya. 3 Na yi farin ciki ƙwarai sa'ad da waɗansu 'yan'uwa suka zo suka shaida gaskiyarka, yadda hakika kake bin gaskiya. 4 Ba abin da ya fi faranta mini rai kamar in ji 'ya'yana suna bin gaskiya.

Yaba Kirkin Gayus

5 Ya ƙaunataccena, duk abin da kake yi wa 'yan'uwa, aikin bangaskiya kake yi, tun ba ma ga baƙi ba. 6 Su ne suka shaida ƙaunarka a gaban ikilisiya. Zai kyautu ka raka su a guzuri, kamar yadda ya cancanci bautar Allah, 7 domin saboda sunan nan ne suka fito, ba sa kuma karɓar kome daga al'ummai. 8 Domin haka ya kamata mu karɓi irin mutanen nan, mu ɗau nauyinsu, domin mu zama abokan aiki da su a kan gaskiya.

Diyotarifis Mai Ƙin Bin Magana

9 Na yi wa ikilisiya 'yar wasiƙa, amma shi Diyotarifis wanda yake so ya fi kowa a cikinsu, ya ƙi bin maganarmu. 10 Saboda haka, in na zo zan tabbatar masa da abin da yake yi, yana surutu game da mu, yana ɓaɓɓata mu. Wannan ma bai ishe shi ba, har ya ƙi yi wa 'yan'uwa maraba, yana kuma hana masu so su marabce su, yana fitar da su daga ikilisiya.

Kyakkyawar Shaida kan Dimitiriyas

11 Ya ƙaunataccena, kada ka kwaikwayi mugun aiki, sai dai nagari. Kowa da yake aikin nagari na Allah ne. Mai mugun aiki kuwa bai san Allah ba sam. 12 Dimitiriyas yana da kyakkyawar shaida a gun kowa, har gaskiya kanta ma tana yi masa shaida. Mu ma mun shaide shi, ka kuwa san shaidarmu tabbatacciya ce.

Gaisuwa

13 Dā kam, ina da abin da zan rubuto maka da yawa, amma yanzu na gwammace kada in rubuto a wasiƙa. 14 Ina sa zuciya mu sadu ba da daɗewa ba, sa'an nan ma yi magana baka da baka. 15 Salama tă tabbata gare ku. Aminanmu suna gaishe ka. Ka gai da aminanmu kowa da kowa.

Yahuza 1

Gaisuwa

1 Daga Yahuza bawan Yesu Almasihu, ɗan'uwan Yakubu zuwa ga kirayayyu, ƙaunatattun Allah Uba, keɓaɓɓu ga Yesu Almasihu. 2 Jinƙai, da salama, da ƙauna su yawaita a gare ku.

Hukuncin Malaman Ƙarya

3 Ya ku ƙaunatattuna, da yake dā ma ina ɗokin rubuto muku zancen ceton nan namu, mu duka, sai na ga wajibi ne in rubuto muku in gargaɗe ku, ku dage ƙwarai a kan bangaskiyar nan da aka danƙa wa tsarkaka sau ɗaya tak, ba ƙari. 4 Gama waɗansu mutane sun saɗaɗo a cikinku, waɗanda tun zamanin dā aka ƙaddara ga hukuncin nan, marasa bin Allah ne, masu mai da alherin Allah dalilin aikata fajirci, suna kuma ƙin makaɗaicin Ubangijinmu Yesu Almasihu. 5 Sai dai ina so in tuna muku, ko da yake kun riga kun san kome sosai, cewa Ubangiji ya ceci jama'a daga ƙasar Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba. 6 Har ma mala'ikun da ba su kiyaye girmansu ba, amma suka bar ainihin mazauninsu, ya tsare su cikin sarƙa madawwamiya a baƙin duhu, har ya zuwa shari'ar babbar ranar nan. 7 Haka kuma Saduma da Gwamrata, da birane kewayensu, waɗanda su ma suka dulmuya cikin fasikanci da muguwar sha'awa ta jiki, an nuna su domin ishara, suna shan hukuncin madawwamiyar wuta. 8 Haka kuma masu mafarke-mafarken nan, sukan ƙazantar da jikinsu, su ƙi bin mulki, su kuma yi wa masu ɗaukaka baƙar magana. 9 Amma lokacin da babban mala'ika, Mika'ilu yake fama da Iblis, suna m�su a kan gawar Musa, shi Mika'ilu bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka.” 10 Amma mutanen nan sukan kushe duk abin da ba su fahinta ba, saboda abubuwan da suka sani bisa ga jiki suna kamar dabbobi marasa hankali, su ne kuwa sanadin halakarsu. 11 Kaitonsu! Don sun bi halin Kayinu, sun ɗunguma cikin bauɗewar Bal'amu don kwaɗayi, sun kuma hallaka ta irin tawayen Kora. 12 Waɗannan mutane kamar aibobi ne a taronku na soyayya, suna ta shagulgulan ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro, suna kula da kansu kawai. Su kamar holoƙon hadiri ne, wanda iska take korawa. Su kamar itatuwa ne, marasa 'ya'ya da kaka, matattu murus, tumɓukakku. 13 Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu kai da kawowa, waɗanda aka tanada wa matsanancin duhu har abada. 14 Anuhu ma wanda yake na bakwai daga Adamu, shi ma ya yi annabci a kan waɗannan mutane cewa, “Ga shi, Ubangiji ya zo da dubban tsarkakansa, 15 don ya zartar da hukunci kan kowa, yă kuma tabbatar wa marasa bin Allah dukan aikinsu na rashin bin Allah, da suka aikata ta hanyar rashin bin Allah, da kuma baƙaƙen maganganu da masu zunubi marasa bin Allah suka yi game da shi.” 16 Waɗannan su ne masu gunaguni, masu ƙunƙuni, masu biye wa muguwar sha'awa, marubata, masu yi wa mutane bambaɗanci don samun wata fa'ida.

Faɗaka da Gargadi

17 Ya ku ƙaunatattuna, lalle ku tuna da maganar da manzannin Ubangijinmu Yesu Almasihu suka faɗa a dā, 18 da suka ce da ku, “A zamanin ƙarshe za a yi waɗansu mutane masu ba'a, masu biye wa muguwar sha'awarsu ta rashin bin Allah.” 19 Waɗannan su ne masu raba tsakani, masu son zuciya, marasa Ruhu. 20 Amma ya ku ƙaunatattuna, ku riƙa inganta kanku ga bangaskiyarku mafi tsarki, kuna addu'a da ikon Ruhu Mai Tsarki. 21 Ku tsaya a kan ƙaunar da Allah yake yi mana, kuna sauraron jinƙan Ubangijinmu Yesu Almasihu mai kaiwa ga rai madawwami. 22 Ku ji tausayin waɗanda suke shakka, 23 kuna ceton waɗansu kuna fizgo su daga wuta. Waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro kuna ƙyamar ko da tufafin da halinsu na mutuntaka ya ƙazantar.

Sa Albarka

24 Ga wanda yake da iko ya tsare ku daga faɗuwa, ya kuma miƙa ku marasa aibi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki, 25 ga Allah makaɗaici Mai Cetonmu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, ɗaukaka, da fifiko, da mulki, da iko su tabbata gare shi, tun fil'azal, da yanzu, da kuma har abada abadin. Amin, amin.

Wahayin 1

Wahayin Yesu Almasihu

1 Wahayin Yesu Almasihu da Allah ya ba shi ya nuna wa bayinsa abin da lalle ne zai auku ba da daɗewa ba, ya kuwa bayyana shi ta wurin aiko da mala'ikansa zuwa gun bawansa Yahaya, 2 wanda ya shaidi Maganar Allah, da kuma shaidar Yesu Almasihu, har da dukan abin da ya gani. 3 Albarka tā tabbata ga mai karanta maganar nan ta annabci, ta kuma tabbata ga masu ji, waɗanda kuma suke kiyaye abin da yake a rubuce a ciki, domin lokaci ya gabato.

Gaisuwa zuwa ga Ikilisiyoyi Bakwai

4 Daga Yahaya zuwa ga ikilisiyoyin nan bakwai da suke a ƙasar Asiya. Alheri da salama su tabbata a gare ku daga wanda yake a yanzu, shi ne a dā, shi ne kuma a nan gaba, da kuma Ruhohin nan bakwai da suke a gaban kursiyinsa, 5 da kuma Yesu Almasihu Amintaccen Mashaidi, na farko a cikin masu tashi daga matattu, mai mulkin sarakunan duniya. Ɗaukaka da mulki su tabbata har abada abadin ga wanda yake ƙaunarmu, ya kuma ɓalle mana ƙangin zunubanmu ta wurin jininsa, 6 ya mai da mu firistoci, mallakar Allah Ubansa. Amin. 7 Ga shi, zai zo a cikin gajimare, kowa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi, duk kabilan duniya kuma za su yi kuka a kansa. Wannan haka yake. Amin. 8 “Ni ne Alfa. Ni ne Omega,” in ji Ubangiji Allah, wanda yake a yanzu, shi ne a dā, shi ne kuma a nan gaba, Maɗaukaki.

Wahayin Ɗan Mutum

9 Ni ne Yahaya, ɗan'uwanku abokin tarayyarku a cikin tsanani, da mulki, da jimiri da suke a cikin Yesu. Ina a can tsibirin da ake kira Batamusa saboda Maganar Allah da kuma shaidar Yesu. 10 A ranar Ubangiji ya zamana Ruhu ya iza ni, sai na ji wata murya mai ƙara a bayana kamar ta ƙaho, 11 tana cewa, “Rubuta abin da ka gani a littafi, ka aika wa ikilisiyoyin nan bakwai, wato ta Afisa, da ta Simirna, da ta Birgamas, da ta Tayatira, da ta Sardisu, da ta Filadalfiya, da kuma ta Lawudikiya.” 12 Sai na juya in ga wanda yake yi mini magana, da juyawata kuwa, sai na ga fitilu bakwai na zinariya. 13 A tsakiyar fitilun nan kuwa, na ga wani kamar Ɗan Mutum, saye da riga har idon sawu, ƙirjinsa kuma da ɗamarar zinariya. 14 Kansa da gashinsa farare fat ne kamar farin ulu, farare fat kamar alli, idanunsa kamar harshen wuta, 15 ƙafafunsa kamar gogaggiyar tagulla, kamar wadda aka tace a maƙera, muryarsa kuma kamar ƙugin ruwaye masu gudu. 16 Yana riƙe da tauraro bakwai a hannunsa na dama, daga bakinsa kuma takobi mai kaifi biyu yake fitowa. Fuskarsa tana haske kamar rana a tsaka. 17 Da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa kamar na mutu. Amma ya ɗora mini hannunsa na dama, ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne na Farko. Ni ne na Ƙarshe, 18 ni ne kuma Rayayye. Dā na mutu, amma ga shi a yanzu, ina a raye har abada abadin, ina kuwa da mabuɗan mutuwa da na Hades. 19 To, ka rubuta abubuwan da ka gani, da abubuwan da suke a nan a yanzu, da abubuwan da suke shirin aukuwa bayan wannan. 20 Asirtacciyar ma'anar taurarin nan bakwai da ka gani a hannuna na dama kuwa, da kuma fitilun nan bakwai na zinariya, to, su taurarin nan bakwai, mala'iku ne na ikilisiyoyin nan bakwai, fitilun nan bakwai kuwa, ikilisiya bakwai ɗin ne.

Wahayin 2

Saƙo zuwa ga Afisa

1 “Sai ka rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Afisa haka, ‘Ga maganar wadda take riƙe da taurarin nan bakwai a hannunsa na dama, wadda kuma take tafiya a tsakiyar fitilun nan bakwai na zinariya. 2 “ ‘Na san ayyukanka, da famarka, da jimirinka, da yadda ba ka iya haƙurce wa mugaye, ka kuma gwada waɗanda suke ce da kansu manzanni, alhali kuwa ba su ba ne, ka tarar na ƙarya ne. 3 Na sani kana haƙuri, kana kuma jimiri saboda sunana, ba ka kuwa gaji ba. 4 Amma ga laifinka, wato, ka yar da ƙaunar da ka yi tun daga farko. 5 Ka tuna da komawa bayan da ka yi fa, ka tuba, ka yi irin aikin da ka yi tun daga farko. In ba haka ba, zan zo a gare ka in kawar da fitilarka daga wurin zamanta, sai ko in ka tuba. 6 Amma a wannan waje kam ka kyauta, kā ƙi ayyukan Nikolatawa, ni ma kuwa na ƙi su. 7 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi izinin cin 'ya'yan itacen rai, wanda yake a cikin Firdausin Allah.’ ”

Saƙo zuwa ga Simirna

8 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Simirna haka, ‘Ga maganar wanda yake na Farko da na Ƙarshe, wanda ya mutu, ya kuma sāke rayuwa. 9 “ ‘Na san tsananin da kake sha, da talaucinka (amma bisa ga hakika kai mawadaci ne), na kuma san yanken da waɗansu ke yi maka, masu cewa su Yahudawa ne, alhali kuwa ba su ba ne, jama'ar Shaiɗan ne. 10 Kada ka ji tsoron wuyar da za ka sha. Ga shi, Iblis yana shiri ya jefa waɗansunku a kurkuku don a gwada ku, za ku kuwa sha tsanani har kwana goma. Ka riƙi amana ko da za a kashe ka, ni kuwa zan ba ka kambin rai. 11 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, mutuwa ta biyu ba za ta cuce shi ba ko kaɗan.’ ”

Saƙo zuwa ga Birgamas

12 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Birgamas haka, ‘Ga maganar wanda yake da takobi mai kaifi biyu. 13 “ ‘Na san a inda kake da zama, wato, a inda kursiyin Shaiɗan yake. Duk da haka kuwa, ka tsaya a gare ni, ba ka bar yi mini bangaskiya ba, ko a zamanin Antibas amintaccen mashaidina, wanda aka kashe a cikinku, a inda Shaiɗan yake zaune. 14 Amma ga waɗansu laifofinka kaɗan. Akwai waɗansu a cikinku, da suke bin koyarwar Bal'amu, wanda ya koya wa Balak ya sa Isra'ilawa laifi, don su ci abincin da aka yi wa gumaka sadaka, su kuma yi fasikanci. 15 Haka kai ma kake da waɗansu masu bin koyarwar Nikolatawa. 16 Saboda haka, sai ka tuba. In ba haka ba kuwa, zan zo a gare ka da wuri, in yaƙe su da takobin da yake a bakina. 17 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi. Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi ɓoyayyiyar manna, zan kuma ba shi wani farin dutse, da sabon suna a rubuce a jikin dutsen, ba kuwa wanda ya san sunan, sai wanda ya karɓe shi.’ ”

Saƙo zuwa ga Tayatira

18 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Tayatira haka, ‘Ga maganar Ɗan Allah, mai idanu kamar harshen wuta, mai ƙafafu kamar gogaggiyar tagulla. 19 “ ‘Na san ayyukanka, da ƙaunarka, da bangaskiyarka, da ibadarka, da jimirinka, ayyukanka kuma na yanzu, sun fi na farkon. 20 Amma ga laifinka, wato, ka haƙurce wa matar nan Yezebel, wadda take ce da kanta annabiya, take kuma koya wa bayina, tana yaudararsu, su yi fasikanci, su kuma ci abincin da aka yi wa gumaka hadaya. 21 Na ba ta damar tuba, amma ta ƙi tuba da fasikancinta. 22 To, ga shi, zan jefa ta a gado, masu yin fasikanci da ita kuma zan ɗora musu matsananciyar wahala, sai ko in sun tuba da irin aikinta. 23 Zan kashe 'ya'yanta tashi ɗaya, dukan ikilisiyoyi kuma za su sani Ni ne mai fayyace birnin zuciya. Zan kuma saka wa kowannenku gwargwadon aikinsa. 24 Amma a game da sauranku, ku na Tayatira, da ba sa bin wannan koyarwa, ba su kuma koyi abin da waɗansu suke kira zurfafan al'amuran Shaiɗan ba, ina ce muku, ban ɗora muku wani nauyi ba. 25 Sai dai ku riƙi abin da kuke da shi kankan, har in zo. 26 Duk wanda ya ci nasara, yake kuma kiyaye aikina har ƙarshe, shi zan bai wa iko a kan al'ummai, 27 zai kuwa mallake su da sanda ta ƙarfe, ya farfashe su kamar tukwanen yumɓu 28 (kamar yadda Ni ma kaina na sami iko a gun Ubana), zan kuma ba shi gamzaki. 29 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”

Wahayin 3

Saƙo zuwa ga Sardisu

1 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Sardisu haka, ‘Ga maganar mai Ruhohin Allah guda bakwai, da kuma taurarin nan bakwai. “ ‘Na san ayyukanka, kai rayayye ne, alhali kuwa matacce ne kai. 2 Ka yi zaman tsaro, ka ƙarfafa abin nan da ya saura, yake kuma a bakin mutuwa, don ban ga aikinka cikakke ne ba a gaban Allahna. 3 Don haka, sai ka tuna da abin da ka karɓa ka kuma ji, ka kiyaye shi, sa'an nan ka tuba. In ba za ka yi tsaro ba, zan zo kamar ɓarawo, ba kuwa za ka san a lokacin da zan auko maka ba. 4 Amma dai har yanzu kana da waɗansu kaɗan a Sardisu da ba su ƙazantar da kansu ba, za su kuwa kasance tare da ni da fararen kaya, don sun cancanta. 5 Duk wanda ya ci nasara, za a sa masa fararen tufafi, ba kuwa zan soke sunansa daga Littafin Rai ba, zan ce shi nawa ne a gaban Ubana, da kuma a gaban mala'ikunsa. 6 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”

Saƙo zuwa ga Filadalfiya

7 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Filadalfiya haka, ‘Ga maganar Mai Tsarkin nan, Mai gaskiya, wanda yake da mabuɗin Dawuda, wanda in ya buɗe, ba mai rufewa, in kuma ya rufe, ba mai buɗewa. 8 “ ‘Na san ayyukanka. Ka ga, na bar maka ƙofa a buɗe, wadda ba mai iya rufewa. Na dai san ƙarfinka kaɗan ne, duk da haka, kā kiyaye maganata, ba ka yi musun sanin sunana ba. 9 To, ga shi, zan sa su waɗanda suke daga jama'ar Shaiɗan, masu cewa su Yahudawa ne, alhali kuwa ba su ba ne, ƙarya suke yi, zan sa su, su zo, su kwanta a gabanka, su sani dai na ƙaunace ka. 10 Tun da yake ka kiyaye maganar da na yi maka ta yin jimiri, Ni ma zan kiyaye ka daga sharrin lokacin nan na gwaji, wanda zai auko wa dukan duniya, don a gwada mazaunan duniya. 11 Ina zuwa da wuri. Ka riƙi abin da kake da shi kankan, kada wani ya karɓe maka kambinka. 12 Duk wanda ya ci nasara, zan mai da shi ginshiƙi a Haikalin Allahna. Ba zai ƙara fita daga ciki ba, zan kuma rubuta sunan Allahna a jikinsa, da sunan Birnin Allahna, wato, Sabuwar Urushalima, mai saukowa daga wurin Allahna daga Sama, da kuma nawa sabon suna. 13 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”

Saƙo zuwa ga Lawudikiya

14 “Ka kuma rubuta wa mala'ikan ikilisiyar da take a Lawudikiya haka, ‘Ga maganar tabbataccen nan, Amintaccen Mashaidi mai gaskiya, wanda ta wurinsa dukkan halittar Allah ta kasance. 15 “ ‘Na san ayyukanka. Ba ka da sanyi, ba ka kuwa da zafi. Da ma a ce kana da sanyi, ko kuwa kana da zafi. 16 To, saboda kai tsakatsaki ne, ba ka da sanyi, ba ka kuwa da zafi, zan tofar da kai daga bakina. 17 Tun da ka ce, kai mai arziki ne, cewa ka wadata ba ka bukatar kome, ba ka sani ba kuwa kai ne matsiyacin, abin yi wa kaito, matalauci, makaho, tsirara kuma. 18 Saboda haka, ina yi maka shawara ka sayi zinariya a guna, wadda aka tace da wuta, don ka arzuta, da kuma fararen tufafi da za ka yi sutura, ka rufe tsiraicinka don kada ka ji kunya, da kuma man shafawa a ido don ka sami gani. 19 Waɗanda nake ƙauna, su nake tsawata wa, nake kuma horo. Saboda haka, sai ka himmantu ka tuba. 20 Ga ni nan a tsaye a bakin ƙofa, ina ƙwanƙwasawa, kowa ya ji muryata ya buɗe ƙofar, sai in shiga wurinsa, in ci abinci tare da shi, shi kuma tare da ni. 21 Duk wanda ya ci nasara, zan ba shi izinin zama tare da ni a kursiyina, kamar yadda ni ma na ci nasara, na kuma zauna tare da Ubana a kursiyinsa. 22 Duk mai kunnen ji, yă ji abin da Ruhu yake faɗa wa ikilisiyoyi.’ ”

Wahayin 4

Sujada a Samaniya

1 Bayan wannan na duba, sai ga wata ƙofa a buɗe a Sama. Muryar farko da na ji dā, mai kama da ƙaho, ta ce mini, “Hawo nan, zan nuna maka abin da lalle ne ya auku bayan wannan.” 2 Nan da nan kuwa Ruhu ya iza ni, sai ga wani kursiyi a girke a Sama, da wani a zaune a kai. 3 Na zaunen kuwa ya yi kama da yasfa da yakutu. Kewaye da kursiyin kuma akwai wani bakan gizo mai kama da zumurrudu. 4 Kewaye da kursiyin kuwa akwai waɗansu kursiyai ashirin da huɗu, da dattawa ashirin da huɗu a zaune a kai, masu fararen tufafi, da kuma kambin zinariya a kansu. 5 Sai walƙiya take ta fitowa daga kursiyin, da ƙararraki, da kuma aradu. A gaban kursiyin kuma fitilu bakwai suna ci, waɗanda suke Ruhohin nan na Allah guda bakwai. 6 A gaban kursiyin kuwa akwai wani abu kamar bahar na gilas, garau yake kamar ƙarau. Kewaye da kursiyin kuma, ta kowane gefensa, da waɗansu rayayyun halitta guda huɗu, masu idanu ta ko'ina, gaba da baya. 7 Rayayyiyar halittar farko kamar zaki take, ta biyu kuma kamar ɗan maraƙi, ta uku kuma da fuska kamar ta mutum, ta huɗu kuma kamar juhurma yana jewa. 8 Su rayayyun halittan nan huɗu kuwa, kowaccensu tana da fikafikai shida, jikinsu duk idanu ne ciki da waje, dare da rana kuwa ba sa daina waƙa, suna cewa, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki, Ubangiji Allah Maɗaukaki, Shi ne a dā, shi ne a yanzu, shi ne kuma a nan gaba!” 9 Duk lokaci kuma da rayayyun halittan nan suka ɗaukaka wanda yake zaune a kan kursiyin, yake kuma raye har abada abadin, suka girmama shi, suka kuma gode masa, 10 sai dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi a gaban wanda yake a zaune a kan kursiyin, su yi masa sujada, shi da yake a raye har abada abadin, su kuma ajiye kambinsu a gaban kursiyin, suna waƙa, suna cewa, 11 “Macancanci ne kai, ya Ubangiji Allahnmu, Kă sami ɗaukaka, da girma, da iko, Domin kai ne ka halicci dukkan abubuwa, Da nufinka ne suka kasance aka kuma halicce su.”

Wahayin 5

Yimƙaƙƙen Littafin da Ɗan Ragon

1 A hannun dama na wanda yake zaune a kursiyin kuma, sai na ga wani littafi rubutacce ciki da bai, an yimƙe shi da hatimi bakwai. 2 Na kuma ga wani ƙaƙƙarfan mala'ika, yana shela da murya mai ƙarfi cewa, “Wa ya cancanta ya buɗe littafin nan, ya kuma ɓamɓare hatimansa?” 3 Ba kuwa wani a Sama ko a ƙasa, ko a ƙarƙashin ƙasa, da zai iya buɗe littafin, balle ya duba a cikinsa. 4 Sai na yi ta kuka da ba a sami wanda ya cancanta ya buɗe littafin, ko ya duba a cikinsa ba, ko ɗaya. 5 Sai ɗaya daga cikin dattawan nan ya ce mini, “Kada ka yi kuka. Ga shi, Zakin nan na kabilar Yahuza, Tsatson Dawuda, ya ci nasara har yake da iko ya buɗe littafin nan da hatimansa bakwai.” 6 Sai na ga wani Ɗan Rago yana a tsaye a tsakiyar kursiyin, kewaye da shi kuma ga rayayyun halittan nan huɗu da dattawan, Ɗan Ragon kuwa kamar yankakke ne, yana da ƙaho bakwai da ido bakwai, waɗanda suke Ruhohin Allah guda bakwai, da aka aika a duniya duka. 7 Sai ya je ya ɗauki littafin nan daga hannun dama na wanda yake a zaune a kan kursiyin. 8 Da ya ɗauki littafin, rayayyun halittan nan guda huɗu, da dattawan nan ashirin da huɗu, suka fāɗi gaban Ɗan Ragon, kowannensu yana riƙe da molo, da tasar zinariya a cike da turare, waɗanda suke addu'o'in tsarkaka. 9 Suna raira sabuwar waƙa, suna cewa, “Macancanci ne kai ka ɗauki littafin nan, ka ɓamɓare hatimansa, Domin dā an kashe ka, ka kuma fanso wa Allah mutane ta jininka Daga kowace kabila, da kowane harshe, da kowace jama'a, da kowace al'umma, 10 Ka mai da su firistoci mallakar Allahnmu, za su kuwa mallaki duniya.” 11 Sa'an nan na duba, sai na ji muryar mala'iku masu yawa, a kewaye da kursiyin, da rayayyun halittan nan, da kuma dattawan nan, yawansu zambar dubu har dubun dubbai, 12 suna cewa da murya mai ƙarfi, “Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka yanka yă sami iko, da wadata, da hikima, da ƙarfi, da girma, da ɗaukaka, da yabo!” 13 Sai na ji kowace halittar da take a Sama, da ƙasa, da ƙarƙashin ƙasa, da bisa teku, da kuma dukkan abin da yake cikinsu, suna cewa, “Yabo, da girma, da ɗaukaka, da mulki sun tabbata ga wanda yake a zaune a kan kursiyin, da Ɗan Ragon nan, har abada abadin!” 14 Sai rayayyun halittan nan huɗu suka ce, “Amin! Amin!” Dattawan nan kuma suka fāɗi suka yi sujada.

Wahayin 6

Hatiman

1 To, ina gani sa'ad da Ɗan Ragon nan ya ɓamɓare ɗaya daga cikin hatiman nan bakwai, na ji ɗaya daga cikin rayayyun halittan nan huɗu ta yi magana kamar aradu ta ce, “Zo.” 2 Da na duba, ga farin doki, mahayinsa kuma yana da baka, aka ba shi kambi, ya kuwa fita yana mai nasara, domin ya ƙara cin nasara. 3 Da ya ɓamɓare hatimi na biyu, na ji rayayyiyar halittar nan ta biyu ta ce, “Zo.” 4 Sai wani jan doki ya fito, aka kuma ba mahayinsa izini ya ɗauke salama daga duniya, don mutane su kashe juna, aka kuma ba shi babban takobi. 5 Da ya ɓamɓare hatimi na uku, na ji rayayyiyar halittar nan ta uku ta ce, “Zo.” Da na duba, ga baƙin doki, mahayinsa kuwa da mizani a hannunsa. 6 Sai na ji kamar wata murya a tsakiyar rayayyun halittar nan huɗu tana cewa, “Mudun alkama dinari guda, mudu uku na sha'ir dinari guda, sai dai kada ka ɓāta mai da kuma ruwan inabi!” 7 Da ya ɓamɓare hatimi na huɗu, na ji muryar rayayyiyar halittan nan ta huɗu ta ce, “Zo.” 8 Da na duba, ga doki kili, sunan mahayinsa kuwa Mutuwa, Hades kuma tana biye da shi. Sai aka ba su iko a kan rubu'in duniya, su yi kisa da takobi, da yunwa, da annoba, da kuma namomin jeji na duniya. 9 Da ya ɓamɓare hatimi na biyar, na ga rayukan waɗanda aka kashe saboda Maganar Allah, da shaidar da suka yi a ƙarƙashin bagadin ƙona turare. 10 Sai suka ta da murya da ƙarfi suka ce, “Ya Ubangiji Mamallaki, Mai Tsarki, Mai Gaskiya, sai yaushe ne za ka yi hukunci, ka ɗaukar mana fansar jininmu a gun mazaunan duniya?” 11 Sai aka ba kowannensu farar riga, aka ce musu, su dai huta kaɗan, har a cika adadin abokan bautarsu, wato, 'yan'uwansu, waɗanda za a kashe, kamar yadda su ma aka kashe su. 12 Da ya ɓamɓare hatimi na shida, na duba, sai kuwa aka yi wata babbar rawar ƙasa, rana ta koma baƙa kamar gwado na gashi, gudan wata ya zama kamar jini, 13 taurari kuma suka faɗa a ƙasa kamar yadda ɓaure yake zubar da ɗanyun 'ya'yansa, in ƙasaitacciyar iska ta kaɗa, shi, 14 sararin sama ya dāre ya naɗe kamar tabarma, sai aka kawar da kowane dutse, da kowane tsibiri daga mazauninsa. 15 Sai sarakunan duniya, da manyan mutane, da sarakunan yaƙi, da ma'arzuta, da ƙarfafa, da kuma kowane bawa da ɗa, suka ɓuya a kogwanni, da kuma a cikin duwatsu, 16 suna ce wa duwatsun, “Ku faɗo a kanmu, ku ɓoye mu daga idon wanda yake a zaune a kan kursiyin, da kuma fushin Ɗan Ragon nan, 17 don babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya jure mata?” 7 .1 Adadin Waɗanda aka Buga wa Hatimin, 144,400 na Isra'ila Adadin Waɗanda aka Buga wa Hatimin, 144,400 na Isra'ila

Wahayin 7

1 Bayan wannan na ga mala'iku huɗu, a tsaye a kusurwa huɗu ta duniya, suna tsare da iskokin nan huɗu na duniya, don kada wata iska ta busa a kan ƙasa, ko a kan teku, ko a kan wani itace. 2 Sai na ga wani mala'ika yana hawa daga mafitar rana, a riƙe da hatimin Allah Rayayye. Sai ya yi wa mala'ikun nan huɗu magana da murya mai ƙarfi, waɗanda aka bai wa ikon azabtar da ƙasa da teku, 3 yana cewa, “Kada ku azabtar da ƙasa, ko teku, ko itatuwa, sai mun buga wa bayin Allahnmu hatimi a goshinsu tukuna.” 4 Sai na ji adadin waɗanda aka buga wa hatimin, dubu ɗari da arba'in da huɗu ne, daga kowace kabilar Isra'ila, 5 wato, an yi wa dubu goma sha biyu hatimi daga kabilar Yahuza, dubu goma sha biyu daga kabilar Ra'ubainu, dubu goma sha biyu daga kabilar Gad, 6 dubu goma sha biyu daga kabilar Ashiru, dubu goma sha biyu daga kabilar Naftali, dubu goma sha biyu daga kabilar Manassa, 7 dubu goma sha biyu daga kabilar Saminu, dubu goma sha biyu daga kabilar Lawi, dubu goma sha biyu daga kabilar Issaka, 8 dubu goma sha biyu daga kabilar Zabaluna, dubu goma sha biyu daga kabilar Yusufu, dubu goma sha biyu kuma daga kabilar Biliyaminu.

Ƙasaitaccen Taro daga Kowace Al'umma

9 Bayan wannan na duba, ga wani ƙasaitaccen taro, wanda ya fi gaban ƙirge, daga kowace al'umma, da kabila, da jama'a, da harshe, suna a tsaitsaye a gaban kursiyin, a gaban Ɗan Ragon kuma, a saye da fararen riguna, da gazarin dabino a hannunsu, 10 suna ta da murya da ƙarfi suna cewa, “Yin ceto ya tabbata ga Allahnmu wanda yake a zaune a kan kursiyin, da kuma Ɗan Rago!” 11 Dukan mala'iku kuwa suna tsaitsaye a kewaye da kursiyin, da dattawan nan, da kuma rayayyun halittan nan guda huɗu, suka fāɗi a gaban kursiyin suka yi wa Allah sujada, 12 suna cewa, “Hakika! Yabo, da ɗaukaka, da hikima, da godiya, da girma, da iko, da ƙarfi su tabbata ga Allahnmu har abada abadin! Amin! Amin!” 13 Sai ɗaya daga cikin dattawan nan ya yi mini magana, ya ce, “Su wanen e waɗannan da suke a saye da fararen riguna, daga ina kuma suke?” 14 Sai na ce masa, “Ya shugaba, ai, ka sani.” Sai ya ce mini, “Su ne waɗanda suka fito daga matsananciyar wahala, sun wanke rigunansu, suka mai da su farare da jinin Ɗan Ragon nan. 15 Saboda haka, ne suke a gaban kursiyin Allah, suna bauta masa dare da rana a Haikalinsa. Na zaune a kan kursiyin nan kuwa, zai kare su da Zatinsa, 16 ba za su ƙara jin yunwa ba, ba kuma za su ƙara jin ƙishirwa ba, ba za su ƙara jin zafin rana ko ƙuna ba sam, 17 domin Ɗan Ragon nan da yake a tsakiyar kursiyin, shi zai zama makiyayinsu, zai kuwa kai su maɓuɓɓugar ruwan rai. Allah kuma zai share musu dukan hawaye.”

Wahayin 8

Hatimi na Bakwai da Tasar Zinariya

1 Sa'ad da Ɗan Ragon ya ɓamɓare hatimi na bakwai, aka yi shiru a Sama kamar na rabin sa'a. 2 Sa'an nan na ga mala'ikun nan bakwai da suke a tsaye a gaban Allah, an ba su ƙaho bakwai. 3 Ga kuma wani mala'ika ya zo ya tsaya a gaban bagadin ƙona turare, riƙe da tasar zinariya ta turaren ƙonawa. Sai aka ba shi turare mai yawa, domin ya haɗa da addu'o'in tsarkaka duka a kan bagadin ƙona turare na zinariya a gaban kursiyin. 4 Sai hayaƙin turaren ya tashi daga hannun mala'ikan tare da addu'o'in tsarkaka, ya isa a gaban Allah. 5 Sai mala'ikan ya ɗauki tasar nan ta turaren ƙonawa, ya cika ta da wuta daga bagadin ƙona turare, ya watsa a kan duniya, sai aka yi ta aradu, da ƙararraki masu tsanani, da walƙiya, da kuma rawar ƙasa.

Ƙahonin

6 Sa'an nan mala'ikun nan bakwai masu ƙaho bakwai ɗin nan, suka yi shirin busa su. 7 Mala'ikan farko ya busa ƙahonsa, sai ga ƙanƙara da wuta, gauraye da jini. Aka zuba su a duniya, sai sulusin duniya ya ƙone, sulusin itatuwa suka ƙone, dukkan ɗanyar ciyawa kuma ta ƙone. 8 Mala'ika na biyu ya busa ƙahonsa, sai aka jefa wani abu a teku kamar babban dutse mai tsawo, mai cin wuta. Sulusin teku ya zama jini, 9 sulusin halittar da suke a ruwa suka mutu, sulusin jiragen ruwa kuma suka hallaka. 10 Mala'ika na uku ya busa ƙahonsa, sai wani babban tauraro ya faɗo daga sama, yana cin wuta kamar cukwima. Ya faɗa a sulusin koguna da maɓuɓɓugan ruwa. 11 Sunan tauraron kuwa Ɗaci. Sulusin ruwa ya zama mai ɗaci, sai mutane da yawa suka mutu saboda shan ruwan, don ɗacinsa. 12 Mala'ika na huɗu ya busa ƙahonsa, sai aka bugi sulusin rana, da sulusin wata, da kuma sulusin taurari, har sulusin haskensu ya zama duhu, wato ba haske a sulusin yini, haka kuma a sulusin dare. 13 Sa'an nan da na duba, na ji wani juhurma mai jewa a tsakiyar sararin sama, yana kuka da ƙarfi, yana cewa, “Kaito! Kaito! Kaitonku, ku mazaunan duniya, in an yi busan sauran ƙahonin da mala'ikun nan uku suke shirin busawa!”

Wahayin 9

1 Mala'ika na biyar ya busa ƙahonsa, sai na ga wani tauraron da ya faɗa a kan duniya daga sama, aka ba shi mabuɗin ramin mahallaka. 2 Ya kuwa buɗe ramin mahallakar, sai wani hayaƙi kamar na babbar matoya ya taso, har hayaƙin ramin nan ya duhunta rana da sararin sama. 3 Fāri suka fito zuwa a cikin duniya daga cikin hayaƙin nan, aka ba su ikon harbi, irin na kunamin duniya. 4 Aka kuwa hana su cutar ciyayin duniya, ko tsiro, ko kowane itace, sai dai mutanen da ba su da hatimin Allah a goshinsu. 5 Aka kuwa yardar musu su yi musu azaba har wata biyar, amma kada su kashe su, azabarsu kuwa, kamar ta kunama take, in ta harbi mutum. 6 A waɗannan kwanaki kuwa mutane za su nemi mutuwa, amma ba za su same ta ba, za su ƙagauta su mutu, mutuwa kuwa sai ta guje musu. 7 Kamannin fārin nan kuwa kamar dawakai ne da suka ja batar yaƙi, a kansu kuma da wani abu kamar kambin zinariya, fuskarsu kuwa kamar ta mutum, 8 gashinsu kamar na mace, haƙorinsu kuma kamar na zaki. 9 Suna a saye da sulkuna kamar na ƙarfe, dirin fikafikansu kuwa kamar dirin kekunan doki masu yawa ne suna rugawa fagyan yaƙi, 10 wutsiyarsu kamar ta kunama, ga kuma ƙari, ikonsu yana ji wa mutane ciwo har wata biyar kuwa a wutsiyarsu yake. 11 Sarkinsu kuwa da yake iko da su shi ne mala'ikan mahallaka, sunansa da Yahudanci Abadan, da Helenanci kuwa Afoliyon. 12 Bala'in farko ya wuce, ga kuma bala'i na biyu a nan a tafe. 13 Sa'an nan mala'ika na shida ya busa ƙahonsa, sai na ji wata murya daga zankayen nan huɗu na bagadin ƙona turare na zinariya a gaban Allah, 14 tana ce wa mala'ikan nan na shida mai ƙaho, “Ka saki mala'iku huɗun nan da suke a ɗaure a gabar babban kogin nan Yufiretis.” 15 Sai aka saki mala'ikun nan huɗu, waɗanda aka tanada saboda wannan sa'a, da wannan rana, da wannan wata, da wannan shekara, su kashe sulusin 'yan adam. 16 Yawan rundunonin sojan doki kuwa, na ji adadinsu zambar dubu metan ne. 17 Ga kuwa yadda na ga dawakan a wahayin da aka yi mini, mahayansu suna a saye da sulkuna, launinsu ja kamar wuta, da shuɗi, da kuma rawaya kamar farar wuta, kawunan dawakan kuma kamar na zaki, wuta kuma da hayaƙi da farar wuta suna fita daga bakinsu. 18 Da waɗannan bala'i uku aka kashe sulusin 'yan adam, wato, da wuta, da hayaƙi, da farar wuta da suke fita daga bakinsu. 19 Domin ikon dawakan nan na a bakinsu da a wutsiyarsu, wutsiyoyinsu kamar macizai suke, har da kawuna, da su ne suke azabtarwa. 20 Sauran 'yan adam waɗanda bala'in nan bai kashe ba kuwa, ba su tuba sun rabu da abubuwan da suka yi da hannunsu ba, ba su kuma daina yin sujada ga aljannu, da gumakan zinariya, da na azurfa, da na tagulla, da na dutse, da na itace ba, waɗanda ba su iya gani, ko ji, ko tafiya, 21 ba su kuma tuba da kashe-kashenkai da suka yi ba, ko sihirinsu, ko fasikancinsu, ko kuma sace-sacensu.

Wahayin 10

Mala'ika da Ƙaramin Littafi

1 Sa'an nan na ga wani ƙaƙƙarfan mala'ika yana saukowa daga sama, a lulluɓe da gajimare, da bakan gizo a bisa kansa, fuskarsa kamar rana, ƙafafunsa kuma kamar ginshiƙan wuta. 2 Ga wani ƙaramin littafi a buɗe a hannunsa. Sai ya tsai da ƙafarsa ta dama a kan teku, ƙafarsa ta hagu kuwa a kan ƙasa, 3 ya yi kira da murya mai ƙarfi, kamar zaki yana ruri. Da ya yi kiran, sai aradun nan bakwai suka yi tsawa. 4 Sa'ad da kuwa aradun nan bakwai suka yi tsawa, kamar zan rubuta, sai na ji wata murya daga sama tana cewa, “Rufe abin da aradun nan bakwai suka faɗa, kada ka rubuta.” 5 Sai mala'ikan nan da na gani a tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama, 6 ya rantse da wanda yake a raye har abada abadin, wanda ya halicci sama da abin da take a cikinta, da ƙasa da abin da take a cikinta, da kuma teku da abin da take a cikinta, cewa ba sauran wani jinkiri kuma, 7 sai dai a lokacin busa ƙahon da mala'ika na bakwai zai busa ne, za a cika asirtaccen nufin nan na Allah, bisa ga bisharar da ya yi wa bayinsa annabawa. 8 Sa'an nan muryar nan da na ji daga sama ta sāke yi mini magana, ta ce, “Je ka, ka ɗauki littafin nan da yake a buɗe a hannun mala'ikan da yake a tsaye a bisa teku da ƙasa.” 9 Sai na je wurin mala'ikan, na ce masa, ya ba ni ƙaramin littafin. Sai ya ce mini, “Karɓi ka cinye, zai yi maka ɗaci a ciki, amma a baka kamar zuma yake don zaƙi.” 10 Sai na karɓi ƙaramin littafin daga hannun mala'ikan, na cinye. Sai ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma da na cinye, cikina ya ɗau ɗaci. 11 Sai kuma aka ce mini, “Lalle ne ka sāke yin annabci a game da jama'a iri iri, da al'ummai, da harsuna, da kuma sarakuna da yawa.”

Wahayin 11

Shaidu Biyu Ɗin

1 Sa'an nan aka ba ni wata gora kamar sanda, aka kuma ce mini, “Tashi ka auna Haikalin Allah, da bagadin hadaya, da kuma masu sujada a ciki, 2 amma kada ka auna harabar Haikalin, ka ƙyale ta, domin an ba da ita ga al'ummai, za su tattake tsattsarkan birnin nan har wata arba'in da biyu. 3 Zan kuma bai wa mashaidana biyu iko su yi annabci kwana dubu da metan da sittin, suna a saye da tsummoki.” 4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun ɗin nan guda biyu, da fitilun nan biyu da suke a tsaye a gaban Ubangijin duniya. 5 In kuwa wani yana da niyyar cutarsu, sai wuta ta huro daga bakinsu, ta lashe maƙiyansu, duk mai niyyar cutarsu kuwa, ta haka ne lalle za a kashe shi. 6 Suna da ikon hana ruwan sama, don kada a yi ruwa a duk kwanakin da suke yin annabci, suna kuma da iko a kan ruwa, su mai da shi jini, su kuma ɗora wa duniya kowane irin bala'i, a duk lokacin da suke so. 7 Bayan da suka ƙare shaidarsu, sai wata dabba mai fitowa daga mahallaka tă yaƙe su, ta cinye su, ta kashe su, 8 a kuma bar gawawwakinsu a kan hanyar babban birnin nan da ake kira Saduma da Masar ga ma'ana ta ruhu, a inda aka gicciye Ubangijinsu. 9 Mutanen dukkan jama'a, da kabila, da harshe, da al'umma za su riƙa kallon gawawwakinsu, har kwana uku da rabi, su kuwa ƙi yarda a binne su. 10 Mazaunan duniya kuma, sai su yi ta alwashi a kansu, suna ta shagali, suna a'aika wa juna da kyauta, domin annabawan nan biyu dā sun azabtar da mazaunan duniya. 11 Amma bayan kwana uku da rabin nan, sai numfashin rai daga wurin Allah ya shiga a cikinsu, suka tashi a tsaye, matsanancin tsoro kuwa ya rufe waɗanda suka gan su. 12 Sai suka ji wata murya mai ƙara daga sama tana ce musu, “Ku hawo nan!” Sai suka tafi sama a cikin gajimare, maƙiyansu suna gani. 13 A nan tāke sai aka yi wata babbar rawar ƙasa, sai ushirin garin ya zube, mutum dubu bakwai aka kashe a rawar ƙasar, sauran kuwa suka tsorata, suka ɗaukaka Allah Mai Sama. 14 Bala'i na biyu ya wuce, ga kuma bala'i na uku yana zuwa nan da nan.

Ƙaho na Bakwai

15 Sa'an nan mala'ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji waɗansu muryoyi masu ƙara a Sama, suna cewa, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Almasihunsa, shi kuma zai yi mulki har abada abadin.” 16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke a zaune a kan kursiyansu a gaban Allah suka fādi suka yi wa Allah sujada, 17 Suna cewa, “Mun gode maka, ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, Wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, Saboda ka ɗauki ikonka mai girma, kana mulki. 18 Al'ummai sun husata, fushinka kuwa ya auko, Lokaci ya yi da za a yi wa matuttu shari'a, A kuma yi wa bayinka, annabawa da tsarkaka sakamako, Da masu jin tsoron sunanka, yaro da babba, A kuma hallaka masu hallaka duniya.” 19 Sa'an nan aka buɗe Haikalin nan na Allah da yake a Sama, aka kuma ga akwatin alkawarinsa a Haikalinsa. Sai aka yi ta walƙiya da kururuwa, da aradu, da rawar ƙasa, da ƙanƙara manya manya.

Wahayin 12

Wata Mace da Macijin

1 Aka kuma ga wata babbar alama a sama, wata mace tana a lulluɓe da rana, tana a tsaye a kan wata, da kuma kambi mai taurari goma sha biyu a kanta. 2 Tana da ciki, sai kuma ta yi ta ƙara ta ƙagauta domin ta haihu, saboda azabar naƙuda. 3 Sai kuma aka ga wata alama a sama, ga wani ƙaton jan maciji mai kawuna bakwai, da ƙahoni goma, da kambi bakwai a kawunansa. 4 Wutsiyarsa ta sharo sulusin taurari, ta zuba su a ƙasa. Sai macijin ya tsaya a gaban matar nan mai naƙuda, don ya lanƙwame ɗan nata in ta haife shi. 5 Ta kuwa haifi ɗa namiji, wanda zai mallaki dukkan al'ummai da sandar ƙarfe, amma aka fyauce ɗan nata, aka kai shi zuwa wurin Allah da kursiyinsa. 6 Matar kuwa, sai ta gudu ta shiga jeji, a inda Allah ya shirya mata wurin da za a cishe ta har kwana dubu da metan da sittin. 7 Sai yaƙi ya tashi a sama, Mika'ilu da mala'ikunsa suna yaƙi da macijin nan, macijin kuma da mala'ikunsa suka yi ta yaƙi, 8 amma aka cinye su, har suka rasa wuri a sama sam. 9 Sai aka jefa ƙaton macijin nan a ƙasa, wato macijin nan na tun dā dā, wanda ake kira Ibilis da Shaiɗan, mayaudarin dukkan duniya, aka jefa shi a duniya, mala'ikunsa ma aka jefa su tare da shi. 10 Sai na ji wata murya mai ƙara a Sama tana cewa, “A yanzu fa, ceto, da ƙarfi, da mulki na Allahnmu, da kuma ikon Almasihunsa sun bayyana, don an jefa mai ƙarar 'yan'uwanmu a ƙasa, shi da yake ƙararsu dare da rana a gun Allahnmu. 11 Sun kuwa yi nasara da shi albarkacin jinin Ɗan Ragon nan, da kuma albarkacin maganar da suka shaida, domin ba su yi tattalin ransu ba, har abin ya kai su ga kisa. 12 Saboda haka, sai ku yi farin ciki, ya ku sammai, da ku mazaunan a ciki. Amma kaitonku, ke ƙasa, da kai teku, don Ibilis ya sauko gare ku da matsanancin fushi, don ya san lokacinsa ya ƙure.” 13 Da macijin nan ya ga an jefa shi a ƙasa, ya fafari matar nan da ta haifi ɗa namiji, da tsanani. 14 Amma aka ba matar fikafikan nan biyu na babban juhurman nan, don ta tashi ta guje wa macijin nan, ta shiga jeji, ta je wurin da za a cishe ta a lokaci ɗaya, da lokatai, da rabin lokaci. 15 Sai macijin ya kwarara ruwa daga bakinsa kamar kogi daga bayan matar, don ya share ta da ambaliya. 16 Amma ƙasa ta taimaki matar, ita ƙasar ta buɗe bakinta ta shanye kogin da macijin nan ya kwararo daga bakinsa. 17 Macijin kuwa ya yi fushi da matar, ya tafi ya ɗaura yaƙi da sauran zuriyarta, wato, waɗanda suke kiyaye umarnin Allah, suke kuma shaidar Yesu. Sai ya tsaya a kan yashin teku.

Wahayin 13

Dabbobi Biyu Ɗin

1 Na kuma ga wata dabba tana fitowa daga cikin teku, mai ƙaho goma, da kawuna bakwai, da kambi goma a kan ƙahoninta, da kuma wani suna na saɓo a kawunanta. 2 Dabbar da na gani kuwa kamar damisa take, ƙafafunta kamar na beyar, bakinta kuma kamar na zaki. Macijin kuwa ya ba ta ƙarfinsa, da kursiyinsa, da ikonsa mai girma. 3 Ɗaya daga cikin kawunanta, an yi masa rauni kamar na ajali, amma rauninsa mai kamar na ajalin nan ya warke. Sai dabbar ta ɗauke wa duk duniya hankali, suna mamaki, 4 har suka yi wa macijin nan sujada, don shi ne ya bai wa dabbar ikonsa, suka kuma yi wa dabbar sujada, suna cewa, “Wa ya yi kama da dabbar nan? Wa kuma zai iya yaƙi da ita?” 5 An kuwa ba dabbar nan baki, tana fariya da maganganun saɓo, aka kuma yarder mata ta zartar da iko, har wata arba'in da biyu. 6 Sai ta buɗe bakinta don ta saɓi Allah, ta yi ta saɓon sunansa, da wurin zamansa, da waɗanda suke a zaune a Sama. 7 Aka kuma yardar mata ta yaƙi tsarkaka, ta cinye su. Aka kuma ba ta iko a kan kowace kabila, da jama'a, da harshe, da al'umma. 8 Duk mazaunan duniya kuma, za su yi mata sujada, wato, duk wanda, tun farkon duniya, ba a rubuta sunansa a Littafin Rai na Ɗan Ragon nan da yake Yankakke ba. 9 Duk mai kunnen ji, yă ji. 10 Kowa aka ƙaddara wa bauta, si ya je aikin bautar. Kowa kuwa ya yi kisa da takobi, to, kuwa da takobi za a kashe shi lalle. Wannan yana nuna jimiri da bangaskiya na tsarkaka. 11 Sa'an nan na ga wata dabba na fitowa daga cikin ƙasa. Tana da ƙaho biyu kamar na ɗan rago, maganarta kuwa kamar ta macijin nan. 12 Tana zartar da duk ikon dabbar nan ta farko, a kan idonta, tana kuma sa duniya da duk mazauna a cikinta, su yi wa dabbar nan ta farko sujada, wadda aka warkar mata da rauninta mai kamar na ajali. 13 Tana yin manyan abubuwan al'ajabi, har ma tana sa wutu ta zuba a ƙasa daga sama, a gaban idon mutane. 14 Tana kuma yaudarar mazaunan duniya, da abubuwan al'ajabin nan da aka yardar mata ta yi a gaban dabbar nan, tana umartarsu, su yi wata siffa saboda dabbar nan wadda aka yi wa rauni da takobi, ta kuwa rayu. 15 An kuma yardar mata ta busa wa siffar dabbar nan rai, har siffar dabbar nan ma ta iya yin magana, ta kuma sa a kashe waɗanda suka ƙi yi wa siffar dabbar nan sujada. 16 Har wa yau, sai ta sa a yi wa kowa alama a hannun dama, ko a goshi, manya da yara duka, mawadata da matalauta, ɗa da bawa, 17 har ba mai iya saye ko sayarwa sai ko yana da alamar nan, wato, sunan dabbar nan, ko kuwa lambar sunanta. 18 Wannan abu sai a game da hikima. Duk mai basira ya ƙididdige lambar dabbar nan, don lamba ce ta wani mutum, lambar kuwa ɗari shida ce da sittin da shida. 14 .1 Waƙar 144,000 Ɗin Waƙar 144,000 Ɗin

Wahayin 14

1 Sa'an nan na duba, sai ga Ɗan Ragon nan a tsaye a kan Dutsen Sihiyona, akwai kuma mutum dubu ɗari da dubu arba'in da huɗu tare da shi, waɗanda aka rubuta sunansa, da sunan Ubansa, a goshinsu. 2 Sai na ji wata murya daga Sama kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, muryar da na ji kuwa, kamar ta masu molo ce na kiɗan molo. 3 Suna raira wata sabuwar waƙa a gaban kursiyin, a gaban rayayyun halittan nan huɗu, da kuma a gaban dattawan nan. Ba mai iya koyon waƙar nan, sai mutum dubu ɗari da dubu arba'in da huɗu ɗin nan, waɗanda aka fanso daga duniya. 4 Waɗannan su ne waɗanda ba su taɓa ƙazantuwa da fasikanci ba, domin su tsarkaka ne. Su ne kuma suke bin Ɗan Ragon a duk inda ya je. Su ne kuma aka fanso daga cikin mutane a kan su ne nunan fari na Allah, da na Ɗan Ragon nan kuma, 5 ba wata ƙarya a bakinsu, domin su marasa aibu ne.

Sanarwar Mala'iku Uku Ɗin

6 Sa'an nan na ga wani mala'ika yana kaɗawa a tsakiyar sararin sama, yana tafe da madawwamiyar bishara, domin ya sanar da ita ga mazaunan duniya, wato, ga kowace al'umma, da kabila, da harshe, da jama'a. 7 Sai ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Ku ji tsoron Allah, ku ɗaukaka shi, domin lokacinsa na yin hukunci ya yi. Ku yi masa sujada, shi da ya halicci sama, da ƙasa, da teku, da kuma maɓuɓɓugan ruwa.” 8 Sai kuma mala'ika na biyu ya biyo, yana cewa, “Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi! Ita da ta zuga dukkan al'ummai su yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita.” 9 Sai kuma mala'ika na uku ya biyo, yana ɗaga murya da ƙarfi, yana cewa, “Duk mai yi wa dabbar nan da siffarta sujada, wanda kuma ya yarda a yi masa alama a goshinsa, ko a hannunsa, 10 zai ci karo da azabar Allah tsantsa ta tsananin fushinsa, za a kuwa azabta shi da wuta, da duwatsun wuta, a gaban mala'iku tsarkaka, da kuma Ɗan Ragon. 11 Hayaƙin azabar nan tasu ya dinga tashi har abada abadin, ba su da wani rangwame dare da rana, wato, waɗannan masu yi wa dabbar nan da siffarta sujada, da kuma duk wanda ya yarda aka yi masa alamar sunanta.” 12 Wannan yana nuna jimirin tsarkaka, masu kiyaye umarnin Allah da kuma bangaskiya ga Yesu. 13 Sai kuma na ji wata murya daga Sama tana cewa, “Rubuta wannan. Albarka tā tabbata ga matattu, wato, waɗanda za su mutu a nan gaba a kan su na Ubangiji ne.” Ruhu ya ce, “Hakika, masu albarka ne, domin su huta daga wahalarsu, gama aikinsu yana a biye da su!”

Girbe Duniya

14 Sa'an nan na duba, sai ga wani farin gajimare, da wani kamar Ɗan Mutum a zaune a kan gajimaren, da kambin zinariya a kansa, da kakkaifan lauje a hannunsa. 15 Sai mala'ika ya fito daga Haikalin, yana magana da murya mai ƙarfi da wanda yake a zaune a kan gajimaren, yana cewa, “Ka sa laujenka ka yanke, don lokacin yanka ya yi, amfanin duniya ya nuna sarai.” 16 Sai wanda yake a zaune a kan gajimaren ya wurga laujensa zuwa duniya, aka girbe amfanin duniya. 17 Wani mala'ika kuma ya fito daga Haikali a Sama, shi ma kuwa yana da kakkaifan lauje. 18 Sai kuma wani mala'ika ya fito daga bagadin ƙona turare, wato, mala'ikan da yake da iko da wutar, ya yi magana da murya mai ƙarfi da wannan mai kakkaifan lauje, ya ce, “Ka sa laujenka ka yanke nonnan inabin zuwa duniya, don inabin ya nuna.” 19 Sai mala'ikan ya wurga laujensa duniya, ya tattara inabin duniya, ya zuba a cikin babbar mamatsar inabi ta fushin Allah. 20 Aka tattake mamatsar inabin a bayan gari, jini kuma ya yi ta gudana daga mamatsar inabin, ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, har mil metan.

Wahayin 15

Mala'iku Masu Bala'i Bakwai

1 Na kuma ga wata alama a Sama, mai girma, mai banmamaki, mala'iku bakwai masu bala'i bakwai, waɗanda suke bala'in ƙarshe, don su ne iyakacin fushin Allah. 2 Sai na ga wani abu kamar bahar na gilas, gauraye da wuta, na kuma ga waɗanda suka yi nasara da dabbar nan, da siffarta, da kuma lambar sunanta, a tsaitsaye a bakin bahar na gilas, da molayen yabon Allah a hannunsu. 3 Suna raira waƙar da Musa bawan Allah ya yi, da kuma wadda ake yi wa Ɗan Ragon nan, suna cewa, “Ayyukanka manya ne, masu banmamaki, Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki! Hanyoyinka na adalci ne, na gaskiya ne kuma, Ya Sarkin al'ummai. 4 Wane ne ba zai ji tsoronka ba, ya Ubangiji, Ya kuma ɗaukaka sunanka? Domin kai kaɗai ne Mai Tsarki. Dukkan al'ummai za su zo su yi maka sujada, Don ayyukanka na adalci sun bayyana.” 5 Bayan wannan na duba, ga Wuri Mafi Tsarki a buɗe a Haikali a Sama. 6 Sai mala'ika bakwai ɗin nan masu bala'i bakwai suka fito daga Haikalin, a saye da tufafin lilin mai tsabta, mai ɗaukar iko, da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu. 7 Sai ɗaya daga cikin rayayyun halittan nan guda huɗu, ta ba mala'ikun nan bakwai tasoshi bakwai na zinariya, a cike da fushin Allah, shi da yake a raye har abada abadin. 8 Sai Haikalin ya cika da hayaƙi mai fitowa daga ɗaukakar Allah da ikonsa. Ba mai iya shiga Haikalin nan, sai bayan bala'i bakwai na mala'ikun nan bakwai sun ƙare.

Wahayin 16

Tasoshin Azaba

1 Sai na ji wata murya mai ƙara daga Haikalin, tana ce wa mala'ikun nan bakwai, “Ku je ku juye tasoshin nan bakwai na fushin Allah a kan duniya.” 2 Daga nan mala'ikan farko ya je ya juye abin da yake a tasarsa a kan duniya, sai kuwa waɗansu mugayen miyaku masu azabtarwa suka fito a jikin mutanen da suke da alamar dabbar nan, suke kuma yi wa siffarta sujada. 3 Mala'ika na biyu ya juye abin da yake a tasarsa a teku, ya zama kamar jinin mataccen mutum, kowane abu mai rai na cikin teku kuma ya mutu. 4 Mala'ika na uku ya juye abin da yake a tasarsa a koguna da maɓuɓɓugan ruwa, sai suka zama jini. 5 Na kuwa ji mala'ikan ruwa yana cewa, “Kai mai adalci ne a hukuncin nan naka, Ya kai Mai Tsarki, wanda kake a yanzu, kake kuma a dā. 6 Don mutane sun zub da jinin tsarkaka da na annabawa, Ga shi kuwa, ka ba su jini su sha. Sakamakonsu ke nan!” 7 Sai na ji wata murya a bagadin ƙona turare, tana cewa, “Hakika, ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, Hukuncinka daidai yake, na adalci ne kuma!” 8 Sai mala'ika na huɗu ya juye abin da yake a tasarsa a rana, sai aka yardar mata ta ƙona mutane da wuta. 9 Sai matsanancin zafi ya ƙona mutane, har suka zagi sunan Allah, shi da yake da ikon waɗannan bala'i, ba su kuwa tuba sun ɗaukaka shi ba. 10 Mala'ika na biyar ya juye abin da yake a tasarsa a kursiyin dabbar nan, sai mulkinta ya zama duhu, har mutane suka ciji leɓunansu don azaba, 11 suka zagi Allah Mai Sama saboda azabarsu da miyakunsu, ba su kuma tuba da ayyukansu ba. 12 Mala'ika na shida ya juye abin da yake a tasarsa a babban kogin nan Yufiretis, sai ruwansa ya ƙafe, don a shirya wa sarakuna daga gabas tafarki. 13 Na kuma ga baƙaƙen aljannu masu kama da kwaɗi gudu uku, suna fitowa daga bakin macijin nan, da bakin dabbar nan, da kuma bakin annabin nan na ƙarya, 14 su iskoki ne, aljannu masu yin abubuwan al'ajabi, masu zuwa wurin sarakunan duniya duka, don su tara su saboda yaƙi a babbar ranar nan ta Allah Maɗaukaki. 15 (“Ga ni nan a tafe kamar ɓarawo! Albarka tā tabbata ga wanda yake a zaune a faɗake, yana a saye da tufafinsa, don kada ya tafi tsirara, a ga tsiraicinsa.”) 16 Sai suka tattara su a wurin da ake kira Armageddon da Yahudanci. 17 Mala'ika na bakwai ya juye abin da yake a tasarsa a sararin sama, sai aka ji wata murya mai ƙara daga Haikali, wato, daga kursiyin, ta ce, “An gama!” 18 Sai aka yi ta walƙiya, da ƙararraki masu tsanani, da aradu, da wata babbar rawar ƙasa irin wadda ba a taɓa yi ba, tun da ɗan adam yake a duniya, gawurtacciyar rawar ƙasa ƙwarai da gaske. 19 Babban birnin nan kuwa ya rabu gida uku, biranen al'ummai kuma suka fāɗi. Sai Allah ya tuna da Babila mai girma, don ya sa ta, ta sha fushinsa mai tsananin gaske. 20 Kowane tsibiri ya ɓace, manyan duwatsu ma ba a ƙara ganinsu ba. 21 Waɗansu manyan ƙanƙara kuma kamar kayan jaki suka faɗo a kan mutane daga sama, har mutane suka zagi Allah, saboda bala'in ƙanƙarar. Bala'in nan da matuƙar bantsoro yake!

Wahayin 17

Hukunta Babbar Karuwar

1 Sai ɗaya daga cikin mala'ikun nan bakwai masu tasoshin nan bakwai, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka hukuncin da za a yi wa babbar karuwar nan, wadda take zaune a bisa ruwa mai yawa, 2 wadda sarakunan duniya suka yi fasikanci da ita, wadda kuma mazaunan duniya suka jarabtu da yin fasikanci da ita.” 3 Sai ya ɗauke ni ya tafi da ni zuwa jeji, Ruhu yana iza ni, sai na ga wata mace a kan wata dabba ja wur, duk jikin dabbar sunayen saɓo ne, tana kuma da kawuna bakwai, da ƙaho goma. 4 Matar kuwa tana a saye da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma ja wur, ta ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu'ulu'u, tana a riƙe da ƙoƙon zinariya a hannunta, cike da abubuwan ƙyama, da ƙazantar fasikancinta. 5 A goshinta kuma an rubuta wani sunan asiri, “Babila mai girma, uwar karuwai, uwar abubuwa masu banƙyama na duniya.” 6 Sai na ga matar ta bugu da jinin tsarkaka, da kuma jinin mashaidan Yesu. Da na gan ta, sai na yi mamaki ƙwarai da gaske. 7 Amma mala'ikan ya ce mini, “Don me kake mamaki? Zan buɗa maka asirin matar nan, da kuma na dabbar nan mai kawuna bakwai, da ƙaho goma, da take ɗauke da ita. 8 Dabbar nan da ka gani, wadda dā take nan, a yanzu kuwa ba ta, za ta hawo ne gaga ramin mahallaka, ta je ta hallaka, mazaunan duniya kuma waɗanda tun a farkon duniya, ba a rubuta sunayensu a Littafin Rai ba, za su yi mamakin ganin dabbar, don dā tana nan, a yanzu ba ta, za ta kuma dawo. 9 Fahimtar wannan abu kuwa, sai a game da hikima. Wato, kawuna bakwai ɗin nan tuddai ne guda bakwai, waɗanda matar take a zaune a kai. 10 Har wa yau kuma, sarakuna ne guda bakwai, waɗanda biyar daga cikinsu aka tuɓe, ɗaya yana nan, ɗayan bai zo ba tukuna, sa'ad da ya zo kuwa, lalle zamaninsa na lokaci kaɗan ne kawai. 11 Dabbar da take nan dā, a yanzu kuwa ba ta, ita ce ta takwas, daga cikin bakwai ɗin nan kuma ta fito, za ta kuwa hallaka. 12 Ƙahonin nan goma kuwa da ka gani, sarakuna goma ne, waɗanda ba a naɗa ba tukuna, amma sa'a ɗaya tak, za a ba su ikon yin mulki tare da dabbar. 13 Waɗannan ra'ayinsu ɗaya ne, za su kuma bai wa dabbar nan ikonsu da sarautarsu. 14 Za su yi yaƙi da Ɗan Ragon, Ɗan Ragon kuwa zai cinye su, shi da waɗanda suke tare da shi, kirayayyu, zaɓaɓɓu, amintattu, domin shi ne Ubangijin iyayengiji.” 15 Sai mala'ikan nan ya ce mini, “Ruwan nan da ka gani, a inda karuwar nan take a zaune, jama'a ce iri iri, da taro masu yawa, da al'ummai, da harsuna. 16 Ƙahonin nan goma kuma da ka gani, wato, su da dabbar nan za su ƙi karuwar, su washe ta, su tsiraita ta, su ci namanta, su ƙone ta, 17 domin Allah ya nufe su da zartar da nufinsa, su zama masu ra'ayi ɗaya, su bai wa dabbar nan, mulkinsu, har an cika Maganar Allah. 18 Matar nan da ka gani kuwa, ita ce babban birnin da yake mulkin sarakunan duniya.”

Wahayin 18

Faɗuwar Babila Mai Girma

1 Bayan haka, na ga wani mala'ika yana saukowa daga Sama, mai iko da yawa, sai aka haskaka duniya da ɗaukakarsa. 2 Sai ya yi kira da murya mai ƙarfi, ya ce, “Ta fāɗi! Babila mai girma ta fāɗi! Ta zama mazaunin aljannu, Matattarar kowane baƙin aljani, Da kowane irin ƙazamin tsuntsu, abin ƙyama. 3 Dukkan al'ummai sun yi tsananin jarabar yin fasikanci da ita, Sarakunan duniya kuma sun yi fasikanci da ita, Attajiran duniya kuma sun arzuta da almubazzarancinta.” 4 Sai na ji wata murya daga Sama, tana cewa, “Ku fito daga cikinta, ya ku jama'ata, Kada zunubanta su shafe ku, Kada bala'inta ya taɓa ku. 5 Domin zunubanta sun yi tsororuwa, sun kai har Sama, Allah kuwa ya tuna da laifofinta. 6 Ku saka mata daidai da yadda ta yi, Ku biya ta ninkin ayyukanta, Ku dama mata biyun abin da ta dama muku. 7 Yadda ta ɗaukaka kanta, ta yi almubazzaranci, Haka ku ma ku saka mata da azaba, da baƙin ciki gwargwadon haka. Tun da yake a birnin zuciyarta ta ce, ‘Ni sarauniya ce, a zaune nake, Ni ba gwauruwa ba ce, Ba ni da baƙin ciki kuma har abada!’ 8 Saboda haka, bala'inta zai aukar mata rana ɗaya, Mutuwa, da baƙin ciki, da yunwa. Za a kuma ƙone ta, Domin Ubangiji Allah da yake hukunta ta Mai Ƙarfi ne.” 9 Sarakunan duniya kuma da suka yi fasikanci da zaman almubazzaranci da ita, za su yi mata kuka da kururuwa, in sun ga hayaƙin ƙunarta, 10 za su tsaya a can nesa, don tsoron azabarta, su ce, “Kaitonka! Kaitonka, ya kai babban birni! Ya kai birni mai ƙarfi, Babila! A sa'a ɗaya hukuncinka ya auko.” 11 Attajiran duniya kuma suna yi mata kuka suna baƙin ciki, tun da yake, ba mai ƙara sayen kayansu, 12 wato, zinariya, da azurfa, da duwatsun alfarma, da lu'ulu'u, da lallausan lilin, da hajja mai ruwan jar garura, da siliki, da jan alharini, da itacen ƙanshi iri iri, da kayan hauren giwa iri iri, da kayan da aka sassaƙa da itace mai tsada, da na tagulla, da na baƙin ƙarfe, da na dutse mai sheƙi, 13 da kirfa, da kayan yaji, da turaren wuta, da mur, da lubban, da ruwan inabi, da mai, da garin alkama, da alkama, da shanu, da tumaki, da dawaki, da kekunan doki, da kuma bayi, wato, rayukan 'yan adam. 14 “Amfanin da kika ƙwallafa rai a kai, har ya kuɓuce miki, Kayan annashuwarki da na adonki sun ɓace miki, ba kuwa za a ƙara samunsu ba har abada!” 15 Attajiran waɗannan hajjoji da suka arzuta a game da ita, za su tsaya a can nesa don tsoron azabarta, suna kuka, suna baƙin ciki, suna cewa, 16 “Kaito! Kaiton babban birnin nan! Wanda dā ya sa lallausan lilin, da tufafi masu ruwan jar garura, da kuma jan alharini, Wanda ya ci ado da kayan zinariya, da duwatsun alfarma, da lu'ulu'u! 17 Domin a sa'a ɗaya duk ɗumbun dukiyar nan ta hallaka.” Sai duk masu jiragen ruwa, da masu shiga, da masu tuƙi, da duk waɗanda cinikinsu ya gamu da bahar, suka tsaya a can nesa, 18 suna kururuwa da suka ga hayaƙin ƙunarsa, suna cewa, “Wane birni ne ya yi kama da babban birnin nan?” 19 Har suka tula wa kansu ƙasa suna ta kuka, suna baƙin ciki, suna kururuwa, suna cewa, “Kaito! Kaiton babban birnin nan! Wanda duk masu jiragen ruwa a bahar suka arzuta da ɗumbun dukiyarsa, A sa'a ɗaya ya hallaka. 20 Ki yi farin ciki saboda an yi masa haka, ya sama! Ku yi farin ciki, ku tsarkaka da manzanni da annabawa, domin Allah ya rama muku abin da ya yi muku!” 21 Sai wani ƙaƙƙarfan mala'ika ya ɗauki wani dutse kamar babban dutsen niƙa, ya jefa a teku, ya ce, “Haka za a fyaɗa Babila babban birni, da ƙarfi, ba kuwa za a ƙara ganinta ba. 22 Ba za a ƙara jin kiɗan masu molo, da mawaƙa, da masu sarewa, da masu bushe-bushe a cikinki ba, Ba kuma za a ƙara ganin mai kowace irin sana'a a cikinki ba, Ba kuma za a ƙara jin niƙa a cikinki ba, 23 Fitila ba za ta ƙara haskakawa a cikinki ba, Ba kuma za a ƙara jin muryar ango da amarya a cikinki ba, Don attajiranki, dā su ne ƙusoshin duniya, An kuma yaudari dukkan al'ummai da sihirinki. 24 Har an tarar hakkin jinin annabawa da na tsarkaka suna a wuyanta, da kuma na duk waɗanda aka kashe a duniya.”

Wahayin 19

1 Bayan wannan na ji kamar wata sowa mai ƙarfi ta ƙasaitaccen taro a Sama, suna cewa, “Halleluya! Yin ceto, da ɗaukaka, da iko, sun tabbata ga Allahnmu, 2 Don hukuncinsa daidai yake, na adalci ne, Ya hukunta babbar karuwar nan wadda ta ɓata duniya da fasikancinta, Ya kuma ɗauki fansar jinin bayinsa a kanta.” 3 Sai suka sāke yin sowa, suna cewa, “Halleluya! Hayaƙinta yana tashi har abada abadin.” 4 Sai dattawan nan ashirin da huɗu, da rayayyun halittan nan huɗu, suka fāɗi suka yi wa Allah sujada, shi da yake zaune a kan kursiyin, suna cewa, “Amin. Halleluya!” 5 Sai aka ji wata murya daga kursiyin, tana cewa, “Ku yabi Allahnmu, ya ku bayinsa, Ku da kuke jin tsoronsa, yaro da babba.”

Bikin Auren Ɗan Rago

6 Sai na ji kamar wata sowar ƙasaitaccen taro, kamar ƙugin ruwa mai gudu, kamar aradu mai ƙara, suna cewa, “Halleluya! Gama Ubangiji Allahnmu Maɗaukaki shi ne yake mulki. 7 Mu yi ta murna da farin ciki matuƙa, Mu kuma ɗaukaka shi, Domin bikin Ɗan Ragon nan ya zo, Amaryarsa kuma ta kintsa. 8 An yardar mata ta sa tufafin lallausan lilin mai ɗaukar ido, mai tsabta.” Lallausan lilin ɗin nan, shi ne aikin adalci na tsarkaka. 9 Sai mala'ikan ya ce mini, “Rubuta wannan, ‘Albarka tā tabbata ga waɗanda aka gayyata, zuwa cin abincin bikin Ɗan Ragon nan.’ ” Ya kuma ce mini, “Wannan ita ce Maganar Allah ta gaskiya.” 10 Sai na fāɗi a gabansa, don in yi masa sujada, amma, sai ya ce mini, “Ko kusa kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da 'yan'uwanka, waɗanda suke shaidar Yesu. Allah za ke yi wa sujada.” Domin gaskiyar da Yesu ya bayyana ita ce ta ba da ikon yin annabci.

Mahayin Farin Doki

11 Sai na ga sama ta dāre, sai ga wani farin doki! Mahayinsa kuwa ana ce da shi Amintacce, Mai Gaskiya, yana hukunci da adalci, yana kuma yaƙi. 12 Idanunsa kamar harshen wuta suke, kansa da kambi da yawa, yana kuma da wani suna a rubuce, wanda ba wanda ya sani sai shi. 13 Yana a saye da riga wadda aka tsoma a jini, sunan da ake kiransa da shi kuma, shi ne Kalman Allah. 14 Rundunonin Sama, a saye da lallausan lilin fari mai tsabta, suna a biye da shi a kan fararen dawakai. 15 Daga cikin bakinsa wani kakkaifan takobi yake fitowa, wanda zai sare al'ummai da shi, zai kuwa mallake su da tsanani ƙwarai, zai tattake mamatsar inabi, ta tsananin fushin Allah Maɗaukaki. 16 Da wani suna a rubuce a jikin rigarsa, har daidai cinyarsa, wato Sarkin sarakuna, Ubangijin iyayengiji. 17 Sa'an nan na ga wani mala'ika tsaye a jikin rana. Sai kuma ya kira dukkan tsuntsaye da suke tashi a sararin sama, da murya mai ƙarfi, ya ce, “Ku zo, ku taru wurin babban bikin nan na Allah, 18 ku ci naman sarakuna, da naman sarakunan yaƙi, da naman ƙarfafa, da naman dawakai, da na mahayansu, da naman kowa da kowa, wato, na ɗa da na bawa, na yaro da na babba.” 19 Sai na ga dabbar nan, da sarakunan duniya, da rundunoninsu, sun taru, don su yaƙi wanda yake kan dokin, da kuma rundunarsa. 20 Sai aka kama dabbar, da kuma annabin nan na ƙarya tare da ita, wanda ya yi al'ajabai a gabanta, waɗanda da su ne ya yaudari waɗanda suka yarda a yi musu alamar dabbar nan, da kuma waɗanda suka yi wa siffarta sujada. Waɗannan biyu kuwa aka jefa su da ransu a cikin tafkin wuta da ƙibiritu. 21 Sauran kuwa aka sare su da takobin wanda yake a kan doki, wato, da takobin nan da yake fitowa daga cikin bakinsa. Dukan tsuntsaye kuwa suka ci namansu har suka yi gamba.

Wahayin 20

Shekara Dubu

1 Sa'an nan na ga wani mala'ika yana saukowa daga Sama, yana a riƙe da mabuɗin mahallaka, da kuma wata babbar sarƙa a hannunsa. 2 Sai ya kama macijin nan, wato, macijin nan na tun dā dā, wanda yake shi ne Ibilis, shi ne kuma Shaiɗan, ya ɗaure shi har shekara dubu, 3 ya jefa shi mahallakar, ya rufe, ya kuma yimƙe ta da hatimi, don kada ya ƙara yaudarar al'ummai, har dai shekarun nan dubu su ƙare. Bayan wannan lalle ne a sake shi zuwa ɗan lokaci kaɗan. 4 Sa'an nan na ga kursiyai, da waɗanda aka bai wa ikon hukunci, zaune a kai. Har wa yau, kuma na ga rayukan waɗanda aka fille wa kai saboda shaidar da suka yi wa Yesu, da kuma Maganar Allah, ba su kuwa yi wa dabbar nan da siffarta sujada ba, ba su kuma yarda a yi musu alamarta a goshinsu ko a hannunsu ba, sun sāke rayuwa, sun yi mulki tare da Almasihu har shekara dubu. 5 Sauran matattu kuwa, ba su sāke rayuwa ba, sai bayan da shekaran nan dubu suka cika. Wannan fa shi ne tashin matattu na farko. 6 Duk wanda yake da rabo a tashin nan na farko, mai albarka ne, tsattsarka ne. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kan irin waɗannan, amma za su zama firistocin Allah da na Almasihu, su kuma yi mulki tare da shi har shekara dubu. 7 Bayan shekaran nan dubu sun ƙare, sai a saki Shaiɗan daga ɗaurinsa, 8 ya kuma fito ya yaudari al'ummai waɗanda suke kusurwoyin nan huɗu na duniya, wato, Gog da Magog, ya tattara su saboda yaƙi, yawansu kamar yashin teku. 9 Sai kuma su bazu, su mamaye duk duniya, su yi wa sansanin tsarkaka da ƙaunataccen birni ƙawanya, sai wuta ta zubo daga sama ta lashe su. 10 Shi kuwa Ibilis mayaudarinsu, sai da aka jefa shi a tafkin wuta da ƙibiritu, a inda dabbar nan da annabin nan na ƙarya suke, za a kuma gwada musu azaba dare da rana har abada abadin.

Ranar Shari'a a gaban Babban Farin Kursiyi

11 Sa'an nan na ga wani babban kursiyi fari, da wanda yake a zaune a kai, sai sama da ƙasa suka guje wa Zatinsa, suka ɓace. 12 Sai na ga matattu manya da yara, a tsaitsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Sai kuma aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne Littafin Rai. Aka kuwa yi wa matattu shari'a bisa ga abin da yake a rubuce a cikin littattafan, gwargwadon aikin da suka yi. 13 Sai teku ta ba da matattun da suke a cikinta, mutuwa da Hades kuma sun ba da matattun da suke a gare su, aka kuwa yi wa kowa shari'a gwargwadon aikin da ya yi. 14 Sa'an nan aka jefa mutuwa da Hades a tafkin nan na wuta. Wannan ita ce mutuwa ta biyu, wato, tafkin wuta. 15 Duk wanda ba a sami sunansa a rubuuce a Littafin Rai ba, sai a jefa shi a tafkin nan na wuta.

Wahayin 21

Sabuwar Sama da Sabuwar Ƙasa

1 Sa'an nan na ga sabuwar sama da sabuwar ƙasa, don sama ta farko da ƙasa ta farko sun shuɗe, ba kuma sauran teku. 2 Sai na ga tsattsarkan birni kuma, Sabuwar Urushalima, tana saukowa daga Sama daga wurin Allah, shiryayyiya kamar amaryar da ta yi ado saboda mijinta. 3 Na kuma ji wata murya mai ƙara daga kursiyin, tana cewa, “Kun ga, mazaunin Allah na tare da mutane. Zai zauna tare da su, za su zama jama'arsa, Allah kuma shi kansa zai kasance tare da su, 4 zai share musu dukkan hawaye. Ba kuma sauran mutuwa, ko baƙin ciki, ko kuka, ko azaba, don abubuwan dā sun wuce.” 5 Sai na zaune a kan kursiyin ya ce, “Kun ga, ina yin kome sabo.” Ya kuma ce, “Rubuta wannan, domin maganar nan tabbatacciya ce, gaskiya ce kuma.” 6 Sai ya ce mini, “An gama! Ni ne Alfa, Ni ne Omega, Ni ne na Farko, Ni ne kuma na Ƙarshe. Duk mai jin ƙishirwa zan ba shi ruwa daga maɓuɓɓugar ruwan rai kyauta. 7 Duk wanda ya ci nasara, zai ci wannan gādo, wato, in zama Allahnsa, shi kuma ya zama ɗa a gare ni. 8 Amma matsorata, da marasa riƙon amana, da masu aikin ƙyama, da masu kisankai, da fasikai, da masu sihiri, da masu bautar gumaka, da kuma duk maƙaryata, duk rabonsu tafkin nan ne mai cin wuta da kibiritu, wanda yake shi ne mutuwa ta biyu.”

Sabuwar Urushalima

9 Sai kuma ɗaya daga cikin mala'ikun nan bakwai, masu tasoshin nan bakwai, cike da bala'i bakwai na ƙarshe, ya zo ya yi mini magana, ya ce, “Zo in nuna maka amarya, matar Ɗan Ragon.” 10 Sai ya ɗauke ni, Ruhu yana iza ni, ya kai ni wani babban dutse mai tsawo, ya nuna mini tsattsarkan birnin Urushalima yana saukowa daga Sama daga wurin Allah, 11 yana tare da ɗaukakar Allah. Hasken birnin yana ƙyalƙyali kamar wani irin nadirin dutse mai daraja, kamar yasfa, garau kamar ƙarau. 12 Yana da babban garu mai tsawo, da ƙofar gari goma sha biyu, a ƙofofi ɗin da akwai mala'iku goma sha biyu. A jikin ƙofofin kuma an rubuta sunayen kabilan nan goma sha biyu na Isra'ila, 13 a gabas, ƙofa uku, a yamma ƙofa uku, a kudu ƙofa uku, a arewa kuma ƙofa uku. 14 Garun birnin kuwa, tana da dutsen harsashi goma sha biyu, a jikinsu kuma an rubuta sunayen manzannin nan goma sha biyu na Ɗan Ragon. 15 Shi wanda ya yi mini magana kuwa yana da sandar awo ta zinariya, domin ya auna birnin, da ƙofofinsa, da garunsa. 16 Birnin murabba'i ne, tsawonsa da fāɗinsa duka ɗaya ne. Sai ya auna birnin da sandarsa, mil dubu da ɗari biyar, tsawonsa, da fāɗinsa da zacinsa, duka ɗaya suke. 17 Ya kuma auna garunsa, kamu ɗari da arba'in da huɗu ne na mutum, wato, na mala'ika ke nan. 18 Garun kuwa da yasfa aka gina shi, birnin kuma da zinariya zalla, garau kamar ƙarau. 19 An kuma ƙawata harsasen garun birnin da kowane irin dutse mai daraja. Yasfa shi ne na farko, na biyu saffir, na uku agat, na huɗu zumurrudu, 20 na biyar onis, na shida yaƙutu, na bakwai kirisolat, na takwas beril, na tara tofaz, na goma kirisofaras, na sha ɗaya yakinta, na sha biyu kuma ametis. 21 Ƙofofin gari goma sha biyun nan kuwa lu'ulu'u ne goma sha biyun, kowace ƙofa da lu'ulu'u guda aka yi ta, hanyar birnin kuwa zinariya ce zalla garau kamar ƙarau. 22 Ban kuwa ga wani Haikali a birnin ba, domin Haikalinsa Ubangiji Allah Maɗaukaki ne, da kuma Ɗan Ragon. 23 Birnin kuwa ba ya bukatar rana ko wata su haskaka shi, domin ɗaukakar Allah ita ce haskensa, Ɗan Ragon kuma fitilarsa. 24 Da haskensa al'ummai za su yi tafiya. Sarakunan duniya za su kawo darajarsu a gare shi. 25 Ƙofofinsa kuwa ba za a rufe su da rana ba har abada, ba kuwa za a yi dare a can ba. 26 Za a kuma kawo darajar al'ummai da girmansu a gare shi. 27 Amma ko kaɗan ba wani abu marar tsarki da zai shiga cikinsa, ko wani mai aikata abin ƙyama ko ƙarya, sai dai waɗanda aka rubuta sunayensu a Littafin Rai na Ɗan Ragon kaɗai.

Wahayin 22

1 Sa'an nan, sai ya nuna mini kogin ruwan rai, yana ƙyalli kamar ƙarau, yana gudana daga kursiyin Allah, shi da Ɗan Rago, 2 ta tsakiyar hanyar birnin kuma, ta kowane gefen kogin, akwai itatuwan rai masu haihuwar 'ya'ya iri goma sha biyu, kowane wata suna haihuwa, ganyen itatuwan kuwa saboda lafiyar al'ummai ne. 3 Ba sauran wani abin la'antarwa, amma kursiyin Allah, shi da Ɗan Rago, zai kasance a cikinsa. Bayinsa za su bauta masa, 4 za su kuma ga fuskarsa, sunansa kuwa zai kasance a goshinsu. 5 Ba za a ƙara yin dare ba, ba za su bukaci hasken fitila, ko na rana ba, domin Ubangiji Allah zai haskaka su, za su kuma sha ni'imar Mulki har abada abadin.

Yesu yana Zuwa da Wuri

6 Sai ya ce mini, “Wannan magana tabbatacciya ce, ta gaskiya ce kuma. Ubangiji, Allahn ruhohin annabawa ya aiko mala'ikansa, ya nuna wa bayinsa abin da lalle ne zai auku ba da daɗewa ba.” 7 “Ga shi kuwa, ina zuwa da wuri. Albarka tā tabbata ga wanda yake kiyaye maganar annabcin littafin nan.” 8 Ni Yahaya, ni ne na ji, na kuma ga waɗannan abubuwa. Sa'ad da kuwa na ji su, na kuma gan su, sai na fāɗi a gaban mala'ikan da ya nuna mini su, domin in yi masa sujada. 9 Amma, sai ya ce mini, “Ko kusa kada ka yi haka! Ni abokin bautarku ne, kai da 'yan'uwanka annabawa, da kuma waɗanda suke kiyaye maganar littafin nan. Allah za ka yi wa sujada.” 10 Ya kuma ce mini, “Kada ka rufe maganar annabcin littafin nan, domin lokaci ya kusa. 11 Marar gaskiya yă yi ta rashin gaskiyarsa, fajiri kuwa yă yi ta fajircinsa, adali kuwa yă yi ta aikata adalcinsa, wanda yake tsattsarka kuwa ya yi ta zamansa na tsarki.” 12 “Ga shi, ina zuwa da wuri, tare da sakamakon da zan yi wa kowa gwargwadon abin da ya yi. 13 Ni ne Alfa, Ni ne Omega, Ni ne na Farko, Ni ne na Ƙarshe.” 14 Albarka tā tabbata ga masu wanke rigunansu, domin su sami izinin ɗiba daga itacen rai, su kuma shiga birnin ta ƙofa. 15 Waɗanda aka hana shiga birnin kuwa, su ne fajirai, da masu sihiri, da fasikai, da masu kisankai, da masu bautar gumaka, da kuma duk wanda yake son ƙarya, yake kuma yinta. 16 “Ni Yesu, na aiko mala'ikana a gare ka, da wannan shaida saboda ikilisiyoyi. Ni ne tsatson Dawuda, da zuriyarsa, Gamzaki mai haske.” 17 Ruhu da amarya suna cewa, “Zo.” Duk wanda ya ji kuwa, yă ce, “Zo.” Duk mai jin ƙishirwa ya zo, duk mai bukata, yă ɗibi ruwan rai kyauta. 18 Ina yi wa duk mai jin maganar annabcin littafin nan kashedi, in wani ya yi wani ƙari a kanta, Allah zai ƙara masa bala'in da aka rubuta a littafin nan. 19 In kuma wani ya yi ragi a maganar littafin annabcin nan, Allah zai ɗauke rabonsa na itacen rai, da na tsattsarkan birnin, waɗanda aka rubuta a littafin nan. 20 Shi wanda ya shaida abubuwan nan ya ce, “Hakika, ina zuwa da wuri.” Amin! Zo, ya Ubangiji Yesu. 21 Alherin Ubangiji Yesu yă tabbata ga dukkan tsarkaka. Amin!